MAI DAKI BOOK 3 Hausa Novels by Sodangi. .docx

Author :  Hafsat C Sodangi Category :  KDP NOVELS

Chapter   5 / 6

12K to 15K   out of 15.7K words

lafiya? Ta ce,

Lafiya kalau Hajiye ce take kiranki.

Gabana ne ya fadi, to menene

kuma? Ba dai naje na gaisheta ba.

Nayi sallama a kofar dakin na shiga.

Har yanzu Ahmad yana nan bai fita

ba, yana zaune can gefe a asa,

kanshi kamar zai dunguri kasa saboda

irin sunkuyon da ya yi.

Jikina a sanyaye na zauna a gefe

nesa da inda yake.

"Ina ce dai ita ce wannan?"

Hajiya ta fara magana.

"Yarinyar da ko darajar sauran

matanka bata kai ba. A kanta ne kuma

nake baka umurni ka ke kin bi.

Abinda ban taba zaton zaka iya yi

ba shi ne take umurnina. Na kyale ku

102

na zuba muku ido amma gaba

dayanku ba ku fahimci hakan ba.

Nan wurin nan kazo mun da

maganar za ka kaita Hajji a bana na

ce a'a banyarda ba, don ina ta binka

ka biya wa Lado dan kanina har

yanzu ba ka biya ba kana daga

tafiyar.

Sai ka dawo min da maganaar

zuwan ku Dubai wanda wannan ma

duk wani salo ne na kin bin umurnin

da na bayar din.

Ka dai nuna mun a yanzu kai ma ka

girma. Ba a wani dauki lokaci mai

tsawo ba yarinyar nan ta zo har dakin

nan ta zage ni.

Na gaya maka ban ji ka dauki

matakin komai a kai ba. A jiya kuma

abinda ka zo da shi shi ne za ka daukec

ta ku koma Kano da zama ko Amadu?

103

To bari ka ji wata magana, idan ba

mantawa nay1 ba, ko a ranar da na

haife ka, nayi nakudar ka ne ni kadai

a dakina na haife ka na yanke maka

cibi da kaina.

Sannan ne nayi maka wanka kafin

wasu ma daga gidan suka san na

haihu, kenan ka gani babu wanda ya

taya ni.

Don haka ba zan haifi da nayi

tarbiyyarshi da irin abubuwan dadi da

wahala da dawainiyar da nasha wata

tazo ta kwace mun shi rana tsaka ina

kallo ba, babu ita.

Zagina da tayi ba ka ce komai ba

saboda ka daina gudun bacin raina sai

nata, to na yafe maka amma ko don

na yi wa tufka hanci ya zama hakan

bai sake faruwa ba.

104

Ga takarda da biro nan na baka

rubuta takardar sakin aurenta

yanzunnan ka bata, auren nata ya ishe

ni haka."

"Inna lillahi wa inna ilaihir raji'un."

A bayyane na furta saboda firgitan da

nayi. Saki kuma? Wannan wacce irin

musiba ce?

Na kalli Ahmad wanda har yanzu

yake a yadda na same shi, sannan na

kalli Hajiya.

Kamar kullum tana zaune ne a kan

dardumarta ta sallah, sanye da

zurmemen hijabinta.

Zan iya cewa a tsawon zaman da

nayi a gidan na watanni ashirin ban

taba ganin ranar da na ganta babu

hijabinta ba.

Sai nayi sha'awar ace ita din mata

ce mai sassauci da rangwame a kan

105

al'amuranta, tunda kowa ya shaideta

mace ce mai yawan Ibada.

To me yasa ita din halinta ya zama

haka. Danta da yake matukar

kokarinsa wajen ganin yayi mata

biyayya ya kaucewa bacin ranta ya

batawa wanda ya bata mata.

Danta da a kullum yake fadin irin

alherinta da dawainiyar da tayi da shi

wajen ganin bai yi maraicin uba ba.

Danta da a kullum yake fadin cewa

ita ce abinda ya fi so da girmamawa a

duniya shi ta ke yi wa irin wannan

kuntatawar da kuma rashin sassauci?

Lallai halinta sai ita.

