MAI DAKI BOOK 3 Hausa Novels by Sodangi. .docx

Author :  Hafsat C Sodangi Category :  KDP NOVELS

Chapter   1 / 6

1 to 3K   out of 15.7K words

SADAUKARWA

Sadaukarwar littafin ta Iyayena ce,

Alhaji Chindo Muhammad Sodangi da

Hajiya Fatima Musa Sodangi, Ubangiji

ya saka muku da alheri ya kuma kara

muku lafiya amin.

TUKUICI

Tukuicin littafin naki ne;

Khadija Chindo Sodangi (Mrs Nasiru

Idiris)

JINJINA

Jinjinar littafin taki ce Amarya ba kya

laifi (Maman Umar) Zuhuriyya Ibrahim

(Mrs Lawal Chindo Sodangi), Ubangiji

ya raya Umar da Imani.

FATAN ALHERI GARE KU

Fatima Abdulkadir Kazaure

Hafsat Iliyasu Unguwar Rimi

3

Khadija Usman Nasarawa

Nafisatu Ibrahim Muhammad

Fatima Ahmad Shehu Kaduna

Maryam Muhammad Gusau, Zamfara

Umaima Abubakar Umar

Maijidda Uba Magaji

Na gode, Ubangiji ya saka da alheri

amin.

KUNA RAINA

Hajiya Maryam (Mami) Dan Hassan

Hajiya Jamila Ibrahim Na-Bature

Hajiya A'isha Balarabe (Jazan)

Ubangiji ya bar zumunci amin.

4

Littattafan SODANGI:

Uwar Mijii

Naga Ta Kaina

Rabon Kwado..

Cikar Alkawari

Wayyo Duniya

Yi wa Wani..

Abu Naka...

Mata Ma su Duniya

Nufin Allah

Kifi Na Ganinka...

Daga Kin Gaskiya...

Da Kamar Wuya..

Mai Uwa...

Duk Daya..

Mata Da Kicin Dinsu

Wacece Ni?

Wata Fuskar...

Mijin Ta ce

Garin Banza..

Ga ni Gare ka

5

Biyan Bukatar Rai

Shamaki

Hattara

Mata Masu Duniya

Kyautata

Ayi Dai Mu Gani...

Tabbataccen Alamari

In Kunne Yaji..

Halin Rayuwa

Mai Daki.

Littattafan ba sa nufin yi da wani ko

habaici ga kowa sai dai an rubuta su ne

don fadakarwa da nishadantarwa, ana

neman afuwa ga duk wanda yaga wani abu

yayi kamar abinda ya shafe shi, ba da shi

ake ba dace ne kawai.

6

MAI DAKI.3

Bin ta da kallo suka yi cikin

mamakin irin yadda ta dangwarar

da kula, wannan kuma wacece?

Ina dan murmushin da ban san na meye ba

na ce, yarshi ce.

Fu Suka hada baki Yarshi? Na ce, Eh, ita

ce ta biyun tana da wa yana Makaranta

Dankaci ke ki ce akwai babbar magana

haka suke sakaka babu tarbiyya.

Ban sake cemusu komai ba mikewa

nayi na shiga kicin na debo plates da

cokala na dawo sai ga Larai ta shigo dauke

da wata kular da kato kular ruwa mai

famfo alamar abin sha ne a ciki.

Ta gaisa da su Baba Ladi sannan ta juya

ta tafi. Na bude kular miya da taji naman

kaji ta ukun kuwa kunun aya ne mai kauri.

Na zuba musu na mika musu sannan

nima na zuba naci sosai saboda yunwar da

ke damuna.

7

Sai da muka gama cin abincin ne Baba

Iya ta ce "To kai mu wurin uwar mijin taki

mu gaisa ko 'yannan."

Na mike suka bi ni. A bakin kofar

dakin muka yi sallama ban shiga ba sai da

ta ce a shiga.

Karba sosai tayi musu sannan suka fara

tattaunawa a kan al'amuran aure da

halayya na ya'yan zamani na rashin

kunya da fitsara har suka kawo kan danta

tana basu labarin rasuwar da mahaifinshi

yayi ya bar mata su tun bata fi shekaru

talatin ba a duniya.

Ya barta da Ahmad da Yayarshi Kausar

da a yanzu take aure a Kano wurin dangin

Babanta, da aure-auren da ya yi guda hudu

mata biyu suka haifan mishi 'ya'yanshi

Zaidu da Zainaba.

Sai kuma wata ta haifi Ziradat da

Zinatu, sai wasu biyu da ba su haihu ba.

8

A raina na ce, "Dankari! To me yasa

bai taba gaya mun cewa ni ce matarshi ta

biyar ba?"

Na kawar da wannan tunanin daga

cikin raina, ko bai gaya mun yawan matan

da ya aura ba ai ya gaya mun yana da

'ya'ya hudu.

