Kanwar Maza 3&4 Complete Hausa Novel

Author :  Aysha Cool Category :  Complete Novels

Chapter   14 / 67

39K to 42K   out of 199.9K words

kuma?" Ruma ta jinjina kai ta ce "Haka nake ji a jikina"

Huzaifa ya ce "Iyeee soyayya da ?auna, bari zamu gani ai"

Rumaisa ba ta iya yi wa Huzaifa martani ba, saboda ji ta yi ?irjinta ya yi nauyi, jikinta kuma yayi sanyi ?alau.

A hankali ta zame ta kwanta a jikin mama, ta lumshe idonta.

"Ki tashi bana son barcin la'asar, ki yi shi ki tashi da fushi ki hanamu sukuni da koke-koke da Sacin rai"
Maimakon ta tashi, sai ta sake langaSewa, ta ri?e hannun mama.

Mama ta kalli rumaisa ta ce "Ke! Lafiya kuwa?"

Ruma ta jinjinawa mama kai alamar eh.

Mintuna ashirin, sai ga sallamar ammi, mamaki ne ya kama mama, dan ba su yi waya ammi za ta zo ba.

Ta Soye mamakinta, ta amsa mata cikin mutuntawa.

Suka gaisa da mama, ammi ta ce "Maman sabir bacci take yi ne?"

Mama ta ce "Rigima dai take ji, wai sai an yi mata wanki, na ce ma ta tashi kar ta yi mini barcin la'asar, ta tashi ta ishi mutane da kukan banza"
Ammi ta yi murmushi ta ce "Haba maman rumaisa, kamar rumaisa idan ba ayi mata wanki ba, ai ba zata iya ba, kar a ramar mini da ita kan ta zo fa"

Suka yi dariya, ruma daga kwancen ta ce "Ammi ina wuni"

"Lafiya ?alau rumaisa, kina lafiya?"

"Lafiya ?alau"

Ammi ta ce "To masha Allah, tare muke da takawa fa"

Mama ta ce "Ahh kuma ki ka bar shi a waje, Yasir ka ce ya shigo mana"

?oye mamakinsu suka yi, dan rumaisa ta ce ta ji a jikinta yana hanya.

Tun da yayi sallama jikinta ya kuma sanyi, ta rasa menene yake yi mata daWi.

Ya shigo Wakin mama, suka gaisa, mama ta ce wa rumaisa "Ba zaki tashi ki gaishe shi ba?" A hankali ta tashi zaune, ta kalli Adam sau Waya, ta kawar da kai ta sake kallonsa na biyu amma ta kasa magana.

Mama ta ce "Ba magana nake yi miki ba rumaisa?"

Ammi ta ce "Wannan ?ar tsamar ta su, idan da sabo sun saba".

Mama ta ce "wannan rashin Wa'a ne, ya girmeta, kuma mutumin da zaka aura ka din ga yi masa haka, iskanci ne kawai, ai ba haka take yi wa sauran mutane ba"

Rirri?e mama ta yi cikin kuka ta Soye fuskarta ta ce "Mama baki san me nake gani ba ne"

A rikice ammi ta ce "Me ki ke gani rumaisa, yi mini bayani?"

"Hararata yake yi, idan ya harareni ni tsoro yake bani" haka kawai mama ta ji rumaisa ?arya take yi, dan ta sha faWa ita fa ban da fuskar mai sunan baba, babu wata fuska da take bata tsoro.

A zahiri kuwa, a karo na biyu yau ta ga abun da ta gani a tare da adam, kamar yadda ta taSa gani, lokacin suna asibiti.

Idonsa gaba Waya ya koma ba?i ?irin, babu wannan farin, sai haya?i da yake fita, kamar ana kunna itace, a wannan karon har da kamar harshen wuta daga idanun nasa.

Shi kansa adam, cikin jikinsa wata irin rawa yake yi, amma a zahiri yana zaune normal, jikinsa ji yake tamkar ana sassra shi, ba bu wani abu da yake muradi, banda ya sha?e ruma ko ya ri?e ta, ya samu sassauci.

Ya sunkuyar da kai, mama kuma ?uluwa ta fara yi, da lamarin rumaisa, dan a ganinta rashin mutunci ne kawai.

