MAI DAKI BOOK 3 Hausa Novels by Sodangi. .docx

Author :  Hafsat C Sodangi Category :  KDP NOVELS

Chapter   3 / 6

6K to 9K   out of 15.7K words

Ziradat.

52

Zama yazo yayi yana gaya mun

abubuwan da yake so nayi mishi, na

sallah saboda bakin abokanshi da za

su kawo mishi ziyara.

Na ce, To ka bari mana idan nayi

na Babanku sai na diban maka a ciki.

Yayi godiya sosai, take kuma farin

cikinshi ya bayyana, ya tashi ya tafi.

Bai dade da fita ba na fita don

zuwa sashen Hajiya kai mata farfesun

kodar da Ahmad ya aiko ya ce nayi

mata da hannuna.

Na isa bakin kofar tun kafin nayi

sallama naji Ziradat tana cewa, "Ai

munafuka ce tunda gashi har Hajiya

ma yanzu ba ta yarda idan mun ce

mata tayı mana wani abu.

Ni a matan da Babanmu ya aura

duk ita nafi tsana. Hajiya ta ce,

53

"Um'um Ziradat na fa kwabe ki da

irin wannan maganganun."

Shi kuma Zubair cewa ya yi "Ni

banä son irin wadannan maganganun

ban san abinda yasa Baba yake biye

muku ba.

Menene laifin wannan matar? Ko

harkar mutum bata shiga ba za ku

taba barin Baba ya zauna lafiya da

mata ba. Shi kuma ku ke sakawa a

matsala."

Sallama nayi na ajiye mata na fito

na dawo wurina, a raina na ce kwaji

da shi, ni kam nawa auren daram in

Allah ya yarda.

Shiri sosai nayi na sallah mutanen

gidan kaf na basu abinci da abinsha

da su kek din da nayi ba tare da nayi

la'akari da Hajiya tayi ba.

54

Makwabta baki daya sai da na

zagaya su da abinci. Ahmad ne kuma

ya taso keyar su Zainab suka kai mun

rabon.

Gidanmu ma duk da ya aike musu

da nama cikin babban baho saboda

yankan da yayi da kuma shinkafa da

tumatur kwando.

Bai hana ni kai musu abincin sallah

ba wannan kuwa Bala direba na aika.

Da yamma ne baki abokan harkar

Ahmad suka zo gidan hakan ne yasa

sashenshi ya cika dankam ba kadan

ba.

Nima gagarumar liyafa na shirya

musu sinasir da farfesun kafar saniya

sai dambun nama da kek da manyan

donghnut na asali mai ridi.

Sai kwalayen juice wanda na hada

musu duka a cikin wani madaidaicin

55



kwando na Rafia da nayi rafin

dinshi da wata 'yar leda da aka rubuta

iyalan gidan Alhaji Ahmad Rufa'i

suna muku barka da Edil Fitr.

Kuma gaba dayansu ya wadace su.

Shima abin yayi mishi dadi ba kadan

ba.

Ya shigo dakina lokacin da nake

shirin shiga wanka har yanzu

fuskarshi a washe take ya sa hannu ya

dauke ni yana cewa bari nima na taya

ki wankan irin wannan gajiya da ki ka

yi haka.

Duk da dai ni da yunwa ki ka bar ni

na ce, "Haba yallabai na dauka ai

yau ba za ka ji yunwa ba."

Dariya yayi ya fita bayan ya gaya

mun yana jirana idan na gama shiri.

Doguwar riga na saka mai gyale na

dauko abincin a babban tire na nufi

56

falon shi na waje don a nan na jiyo shi

alamar ya sake yin wasu bakin.

Ni kuma ba zan iya jiran tafiyar su

ba tunda na gane yana 1in yunwa.

Wani irin santsi ne ya debe ni gaba

daya na zame na kife a kasa tire yayi

nesa ya kife abubuwan ciki suka

tarwatse.

Karar fashewar abu da salatin da

nayi ne yasa Ahmad tahowa wurin

cikin sauri har ya karaso inda nake.

Ba iya motsawa ba sa hannu yayi

ya dauke ni zuwa cikin dakinshi

tunda daga inda nake nan dinne ya fa

kusa.

