MAI DAKI BOOK 3 Hausa Novels by Sodangi. .docx

Author :  Hafsat C Sodangi Category :  KDP NOVELS

Chapter   6 / 6

15K to 15.7K   out of 15.7K words

fa

ina gudun magana.

Amma idan kin ga a matse ki ke shi

kenan kije amma kada ki dade."

Babban shagon da muka yi

siyayyan kayan aurena naje, mutumin

kuma ya gane ni.

Nayi mishi bayanin bukatata na son

canza kayan tare da neman sanin

cikon da zan yi mishi.

Cikin sauki da mutunci muka

daidaita na zabi wasu masukyau nayi

127

mishi ciko na dawo gida da motar

kaya.

Su kuma suka saka nawa da damna

suke jingine a dakin su Tasi'u suka

tafi da su.

Sai da nasa a ka yi wa Umma

fentin dakinta tsaf sannan a ka zuba

mata sabbin kayanta a ciki.

Abin sai wanda ya gani, duk da irin

fadan da Babana yayi mun wanda bil

hakki abin ya ba shi haushi.

Ni a raina dadi naji don kuwa

nasan shima Babana idan ya hau

gadon zai huce.

Tun ana saura kwanakki ake ta

isowa yan biki kowa da shirin shi,

yan uwan Umma daga Gamawa da

na Babanmu daga birnin Kudu.

Su Inna Hadiza suka tasa ni a gaba

kowa da abinda yake fada.

128

Ba ni da abinda zan ce musu don

na riga na gaji da bayani.

Da daddare Baba Ladi ta kira ni

dakin da aka sauketa da yake na Yaya

Auwalu ne tana yi mun magana ne ita

ma kamar kowa a kan rabuwata da

Ahmad.

Ban ce matakomai ba ta yi ta

maganganunta ina jinta. Ta ce, "Wato

ina miki magana kin yi shiru ko?

Na dan yi murmushi daidai wayata

tayi kara na dauka Ahmad ne.

Gabana ya fadi kamar kowanne

lokaci idan ya kira abinda ban san

dalilin faruwar hakan ba.

Nayi mishi sallama ya amsa.

"Ya ya shirin biki?

Na ce, "Mun gode Allah."

Ya ce, Wato sai a yanzu nasan

rashin kirkinki."

129

Na ce, Da na yi me kuma

'Yallabai?"

Ya dan yi murmushin da na jiyo

sautinshi har a cikin wayar. Ya ce, "Ba

kya kirana Hauwa'u, ba ki damu da ni

ba a yanzu.

Yau kwana goma sha hudu ban kira

ki mun gaisa ba, hakan bai sa kin yi

tunanin ke ki neme ni ba.

Sannan sai aka saka auren Yaya

Auwalu ba ki saka ni cikin wadanda za

ki gayyata ba."

Na ce, "To kayi hakuri.

Ya ce, "An ya zan iya kuwa? Ina dai

so a duk lokacin da ki ka tunani ki rinka

yi mun adalci."

Na ce, "To."

Ban san adalcin me Ahmad yake

sonayi mishi ba. Sannan a tsakaninmu

wanene ya kamata ya yi wa wani

adalci?

130

Ni ce zan yi mishi adalci ko shi ne zai

yi mun'? Wayar da na tsirawa ido ita ce

ta sa Baba Ladi fara sabuwar magana ta

bar wacce da take yi.

"Kina yi mishi irin wannan so me ya

fito da ke? A hankali na kalleta na ce

mata, "Mahaifiyarshi."

Da yamma kawai sai mota ta tsaya

aka fara sauke kaya, buhun shinkafa

biyar, sugar, filawa, wake, gero,

mangyada, manja, maggi, tumatir da su

albasa kwando-kwando.

Sai cinyoyin bayana Saniya guda

biyu, sakon Ahmad ne. sai yadin

material 'yan asalin Dubai guda biyu,

boyil biyu.

Sai atamfa Erclusive guda biyu duka

a dinke. Takalma set kafa biyu da za su

iya shiga da kayan.

131

Sai gyale biyu, kayan duk a dinke

suke. Na zuba musu ido ina kallo. Wani

sanyi ya rinka kwarara a cikin zuciyata.

Shi ma har a yanzu da alama bai

fidda rai ba. Text nayi mishi na godiya,

duk da korafin da ya yi na ba na

kiranshi.

Don kuwa ban ga dalilin yin hakan

ba. Text din yana shiga sai ya kira, na

ce "Mun ga sako mun gode."

To fa! Lallai kam da gaske Ahmad

yake ba zai iya hakura da Hauwa'u ba.

To idan kuma Ishak ya ji labarin

abinda ya faru shi ma zai dawo?

Bari in dan huta a nan kafin na dora

daga baya, don haka sai mu tara a littafi

na (4) kuma na karshe insha Allahu.

Taku;

Haj. Hafsat C. Sodangi

(Mrs Yunus Abdullahi Dabai)

08025078968, 07035586299

132

6 / 6