Noor Albii Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Complete Novels

Chapter   33 / 36

96K to 99K   out of 107.4K words

tasake wani irin kuka Mai tattareda ciwon da zuciyarta ke Mata.,

Ba'a taba cin Amanarta ba arayuwarta sai yau,
Cin Amana mafi muni Laylah tayi Mata Bayan tagama sanin duk duniya Babu abinda tafi tsana irin cin Amana da zafin kishinta akan Turaki..

Kuka take Yi sosai hawaye na gangara gefen idanuwanta suna Isa har kunnunta
Radadi da zafin datake ji tamkar zasu qarasa Zauta Yar sauran hankalin data rage Mata cikin qwaqwalwa..

Ita kanta Haj Zinat damuwa da baqin ciki Mai girma tashiga ganin yau Na'ima ce ke kuka Haka,
Tabbas al'amarin ya baci Dan Na'ima Bata kuka sbd Allah ya Ara Mata dama dakuma lokaci tana yanda takeso sai yanzu da babban alamari mafi girman mamaki daya samesu..
Allah yasa ba darasin duniya zasu fara ganiba Dan basa fata.

Jin tayi ita kanta wata irin tsana mafi girma da nauyi ta Laylah na sake mamayeta,
Badan sanin girman power da Turaki yakeda itaba da ayau ko ita da kanta saita dauka mataki mummunan gaske akan Laylan...
Ko ahakan tabbas saisun dauka fansar wannan Cin Amanar da wannan toazarcin....

Sam Na'ima batajin zafi ciwukan Dake jikinta da fuskarta datai jajir sbd Girman Marin datasha,

Zafi zuciyarta ke Mata sosai,
Bata taba dauka abin zaizo ahakan ba sbd Koda Zinat ke fada Bata taba yarda da hakan zai tabbataba LAYLAH DA CIKIN TURAKINTA ajikinta,
Abokin mahaifinta, mijin Yar uwarta hakama mijinta ita uwar datai Mata riqon da Matar ubanta batai Mataba...

Yanda Na'iman ke kuka sosai ya Kuma tada hankalin Zinat jikinta duk yabi ya mutu sbd a fili yake bayyane alamarin daki Na'iman sosai sbd Bata taba kawo hakan zai faruba.


Daqyar allurar ta sanyata baccin qarfi da yaji tanayi tana fizga kadan kadan Kuma badan idonta ya daina tsiyayar hawaye ba.

Fitowa Palo Haj Zinat tayi ta zauna tareda Shiga tunanin mafita dakuma yanda zasuyi ta tafi da Na'ima gidanta su samu zuwa ganin likitanta Dan wannan karon abun yayi nisa saisun hada da ganinsa
Daf Na'ima take da bayyanarda haukarta afili asani...

Daga lokacinda Turaki yasani ta tabbata ko ganin Na'iman bazai Bari kowa yasake yiba sai ya nemar Mata lafiya,
Itakuma idan tabari ta warke sarai yanzu suna cikin gagarumar matsala sbd ba kudi a hannunsu sosai,
Komai nasu yayi qasa sbd wainnan fitintinun dasuketa faruwa
Komai tsaya Mata zaiyi.
##MAMUH#
[7/10, 9:38 PM] +234 704 076 8969: *_Mamuhgee 53_*
Suna Isa asibiti aka karbi Ms Na'ima aka karbeta tareda shigewa emergency da ita sbd ta shaqa hayaqin sosai gashi har lokacin Allurar da akai Mata Bai saketaba jikinta a mace yake Sosai fuskarta da jikinta sunyi duhun hayaqi daya Bata jikinta.,

Zama Turakin yayi a office din Dr faruk daya bude Masa Dan ya zauna anan,
Sai alokacin ya sauke numfashi tareda kallon A Abdoul daya shigo office din da wayarsa a hannu sbd shi yabaro tasa wayar.

Kai tsaye A Abdoul wayar Anne yafara Kira dan sanar dasu Inshallah komai yafara daidaita tunda anshiga da Na'iman gashi dama ba konewa tayiba kawai dai hayaqin ne yashiga cikinta.

Wayar Annen Bata shiga Dan Haka saiya kalla Turakin a hankali ya sanar Masa.