Ammi ta ce "Haba rumaisa, shi ne har da kuka, ba hararki yake yi ba, haka yake dai bai fiye fara'a ba, ku da kun kusa zama abu guda ma. Maman rumaisa dama zuwa na yi na gaya muku, a sanar da dangin mahaifinta, ranar Juma'a za a kawo kuWin aure"

Mama jikinta yayi sanyi ta ce "Da wuri haka?"

"Kar ki ce haka maman rumaisa, jinkirin ba shi da wani amfani, kin san mu masaurata ba sa son jira, ayi musu addu'a dan Allah, in sha Allah za a kawo kuWin aure"

Har mama da ammi da suka gama tattaunawar su, babu wani ?warin gwiwar cewa wani abu, a tsakanin adam da rumaisa, kowannensu shi ya san halin da suke ciki.

Bayan sun gama magana, suna fita rumaisa ta tubure da kuka ta ce ita fa ba ta so, ba zata aure shi ba, da fari mama ta fara rarrashin ta, ta zaci abun na ta na hankali ne, amma ta ga ba ta da niyyar nutsuwa, ita dai ba ta gaya wa mama, me take gani ba, amma ta ce ba zata aure shi ba.

Shihowar mai sunan baba ce, ta sanya ta Wan nutsu, Aikuwa tambayar da ya fara yi, shi ne meya sameta take kuka.
Mama ta sanar masa da duk abun da ya faru, rumaisa ta zaci yanzu ma zai turje, sai ji ta yi ya ce "Allah ya tabattar mana da alkhairi, nan kano zasu kai, ko can katsina?"

Mama ta ce "Wai da su kai wa kawunku na mandawari, ba sai an wahalr da su ba"

Mai sunan baba ya ce "Babu laifi, Allah ya kaimu"

Cikin kuka rumaisa ta ce "Mai sunan baba ni fa na fasa bana son shi".

Wani mugun kallo ya yi mata ya ce "Suwa zaki mayar ?an iska, ko yau suka ce a Waura, sai an Waura, ki bari na fita na dawo na tarar kina wannan kukan, ki ga yadda zan yi ?asa-?asa da ke".

Haka nan rumaisa ta tsinci kanta da kasa gaya musu abun da take gani a tare da adam, da alamu suka nuna mata su basa gani, ita kaWai kawai take gani.

Usman kuwa cewa yake "Wallahi ba zaki yi mana ba?in ciki ba dan ubanki, haka kurum ke fa ki ke son auren mai kuWi, kuma Allah ya kawo, ki ce ke ba kya so, kin yi kaWan yarinya, dole ayi auren nan, ko ba komai ma hau doki, kina kallo albarkacinsa aka fito da Aliyu, yanzu malam shamsu har gaisheni yake, saboda yadda ya kankaro mana mutunci, sai kin je".

Cikin kuka ta ce "To ni bana son shi"

"Uban da ya sanya, ki ka amince tun da fari, shi zai sa ki ha?ura ma a yanzu" gaba Waya aka ?i goya mata baya, ta din ga surutai da koke-koke suka ?i kulata.

Ammi da suka tafi gida, jikinta sanyi yayi, da ganin yadda rumaisa duk ta rikice lokaci Waya, kuma ta ga bai kamata ta Soye musu wasu abubuwan a kan Adam ba, amma tana ji a jikinta rashin lafiyar ta sa abu ne da ya shafe shi, da shi da ita rumaisan, ta din ga fatan Allah ya sanya hakan ba zai zama cutarwa ga rumaisa ba.
Nusaiba ta din ga tambayar ammi yadda suka yi.

Ammi ta ce "Sun amince, rumaisa ce dai take nema ta ce ta fasa, amma ina ganin rigima ce kawai irin ta ta, kuma kai takawa, kamar yadda na gaya maka a baya, dole ka sassauta ka mayar da kanka dai-dai da ?uriciyarta, bana son ayi auren nan ya zaman tana jin tsoronka, ko tana ganin kamar ba ka da imani"

Adam bai iya fahimtar abun da ammi take faWa sosai, ya kwanta a kan 3seater, ya lumshe tabbas.

