MAI DAKI BOOK 3 Hausa Novels by Sodangi. .docx

Author :  Hafsat C Sodangi Category :  KDP NOVELS

Chapter   4 / 6

9K to 12K   out of 15.7K words

/>
ni. Ta ce, To a dawo lafiya. Muka

fito.

A wani babban shago ya tsaya ya yii

siyayya mai yawa, sannan muka wuce

gida.

Hira muke yi sosai da Umma shi

kuwa yana wurin Babana ba mu dawo

ba sai wajen karfe goma na dare.

Tashi nayi naga jini kadan-kadan

yana fitar mun, sai dai ban kula na

gani ba sai bayan da Ahmad ya tafi

kasuwa.

Bana son daga mishi hankali, don

haka nayi nufin bari sai ya dawo naayi

mishi bayani.

Nayi ta aikace-aikacena ba tare da

wani abu a raina ba, tunanina dai bai

wuce laulayi irin na ciki ba.

77

Sai da na gama ayyukana na shiga

bayan gida da nufin yin wanka, sai

kawai na ganni kace-kace cikin jini.

Sauri nayi na fito na dauki waya na

sanarwa Ahmad cewa ina son Zuwa

asibiti, ya ce lafiya? Na ce ch, ba na

dai jin dadi ne kawai, ya ce to Allah

ya sauwake.

Bala ya kai ni asibiti sai dai tun

kafin nan a takure nake cikin sauri

aka kai ni dakin Likita sai dai gwajin

farko ya tabbatar mana cikin ya

lalace, ya fita daga mahaifa dole a

cire.

Duk da halin da nake ciki a haka na

daure na kira Ahmad.

Cikin kankanin lokaci ya iso

asibitin, sai dai duk da saurin da ya yi

har an shigar da ni don wanke mun

mahaifa.

78

Duk da kokarin da nayi tayi na

hana kaina kuka kasa daurewa nayi da

Ahmad ya iso kaina.

Wannan karon ma bari nayi na ciki

wata hudu har da sati biyu, kamar dai

wancan kenan.

Kwana nayi a asibitin kowa kuma

yazo duba ni har daga gidanmu.

Likita ya shigo saboda sallama ta da

za a yi Ahmad yana yi mishi wasu

yan tambayoyi.

Ya ce, To dai a fayil dinta na ga ta

samu matsala makamanciyar wannan

shima a watanni hudu, don haka

tunda ga abinda ka fada zamu sake yi

mata scarming don mu gani ko da

matsala.

Likitan ya jawo wata 'yar takarda

yayi rubutu ya bamu. Ahmad ne da

kanshi ya kai ni wurin scarning din

79



muka dawo Likita ya duba ya ce, "To

a gaskiya ta samu matsala ne a

mahaifa saboda jijigar farat-daya da

mahaifarta tayi a wancan karon.

Saboda irin faduwar da tayi, hakan

ne yasa mahaifarta ba za ta iya rikke

wani ciki da zai yi fiye da watanni

hudu a mahaifarta ba.

Saboda bakin mahaifarta da ya riga

ya bude. Kuma shawarar da zan ba ku

a yanzu shi ne, kafin a san matakin da

za a dauka a kan matsalar, ta dan yi

hutu.

Don kuwa idan tayi wani cikin ma

a yanzu abinda zai faru kenan.

Dawowa gida muka yi jikinmu a

sanyaye, ni kam Ciwo ne ya rufe ni

jinya sosai Ahmad kwata-kwata ranar

bai fita kasuwa ba.

80

Bai kuma fadawa kowa abinda

Likita ya ce ba. Kwana biyu ko

abincin da zan ci daga wurin Hajiya

ake kawo mun.

Kullum kuma Ahmad zai ba ni

hakuri saboda lurar da yayi na dan

saka damuwa a raina.

Duk kokarin da nayi kada ya

fahimci wani abu kasawa nayi. Yau

ma yana zama zai fara mun magana

kuka na kama yi.

Sai da nayi ya ishe ni sannan na

share hawayena, babu abinda ke tsaya

mun a rai naji zuciyata ta baci irin na

tuna 'ya' yan Ahmad ne suka yi mun

wannan sanadin.