Gyada Kai kawai yayi hankalinsa na rabuwa biyu kowanne da damuwa,

Laylah yakeji wadda ya tabbatarda hankalinta ya tashi Sosai ga yanayinta
Sam baya son abinda yake daga hankalinta gashi ba waya bare ya kirata,
Wayar A Abdoul bazataiji wani dadin wayar da itaba Dan Haka zai hakura harya koma gidan...

Bangare daya Kuma Na'iman ce da matsalolinta,

Tashin hankalin kishinta yayi yawa,
Sam takasa saduda akan lamarin gashi tana neman halaka kanta sbd tunanin banza,

Sam yakasa gane ace Mai cikakken hankali ne zai cinnawa kansa wuta sbd kishi,
To idan ta mutu ai tayi abanza kenan tunda Wanda take kishin tabarsa da wadda take kishin itama,Dan Haka gskia lamarin nata yayi Muni..
Tana warkewa zai maidata Lagos idan Kuma Nan takeso LAYLAH na haihuwa zata koma US ita tabar Mata Nan.

Sai Asuba Ms Na'iman ta dawo daidai bacci Mai nauyin gaske ya dauketa
Suna kokarin baro asibitin Haj Zinat ta iso cikin tsananin firgici da tashin hankali tana ganin Na'iman tafara kuka tana riqe hannunta.

Ganin zuwanta yasa Turakin samun saukin barin Na'iman tareda siddika Dan Haka ya wuce yabarsu agurinta.

Yana tafiya Haj Zinat kallo daya kawai tayiwa siddika datake firgice har lokacin ta Dan jinjina Mata Kai.

Siddika dai Bata samu damar cewa komaiba sbd hankalinta bai gama dawowa jikintaba,
Saura kadan yau tayi kisan Rai takeji,
Meya kaita wannan aikin rashin Imanin akan kwadayi?
Yanzu da Ms Na'ima ta mutu koda ba'a ganesu ba tasan wlh shikenan haukacewa zatai nauyin Rai data kashe bazai bar qwaqwalwartaba.

Hawaye ne Suka ciko idanuwanta jikinta na sake daukan rawa Amma Ta hadiyesu sbd Kar Haj Zinat tagani tasan zuciyarta ta raunana ta illatata gudun kawo Mata matsala,Dan hak ta hadiyesu tareda maidasu suka koma tana kokarin nutsar da kanta.



****Washe gari tunda safe Anne da kanta ta shirya gurin tafiyarwa dasu Na'iman breakfast Wanda su halima suka hada tunda safiyar Dan akai asibitin.,

Sai data duba Laylah Dake kwance tana bacci ta shafa kanta ahankali cikin kulawa da kauna sbd tasan Laylan Bata cikin kwanciyar hankali na wannan abun daya faru kafin ta juya ta fice Suka wuce asibitin itada halima aka bar Ruky sbd Laylah.


Cikin bacci taji qamshinsa na shigar Mata hanci
Ta dan motsa Ahankali tareda Jan numfashin kadan hancinta yasake shaqar numfashin ta bude idanuwanta ahankali tareda saukewa akan fuskarsa..

Zaunen yake bakin gadon Yana kallonta cikin nutsuwa da tsananin sonta dayake bayyane akan fuskarsa da yanayin kallon dayake Mata.

Ajiyar zuciya ta sauke ahankali tareda lumshe ido ta bude ta kallesa hawaye na ciko idanuwanta na kewansa dama kewan kwanciyan hankalinsu ta bude Baki muryarta na rawar son yin kuka tace"

Abbah.

Lumshe fararen nasa idon yayi shima sbd yayi kewan Jin sunan abakinta Dan Haka yakai hannu ahankali ya Kama hannunta ya tayar da ita zaune ajikinsa hannuwansu sarke da juna.

Kallonta yayi cikin kulawa da azabtar da zuciyarsa keyi akan rashin ganinta da jinta ya shafa fuskarta tareda taba cikinta dage gabansa cikin muryarsa data kashe jikinta da sonsa yace"

Lafiyanki kalau kuwa??

Gyada Kai tayi tana kwantar da kanta jikinta ta zura hannuwanta ta rumgumesa tana rufe Ido.

