Author : Halima K Mashi Category : Complete Novels
Abba ya ci gaba da cewa, "ina so ku sani cewa, dukkan mai rai mamaci ne, haka nan matansa da suka riga mu gidan gaskiya,ku yarda wa'adinsu ne ya zo, batun yana yankan kai babu gaskiya cikin zargin da mutanan unguwar suke mishi."
Umma cikin matsananciyar damuwa ta ce, "to yanzun Abbansu matan nasa suna mutuwa haka za'a bashi A'ishan?.
Ya ce, "Haba Fatima,ya ya ki ke dawo da hannun agogo baya? Na gaya miki na sake gaya miki aure babu fashi, mutum baya mutuwa face ƙwananshi ya ƙare. Ya fita yana cewa "ki zo."
Ɗakinta ya shiga, Umma ta biyo shi jikinta babu ƙwari. Ya dube ta yace, "Haba Fatima,me zai sa kiyi min haka? Ke kin san son da nake ma A'isha,kin sani ba zan cutar da ita ba, aure bautar ubangiji ne, zan yi murna a ce ta mutu tana ibada,don haka ki natsu kuma ki ƙwantar da hankalin ki,ki bani goyon baya. Ki yaƙi shaiɗan mu tattaushe ta,nima wallahi ƙarfin hali nake yi,in tana ganinmu cikin damuwa zata kasa ƙwantar da hankalinta kullum zata zama cikin fargaba."
Umma ta ce, "Shikenan, zan yi yanda ka ce," ya ce "yauwa, addu'a kurum ita ce magani,ki tsaya tsayin daka da addu'a,ba dare babu rana. Itama A'ishan ki tsaya kanta ta dage da yin azkar safe da yamma. Cikin fargaba ta ce "To."
Sanda Umma ta shigo ɗakin A'isha, ta samu A'ishar tana zaune gabanta wayar ta ce tana ta ruri tsabar tsoro ya hana A'ishar ɗaga wayar Umma ta kalli fuskar wayar Uncle ɗina haka taga an rubuta nan take ta gane,ta cewa A'isha an sa shi mana? Ki natsu ki ƙwantar da hankalinki,ki mishi magana cikin natsuwa,kada ki ɗaga mishi hankali,kin ji?" Ta ce "Ina jin tsoron shi ne Umma" Umma ta ce "Daina tsoron shi, shi ba mugu bane sharri ne mutane suke masa, ɗauki wayar." Ta kai hannu zata ɗauki wayar, ta katse a karo na biyu.
Ya sake kira a karo na uku, Umma ta ɗauki wayar ta miƙa mata, hannunta yana rawa ta amsa ta danna green ta sa a kunne. Cikin muryar nan tashi mai natsuwa da hikima yace, "amincin Allah ya tabbata a gareki Humaira Beby". A'isha ta dubi Umma,harara Umma ta zabgo mata, sannan ta fita can gefen. Ya ce "kina jina ƴar Abba?" Ta daure, sannan ta ce, "Ina yini Uncle?" Ya ce, "lafiya lau,kin dawo lafiya?" Ta ce, lafiya lau, ya ce "Masha Allah" a zuciyarta kuma faɗi take, Allahumma kafihim bima shi'ita,tana maimaitawa tana sake faɗa,ya ɗan yi gyaran murya,ya ce "A'isha ina labari?" Ta yi shiru,ya ƙara sanyaya murya,ya ce "A'isha kina ji na?" Ta ce, "Umh" ya ce, "zan zo week end,tun Friday kin ji? Kamar ta ce A'a, sai kuma ta ce Umh, ya yi ƴar dariya sannan ya ce "to Bebyna,me da me zan kawo miki?" Ta ce,babu komai.ya ce Shikenan, sai na zo, tace, "To ka gaida Nafisa" cikin jin daɗi ya ce "ita kaɗai ban da Hajiyarmu?" Da sauri ta ce "har da su." Ta ƙosa ƙwarai ya gama maganganunshi, kamar ko ya sani, ya ce "to bari na ƙyale ki sai kin ganni ko?" Ta ce Uhum, ta riga shi kashewa,ana shi gefen bai damu ba zaton shi kunya ce.
Daran juma'a,sam A'isha bata runtsa ba, tama rasa tunanin da zata yi, duk da lallashin da Umma take mata, bayan sun karya, Umma ta matsa mata suka shiga kitchen don girka abin tarbar baƙo.
