Kanwar Maza 3&4 Complete Hausa Novel

Author :  Aysha Cool Category :  Complete Novels

Chapter   48 / 67

141K to 144K   out of 199.9K words

jabir auren Iman ba, amma ita ba ta ce ba ta so ba.

Masifar da wambai yake yi, tuni idonta ya cika da hawaye.
Turaki kansa ya san sharri ne, da tsabar mugunta, irin na hajiya Lubabatu.

"Tun da abun naki haka ne, ba kara ba mutunci a cikinsa, ai dama a kwanakin baya, da ake ta surutu a kak yarinyar da takawa, na ce lallai ki aurar da ita, to zan sake jaddada miki, nan da watanni uku, ko dai ki aurar da yarinyar nan, ko kuma ki mayar da ita in da ki ka tsinto ta, kuma a wannan karon ba zan canza magana ba.
Sannan abu na gaba, ?ara tayi yawa a kan wannan yarinyar sirikarki, daga zuwanta gida tana yi wa mutane sharri, tana haddass husuma, jamila ta kawo mini ?ara, na so na zauna da ku, ta ce a bar maganar, still na samu labari a kan tana yayaya cewar jamil ne ya saka aka yi garkuwa da ?anwarsu, to ahir Win ta, ki ja mata kunne, gidan sarauta ba wurin wasa bane ba" Ammi ta risunar da kai sannan ta tashi ta bar Wakin, ranta babu daWi, yayin da tausayinta ya mamaye zuciyar turaki, tana da kyakywar zuciya, sai dai tana ta fuskantar ?alubale kashi-kashi a rayuwarta da ta iyalanta.

Yanayin yadda ammin ta dawo ne ya tabbatar musu akwai damuwa, har ruma za tayi magana, amma laila ta hanata.

Yau wunin yau idon mai sunan Baba yana kan waya, ko zai ga sa?on iman, amma shiru, shikuma ya kasa yi mata magana, har dare shiru, gashi ya riga ya saba da daddare Wan jan sa da take da hira, yana yi masa daWi.
Haushi ne ya ishe shi, jin yadda Aliyu ya cika masa kunne da surutu shi da habiba, ya saka waya a speaker sai ?yal?yala dariya yake yi, habiba ta karkace murya tana yi masa wa?a, murya kamar an sha?e kuliya.

"Kaga ka cika mini kunne, ko dai ka fita, ko kayi mini shiru.

Aliyu ya mi?e tsam da wayarsa, ya koma tsakar gida, duk da sanyin da ake zabgawa.

***
Jabir ne a zaune, hajiya Lubabatu da Mummy sun saka shi a gaba, suna ta yi masa famfo.

"Na sha gaya maka giwa ba ?aunarka take yi ba, ka din ga nane musu, to gashi ?iri-?iri ta hanaka auren ?a, saboda azabar ?arya ta je ta ce wai ni ce bana son auren nan, mun yi haka da kai? Da na nuna bana so ka dage, cewa nayi Allah ya sanya albarka, amma da yake mukafuka ce, ba ta yi niyyar baka auren ba, ta je ta ce nice bana so".

Mummy ta amshe ta hanyar cewa "Banda abun jabir, kai da ake yi wa fafutukar samun kujerar mahaifinka, ina kai ina wata ?ar tsintuwa, mara asali mata gata, kai ana ?o?arin ka samu kujera, amma ka nacewa Adam, shi ka san me suke yi ta ?ar?ashin ?asa, dan ganin kujerar ta koma garesu, ga mata nan bila adadin a gari, ni ko ru?ayya ma sai na baka"

Hajiya Lubabatu ta ce "A'a wace irin ru?ayya kuma? A dai cigaba da neman kujerar, shima uban nasu ban taSa tunanin zai kai haka a raye ba, kalli shi adam Win da kake li?ewa, yadda yayi suna a ?asar nan, duk gaku matasa amma aka ware shi, aka tura shi wakilci, yayi aure ya haifi Wa, ga aikinnsa ga kasuwanci, kai kana nan kana fama daga kai har jamil Win uwar me ku ke da shi, duk da dukiyar iyayenku ku ke ta?ama"

Jabir yayi shiru tare da gazgata maganganun da tun a baya su mummy suke gaya masa bai Wauka ba, tare da mantawa da asirin da takawa ya daWe yana rufa masa tsawon shekaru.

