Mummunan Zato 1 Complete Hausa Novel

Author :  Halima K Mashi Category :  Complete Novels

Chapter   2 / 10

3K to 6K   out of 29.6K words

sannan ta ce " ba fa a yiwa ɗan adam saurin yarda,yanda mutanen duniya suka lalace da son kuɗi"

Ya aje cokalin hannun shi Sannan ya dube ina zaton na jima ina miki bayani halayen dattako tare da riƙe amanar da Friend ya ke da shi kar ki ji komai." Ta yatsina baki bata kuma magana ba,shi ko miƙewa ya yi don ya shiga ɗakinshi,ya warware gajiya. Yana shiga wayar shi ta soma tsuwwa,ya duba. Murmushi ya yi tare da ɗaga wayar.

"Friend na iso har na yi wanka, kuma na ci abinci yanzu ma ƙwanciya zan yi" a can Abba ya ce" to Alhamdulillah,na barka lafiya ka huta."



Umma ta dubeshi "Abban yara mene ne abin damuwa kan wannan? Ai abin murna ne sai muyi ma Allah godiya." Ya ce"haka ne Umman yara,ina tunanin amana ne,kin san amana tana da wahala,sai dai Allah ya taya mu riƙo" ta ce"Amin".

A'isha ta shigo da sallama ta zauna cike da fara'a,"Abba nagode da siyayya, gaskiya ban taɓa sa'ar samun guzurim zuwa makaranta kamar wannan ba." Ya yi murmushi,"Uncle ɗin ku ne ya ba da yace ai miki siyayya, " ta ce kai gaskiya Uncle akwai shi da kirki,ina jin tausayin shi gashi Allah be Baby ba" Umma ta ce"Allah zai ba shi insha Allahu" Abba ya miƙe domin zancan su ya yi mishi tuni ne da wani al'amari da ke gabanshi.


Zaune ya ke gaban Malam Dari,ya koro ma Malam Dari bayani kan matsalar abokin nashi,shi kan shi Malam Dari ya jinjina matsalar, sannan ya ce zai yi wasu bincike a kai, bayan ya tambayi sunan abokin Abba,ya ce mishi Alhaji Sadiƙ Usman,Malam Dari ya ce ka bani zuwa gobe ko dai ma jibi ka zo kaji batu,,ya miƙe bayan ya ajiye mishi dubu ɗaya, tare da faɗin "Ga sadaka" Malam Dari ya ce "to Allah ya karɓa,kuma ya shige mana gaba."sai na ganka" "to" inji Abba "sai na zo ɗin kenan."


___________________________
Ya yi parking a harabar gidan mahaifan nasa,ya fito ɗaukacin masu hidima a gidan suna ta isowa don gaishe shi,shi kuma ya shiga amsa musu ya shiga yi musu ihsani, kamar yadda ya saba, duk sanda ya zo, sannan kai tsaye ya nufi falon Hajiyar mu.

A zaune ya same ta kan kujera.Dirariya mace mai kyaun haiba, tare da taƙawa.tana da son addini,kana ganin ta ka san itace mahaifiyar Saddiƙ, tana taimako musamman asibitoci zuwa masallatai, cike da fara'a ya shiga ya zauna gabanta ita da shi suna yiwa juna kara nauyin shi kasancewar shi ɗan fari shi kuma bai shaƙu da ita ba,shi yasa ya ke jin nauyin ta, yanda ya zauna gabanta da ace akwai mutane a gurin tashi zatayi.

Ya dube ta, sannan ya sunkuyar da kai. "Ina kwana Hajiyar mu?"

Ta amsa da "lafiya lau, ashe ka dawo?" Ya ce"eh,na dawo jiya ban samu shigowa in duba ku jiyan ba, dafatan za ku min afuwa?" Ta dube sannan ta kauda kai, tunda dai an iso lafiya Alhamdulillah,ina kuma fatan tafiyar ta yi nasara?

Ya yi murmushi.