Sun gama sha biyu da rabi nan Umma ta bar ta ta haɗa mishi zoɓo da sauran kayan sha. Ta shigo falo ta ƙwanta kan kujera, Umma ta fito don zuwa kitchen ta ce har kin gama?" A'isha ta ce,eh, Umma ta miƙa mata waya ga shi yana ta kira ni ina wanka." A'isha ta amsa Umma ta koma ciki.
Wayar ta soma ringing. Ta tsurawa wayar ido, ita dai kullum ƙara tsoron shi ma take yi, amma ba ta da yanda zata yi dole ta ɗaga wayar tare da addu'a a can ƙasan zuciyarta. Sannan ta ce, "Salamu alaikum" ya ce "wa'alaikumus Salam, Beby ina ki ka shiga ne? Ina ta kiran wayarki?" Ta soma magana cikin in'ina, "ina....am......wannan ne a kitchen ne," ya yi ƴar dariya, "ni kike yiwa girki kenan?" Ta yi shiru, ya ce "ok,shiru yana nufin eh ne,to na gode. Yanzu haka na shigo Jigawa, masauki kawai zamu je, sai na iso kenan" ta ce,to, Ya kashe wayar.
Ta tsaya tana kallon wayar,daddaɗar muryarshi har yanzun tana yi mata gizo, murya mai cike da kamala kamar yarda fuskarshi take nunawa ta tuno suffarshi a fili ta ce lallai Uncle bashi da makusa in ban da na mugun halinshi koda dai su Umma suna ƙaryatawa.
Ta fito wanka tayo alwalla tana idar da sallar azahar mai ta shafa sama-sama saboda zafin garin ta zazzago farar hoda a hannunta,ta ɗan murza a fuskarta ko madubi ba ta duba ba,dama ita bata ƙwalliya. Don haka ba ta ma duba madubi,kai ita fa ko kaya bata da zaɓi duk wanda Abbanta ya sai mata sun yi,don tana saka kaya ne don suturta jiki ba wai don gayu ba, ta ɗaga aƙwatinta ta ciro kayan da ke sama. Wata atamfa ce ta mutanan Ghana, fara ce ta saka taje ta ɗauko abincinta,ta zauna tana ɗan cakula tana dai cin abincin ne amma hankalinta duk yana kan Uncle ganinta ƙila ma tun yau zai gama da ita. Jafar da Munnir suka shigo,suna cewa Umma ga Uncle ɗin mu ya zo yana waje yana waya. Umma ta ce, "tare da Abbanku su ke?" Suka ce "a'a shi kaɗai ne, amma Yaya Abdulrahman yana gurinshi, ta ce "Abbanku yau ina ga aiki ya mishi yawa ne,ko gida bai dawo ba, ina ganin daga Office ɗin ya wuce Masallacin juma'a.
Jafar ya fita waje,jim kaɗan ya dawo. "Umma Yaya Abdulrahman,ya ce ki bada makullin ɗakin baƙi" taje ta ɗauko, A'isha kam tana zaune kamar gunki tana jin su. Yaya Abdulrahman ya shigo, "Umma Uncle yana ɗakin baƙi ya ce yabi ta Ofis ɗin Abba,sun tafi masallaci, shima yaje ya yi sallah ya koma Ofis ɗin basu dawo ba shi ne ya zo nan gida". Umma ta ce, "bai kira wayarshi ba?" Yana ta kira bai samu ba sai yanzun. Umma ta ce, "To ai shi kenan, tunda ma ya sameshi. Ta leƙo falo "A'isha tashi ki je ki shirya mishi abinci,ki kai mishi." Jiki babu ƙwari ta tashi ta fita.
____________________________
*📗MUMMUNAN ZATO📗*
*NA*
*HALIMA ABDULLAHI K/MASHI*
*Ɗandano page 8*
*Wannan littafin na kudi ne masu son DOCUMENT book 1&2&3 Complete ₦600,masu son PAGES ₦400 idan kuna bukata zaku turo kudin ku ta wannan account number👇🏻*
```ACT}:--1632036584
Sa'adatu Balarabe
Access Bank,a turo shaidar biya ta 09068032427 wancan account ɗin namu ya samu matsala ne, idan mun gyara zamu dawo dashi```
*Ko kuma katin Mtn ta wannan number 09068032427 idan baki shirya siya ba ki bari sai kin shirya sai kiyi magana*
*Masu son tallata masu hajar su suyi magana ta wannan number 09068032427*```
Babban tire ne ta shaƙe shi da kuloli masu ɗauke da kalolin abinci. Sai plate da cokali, da sallama ta shiga,ƙasan zuciyarta kuma tana maimaita addu'ar Allahumma kafihim bima shi'ita.
