Author : Hafsat C Sodangi Category : KDP NOVELS
Ziradat.
52
Zama yazo yayi yana gaya mun
abubuwan da yake so nayi mishi, na
sallah saboda bakin abokanshi da za
su kawo mishi ziyara.
Na ce, To ka bari mana idan nayi
na Babanku sai na diban maka a ciki.
Yayi godiya sosai, take kuma farin
cikinshi ya bayyana, ya tashi ya tafi.
Bai dade da fita ba na fita don
zuwa sashen Hajiya kai mata farfesun
kodar da Ahmad ya aiko ya ce nayi
mata da hannuna.
Na isa bakin kofar tun kafin nayi
sallama naji Ziradat tana cewa, "Ai
munafuka ce tunda gashi har Hajiya
ma yanzu ba ta yarda idan mun ce
mata tayı mana wani abu.
Ni a matan da Babanmu ya aura
duk ita nafi tsana. Hajiya ta ce,
53
"Um'um Ziradat na fa kwabe ki da
irin wannan maganganun."
Shi kuma Zubair cewa ya yi "Ni
banä son irin wadannan maganganun
ban san abinda yasa Baba yake biye
muku ba.
Menene laifin wannan matar? Ko
harkar mutum bata shiga ba za ku
taba barin Baba ya zauna lafiya da
mata ba. Shi kuma ku ke sakawa a
matsala."
Sallama nayi na ajiye mata na fito
na dawo wurina, a raina na ce kwaji
da shi, ni kam nawa auren daram in
Allah ya yarda.
Shiri sosai nayi na sallah mutanen
gidan kaf na basu abinci da abinsha
da su kek din da nayi ba tare da nayi
la'akari da Hajiya tayi ba.
54
Makwabta baki daya sai da na
zagaya su da abinci. Ahmad ne kuma
ya taso keyar su Zainab suka kai mun
rabon.
Gidanmu ma duk da ya aike musu
da nama cikin babban baho saboda
yankan da yayi da kuma shinkafa da
tumatur kwando.
Bai hana ni kai musu abincin sallah
ba wannan kuwa Bala direba na aika.
Da yamma ne baki abokan harkar
Ahmad suka zo gidan hakan ne yasa
sashenshi ya cika dankam ba kadan
ba.
Nima gagarumar liyafa na shirya
musu sinasir da farfesun kafar saniya
sai dambun nama da kek da manyan
donghnut na asali mai ridi.
Sai kwalayen juice wanda na hada
musu duka a cikin wani madaidaicin
55
kwando na Rafia da nayi rafin
dinshi da wata 'yar leda da aka rubuta
iyalan gidan Alhaji Ahmad Rufa'i
suna muku barka da Edil Fitr.
Kuma gaba dayansu ya wadace su.
Shima abin yayi mishi dadi ba kadan
ba.
Ya shigo dakina lokacin da nake
shirin shiga wanka har yanzu
fuskarshi a washe take ya sa hannu ya
dauke ni yana cewa bari nima na taya
ki wankan irin wannan gajiya da ki ka
yi haka.
Duk da dai ni da yunwa ki ka bar ni
na ce, "Haba yallabai na dauka ai
yau ba za ka ji yunwa ba."
Dariya yayi ya fita bayan ya gaya
mun yana jirana idan na gama shiri.
Doguwar riga na saka mai gyale na
dauko abincin a babban tire na nufi
56
falon shi na waje don a nan na jiyo shi
alamar ya sake yin wasu bakin.
Ni kuma ba zan iya jiran tafiyar su
ba tunda na gane yana 1in yunwa.
Wani irin santsi ne ya debe ni gaba
daya na zame na kife a kasa tire yayi
nesa ya kife abubuwan ciki suka
tarwatse.
Karar fashewar abu da salatin da
nayi ne yasa Ahmad tahowa wurin
cikin sauri har ya karaso inda nake.
Ba iya motsawa ba sa hannu yayi
ya dauke ni zuwa cikin dakinshi
tunda daga inda nake nan dinne ya fa
kusa.
"Sannu Hauwa'u."
