Author : Halima K Mashi Category : Complete Novels
ai daɗin ji ne da shi. Ya bita da kallo,wato ita bata san ma ta mishi laifi ba,bare ta bashi haƙuri ko ta mishi bayani shi ne ta zo tana tuhumar shi,ya samu labarin ta saida motar da ya siya ma su Safiya da Suwaiba, domin wanda ya gyara motar ne yake sanar dashi lokacin da ya je ɗaukar tashi motar. Da be ga ta su Suwaibar ba yace sun zo sun ɗauka ne? Sai yaron mai gyaran motar ya ce, a'a wani ne yazo ya ɗauka, kuma ya gaya mishi cewa Babanshi ne ya sayi motar. Alhaji Saddiƙ shi dai alwashi ya sha ba zai ƙara sai wa yaran koda mashin ba.
Hajiya Jummai ta kalli Hajiya Kari.
"To kin ji yanda muka ƙwashe da Alhaji,babu abinda ya fi bani haushi wai har an kai lefe bani da labari saboda rainin hankali, ke kayan faɗar kishiya ma shi ya siyo min, saboda haka ina son mu koma gurin Boka, gashi bakon ya ce in biki ya rage ƙwana goma in koma,to gashi yau sauran ƙwana taƙwas. Tunda jiya tara ya ce min ne ko nawa ne ma oho."
Hajiya Kari ta ce, "To gobe sai mu je,in ce dai kin binne abin da ya baki?" Ta ce "ina fa ni ban fa san taƙamaiman lokacin ba sai jiya,na san zai kama zigar waɗannan ƴan iskan ƙannan nashi ne" Hajiya Kari ta ce "Bari mu gama da amaryar, har su ba za'a barsu haka ba, sai mu shiga tsakaninsu." Hajiya Jummai ta ce, "Da ko kin taimaka min,ba ma dai irin tsinanniyar Nafisan nan, gashi yafi ji da ita duk cikin su."
Ta binne surkullen da aka bata,ta kuma yayyafa na yayyafawa kamar yadda aka umarce ta. Sannan ta nutsu don tana son samun kuɗi a hannunshi, duk da wannan karon ya tsuke mata bakin aljihunshi, ta samu dai-dai gwargwado.
Lokaci na ta zuwa gida kam ya sha fenti da gyara, yanda ya ba ta kuɗin canjin kayan ɗaki, haka ya ba su Fatima da Sadiya da Nafisa kuɗi su siyo na ɗakin A'isha, sannan shima nashi gefen sai da ya canza komai. Nan fa ta tada balli kan cewa shin wannan amaryar ta fi sauran ne yake ta faman kashe kuɗi har da sa mata kayan ɗaki? To ba zai yiwu ba,ya ce Jummai ki daina tada jijiyar wuyanki akan abinda ba za ki hana ba,yarinyar nan ko ba ni ne zan aureta ba kusan dole ne in mata kayan ɗaki, ballantana gidana za'a sa,kina cewa ba zata yiwu ba,za ki hana ne? Kema fa na baki haƙƙinki."
Su Hajiya Karima ne suka tausasheta da cewa yarinyar da ba mazauniya ba ki ke damun kanki? Gawa ce fa.
Ita ko A'isha, amarya duk ta gama sukurkucewa,iyayanta ma suna daurewa ne kurum,tuni ƴan'uwa da abokan arziki sun cika gida don yin biki.
Ranar ɗaurin aure ta kasance asabar,don haka ƴan ango sun iso juma'a domin ana gama ɗaurin aure za'a ɗauki hanya da amarya. Alhaji Saddiƙ ya kasa zuwa ɗaurin auren,waya ya yi wa Friend ɗin shi kan cewa ba zai samu zuwa ba,don ba ya jin daɗi. Lafiyar shi lau sai dai yana ganin kamar za'ayi ta nuna shi,ko kuma Friend ya shaidama ƴan'uwanshi halin da ake ciki,ko su iyayan in sun ganshi su dinga mishi kallon wanda zai yi musu sanadin ƴarsu da dai sauran tunani kala-kala.
