Author : Hafsat C Sodangi Category : KDP NOVELS
fa
ina gudun magana.
Amma idan kin ga a matse ki ke shi
kenan kije amma kada ki dade."
Babban shagon da muka yi
siyayyan kayan aurena naje, mutumin
kuma ya gane ni.
Nayi mishi bayanin bukatata na son
canza kayan tare da neman sanin
cikon da zan yi mishi.
Cikin sauki da mutunci muka
daidaita na zabi wasu masukyau nayi
127
mishi ciko na dawo gida da motar
kaya.
Su kuma suka saka nawa da damna
suke jingine a dakin su Tasi'u suka
tafi da su.
Sai da nasa a ka yi wa Umma
fentin dakinta tsaf sannan a ka zuba
mata sabbin kayanta a ciki.
Abin sai wanda ya gani, duk da irin
fadan da Babana yayi mun wanda bil
hakki abin ya ba shi haushi.
Ni a raina dadi naji don kuwa
nasan shima Babana idan ya hau
gadon zai huce.
Tun ana saura kwanakki ake ta
isowa yan biki kowa da shirin shi,
yan uwan Umma daga Gamawa da
na Babanmu daga birnin Kudu.
Su Inna Hadiza suka tasa ni a gaba
kowa da abinda yake fada.
128
Ba ni da abinda zan ce musu don
na riga na gaji da bayani.
Da daddare Baba Ladi ta kira ni
dakin da aka sauketa da yake na Yaya
Auwalu ne tana yi mun magana ne ita
ma kamar kowa a kan rabuwata da
Ahmad.
Ban ce matakomai ba ta yi ta
maganganunta ina jinta. Ta ce, "Wato
ina miki magana kin yi shiru ko?
Na dan yi murmushi daidai wayata
tayi kara na dauka Ahmad ne.
Gabana ya fadi kamar kowanne
lokaci idan ya kira abinda ban san
dalilin faruwar hakan ba.
Nayi mishi sallama ya amsa.
"Ya ya shirin biki?
Na ce, "Mun gode Allah."
Ya ce, Wato sai a yanzu nasan
rashin kirkinki."
129
Na ce, Da na yi me kuma
'Yallabai?"
Ya dan yi murmushin da na jiyo
sautinshi har a cikin wayar. Ya ce, "Ba
kya kirana Hauwa'u, ba ki damu da ni
ba a yanzu.
Yau kwana goma sha hudu ban kira
ki mun gaisa ba, hakan bai sa kin yi
tunanin ke ki neme ni ba.
Sannan sai aka saka auren Yaya
Auwalu ba ki saka ni cikin wadanda za
ki gayyata ba."
Na ce, "To kayi hakuri.
Ya ce, "An ya zan iya kuwa? Ina dai
so a duk lokacin da ki ka tunani ki rinka
yi mun adalci."
Na ce, "To."
Ban san adalcin me Ahmad yake
sonayi mishi ba. Sannan a tsakaninmu
wanene ya kamata ya yi wa wani
adalci?
130
Ni ce zan yi mishi adalci ko shi ne zai
yi mun'? Wayar da na tsirawa ido ita ce
ta sa Baba Ladi fara sabuwar magana ta
bar wacce da take yi.
"Kina yi mishi irin wannan so me ya
fito da ke? A hankali na kalleta na ce
mata, "Mahaifiyarshi."
Da yamma kawai sai mota ta tsaya
aka fara sauke kaya, buhun shinkafa
biyar, sugar, filawa, wake, gero,
mangyada, manja, maggi, tumatir da su
albasa kwando-kwando.
Sai cinyoyin bayana Saniya guda
biyu, sakon Ahmad ne. sai yadin
material 'yan asalin Dubai guda biyu,
boyil biyu.
Sai atamfa Erclusive guda biyu duka
a dinke. Takalma set kafa biyu da za su
iya shiga da kayan.
131
Sai gyale biyu, kayan duk a dinke
suke. Na zuba musu ido ina kallo. Wani
sanyi ya rinka kwarara a cikin zuciyata.
Shi ma har a yanzu da alama bai
fidda rai ba. Text nayi mishi na godiya,
duk da korafin da ya yi na ba na
kiranshi.
Don kuwa ban ga dalilin yin hakan
ba. Text din yana shiga sai ya kira, na
ce "Mun ga sako mun gode."
To fa! Lallai kam da gaske Ahmad
yake ba zai iya hakura da Hauwa'u ba.
To idan kuma Ishak ya ji labarin
abinda ya faru shi ma zai dawo?
Bari in dan huta a nan kafin na dora
daga baya, don haka sai mu tara a littafi
na (4) kuma na karshe insha Allahu.
Taku;
Haj. Hafsat C. Sodangi
(Mrs Yunus Abdullahi Dabai)
08025078968, 07035586299
132