"Nasarori ma kuwa, domin bayan nasarar sayan kamfanin na haɗu da Aminina Mustapha Gumel, wanda ko yaushe ya ke raina." Ta dube shi tare da faɗin"ikon Allah! Lallai tafiya ta yi nasara, domin ba ta manta yanda koyaushe yake ɗalibta da batun Mustapha Gumel. Ya ce"Alhajinmu yana nan?" Ta kalli gefen ɗakinshi, "yana ciki amma yanzun zai fito."

rufe bakinta ya yi daidai da fitowar Alhajinmu,miƙewa tsaye ya yi tare da faɗin,"sannu da fitowa Alhajinmu" ya amsa da cewa"yauwa Abubakar Saddiƙ ,ka dawo lafiya" daidai sanda ya zauna,shima Saddiƙ ya zauna inda dama yake "lafiya lau kuma anyi nasara" ya shiga yi mishi bayanin yanda kamfanin yake girmanshi zuwa kyan injinanshi tare da gyare-gyaren da za a yi, sannan ya bashi labarin haɗuwarshi da abokin nashi tare da hukuncin da ya yanke.Alhajinmu ya ce," to Allah ya yi jagora?". Hajiyar mu ta yi gyaran murya, alamun zata yi magana, sannan ta ce "Fatima ta ce a gaya maka alkawarin motar da ka yi mata, Nafisa kuwa tayo waya daga can makaranta ka tura mata kuɗi don kuɗin ta sun ƙare."

Ya yi murmushi.

"Nafisa ƴar auta, ta dai kusa gama karatun nan ta huta."

Alhajinmu ya ce"ai ni na ƙosa ta ƙarasa karatun nan,na fi son auren ta." Sadiƙ Ya ce"insha Allahu zata yi Alhajinmu." dube shi "Dama na jima ina zargin kai ke ɗaure mata gindin ƙin auren nan ko?" Ya yi ƴar dariya , "ba haka ba ne Alhajinmu, Allah za ta yi ka san shi aure lokaci ne, kuma insha Allah kwanan nan zata yi" Ya miƙa ta Saddiƙ ni zan fita zuwa ofis, da akwai masu jirana." Cikin tausayawa Alhaji Saddik ya dubi tsohon nasa, sannan ya ce"ya kamata Alhajinmu ka zauna ka huta da zuwa ofis ɗin nan tunda ina kula da kusan duk harkokin ka,na fi son ka huta."

Cikin jin daɗi Alhajinmu ya ce "kada ka damu Saddiƙ,nima ina jin tausayinka ne abubuwa sun maka yawa,ni dai roƙona ga Ubangiji koda yaushe bai wuce Allah ya baka mai rama maka, inason naga zuri'arka."

Zan can Alhajinmu ya taɓa shi,don haka shima sai ya yi shiru yana jin wani abu a iranshi sai yana jin tamkar ya yi shela ya gaya wa matan duniya cewa duk wadda ta haihu da shi zai raba dukiyar shi ya bata rabi, Hajiya dake zaune tafi su damuwa tana matuƙar son ta ga ƴaƴan ɗan su namiji guda ɗaya,shi kaɗai ne namiji gun su sai ƙananan shi mata guda uku,Sadiya ta na auren ɗan gidan Sarki, Fatima tana auren shugaban ƙaramar hukuma.sai auta Nafisa ƴar lelen yayan ta Saddiƙ,yana matuƙar son Nafisa,sai dai kuma sam ba shiri da matarshi Jummai, duk da kasancewar ta ƴar uwar su. Ya fito don raka Alhajinmu wurin mota sannan ya dawo gurin Hajiyar mu don ƙara gaisawa duk da ba wata hira suke yi ba,yana son ya ganshi zaune gaban ta sai ya dinga jin shi tamkar ɗan yaye.

*Page 3*



Abba zaune gaban Malam Dari,suka gaisa da masabaha,sannan Malam Dari cikin al'ajabin abinda binciken shi ya nuna mishi,ya soma magana.

"Malam Mustapha,bayan kai abokin ka yana da wani Amini a garin nan?"

Ya girgiza kai,"ba shi da wani aboki da ya wuce ni." Ya gyara zama " abinda na gani cikin Istaharata shine,zai auri yar Amininshi da ke nan garin,abinda na yi ta bincike. Nayi bincike zata mutu ko bazata mutu ba,zata haihu ko bazata haihu ba? Allah be sa na fahimta ba,amma lallai yarka ce mata ta goma sha daya da zai aura,kuma kila ta zama uwar ya'yanshi,Allah shi ne masanin gaibu."

Zufa ce ta keto mishi ko ta ina. Ya yi shiru yana mamaki,can ya ce "Malam...." Malam Dari ya katse shi da cewa Istihara ce,in kana shakku kaima bari in baka kaje ka yi ta,ka yi ta da kyau insha Allahu ko cikin mafarki ne Allah zai nuna maka."