To tambayar ita ce, shin idan da ni

ce nayi wa wani a cikin su haka anya

zan zauna lafiya kuwa?

81

Amma gashi nan ni sun yi mun sun

zauna lafiya, sun ma mancc in ban da

shi Ahmad da yake ba ni hakuri.

Duk da warkewan da nayi a duk

lokacin da na tuna ina jin wani iri na

kuma kasa sakewa nayi harkokina

kamar da.

Ko shi Ahmad din ya lura ya gane

hakan, don yau ma muna zaune a

falonshi muna kallon labarai ya Juyo

yana kallona.

Hauwa'u magana nake so nayi

miki. Na lura duk tsawon lokacin nan

har yanzu ba ki saki jikinki ba.

Na kuma tambaycki shekaran iya

ko wani abu na damunki ne kin ce

a'a, lafiyarki kalau.

Ina so ki san wannan abun ba ke

kadai ya samu ba har da ni, amma

82

kuma kin takura ni na rasa walwalar

da a da nake farin cikin samu.

Idan ni ne nayi miki wani abu ki

gaya mun na gyara, idan kuma a kan

matsalar nan ne ina so kiyi hakuri.

Ina kokarin a wannan watan da zai

kama idan zan yi tafiya mu tafi tare

saboda wannan matsalar, sai ki ga

Likita a Dubai."

Ban ce mishi komai ba, amma nayi

kokari wajen ganin na rage takura ko

don saboda Ahmad.

Sai dai har karshen wata yazo ya

wuce Ahmad bai yi tafiyar ba, bai

kuma ce mun komai ba.

Muna kwance a dakinshi da

daddare a daren da ya dawo daga

Legos dauko wasu kayan shi da suka

shigo.

83

Nayi mishi maganar tafiyar da ya

ce zamu yi don ganin Likita. Ya ce,

"Kiyi hakuri Hauwa'u, ina nan ina

wasu shirye-shirye ne kawai."

Sai dai ba a wani jima ba ya shirya

ya tafi Dubai ya dawo ba tare da ya ce

mun komai ba.

Na shiga dakinshi na same shi

zaune ya baje takardu, lissafi yake yi.

Na zauna a gefe ina jiranshi ya gama

shiru bai gama ba har na gaji' na mike

na kwanta nayi barci.

Washegari tun da Asuba yayi shirin

shi gaba daya alamar daga wurin

Hajiya zai wuce.

Haka ina ji ina ganin babu yadda

zan yi ya fita. Da daddare kuwa da ya

dawo sai da na gama mishi komai

sannan na kwashe kwanukan.

84

Wai kafin naje na dawo nayi mishi

maganar da ke Cina a zuciyata nan ma

dawowa nayi na samu wai Hajiya ta

ira shi.

Zama nayi daram a kan kujera ina

jiran shigowarshi, bai shigo ba sai

wajen karfe goma da kwata.

Har yanzu ba ki yi bacci ba?" Na

ce, "Eh kai nake jira." Ya ce, "Akwai

magana kenan? Na ce, "Eh."

Ya gyara ya kwanta ya ce, "To ki

barta gobe kafin na fita kasuwa sai

muyi."

Na ce, Idan kuma a wurina tana da

muhimmanci fa? Ya ce, "Komai

muhimmancinta ki barta sai gobe, don

a yanzu na gaji."

Wani irin gululun bakin ciki ne ya

tokare mun makogorona. Da kyar

nake iya numfashi.

85

Tashi nayi na dawo dakina na hau

gadona na kwanta. Sai dai ban iya yin

barcin ba.

Ji nake yi kamar na koma na samu

Ahmad muyi duk wacce zamu yi da

shi daren nan amma ba zan iya ba.

Ko wani sauraron shi ban yi ba da

safe haka nan shi ma bai bukaci ya ji

maganar da nake son yi da shi ba.

Da dai ya gama shirinshi ne zai fita

ya leko dakin.

"Hauwa'u ina son burabusko da

miyar bindi". Na ce, To babu tsakin

shinkafa." Ya ce, "Ki karba a wurin

su Hajiya." Ya tafi.

