Author : Hafsat C Sodangi Category : KDP NOVELS
SADAUKARWA
Sadaukarwar littafin ta Iyayena ce,
Alhaji Chindo Muhammad Sodangi da
Hajiya Fatima Musa Sodangi, Ubangiji
ya saka muku da alheri ya kuma kara
muku lafiya amin.
TUKUICI
Tukuicin littafin naki ne;
Khadija Chindo Sodangi (Mrs Nasiru
Idiris)
JINJINA
Jinjinar littafin taki ce Amarya ba kya
laifi (Maman Umar) Zuhuriyya Ibrahim
(Mrs Lawal Chindo Sodangi), Ubangiji
ya raya Umar da Imani.
FATAN ALHERI GARE KU
Fatima Abdulkadir Kazaure
Hafsat Iliyasu Unguwar Rimi
3
Khadija Usman Nasarawa
Nafisatu Ibrahim Muhammad
Fatima Ahmad Shehu Kaduna
Maryam Muhammad Gusau, Zamfara
Umaima Abubakar Umar
Maijidda Uba Magaji
Na gode, Ubangiji ya saka da alheri
amin.
KUNA RAINA
Hajiya Maryam (Mami) Dan Hassan
Hajiya Jamila Ibrahim Na-Bature
Hajiya A'isha Balarabe (Jazan)
Ubangiji ya bar zumunci amin.
4
Littattafan SODANGI:
Uwar Mijii
Naga Ta Kaina
Rabon Kwado..
Cikar Alkawari
Wayyo Duniya
Yi wa Wani..
Abu Naka...
Mata Ma su Duniya
Nufin Allah
Kifi Na Ganinka...
Daga Kin Gaskiya...
Da Kamar Wuya..
Mai Uwa...
Duk Daya..
Mata Da Kicin Dinsu
Wacece Ni?
Wata Fuskar...
Mijin Ta ce
Garin Banza..
Ga ni Gare ka
5
Biyan Bukatar Rai
Shamaki
Hattara
Mata Masu Duniya
Kyautata
Ayi Dai Mu Gani...
Tabbataccen Alamari
In Kunne Yaji..
Halin Rayuwa
Mai Daki.
Littattafan ba sa nufin yi da wani ko
habaici ga kowa sai dai an rubuta su ne
don fadakarwa da nishadantarwa, ana
neman afuwa ga duk wanda yaga wani abu
yayi kamar abinda ya shafe shi, ba da shi
ake ba dace ne kawai.
6
MAI DAKI.3
Bin ta da kallo suka yi cikin
mamakin irin yadda ta dangwarar
da kula, wannan kuma wacece?
Ina dan murmushin da ban san na meye ba
na ce, yarshi ce.
Fu Suka hada baki Yarshi? Na ce, Eh, ita
ce ta biyun tana da wa yana Makaranta
Dankaci ke ki ce akwai babbar magana
haka suke sakaka babu tarbiyya.
Ban sake cemusu komai ba mikewa
nayi na shiga kicin na debo plates da
cokala na dawo sai ga Larai ta shigo dauke
da wata kular da kato kular ruwa mai
famfo alamar abin sha ne a ciki.
Ta gaisa da su Baba Ladi sannan ta juya
ta tafi. Na bude kular miya da taji naman
kaji ta ukun kuwa kunun aya ne mai kauri.
Na zuba musu na mika musu sannan
nima na zuba naci sosai saboda yunwar da
ke damuna.
7
Sai da muka gama cin abincin ne Baba
Iya ta ce "To kai mu wurin uwar mijin taki
mu gaisa ko 'yannan."
Na mike suka bi ni. A bakin kofar
dakin muka yi sallama ban shiga ba sai da
ta ce a shiga.
Karba sosai tayi musu sannan suka fara
tattaunawa a kan al'amuran aure da
halayya na ya'yan zamani na rashin
kunya da fitsara har suka kawo kan danta
tana basu labarin rasuwar da mahaifinshi
yayi ya bar mata su tun bata fi shekaru
talatin ba a duniya.
Ya barta da Ahmad da Yayarshi Kausar
da a yanzu take aure a Kano wurin dangin
Babanta, da aure-auren da ya yi guda hudu
mata biyu suka haifan mishi 'ya'yanshi
Zaidu da Zainaba.