Daren juma'a aka sanya amarya a lalle,ba ta saka kowace ƙawa ba, sai dai ƴaƴan ƴan'uwa sa'anninta. Da dare suna ƙwance a kan katifa zuciyar A'isha cike da tunanin gobe zata rabu da Ummanta da Abbanta,ƙila ma rabuwar kenan. Hawaye ne suke bin gefen kumatunta, wayarta tana ta ruri. Naja ta ce Amarya wayar ki na neman agaji, A'isha tasa hannunta ta lalubo wayar,muryarta a dusashe ta ɗaga wayar tare da cewa "Assalamu alaikum, Nafisa ce?" Ta ce "amaryar mu,na so in zo ban samu zuwa ba, sai dai in kin zo gobe mun haɗu, " ta ce "to ina yini ya ya su Hajiya? Nafisa ta ce, kowa lafiya, gama Hajiya nan,sai dai nasan ba zata ɗaga wayar ki ba saboda Brother ɗinmu ɗan fari ne,tana mishi kara.
A'isha ta ce,to ki gaida ta,ta ce to ga Uncle ɗin naki dama yazo ne nace ya kira min ke gobe. Ta ɗan yi ƙasa da murya kada ki manta da addu'o'i daren yau, saboda Allah ya yi mana jagora a cikin ɗaurin auren da za'ayi a gobe. Shiru kawai A'isha ta yi mata, sai kawai ta ji Muryar Uncle yana cewa, Beby kina jina? Ta ce eh, zuciyarta kuwa sake karyewa ta yi hawaye ya shiga sintiri a kumatunta, ya ce na kasa zuwa ne Beby sai ina ganin tamkar ban yi wa mahaifin ki adalci ba, ina jin nauyinsu, kukan da take maƙalewa ya kufce mata, ranshi ya daɗa tsinkewa, ya ce "A'isha kiyi haƙuri daina kukan zan yi miki magana ne," ta share hawayen ta sannan ta yi ƙoƙarin tsaida kukan ta ce, ina jin ka, ya ce ina son ki tashi daga wannan kukan ne kiyi alwala, nafila za kiyi tare da addu'o'i kin ji ko? Alkhairin da ke tare da auren,ki tsaida zuciyarki,ki daina wasi-wasi,ki saka a cikin ranki cewa duk yanda Ubangiji ya yi dake dai-dai ne,kin amince?" Ta ce "Uncle dama ni bani da wani zaɓi sai wanda Allah ya yi min, sannan zan yi duk yanda kace." Ya ce yauwa Beby sai da safe.
Tsam,ta miƙe,Naja ta bita da kallo,ta shige (toilet) ta ɗauro alwala.
Naja ta dube ta, Angon yayi lallashi kenan mu ko munyi mun gaji kin ƙi kiyi shiru? Ɗan murmushi ta yi sannan ta ce,Naja kenan ba zaki gane ba ne, sannan ta tada sallah. Sai ya kasance wannan dare duk wanda yasan halin da ake ciki tsakanin Katsina da Jigawa idanunshi biyu ya kwana, kuma tsaye gaban Ubangiji, ana ta kai kuka. Zuwa wayewar gari kowa ya tattara komai ya miƙa wa Allah, sai sauraro duk sun nutsu da cewa duk abinda Allah ya yi daidai ne.
A'isha kam sai ta wayi gari zuciyarta sake duk ƙuncin da take ji ya washe, sai dai ɗan abinda ba za'a rasa ba. Hakan ya yiwa Umma daɗi har ta isko Abba cikin ɗakinshi,tana shaida mishi cewa...
____________________________
*📗MUMMUNAN ZATO📗*
*NA*
*HALIMA ABDULLAHI K/MASHI*
*Ɗandano page 11*
*ƘARSHEN FREE PAGES*
*Alhamdulillah ƙarfe free Pages kenan idan baki siya ba kiyi ƙoƙari ki mallaki naki akan farashin masu son DOCUMENT book 1&2&3 Complete ₦600,masu son PAGES ₦400 idan kuna bukata zaku turo kudin ku ta wannan account number👇🏻*
```1632036584
Sa'adatu Balarabe
Access Bank,a turo shaidar biya ta 09068032427 wancan account ɗin namu ya samu matsala ne, idan mun gyara zamu dawo dashi```
*Ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427 idan baki shirya siya ba ki bari sai kin shirya sai kiyi magana*
Shaida mishi cewa yau kam A'isha ta saki ranta,suna cikin zantawa sai ko ga A'isha ta yi sallama domin gaida Abbanta, bayan ta gaisheni ne ya ce "yauwa ƙawar Ummanta dama ina son in kira ki domin inyi miki nasiha duk da cewa tun da bikin nan ya matso muna tayi miki,na farko dai nasihar da zan miki ita ce, zaman aure ya banbanta da zamanki na gida,don nan iyakaci kici abinci ki ƙwanta da dai sauransu. Yanzun kam da zaran an ɗaura aure Akwai wasu haƙƙoƙi guda goma da suka hau kanki na mijinki.