Babu abinda na tsana yanzu a

rayuwata irin zuwa wajen su Hajiya.

Tun da dai gaisheta ya zama mun

dole, to kullum da safe ina zuwa

86

amma baya ga haka bana komawa sai

wata safiyar.

Sai da aka yi sallar Azahar sannan

na dauki roba na shiga wurin Hajiyan

na gaya mata ina son tsakin shinkafa.

Ta kalli Zainab ta ce, "Zainaba

tashi ki debowa Mamanku tsakin

shinkafa."

Ta dago ido ta kalle ni, sannan ta

ce, "Maman wasu dai Hajiya, ammna

ban da mu."

Ta ce, "To naji bana dai son rashin

kunya, karbi ki debo mata. Kin dai

kusa tafiya Makaranta a huta."

Ta ce, "Ai idan na ganc tafiyata zai

sa wasu murna ma sai na cc na fasa."

Ta dawo da tsakin a hannunta ta

dangwarar a kasa.

Ban tsaya sauråronta ba, dauka

nayi na yi tafiyata.

87

Zainab a yanzu ta rubuta

jarrabawarta na gama makaranta

sceondary, Jami'a ake neman mata

har ma an samu.

Dawowa wajena nayi na shiga

kokarin ganin na kammala cikin

lokaci, kuma nayi sa'a yayi kyau ya

yi dadi.

Ga kamshi ko ina a cikin gidan. Ina

gamawa na shiga bandaki nayi wanka

na fito kenan naj1 motsi a falona.

Don haka na fito falon bayan na

sanya zulumbun hijabina don ganin

ko waye.

Zainab ce rike da tircn abincin

Babansu, gabaki dayan shi zata fita.

Sa hannu nayi na rike na ce "Yau

kam a'a, abin ya ishe ni haka ba zai

yiwu ba.

88

A duk ranar da ki ka ga kina da

bukatar cin abincina to rinka gaya

mun sai na rinka saka sanwa da ke.

Ba haka kawai idan na gama girki

ki saka hannu ki sunkuci na mijina

kiyi gaba ki bar ni da dora sabo ba."

Ta zuba mun ido tana kallona, nimna

ita nake kallo, don na lura su gaba ki

dayansu ba su san zuru ba.

Kuma a gaban kowa sai Zainab ta

caccaba mun magana ba za a ce

komai ba.

Ba tun yau ba lokuta da dama sai

na gama abinci sai tazo ta sunkuta

gaba daya ta tafi da shi wurinsu ta ci

1ya cinta ta rabar da saura.

Wani lokacin ma ko rabi ba a ci sai

ta bar shi haka ya lalace, sannan ba za

ta dauko kwanukan ta dawo da shi ba

sai dai ni nabi bayan su.

89

Sau daya Hajiya bata taba yin

magana a kan hakan da take yi ba,

duk da tasan abincin danta Zainab

take dauka.

Kallon da take yi mun ne ya ishe ni

nayi nufin karbe tiren, sai kawai

yarinyar nan ta kabar da tiren gaba

daya abubuwan ciki suka watse.

Abincin ya zube a kasa, sannan tayi

murmushi ta raba ta gefena ta wuce.

Zubawa abincin da ya tarwatse din

ido nayi ba na ko kyaftawa.

Ban taba ganin danyen rashin

mutunci irin wannan ba.

Cikin dakina na koma na sanya

doguwar riga na futo zuwa wurin

Hajiya don na gaya mata abinda ke

faruwa.

Na shigo na zauna a kasa zan fara

magana sai ta ce "Dakata! Yau kuma

90

abin naki har ya kai ma ki hana

Zainaba abinci?

Ta dauko kuma kin biyo ta kin

kifar. Me ki ke nufi da abinda ki ka

yin?

Kin taba siyo abinci kin shigo da

shi gidan nan ne da ki ka samu damar

hana wani?"

Na ce, "Hajiya..". "Bana son jin

komai daga bakinki, nasha gaya miki

ba sau daya ba ba sau biyu ba cewa

duk abinda za ki yi a gidan nan to ya

tsaya tsakaninki da wasu amma kada

ki tsallako hurumina, don ba za ki ji

da dadi ba.