Ya yi matuƙar ƙyau cikin shadda mai tsada kalar ja mai duhu,hular da takalman duk kalar jan ne,ƙamshin daddaɗan turarenshi ya cika falon. Duk da tsoronshin da take ji bai hana zuciyarta yaba ƙyanshi ba. Ta dire tire kan tebur ɗin, gabanshi ta jawo teburin sannan ta sunkuyar da kanta ƙasa ta ce sannu da zuwa Uncle, ya ce "yauwa ƴar Bebyn Uncle,I hope kina lafiya?" Ta ce "lafiya lau,ya ya su Nafisa da su Hajiya?" "Duk suna gaishe ki, cikin jin daɗi yake bata amsa, domin yarinyar ta shiga ranshi har yana mamakin yanda wasu lokutan ya kan shagala da tunaninta,ya kan ji kewar ƴar siririyar muryarta, da Beby face ɗin ta, abinda bai taɓa yi kenan a kan mace ba, duk matan da ya aura baita jinsu kamar yanda yake jin A'isha ba,a ranshi. Ta cika kofi da ruwan zoɓo mai sanyi ta miƙa mishi cike da ladabi, ta koma gefe ta zauna, ya ce "No, come on hau kujera ki zauna,ta ce nan ya yi Uncle, ya ce to nima bari na sakko ƙasan, ta yi sauri ta hau kan kujerar ta ɗan ɗofanu yana ƴar dariya shima ya gyara zaman shi.
Sannan ya soma shan zoɓon ta gefen idanunta ta ke kallonshi. A ranta ta ce "Oh,ga mutum har mutum, amma cikin zuciyarshi gara kura da shi. Ya katse shirun da cewa "Beby in Allah ya gwada mana ki ka koma gidana, ina son kina min wannan zoɓon kin ji?" Ta ɗaga kai alamar ta ji ya ce "to abincin fa zo ki zuba min," ta ce to, tana buɗe kular farko yaga saƙwara fara ƙar-ƙar, ya ce "ai shikenan Beby yau kuwa har in tafi ita zan ta ci.
Nan ta zuba mishi da miyar agushi, ga nama manya-manya,ya cika cikinsa dam,ko magana ba ya iya yi, sai da ya gama sannan ya dube ta yana goge fuska da fari ƙar ɗin handkachief ya ce, Beby kin ganni babu ba ka sai kunne ko? Ta sunkuyar da kai.
Ya ce,"Beby sai naga kamar kin rame min a ido hakane?" Ta ce na ɗan yi mura bayan haka kuma ga makaranta," ya ce "kin manta ɗayar ga kuma maganar aure". Ta rufe fuska, ya yi ƴar dariya sannan ya ce zan sa su kawo kaya da zarar na koma gida nan da sati biyu zuwa uku,kin zama ƴar mutanen K.T? ko?" zancan ya daki zuciyarta, nan take ta raya ma ranta haka yana nuna nan da sati huɗu zuwa biyar zata baƙunci kabarinta, tunda an ce matan nashi ba sa wuce sati biyu zuwa uku suke mutuwa.
Ya katse ta. "Ko ya yi nisa a rage?" Da sauri ta girgiza kai,ya ce "a barshi haka?" Ta ɗaga kai alamar Eh. Nan ya ciro mata tsarabar ta, abubuwan ci ne tare da turaruka har da wata ƴar Tedi ta wasan yara. Ya miƙa mata ledojin ya ce "to duk da kin ce baki son tsaraba gashi nan ki basu Jafar ke kuma ga naki" ya miƙa mata Tedi.
Baki ta saki tana kallonshi, shima ita yake kallo tamkar masu kallon soyayya, sannan cikin sanyin murya ta ce "Uncle me zan yi da wannan?" Ya ce "wasa mana" ta ce, "am not a small girl," ya ce haba? Ta sunkuyar da kai tace,da gaske,ya ce shikenan to ki ajiye min in kin haifa mana Small boy sai ki na bashi yana wasa," ga mamakin shi sai ya ji tace "in kuma na mutu fa?"