Iman kuwa tausayinsa da na ita kanta rumaisan ya kamata, mussaman da ta ji cewar nan kurkusa sosai za ayi auren.

Har dare yayi, ko abincin kirki rumaisa ta ?i ci, sai koke-koke, suka shareta suka cigaba da harkokinsa, usman sai tsara yadda abubuwa za su kasance yake yi.

Mama ta kira yaya Abubakar a waya, ta sanar masa da batun, ya ce zai shigo kano, Yakamata tun wuri su san me suke ciki, su san mai yakamata a fara tanada na auren rumaisa.
Jin abun da yaya Abubakar ya faWa, ya sanya rumaisa jin kome za ayi mata ba zata iya barin gidan nan ba, sai dai idan an yi auren ya dawo gidan ya zauna, ko ya barta a gida ya bata sabir kamar yadda aka yi mata al?awari.

Tashi ta yi ta nemi wuri ta yi kwanciyarta, saboda hirarrakin Sata mata rai suke yi.

Daga nesa take hango shi cikin haya?i, a hankali haya?in yake bajewa, yana ?ara kusantota, ganinsa ta yi cikin sar?a hannu da ?afa, ga idonsa na ci da wuta a wannan karon ba haya?i kawai yake yi ba, fi?arsa duk ta fito daga bakinsa, ga faratansa sun yi za?o-za?o. Tunkarota yake yi, yayin da ita kuma take ja da baya, cikin tsoro da razani.

Duk iya ?o?arin ta na addu'a, ta kasa dan ji ta yi tamkar an danne mata masarrafar tunaninta, zuwa ma?oshinta, ta kasa Addu'a.

Tun tana ja da baya, har ta kai bango, fizgota yayi da ?arfi, ya danna mata faratansa a ma?oshinta.

"Wayyo Allahana mama na shiga uku, Innalillahi wa Innalillahi raji'un"

Ko sallame sallar da take mama ba ta yi ba, ta yo kan rumaisa jin tana ihu, kamar wadda za a kashe.

Mama ta fizge net Win rumaisa, ta ri?ota tana tambayarta "Lafiyarki kuwa? Menene?"

Rirri?e mama ta yi tana mayar da numfashi, hannu Waya kuma ta ri?e wuyanta, da take jin kamar yana yi mata zafi.

Tuni Aliyu da mai sunan Baba suka taso da gudu suka yo Wakin mama, saboda yadda kururwar rumaisa ta cika gidan.

Mama ta jijjigata ta ce "Rumaisa menene ki yi magana mana"

"Mama baban Sabir ne, shine"

"Me yayi miki?" Numfashi take saukwa, amma ta kasa gayawa mama abun da ta gani.

A fusace mai sunan baba ya ce "Wula?ancin naki da iskancin har ya kai ki din ga yi mana ihu cikin daren nan? Kar ki kuskura ki kaini bango, na kuma jin bakinki sai na zaneki, ki yi addu'a ki kwanta, idan ma kina yi ne saboda ba kya son auren, to kin yi kaWan"

Mama gaba Waya jikinta yayi sanyi ta kuma cewa "Me ki gani ya razanaki haka?" Rumaisa ta yi shiru.

Mai sunan baba ya ce "Ba wani abu da ya razanata, shirmenta da take yi ne yake zuwar mata har a mafarki"

Aliyu ya yi tsaki ya ce "Rigimarki ba ta ?arewa, har tausaya bawan Allah nan nake faman da zai sha" ya fice daga Wakin, mai sunan baba ma ya fice.

Duk iya rarrashin mama, da lallaSa yaro a matsayin ta na uwa, ta yi, amma rumaisa ta ?i gayawa mama ainihin abun da ya faru, haka mama ta ?yaleta ta sake tayar da salla.

Tsoro ya hana rumaisa ko rufe idonta, dan haka ta tashi ta je ta yi alwala, ta zo ta tayar da salla ita ma, sai dai tana yin raka'a biyu, wani nannauyan bacci ya Wauke ta.
Mama tana jin yadda rumaisa ke ta surutai a baccin, kamar tana hannun ?an bindiga.