Sai kuma wata ta haifi Ziradat da
Zinatu, sai wasu biyu da ba su haihu ba.
8
A raina na ce, "Dankari! To me yasa
bai taba gaya mun cewa ni ce matarshi ta
biyar ba?"
Na kawar da wannan tunanin daga
cikin raina, ko bai gaya mun yawan matan
da ya aura ba ai ya gaya mun yana da
'ya'ya hudu.
Shi kenan magana ta kare.
Hira sosai suka y1 sannan suka taso
muka dawo sashena. Hajiya ce tasa aka
mayar da su Baba Ladi gida bayan nayi
musu kyaututtuka daga cikin kayan
aurena.
Kwalliya sosai na sake tsalawa da
yamma shadda danya da aka yi wa wani
irin dinki na Senegal ruwan kofi na saka,
na saka dan kunne fashion ruwan zaren
jikin shadar.
Na feshe jikina da turaruka sannan na
kunna bumer na saka na daki yabi gidan gaba
daya. Karfe shida daidai naji tsayuwar mota a
Wurina.
9
Na leka, Ahmad ne. Na dawo na zauna ina
jiran naga shigowarshi ban ji ba, har aka yi
magriba aka yi Isha'i sannan ya shigo dakin.
Yana kallona ya ce "Wow! Allah na gode
maka da kayi mun baiwa da samun Hauwa' u
a matsayin mata ka bani zaman lafiya da ita
ka albarkace mu da albarka da ka ke yi wa
Ma'aurata.
Murmushi na rinka yi har ya iso in da
nake ya jani zuwa jikinshi ya rungume
ni yana rada mun a kunnena ke baki iya
yiwa mijinki oyoyo ba ne?
Rike hannuna yayi ya jani zuwa wani
wuri da ban kula da shi ba a gidan. Kofa
ce ya budeta muka shiga.
Babban wuri ne, don falon yafi nawa.
Duk wani abu da ke falon faci ne tas tun
daga kujeru har zuwa labule.
Falon ya matukar kawatuwa ba
kadan ba, bai bar ni a nan ba cikin
dakinshi ya wuce da ni.
Wanka za ki taya ni nayi."
10
Na gwalo ido ina kallonshi, ya ce
"Ko ba za ki iya ba?
Nayi shiru, murmushi yayi ya soma
cire kayan jikinshi na kawar da kaina
zuwa kallon wani wawakeken hoton da
ke manne jikin bangon gadon shi na
wani irin ruwa da ke zubowa daga wani
tsauni zuwa wani dan koramai masu
tsuntsaye.
Kafin na juyo har ya shiga bayan
gidan dakin. Mintuna kadan ya sake
fitowa da tawul daure a kugunshi yana
goge jikinshi da wani.
Dauko mun kaya a cikin wardrop
din gabanki. Na bude ina dubawa.
An kakkasa kayan kashi-kashi, under
wears, kayan barci, jallabiya da tract
suit alama na babu kayan fita a wurin na
ce wacce zan dauko maka?
Ya zubo hannayenshi ta kwibina tare
da dora kanshi a kan kafadata har ina
11
shakan kamshin man wankan da yayi
amfani da shi da ke jikinshi.
Ya ce, "Kamshin turarenki mai dadi
Hauwa'u. Ban iya ce mishi komai ba
don ban saba irin wannan mu'amallar
ba.
"Idan ba ki san wacce za ki ba ni ba,
to bar shi haka mana kawai ba shi kenan
ba, dama ai ba fita zan sake yi ba."
Na jawo wata rigar barci da ke can
sama saboda ya sassauta rikon da yayi
mun, na ce "To ga wannan. Ya ce, "To
juyo ki saka mun.
"To ai saika sake ni tukuna
zan iya saka makan.". Na juyo ina saka
mishi rigar tun daga hannu har na daure
mishi belt dinta.
Yayi murmushi ya ce, "Hauwana
kenan." A falon shi muka zauna yana
kallonlabarai yana yi mun yan
12
hirarraki ya ce, "So nake na dan takura
miki kadan."
Na ce,"Wacce irin takura kuma?" Ya
ce, To ban sani ba ko ba za ki ji dadin
ta ba, so nake daga gobe na fara cin
abinciki. Idan ki ka yi mun haka zan ji
dadi."