Da sauri ya dube ta,a ranshi ya soma zargin ko taji cewa matanshi suna mutuwa ne? Amma a fili sai ya ce,"nima ina yawan tuna haka, sai dai duk sanda na tuna cewa zan iya mutuwa ko ke ki mutu ban ga ɗan kaina ba, ina shiga wani mawuyacin hali, zuciyata tana sonki da yawa." Ta sunkuyar da kanta ƙasa,ko dai mummunan zato ne a ke mishi? Ko dai zargi ne? Ƙwanan matan nasa ne suke ta ƙarewa? Ya katse mata tunani da cewa, "ki na tsoron mutuwa ne? Ko kina zaton in kin aureni zaki mutu ne?".
Cikin dabara ya sako mata tambayar,don yana son ji ko ta samu labarin matanshi suna mutuwa ne? Nan take ta gane nufinshi,don haka sai ta ce "a'a bana tsoron mutuwa,sai dai kullum tunanina yana kan ayar da ke sanar damu (kulli nafsin za'ikatul mauti), kaga dukkan Musulmi yana da ƙyau ya dinga tunawa ranshi zata ɗanɗani mutuwa, sannan in ajali ya yi kira ko ince in ajali ya zo ba za'a ƙara ma mutum ko second ba.
Alhaji Saddiƙ ya dube ta cike da farin ciki,ya ce haka ne Beby, lallai kina da kaifin basira. Haka nan duk bawan da yake yawaita tunanin mutuwa zata iya riskarshi a kowane lokaci,za ki sameshi yana mai matuƙar kiyaye dokokin Ubangijinshi, ina saka rai kema kina ciki? Ta sunkuyar da kai tare da faɗin insha Allah ya ce, to ba zaki taɓe ba.
Sannan ya canza zancen da cewa,me kike shiryawa bikin? Ina nufin waɗanne shagulgula za kiyi ke da ƙawayanki? Saboda in na tafi ba zan dawo ba, sai ɗaurin aure, shiyasa nake son in sallame ki."
Ta dube shi,a ranta ta ce, inyi shagalin me? Bayan ni ƴan ƙwanaki ne suka rage min,a fili kuwa sai ta ce, "ba zan yi komai ba." Ya ce, "Haba! Ko walima?" Ta girgiza kai tare da ƙoƙarin maida ƙwallar da ke son zubo mata. Ta ɗan saka hannu ta ja hancinta kamar tana mura, sannan ta ƙago murmushi ta ce "kasan Uncle bani da ƙawaye bayan haka ma ni ban cika son hayaniya ba,so kaga gara na barshi ko?" Ta faɗa tare da duban shi,ya ce "shikenan Bebyna" ya saka hannu cikin aljihun ya ciro rafar ƴan ɗari biyar guda biyu dubu ɗari kenan,"gashi gudunmawata," zatayi magana ya tare ta da cewa, "kul ki kakiyi magana, ke dai ce ne Allah ya cika mana burinmu,a ranta ta ce Amin in ba shanye mini jinina ba ne. Ya ce zaki shiga gida ko? Da sauri ta ce,eh tare da kallonshi ya yi ɗan murmushi sannan ya ce, "kin ƙosa ki tafi ko?" Ta sunkuyar da kai tare da girgiza kan alamar a'a, ya ce "to ga kayanki nan ƙwashe. Ta miƙe tare da ƙwashe kayan ta ce mun gode. Ya ce,ba ki ɗauki Tedi ɗin Small beby ɗin tamu ba,ta kalli Tedin sannan ta ɗauka ya ce in Abbanki ya shigo sai ki ce ina jira, sannan ki bar wayarki a kunne kin ji? To tace,ta fita.
A gadon Ummanta ta zube kayan tare da zama gefen gadon ta rafsa tagumi. Umma ta fito daga (toilet) ta tsaya tana kallon kayan da iyayen kuɗin da ke zube a kan gadonta, ta ce "A'isha waɗannan kayan fa?" Ta ce "Uncle ne ya ce in kawo ma su Jafar?" Ta ce, "wannan kuɗin fa?" Me yasa ki ka amsar masa kuɗi?" Ta ce "Umma nayi-nayi ya bar su yaƙi wai cewa ya yi gudunmawa ya bani don na ce mishi ni ba zan yi shagalin biki ba.
