Noor Albii Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Complete Novels

Chapter   1 / 36

1 to 3K   out of 107.4K words

??????>?? ? ????????????? ?
?
? ? ????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? p 

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Root Entry???????? ?F? WordDocument????1?0Table?????????Data
????????????????????? P?vKSKS?1?;? ???????rr????
+ ? ?rrrrrrrrt$???*rrrr????r?r??rr? ?^`????^Normal d??,CJmH sH nHtH_HOJPJQJ^JaJTA`????TDefault Paragraph FontOJPJQJ^Jfi`????f Table Normal :V ?4?
l4?a? OJPJQJ^J(k`????(No List ;? ?(?<?W?[
dt?j???L?l?????t?%?7R jll&}?????\?|??[7/10, 9:09 PM] +234 704 076 8969: *_NOOR ALBI_*
_Hasken Rayuwata_

*_Mamuhgee_*

1

*_Bismillahir-rahmanir Raheem_*

Kokarin komawa ta zauna Kan kujerar robar Dake gaban wheelchair dinda mahaifinta yake zaune akai tayi bayan ta aje cup din data Gama basa magani abaki Kan qaramin table din Dake gurin ta dago idanuwanta ahankali cikin nutsuwa ta kallesa batareda tace komaiba ta tsawon mintina biyu kafin ta Dan motsa Bakinta cikin wata nutsuwar ta sakar Masa murmushinda yake narkarda zuciyarsa da tsananin tausayinta da qaunarta Dan kuwa yanajin radadi da zafin dukkanin murmushinta Wanda yariga yasan ba komai cikinsa face damuwa, kadaici,maraici da rashin uwa dakuma rashin uba dukda shi uban gashi a raye Amma tamkar baya raye yake Dan baida wani abun dayake iya yimata bayan nuna Mata zallar qaunarta daga zaune sai kwance.

Ganin irin kallon dayake matane Wanda koyaushe yake nuna gazawarsa amatsayi na uba
Ita Kuma Bata taba yimasa kallon ya Gaza din sbd tasan hakan qaddararsu ce su duka tun daga kan mahaifiyarta da Bata Raye har Momy wadda take ganin itace tafi cutatuwa ato kowane bangare na rayuwarsu.

Sauke idanuwanta tayi daga kallonsa tareda Kai hannu ta zari tissue Mai Dan yawa tahau goge Masa gefen rigarsa da ruwan maganin masu kala suka zuba ta sauke siririn numfashi ahankali ta bude Baki ta furta"

Abba!!
Kadaina kallon kanka da yanayinka amatsayin ka cancanta hakan sbd abunda yafaru,
Kadaina kallon kanka amatsayin Wanda ya lalata rayuwar yarsa yakasa Mata komai bayan Kaine komai nawa,
Nice rabon haihuwata da zuwana duniya ya tarwatsa kwanciyar hankalin rayuwark......

Rintse idanuwa da yayi cikin Jin dacin? zancenta yayi daidai da dafata da akai da hannuwa biyu a kafadarta Dan hanata qarasa zancen.

Ahankali ta sauke ajiyar zuciya? batareda ta dagoba
ta Dan sake sauke numfashi Mai sanyi da rashin sauti kafin ta waiwayo da kyakkyawar fuskarta
idanuwanta basu sauka Kan Yar uwarta Kuma Antynta data dafata sai akan Momy suka fara sauka wadda ke tsaye bayan Anty SA'ADAH din kyakkyawar fuskarta ta Kamar yanda tasanta tun tashinta a daure Babu sakewa Babu fushi sai yanayinta dake sake nuni da har lokacin kallon Rabon daya lalata rayuwarta data yarta take Mata.

Ahankali ta dauke kallonta daga kanta tana Mai Dan Sunkuyar da kanta? ahankali tareda miqewa tsaye daga gurin ta raba gefen Anty Sa'adah ta koma bayanta ta tsaya cikin tattausan muryanta batareda tasake kallon momynba cike da biyayya tace"

Barka da safiya Momy.

Kamar yanda tasani tun tasowarta harzuwa shekarunta na yanzu datake dasu Momy Bata taba amsa gaisuwartaba wanda hakan sabone agareta Kuma baya damunta Kamar yanda ko so daya Bata taba tsallake ranar gashetaba Dan kuwa Bata taba ganin laifi ko Jin haushin momynba,
Kallon uwa Kuma mariqiya take Mata tareda wani girmanta Mai tsanani datake gani.

