Noor Albii Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Complete Novels

Chapter   29 / 36

84K to 87K   out of 107.4K words

Ms Na'ima tanada tabbacin wataran Ms Na'iman idan Bata kashe wani ba akan masifar kishi, zata kashe kanta to,
Idan Kuma duk hakan Bai faruba to zata haukace.

Ganin abin na Ms Na'ima ba qarewa zaiyiba ta fidda wayarta takira Haj Zinat ta fada Mata abin dayake faruwa ta kashe wayarta tana ajewa gefe ta nufi fridge tana cewa"

Yau ranar Jin dadina tunda batada kwanciyar hankalin yimun fada Bara na girka abinda nakeso naci abuna hankali kwance.

***Haj Zinat cikin quluwa da lamarin Na'ima da haukarta ta dauki wayarta tafara Kiran Na'iman Amma Bata dagawa,
Tsoki ta saki tareda jefar da wayar Kan gadonta tana cewa"

Na'ima haukarki tafara yawa wlh muna buqatan komawa ganin likitan qwaqwalwanki tun kafin Turaki yagama gano kinada matsalar hankali,
Yanzu da Daren Nan bazan iya zuwa gidanki ba sbd dare yayi Kuma Turakin na gari ba'a Shiga gidan idan karfe bakwai ta wuce matuqar ba Yan gidaba,
Indama baya garine sun Saba take dokar sbd securities na ragewa idan bayanan,
Amma yanzu Yana gari ubanwa zai Bari tashiga gidan da wannan lokacin?

Allah yasa dai haukarki ta tsaya iya bangarenki kafin nasamu safiya tayi nazo karta budemun aiki Turaki ya gano batada cikakkiyar lafiyar qwaqwalwa mun shiga uku Dan kuwa take zai gano duk wani abun da Na'iman keyi kusan itace take dorata akai.

Ms Na'ima kuwa tun tanada karfin iya tashin hankalin ita kadai har qarfinta yaqare ta zube kwance qasan dakinta tana Jin kamar ta cinnawa gidan wuta kowa ya mutu har ita...

***Washe gari tun qarfe 6 na safe ta kwadawa zinat Kira batareda ta damu da lokacinba,

Dayake itama da ita ta kwana cikin ranta ba wani baccin arziki tayiba Dan Haka Kai tsaye ta daga Kiran tana cewa"

Thank God nasamu kin dawo hayyacinki,
Na'ima Ina fatan bakiyi abunda zai Bata Mana komaiba da janyo Mana matsala?

Bata amsa tambayar Zinat din ba tafara koro Mata bayanin abinda ya faru jiyan ta qara da cewa"

Zinat wlh saina tafi tunda ya nuna bayason zuwan nawa na tabbatarda yasan idan naje zansan sirrin dayake boyewa shida Waccar tsohuwar.,
Wlh Zinat idan ban illata ko waceceba qwaqwalwata bazata dawo daidaiba....

Can you imagine Ni Turaki yake cewa idan naje karna Isa ko kofar gidansa......

Wait wait"" Haj Zinat tafada tana tashi zaune daga kwancen datake cikin wani tunanin daya shigeta tana kasa yarda da hakan tace"

Idan yace ko gidansa karki Isa kenan ba tafiyar takice matsalarba zuwa gidan nasane?

Idan hakan ne kuwa to wlh kila bayan barowarki akwai wata a gidan kokuma Laylah Dake gidan tasan wani abun bayason ki koma ta sanar Miki...

Shiru Na'ima tayi sbd yanzu Bata Gane komai Bayan taganta a jirgin komawa, idan ta Isa koma menene ayi sauran tunanin acan...

Kira Laylah ki tambayeta komai gameda gidan kiji idan wani Abu yafaru Bayan barowarki sbd itama bazata yadda acucekiba.

Cikin yanayi na kosawa tace"

Zinat me Laylan zata iya fadamin ko bincikamun wadda sanyin jikinta kawai ya Isa yasa na isa qasar Bata Gama sanin me gidanma yake cikiba bare wajensa,
Zinat Naga Kamar kin daina Gabe baqin cikina dakike maganar tsayawa ayi magana da Laylah....