Nayi murmushi "Nima hakan yafi
mun ai, kamar na gaya mishi haka sai
na fasa. Ya ce, "Ba ki ce komai ba."
Na ce,Yadda duk ka ke so haka zan
yi." Ya ce, "To na gode."
Washegari daga fitan shi sai ga
cefane rigigif babu abinda babu, kaji,
kifi, nama, tumatir, komai dai na
bukatar gida.
Wayata na dauka na kira shi na ce,
"Za a yi na rana ne da za a kawò
maka?'
13
Ya ce, "A'a Hauwa'u wannan Haj1ya
tana sawa a kawo na dare kawai za ki
yi."
Na ce, "To me za ka ci da daddaren?
Yayi shiru zuwa can ya ce, Na baki
zabin yau dai kam ko meye ki ka yi zan
ci."
Tsayuwa nayi ina kallon cefanen da
aka yi, na rasa yadda zan yi na fara
tamfar wacce bata taba girki ba.
Karaf na tuno da littafin Momin
Hindu, shi na dauko na bude ina
dubawa amma na kasa zaben abinda zan
yi.
Da kyar na iya zaben wani da na
gani ina dubawa meat 'tagine' sunan
ne ya yi mun dadi, har nake dubawa
ganshi ba mai wahala sosai ba.
14
Sannan akwai kayan hadin gaba
daya, yanayin yadda naga girkin a
hoto.
Na fara hada kayan amfanin nama,
mangyada, yaji, tattasai, attarugu,
albasa, tafarnuwa, gishiri, maggi,
karas, citta, bawon lemon tsami,
tumatirin gongoni da ruwa.
Nan da nan na hada abubuwan na
rangada miyata mai wani irin kyau da
sha'awa. Na daukó ledar cous-cous
na dafa saboda ganin da nayi da shi
zai dace.
Na kira Momin Hindu ina bata
labarin abincin da nayi. Tayi
murmushi ta ce, "To saura abin sha."
Na ce, To ai ban san me zan yi na
sha ba. A gajarce ta gaya mun.
Ina gamawa na shiga bayan gida
nayi wanka.
15
Yau ma kwalliya nayi ta materia
ya kuma yi mun kyau sosai. Na yane
jikina da babban gyale na dauki
babban food flask din da na zubawa
Hajiya abinci a ciki na dauka nayi
sallama a bakin dakin na shiga, bayan
an ba ni 1zinin shiga.
Na ajiye abincin a gefe na zauna.
Ta kalli food flask din ta ce "Ai ba sai
kin rinka sako abinci ba don ba ci
suke yi ba, sannan ga Larai nan idan
muna bukatar abu zata rinka girkawa,
mijinki kawai ban da mu."
Na kai kamar mintina goma na
tashi na dawo wajena, na kalli agogo
har yanzu karfe shida bata yi ba.
Na gyara kwanciyata a kan
doguwar kujera na kunna TV ina
kallon CCTV Documentry da ake yi
akan wani kabarin tsohon Sarkin
16
Kasar Sin da ya mutu shekaru dari
biyar da suka wuce.
Yau ma Ahmad bai shigo ba sai
bayan sallar Isha'i. A dakin shi na
ajiye mishi abincin saboda wankan da
yake yi.
Ya fito yana goge jikinshi da tawul,
ya samu na ciro mishi riga da wando
na hutawa masu sauki.
Ya dan yi murmushi yana kallona
tare da amsa gaisuwar da nake yi
mishi.
Yasa hannu ya dauki kayan da na
ajiye ishi akan gadon yana sakawa, ya
gama ya riko hannuna.
"Muje ki bani abinci." A kasa ya
zauna a kan kafet yana duba wani
sako da ya shigo wayarshi, ni kuma
ina zuba mishi abinci a plate.
17
Na gama na tsiyaya mishi coconut
juice din da nayi mishi na fara mika
mishi.
Ya karba ya dan yi murmushi ya
ce, "Bismillah zan fara cin abincin
amarya. Nayi murmushin jin abin da
ya ce. Ya kai juice din bakinshi ya
kwankwade ya ajiye kofin a kasa.
Ya kalle ni na dauka madara ce, na
ce a'a ba madara ba ce, ya ce To
menene'? Na ce Juice din kwakwa
ne."