Qarasowa cikin palon gabaki daya momyn tayi cikin tafiyar nutsuwa ta Isa Kan kujerar dake gurin ta zauna sai alokacin ta kallesa dakyau murya? natse tace"

Barka da safiya!

Shiru sukayi dukkaninsu sbd sanin ba wani iya mgn Abban keyiba musamman da kwana biyun jikin nasa ke Dan sake rikicewa duk da tsawon shekaru masu yawa daya debo daga zaunen da kwancen.

Saida yamata kallon mintuna kamar yanda yasaba yimata kullum kafin ya iya daga kansa ahankali cikin wani irin yanayi na sanyi da jikin dayake Dan ji.

Numfashi Mai sanyi ta sauke ahankali kafin ta dauke kallonta daga kansa cikin sanyin murya tace"

Dr Abbakar yakira akan Yana hanyar qarasowa kana tunanin hakan zai.....

Dakatawa tayi da maganar Tareda yin shiru kafin ta Dan waiwaya ahankali ta kalli inda Sa'adah ke tsaye batareda tace komaiba
Suna ganin hakan suka nufa kofa itace agaba jikinta na qara bayyanarda sanyinta Amma taurin zuciyarta na sake boye hakan.

Kai tsaye dakin anty Sa'adah din Sa'adahn ta jata suka shiga ta nuna Mata bakin gado da ido tana cewa"

Zauna anan Ina zuwa.

Fita tayi ta nufa kicin ta duba abincin da akai Karin safiya dashi taga sauran doyar Dake cikin kular da alama ba'aciba
Ta dauka plate ta zuba Mata farar doyar tareda soyayyar jar miyar dataji albasa ta bude Dan qaramin fridge dinsu daya Dan tsufa Amma Yana aiki ta dauko Mata pure water daya masu sanyi ta nufo dakin ta qarasa har gefenta ta zauna ahankali tareda Kiran sunanta cikin tattausan lafazin dake nuni da irin tsananin son datakewa Yar uwar tata Wanda bayan Momy data haifeta Babu Wanda takeso kamarta.

*_LAYLAH_* Takira sunanta cikin kulawa da sautin Mai Dan girma Kai tsaye tace"

Ahakan Zaki zama likitan kina skipping lokacin cin abinci?
Cinye ki tashi kije ki gyara palon Abba kafin baqinsa suzo.

Kamar yanda yake dabiarta dagowa tayi ta kalli Anty Sa'adah din kadan tareda Dan yaqen guntun murmushi tana daukan plate din tafara cin abincinta a natse.

Qura Mata ido anty Sa'adah tayi tana qarewa kyakkyawar fuskarta zuwa yanayin sanyi da nutsuwarta kallo,
Duk yanda kakai qarshe da sanin halin mutum da yanayinsa bazaka taba iya gane halinda zuciyar *_ZAINAB LAYLAH_* take cikiba,
Yarinyace Mai tsananin zurfin ciki da wata irin juriya da tawakkali,
Bata bayyanarda fushi ko bacin Rai,
Batada hayaniyar da zaka Kuma gane farin cikinta
Abu daya ke bayyanarda halinda zuciyarta ke ciki ko yanayinta shine murmushinta Wanda shine abinda ke bayyanarda zallar 'dacin datake ciki.

Mahaifinta yayi auren sirri da Yar uwar dangin nesa sosai ta Babban amininsa da baida tamkarsa sun taso tare sun girma tare tarin Arziki,suna da daukaka ya rage kusancinsu sbd nisa da aminin nasa yai Masa bawai Dan sun rabu ba haryanxu suna tare matuqar Aminin nasa Yana qasar,
Yayi auren sirri ne da Yar uwar dangi ta Aminin nasa batareda sanin matarsaba wadda dukkanin yardarta,soyayyarta,kaunarta da gatanta suna kansa sbd tsananin yardarta dashi dari bisa dari,
Bata taba zarginsaba ko kawo tunanin zai iya cin amanarta ko ha'intarta takowane bangare musamman sbd sunada 'yarsu daya tak dasuke tsananin so da kauna Sa'adah.,

Saida ya shekara shida da auren ZAINAB cikin sirri Da tsananin so da kauna Mai qarfi da baya iya rabuwa da ita kafin Allah yabata cikin dayayi sanadiyar fitowar auren.