Cikin gundura Haj Zinat ta katseta da cewa"

Na'ima meyasa kanki yafi na kowa tashewa ne Ana ce Miki ga abinda Zakiyi kina cewa aa,
Idan Kika tafi kin manta abinda yace ne?
Gidansa yace karkije,
Idan Kika tafi a yanda yakeda wata a zuciyarsa yanzu wlh Kika take dokarsa igiyarki daya data rage sakinta zaiyi kila Kinga shikenan kowama saiya huta,
Mama Baraka da bakya kaunar komawa gurinta saiki Koma can Dole Dan ayanda kasuwanci yake rawar Nan yanzu anata samun asara tako Ina wlh bazaki wafta kudi acikiba ki siya gida ko kamawaba,.

Dan Haka idan Zaki nutsu ki nutsu mubi komai a daki daki
A hannu zamu Kama komai kafin mu lalata koman kuma.,

Yanzu kiyi hkr ki aje maganar tafiyar a gefe kizo Nan muyi magana a tsanake idan yasan wata baisan wata ba ai.

Ba Haka Na'ima tasoba Amma Kuma tasan yanda Zinat ke cewa ayin koyaushe itace Hanya Mai bullewarsu Dan Haka Dole tabar maganar tafiyar saidai Bata fasa fitaba tunda uwar safiyar ta fice daga gidan cikin motarta _Mercedes Benz C-class_ da Bata cika hawaba ta fice gidan cikin wani Irin speed dayasa har securities din gidan Gane madam din na cikin bacin Rai.

Turaki dake zaune cikin sofa a dakinsa tun bayan Gama sallar asubarsa Yasan dama ba zataji maganarsa ba sbd idonta yagama rufewa da taje din...

Wayarsa Dake gefensa yakai hannu ya dauka a hankali tareda saka Kiran Numbern A Abdoul Dake qasan ta Laylah daya Gama waya da ita ya Danna kiransa cikin nutsuwa.

Cikin bacci A Abdoul yaji wayarsa na ringing ya Dan mirgina tareda Kai hannu inda wayar take ya daga yana duba Mai kiransa wannan lokacin..

Ganin sunan TURAKI akai yasashi sake Ajiyar zuciya Dan dama yasan bayan Turaki Babu Wanda zai Masa wannan Kiran yanzu
Dan Haka ya tashi zaune Yana wartsakewa daga bacci cikin girmamawa ya daga wayar Yana cewa"

Good morning TURAKI.

A gajarce ya amsa cikin nutsuwa ba hayaniya tareda cewa Kai tsaye"

Ayiwa Zainab komai na Shirin tafiya duk ko yayane inason ta baro Atlanta ta sauka Lagos zuwa jibi.

Yes Turaki Inshallah angama.

Kashe wayar yayi tareda maidata gefe ya ajiye Yana maida kansa ya jinginar? jikin kujeran dayake zaune tareda rufe fararen idanuwansa dasuka kasa samun komai face ganin Laylah ta iso garesa cikin koshin lafiya Dan baisan iya abinda zai iya faruwa idan Na'ima ta Isa qasar ta taba lafiyarta Dana cikin jikinta.

Ms Na'ima ma data Isa gidan Haj Zinat kasa Shan Koda ruwa tayi sai data Kira Laylah Dake fama da kanta ta ringa jeho Mata tambayoyin dasuka sakata shiga fargaba da shakka saidai duka amsoshin data bawa momyn basu gamsar da itaba Dan Haka ta kashe wayarta tana cewa"

Dama nasan ba???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? wani amfani ne da Laylan ba kikace sai ankirata gashinan na batawa kaina lokaci da Rai abanza.

Da qyar da dabara Haj Zinat tasaka Ms Na'ima Shan tea kafin ta banka Mata maganin qwaqwalwan datake akai aikuwa tana shansa ba jimawa baccin Dole ya dauketa ta zube a gadon Haj Zinat Dake cikin lafiyayyar bedroom dinta tana baccinda ba shiri.