Na farko shine ki yi masa biyayya duk abinda ya ce kiyi,ki yi masa, matsawar bai saɓawa addini ba, kamar yanda ki ka sani babu biyayya ga abokin halitta don saɓawa mahalicci.
Kima zama mai tsafta kamar yanda ki ka ga Ummanki tana yi, tsafta bata jiki kurum ba har da muhallinki.
In kuma ya kira ki zuwa shinfiɗarshi kada ki bijire.
Ta dubi Abba da sauri kamar tana neman ƙarin bayani, domin A'isha yarinya ce sannan ba wai suna zama da ƙawayanta suna hirar samari ko ta aure ba ne,haka nan bata da wata ƙawa wadda ta yi aure ballantana ma taji labarin zaman auran, kazalika ita ba ma'abociyar karance-karance ba ce, ita ana ta zaton in an mata aure zata na girki tana kai ma mijin ruwan wanka tasa mishi na buta kamar yanda ta gani Ummanta tana yi, sai ko gyaran ɗakin Abbanta da Umman bata bari wani ya yi sai ita.
Abba ya katse mata tunani da cewa, ma'ana in ya neme ki kada ki guje shi, Umma ta ce,nima na miki duk nasihar da ta dace,na sani ke dama mai biyayya ce,ki girmama ƴan'uwansa,ki ɗauki mahaifiyarsa tamkar taki, haka mahaifinshi, matarsa ki yi mata biyayya."
Hawaye suna zuba daga idanunta, ta ce insha Allah zan yi Abba da Umma, suka sa mata albarka tare da yafe mata,ta miƙe ta fita suka bita da kallo cikin tausayin ta yayin da ita kuma ta wuce cikin tsananin damuwa.
Ƴan ɗaurin aure sun hallara in da aka ɗaura aure. Maroƙiya ta shigo tana rangaɗa guɗa, A'isha dai-dai lokacin tana wanka wanda Umma Rabi ta matsa mata ta yi umma Rabi ƙawar Ummanta ce,tun suna dutse tana fitowa ta ji gidan ya kaure da guɗa, duk sai taji wata fargaba a cikin zuciyarta. Inna Uwani Ƙanwar Umma, ita ta ciro mata wani leshi baƙi mai ado, ruwan lemon zaki tasa ka,sun bata siket da bes da kuma pant duk baƙaƙe.
Aunty Hasiya mata ƙanin Abba ta ce ni ban ga ma rigar nono ba cikin kayan? Umma ta ce ba a saka ba, Umma Rabi ta ce to me za'a sakama ƙirjin ba komai, ita dai A'isha tana jin su, Ummanta ta ce kin ji saka kayanki ki tafi nan duk iyayan banza ne suka taru. Ta gama shirinta ta fita, bayan an ɗan natsa da gama ɗaurin aure sai kuma aka shiga shirin tafiya Katsina,kai amarya. Duk wanda ya cancanta ya yi wa amarya nasiha ya yi mata,dangin Uwa da na Uba. Idanu ta zuba ma Ummanta a zuciyarta tana raya cewa, ta yi wa mahaifiyarta kallon ƙarshe. Haka nan aka fita da ita tana ta rusa kuka.
Abbanta da sauran mutane suna waje gurin mota suna ta ce waɗanda zasu je Katsinan,don kowa yana son zuwa, kuma tafiya ta gari ba kusa ba,don haka suka ce dole ne wasu su haƙura ba kowa da kowane zasu je ba, an fito da ita tana cin kuka ganin Abbanta sai kuma ta ƙwace ta nufi gurinshi.