Mummy kuwa ?ulattar Hajiya Lubabatu ta yi, da ta ce ya auri ru?ayya ta ce a'a, wato a tunaninta ya samu mulki, aci moriyar ganga a yada kwauronta.

Mummy a ranta ta ce 'Lubabatu baki da hankali, da ni ki ke zancen, lokaci yayi da zamu raba gari, kowa ya san in da ya kama'.

Kasa jurewa mai sunan baba yayi, ya fara tunanin ko jikin iman ne ya dawo, dan haka da kansa ya kira iman a waya.
Sallamar da yayi ta amsa cikin siriryar muryarta.

"Jikin ne dai?"

"A'a barka da safiya yaya umar"

"Meyafaru?"

"Bakomai" tayi maganar cikin sauke numfashi.

"Something is going wrong, feel free to share it with me"

"Yaya umar ba zan dameka da matsalolina ba?"

Cikin nutsuwa ya gyara zamansa ya ce "If you are free with me, let's share it together"

Wata irin nannauyar ajiyar zuciya ta yi ta ce "An yi cancel Win engagement Wina da za ayi".

"Ba abun da ki ke so kenan ba?"

"Ba cancel Win ya dameni ba, tun da Allah ya sa na buWe ido a hannun ammi, take bani kariya da nuna mini ita ta haifeni, amma mutanen da suke kusa da ita, basu bata goyon bayan hakan ba. Saboda ni ba irin tashin hankalin da bata shiga ba, kullum cikin damuwa take, kullum cikin sintiri kaini asibiti, kullum cikin neman abun da zai sani farinciki take,. Amma ni na kasa kawo mata farinciki ko sau Waya.
Ban san dalilin fasa Engagement Win ba, mai girma wambai ya ce ko tayi mini aure nan da watanni uku, ko ta mayar da ni in ta tsinto ni, babban abunda ya dameni kukan da ammi ta sha, ta ce da ta rabu da ni, gara ta Wauke ni mu bar gidan, ni rasa me ma zan yi, ina son ammi amma ba zan so ta bar gidanta ba".

A tsakiyar zuciyarsa ya din ga jin kukan iman, ya jingina jikinsa da bango, wata irin karaya ta kama shi.

A hankali ya ce "Khadija, kukan nan yana taSani sosai, bana son jin kukan mace, ko ban santa ba, zamu yi waya anjima. Amma dan Allah bana son sake jin labarin kina asibiti, ya isa haka"

A hankali take sassauta kukan, ta ce "Yaya Umar, na gode da ka bani dama ka ji abun da yake damuna, na gode sosai"

"Don't mentioned, ki ci abinci ki kwanta ki yi baccinki, ki cigaba da addu'a, ba abun da zai faru sai ikon Allah khadija" shi kansa mamakin yadda ya tausasa murya sosai yake, bai taSa zaton ya iya rarrashi haka ba.

Rumaisa kuwa Mahmud ta kira a wayar Anty laila, ta ce tana son ganinsa a in da suke haWuwa.

Babu jimawa kuwa suka haWu, sai dai cikin tsananin fushi ruma ta ce "Daddy anya mummy na son taga Annabi kuwa, daga ita har babar jabir fuska kamar an mari biri? Ya za ayi ta zo ta ce ba zata bari Wanta ya auri Iman ba, ammi ta ce a fasa a janye, ta ce ita ?arya aka yi mata ba ta faWa ba?

Ammi sai kuka take yi, har da masu kiranta a waya, ana bata kyauta ba, ta hana jabir iman, gashi wambai ya ce idan ba ta aurar da iman ba ta mayar da ita in da ta tsinto ta, wai ya suke so baiwar Allah nan tayi ne, daga ita har Iman Win sai koke-koke suke yi, wai kai ba abun da zaka iya yi a kai? To ni zan je wurin wamban sai na tonawa kowa asiri da kaina, ayi wadda za ayi ta ?are!

Ayshercool.
08081012143
*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*

*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ?URAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHE?I KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*

*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*

=?I? *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*

*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*

*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*

*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*

*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*

*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*

*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*

*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*

*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*

*9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*

*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*

*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*

*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*

*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*

*15. Supplement for Acne, dark spots remover*

*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*

*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka ????? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ?  kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*



Paid book ne, ? 500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012143, ga masu bu?atar vip post, suna iya garzayawa arewabooks su yi searching sunan book Win. Kar ku manta da subscribing YouTube channel Winmu na Cool hausa novels, domin samun daWaWan litattafan hausa na sauraro, ciki har da ?anwar maza da yake daf da fara zuwar muku a kan channel Win*

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Susbcribe my YouTube channel please =?O?