Bata farka ba sai yamma wanda daman Haka maganin yake wani irin mugun bacci yake sanyata harsai qwaqwalwanta ya dawo Yana Dan aiki daidai,
Hakama da mutuwar jiki zatai kusan wuni biyu sbd bazata samu qarfin wani tashin hankalin ba shiyasa batason maganin idan tanajin masifarta Amma so da yawa Zinat ke yaudararta tabata gashi yanzu Bata iya wani dogon tashin hankali sai bayan kwana biyu kuma Dan Haka ta tattara Fahad babban Dan Haj Zinat din ya dawo da ita gida.

Tana Shiga bangarenta tun a Palo siddika dake Mata sannu da zuwa tana karban handbag dinta ta fahimci maganintane ke aikinsa Dan Haka wani dadi ya mamayeta tana Jin kwanakin duka na Sa'artane Dan kuwa yanzu rayuwar Jin Dadi da kwanciyar hankali takeyi a gidan tunda masifar gaban Ms Na'iman ta isheta da Bata lokacinta
Dan Haka daki takaita ta kwanta ta fito tareda janyo Mata dakin ta wuce kitchen tana cewa"

Faduwar wani tashin wani.

Kwananta biyu Bata tako ko kofar fita Dana bangarentaba tana fama da kanta sai data cika kwanan biyu cif tadawo daidai ta nufa Sashen Anne ta gaidata Kamar Dole ta fito Takoma bangarenta tana wayoyinta da Zinat data dagawa hankali akan ita ta tafi Ta binciko musu sbd zaman Nan a baibai bazai kaisu koinaba sai gurin baqin ciki da bacin Rai sbd suna Bata lokaci cikin Yana da uwar cikin suna sake samun qarfi tunda ciki zaina cigaba da girma.

*****
Qarfe 5 na asuba jirginsu ya sauka a Murtala Muhammed International airport dake Lagos,

Sanye take da _Moja majka_ Abaya maroon Mai shaking material
Kanta nade cikin Marron veil qarami na Abayar sai black Gucci suede loafers a qafarta da qaramar _Bottega veneta_ small shoulder bag Dake rataye a kafadarta,fuskarta tayi haske sosai ta yanda ko kafin idonka ya sauka a cikinta zakasan tana daukeda juna biyu dayayi Mata kyau matuqa,

Bata qara wata qiba ba hakama Bata rameba shiyasa cikin ya fito sosai iya watanninsa...

Wani numfashi ta sauke lokacinda ta shaqi iskar Nigeria ta lumshe ido cikin gajiya da Yar yunwar Dake damunta ta fito Ana biyeda ita da luggages dinta.

Tana fitowa Wanda idonta yafara sauka akansa ne tsaye Yana waya cikin black Rugby's Riga da wando da jacket Mai girma datakai Masa har gwiwa...

Duk da Yana sanyeda face mask black da hular sanyi,
kallo daya tayi Masa tagane shine duk koina nasa kusan a rufe yake Kuma Bata taba tunanin zai iya zuwa airport da kansa tarbonta ba
Da haka wani sanyi ne ya mamaye zuciyarta har batasan idonta Yana cikowa da hawayen kewarsa dataiba da farin cikin ganinsa...

Ahankali take takowa idonta cikin nasa daya zuba matasu cikin kallo Mai wuyar fassarawa,

Akan cikinta daya turo Ana ganinsa da kyau ya sauke idanuwansa kafin ya ware Mata hannuwansa ahankali Yana cewa"

Finally.

Ahankali tashige jikinsa tareda rungunmesa da sauri hawayenta suka sauko tana cewa"

Abbahhhh.

Hannunta ya Kama A Abdoul ya wuce gaba tareda kayanta aka shigar mota kafin ya bude motar Turakin da kansa ya bude Mata motar yana riqeda hannunta ta shiga kafin shima ya Shiga A Abdoul yaja motar suka bar airport din.

Hannunta na cikin nasa a sarke yake kallon cikinta Yana kallon fuskarta Dake glowing tana daukan idonsa da hankalinsa..