Ya riƙe mata hannu yana cewa haba menene haka kuma? Ganin yanda take rusa kuka har ma wasu daga cikin dangi suma sun soma taya ta, sai Abban ya kama hannunta ya ce,zo muje, ɗakinshi suka je ya zaunar da ita ya shiga lallashinta da cewa menene na damuwa bayan ta yi musu biyayya sannan ya san Friend ɗin shi zai kula da ita, zatayi karatun ta duka biyun, kuma suma da an ƙwana biyu za su zo shi da Ummanta. Ya miƙe ya ɗauko alƙur'ani izifi sittin da fiƙihu da Tauhidi ya ce ki riƙe wannan kin ji A'isha?" Ta share hawayenta tasa hannu biyu ta amsa tare da cewa , to Abba da gaske za kuzo? Ya ce in Allah ya so, tashi muje ga mutane can sun shiga mota ke dama ake jira. Allah ya yi miki albarka zan kira ki in kun isa,ta ce to. Abba da kanshi ya kai ta har mota inda ta zauna tsakiyar Inna Uwani da kuma Aunty Rabi matar ƙanin Abba. Suka nufi Katsina bayan ta yiwa gidan su kallon ƙarshe, tare da duban Abbanta da Yaya Abdulrahman Munnir da kuma Jafar.
Alhamdulillah ƙarfe free Pages kenan idan baki siya ba kiyi ƙoƙari ki mallaki naki akan farashin masu son DOCUMENT book 1&2&3 Complete ₦600,masu son PAGES ₦400 idan kuna bukata zaku turo kudin ku ta wannan account number👇🏻*
```1632036584
Sa'adatu Balarabe
Access Bank,a turo shaidar biya ta 09068032427 wancan account ɗin namu ya samu matsala ne, idan mun gyara zamu dawo dashi```
*Ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427 idan baki shirya siya ba ki bari sai kin shirya sai kiyi magana*
[12/4, 20:23] Ummi Tandama😇: *📗 Page 12*
Can katsina kuwa, gidan Alhaji Saddiƙ yana cike da danginshi, na gefen Hajiya Jummai da kuma ƙawayanta. Amma shaƙiƙan ƴan'uwanshi irin su Fatima, gidansu Hajiyarmu suke yin bikin su. Kuma a nan suka yi girkin saukar amarya domin suna isowa direbobin zasu kira su a waya kamar yanda suka shedawa direbobin.
Gefen Hajiya Jummai kuwa tana ɗaki tsakiyar aminanta suna ta tofin Ala tsine ga Alhaji Saddiƙ ɗin da ƴan'uwanshi da kuma amarya da danginta. Tuni suka sa ma amaryar suni mai ƙararran ƙwana.
Yamma ta yi sanda motar amarya ta iso, tunda suka shigo Katsina direbobin suka yi waya suka sanar da su Hajiyarmu. Nan take su Fatima Anty Sadiya su Nafisa da sauran dangi suka ciko mota da kuloli ɗauke da nau'ikan abinci kalolin abin sha, suka nufo gidan Brother ɗinsu. Suna shigowa kallo ya koma kan su nan dai aka je aka tsegun tama Hajiya Jummai ita da ƙawayenta suka fito falon suka shiga yada habaici, domin tsarin gidan ƙaton mahaukacin falo ne mai ɗauke da ɗakuna huɗu, falon ya shiryu da kalolin kujeru na alfarma gefe-gefe.
Kusan seti uku ban da (dinning), ɗakin Hajiya Jummai sai na su Suby sai ko na A'isha, yanzun ɗayan na baƙi ne, sai hanyar da zaka bi don zuwa gefen shi yanda ya shirya kujerun falon yana nufin kamar kowace mace da nata, domin kalar kujerunki kalar labulanki kuma suna daf da ɗakinki kayan kallonki kuma suna nan a gurin, domin tsakanin kowane ɗaki zuwa wani ɗaki da ɗan tazara. Akan kujerun A'isha suka zauna babu jimawa sai ga motocin amaryar sun iso,suka fito suka tari amarya,in da Nafisa taje ta rungumo A'isha tana cewa amaryarmu sannu da zuwa. Ta laluba kunnan A'isha tana cewa kada ki manta ki shiga gidanki da ƙafar dama tare da addu'o'i,kai A'isha ta ɗaga. Dama tun kafin su shigo gidan take zabga addu'o'i,suna shigowa sai wata cikin matan ta soma rangaɗa guɗa.
