Author : Sumayya Abdulkadir Category : Romantic Hausa Novels
musu wasa sosai
kasancewarsa mai son yara.
Sannan ta kaishi bangaren yara mata masu tashen balaga (teens) ‘yan makaranta. Anan
idanunsa ya kyallo masa ita, bahaushiya ce, babu ko tantama mai kyau ce sosai, daga duba na
farko zaka ga kyawun nata a zahiri, duk ‘yammatan sun lura da shigowar Madam tareda bakon,
amma ita yarinyar bata lura ba, suka soma gaishe su duk hankalinta bai kai kansu ba, sai da
Madam Taibat tace “Haseenah baki ga baki bane?”
Da sauri yarinyar ta dago jin an ambaci sunanta, yayi mata murmushi ya karaso har gabanta
yace “sannu da karatu Haseenah!” ta amsa, ta kuma gaishe shi sai ya karbi littafin hannunta
yana dubawa. “Basic Science and Technology” ya ga an rubuta a jiki. (For junior secondary
schools). Yarinyar zatayi sa’ar Hakeem dan abokiyar tagwaitakarsa Murjanatu. Don haka kawai
babu shawara da Nenne yace bari ya dauketa daga nan ya kaiwa Murja in yaso ta hadata da
Hakeem su cigaba da makaranta. Kyawunta ya fisgeshi sosai a matsayinsa na namiji, sannan
jan ajinta. Dama ance irin wadannan ‘ya’yan kyau ne dasu.
“Ajinki nawa Haseenah?”
“Bana na gama JSS” (tana magana kai a sama, cikin ko’in kula) da gani ba wadatar
tarbiyyah.
“Kinada burin cigaba?”
“Sosai ma kuwa, Enginiya nake so na zama”. Sosai yaji yarinyar ta bashi tausayi ko don
yadda take magana kanta tsaye da boldness kamar ba marainiya a gidan marayu ba, don
mostly yaran zaka same su basu da karsashi, basu da ko guts na karfin gwiwar kallon mutane
ma cikin ido, sabida (inferiority complex) dake dabaibaye dasu, amma ita kar take kallonsa cikin
ido, idanunta a tsaitsaye, ko kuma don kasancewar fanninsa kenan wanda ta zaba din a
matsayin burinta yasa yaji ta burge shi?
Don haka koda suka koma ofis shida Mrs Taibat yayi abinda bai taba yi ba tunda yake zuwa
gidan marayu daban daban, watau yabi duk process din da ake bi na daukar yaro a gidan, na
daga cike-ciken takardu ha a karshe yayi (adopting) dinta.
Amma a ransa ya san ba dai ya kaiwa Nenne ba, yayi abunsa kai tsaye without a second
thought, saidai ya kaiwa Murjanatu, it ace mai biyewa komai yake so mai kyau ko mara kyau, in
yaso ya dinga daukar nauyin karatunta a makarantar kwana, shi dai yaji ransa na son
kyakkyawar yarinyar, in yaso in akayi hutu ta zauna gidan Murjanatu har ta isa shiga jami’a ya
nema mata admission a fannin Engineering din duk da take so. Ko iya haka aka tsaya ya gina
rayuwarta, tunda in ta gama zata iya samun aikin da zai isheta kula da kanta har watarana ta
tallafi gidan marayunsu da marayu ‘yan uwanta.
***** ***** ****
Ya damka amanar yarinyar a hannun wato Aunty Murjanatu, ya kuma fara biyan komai na
karatunta tareda Hakeem yaron Murja. Lokacin ba’a haifi Kiki ba. Murja ta kaisu makarantar
kwana ta British int’l school a garin Lagos. Kasancewar duk abinda dan uwanta ke so bata
opposing tana taya shi ne su cimma abinnan. Ta dade da sanin philanthrophic heart dinshi, na cikin dabi’un shi masu kyau, da suka
banbanta shi da sauran matasan zuri’arsu kaf!