Wani malalacin murmushi ya saki Mara sauti ko kadan alokacinda idonsa yagama shawagi Kan cikinta Kuma maganar Abbanta ya fada Masa alokaci daya.

Dagowa tayi ta kallesa ganin murmushin daya sake,
a hankali ta bude Baki zatai magana ya Dan rufe Ido Yana girgiza Mata Kai alamar Bata buqatan magana.

Lumshe fararen idanuwanta tayi tareda Dora hannunta daya Kan hannuwansu dake sarqe cikin kulawa da son abun Dake ranta ta bude Baki ba sauti tace"

I love you Abbahh.

Wannan karon murmushinsa sai daya bada sauti kadan sbd shigarsa da kalmar Tayi da dagashi sai itane bazata hadiye yawun datake bakinta lokacinda tafada Masa wannan kalmar saiya shanyesu tas Dan kuwa sauran zaqin kalmar na cikinsu...Dan Haka sai kawai ya sake damqe hannunta cikin nasa cikin kulawa Yana Dan dauke Kai daga kallonta ya maida Kan wayarsa da aka sake Kira.

Lafiyayyan gidansa Dake Lagos din suka Isa Madam sarat Dake gidan tareda sabuwar Mai aiki daya da aka kawo Ruky sungama gyare koina a gidan sai qamshi da Sanyi ke tashi koina
Ga aikin breakfast dasuke Yi cikin qwarewa da mutsuwa...

Hannunta cikin nasa Suka shigo palon bayan A Abdoul ya miqawa Madam sarat akwatinan Lv0 na Laylan ya juya ya nufi sashensa dake gidan dan komawa baccin Dake cinsa.

Madam sarat kallo daya tayiwa hannuwansu dake sarqe ta dauke Kai tana neman Yar rudewa dai kafin ta Kama nutsuwarta sukai ciki da kayan itada ruky tana kyafta idonta Dan tabbatarda cikin Dake gaban Laylan da alama da Turakin ne tunda ga hannuwansu a sarqe...

To kodai Ms Na'ima ta rasu ne?

Da wannan rudadden tunanin Suka kai kayanta duka makeken bedroom dinsa daya Dake palonsa na sama Suka sauko.
##MAMUH#
[7/10, 9:37 PM] +234 704 076 8969: *_Mamuhgee 47_*
Parking motocinsu sukai a harabar gidan,

A Abdoul ne yafara fitowa motar dayake ciki zaune a gaba sai Ruky a sit din baya,

Motar da Turakin suke ciki ya nufa da niyar bude Masa sai gashi ya bude da kansa tareda zuro qafafunsa Dake sanye da black Camilo Italian leather loafers ya fito motar.

Hannu ya miqa Mata ahankali ta Kama zuciyarta na bugawa ta fito motar sanyeda Ash turkish abaya da light Ash gyale akanta nade.

Handbag dinta ma qarama ce sosai sbd yanzu batason masu girma suna damunta,

Ahankali ta zare hannunta daga nasa Bayan fitowarta motar sbd tasan yanzu Kuma ita dashi sai kallo daga nesa tunda suna gida daya da mum Na'ima gakuma Anne.

Kai tsaye Sashen Annen Suka nufa Ruky da A Abdoul tuni sukai gaba da Suitcases dinta zuwa bangaren Annen,

Ahankali jiki a matuqar sanyaye take tafiya gashi kamarma yanzu tafi ganin girman cikin nata,

Dan Haka duk tabi ta sake shiga halin firgici da damuwa...

Suna gap da Isa su shige babbar kofar dazata sadasu da babban palon bangaren Annen motar Ms Na'ima ta sako Kai harabar gidan ita ke tuqawa da kanta Haj Zinat na gefenta zaune
Kowaccensu cikin Shiga ta alfarmar manyan Mata Kuma matan masu abin duniya...

Motacin Turakin da aka daukosa daga airport dake sarari a pake ta kalla kalla batareda idonta yakai Kan gabansuba hanyar Sashen Annen
Tana kokarin parking tace"

TURAKI ya dawo kenan?Amma dazu da mukai waya baicemun yau zai dawo din ba,
Zinat shiyasa nake fada Miki Turaki ya......