Sai dai ko amsawa na kasa yi
saboda wani irin gigitaccen ciwo da
nake jiwowa daga gadon bayana yana
hadowa har gabana zuwa marata.
57
Ya juya yana kiran Larai don tazo
ta kwashe barin da aka yi yana kumna
gayawa Hajiya.
Durkusawa nayi saboda murdawan
da yake yi mun da irin azabar da na
ke sha.
Ahmad yana shigowa tare da
Hajiya daidai lokacin dá naji kamar
fitsari yana zubo mun.
Hajiya ce ta fara salati tana karawa,
wannan wane irin mummunan
faduwa ki ka yi 'yannan. Ai jini nake
gani."
*Jini Hajiya?" Ahmad ya fadi
daidai ya kara matsowa inda nake
cikin sauri ya dauke ni zuwa mota
muka tafi asibiti.
Jinin da ya zuban ya yi yawa, don
haka cikin ya lalace wankin ciki aka
yi mun aka sallamo ni da magunguna
58
muka dawo gida wajen karfe sha
biyun dare saboda cewar da Ahmad
yayi a sallamo ni mu dawo gida.
Cikin dan kankanin lokacin da abin
ya faru nayi wani irin ramewa saboda
bakar azabar da na sha.
A daren Hajiya tazo duba ni ta
kuma hado mun da abincin da ta girka
mun, tuwo miyar kuka ta ce na ci na
sha maganina.
Ba karamin jjjaga Ahmad ya yi da
barin da nayi ba, don kuwa shi mutum
ne mai son haihuwa.
A yanzu kuma Zinatu ita ce
karamar 'yarshi, wacce a bana ya ce
mun shekarunta takwas.
Hakanne yasa ni daurewa nayi
niyyar wartsakewa duk kuwa da abin
da ke damuna a zuciyata.
59
Da safe ma Hajiya ta shigo ta
gaishe ni, haka Larai da Bala direba
de matarshi sai Zubairu.
Wajen karfe tara ne Ahmad ya sake
shigowa ya kalle ni, ganin ina zaune a
kan gadon "Har kina iya tashi?
Na dan yi murmushi na ce, "Ai naji
sauki. Ya zuba mun ido tare da
kamo hannayena duka biyu ya rike a
nashi hannuwan yana dan matsawa.
Yace, Kin dai daure Hauwa'u ba
kin ji sauki ba, ki taya ni addu'a
Ubangiji ya ba mu. wasu masu
albarka." Na ce, "To amin."
Yayi shiru zuwa wani lokaci ya ce
"Ina son zama da ke Hauwa'u. Ina
rokonki ki kara hakuri da duk wata
matsala da ki ke fuskanta a tare da ni
ko wai nawa."
60
Ban fahimci inda maganar tashi ta
dosa ba, amma sai na dan yi
murmushi kawai.
Duk kokarina bai wuce na ganin na
nunawa Ahmad cewa naji sauki ba.
Na dan daure na yi kwalliya na sanya
doguwar riga na fito ina lallabawa
zan shiga dakin, shi ne naji maganar
Zubair.
Kamewa nayi na kasa shiga.
"Na rantse Baba naga lokacin da
Ziradat ta saka ai ba zan yi maka
karya ba, amma ina gaya maka ne
don kada wata rana suyi abinda yafi
haka."
Ahmad ya ce "To kai Zubairu me
yasa da ka ganta ba ka ce komai ba?"
Ya ce, "Ai ni ban san da wata
manufa tayi ba. Na juyo. na dawo
dakina saboda na fahimci wani
61
muhimmin abu ne duk da dai ban san
ko menene ba.
Wajen La'asar na rinka jiwo ihun
yaran, sai dai n1 kam ban je ba, don
ban san abinda yake faruwa ba kumna
babu ruwana ko ma menene.
A dakina yau ma na kwana sai dai
tare da Ahmad.
Washegari matar Bala direba ta
dawo gaishe ni tana zaune a kan
kujera muna yar hira saboda
mutuntani da matar take yi da kuma
kokarin shiga sabgata yasa nake dan
hira da ita.
Don ba za ta wuce sa'ata ba.
"Oh ni 'yasu, wadannan yara kuma
ashe sune."