*TALLA! TALLA!! TALLA!!!
*?AN?ANO DAGA LITTAFIN NAZEEFA SABO NASHE, MAI SUNA ?UDURAR ALLAH*

Ta Yaya zai zama jinina alhali ni na san bayan matana ban tab a kusantar wata mace ba? Ya furta kai tsaye yana kallon likitan da sakamakon gwajin yake hannunsa. Likitan yana jinjina kai ya sake furta  Tabbas Jaheed jininka don gwajin k wayar halittarku da komai ya tabbatar kai ne mahaifinsa kafin a kai ga haka ma ko Kamanninku da suka zamo kwabo da kwabo sun tabbatar da Hakan koda Ba a yi gwajin ba.

Shiru na tsawon lokaci d akin ya d auka kowa da irin tunanin da yake a ransa ya kasa yarjewa zuciyarsa shine Mahaifin Jaheed duk da k wararan shaidu. Abinda ya sani ko da wasa bayan matansa na aure na Sunna bai tab a rik ewa wata mace hannu ba, idan kuwa ya tabbata Jaheed d ansa ne ta yaya ya samar da cikin nasa a jikin wacce aka kira mahaifiyarsa da ko a mafarki bai tab a ganin mai kama da ita ba TABBAS AKWAI LAUJE CIKIN NAD i. Mahaifiyar Jaheed ma Zata iya zama abar tuhuma da zargi. Kai tsaye zai iya cewa hakan zai iya zama K UDIRAR ALLAH& .

(*Ina ma'abota karance-karancen litatafan hausa, na san kun santa, Nazeefa sabo nashe, tsohuwar marubuciya, da ta saba nishaWantar da ku, da WaWan litatafan hausa masu ma'ana da ilimantarwa, ya kuke tunanin wannan turka-turka, DNA Win sa ya kasance daidai da na yaron da bai taSa ganin mahaifiyarsa ba, haka zalika a iya saninsa tun daga ?uruciya har girmansa, bai taSa aikata zina ba? Ku kasance da Nazeefa sabo nashe, dan jin yadda zata warware wannan turka-turka a cikin littafin ?udurar Allah. Masu bu?ata kai tsaye za su iya tuntuSar ta a kan lambar wayarta 08033748387*)







Cikin hanzari Mahmud ya ce "A'a rumaisa kar ki ce zaki yi wannan gangancin, Mummy ta fi gaban yadda ki ke tunani"

"Shikenan saboda ana tsoron ta, sai a zuba mata ido ta yi ta abun da ta ga dama? Tayi ta yi wa mutane fuska biyu"

"Kina da gaskiya rumaisa, amma Mummy ta wuce tunaninki, ki bi komai a sannu, kar aikin da muke tayi ya rushe, ina ?ara baki ha?uri, komai zai wuce dan Allah kar ki rusa mana aiki".

Rumaisa tayi ajiyar zuciya tare da share hawayen da ya taru a idonta.

Ta ce "Shikenan, akwai Allah ai".

Mahmud ya numfasa ya ce "Haka ne. Ammm rumaisa"

Ta Waga kai ta kalleshi.

"Ya aka yi ki ka san zancen filin turaki, har ki yi wa jamil maganar, na ji zancen a bakin jabir, yana yi wa mummy".

"Wai shi jabir Win nan wane irin munafuki ne?"

Mahmud ya ce "Kusan duk bakinsu Waya, kuma Mummy ta fara saka mini ido, shiyasa nake son ki din ga ha?uri, komai zai zo ?arshe in sha Allah"

Ta jinjina masa kai, ta juya za ta tafi ya ce "Na ce ba" ta tsaya ta waiwayo.

"Ya ake ciki game da iman?"

"Kana da labari ai, ko ayi mata aure nan da watanni uku, ko a mayar da ita in da aka tsinto ta, haka Wambai ya ce".

Mahmud ya ce"Ina ga rabon abokina ne ya rantse".

"Wa kenan?"

"Yayanki umar" rumaisa ta kalleshi ta ce "Kana nufin ka san yana son iman?"