Take na fara kokarin rarrashin

zuciyata don ta samu sassaucin

tsananin da zata fuskanta a gaba.

106

Na rinka tunanin abubuwan da zan

yi wadanda za su taimaka mun a

rayuwata da zan shiga nan ba da

dadewa ba.

Tunda nasan babu makawa Ahmad

zai aikata abinda Hajiya ta umurce shi

tunda da bakinshi ya tabbatar mun

cewa ita din bata taba bashi wani

umurni da ya ketare ba, face ya

aiwatar da shi komai tsananin shi.

** ** **

Ina kwance a kan shimfidaddiyar

katifata da ta sha lallausan shimfidan

zanin gado na yadin (American bed

sheet) dan asali da bargonshi.

Na kai hannu na shafa yadin zanin

gadon tare da tuna ranar da na fara

shimfida shi a kan gadona, lokacin da

107

nake ganiyar cin amarcina a gidan

Ahmad.

Na runtse idanuwana da karfi

saboda wasu tunane-tunane da suke ta

kawowa zuciyata ziyara.

Tunanin abubuwan da suka zo suka

kuma wuce tamfar a mafarki tamfar

dai ace wani barci kawai nayi mai

dadi na kuma farka.

A da can, ban taba tunanin haka

al'amurana za su kasance ba. A

matsayin shekaruna a yanzu ashirin

da uku kacal a duniya.

Amma har an fara kirga mun

aurena. Yanmata da yawa sa'o'ina ba

su ma yi auren ba, ballantana har ace

ya kare.

Take kuma nayi hanzarin yin

Istigfari da na tuna akwai wasu mata

kuma da suke zuwa duniya su gama

108

rayuwarsu a cikinta su koma ga

mahaliccinsu ba tare da sun yi auren

ba.

Don haka ba zai yiwu nayi wa

Ubangijina butulci ba, a kullum zan

kasance mai yawan godiya a gare shi

bisa irin yawa-yawan n imomin da

ya yi mun a rayuwata.

Ban kuma dauka wannan

mummunan jarrabawa ba ce sai na

dauka cewa ni kuma tawa kaddarar

kenan ba kuma zai yiwu na tsallake

wata kaddara tawa ba face kawai na

roki Ubangijina da kowacce ta tashi

zuwa mun, to ta zamto mai sauki.

Ya kuma ba ni ikon dauka don

Imanina ya zamto cikakke tun da aan

gaya mana cewa Imaninmu ba zai

cika ba sai mun yarda da kaddararmu

ta alkairi ko wanin alkairi.

109

Bai kuma jarraba ni da ciwo ba ko

wanina ko kuma ya jarrabe ni da rashi

na wata gaba a jikina ba.

Sannan da aurena ya mutu a farko

sai ya bani wanda ya fi mun na

farkon, to ina rokon shi a yanzu ma

ya bani wanda ya fi mun na biyun.

Sai dai tunanina yana kawowa

daidai nan sai naji gabana ya yanke ya

fadi ras!

Kenan na rabu da Ahmad ba zan

sake komawa gidanshi ba? Ina son

mijina shima kuma yana sona.

Mahaifiyarshi ce matsalarmu, don

kuwa idan ba don shigarta cikin

lamarin ba to don ta ya'yanshi zan

iya zama da su a yadda suke, tunda

ina son ubansu.

Sabanin matsalata da Ishak wanda

a lokacin da aka yi aurena da shi

110

shekaruna goma sha bakwai ne a

duniya.

Ba komai yasa a ka yi auren ba

face rashi da mahaifina yake ciki ga

kuma kwadayinshi a kaina na ganin

ni din nayi karatu.

Ya dauke ni ya ba shi ni ba tare da

wani dogon nema ko bincike ba,

saboda jin irin alkawuran da yayi a

kaina.

Alkawuran da suka zamo shi ne

sanadin faruwar auren da kuma

rugujewarshi.

Idan kuma da ace zaman da yayi da

ni akwai adalci a ciki ko kuma

sassauci ko tausayawa wadanda

wadannan abubuwa sune suka hadu

suka zamo soyayya da kauna to duk

da da sauki.