Haj Zinat da tun shigowarsu idonta ya sauka kansu Laylan dake kokarin Isa kofar bangaren Anne
Batareda ta dauke idontaba akansu cikin zallan mamaki da shakkar abin datake gani a idonta tace"

Na'ima Kamar fa mace Mai ciki ce tareda turakin gasu can zasu shige gurin Anne......

Baammmmm.....wata irin qara Mai qarfi ta tashi na buga motar gabansu da Na'ima tayi ba shiri sbd zancen Zinat...

Ware idonta tayi a bangaren daidai sun sunshige lokaci daya atare....

Bata kashe motarba barewa tsayawar ta bude kofa tana kokarin fita Zinat cikin tashin hankali biyu da biyu ta riqota tana cewa"

Tsayar da motar ki kashe tukuna kafin ki kashemu da sauran kwananmu a gaba..

Tsayar da motar tayi Amma Bata tsaya kashewaba ta fito
Tana cewa"

Zinat wlh itace ya kawo gidan,
Anne ta sane kenan,
Aikuwa yau za'ayi budaddiyar wasika kowa ya dauki sakamonsa....

Gaba tayi har tana tuntube saura kiris ta kife,
Haj Zinat da sauri ta fito tabiyo bayanta batareda itama ta tsaya kashe motarba sbd Ganin ko ganin gabanta Na'iman batayi,

Tasan Sarai Yau mahaukaciyar hauka zata buga idan tayi Ido biyu da Matar Nan,
Yau Babu maganar aro hauka koina original tata din zata buga abarta,

Itakuma bazata yarda ba Na'iman tayi abinda zaisa agane lalurarta gwara ta bita ta danneta duk da itama dazata samu damar idonta idon Matar data rigasu daukan cikin Turaki da hannunta zata halakar da cikin kafin ita Daga baya sayi lokacinta.


Anne ce zaune a Palo tana Amsa wayar Sa'adah cikin kwanciyar hankali nutsuwa,

Palon sai qamshin Turaren wutar YERWA INCENSE yake tashi tareda sanyin Ac da hayaqin Oud Dake fita ahankali daga qatuwar humidifier Dake can gurin hanyar kofar shigowa palon.

Shigowar A Abdoul da ruky Dake janye da set din akwatinan Louis Vuitton guda hudu yasata kallonsu da mamaki akan fuskarta,

Ruky data gefe tana gaidata cikin tsananin girmamawa ta kalla kafin ta kalli A Abdoul din shima tace"

Abdoul-Hameed baqi mukayi ne da Kaya Hakan?

Fara gaidata yayi cikin girmamawa da sakewar Dake tsakaninta dashi yace"

Ms Laylah ce ta dawo..

Da sabon mamaki Mai girma ta Kuma kallonsa murmushi na sauka Kan fuskarta tace"

Laylah Kuma?
Zuwan bazata ba sanarwa....

Shigowar Laylan ne yasa ta dakata da maganarta tana zuba Mata dukkanin idonta da hankalinta saidai har lokacin murmushin fuskarta Bai gusheba saima fadada da yayi
Harma batasan ta zubawa cikin Laylan idoba.

Kunya Mai tsananin girma ta Sanya idanuwan Laylan cikowa da hawaye tana Sunkuyar da Kai qasa a sanyaye take takowa..

Halima ce data fito kitchen tagansu
Aikuwa bakinta yakasa rufuwa da sauri ta ja kayan tana cewa Ruky ta biyota da sauran kayan
Suka nufi dakin Laylan tun na farko dake guri daya Dana Sa'adah
take halima tasa Ruky din ta Kama aiki suka hau gyaran dakin dukda yananan da komai na tsari da buqata acikinsa.

Sir Turakin kuwa qarasowa yayi zai gaida Annen ya wuce nasa bangaren,

Ita Kuma a silale ta nufa inda Annen take zaune tana kokarin Nemo muryarta data maqale a maqoshinta zata gaidata Ms Na'ima ta shigo palon Kai tsaye ta sallamar da kwata kwata batamasan Yaya ta fito abakintaba..