Babyn fa?
Ba damuwan komai right?

Sake gyada Kai tayi Ahankali kafin bude Baki cikin sautin kulawa tace"

We miss you Abbahh.

Hannunta yakai bakinsa yayi kissing ahankali kafin ya shafa fuskarta ahankali Yana cewa"

I love you.

Ajiyar zuciya ta sake ahankali tareda sake lafewa jikinsa,
Sun Jima a hakan Saida kowannensu yasamu nutsuwar zuciya data ruhi kafin ta dago da idonta ta kallesa A natse tace"

Yaya jikin Mum?
Hope bata samu rauni ko matsalaba a koina?

Jinjina Mata Kai kawai yayi Ahankali Yana cewa"

Ba matsalar komai bane hayaqin ne yaso yayi Mata illa Amma tana lafiya.

Ajiyar zuciya ta sauke tareda tasowa daga jikinsa ta zauna daidai ta sauke Kai ahankali tareda sake riqe hannunsa Dake cikin nata murya a Sanyaye tace"

Abbah please kabarni naje gida.?
Mum na buqatan abata space tayi digesting wannan abun,
Ranta ya baci Sosai sbd yanda abun yazo Mata nakuma fahimci Jin zafinta sbd yanda nakejin zafin kishinka na tabbatarda idan nice mutuwa zanyi Abbah idan ka tafi gurin wata,
Dan Haka mum na buqatan abarta abata guri da lokaci ta Gama daukan dumin abin kafin ta sauko...

Dan Allah kabarni naje gida Nima zanfi samun nutsuwa kwana biyu..
Please Abbah.

Girgiza Mata Kai yayi Kai tsaye tareda cewa"

Bazaki ko'inaba kina hankalina zai rabu biyu.
Ki jira idan kin haihu zakije gidan kafin ki koma US.

Riqe hannunsa tayi hawaye na ballewa daga idanuwanta tana kokarin tausar zuciyarta Amma takasa sai kawai kuka Mai qaramin sauti ya balle Mata.

Abbah bazai gane halinda zuciyarta take cikiba,
Tana tsananin sonsa Amma take nesanta kanta dashi sbd tashin hankalin da ake ciki,
Idan tana gidan bazasu taba samun damar magance komaiba har a zauna lafiya,
Gashi saidai taji qamshinsa kawai idan yashigo gurin Anne
zuciyarta na galabaituwa da hakan Wanda shima tasan Yana damuwa da hakan shiyasa bama zai iya tsayawa ayi gyaran ba,

Ita kanta kullum da kwanan tunanin Yana tareda mum Na'ima take
Shedan ya Hana zuciyarta sakat Dan Haka takeson tafiya gidan.

Kukanta yasashi zuba Mata ido Yana kallonta cikin qunci da damuwar ganinta ahalin ya janyota jikinsa ahankali ya rungume sbd baisan Me zai fada mataba,
Hankalinsa bazai taba kwanciya ba idan Bata kusa dashi ko Dan sbd irin wannan fitintinun na Na'ima..

Ahankali ya dagota daga jikinsa tareda Kai bakinsa yayi kissing idonta Dake tsiyayar hawaye ya kalleta ya bude Baki cikin Taushin murya yace"

Ya isa hawayen,
Zakije gida Amma Na'ima na Jin sauki aka dawo da ita gida Zaki dawo kin yarda?

Gyada Kai tayi tana tsayar da hawayenta cikin sanyin jikin kewarsa da zatai.

Kallon kyakkyawar fuskarsa tayi tana Jin dumin hannunsa daya sauka cikin rigarta ya Dora Kan cikinta..

Lumshe ido tayi Ahankali tareda Kai hannuwanta biyu ta kamo fuskarsa takai bakinta Kan NASA ta Dora tareda Kama lips dinta ta tsotsa kafin ta zira harshenta cikin bakin ta kamo harshensa shima ta fara tsotsa.

Lumshe ido yayi tareda matso da ita jikinsa sosai ya karbe kissing din yanayi.

Sosai sukai kissing juna kafin ya saketa Suka ya miqe tsaye tareda daukanta yakaita toilet.