Ta yarda ta amince babu mutum mai zuciyar halin girma da daukar girma tun bai girma ba
cikin jikokin gidansu kamar Prince, duk wani hali irin na Kakansu Emir Abdulrasheed ya kwashe
shi ya bar kowa da sudin kwano. A kafatanin zurri’ar gidansu ba mai kyakkyawar zuciya ta
taimakon mara galihu irin ta dan uwanta Prince. Tun daga kan kannen mahaifin su, har zuwa
tulin ‘ya’yan da suka haifa, ba wanda baya shan rabar taimakonsa (in one way or the other).
Shi Da daya ne tamkar da goma ga iyayensu. Gidansu ba’a tara ‘ya’ya maza ba, shikadai ne
namiji a cikinmata amma ya tarewa iyayensu gurbin misalin yara maza goma!
**** **** ****
Shekaru uku suka zo suka wuce da tarin cigaba ga yarinya Haseenah, bai yi kasa a guiwa ba
yana biyan kudin karatunta tare dana Hakeem duk shekara, wadda da aka tashi bata
permanent name a makaranta sai ya bata surname da sunan marigayin abokinsa Bello
Ambursa, wanda ya rasu gaba kadan da daurin aurensa. Hakika Prince ya ji mutuwar Bello ba dan kadan ba, kullum ya ga Hasinah sai ya tuno shi har
kaunarshi da Bello Ambursa ta shafi Haseenah Ambursa, ko bakomai sanadinsa yaje har inda
take ya daukota. Daga kan Bello bai kara yin aboki ba sai Tokumbo wanda dama Cousin dinsa
ne da suka taso tare. Duk sanda ya zo kasar Najeriya zai je wajenta a makaranta suyi ta tadi, in kuma suna hutu
ne tana gidan Murjanatu acan yake ganinta har sabo mai tsanani ya gitta a tsakaninsu.
A haka har Haseenah ta gama sakandire, a shekarar data kammala ya samar mata gurbi ya
kuma yi sponsoring karatunta a wata jami’a a kasar da yake nasa karatun a lokacin, wato
Tokyo.
Wannan ne ya kawo kusanci na kamshin soyayya tsakanin sa da marainiyar da yake riko
Haseenah, wanda (in no time) ya rikide musu zuwa soyayya. Har shi da Murjanatu suka yanke
shawarar ya aureta kawai, don a zamanta a Japan duk da a hostel take rayuwa, tofa kullum
tana like dashi a gidansa fiyeda sanda take hannun Murjanatu da gaisuwa da hirar makaranta
kadai ke shiga tsakaninsu, acan kuwa bata san kowa ba sai shi, shiyasa koyaushe take like
dashi a gidansa a lokutan da bata da karatu, musamman da idanunta suka fara budewa da
maza ta san menene soyayya.
Sun yanke shawarar shawo kan Nenne don ta yarda ya auri Haseenah shida Murjanatu
gudun sharrin shaidan ya gifta tsakaninsu, to kullum suna tare a inda ba idon kowa nasu a
kansu, yace da Murjanatu yana tsoron watarana ayi abinda ba shikenan ba duk da yana fin
karfin zuciyarsa, amma Nenne ta kafe ta ki. Soyayyarsu shi da Hasinah tayi tsananin karfi a
lokacin har suka soma sakin layi. Sun buga sun buga da Nenne ta bari ayi auren har lokacin ta
ki, don zaman da take yi dasu ma Nenne bata so, tafi so kowanne irin taimako zata yi maka tayi
maka shi daga nesa, ba tareda ta dauko ka ta saka cikin zuri’arta ba gudun kada a bata mata
tarbiyyarsu. Wannan ne dalilin da yasa suka kawo har lokacin da Hasinah ta shiga mataki na
uku a jami’a suna soyayya ba tareda sunyi aure ba.