Ya ya za ki hanata cin abincin da

ubanta ya kawo ya ajiye takamar kina

matarshi?"

91

Tun ina daurewa bacin raina har

ban san sanda na fara zazzago

maganganu ba.

"Ai tun farko da nazo gidannan na

fara kawo abinci sashen nan aka ce na

daina don kuwa akwai mai girki.

Me yasa tunda haka ne idan tana

son abincina ba za ta fada mun tun da

wuri ba sai na girka da ita, sai ta bari

na gama tazo ta dauke gaba daya

haka ake yi?

Duk hakurin da nake yi da yarann

nan bai isa ba kullum kokarinsu bai

wuce na ganin sun kure ni ba.

Menene na yi musu?

Tunda na fara magana har na gama

Hajiya bata sake cewa komai ba, sai

kallona kawai da take yi.

Zuwa can ta ce, Lallai kin isa, ni

ki ke gayawa irin wadannan

92



maganganun? Dama ai biri ya yi

kama da mutumn.

Tun kwanakin baya na gane ya ba

ki isasshen damar da ta wadace ki. To

amma ba laifinki ba ne.

Tashi ki ba ni wuri, bari yazo ya

same ni mu san wacce muke ciki da

nida shi."

Mikewa nayi na dawo dakina na

kara tsallake abincin a wurin na shiga

uwar dakina na zauna.

Ni kaina na gane nayi kuskure

amsawa Hajiya da nayi, to amma ya

ya zan yi da raina?

Rashin 'yancin yayi yawa, ace wai

har a kan budurwar yarinya mai

shekara goma sha shidda kamar

Zainab za a zaunar da ni a titsiye ni

wai nayi laifi!

93

Kawai takamar ina auren ubanta

bayan da za a bi Silsilar abin za a iya

fahimtar ba ni ba ce mai laifin.

To amma saboda daurin gindi da

Son kai sai ya zama komai suka yi

daidai ne.

A madadin abubuwa su gyaru

kullum kara cabewa suke yi?

Kamar yadda ya saba dawowa haka

ya dawo yau ma. Ko inda yake ban je

ba ballantana na ba shi wani abu.

Don kuwa babu, na kuma san an

gaya mishi komai da ya faru.

Karfe tara har ta wuce ina zaune a

kan sallayata da nayi sallar Isha'i a

kai ban tashi ba.

Jiran kawai abinda zai biyo baya

nake yi. Bai shigo dakin ba sai wajen

karfe goma na dare.

94

Yadda nayi zaton zai shigo ba haka

ya shigo mun ba. Ya karewa abincin

da har yanzu yake shimfide a kasan

falon da food flask din da kuma

fasassun plates din kallo.

Ya sunkuya ya kwashe plates din

da kofunan da suka faffashe ya zubar

a abin zuba shara na nan kicin.

Sannan ya fito ya dawo da abin

kwashe shara da tsintsiya yasa ya

kwashe ya gyara wurin tsaf, sannan

ya wanke hannunshi ya zo ya zauna a

inda nake muna fuskantar juna.

"Ba kya jin maganata Hauwa'u, ko

nayi miki magana ba kya ji. me ya

hada ki da Zainab?"

Nan take na fahse da kuka saboda

karayar da nayi. Nayi kukana sai da

na gaji nayi shiru, sannan nayi mishi

bayanin komai.

95

Tun daga lokacin da Zainab ta tsiro

da abubuwanta har zuwa yau abinda

ya faru.

Ya yi shiru zuwa can ya ce, "Me

yasa ba ki taba gaya mun ba? Na

kalle shi.

"Na gaya maka fa ka ce? Idan na

gaya maka me za ka yi? Na taba gaya

maka wani abu da aka yi mun ka

dauki mataki?

Sannan ko karata aka kawo

wurinka ko ni ce da gaskiya ko ba ni

ba ce ba ka taba saurarona ka ji ta

bangarena ba.

Ni dai a kullum ni ce maras

gaskiya, 'ya'yanka kuma masu

gaskiya. A ina ne aka ce a yi haka don

daidaita zaman lafiya?