Da kansa ya tayata brush tayi tagama tayo wanka ya tayata shiryawa cikin doguwar riga purple Mai haske suka fito shirye tsaf suka nufa dining.

Suna zama Anne na dawowa Dan Haka kusan atare sukai breakfast din tana Binsu da kallon ikon Allah sbd gabaki daya yau Kam sun manta da Jin nauyinta sbd kewan junan da zasuyi...

Duk tabi tayi wani sukuku komai batajin dadinsa Jin takeyi tamkar zata rabu da 'barin jikinta,
Ga fargabar abinda zata tadda acan,
Ga fargabar yanda zata hada Ido da mahaifinta da qaton ciki a gabanta.,
Dan Haka duk tabi tayi sanyi.

Baiso tafiyar tata ba Amma damuwarta akan son tafiyar yasa yabarta taje din saidai yasan kwana uku zatai zaizo da kansa ya taho da ita yakuma sanarda Mahmoud ba maganar saki har abada a tarihinsa da matarsa Zainab LAYLAH.

Anne dataji maganar tafiyar Bata hanaba sbd Laylan dama tana buqatan matsawa daga wannan fitintinun kafin asamu a sauko da Na'iman sbd wannan damuwar da tashe tashen hankulan zai iya kawo musu damuwa akan cikin Laylah
Basa fata,basa buri Allah dai ya saukar musu da ita lafiya.

Dan Haka itace da kanta ta qarasa hada kayan Laylan sbd tuni A Abdoul ya siya musu tickets itada Ruky Dan Haka qarfe biyu da mintuna aka kaisu airport Suka wuce kafin Turakin yasamu komawa asibiti.



*******Yamma sosai jirginsu ya sauka suka fito Ruky na janyeda akwatinta
Ita hanbag ce kawai rataye a hannunta qarama.

Anty Sa'adah ce tazo daukansu Airport din da lafiyayyar motar Abbansu E-class da Turakin ya siya Masa.

Takowa suke ahankali zuwa gurin motar bayan Anty Sa'adah din ta tarbosu ta zubawa Laylah Ido cikin tsananin farin ciki da murnar ganinta da lafiyayyan cikinta dake bayyanarda tayi gaba yanzu saidai abita da kallon burgewa,

Fatarta da yanayin rayuwarta sun sauya gabaki daya tako Ina,
Komai nata Mai tsari da kudi ne na masu da akwai,
Kallo daya zakai Mata kasan Matar babban mutum Mai abun duniya ce sbd komai nata ya nuna Dan Haka sai murmushi anty Sa'adah keyi tana cewa"

Laylah zamtowa uwa shine babban abin farin cikin danake tayaki murna akansa yanzu.

Dan dago Kai tayi ta kalli Anty Sa'adah din dake tuqi tana maganar sai taji nauyin maganar ta kamata ta saki murmushin yaqe batareda tace komaiba.

Fira suke sama sama har Suka Kama ha Yar gidan qatoton gidan Turaki Dake garin ta waiwayo ta kalli Sa'adah a natse tace"

Anty Sa'adah gidan Zan zauna gurinku.

Dariya anty Sa'adah tayi tana karya kwanar titin da zasu shiga da motar tace"

Tun dawowarmu Muna sabon gidan Abba Turakin sbd wancan namu An rushe ana sabon gini.

Shiru tayi daidai Lokacinda suka iso bakin tangamemen gate din gidan Sa'adah tayi horn Mai gadi ya wangale musu gate din Suka shige.

Gabantane yafara faduwa tana shiga wani yanayi na fargaba duk da ta Saba da komai na dangin Momy Amma wannan karon Jin take fargaba Tai Mata yawa sbd batasan Yaya zasu karbi lamarintaba da cikin dake jikinta ita da akaje da ita da sunan riqo gata tadawo da cikin Mai gida a jikinta.

Babban sashensu Suka nufa Kai tsaye Laylan na tafiya jiki mace zucuyarta bugawa kawai takeyi Amma a natse take Kamar koyaushe.