Bayan barin shi gidan Dari,guri ya samu ya zauna don jikinshi ya yi sanyi,shi kan shi ya kasa sanin dalilin da ya sa shi shiga cikin tashin hankalin duk da hana zaton baya rasa nasaba da mutuwar da duk matar da Alhaji Sadiq ya aura take yi. Yana son yin nazari kan lamarin,da kyar dai ya isa gida.Umma taso ta gane yana cikin damuwa ganinshi da ta yi wani iri,amma dage mata ya yi kan cewa babu komai kanshi ne ke dan ciwo yama sha magani,sallah yake son ayi ya samu ya dan huta kila bacci ne.

Bayan ya yi nafilar sannan ya gabatar da addu'o'in kamar yanda Malam Dari ya yi mishi bayani. Ya kwanta shiru maimakon bacci sai tunanin yanda zai yi,shi dai damuwarshi daya kada ya bashi itama ta mutu. To zai iya hana Saddik wani abu nashi? In ko ya yi haka bai yi butulci ba kuwa?Me zai sa ya manta da abinda Aminin nashi ya yi mishi a baya? Sai dai kuma yana tausayin Aisha,don yarinya ce karama,kashinta bai yi kwari ba. To ko dai ya yi shiru ne tunda Aminin nashi bai san komai game da maganar Malam Dari ba? Nan take wata zuciyar ta soki hakan,da cewa ka sani ko tun can Katsinan an gaya mishi cewa yarka ce zai aura? Nan take ya yardar ma kanshi cewa ga shi ma ya misalta mishi cewa tsakaninsu da nisa,tabdi! In ko Sadiq ya sani dole ne ma ya hakura da Aisha,ya aura mishi koda hakan ya na nufin itama zata bi 'yan'uwanta,wato matan da ya yi ta aure suna mutuwa. Da wannan tunanin bacci ya yi awon gaba da shi.

Aisha ya gani cikin mafarkinshi goye da yaro,sai dai ba ta walwala,tana tafiya da alama cikin tashin hankali ta ke. Firgigit! Ya farka ya na addu'o'i,ya koma ya kwanta yana tausayi 'yar ta shi.Karama ce Aisha 'yar shekaru sha biyar,ga ta siririya,damuwar Aisha ita ce karatu. Tana da burin zama likita,ko yaushe ta zo hutu daga makaranta sai tace Abbanmu don Allah ka cika min alkawarin da kai mini wanda ka ce insha Allah sai na zama likitar mata,ni ina son na taimaki musulmi,ya kan ce insha Allah zaki zama,Aisha kin ma zama in dai kin dage da karatu,wannan burinta ne tun tana yarinya,gashi Allah bai yi ba. Tunda a daren ya yanke hukuncin ba yar da Aisha ga Amininsa,sai dai ya kwana addu'a,Allah yasa ita ce uwa ga yaran shi,Aminin nasa.


Da safe gurin karin kumallo bayan sun gama ya sallami 'yan mazan sannan ya dubi Ummar su "ina kawallin ta ki ? Ta ce "ta na dakina,tana gyarawa." Ya ce " da ta bari ta karya ai ko?" Umman ta dube shi "ka manta yau alhamis ? Aisha tafi mu kokarin Azumin nan na Litinin da Alhamis,tun dan zazzabin da ka yi kwanaki ni da kai muka saka shiririta cikin azumin"'. Ya gyara zama "shi yasa ina matukar son Aisha ,duk da haka kuma gashi lokaci ya yi da zamu rabu,ta dube shi da sauri "ban gane zaku rabu ba? Ya dan yi jim sannan ya ce "Aure zan mata" da sauri ta mike,"Aure! Aure dai? Ya yi karfin hali,"mene ne to na daga hankalin?". Ta zauna cike da damuwa,tare da fadin "dole ne na tada hankali,to ko dai kana tsokanata ne?" Ya dube ta" kin ga na taba miki irin wannan maganar?" Ta girgiza kai tare da shafe zufar da ke keto mata, "amma Abban yara Aisha ba ta isa aure ba,gata dama ita ba kiba ba baka ganin da kwara?".