Na ce, Su ne kamar ya ya?
Wadanne yara? " Nayi mata
tambayoyin a tare kuma lokaci daya.
62
"Au, jiya ba ki jiyo ihunsu ba? Ai
Baban ne ya yi musu duka ba na wasa
ba, don wansu yaje ya gaya mishi
cewa ita wannan shu'umar ita ce ta
saka miki abu ki ka fadi."
Nayi shiru ina kallonta saboda jin
abin da take fada, abin dai ya yi
matukar bani mamaki, sai dai duk da
haka ban tanka ba don tsoron halin
mutane.
Shiru nayi a kwance ina tunani me
nayi wa wadannan mutane haka?
Ahmad ya shigo ya nemi wuri kusa da
ni ya zauna.
"Ya ya Amarya me ke faruwa ne?"
Ban ce mishi komai ba sai zuba
mishi ido da nayi. Ya jawo ni jikinshi
yana cewa.
63
"Kin san fa tunda wannan ya fita to
aiki ya koma baya, sabon zubi kumna
zamu yi yanzu."
Daurewa nayi na ce mishi "To,
amma dai ai ba yanzu ba ko?" Ya ce,
"Eh to, ko gobe tunda Likita ya ce
bari ba a wuce kwana uku, ko ba haka
ba?"
Wartsakewa nayi saboda
farantawa maigidan rai na nuna mishi
naji sauki don hankalinshi ya kwanta.
Haka nan kuma abubuwa sun
matukar yi mun sauki ba kadan ba,
tunda dai yanzu zan iya ganin Ziradat
a hanya ba tare da ta ja mun tsaki ba.
Abin har mamaki nake yi, wai 'yar
karamar yarinya mai shekaru goma
sha uku ce ta ke irin wannan abin.
64
Lokacin komawan Zubair
Makaranta ya yi, don dama hutun
nasu ba mai yawa ba ne.
Tambayar shi nayi abinda yake so
nayi mishi na tafiya. Ya yi shiru yana
'yan tunane-tunane.
Ya ce, Ai ba na so ne Baba ya ji
zai ce na cika fitina, tun da ana siya
mun komai."
Na ce, "To fada mun ba zan bari ya
ji ba." Ya ce, "To ina son kek irin
wanda ki ka yi da sallah."
Na ce, "Sai me?" Ya ce, "Ko shi
kadai aka yi mun Aunty na gode. Na
ce, "To shi kenan.
Cefane sosai nasa aka yi na kira
Larai muka yi aikin tare. Cincin nayi
mishi mai yawa, nayi mishi kek na
sassaka su a leda daidai saboda kada
su bushe tunda Makaranta ce.
65
Sai dambun naman da nayi mishi
cikin babbar roba fara.
Ana gobe zai tafi na ba shi tsalle ya
rinka yi kamarzai yi ya ya don murna.
Sallamaa muka yi mai dadi ya kumaa
roke ni idan Babanshi zai je mishi
visiting na raka shi muje tare, na ce
to.
Da yamma ne Ahmad ya shigoo
bayan ya kai shi Makaranta ya dawo
na kawo mishi ruwa mai sanyi yasha
sannan ya yi hamdala ya ce "Zubairu
ya ce na sake yi miki godiya."
Ban saurare shi ba kicin na koma
na hado mishi fruit salad na kawvo
mishi, ya karba yana sha ya ce "To ni
ina nawa dambun naman?"
Na kalle shi na gane da gaske yake
yi na ce "Ban ajiye maka ba saboda
ya ce ba ya so ka sani."
66
Ya dan yi murmushi ya ce, "Haka
ya gaya mun, to amma kuma sai ya
kasa yin shirun ya fada mun da
kanshi.
Kin san alheri komai kankantarshi
yawa ne da shi, to ballantana irin
wannan."
Na ce, "Kai dai don Allah bari zuga
ni, ai ba da kudina nayi ba a cikin
cefanen gida na saka."
Ya ce, "Ko ma dai ya ya ne ai
cefanen gida idan wata ce ba za ta yi
ba, ina so kuma na gaya miki cewa ba
Zubairu ki ka yi ma ba ni ki ka yi ma,
zan kuma tabbatar. ban mance
alherinki ba."