Ya sa cokali ya fara cin abincin
gaba daya muka yi shiru sai da ya
cinye abincin tas sannan ya ce, "To
masallah Allahu, na gode Hauwa u.
Allah ya yi miki albarka, ya kuma
ba mu zaman lafiyamai dorewa.
Abinci yayi kyau."
18
Nasa hannu na kwashe kwanukan
na fitar na kai kicin, sannan na dawo
na zauna. Ya fara magana, "Tunda ki
ka zo ban samu wani lokaci na zaunar
da ke don nayi miki magana dangane
da al'amuran gidana ba.
Amma duk da hakan dai nasan kin
ga abinda ki ka gani na zahiri. Akwai
mahaifiyata wacce idan kin lura za ki
gane ba ni da wanda nake girmamawa
nake kuma so fiye da ita.
A rayuwata ita kadai ce na mallaka
ina nufin mallakar da ban taba wayar
gari na gane na rasata ba.
Ina yi mata soyayyar da bana yiwa
kowa shi a duniya Hauwa'u, don
kuwa nasan itama tana yi mun fiye daa
hakan.
Babana ya rasu ne ya bar ni ban fi
shckaru biyar ba a duniya, amma
19
kuruciyarta bai sa ta barni zuwa wani
mijin ba.
Sai ta zauna da ni da Yata don ta
tarbiyyantar da mu, ta ilimantar da mu
ta hakura ta sadaukar da jin dadin
rayuwarta.
Don haka duk wani abu da ki ka ga
nayi a yau ko na zama a yau din nan
to da bazarta ne. Ina rokonki daki
taimake ni ki zauna lafiya da ita.
Zan iya yin hakuri idan ki ka saba
mun, amma ina da gajen hakuri ta
fannin sabawa mahaifiyata.
Sai abu na biyu, nasan kin ga yara
to ina so ki san ko ni da nake ubansuu
Hajiya bata yardar mun ta bani
yancin shiga harkarsu ba.
ldan kin ga wani abu da suka yi
miki da bai yi miki dadi ba, to na
roke ki da kiyi hakuri, idan kuma kin
20
ga ba za ki iya ba to ki jira ni na dawo
ko menene a lokacin sai ki fada mun.
Ina yi miki wannan maganar ne
saboda ni nasan kan gidana, na kuma
san matsalar da ke cikin shi. Ina so ki
taimake ni na samu nutsuwar da nake
bukata a cikin gidana."
Na yarda da duk abubuwan da
mijina ya gaya mun da kanshi ya
kuma roke ni a kai ina kuma iyakacin
kokarina wajen ganin na biya mishi
bukatunshi.
Gara nake shirya mishi kullum mai
dadi, daga cikin littafin girkina a
kullum kuma bai gajiya wajen yaba
mun.
Haka nan baya gajiya da yabon
kwalliyata, don kuwa kullum a cikinta
nake safe da yamma, matukar yana
gidan.
21
lna son mijina ina kuma son zama
da shi. Zama nake yi na yanci da
walwala. A yanzu ne kuma na gane
me ake nufi da zaman aure.
Zama na hakika ba mai cike da
kunci ba. Zama na sanin hakki da
yancin dan Adam.
A yanzu ne nasan so nasan abinda
kalmar take nufi don abinda nake ji a
game da Ahmad.
Shima burinshi a kullum bai wuce
na ganin ya faranta mun ba. Da
matukar wuya ya dawo gida ba tare
da ya riko mun wani abu ba, wanda
zan yi amfani da shi don kaina ba don
shi ko wani ba.
Iyayena kuwa yana mutunta su
tamfar nashi. To abinda nake so
kenan na kuma samu, zan kuma
jurewa zama da ya' yanshi da
22
mahaifiyarshi kamar yadda ya ce, don
na tabbatar mishi matsayin shi a
wurina.
Watana biyu cif, Ahmad ya ce na
shirya a kai ni gida wuni. Cikin doki
ranar na kama shiri. Tsaraba sosai
yayi mun wanda zan tafi dashi tamfar
wacce take nesa.
Nayi sallama a kofar dakin Hajiya
na shiga a gefe na durkusa na gaya
mata zuwana gida.
Ta ce, Eh mijin naki yazo ya gaya
mun. Allah ya kiyaye hanya, ki gaida
manyan naki. Na fito na shiga mota.