111

Idan har akwai abinda nake tunawa

da Ishak da ke sake sani kin shi to bai

wuce dukan rashin tausayi da yake yi

mun ba.

To sai na auri Ahmad, mutumin da

ya an yanci na walwala. Nayi

rayuwar aure irin wacce ban taba

mafarkin ana yin irinta ba a gidan

aure.

Saboda irin sona da tattalina da

mijina yake yi. Ya nuna mun cewa ni

din ina da matukar muhimmanci a

wurinshi.

Ya kuma so ni so na hakika, ya

mutunta iyayena da yan uwana, ya

guje mun bacin raina, ya tattali farin

cikina.

Amma sai gashi 'ya'yanshi da

mahaifiyarshi sun ki yarda su bar ni

112

na zauna da shi duk da hakuri da

halinsu da nake yi.

Idan har ina da laifi ko kuma wani

ganganci da na aikata a lokacin da

aurena na fari ya mutu, to a wannan

karon kam nasan ba ni da wani laifi.

Sai dai na kasa hakura, fatana bai

wuce da ni da shi mu samu maslaha

kan al'amarin aurenmu ba.

Tunda dai an yi sa'a saki daya ne a

tsakaninmu.

An kwaso kayana tas daga gidan

Ahmad, ba wai don na hakura da

zama da shi ba.

Sai dai kawai don jiran shawarar da

shi da kanshi zai zartar a kan maganr.

Sakon da ya turo mun kenan a waya

daren da na dawo gida.

113

Cewa na saurare shi kan shawarar

da zai yanke na neman mana mafita

nan da kwanaki uku.

Sai kuma kudi da suka shigo

account dina masu auki.

Ta bangaren Babana dai abin ba a

cewa komai, don kuwa bakin cikinshi

ba ya' misaltuwa.

Umma kam har a wannan karon ba

ta ce komai ba, harkokinta take yi.

Nayi matukar kokarin ganin ban

takura kaina da tunane-tunane ba, ta

hanyar shiga duk wani hidima na gida

da ake yi.

Har girki na karba ni nake yi da

sassafe kan bakwai zuwa bakwai da

rabi na kammala abin karyawa.

Idan na gama kumana zauna taya

Umma saye da sayarwanta, muna

kulla na kullawa.

114

Babbar matsalata ba ta wuce na

rashin barciba. Sai nayi matukar sa'a

ne kwarai nake samu na dan runtsa.

Al'amurana ne kawai za su yi ta

dawo mun rayuwar da nayi da Ahmad

mu'amallarshi da kuma yadda yake

harkokinshi a cikin gidanshi.

Daga manya zuwa yara da kuma

masu yi mishi hidima bisa sassauci da

ganin mutuncin kowa.

Ranar shi da farin cikinshi dakuma

fushin shi da kuma wasu abubuwa

masu dama.

Me yasa mutane ba su da tausayi

ne, babu sassauci a cikin al'amura

amma kuma mu sai muce muna

neman sassauci a wurin Ubangijinmu.

Bayan mun san shi ne ya yi umurni

da mu yi wa na kasa damu sassauci da

adalci.

115

Duk da abin da Hajiya tasa danta

ya yi mun zama dashi bai fita a kaina

ba, har yanzu kuma jiran shi nake yi

naji abinda zai ce.

Satina uku cif a gida Ahmad yazo

sai da ya gaisa da Babana da Umma

sannan na same shi a zauren gidanmu,

bayan Babana ya aiko Tasi'u cewa

naje na same shi.

Cikin kyakkyawar shiga na dogon

hijabi da na dora akan kayan dake

jikina dinkin atamfa riga da zani na

same shi.

Nayi matukar kokarin daurewa ta

ganin bai fahimci wani abu game da

halin da na shiga ba.

Kaina na sunkuye na gaishe shi

bayan na zauna akan shimfidar

tabarmar da aka yi mishi.

116

Ya amsa cikin yanayin shi kadaran

kadahan. Ban kalle shi ba na ce, "Ya

su Hajiya?"

Ya dan yi jim bai amsa ba kafin ya

ce, "Suna nan kalau." Abinda a sani

kuma shi ne kallona yake yi duk da

kin yarda mu hada ido da nayi ta

hanyar kallon 'yan yatsun hannuna da

na yi wa lalle a safiyar yau.