Komawar Zubairu Makaranta sai
abubuwwa suka sake rincabewa. Ashe
dama sun bari ne don sun gane yana
kai kararsu wurin Babansu.
67
To yanzu ba ya nan sun ci gaba
daga inda suka tsaya. Sai dai Ziradat
ta riga ta tsorata saboda dukan da
Baban ya yi mata a kaina.
Zainab ce take nuna mun salo iri-iri
na rashin kunya da kuma nuna 1sa,
amma na danne zuciyata ko kallon
iya-shegenta bana yi.
A daidai nan ne kuma wani sabon
laulayin ya kama ni, watanni uku
bayan barin da nayi.
Amma a hakan na tsaya tsayin daka
wajen ganin na gamsar da mijina duk
wata lalura tashi.
Kullum nayi mishi maganar zuwa
gida sai ya yi mirsisi ya hana ni, ya ce
ba na yi mishi adalci da yana gari
amma sai na tsallake hidimominshi na
tafi gidanmu.
68
Na ce, To ai kai da rana kana
kasuwa, da daddare ne ka ke dawowa
gida ka bar ni mana naje da rana na
dawo kafin lokacin dawowarka gida?
Sai ya ce, Wai a'a yafi son idan ya
tuna ni a lokacin da yake kasuwa ya
rinka tuna ni a cikin gidan shi ina
harkokina.
Kallon Ahmad kawai nayi nayi
murmushin takaici, amma a raina
tunda ba ni da abin yi a kai, ba na
musu dashi koda kuwa hukuncin da
ya yanke bai yi mun dadi ba.
Hakanne yasa da yazo tafiya Kano
gaida kanin Babanshi da ya yi rashin
lafiya, tafiyar kwana daya sai na tuna
mishi da zuwana gida.
Ya ce, Ba ki fa da lafiya Hauwa'u.
Na dakatar da hada mishi kayan da
69
nake y1, na ce "Haba yallabai, ba
haka muka yi da kai ba fa."
Ya ce, "Eh na sani, amma ai
wannan karon tafiyar tawa ba mai
jimawa ba ce, kwana daya zan yi."
Na ce, To ni ai tawa tafiyar wuni
ce. Shiru yayi sai da ya fita wurin
Hajiya ya dawo sannan ya ce naje
gidan yau Bala zai kai ni."
Nayi tsalle don murna ya ce, "To
kin gani ba. Nayi-nayi da ke ki rinka
kula da irin wadannan abubuwan kin
ki kanmar kin mance da abinda ya
same ki wancan karon."
Ahmad yana tafiya nayi shirina tsaf
na rufe sashena na fito na shiga wurin
Hajiya don nayi mata sallama.
Sannan na fito harabar gidan na
samu Bala har ya yi warming din
mota ni yake jira.
70
Sai kawai ga Zainab da Ziradat sun
fito su ma za su je unguwa. Kai tsaye
suka nufi motar za su shiga.
Bala ya ce, "A'a Zainab kada ki
shiga motar nan, Hajiya zan kai
unguwa a ciki."
Tayi mishi wani wawan kallo.
Akwai wata HHajiya nc a gidan nan
baya ga wacce dama can na sani? Ina
tsaye a gefe ina kallonsu ban tanka
ba.
Ita dai Ziradat ta dan nutsu duk da
dai nasan ba wani hankali ta kara ba.
Zainab ce da Bala dircba suke ta
jayayya ya shiga mota ya tuka ya ki,
ita kuma ta fita a motar ta ki.
Ziradat fita kije ki kira mun
Hajiya. Ba a wani jima ba sai ga
Hajiya ta iso wurin cikin hijabinta.
71
"Lafiya?" Ta kalli Bala dircba. Nan
da nan ya fara yi mata bayanin abinda
ke faruwa.
Hajiya ta kalli Zainab ta ce, "To ke
Zainaba ku shiga mana idan aka
sauke ta a gidansu sai a kai ku taku
unguwar ba shi kenan ba."
Nan take ta fashe da kuka ita
gaskiya ba za ta shiga mota da ni ba,
bayan ba sonsu nake yi ba.