A irin hakane har ta saba da cousin dinsa mai zuwa gidansa lokaci-lokaci yana sauka a
wurinsa wato Adetokumbo Akanni.
Tokumbo a Japan yake harkokin kasuwancinsa, Automobile Business Mogul ne. A daya
gefen shi da Murjanatu suna cigaba da fama da Nenne akan dai ta yarda ayi auren haka, amma
Nenne tayi tsalle ta dire tace sai a bayan ranta danta zai auri adopted orphan.
A girman nasaba irin tasu, wannan babban abin gori ne a gareta ko a wurin faccaloli, ace duk
matan duniya da wadanda ke cikin family din mahaifinsa da nata ace wai Prince ya rasa matar
aure sai akan Haseenah da take tsintacciya zai kare kamar wanda uwa tacewa jeka ka gani?
Cikin wannan rikicin suke shi da Nenne har kawo yau, Murjanatu na taya shi fighting gun
Nenne don shi Dade dinsu duniya ta shaida mijin tace din Nenne ne, shima da bakinsa yana
fada “I obey her decisions because she leave no stone unturned”. Duk hukuncin da Nenne tayi
bashi da ja, saboda tsabar yarda da sahihiyar soyayyarsa gareta. A ganinsu shi da Murjanatu babu wadda zai aura da zata girmama shi, ta kaunace shi
saboda Allah irin Haseenah, ga Prince da son girma musamman daga matar da yakeso, kai duk
bayeraben basarake akwai tsananin son respect daga mace, a ganinsu ita kadai zata aure shi
ba don arzikin su ko don tarin “FAME” dinsa ba (shahararsa a idon duniya). Duk wata mace da zata aure shi a halin yanzu abubuwan da zata duba kenan (sarauta, kyau,
arziki, da shahararsa), sun yi amanna banda ‘yar da ya raina ya ginawa rayuwa da kansa, har a
yau take jera kafada da ‘yammata masu gata da ilmi ‘ya’yan manyan Najeriya a jami’ar da take
wato Haseenah Bello Ambursa. Hasinah ta tsinci kanta rana daya a soyayyar ubangidanta kamar koma fiye dashi, bata
kuma san daga wane lokaci shakuwarsu ta rikide zuwa soyayyah ba. Duk da banbancin yare
dake tsakaninsu, ita Hasinah bata tuna cewa ma ita bahaushiya ce saboda cakuduwa dasu
Aunty Murja dashi kansa Prince da ba hausar yake yi bama kwatakwata, ko ya iya ko bai iya ba
Allah masani. Duk da ita Haseenah na ganin bata kai matsayin da Prince zai aure ta ba, amma
kaninsa Tokumbo dake tare da shi kuma suke shiri itada shi irin sosai kullum yana yawan
karfafata da cewa.
“If she’s lucky…. Probably zata iya samun auren PRINCE!”
A bakin Tokumbo Haseenah taji cewa Mamanshi ma bahaushiya aka auro musu ita, tazo ta
haifesu shi da su Murja. Shiyasa taga shi da Prince duk da suke ‘yan maza zarr basa kama da
juna.
Yace su din surki ne na yare guda biyu; Fulani/Yoruba wato sun hada duka jinin yammaci da
arewacin Najeriya, ba kamar sauran ‘ya’yan family dinsu ba da gabansu da bayansu Yarbawa
ne.
**** **** ****
Taiwo tayi ajiyar zuciya data tuna asalin haduwar shi da Hasinah da kuma irin sakayyar da
Hasinah tayi musu yau. Ita ba suruka ta dauki Haseenah bama face ’yarta ko kanwarta. Don
haka taji ciwon lalacewarta duk da tayi iya kokarinta a kanta.
Tafi ganin laifin Haseenah akan na Tokumbo. Ko maiyasa? Don itace mace, kuma ita ta bada
kafa har ya sayi mutunci da martabarta daga ido da zuciyar Prince.