Hajiya Jummai ta miƙe zumbur tana haki,su Hajiya Karima suka riƙe ta tare da cewa,haba-haba Hajiya Jummai ai an wuce nan,me yasa ki ke tada hankalinki? Kada idanunki su rufe ki manta matsayinki, ta sauke huci, da zuwa zan yi in ɗauke matar da ta zabgo min wannan guɗar a cikin gidana da mari suka ce a'a Hajiya Karima ta jata cikin toilet me zai sa ki nuna kanki? Kada ki manta da zaran ya sadu da ita ta zama gawa kamar yanda yake faruwa da sauran matan,nuna musu faran-faran yanda za'a tafi ana yabonki,me yasa wannan karan duk ki ka kasa control ɗin kan ki ne?.
Ta dubi Hajiya Karima nima ba zan ce ga dalili ba, sai dai ina samun kaina da matsanancin Kishin yarinyar. Na tsane ta fiye da sauran kuma naga Alhaji ya fi nuna ɗokin aurenta fiye da sauran na baya. Hajiya Karima ta ce don Allah manta da kishin nan gawa ce fa, yanzu dai zo muje mu taryesu ki canza kayanki kiyi sabuwar shiga,mu rufa miki baya ki gaishe su kada ki nuna mata kishi don Allah, ta ce shikenan suka fito. Nan ko take ta zabga wani uban sun less mai shegiyar tsada, suka rufa mata baya zuwa ɗakin amarya.
Lokacin wasu suna sallah yayin da wasu ke cin abinci, A'isha dai lokacin tana zaune bakin gado. Nafisa tana kusa da ita tana waya, tamkar mutuniyar ƙwarai ta durƙusa tana gaishe su ƙawayanta ma suka gaishe su,ta ce ina ƙanwar tawa? Umma Rabi ta ce gata nan ta ƙudundune kai, Hajiya Jummai ta ce zamu ganki ne har mu gaji suka ce ƙwarai kuwa, Nafisa dai ko kallon ta batayi ba, amma don makirci har da cewa Hajiya Nafisa waton yau ana gurin amarya kenan ko?.
Nafisa ta gama waya amma sai ta cigaba da magana tamkar ba ta gama ba, don kada ma suyi magana da Hajiya Jummai. Suna fita kuwa su Umma Rabi suka soma yabonta kan cewa gaskiya wannan mata tana da kirki, Allah ya haɗa kansu. Nafisa dai bata ce komai ba,don ba wai suna zarginta da kisan matanshi ba ne, a'a shirine kawai basayi da ita,su kuwa suna komawa ɗaki Hajiya Karima ta ce,ni ban ga mutum ba a nan? Jummai ta ce,ai shine duk da tana rufe amma yarinya kamar ƴar kalan hanji? Wata da suke kira Hajjaju ta ce don rashin tausayin namiji sai fa ya ce zai neme ta ko? A, sosai ma, inji Hajiya Jummai, duk matan haka yake auro su amma ba ya ɗaga musu ƙafa, wannan ma ba zai kalleta ba,bugu da ƙari ma ni nafi son ya take ta. Hajiya Karima ta yi saurin ƙwabarta da cewa to ke dai ya isa zancan haka,mu dai Allah ya bada zaman haƙuri ki dai kauda kanki kawai,ta yi haka ne saboda wannan kashe-kashen sirrinsu ne sauran ƙawayan ba su sani ba. Nan take Jummai ta gano kuskuran da ta so tayi don haka sai suka shiga wani zancan.
A'isha tana zaune kan sallaya ta idar da sallar isha'i, Nafisa ta durƙusa ta ce sai da safe tunda kin ƙi cin komai sai dai zan faɗa ki da Uncle ɗin naki cewa tunda ki ka zo kin ƙi shan ko da ruwa ne.
A'isha ta dube ta,haba don Allah kar ki gaya masa. Umma Rabi ta ce ai gara dai ki sanar da shi ɗin. Nafisa ta fita tana cewa to sai da safenku, suka ce to ki gaida Hajiyarmu mun gode sosai,ta fita Inna Uwani ta ce yanzun A'isha haka za ki ƙwana da yinwa? Ta dube ta Allah Inna ni bana jin yunwa fa.
Hajiya Jummai ta shigo da sallama, fuskarta ɗauke da fara'a ta ce,sannunku, sannunku fa suka ce yauwa ta ce duk kun yi sallah kenan? Suka ce mun yi Hajiya. Ta ce,to bari a kawo muku abinci, suka ce wallahi duk mun ƙoshi,kin gan shi can ma wani ne ko buɗa shi bamu yi ba,ta ce to shikenan ku zo muje in kai ku masaukin baƙi,in ya so sai amaryar da ƙawayanta su