Na kalli Bala na ce, "Bala idan ka
kai su ka dawo kayi mun magana.
Ya ce,"To Hajiya. Na dawo na shiga
dakina na zauna.
Ban san yadda zan yi da yarannan
ba, abinda na sani shi ne bana kin su.
Na zauna kato-kato ina jiran Bala ya
dawo da su Zainab mu tafi bai dawo
gidan ba sai wajen karfe hudu da rabi.
72
Har sashena ya iso yayi sallama, na
ce "Kun dawo Bala? Ya ce, "Eh
Hajiya kiyi hakuri zai fara yi mun
bayani na ce a'a Bala babu komai je
ka kawai."
Ya tsaya zai ci gaba da ba ni
hakuri, na ce ba fushi nayi ba Bala,
amma kaga gidanmu zan je yanzu
kuma yamma ta riga tayı, ya ce to
Hajiya na gode.
Washegari ba ni da halin fita tunda
Ahmad zai dawo gida a ranar, don
haka tashi nayi don nayi mishi shiri.
Da aikin wurinshi na fara. Na
wanke bayan-gida, nayi shara ko ina
fes sannan na canza labilayen dakin
gaba daya na zuba wasu na kira mai
wanki na ba shi.
Na sake shimfida ko ina ya yi kal,
sai kamshi kawai. Na dawo sashena
73
na shirya mishi abinci na yi mishi
fruit salad sannan na shiga bandaki
nayi wanka nayi kintsi na sosai.
Nayi kwalliya mai kyau ta riga da
siket, ina gamawa ko sai ga isowar
motarshi cikin gidan.
Sai da ya shiga wurin Hajiya kamar
yadda ka'idar shi yake, sannan ya
shigo wurina da gudu na isa inda yake
na rungume shi ina mishi oyoyo.
Yana dariya ya ce, Anya Hauwa'u
ce kuwa ba canje aka yi mun ba da ba
na nan?
Na ce, Canje kuma 'Yallabai? Ya
ce, Eh mana naga ne sai wani
danyacewa ki ke yi kina dawowa 'yar
karamar yarinya.
Sashen shi muka shiga don ya yi
wanka, yana ganin irin gyaran da na
yi wa wurin ya ce, "Wow! Ke da
74
waye ku ka yi wannan aikin
Hauwa'u?
Na ce, "Da waye ka ke tsammanin
zan yi?" Ya dan yi shiru zuwa can ya
dan kada kai ya ce, "Ke kadai ko?"
Na ce, Yauwa ashe ka gane kenan?
Ya ce, To Allah yayi miki albarka. Na
wuce shi na shiga bandakin shi ina
hada mishi ruwa da turarukan wanka.
Ya shiga ni kuma na fito na ciro
mishi jallabiya ruwan kasa saboda
sanin da nayi zai fita zuwa Masallaci
idan anyi magriba.
Yana cin abinci ina zuba mishi
yana ba ni labarin garinsu da mutanen
garin.
Ya ce, "Sai kin haihu zamu je su
ganki suga abin da muka samu. Ya ce
kin ga ma na manta jiya da muka yi
waya ban tambaye ki su Umma ba.
75
Na ce, Ai ma ban je ba. Ya kalle ni
ya ce, Ba ki je ba kuma? Na ce, Eh. to
saboda me? Nayi shiru ban ce mishi
komai ba.
Ya ce, Ke dinnan fitanarki yawa ne
da ita, da ban bar ki ba da har yanzu
kina yi mun mitar na hana ki zuwa
gida.
Ya fita sallar Magriba ya wuce
wurin Hajiya, bai dawo ba sai da aka
yi sallar Isha'i sannan ya shigo.
Tashi ki shirya muje gidan tare.
Sannan ya wuce sashenshi. Ya dawo
sanye da jamfa da wando na yadin
material din maza yana rike da
mukulln mota a hannunshi.
Ni ma yadin material na saka mai
hadari ya kuma yi mun kyau sosai.
Muka fito tare muka shiga wurin
Hajiya don yi mata sallama.
76
Ta ce, lna zuwa haka a daren nan?
Ya ce, "Yar wata unguwa zata raka