Bala direba ya tuka muka tafi.
Babu wanda bai yi murna da ganina
ba.
Umma ta ce, "Haka fa Allah ke
lamarinsa, ki duba ki gani wannan
auren naki nutsuwarshi ma daban. "
23
Wajen karfe uku Ahmad ya kira ni
a waya. Na dauka "Yaushe ki ke
shirin zuwa gida ne?
Na ce, "Ina ce wai ko za ka bari ne
na yi sallar Magriba tukuna daidai
lokacin dawowarka kenan."
Ya ce, "To abincina fa? Ko zan
zauna da yunwa ne yau tunda nayi
karambanin yi miki gwaninta?
Nayi maza na ce, "A'a yallabai
mu tafi." Ban iya tsayawa jiran
Babana ba na kama shiri.
Tasi'u ne yake ta magana yana
cewa, Zai bini yaje yaga gidana,
Umma ta ce, Aa a wane dalili ka
bari dai a kai ku wani lokacin." Ba
tare da wata fargaba ba na ce a hada
musukayansu shi da Sabi'u.
Wurin Hajiya muka fara shiga, na
gaisheta. Su Tasi'u ma haka, na mike
24
zan fito ta ce mun, "Zo mana. Na
dawo na sake tsugunnawa ta ce, Su
waye wadannan?
Tana nuna su da baki, na ce
Kannena ne. ziradat ta leko daga cikin
dakinsu ta kalli su Tasi'u ta ce, Wai!
Sannan ta kwashe da dariya.
Ta ce, Lallai kuwa. Na tashi bayan
ta bani umarnin tafiya, na dawo
sashena amma ina jin wani abu a
raina maras dadi.
Muka shigo falona sannan na kara
bin yaran da kallo wadanda tuni suka
bi lafiyar kujera suka zauna. Ni nasan
mu ba masu kudi ba ne.
Amma daidai gwargwado Umma
tana iyakacin tawajen ganin ta
tsaftace danta babu kazanta a tare da
shi.
25
Tsarguwar da nayi ita ce tasa na
leka na kira Bala direba na ba shi
kudi na ce ya sayo mun kaya daidai
nasu Tasi'u set bibbiyu wadanda zan
yi musu amfani da shi.
Aikina na fara yi gadan-gadan
saboda kada na makara. Abinci mai
kyau sosai nayi mishi. Sai da na gama
sannan nayi wa su Tasi'u wanka na
saka musu sababbin kayansu nima
nayi wankan nayi alwala, sannan nayi
kwalliyata.
Ka'idar Ahmad shi ne, yana
dawowa zai shiga wurin
Mahaifiyarshi, idan aka yi sallar
Magriba ya dawo zai shiga suyi hira.
Daga sallar Isha'i ne zai shigo
wajena, don haka yau ma hakan ya yi.
Yana ganin su Tasi'u ya sai
murmushi.
26
"A'a'a, ke ki ce yau muna da
manyan baki a gidan nan, amma ba ki
sanar dani ba, ai da na shigo da kayan
tsaraba. To yanzu me ki ka ba su na
saukan baki?"
Na bude baki zan yi magana ya ce,
"A'a bar su kawai su bani amsa.
Suka fara lissafa mishi abubuwan da
suka ci tun da suka zo.
Sai da suka gama ya ce, "Ba ta ba
ku sweet ba, ba ta ba ku Ice Cream ba
kenan kun ga bata iya karbar baki
ba."
Ya jawo wayarshi daga aljihu ya
kira Bala direba ya ba shi kudi ya ce
yaje ya siyo mishi Ice Cream da
candy.
Sannan ya kalleni, "To baiwar
Allah ya ya ki ka samu gida? Nayi
murmushi har cikin zuciyata na ce
27
"Lafiya lau yallabai, kowa yana
gaisheka tare da godiya mai yawa, sai
dai ban ga Baba ba saboda gudun
kadana makara."
Ya mike ya nufi hanyar sashen shi
ina bin shi har muka shiga. Ya tsaya a
bedroom din shi yana tube kayanshi,
ni kuma na wuce bayangida ina hada
mishi ruwan wanka a kwarmi.
Ya ce, Ki koma wurinki kawai
saboda yaran nan na ce to. Ban dawo
ba sai da na ajiye mishi dukkan abin