96



Ni kenan kullum ina da matsala da

'ya'yan miji, to menenhe aibuna? Me

nayi musu?"

"Za ki iya zama a Kano?"

Tambayar ta yi mun kwatsam! Na bar

kukan da nake yi a take na kalle shi.

"Ina da gida a Kano, idan kin yarda

za ki zauna a can sai na mayar da ke

can tunda ina shirye-shiryen bude

wata harkar a Kano kwanannan.

Ina son zama da ke Hauwa'u. Ni

kaina nasan ina da matsala a cikin

gidan nan. Kiyi hakuri a yanzu ko

meye Zainab zata yi miki ki daure ki

jure saboda ni da ke mu samu biyan

bukatarmu."

Hankalina ya dan kwanta, ya ce

"Ina neman alfarma idan ba zan

takura miki ba?"

97

Na ce, "Ta meye?" Ya ce, "Abinci

nake so ki samar mun wanda zan ci,

yunwa ta dame ni."

Tashi nayi a daren nayi wa Ahmad

dan girki mai sauri yaci sannan muka

kwanta.

Tun daga nan na samu sassaucin

damuwa, sai dai Hajiya ta daina amsa

gaisuwata, duk da haka kuma ban

daina zuwa gaisheta ba.

Zan zauna na kai mintina goma

bata saurare ni ba. Shi ma na lura

yana da 'yar matsala amma tunda dai

bai bude bakinshi ya fada mun ba sai

ban tambayar shi ba.

Na dai tsaya tsayin daka wajen

ganin bai kuntata da yawa ba, don

nasan matsalar ba ta wuce ta Hajiya

ba.

98

Ba a fi wata daya zuwa kwanaki

arba'in ba sai shirin Ahmad ya

kammala na bude babbar harkarshi ta

kasuwanci a Kano.

Har yaje ya yi sati daya a can don

ya tabbatar komai ya daidaita, sannan

ya dawo.

Muna kwance a dakinshi yana bani

labarin yadda abin yazo cikin

gagarumar nasara, ni kuma dokina sai

karuwa yake yi zai bar zama da su

Hajiya da 'yan fitinannun jikokinta,

zan koma Kano tare da mijina.

Ina ta ayyano irin tattalinshi da zaan

kara yi da irin abubuwan da zan yi na

ci gaba don kaina.

Don kuwa nima yanayin

kasuwancin Ahmad yana ba ni

sha'awa, har nima na kan yi tunanin a

99

matsayina na mace idan zan gwada

babu mamaki nayi nasara.

Na ce, Kaga idan muka koma ni ma

sai na gwada kasuwancin mata na

cikin gida.

Kallona ya yi cikin mamaki.

"Kasuwanci kuma Hauwa'u?

Na ce, "Eh mana, na zannuwa da

gwala-gwalai irin naku ba."

Shiru yayi yana kallona, ya ce

"Ashe kina sha'awar kasuwanci?"

Na ce, "Eh, zama da kai ne yasa

hakan, da can ba na yi."

Ya ce, To bari kayan da nayi oda

wannan watan su zo sai na diban miki

a ciki ki gwada muga irin taki nasarar.

Kin san mata da yawa suna karban

kaya a hannuna kuma suna samun

riba ba kadan ba.

100

Amma abin da na lura da shi shi ne,

sai wacce ta iya rikici saboda siyan

kayan gida yawanci bashi ne.

Ke kuma ban ga wannan a tare da

ke ba."

Ba mu yi bacci ba sai karfe daya

saboda 'yan hirarrakin da muke yi.

Washegari bai kintsa da wuri ba

saboda bakin da yayi abokan

kasuwancinsa.

Sai kusan sha daya na rana. Ya

shigo dakina rike da mukullin

motarshi yana ba ni sakon da zan bai

wa Bala direba idan yazo, saboda

haihuwar da matarshi tayi.

Sannan ya shiga wurin Hajiya.

Kwanciya nayi don na dan yi barci

kafin Azahar tayi. Sai dai ban ko yi

nisa ba naji sallamar Larai.

101

Daga cikin dakin na daga murya

ina tambayarta ko

4 / 6