Ta tabbatar Hasinah tayi rashi, rashin da duk duniya ya kamata ta taru ta jajanta mata, domin
tabbas tayi rashin mai kaunarta da gaskiya sabida son duniya, kwadayi da biyewa zuciya da
rashin sanin girman zina da illarta aikatata ga mai yinta a addinin musulunci. But who knows?
Ko itama ta hanyar da aka sameta kenan? Sannan bata yi islamiyya ba. Dr. Taiwo, ‘yar uwa mai rike sirrin dan uwanta, ko bai roketa ba, ya san wannan magana
zata cigaba da zama sirri ne a tsakaninsu su kadai, sai ko Allah da ya halicce su, da kuma
Hasinan da Adetokumbon. Ko iyayensu tayi alkawarin bazasu ji wannan mummunar maganar
daga bakinsu ba. Domin wani abu ne da zai kawo hargitsi mai girma ga zuri’ar Akanni gabadaya, watakila
har ya jawo rarrabuwar kai, wanda basa fata. Jiharsu bakidaya ta shaida hadin kan zuri’ar
Akanni da duniya bakidaya, na kasancewarsu tsintsiya madaurinki guda, don in wani ya yarda
Adetokumbo zai aikata hakan a gareshi, duba da irin amintakar dake tsakaninsu, da irin
taimakon da Abdulrasheed din keyi ga business din Tokumbo, wani bazai taba yarda ba, za’a ce
sharri ne, ba don komai ba sai don kasancewar zuri’ar Sarki Akanni tsaftatacciyar zuri’ar kabilar
Yoruba da basu yarda da ko bakar al’adar nan tasu ta a fara yin ciki a waje kafin aure ba,
sannan bai da amini kaf zuri’arsu irin Adetokumbo Abdulfatahi Akanni.
Adetokumbo shine (favourite cousin) dinsa a cikin tarin kannensa maza da suke ‘yan maza
zar kaf a family din Emir Abdulrasheed Akanni, wanda ya kasance Da yake ga Dan Iyan of
Ilorin, daya daga cikin kannen mahaifinsa.
**** **** ****
ASALINSU
(ILORIN EMIRATE)
B
ari mu dauko tarihin tun daga tushe, wato asalin kafuwar masarautar Ilorin. Kamar yadda kowa
ya riga ya sani Masarautar Ilorin da aka fi sani da ‘Ilorin Emirate’ tana nan a jihar Kwara a
yammacin Najeriya, tana daya daga cikin manyan masarautun Najeriya masu dimbin arziki,
Ilorin Emirate, wata babbar attajirar masarautar Musulman Yarbawa ce a kasarmu mai dimbin
albarka, wadda kafuwar tarihinta ya faro ne daga rayuwar Shaihu Salih Janta, da aka fi sani da
(Shehu Alimi).
Kenan su din duk da kasancewarsu Sarakai, kuma manyan sarakunan kabilar Yoruba, to
manyan Malamai ne, ma’abota sani na na addinin Musulunci da kyakkyawan riko dashi. Su din,
har ila yau, sun kasance Shehunnan Yarbawa ne masu dauke da sani na Alqur’ani da Hadisi,
wadanda sukayi gadon sahihiyar sarauta ta malunta da arziki mai dimbin yawa daga
Kakan-Kakan su Shehu Alimi, sarautarsu sarauta ce mai asali da da kyakkyawar nasaba tun
kafuwar kasar Ilorin.