Babban palon Suka fara shiga da sallama Wanda shine palon farko kafin kashiga kofar da zata kaika palon abbansu da bedroom dinsa da toilet dinsa aciki,

Gefe daya Kuma hanyace da zata kaika wani palon da dakunan Momy Dana Sa'adah suke ciki kowa da toilet dinsa sai wani qaramin dakin kusa da lafiyayyan kitchen dinsu na gidan masu abun duniya Wanda yake na Mai aikinsu ce hadiza.

Suna shigowa babban palon da Abban Dake zaune suka fara cin Karo Yana karatu a jarida idonsa sanyeda farin medical glass ya dago cikin tsananin farin cikin zuwan laylansa ya kallesu Yana sakarwa Laylah murmushi fararen haqoransa a bayyane Dan Bai lura da cikinba farko sbd idonsa akan fuskarta ya sauka Yana cewa"

Barka da zuwa Laylan......

Cikin dake gabanta ya sanyashi qarasa kalmar a rarrabe Yana kallon cikin dakyau.

Tabbatarda cikine a jikinta ya sanyashi kallon Sa'adah daketa washe bakinta cikin farin cikin murnar zuwan 'yar uwarta taga yanda Abban ke raba Ido jikinsa na neman yin sanyi tayi saurin cewa"

Abbah wancan takardan Daman na Laylah ne su Anne sun sani Suma tun lokacin..

Akaro na farko da Abban yaji kunyar yarsa Laylan Dan shi kunyama abin yazo Masa dashi sbd yagama sakawa ransa Raba auren sbd zaunawa yayi yai tunanin Turakin bazai taba karban Laylah Amatsayin matabe duba da shaquwarsa da Zainab uwarta dakuma duba da shine yabiya sadakin aurensu Dan Haka tako wane bangare Laylah dai bazata taba wuce wani matsayinba Bayan na 'yar cikinsa dazai ringa kallonta.....

Yanzu Kuma ga wannan al'amari ya bullo,
Kenan Koda yayi Masa maganar rubuwar shine yasa Bai Masa amsaba Kuma tun lokacin yake ignoring calls dinsa koma ya dauka baya Bari suyi doguwar magana sbd karya Kuma kawo masa zancen rabuwar kenan??

Wani murmushin farin cikine ya saukar Masa,Allah sarki Turaki nawa Ashe 'yar Zainab ce zata zama uwar yayansa shiyasa Allah ya kaddaro musu duk wannan qaddarar sbd wannan Rabon na haihuwa tsakanin Turakin da Laylah.

Kallon Laylah yayi da duk tagama muzanta jikinta yayi Sanyi cikin farin ciki yace"

Qaraso gurin Abbanki Mana Laylah..

Allah sarki Laylan Abbah,
ALLAH na gode maka daka ingantamun rayuwarsu kafin nabar duniya nagani.

Jiki mace har idonta na cikowa da hawayen kunya ta qaraso gurin Abban ta zauna ya riqo hannunta Yana kallonta yafara jero Mata addua tareda sannu da hanya.

Cikin Jin nauyi take amsawa tareda gaidasa.

Shigowar Abdullahi ne cikin farin cikin zuwan laylan ya qaraso Yana Mata sannu da zuwa yana kallonta cikeda kulawa da kauna.

Duk yanda takejin nauyin Saida suka matsa Suka rage Mata Jin nauyin tafara sakewa kafin suka tashi sukayi ciki.

Momy na zaune a Palo Kan lafiyayyar sofa tana waya da tsadaddiyar wayarta sbd yanzu Kam duniya tafara zauna musu tunda Turaki ya sake musu abun duniya suna Jin dadinsu shiyasa yanzu gidan koyaushe Yan uwanta suna hanyar zuwa.

Batasan da zuwan laylanba sbd Sa'adah Bata sanar Mata ba tunda itama yau din tasamu labarin zuwan na Laylan bayanma sun Isa airport kafin su baro A Abdoul ya sanar Mata.

Ido ta zubawa Laylan akaro na farko tayiwa cikinta kallon mintuna kafin ta dauke kanta daga kansu tana kokarin cigaba da amsa wayar saidai Sam taji takasa wayar ta kashe tareda aje wayar gefe tana sauke numfashi....


Momy Ina wuni?" Muryar Laylah data qaraso gabanta ta fada cikin sanyin murya.