Batada labarin aurensa saidai tasamu labarin hadarin daya samu Mai tsananin gaske akan hanyarsa takai Matar asibiti tana nakuda a jahar daba tasuba,
Akaron farko da wani babban alamari ya jijjiga izzarta datake ganin tanada ita a zuviyar mijinta duk wata yardarta da soyayyarsa ta rushe tareda wani irin kunci daya cike zuciyarta tsawon shekarunda take dakonsa har yanzu,
Batasan auren mijintaba saidai gawar matarsa tagani da lafiyayyar jaririya da aka bar Mata wadda kallo daya takasa Mata sbd batason shedan ya ribaci zuciyarta ta cutatarda 'dan kowa,

Bata taba son 'yar ba wadda taci sunan mahaifiyarta Kuma sunanta wato *ZAINAB*
Bata taba sontaba kamar yanda Bata taba Jin qintaba,
Bata kallonta sbd kada ta cutatar da ita,
Ita ba jahila bace tasan Babu haqqi akan yarinyar na abundaya faru saidai Kuma takasa Hana zuciyarta yimata kallon Itace asalin dalilin tarwatsewar rayuwarsu duka sbd rabon haihuwartane yayi sanadin komai,
Tun accident din abban yarasa qafafunsa a zaune yake cikin kujera daga zaune sai kwance tsawon shekarunda sukaja masu tsayi sosai,

Bai taba ganin laifin momy ba Amma Kuma Bai taba daina rokontaba daga kwancen akan ta samu wani fili kadan a zuciyarta da zata saka Masa Laylah sbd batada kowa saishi shikuma Haka tasa qaddarar tazo baida wani Abu dazai iyayi Mata amatsayin uba,

Rayuwar Laylah rayuwace Mai cikeda zallan kadaici da maraici,
Tunda tafara wayo taga yanda Momy Bata taba kallontaba bare amsa ko gaisuwarta Amma Kuma Bata taba hantarartaba saita taso cikin juriya da rungumar rayuwar ahakan tareda yarda da cewa tabbas itace sakamakon cin Amana da haincin da akaiwa Momy Wanda ya rusa rayuwarta da kwanciyar hankalinta na gidan aurenta Dan kuwa tun lokacin Momy ta Rasa miji tunda yakoma baida wani amfani agareta da yarta tun daga kan auratayya har Kan sauran haqqoqin.,

Da wannan zuciyarta take kasa Jin 'dacin Momy sbd takowane sashe tabbas itace mummanar qaddarar data Bata rayuwarsu shiyasa ta sadaukar da kanta da rayuwarta gurin bautawa Momy da anty Sa'adah ko zata iya biyansu ta wani sashen da abinda abbanta da mahaifiyarta da Bata Raye sukai musu,
A rayuwarta cinta da Shanta tareda karatunta momynce ta dauka nauyi abisaga aikin wahalar datake musu tun bayan data girma aka sallami Mai aikin data raineta harta girma ragamar aikin gidan tadawo hannunta tun daga kan girki da tsaftar gidan,

Sam rayuwar Momy a baude take wanzuwar laylah a rayuwarta sbd tuni ta Rasa annashuwa da dariyarta harma da murmushinta,
Rayuwarta Takoma ta wata irin cunkusashiya kasancewarta cikin mutane masu tsananin riqo a zuciya shiyasa duk tsawon shekarun Bata tabajin sassaucin abunda takejiba akan al'amarin.

Babban abunda yake tattareda rayuwar Layla na nutsuwa da kwanciyar hankali shine tsananin kauna da soyayyar da mahaifinta ke Mata Mai tsanani da wadda 'yar uwarta Anty Sa'adah ke Mata Dan kuwa anty Sa'adah itace gatanta a fili da boye sbd itace ta tsaya Kai da qafa agurin mahaifiyarta ta roqu alfarmar bawa laylan damar karatu bisaga neman alfarmar zata karba ragamar aikin gidan,
Da wannan Laylah tasamu tayi karatu a makarantar gwamnati Mai dama dama harta samu ilimin bokon datake dashi sabanin ita Sa'adah datai karatun private school Mai kyau,

Anty Sa'adah ce gatanta a duk abinda ya danganci haqqin dake rataye akan iyayenta na kula da ita shiyasa koyaushe Abba ya bude idanuwansa akan Sa'adah yake Mata godiya cikin ganin qimarta itada momyn sbd koma yayane da dukiyar momyn Sa'adah ke yiwa Laylah hidima Wanda itama momyn rufin asirine kawai na 'yar kasuwancin buga buga datake Dan tallatawa rayuwar yarta da abban da yarsa dasuka zamar Mata wani babban jarabawan rayuwa.