Yana ganin Na'ima ya dakata daga inda yake tsaye Bai qarasa gurin Annenba ya tsaya kallonta fuska a kame hankalinsa kwance.

Anne kuwa tashi daga zaunen datake tayi Tana qarasawa gaban Laylan Kai tsaye tace"

Wuce ciki kifara hutawa tukuna.

Duk yanda take tunanin tashin hankalin fuskantar mum dinta abin ya wuce hakan a zuciyarta sbd daukewa numfashinta yayi Jin muryar mum din? daga bayanta,

Yanda zuciyarta ke harbawane yasa takasa juyowa ta tsaya cak a inda take tareda rufe idanuwanta hawayen dasuke ciki suka gangaro har sai dataji saukan muryan Anne datace ta wuce ciki.

Daga kafa tayi zata wuce batareda ta juyoba har lokacin,
Cikin tsananin bacin Rai Mai girma daya sake rufe Ran Ms Na'ima tace"

Laylah? Tsaya agurin,
Yaushe Kika dawo?
Meyasa Baki fadamun ba?
Wacece kuka dawo da ita tareda Turaki??

Cak Laylan ta tsaya agurin cikeda mamaki da fargaban yanda mum din tagane itace zuciyarta na karyewa da abubuwa da dama,

Har cikin ranta tasan Bata kyautawa riqon da Mum tayi Mataba,

Ta wani bangaren ta yarda da tabbas taci Amanar mum sbd koma yayane tayi Mata riqon 'ya ba irin Wanda ta taso acikinsaba Amma ace itace take dauke da cikin mijin Mum.,

Da wane idon zata kallo mum data kamu da tsananin son Turakinta Mai tsananin datake Jin rabata dashi shine mafi Munin illar da zaaiwa rayuwarta....

Cikin fushi Ms Na'ima ta tinkari Laylan idonta rufe da bacin ran wadda suke boyewa da Turaki yazo da ita tana cewa"

Magana nake Miki amsa Zaki juyo kibani Raina abace yake
karki dora wani laifi akan wannan na zuwan da kikai batareda kin sanar dani b......

Hannunta Turaki ya riqo akaro na farko tun shigowarsu gidan daya bude Baki Yana kallon cikin idonta Kai tsaye murya a kame yace"

Ki nutsu banason hayaniya Anan,

Wuce,koma kije bangarenki....

Qwace hannunta tayi da qarfi tana kallon Anne idonta jajir tace"

Anne gwara ayi komai a gabanki tunda da alama kinsan komai,
Turaki Wlh nasan yanada wata macen daban bayan Ni da waccar dayar,

Najima da Dani Dan Haka gwara a fadamun meyasa za'a rufeni akan wani auren daya Kuma.....

Just shut up Na'ima,
Ki fita kibar Nan nace...

Gurin Laylah takuma nufa gadan gadan tana cewa"

Wallahi bazan fita ba sai nayi magana da Laylah kokuma tabiyoni muje ai dama nice mum dinta,
Nice nake riqonta,
Ta wuce muje da kaina zanyi magana da ita.

Kallonta Anne tayi cikin kulawa kafin tayi mgn
Baice komaiba ya Kama hannun Na'iman ya juya da ita
yana ganin Haj Zinat bayansu ya sakar Mata ita Kai tsaye yace"

Jata ku tafi.

Kama hannun Na'ima Zinat tayi dukkanin wutarta na daukewa da zallan mamaki da firgici harma da tashin hankali dan kuwa kallon tsaf dataiwa Laylah daga bayanta sbd a hangi ciki a jikinta wallahi.....

Kokarin Jan Na'ima takeyi Amma ta fizge da qarfi kafin kowa ya Ankara ta Isa gurin Laylah Dake tafiya zuwa daki Tasha gabanta....
##MAMUH#
[7/10, 9:37 PM] +234 704 076 8969: *_Mamuhgee 48_*
Cak ta tsaya gaban Laylah tareda mutuwar tsaye tana fiddo dukkanin girman idanuwanta afili tana kallon ciki

29 / 36