Ya girgiza kai ba wani kwara a cikin aure,bautar Ubangiji ne,bana son ki nuna damuwarki,har ki karya mata gwiwa ina son mu lallashe ta nasan zata damu ko don yanda take matukar son karatu,ki bani goyon baya,nima inason na rama akhairan da Aminina ya jima yana min ne,wato Alhaji Saddik." Ta dube shi.Tsura mishi ido ta yi "Alhaji Saddik za ka ba ta?" Ya ce "shine" shiru ta yi yace "me ki ka ce?" Ta girgiza kai " babu komai,sai dai tausayin ta,yarinya ce ga shi kuma suna katsina ba kusa ba ne" ya ce"kada ki damu,aure babu in daba ya ksi mutum,batun yarinta kuwa duk ba komai bane,shekara kusan sha biyar ai ta girma,jiki ne ba ta dashi.Nasan Friend za ya kula da ita,yanzun kira ta in sanar da ita" Cikin jimami ta ce " To Allah ya tabbatar mana da alkhairi." Ta tashi ta kira Aishan,kallon ta yake yi a ranshi shima yana kara tausaya mata,saboda sam batada kauri don tsinken hannun tamkar na yara kanana.

Ta zauna kusa da Umma ,kuma ganin Abban nasu ba da alamun wasa ba,yasa ta nutsu ta san magana ce mai mahimmanci zai mata,kila batun komawarta makaranta ne nan da kwana hudu,ya katse mata tunaninta da fadin "Aisha" ta amsa "na'am Abba." Ya ci gaba "ina son zan miki wata magana,sai dai ina shakka." Cikin mamaki ta dube shi,sannan ta ce "Shakka Abba?" Ta ci gaba "bazan so in zama 'yar da iyayenta za su rinka shakka a kanta ba,domin bani da burin bijire ma umarnin ku,ko haninku,ka fadi ko ma me ka keson fada ba tare da shakka ba." Ya numfasa tare da jin dadin maganar ta,sannan ya furta zancan zan miki aure ne." A tsorace ta dube shi,domin batayi zaton faruwar haka ba,amma sai ta dake ta kuma hadiye wani abu da ke taso mata ,ta ce "to Abba." Ya ci gaba "kuma Alhaji Sadiq wanda yazo daga katsina,shi na zaba miki." Kanta na kasa ta ce "to" Ta dube shi kamar zata yi magana,amma tana jin da ta bude baki hawaye zai zubo mata,don haka sai ta yi shiru.

"Ki yi magana mana." In ji Abba,don ya fahimci tana son ta yi magana ne ta fasa.Sai ta yi dan murmushi sannan hawayen data ke makalewa suka zubo,ba ta share ba,ta ce "dama zancan karatu ne zan yi sai kuma na tuna cewa ai babu sauran karatu."

Tausayinta iyayan suka ji,Abba ya ce " insha Allahu za ki ci gaba,yanzun ma zaki koma kafin mu tsaida lokaci,ina so ne dai ki sani,ta ce "to" ya ce " tashi kije,Allah yayi miki albarka."

Wanka ta shiga,amma zama ta yi a bayi ta kasa wankan,tunaninta shin mene ne dalilin Abba na aurar da ita bayan ya yi mata alkawarin zama Doctor? Kuka ta yi sosai cikin bayin,tana tausayin kanta, Ta sani duk yanda aka yi Abba yana da dalili mai karfi na yin hakan gare ta,sai dai ta sani ba yana nufin cutar da ita ba ne,ba ta taba soyayya ba,ballantana ta ce bata son shi,ta sani dole ne ta girmama shi musamman in ta tuna taimakon da ya yi ma mahaifinsu,gashi mai kyau da kuma tsafta,ma'abocin kamshin turaruka,ta tuna san da yazo suke falo kamshinsa ya cika gidan ko ina,sam bai yi kama da shekarunsa ba tamkar wani matashi dan shekara talatin,daga karshe dai tayo wankanta ta fito,ko a daki lallashinta Umma ta kara yi,kan cewa kada ta damu.



___________________________
Hajiya Jummai tana zaune bakin gadonta kafarta daya kan daya,tunanin ta yana can Jigawa ita kam sam ba ta so ba,Alhaji ya yanke hukuncin bawa abokin shi Manajan wannan kamfanin ba,bayan ta jima tana mishi maganar kaninta,bataso ta ga wani kusa da dukiyar mijinta domin duk abinda ya tara nata ne,tunda ba d'a gareshi ba,don haka dole ta kula da dukiyar ta,ta san kuma tunda shine gaba da ita zai rigata mutuwa,dole ma ta san matakin dauka kan wannan kamfanin bari dai ta bari a gama gyaran.



Dai dai yayi parking wayarshi ta soma tsuwa,ya duba Friend ya furta,sannan ya dauka.

"Assalamu alaikum,Friend mun wuni lafiya?"