Mahaifiyarta ta rasu tabarta a ranarda ta haifeta Dan Haka batasan wani shaquwaba ko sake tayi Wasa tareda wani,
Mahaifintane Kuma kwance ta bude ido tagansa,
Anty Sa'adah Kuma kallon wadda ke tallafe da rayuwarta take Mata duk da a zuciyarta matsayi da girman kaunar datakewa anty Sa'adahn daban ne.
#MAMUH#

*_NOOR ALBI_*
*_Rabo sai Mai shi...Bata taba saka ran shigowarsa ko zama jigo a rayuwarta ba sbd kallon datake Masa amatsayin Uba,Abokin mahaifinta,Amininsa Kuma Mariqi.!_*
*_Soyayyace tashiga tsakaninsu Mai girma da qarfi batareda sun ankare da hakanba bayan dukkaninsu sun haramtawa kansu hakan,Shin ta yaya zata kalla mijin yayarta,Yar uwarta wadda ta riqeta tamkar yanda uwa me riqon 'da amatsayin nata mijin?_*
*_Qaddararsu wannan kokuwa itace rabonsa tun farko?_*
*_NOOR ALBI Hasken rayuwata_*
_Littafina dayazo muku da wani salon na dabam Wanda soyayyarsa ta kere sauran labaraina,salonsa ya bambanta da sauran,nishadinsa da shauqinsa na musamman ne_
_Fata dai ku kasance taredamu kuji zafi zafin damuka dawo muku dashi_
*_NoorAlbi#MAMUH_*


*_FOLLOW ME@_*
_Mamuhgee_
Wattpad
*_ArewaBooke@_*
_Mamuhgee_


*ZAFAFA BIYAR*


*_KUFAN WUTA_*
_Safiyya Huguma_

*_BAQAR INUWA_*
_Billyn Abdul_

*_RAYUWAR MACE_*
_Hafsat Rano_

*_MASARAUTA_*
_Miss Xoxo_

*_NOOR ALBI_*
_Mamuhgee_

Bilkisu Ibrahim Musa
1487616276
Access bank

Number shaidar biya=?G?
*_09032345899_*

*KATIN MTN*

09166221261
[7/10, 9:09 PM] +234 704 076 8969: *_NOOR ALBI_*
*_Mamuhgee_*


3
Tana zaune tsakar gidan tsaye bakin kicin tana wanke hannu a fanfo Dr Abbakar yafito ya fice Tai Masa asauka lfya cikin biyayyarta
Ya amsa Mata cikin kulawa shima ya fice.
Qarasa wanke hannayenta tayi sbd miyar abincin da anty Sa'adah ta zubar a Palo batareda sani ba tagama kashewa shine take wanke hannun,
Kofar palon abban ta nufa Kai tsaye tashiga da sallama
Har lokacin Yana yanda Dr Abbakar yafita yabarsa cikin zurfin tunanin abinda ke addabar zuciyarsa da shawarar dayake nanatawa kansa akan ya yanke Dan inganta rayuwar yarsa ko baya Raye ko Yana raye
Tabbas idan tana qarqashin inuwar Amininsa Kuma Aminin mahaifiyarta zata samu gata da kulawa tareda samun Amintacciyar rayuwar kwanciyar hankali.

Kai tsaye gurinda flask din abincinsa yake ta nufa tafara daukan flask din ta bude wani tiririn zafi da qamshin kunun alkama da gyada ya ringa fitowa daga ciki
Ta dauki dauki cup daya cikin cups din Dake gurin wainda aka Ware musu aka Bata na Abban
Ta tsiyaya kunun Mai Dan yawa aciki kafin ta maida sauran ta rufe ta dauki kofin ta baro gurin bayan ta jefa cokali aciki tana juyawa ahankali ahankali Dan ya huce ta nufi gurin Abban tana kallon yanayinsa da a fili qarara yake nuna yayi nisa a tunani.