"Sannu Hauwa'u."

Sai dai ko amsawa na kasa yi

saboda wani irin gigitaccen ciwo da

nake jiwowa daga gadon bayana yana

hadowa har gabana zuwa marata.

57

Ya juya yana kiran Larai don tazo

ta kwashe barin da aka yi yana kumna

gayawa Hajiya.

Durkusawa nayi saboda murdawan

da yake yi mun da irin azabar da na

ke sha.

Ahmad yana shigowa tare da

Hajiya daidai lokacin dá naji kamar

fitsari yana zubo mun.

Hajiya ce ta fara salati tana karawa,

wannan wane irin mummunan

faduwa ki ka yi 'yannan. Ai jini nake

gani."

*Jini Hajiya?" Ahmad ya fadi

daidai ya kara matsowa inda nake

cikin sauri ya dauke ni zuwa mota

muka tafi asibiti.

Jinin da ya zuban ya yi yawa, don

haka cikin ya lalace wankin ciki aka

yi mun aka sallamo ni da magunguna

58

muka dawo gida wajen karfe sha

biyun dare saboda cewar da Ahmad

yayi a sallamo ni mu dawo gida.

Cikin dan kankanin lokacin da abin

ya faru nayi wani irin ramewa saboda

bakar azabar da na sha.

A daren Hajiya tazo duba ni ta

kuma hado mun da abincin da ta girka

mun, tuwo miyar kuka ta ce na ci na

sha maganina.

Ba karamin jjjaga Ahmad ya yi da

barin da nayi ba, don kuwa shi mutum

ne mai son haihuwa.

A yanzu kuma Zinatu ita ce

karamar 'yarshi, wacce a bana ya ce

mun shekarunta takwas.

Hakanne yasa ni daurewa nayi

niyyar wartsakewa duk kuwa da abin

da ke damuna a zuciyata.

59

Da safe ma Hajiya ta shigo ta

gaishe ni, haka Larai da Bala direba

de matarshi sai Zubairu.

Wajen karfe tara ne Ahmad ya sake

shigowa ya kalle ni, ganin ina zaune a

kan gadon "Har kina iya tashi?

Na dan yi murmushi na ce, "Ai naji

sauki. Ya zuba mun ido tare da

kamo hannayena duka biyu ya rike a

nashi hannuwan yana dan matsawa.

Yace, Kin dai daure Hauwa'u ba

kin ji sauki ba, ki taya ni addu'a

Ubangiji ya ba mu. wasu masu

albarka." Na ce, "To amin."

Yayi shiru zuwa wani lokaci ya ce

"Ina son zama da ke Hauwa'u. Ina

rokonki ki kara hakuri da duk wata

matsala da ki ke fuskanta a tare da ni

ko wai nawa."

60

Ban fahimci inda maganar tashi ta

dosa ba, amma sai na dan yi

murmushi kawai.

Duk kokarina bai wuce na ganin na

nunawa Ahmad cewa naji sauki ba.

Na dan daure na yi kwalliya na sanya

doguwar riga na fito ina lallabawa

zan shiga dakin, shi ne naji maganar

Zubair.

Kamewa nayi na kasa shiga.

"Na rantse Baba naga lokacin da

Ziradat ta saka ai ba zan yi maka

karya ba, amma ina gaya maka ne

don kada wata rana suyi abinda yafi

haka."

Ahmad ya ce "To kai Zubairu me

yasa da ka ganta ba ka ce komai ba?"

Ya ce, "Ai ni ban san da wata

manufa tayi ba. Na juyo. na dawo

dakina saboda na fahimci wani

61

muhimmin abu ne duk da dai ban san

ko menene ba.

Wajen La'asar na rinka jiwo ihun

yaran, sai dai n1 kam ban je ba, don

ban san abinda yake faruwa ba kumna

babu ruwana ko ma menene.

A dakina yau ma na kwana sai dai

tare da Ahmad.

Washegari matar Bala direba ta

dawo gaishe ni tana zaune a kan

kujera muna yar hira saboda

mutuntani da matar take yi da kuma

kokarin shiga sabgata yasa nake dan

hira da ita.

Don ba za ta wuce sa'ata ba.