Shiru tafara Yi kafin ta daga Kai ahankali batareda ta juyo ta kalli Laylan ba.

Sanin Babu abinda zata qara amsawa koda takuma wata gaisuwar yasa Sa'adah janta Suka nufi dakinta dake tsare da komai na Jin Dadi da kwanciyar hankali.

Zaunawa tayi bakin gado tana sauke numfashi sbd kwanciyar hankalin data gudo Nan Dan tasamu batajin zata samu din sbd kewansa da tunaninsa bazasu Bari ba.
##MAMUH#
[7/10, 9:38 PM] +234 704 076 8969: *_Mamuhgee 54_*
Wanka tayi tareda alwala ta fito daureda towel Mai girma kanta sanyeda hula ta qaraso kujeran dakin ta zauna tareda daukan wayarta dake Hasken shigowan Kira Kuma vidcall ne Dan Haka ta waiwaya ta kalli kofar da anty Sa'adah ta fice kafin ta dauki kiran.

Kallonta yake yanda koyaushe fatarta take fresh,
Ya maida idanuwansa ahankali ya kalli wuyanta dayaga kaman yayi tsayi ya Dan dauke idonsa akai anatse yace"

Haryanxu kinajin damuwa ne?
Yaya gidan?
Zaki iya zama?
Ba matsalan komai?

Ajiyar zuciya ta sauke tareda kallonsa tana kokarin sake fuska sbd tasan tambayarsa ta yanayin rayuwarta dasu Momy yake mgn akai sbd duk da Bata taba sanar dashi irin Rayuwar data taso acikiba sbd koma yayane bata buqatan kowa yasani idan har ba Momynce ta nuna irin zaman dasukeba sbd har abada ita bazata daina daukan momyn matsayin uwa ba.

Sai data nuna Masa Babu komai hankalinta yafara kwanciya tukuna Suka Gama wayar tasamu ta shirya cikin doguwar Riga da hula Mara nauyi sai qamshin turarenta daya Gama cika dakin har Yana Isa Palo da sanyin qamshinsa Mai nutsuwa.

Sallah tayi tana idarwa Ruky da aka sauke dakin hadiza Mai aikinsu tashigo dakin daukeda fruits da aka shiryawa Laylan masu sanyi da tsafta ta aje Mata tareda kallonta cikin girmamawa tace"

Ma za'a dafa madaran ne?Naga basu dashi a fridge na duba.

No kibarshi Fruits dinma sun Isa Inshallah.

Ok Ma.

Juyawa tayi ta fice daga dakin daidai anty Sa'adah tashigo Mata da abinci lafiyayye data dafo Mata da kanta tana cewa"

Ko a aje Miki a dining abincin?

Murmushi tasake tana cewa"

Anty Sa'adah abincin mafa basai kin dauko da kankiba Ruky zata dauko,
Dan Allah ki daina aikin
Gatanan ta ki ringa sakata zatayi komai.

Abincin tafara daukan spoon ta saka cikin plate din fried rice da aka sakawa hanta da qananun Naman kaza sosai ta diba kadan tana kaiwa bakinta tafara ci ahankali sbd ba wani sosai takeson Naman kazaba tunda tasamu cikin Amma sbd kokarin anty Sa'adah taci sosai ba laifi tana gamawa suka fito A rakube ta wuce palon abbanta sbd ganin Momy Dake zaune palon tana amsa waya sbd Yan uwanta yanzu kowa yanayi da ita tunda sunyi arziki.

A palon abbanta tayi dare suna magana tsakaninta da Abbanta ya tambayayeta yanayin zamanta da Ms Na'ima yanzu datasan komai.

Sanar dashi komai tayi saidai Bata sanar Masa yanda Ms Na'iman ta gansu da Abban ba.

Sosai Abban yayi Mata nasiha Yana sake tunatar da ita mahimmanci hakuri da tawakkali akan komai tunda gashinan hakuri da barwa Allah komai yakawo haske da sauyi Mai girma a rayuwarta.

Ko data dawo ciki kowa ya shige Dan Haka Kai tsaye dakin anty Sa'adah ta Isa ta tube tayi Shirin

33 / 36