Sai da mama ta sanyata a gaba tana ta tofa mata adduoi, har mama ta fara tunanin, ko rumaisa na da aljanu ne, maganar aure ta taso za su fara motsawa.
Dan haka ta ?udurce a ranta, dole ta nema mata maganin sheWanu.

Ta cigaba da sallolinta, tare da tsananta addu'a a kan lamarin auren nan da yake tunkarosu.

***

Mamaki Samha take ba Wan kaWan ba, ganin irin sur?u?in ?auyen da suke kurWawa, ita da Mummy da kuma Hajiya Lubabatu.
Kasa Soye mamakin ta yi ta ce "Wai yanzu Mummy har nan ku ke zuwa? Ni fa ma fara jin tsoro"

Mummy ta yi murmushi ta ce "Yaro yaro ne, ke ranar biyan bu?ata, rai ba a bakin komai yake, tafiya duk nisanta da sur?u?inta, in dai da biyan bu?ata ai shikenan, tafiya Wazu ce".

Hajiya Lubabatu ta ce "Ke idan babu wannan ?an biye-biyen mutum ya zauna lafiya, mussaman a irin gidajen sarautar nan, ai ni tun da Allah ya taimakeni, na kaWa duk wata mata da ta raSi gidana, na ga tsuguno ba ta ?are mini ba, sai na dangana da mallakawa Jabir kujerar galadima,"

Samha ta ce "Takawan fa? Ba gidansu sarautar za ta koma ba".

Mummy ta zunguri Hajiya Lubabatu, sannan ta Wora da cewa "Yauwwa, mun kusa ?arasawa, daWinta kowa yake gani, idan muka je sai ya katse ya sauraremu".

Samha ta ce "Ni fa idan za a kasheni, ban san hanyar komawa ainihin titi ba, gaba Waya kaina ya juye".

Hajiya Lubabatu ta ce "Zaki zama ?ar gari ne da zarar kin waye".

A cikin sur?u?in ?auye sosai mutumin yake, dan an fita daga gari sosai wurin kamar daji, a nan aka yi masa wani shinge, suka tarar da tarin mata da maza a wurin, da masu zubin hannu da shuni, da masu saffa-saffa, ga marasa lafiya kuma, wasu abun nasu ma dai ba kyawun gani.

Ba tare da Sata wani dogon lokaci ba, bayan an sallami na ciki, suka shiga, wurin duk an kafe ?ahuhuna da ?warangwal Win dabbobi, ga wani irin wari da tsamin turaruka da magunguna da Wakin yake yi. Mutumin yana zaune cikin wasu tsummokaran kaya, ga wasu irin kayan tsubbu a gabansa shi kansa du?un-du?un da shi, kamar ba Wan Adam ba, ga idonsa Waya hakiya ta rufe, Wayan kuma a juye ga idon jawur.
Sai da kan Samha ya sara, ta nemi faWuwa, Hajiya Lubabatu ta ri?eta suka zauna.

Mummy ta ce "Barka da warhaka malam, ya aiki ya ?o?ari"

"Lafiya ?alau, kin yi nusau, ko bu?ata ta biya ne, ko kuma dai kin fasa aikin da ki ka bu?ata, tun da ki ka ce mana akawai maganin da ake masa amfani da shi, muke jiran ki kawo mana maganin mu yi aiki a kai, amma mun ji ki shiru".

"Ai malam maganin ne ya?i samuwa, duk wata hanya da zan bi a samu, ba a dace ba, amma ba ha?ura na yi ba, ina nan zan dawo. Gamu tare da ba?uwa, ?ar facalarmu ce, da ita da shi yaron Adam, duk iyayensu ?an uwa ne, ta daWe tana son shi, amma ya auri ?anwarta, yanzu ?anwar ta mutu, amma uwarsa na son aura masa wannan ?ar tsintuwar da na taSa baka labari, kuma wannan Win ta kuma rasawa, shine muke son ayi wani abu a kai".

Yayi shiru, sannan ya Webi wata ?asa ya zuba a wani fai-fai, ya dinga juya hannunsa, sannan ya kalli fai-fan ya ce "Tir?ashi, tabbas ga maganar aure nan, sai dai ita yarinyar tana tafe da wata irin guguwa mai ?arfin gaske, sai kun tashi tsaye sosai"

Cikin sauri Samha ta ce "Malam so nake kar auren ya yiw....."