"Oh ni 'yasu, wadannan yara kuma

ashe sune."

Na ce, Su ne kamar ya ya?

Wadanne yara? " Nayi mata

tambayoyin a tare kuma lokaci daya.

62

"Au, jiya ba ki jiyo ihunsu ba? Ai

Baban ne ya yi musu duka ba na wasa

ba, don wansu yaje ya gaya mishi

cewa ita wannan shu'umar ita ce ta

saka miki abu ki ka fadi."

Nayi shiru ina kallonta saboda jin

abin da take fada, abin dai ya yi

matukar bani mamaki, sai dai duk da

haka ban tanka ba don tsoron halin

mutane.

Shiru nayi a kwance ina tunani me

nayi wa wadannan mutane haka?

Ahmad ya shigo ya nemi wuri kusa da

ni ya zauna.

"Ya ya Amarya me ke faruwa ne?"

Ban ce mishi komai ba sai zuba

mishi ido da nayi. Ya jawo ni jikinshi

yana cewa.

63

"Kin san fa tunda wannan ya fita to

aiki ya koma baya, sabon zubi kumna

zamu yi yanzu."

Daurewa nayi na ce mishi "To,

amma dai ai ba yanzu ba ko?" Ya ce,

"Eh to, ko gobe tunda Likita ya ce

bari ba a wuce kwana uku, ko ba haka

ba?"

Wartsakewa nayi saboda

farantawa maigidan rai na nuna mishi

naji sauki don hankalinshi ya kwanta.

Haka nan kuma abubuwa sun

matukar yi mun sauki ba kadan ba,

tunda dai yanzu zan iya ganin Ziradat

a hanya ba tare da ta ja mun tsaki ba.

Abin har mamaki nake yi, wai 'yar

karamar yarinya mai shekaru goma

sha uku ce ta ke irin wannan abin.

64

Lokacin komawan Zubair

Makaranta ya yi, don dama hutun

nasu ba mai yawa ba ne.

Tambayar shi nayi abinda yake so

nayi mishi na tafiya. Ya yi shiru yana

'yan tunane-tunane.

Ya ce, Ai ba na so ne Baba ya ji

zai ce na cika fitina, tun da ana siya

mun komai."

Na ce, "To fada mun ba zan bari ya

ji ba." Ya ce, "To ina son kek irin

wanda ki ka yi da sallah."

Na ce, "Sai me?" Ya ce, "Ko shi

kadai aka yi mun Aunty na gode. Na

ce, "To shi kenan.

Cefane sosai nasa aka yi na kira

Larai muka yi aikin tare. Cincin nayi

mishi mai yawa, nayi mishi kek na

sassaka su a leda daidai saboda kada

su bushe tunda Makaranta ce.

65

Sai dambun naman da nayi mishi

cikin babbar roba fara.

Ana gobe zai tafi na ba shi tsalle ya

rinka yi kamarzai yi ya ya don murna.

Sallamaa muka yi mai dadi ya kumaa

roke ni idan Babanshi zai je mishi

visiting na raka shi muje tare, na ce

to.

Da yamma ne Ahmad ya shigoo

bayan ya kai shi Makaranta ya dawo

na kawo mishi ruwa mai sanyi yasha

sannan ya yi hamdala ya ce "Zubairu

ya ce na sake yi miki godiya."

Ban saurare shi ba kicin na koma

na hado mishi fruit salad na kawvo

mishi, ya karba yana sha ya ce "To ni

ina nawa dambun naman?"

Na kalle shi na gane da gaske yake

yi na ce "Ban ajiye maka ba saboda

ya ce ba ya so ka sani."

66

Ya dan yi murmushi ya ce, "Haka

ya gaya mun, to amma kuma sai ya

kasa yin shirun ya fada mun da

kanshi.

Kin san alheri komai kankantarshi

yawa ne da shi, to ballantana irin

wannan."

Na ce, "Kai dai don Allah bari zuga

ni, ai ba da kudina nayi ba a cikin

cefanen gida na saka."

Ya ce, "Ko ma dai ya ya ne ai

cefanen gida idan wata ce ba za ta yi

ba, ina so kuma na gaya miki cewa ba

Zubairu ki ka yi ma ba ni ki ka yi ma,

zan kuma tabbatar. ban mance

alherinki ba."