"Nayi tafiya ne Hauwa'u, shi ne

abinda yasa ba ki ganni ba, tafiyar ta

dauke ni tsawon kwanaki goma sha

takwas, sai a daren jiya na dawo. Don

haka kiyi hakuri."

Shi dai mai yawan bada hakuri ne,

abinda zuciyata ta ke fada mun kenan.

To amma hakurin da ya bani a yanzu

menene ma'anarshi?

117

Nayi hakuri ne a kan sakin da ya ya

mun, ba zai iya sake zama da ni ba ko

kuwa nayi hakuri ne na koma dakina?

A yanzu ne nasan na daga kaina na

kalle shi muka hada ido alamar ya

dade yana kallona hakan bai sa na

daina kallon shi ba babu abinda ya

canza a tare da shi.

Komai nashi yadda yake illa

idanunshi da launin su ya dan surka.

"Kiyi hakuri Hauwa'u." Abinda ya

sake fada kenan a lokacin da na

sunkuyar da kaina na hadiye wani abu

mai tsanani da ya rike mun wuya.

"Ina so ki san kowa da irin

jarrabawarshi a rayuwa ni tawa

jarrabawar kenan.

A tafiyar da nayi nasa mutane

daban-daban sun je don su taushi

zuciyarta har sau úku.

118

A tunanina idan na dawo zan samu

wani dan sauyi daga gareta a game da

maganarmu wanda har da hakan ne

yasa na kara jan kwanakina na

dawowa.

Amma da na iso gida sai ban ga

hakan ba, don haka ne nayi

sammakon zuwa Kano a yau na gana

da kanin Mahaifina da a gobe nake sa

ran zai zo don ya samu Hajiyan."

Wani irin tunani ne ya yi gaggawan

shiga zuciyata da kwakwalwata, duk

da irin kwabata da zuciyata take yi sai

da bakina ya furta na ce.

"Idan a kaina ne ka ke tura mutane

wajen Hajiya to na roke ka ka daina

saboda kai da kanka ka gaya mun

cewa baka taba saba mata ba.

119

Kenan kana so ka tilastata ta

hakura ta barka ka zauna da ni ba bisa

son ranta ba.

Wanda hakan ba zai sa ta yi

sassauci a kan kiyayyar da take yi

mun ba."

"Ba a kanki nake turawa ba, a

kaina ne saboda halin da na shiga,

barin ki gidan da kuma dawowan da

nayi ba kya cikin shi.

Gaskiya ki ka fada, ban taba yin

makamancin hakan ba sai a yanzu

wanda nasan ko ta sassauto ta hakura

to akwai wani tsanani da za ki iya

fuskanta.

Amma ina so nayi miki alkawarin

ba zai yiwu na barki haka ba.

Har a yanzu ina da niyyar dauke ki

a gidan zuwa Kano. A karo na biyu na

120

dago kai na kalli Ahmad da har yanzu

yake kallona.

"Ba zan jagoranci batawarka da

Mahaifiyarka ba. Burina bai wuce

naga mun daidaita matsalolinmu sun

kare mun maida aurenmu ba.

Amma sai dai dama matsalar ba

tamu ba ce a inda matsalar take kuma

banga alamar wani sauki ba.

Ina rokonka kada ka tilasta

Mahaifiyarka zama da ni, don Allah.

Yadda a yanzu zuciyata ta hakura

ina rokonka kaima ka sakawa taka

Zuciyar sassauci.

Ina kaiwa nan na mike na shiga

gida, na fada kan katifata, kuka nake

yi irin wanda na dade ban yi ba.

Duk yadda na kai da son zama da

Ahmad abin ba zai yiwu ba.

121

Ya zama dole na taushi zuciyata na

danganaa na fawwalawa Ubangiji

lamarinshi, don ya isar mun ya bani

abin yi.

Kwana nayi cikin wani yanayi da

ba zan iya kwatantawa ba, don saukin

abin ma nayi alwala nayi ta nafilfili

ina rokon Ubangiji sauki, da

kyakkyawan zabi.