Aje kofin tayi tafara tura kujerarsa zuwa bakin windo bayan tasake yaye musu labule sbd iska Dan yanzu tana basa kunun zufa zai taso Masa.

Janyo tata kujerar tayi ta zauna gabansa tareda aje tissue gefensu ta dago fararen idanuwanta ta kallesa cikin kulawa shima ita yake kallo
Ahankali tasaki wani irin murmushin dayasa Abban rufe idanuwansa ahankali sbd murmushinta bakomai yake bayyanawa ba sai zallar tausayinta.

Saida ta tabbatarda ya huce ba zafi kunun ta dauka tafara basa ahankali da spoon ta nufa bakinsa,

Sam bayajin yunwar Shan komai ayanzu sbd damuwar dayake cikinta sosai,
Jin inda lafiyarsa ta dosa ya wargaza duk wani Dan sauran qwarin gwiwarsa da dukkanin jarumtarsa
Tunaninsa 'daya yanzu yanda zai Fadawa *_TURAKI_* buqatarsa Dan kuwa wannan babban abune Mai girma zai roqa agurinsa duk da girman banbanci masu tarin yawa dasuke cike a tsakani.

Sbd kawar da sabuwar damuwar da hanata shiga wani sabon halin yasa hakanan take basa abincin Yana sha tanayi tana goge Masa da tissue
ahaka yakesha har sukai nisa yakusa shanyewa.

Cikin nutsuwa ta Dan kallesa kafin ta bude Baki kamar ko yaushe da taqaitaccen sauti tace"

Koma menene sakamakon asibitinka
Bana cire Rai ga falalan ubangiji akan samun sauki da lafiyarka.
Karka saka sabuwan damuwa
Ko ahakan Ina godiya ga ubangiji daya bani ikon tasowa nayi rayi rayuwa da mahaifina.

Kallonta yake da idanuwansa dasuke jajir har lokacin zuciyarsa na sake zurfafa da tunani.

Tas tagama basa kunun ta dauko maganinsa shima tabasa kafin ta goge Masa ta dauko wani Dan turarensa da baya yanke musu Abdullahi ke siyowa ta 'dan fesa Masa kadan sbd abdullahi din yamasa wanka kafin zuwan dr Abbakar
Tana gamawa ta fice Dan yau tana Dan da ayyuka
Ga wankin Momy ma ta Tara gwara na anty Sa'adah ta rage Mata jiya tayi abunta da kanta.

Harta fita Jin zafi a garin yasa tadawo ta turo kujerarsa ta fito dashi tsakar gidan Dan Tasha iska musamman dayake yamma tafarayi ba rana.

Wankin kayan Momy tafara a natse sai kayan anty Sa'adah kadan Wanda anty Sa'adah din Bata qarasa ba jiyan tana cikin Yi anty Sa'adah ta fito ta zaune gefen Abban daukeda takardunta na makarantar jami'a datakeyi tana karatu Dan tanada test a satin.

Sama sama take karatun tanayi tana Jan laylan da surutu duk da tasaba Laylah ba wani surutun zataiba musamman ma datake aiki Amma dai Haka sukeyin surutun sama sama tana yiwa Laylan bayanin wasu abubuwan dake cikin handout dinta tunda ita Layla Bata karatu tunda tagama secondary School last year shikenan iya inda nata karatun zai tsay kenan Kuma
Dan Momy tariga tafadawa Sa'adah da Abban hakan,
Bazata iya qarawa daga Nan
Tayi iya abinda taji zata iya
Idan akwai Wanda zai iya daukan karantun nata acikinsu biyun bismillarsu zasu iya dorawa daga Nan,
Shi dai Abba yasan baqar maganace tafada Masa Amma ko ahakan ya gode Mata Dan Koda laylan makarantar datai ta gwamnati ce yaga alamar tasamu ilimin Dan Haka shi ahakanma ya gode matuqa.

Sallamar momyn ce data dawo daga fitar datai tasaka Anty Sa'adah kallon kofa ita Kuma Laylah sauke kanta tayi qasa tana cigaba da wankin sbd sanin fuskartace abinda yafi komai tada zafi da ciwon Dake qunshe cikin ran momyn na shekaru yasa so da dama ita da kanta take dauke kanta da duk inda momyn zata kalleta din.