Komawar Zubairu Makaranta sai

abubuwwa suka sake rincabewa. Ashe

dama sun bari ne don sun gane yana

kai kararsu wurin Babansu.

67

To yanzu ba ya nan sun ci gaba

daga inda suka tsaya. Sai dai Ziradat

ta riga ta tsorata saboda dukan da

Baban ya yi mata a kaina.

Zainab ce take nuna mun salo iri-iri

na rashin kunya da kuma nuna 1sa,

amma na danne zuciyata ko kallon

iya-shegenta bana yi.

A daidai nan ne kuma wani sabon

laulayin ya kama ni, watanni uku

bayan barin da nayi.

Amma a hakan na tsaya tsayin daka

wajen ganin na gamsar da mijina duk

wata lalura tashi.

Kullum nayi mishi maganar zuwa

gida sai ya yi mirsisi ya hana ni, ya ce

ba na yi mishi adalci da yana gari

amma sai na tsallake hidimominshi na

tafi gidanmu.

68

Na ce, To ai kai da rana kana

kasuwa, da daddare ne ka ke dawowa

gida ka bar ni mana naje da rana na

dawo kafin lokacin dawowarka gida?

Sai ya ce, Wai a'a yafi son idan ya

tuna ni a lokacin da yake kasuwa ya

rinka tuna ni a cikin gidan shi ina

harkokina.

Kallon Ahmad kawai nayi nayi

murmushin takaici, amma a raina

tunda ba ni da abin yi a kai, ba na

musu dashi koda kuwa hukuncin da

ya yanke bai yi mun dadi ba.

Hakanne yasa da yazo tafiya Kano

gaida kanin Babanshi da ya yi rashin

lafiya, tafiyar kwana daya sai na tuna

mishi da zuwana gida.

Ya ce, Ba ki fa da lafiya Hauwa'u.

Na dakatar da hada mishi kayan da

69

nake y1, na ce "Haba yallabai, ba

haka muka yi da kai ba fa."

Ya ce, "Eh na sani, amma ai

wannan karon tafiyar tawa ba mai

jimawa ba ce, kwana daya zan yi."

Na ce, To ni ai tawa tafiyar wuni

ce. Shiru yayi sai da ya fita wurin

Hajiya ya dawo sannan ya ce naje

gidan yau Bala zai kai ni."

Nayi tsalle don murna ya ce, "To

kin gani ba. Nayi-nayi da ke ki rinka

kula da irin wadannan abubuwan kin

ki kanmar kin mance da abinda ya

same ki wancan karon."

Ahmad yana tafiya nayi shirina tsaf

na rufe sashena na fito na shiga wurin

Hajiya don nayi mata sallama.

Sannan na fito harabar gidan na

samu Bala har ya yi warming din

mota ni yake jira.

70

Sai kawai ga Zainab da Ziradat sun

fito su ma za su je unguwa. Kai tsaye

suka nufi motar za su shiga.

Bala ya ce, "A'a Zainab kada ki

shiga motar nan, Hajiya zan kai

unguwa a ciki."

Tayi mishi wani wawan kallo.

Akwai wata HHajiya nc a gidan nan

baya ga wacce dama can na sani? Ina

tsaye a gefe ina kallonsu ban tanka

ba.

Ita dai Ziradat ta dan nutsu duk da

dai nasan ba wani hankali ta kara ba.

Zainab ce da Bala dircba suke ta

jayayya ya shiga mota ya tuka ya ki,

ita kuma ta fita a motar ta ki.

Ziradat fita kije ki kira mun

Hajiya. Ba a wani jima ba sai ga

Hajiya ta iso wurin cikin hijabinta.

71

"Lafiya?" Ta kalli Bala dircba. Nan

da nan ya fara yi mata bayanin abinda

ke faruwa.

Hajiya ta kalli Zainab ta ce, "To ke

Zainaba ku shiga mana idan aka

sauke ta a gidansu sai a kai ku taku

unguwar ba shi kenan ba."

Nan take ta fashe da kuka ita

gaskiya ba za ta shiga mota da ni ba,

bayan ba sonsu nake yi ba.