A cikin satin ne aka kai sadakin

Yaya Auwalu abin da muka dauka shi

ne za su saka ranar auren da nisa.

Sai kawai muka ji sun saka sati

hudu kacal.

Muna zaune da Umma a tsakar

gida muna kullin kukar da Baba Ladi

ta aikowa Umma na siyarwa.

Na ce, "Amma Umma gaskiya

auren nan da suka saka ya yi kusa da

yawa."

122

Ta ce, ""To ai na Allah ne, sannan

shi Babanku jiya ya same shi yayi

mishi bayanin komai.

Ya ce, Babu damuwa, don yana da

dan abin da ya dade yana tanadawa

don shirin auren.

Na ce "To ai shi kenan."

Umma ta ce, "To sannan kin san

shi hidima irin wannan ba ka shirya

mata nemi taimako kawai a wurin

Ubangiji idan tazo maka."

Na ce Haka ne, Allah yasa mu

gani lafiya." Ta ce, To amin.

Ke kuma Ubangiji ya baki mafita

kan wannan matsala da ta same ki na

mutuwar aure, ya ba ki miji nagari da

zai zauna da ke bisa adalci da

kyautatawa.

Ya kuma zaunar da ke a dakinki ba

tare da kin sake fitowa ba."

123

Ban iya amsawa Umma ba, don

kuwa babu abin da nake so naji irina

ce Allah ya sassauta zuciyar Hajiya ta

bar ni na koma dakina.

Gidan Alhaji Ahmad Rufa'i, don

kuwa har a yanzu dinnan burina

kenan ko zuciyata tayi kamar ta

hakura sai kuma ta kara harzukowva.

Idan na tuna da irin rayuwar da

nayi tare da shi, daurewa kawai nake

yi nake rokon zabin alkairi a wurin

Ubangiji a lokacin da nayi sallah.

Amma idan da da hali to da rokon

komawa kawai na rinka yi ko da

hakan yana nufin batawar Ahmad da

Mahaifiyarshi.

To amma abinda na sani shi ne,

idan nayi haka ban yi mishi adalci ba,

don kuwa da kanshi ya gaya mun

124

cewar ta sadaukar da farin cikin

rayuwarta domin shi.

Da kuma Yarshi da har a yau din

nan ban ma santa ba.

Sannan shi din ko ba don haka ba

mahaifiyarshi ce da Aljannarshi take

karkashinta.

Hakan da na sani shi ne yasa na

danne zuciyata na kara ba shi

shawarar cewa mu hakura har a jiya

da ya kira ni.

Don na tabbatar da ban zalunce shi

ba. Idan yaso ni kuma Allah sai yayi

mun kyakkyawan sakamako.

Shiri sosai muke yina shirin bukin

Yaya Auwalu. Ya hada lefenshi rigijif

gwanin sha'awa.

Samun Umma nayi na ce mata ina

so na kwashe kayan dakinta na zuba

mata nawa na gidan Ahmad.

125

Ta kalle ni ta ce, To a wane dalili?

Ki zuba mun kayanki ke kuma idan ki

ka tashi yin wani auren ko kuma ki ka

koma dakinki fa?

Tunda ai ba gama iddah ki ka yi

ba. Na dan yi murmushi na ce,

"Umma ai komawata gidan Ahmad

abu ne mai wuya.

Tunda ba matsala ce a tsakanina da

shi ba, matsalar Mahaifiyarshi ce ba

ta kuma da niyyar yin sassauci a kai."

Ta ce, "Eh dai duk da haka ki bar

Umma ba sai kiyi mun addu'a ba

su ba ni da bukata." Na ce, "To ba

kawai idan na tashi yin wani auren

Allah ya bani wadanda suka fi

wadannan ba."

Ta ce, "To amin, amma dai duk da

haka ba zan saka kayan dakinki a

126

nawa dakin ba, haba abin ma ai bai yi

tsari ba."

Da safe na shirya na gama aikina

da wurwuri na samu Babana na roke

shi ya bani izinin fita don ina da

uzuri.

Yayi shiru zuwa can ya ce, "To kin

dai san mutane ba a iya musu, ni

5 / 6