Shi kenan magana ta kare.

Hira sosai suka y1 sannan suka taso

muka dawo sashena. Hajiya ce tasa aka

mayar da su Baba Ladi gida bayan nayi

musu kyaututtuka daga cikin kayan

aurena.

Kwalliya sosai na sake tsalawa da

yamma shadda danya da aka yi wa wani

irin dinki na Senegal ruwan kofi na saka,

na saka dan kunne fashion ruwan zaren

jikin shadar.

Na feshe jikina da turaruka sannan na

kunna bumer na saka na daki yabi gidan gaba

daya. Karfe shida daidai naji tsayuwar mota a

Wurina.

9

Na leka, Ahmad ne. Na dawo na zauna ina

jiran naga shigowarshi ban ji ba, har aka yi

magriba aka yi Isha'i sannan ya shigo dakin.

Yana kallona ya ce "Wow! Allah na gode

maka da kayi mun baiwa da samun Hauwa' u

a matsayin mata ka bani zaman lafiya da ita

ka albarkace mu da albarka da ka ke yi wa

Ma'aurata.

Murmushi na rinka yi har ya iso in da

nake ya jani zuwa jikinshi ya rungume

ni yana rada mun a kunnena ke baki iya

yiwa mijinki oyoyo ba ne?

Rike hannuna yayi ya jani zuwa wani

wuri da ban kula da shi ba a gidan. Kofa

ce ya budeta muka shiga.

Babban wuri ne, don falon yafi nawa.

Duk wani abu da ke falon faci ne tas tun

daga kujeru har zuwa labule.

Falon ya matukar kawatuwa ba

kadan ba, bai bar ni a nan ba cikin

dakinshi ya wuce da ni.

Wanka za ki taya ni nayi."

10

Na gwalo ido ina kallonshi, ya ce

"Ko ba za ki iya ba?

Nayi shiru, murmushi yayi ya soma

cire kayan jikinshi na kawar da kaina

zuwa kallon wani wawakeken hoton da

ke manne jikin bangon gadon shi na

wani irin ruwa da ke zubowa daga wani

tsauni zuwa wani dan koramai masu

tsuntsaye.

Kafin na juyo har ya shiga bayan

gidan dakin. Mintuna kadan ya sake

fitowa da tawul daure a kugunshi yana

goge jikinshi da wani.

Dauko mun kaya a cikin wardrop

din gabanki. Na bude ina dubawa.

An kakkasa kayan kashi-kashi, under

wears, kayan barci, jallabiya da tract

suit alama na babu kayan fita a wurin na

ce wacce zan dauko maka?

Ya zubo hannayenshi ta kwibina tare

da dora kanshi a kan kafadata har ina

11

shakan kamshin man wankan da yayi

amfani da shi da ke jikinshi.

Ya ce, "Kamshin turarenki mai dadi

Hauwa'u. Ban iya ce mishi komai ba

don ban saba irin wannan mu'amallar

ba.

"Idan ba ki san wacce za ki ba ni ba,

to bar shi haka mana kawai ba shi kenan

ba, dama ai ba fita zan sake yi ba."

Na jawo wata rigar barci da ke can

sama saboda ya sassauta rikon da yayi

mun, na ce "To ga wannan. Ya ce, "To

juyo ki saka mun.

"To ai saika sake ni tukuna

zan iya saka makan.". Na juyo ina saka

mishi rigar tun daga hannu har na daure

mishi belt dinta.

Yayi murmushi ya ce, "Hauwana

kenan." A falon shi muka zauna yana

kallonlabarai yana yi mun yan

12

hirarraki ya ce, "So nake na dan takura

miki kadan."

Na ce,"Wacce irin takura kuma?" Ya

ce, To ban sani ba ko ba za ki ji dadin

ta ba, so nake daga gobe na fara cin

abinciki. Idan ki ka yi mun haka zan ji

dadi."

Nayi murmushi "Nima hakan yafi

mun ai, kamar na gaya mishi haka sai

na fasa. Ya ce, "Ba ki ce komai ba."

Na ce,Yadda duk ka ke so haka zan

yi." Ya ce, "To na gode."

Washegari daga fitan shi sai ga

cefane rigigif babu abinda babu, kaji,

kifi, nama, tumatir, komai dai na

bukatar gida.

Wayata na dauka na kira shi na ce,

"Za a yi na rana ne da za a kawò

maka?'

13

Ya ce, "A'a Hauwa'u wannan Haj1ya

tana sawa a kawo na dare kawai za ki

yi."

Na ce, "To me za ka ci da daddaren?

Yayi shiru zuwa can ya ce, Na baki

zabin yau dai kam ko meye ki ka yi zan

ci."

Tsayuwa nayi ina kallon cefanen da

aka yi, na rasa yadda zan yi na fara

tamfar wacce bata taba girki ba.