Ilorin Emirate, ta kasance (multiethnic Muslim Kingdom) wato cakude take da kabilu da
yarurruka daban – daban na kasar Najeriya guda hudu, wadanda suka hadu suka samar da
Ilorin Emirate din, sun hada da; Balogun Gambari (Hausa), Balogun Ajikobi (Yoruba), Balogun
Fulani (Fulani), Balogun Alanamu (Yoruba). Kowanne bangare wato kowanne Balogun, nada (district head) wato sarkin dake wakiltar
wannan bangaren/yankin, karkashin babban Sarki Emir of Ilorin, dattijo mai ran karfe Sarkin
wannan zamanin da muke ciki a lokacin yanzu, wato Emir AbdulRasheed Dan Abdullateef
Akanni. Engnr. Edrees Abdulrasheed Akanni, ya kasance Da na farko ga Sarkin Ilorin; Maimartaba
Sarki AbdulRasheedu Akanni, (the 11th Yoruba-Speaking Fulani Emir) wato Sarkin Ilori na
goma sha daya.
Engnr. Idris shikadai ne Da a wurin mahaifiyarsa marigayiya Olori Murjanatu (Olori na nufin
Queen bisa ga al’adar masarautar), tun Edrees yana yaro ta rasu sanadin cutar sankarar
mahaifa.
Sai bayan rasuwarta ne aka bawa Emir Abdulrasheed Sarautar mahaifinsa, aka kuma kawo
masa mata har hudu daga garuruwan yammacin Najeriya daban-daban ya sake aure, sune
suka haifa masa sauran ‘ya’yan sa maza guda tara, har Edrees da matarsa ta farko Morjanatu
ta haifa in an hada su goma kenan gabadaya maza ‘ya’yan Sarkin na Ilorin. Emir Abdulrasheed da ya tashi yiwa dansa na fari aure wato Edrees Akanni, sai ya tsallaka
ya auro masa Gimbiyar Gombe mai suna (Sappa) diyar abokinsa maimartaba Sarkin Gombe,
Ahmadu Umar Jalloh (CFR) daga can cikin yankin jihar Gombe dake arewacin Najeriya.
Engr. Idris Akanni tun lokacin da mahaifinsa ya aura masa Sappa Allah ya zuba masa
matsananciyar soyayyarta, aure ne na gata irin na ‘ya’yan sarakuna don bai wuce shekaru 27
ba lokacin da aka aura masa Sappa, ita kuma bata fice 17 ba, tun daga lokacin yake kula da ita,
don yana matukar son ta kamar ya hadiyeta. Sappa a hannun mijinta Engnr. Idris ta karasa girma ta kuma san rayuwa, ya shiga da ita
duniya ta budi ido, wata irin soyayya Idris Akanni yake mata irin dai soyayyar Yarbawa ga
kyawawan matan Fulani, (mazan Yarbawan Ilorin na matukar son matan Fulani) har dai in aka
yi katari kyawawa ne masu farar fata da gashi yalalaa kamar dai ita Nenne Sappa din. Auren nan nasu ya kafa tarihi a cikin duka zuri’arsu daga bangarensa da nata, domin aure ne
irin wanda ba'a taba yi a masarautar Ilorin da masarautar Gombe ba, wato aure tsakanin
masarautar Ilorin data Fulanin Gombe, albarkacin amincin dake tsakanin Babansa Emir da
mahaifinta Sarki Ahmadu Umar Jalloh (Uban Kasar Gombe).
Sarki Ahmadu Jalloh Umar wato (Uban Kasar Gombe) da Sarki AbdulRasheed Abdullateef
Akanni (Emir of Ilorin) sun hadu ne tun kafin su zama sarakuna magadan iyayensu, wato tun
suna samari ‘yan bana bakwai a jami’a, sun hadu ne a yayin karatun digiri na farko da sukayi
tare a can kasar Venezuela (South America) da iyayensu suka turasu inda dukkanninsu suka
karanta siyasar duniya (International Politics).
Kenan mahaifinsu Idris Akanni wato Emir of Ilorin (AbdulRasheed Abdullateef Akanni aboki
ne na jiki tun na kuruciya ga Baban Nenne Sappa, sarkin Gombe Ahmadu Umar Jalloh.
Kowa da ya sansu ya shaida Idrisu Akanni na ma Sappa wani irin mashahurin so,