Kallon abban Dake zaune zugum idanuwansa a rufe yanajinsu sbd ganin yanda rayuwar yaransa biyu takeda banbanci Mai girma.

Direct Palo take neman shigewa Sa'adah tace Mata"

Momy zafi ake sosai fa gashi kin dawo kilama kin gaji.

Matuqar Laylah ko abba na guri bakajin muryarta cikin sakewa ko walwala Dan Haka batareda ta juyoba ta qarasa ciki tana cewa"

Bari nayi sallar la'asar saina fito ai.

Tana shigewa ciki Laylah ta tsame hannuwanta daga ruwan wankin ta dauraye tareda gogewa ta miqe taje ta dauko babbar daddumar da momyn ke zama akai ta dawo ta Kama kujeran abbanta ta matsar dashi gefe kusada ita sosai kafin ta shimfidawa momyn daddumar ta dauko Mata ruwa da abincinta duk ta aje Mata akai kafin ta koma ta juyarda kayan wankinta dayan gefen tana fuskantar abbanta sbd bawa momyn baya kamar yanda yake tun yarinta.

Wankinta taci gaba dayi har lokacin Sa'adah na janta da labari Amma tunda momy ta fito tayi tsit bayan motsin wankinta Babu abinda ke tashi sai qarar cokalinda momyn kecin abinci
Sa'adah ma datasan Laylah bazata Kuma maganaba Kuma saitayi shiru tamaida firarta gurin momyn.

Kusa rayuwar gidan gabaki dayansu Sa'adah ce kawai wadda Allah yabawa ikon gudanar da rayuwarta cikin walwala da sakewa tareda wadataccen kwanciyar hankali da nutsuwa harma da farin ciki sbd Sam bata dauka komai tasakawa rantaba,
Abban nema so da dama batada shaquwa dashi Sam Sam sbd farko datana yarinya abunda yafaru yaso cusa Mata tsanar mahaifin nata Amma Kuma qaunarta da 'yar uwarta da batada kowa saishi dakuma yanda shima Bai boye qaunar Laylah din ba ko a idanuwansa yasa takasa riqe komai aranta saima Suka dawo tausayinsu yayi rinjaye akan Jin zafin cin amanar da yayiwa momynta da mahaifiyar Laylah din Dan Haka tana qaunarsa saidai ba wani shaquwa a tsakaninsu musamman dayake Mata kallon wadda sbd itane mahaifiyarta take taimakonsu take riqe dasu duk da hakan ta wani bangaren itama Yana farin ciki da ingantacciyar rayuwar farin ciki da kwanciyar hankalin datake.

Sai gab da magriba tagama wankin lokacin tuni Momy tayi baquwa suka shige ciki Dan hakama wankin nata yayi sauri cikin tayita tashi kaiwa baquwar momyn ruwa da abinci.

Jin anfara Kiran sallar magriba yasa ta aje shanyar datake ta goge hannuwanta dasukai sanyi ta nufi gurin Abban da idanuwansa suke zuru dan dama hakan suke rayuwar kullum.

Maidasa ciki tayi tasaki labulai sbd sauro tana kokarin fitowa saiga abdullahi yashigo tace"

Anyi sallah Yaya abdullahi shima Abban sai yayi.

Eh dama shine nashigo Dan dubawa.

Ficewa tayi shikuma ya qarasa ciki yaja Abban zuwa toilet din dake dakinsa Dan Koda Abban na buqatan toilet.

Har aka gama sallah Bata Gama shanyarba Saida aka sallame tagama ta tattara gurin ta share ta tsaftacesa ta watsa ruwa tayo tata alwalar ta nufi ciki ta wuce dakinta direct tasaka wata baqar jallabiya ta tada sallah.

Bayan tagama sallar dakin Anty Sa'adah taje ta dauka Qur'an ta nufi palon abbansu ta zauna gefensa tafara karatun al qur'an din cikin zuciyarta har akai sallar ishai anan palon tayi sallah bayan tagama taga alamar shima sallar yakeyi Dan Haka Kai tsaye ta nufa abincinsa ta zubo ta tareda zuba Masa ruwa a wani kofin ta daukosu tareda magani tadawo gabansa.

Tana Gama basa komai ta gyara Masa koina abdullahi yazo ya daukesa daga kan kujera ya maidasa Kan gadonsa Tai Masa addua ta

1 / 36