"Lafiya lau Friend.Alhaji Saddik ya fada.

"Yarana suna lafiya?"

"Lafiya qalau,batun aiki ne nake son ce maka an kusa kammalawa,sannan sai batun taimakon da na ce maka zan nemo game da matsalarka. Da fatan kana da lokaci zan maka bayani." Alhaji Saddik ya ce " ina jinka,ni kadai ne." Abba ya ci gaba...


[11/30, 07:51] Ummi Tandama😇: ____________________________
*📗MUMMUNAN ZATO📗*

*NA*
*HALIMA ABDULLAHI K/MASHI*


*Ɗandano page 4*


"Bayan Istihara mun ga alkhairin aurenka da wata yarinya,zan so ka samu lokaci ka zo," Shiru Alhaji Sadiƙ ya yi,can ya ce, "Friend na haƙura da duk wani aure yanzun, mutane sun camfani da yawa,ba na son ƴaƴan mutane su yi ta mutuwa a hannuna....." Abba ya katse shi "kai dai in ka samu lokaci kazo." Yace,"shikenan,na gode."

Sai da ya sauka masauki ya huta sannan ya yi ma Friend ɗin shi waya cewa yana nan a Dutse fa, Abba yace "ka min bazata fa,to bari inzo in same ka inda ka sauka wancan karon ne?" "Eh,nan ne" inji Alhaji Sadiƙ. Ya idar da sallar la'asar yana jan carbi, Abba yayi sallama ya shigo, Alhaji Saddiƙ ya tare shi cike da fara'a tare da yi wa juna musabaha, suka zauna. Sun gaisa Alhaji Saddiƙ yace "Friend ina yaran nawa,sun koma karatu hutu ya ƙare ko?" Abba yace, "Sun koma,ya ya Madam?" "Tana lafiya" inji Saddiƙ, tace in gaishe ku,(ya ari bakinta ya ci mata albasa). Ya ci gaba,"Naso ince ka zo min da zoɓon nan da nasha a gidan ka"Abba ya yi ƴar dariya,"ai na zata gidan ma zamu je yanzun," inji Abba, "Na fi son mu gama magana a nan shi yasa na sauka,yi man bayani Friend danni fa bana son yanda ƴan garinmu suka shiga tsorona,nan ma in shiga wannan halin" Abba yace "bari dai in baka labarin komai ."nan ya koro mishi bayanin yanda suka yi da Malam Dari, Alhaji Saddiƙ bai ji mamaki sosai ba, saboda ya san ita ce shima ya sha ganin ta cikin mafarkinshi.

Ya dubi Abba, "Friend ban sha mamaki ba, saboda ran da naga yarinyar nan na san cewa ita ce nake gani cikin mafarkina, amma hakan ba zai sa in aureta ba,sam ba zan zama sanadin mutuwar ƴarka ba,bayan haka ma da kunya in auri ƴarka,ai ƴata ce, kuma da kunya sa......." Abba ya ɗaga mishi hannu alamar yayi shiru, sannan ya ce "amma ka san cewa bai saɓa ma Shari'a ba ko? Hasali ma wata sunna ce mai ƙyau ta Manzon Allah (S.A.W) muka yi koyi ko? Ka manta Sayyidina Abubakar (A.S) babban abokin Manzon mu ne, sannan ya aura mishi ƴarsa Nana A'isha, Allah ya yarda da ita,Tana da ƙarancin shekaru, shi kuma ya soma manyantaka,sam wannan ba abin kunya ba ne kamar yanda wasu ke faɗi."

Alhaji Saddiƙ ya ce "Friend yariyar nan ƙarama ce, bayan haka mu duba irin yanda mata suke mutuwa a gidana...." Abba ya sake katse shi da cewa "kai ne ka ke kashe su?" Alhaji Saddiƙ ya girgiza kai, "To!" Inji Abba,"ƙwanansu ne ya ƙare itama in nata ƙwanakin suka ƙare ko ba a gidanka ba dole ta tafi, batun ƙanƙanta kuwa wannan ba wani uzuri ba ne, iyayenmu ko shekarunta ba su kai ba,me ya same su? In dai baka sonta ne shi kenan."

Alhaji Saddiƙ ya dafa kafaɗar Abba "ba za ka taɓa haihuwar ƴa in ce bana sonta ba,na amsa kuma ban san bakin da zan iya maka godiya ba, saboda kai masoyina ne, cikin kowanne hali,in ba mai sonka ba,wanene zai yarda ya kai

2 / 10