Na kalli Bala na ce, "Bala idan ka

kai su ka dawo kayi mun magana.

Ya ce,"To Hajiya. Na dawo na shiga

dakina na zauna.

Ban san yadda zan yi da yarannan

ba, abinda na sani shi ne bana kin su.

Na zauna kato-kato ina jiran Bala ya

dawo da su Zainab mu tafi bai dawo

gidan ba sai wajen karfe hudu da rabi.

72

Har sashena ya iso yayi sallama, na

ce "Kun dawo Bala? Ya ce, "Eh

Hajiya kiyi hakuri zai fara yi mun

bayani na ce a'a Bala babu komai je

ka kawai."

Ya tsaya zai ci gaba da ba ni

hakuri, na ce ba fushi nayi ba Bala,

amma kaga gidanmu zan je yanzu

kuma yamma ta riga tayı, ya ce to

Hajiya na gode.

Washegari ba ni da halin fita tunda

Ahmad zai dawo gida a ranar, don

haka tashi nayi don nayi mishi shiri.

Da aikin wurinshi na fara. Na

wanke bayan-gida, nayi shara ko ina

fes sannan na canza labilayen dakin

gaba daya na zuba wasu na kira mai

wanki na ba shi.

Na sake shimfida ko ina ya yi kal,

sai kamshi kawai. Na dawo sashena

73



na shirya mishi abinci na yi mishi

fruit salad sannan na shiga bandaki

nayi wanka nayi kintsi na sosai.

Nayi kwalliya mai kyau ta riga da

siket, ina gamawa ko sai ga isowar

motarshi cikin gidan.

Sai da ya shiga wurin Hajiya kamar

yadda ka'idar shi yake, sannan ya

shigo wurina da gudu na isa inda yake

na rungume shi ina mishi oyoyo.

Yana dariya ya ce, Anya Hauwa'u

ce kuwa ba canje aka yi mun ba da ba

na nan?

Na ce, Canje kuma 'Yallabai? Ya

ce, Eh mana naga ne sai wani

danyacewa ki ke yi kina dawowa 'yar

karamar yarinya.

Sashen shi muka shiga don ya yi

wanka, yana ganin irin gyaran da na

yi wa wurin ya ce, "Wow! Ke da

74



waye ku ka yi wannan aikin

Hauwa'u?

Na ce, "Da waye ka ke tsammanin

zan yi?" Ya dan yi shiru zuwa can ya

dan kada kai ya ce, "Ke kadai ko?"

Na ce, Yauwa ashe ka gane kenan?

Ya ce, To Allah yayi miki albarka. Na

wuce shi na shiga bandakin shi ina

hada mishi ruwa da turarukan wanka.

Ya shiga ni kuma na fito na ciro

mishi jallabiya ruwan kasa saboda

sanin da nayi zai fita zuwa Masallaci

idan anyi magriba.

Yana cin abinci ina zuba mishi

yana ba ni labarin garinsu da mutanen

garin.

Ya ce, "Sai kin haihu zamu je su

ganki suga abin da muka samu. Ya ce

kin ga ma na manta jiya da muka yi

waya ban tambaye ki su Umma ba.

75



Na ce, Ai ma ban je ba. Ya kalle ni

ya ce, Ba ki je ba kuma? Na ce, Eh. to

saboda me? Nayi shiru ban ce mishi

komai ba.

Ya ce, Ke dinnan fitanarki yawa ne

da ita, da ban bar ki ba da har yanzu

kina yi mun mitar na hana ki zuwa

gida.

Ya fita sallar Magriba ya wuce

wurin Hajiya, bai dawo ba sai da aka

yi sallar Isha'i sannan ya shigo.

Tashi ki shirya muje gidan tare.

Sannan ya wuce sashenshi. Ya dawo

sanye da jamfa da wando na yadin

material din maza yana rike da

mukulln mota a hannunshi.

Ni ma yadin material na saka mai

hadari ya kuma yi mun kyau sosai.

Muka fito tare muka shiga wurin

Hajiya don yi mata sallama.

76



Ta ce, lna zuwa haka a daren nan?

Ya ce, "Yar wata unguwa zata raka

3 / 6