"Aure sai an yi shi, ma'aunin ?addarar yarinyar da zai aura ya rinjayi tasa, sai dai idan Wayansu ne ya mutu"

Kamar Samha za ta yi kuka ta ce "Dan Allah malam a kasheta, ba zan iya jurewa ba a wannan karon"

Mummy ta ce "Malam, ka san yarinyar, wadda ka taSa yi mini aiki a kanta ce shekarun baya, kawai ka yi wani abu a kai"

"To ya aka yi ?asa ba ta nuna mini ita ce ba? Ban ga taurarinta sun fito a cikin nasa ba, amma duk da haka babu damuwa, ta jiramu a waje, zan bata abun da za ta yi"

Samha ta jinjina masa kai, ta yi godiya, sannan ta tashi ta fita ta bar su Mummy.

Hajiya Lubabatu ta ce "Malam, ya ake ciki ne? Haryanzu galadima yana nan a raye, ga lokaci yana ?urewa, bana son wani dalili da zai gifta, da Jabir zai gaza mallakar zunzurutun dukiyar nan da sarauta".

"Allah ne mai kashewa da rayawa ba ni ba, dole ki cigaba da jira, ke kuma ya aka yi?" Yayi maganar yana kallon Mummy.

"Malam, kamar aikin da yake tsakanin yaran nan ya fara sanyi, kamar mahamud ya sassauta ?iyayyar da yake yiwa Wan uwan, sannan malam yadda yake yin?urin yin auren nan, a sake damalmala lamarinsa, bana ?aunar ganin wani cigaba a tare da yaran nan".

Malamin ya ce "Ina iya Sata aiki ne, ba sauya ?addarar bawa ba, zan yi abun da ya dace a kai, ku tafi ta kudu, ku ajiye abun sadaka a mararraba ta uku, sannan shekara ta kusa, za a shayar da ?ar ba?a ta arewa da jini, sai dai ta daina samun jinin da take sha, dan haka za ayi mata sadaukarwa da wani abun, na sallameku".

Da haka suka fita, Samha take ce musu bai faWa mata mai za ta bashi na aiki ba, suka ce kar ta damu, suka yi abun da ya ce sannan suka tafi gida.

***
Abubakar ya dawo, sun kuma tattauna sosai a tsakaninsu, a kan auren rumaisa, suka yanke shawarar a sake jarraba sayar da gonarsu, domin a samu abun yi mata kayan Waki.
?angaren rumaisa kuwa, sai koke-koke take a kan ita fa ba ta so, gashi har fargabar kwanciya bacci take yi, saboda munanan mafarkan da take yi, ta je ta samu malaminsu a islamiyya ta ce ya bata Addu'a, tana yawan yin mugun mafarki ya bata shawara da cewa "A duk lokacin da ki ka yi mummunan mafarki, ki nemi tsari sannan kar ki gayawa kowa, ki din ga kwanciya da alwala, sannan ki kwanta da Sangaren dama, ya zamana kina Adduoi na safe da na maraice, sannan ki karanta na kwanciya barci, idan razana ki ake yi a mafarkin, ki daina tsorata, ba abun da yake samun bawa sai da iznin Ubangiji, kin riga kin yi azkar kin nemi tsari, babu abun da kuma zai cutar da ke".
Rumaisata ri?e maganar malaminsu, ta dage da addu'a da alwala, shine ta Wan samu rangwame.

Rana bata ?arya, sai dai uwar Wiya ta ji kunya, tun da su ammi suka tafi, sai ana gobe kai kuWi suka yi waya da mama, ranar juma'a bayan an saukko daga Masallacin juma'a, mai girma turaki da wasu manya a masarautar kano, suka kai kuWin auren rumaisa gidan ?anin mahaifinsu, naira dubu Wari biyar, suka saka wata Waya rak.

?anin mahaifin rumaisa ya nemi su ?ara musu lokaci, saboda shirin aure, ba abu ne mai sau?i ba, amma suka ce basa bu?atar komai, rumaisa kawai suke son a kai musu, dan haka wata Waya suka saka.

Ayshercool
*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*

*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ?URAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHE?I KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR

14 / 67