Umma ta ce duk da haka da dai baki amso ba, A'isha ta dubi Ummanta ta ce, "ki aje a gurinki ni sai in dinga ganin tamkar yana biyan kuɗin jinina ne da zasu sha....." Ke! Tsawa Umma ta daka mata, sannan ta ce "A'isha bana son jin irin waɗannan surutan daga bakinki kenan kema kin yarda da mummunan zargin da al'umma suke ma mutumin da zai zama mijinki? Duk kin bi kin ɗaga hankalinki, maimakon ki tsaya kan addu'a Allah yasa ki shiga gidanki cikin Sa'a ko? Ta miƙe ranta ɓace ta fita falo ta bar ta ɗauke da tagumi tana nazarin yanda ma za'ayi ta iya ƙwantar da hankalinta.
"Sofy! Sofy," Hajiya Jummai ce ke ƙwala ma ɗaya daga cikin ƴammatan da take ɗaukowa cikin danginta kira. Sofy ta zo cike da yatsina, ta ce "gani Anty Jummai," ta ce suby fa? Sofy ta yi wani luu da idanu, sannan ta ce tana bedroom in kirata ne?" Jummai ta ce, "eh kirata aikenku zan yi yanzun ku fito cikin shiri." Suka fito cikin riga da wando ya ɗame kowacce cikinsu, Sofy ce ma ta ɗan yafa wani ɗan kucilin gyale, Jummai ta dube su kun yi ƙyau, sai dai kema Suby je ki yana ko ɗan irin na Sofy ɗin kin san Alaramma yana gari. Haka take kiran Alhaji Saddiƙ in zata yi wani abu daya hane ta. Ko in ya yi mata nasiha, to ranar yini zata yi tana ce mishi Alaramma,ko Alagafarta. Soby taje ta ɗauko tana mitar ita bata son wani yafe-yafen gyale duk takura ne, Jummai ta ce "ya ya zakiyi tunda kina gidan Ustazai,ka ce shi yafi kowa sanin Allah" ta ce "ga wannan ta miƙa musu wani ƙullin abu cikin tsumma,ku kai ma Hajiya Kari,ku ce mata ga ƙasar ƙafar nan za kuma mu yi waya.
Sofy ta ce, "motar wa zamu ɗauka tunda ta mu tana gurin gyara?" Hajiya Jummai ta soma masifa, "ku hau mashin ba zan ba ku motata ba,ku je ku buga min ku ja min asara." Suby ta ja tsaki tayi gaba tare da cewa, "Sofy ta baki kuɗin mashin ɗin, amma ai ba mutuncinmu bane hawa acaɓa." Hajiya Jummai ta ce "shegun yara kada ku yi mutuncin mana, tare da jeho musu ɗari biyu Sofy ta ɗauka tana mita haka suka tafi suna zaginta, da cewa masifaffiyar mata.
Sofy ƴat ƙanwarta ce,Suby kuwa ƴar autar su ce,yaran sam basu da tarbiyya,ba sa shakkar kowa sai maigidan. Hatta Hajiya Jummai maida mata magana suke yi. Foly suke zuwa da ke nan Katsina. In kin ga yanda suke ɗaukan kai da shan ƙamshi zaka zata ƴaƴan shugaban ƙasa ne. Alhaji Saddiƙ kaɗai ke taka musu birki in yana gari.
Hajiya Kari da Jummai cikin motar Hajiya Kari, ita da kanta take jan motar suna hirar yanda zasu tsara mutuwar Amaryar ta Alhaji Saddiƙ,waton A'isha. Hajiya Jummai ta ce "kin san Allah Hajiya Kari, (ta cigaba) wannan karon sati ɗaya nake son a aika yarinyar nan barzahu, domin duk cikin matan da ya yi,yayin auren ban taɓa jin kishin wata ba kamar wannan". Kari ta dube ta "menene na ɗaga hankali,yarinyar da ƴan ƙwanaki za ta yi ta sheƙa barzahu, har ki ke damun kanki." Jummai ta yamutsa baki,"ina mugun jin takaicin yanda ya damu da yarinyar, duk abokansa ya bi ya sanar da su alhalin da a ɓoye yake aurensa, sai in amaryar ta mutu sannan su ji, amma wannan fa shi da kanshi yake buga musu waya yana cewa,zai yi aure su taya shi da addu'a,ke wani takaici ma sai suna waya da yarinyar in kin ji yanda yake ƙara saisaita murya zaki sha mamaki." Hajiya Kari ta ce, "dama ga muryarshi kamar ta mata,anya ma ba salabane yake yi kuwa?" Jummai ta ce,"shi dai ya sani,ni yanzun damuwata ba ta wuce ya Boka na kan Dutse ya