Ya ce "Na sani"

Ta waro ido ta ce "Ya aka yi ka sani?"

"Actions Win sa sun nuna mini, kina ganin zai iya auren iman nan da watanni uku?"

Ruma ta yi shiru sannan ta ce "Daddy, rayuwa a ?asarmu akwai wahala sosai, yaya umar ya sadaukar da rayuwarsa a kan inganta tamu, ya riga yaya Abubakar gama karatu, ya koma master's. Yanzu an kaiwa yaya Abubakar kuWin aure, ya ce ba shi da shirin aure shi yanzu, dan haka ya mayar da hankali a kan ginin yaya Abubakar sosai, ya bar nasa, ga yaya Aliyu shima ya ce za a kai masa kuWin gaisuwa, duk da yaya umar mutum ne mai zafi, amma kullum burinsa mu cigaba, duk wanda ya raSe shi zai gane hakan.
Sun haWa gwiwa, sun buWe shagon sayar da takalma, shi da wani cousin Win mu, yana da ?o?arin neman na kansa, amma duk mu muke cinye komai, ba shi da komai a sanina, daga filayensu da aka ce tun kan babanmu ya rasu ya sai musu, ya fara gina nasa ya ajiye, sai babur Win sa, dan ma yanzu yaya Huzaifa yana Winki, Yasir harkar wayoyi yake, yaya Umar ba zai iya auren iman nan da wata uku ba gaskiyar magana".

"Kina ganin zai amince ayi supporting Win sa daga nan Sangaren mu?"

Ruma ta ce "TaS, ba zai yarda ba gaskiya"

Mahmud ya ce "I see"

"Amma ya dai rarraba takardunsa, amma dai bai samu aiki ba. Daddy dan Allah idan da yadda za ayi, ka tayani ya samu iman, yana sonta sosai, amma ban sani ba ko za a bashi ita".

"Zasu bashi, zan san abun yi".

"Na gode sosai Daddy"

"Ni yakamata na yi miki godiya daughter" Rumaisa ta yi murmushi, ta tafi.

Kamar wutar daji, haka aka cigaba da yi wa ammi surutu, na bata da halacci, duk irin ?aunar da Jabir yake nunawa Wanta, amma ace ta kasa bashi ?a.

Laila ta din ga bata ?warin gwiwar ta daure, ta kawar kai, kada ta tankawa kowa.

Tsananin tausayin iman da Mai sunan baba yake yi, ya sanya kusan kullum sai ya kirata ya rarrasheta, ya bata baki, sai dai ya shiga zullumi shi dai ya san bashi da halin aure a nan da watanni uku kawai, duba da auren Abubakar suke ta shiri, kuma yana jin yadda yake ?ara so da tausayin iman, ba shi da burin da ya wuce ya ganta a kusa da shi, ya gatan ta ta, ya bata kulawa.

Babu kunya babu tsoro, jabir ya kira Adam a waya, ya ce da haWin bakinsa da na matarsa aka hana shi auren Iman.

Takawa ya ce "Jabir ni da nake nan, ya za a yi na ziga cewar a hanaka iman"

"Saboda tun asali da na zo maka da zancen, ka ce baka so"

"And you keep going, ka dage sai ka aureta, ai Allah ba azzalumin sarki bane ba jabir, kuma shi Allah na kowa ne, tun ina nan aka fara maganar nan, sai dai bance komai ba na cigaba da yi wa iman addu'a da fatan alkhairi"

Jabir ya ce "Dole ka faWi haka Adam, a duniyar nan waye ba ya yi wa Allah laifi?"

"Idan ma so kake ka ce ina aikata wani abun a Soye nima, Wan adam ne ni, amma na san dai bai kai naka muni ba jabir".

"Na gode sosai da sosai Adam, tukuicin ?an uwantaka kenen, na gode ka nuna mana iyakarmu daga ni har Jamil, saboda ka auri wannan yarinyar, har ni za ta gayawa ban isa na auri iman ba, tun da yayanta yana son iman, kun kyauta" ya kashe wayar sa.

Adam ya dafe goshin sa ya ce "You again mimi? Subhanallah"

Ammi kuma rarrashin iman ta din ga yi, da nuna mata komai na Allah ne, kuma yana da iyaka, dan haka ta kwantar da hankalinta, a wannan karon

48 / 67