Karaf na tuno da littafin Momin

Hindu, shi na dauko na bude ina

dubawa amma na kasa zaben abinda zan

yi.

Da kyar na iya zaben wani da na

gani ina dubawa meat 'tagine' sunan

ne ya yi mun dadi, har nake dubawa

ganshi ba mai wahala sosai ba.

14

Sannan akwai kayan hadin gaba

daya, yanayin yadda naga girkin a

hoto.

Na fara hada kayan amfanin nama,

mangyada, yaji, tattasai, attarugu,

albasa, tafarnuwa, gishiri, maggi,

karas, citta, bawon lemon tsami,

tumatirin gongoni da ruwa.

Nan da nan na hada abubuwan na

rangada miyata mai wani irin kyau da

sha'awa. Na daukó ledar cous-cous

na dafa saboda ganin da nayi da shi

zai dace.

Na kira Momin Hindu ina bata

labarin abincin da nayi. Tayi

murmushi ta ce, "To saura abin sha."

Na ce, To ai ban san me zan yi na

sha ba. A gajarce ta gaya mun.

Ina gamawa na shiga bayan gida

nayi wanka.

15

Yau ma kwalliya nayi ta materia

ya kuma yi mun kyau sosai. Na yane

jikina da babban gyale na dauki

babban food flask din da na zubawa

Hajiya abinci a ciki na dauka nayi

sallama a bakin dakin na shiga, bayan

an ba ni 1zinin shiga.

Na ajiye abincin a gefe na zauna.

Ta kalli food flask din ta ce "Ai ba sai

kin rinka sako abinci ba don ba ci

suke yi ba, sannan ga Larai nan idan

muna bukatar abu zata rinka girkawa,

mijinki kawai ban da mu."

Na kai kamar mintina goma na

tashi na dawo wajena, na kalli agogo

har yanzu karfe shida bata yi ba.

Na gyara kwanciyata a kan

doguwar kujera na kunna TV ina

kallon CCTV Documentry da ake yi

akan wani kabarin tsohon Sarkin

16

Kasar Sin da ya mutu shekaru dari

biyar da suka wuce.

Yau ma Ahmad bai shigo ba sai

bayan sallar Isha'i. A dakin shi na

ajiye mishi abincin saboda wankan da

yake yi.

Ya fito yana goge jikinshi da tawul,

ya samu na ciro mishi riga da wando

na hutawa masu sauki.

Ya dan yi murmushi yana kallona

tare da amsa gaisuwar da nake yi

mishi.

Yasa hannu ya dauki kayan da na

ajiye ishi akan gadon yana sakawa, ya

gama ya riko hannuna.

"Muje ki bani abinci." A kasa ya

zauna a kan kafet yana duba wani

sako da ya shigo wayarshi, ni kuma

ina zuba mishi abinci a plate.

17

Na gama na tsiyaya mishi coconut

juice din da nayi mishi na fara mika

mishi.

Ya karba ya dan yi murmushi ya

ce, "Bismillah zan fara cin abincin

amarya. Nayi murmushin jin abin da

ya ce. Ya kai juice din bakinshi ya

kwankwade ya ajiye kofin a kasa.

Ya kalle ni na dauka madara ce, na

ce a'a ba madara ba ce, ya ce To

menene'? Na ce Juice din kwakwa

ne."

Ya sa cokali ya fara cin abincin

gaba daya muka yi shiru sai da ya

cinye abincin tas sannan ya ce, "To

masallah Allahu, na gode Hauwa u.

Allah ya yi miki albarka, ya kuma

ba mu zaman lafiyamai dorewa.

Abinci yayi kyau."

18

Nasa hannu na kwashe kwanukan

na fitar na kai kicin, sannan na dawo

na zauna. Ya fara magana, "Tunda ki

ka zo ban samu wani lokaci na zaunar

da ke don nayi miki magana dangane

da al'amuran gidana ba.

Amma duk da hakan dai nasan kin

ga abinda ki ka gani na zahiri. Akwai

mahaifiyata wacce idan kin lura za ki

gane ba ni da wanda nake girmamawa

nake kuma so fiye da ita.

A rayuwata ita kadai ce na mallaka

ina nufin mallakar da ban taba wayar

gari na gane na rasata ba.

Ina yi mata soyayyar da bana yiwa

kowa shi a duniya Hauwa'u, don

kuwa nasan itama tana yi mun fiye daa

hakan.

Babana ya rasu ne ya bar ni ban fi

shckaru biyar ba a duniya, amma

19

kuruciyarta bai sa ta barni zuwa wani

mijin ba.

Sai ta zauna da ni da Yata don ta

tarbiyyantar da mu, ta ilimantar da mu

ta hakura ta sadaukar da jin dadin

rayuwarta.

Don haka duk wani abu da ki ka ga

nayi a yau ko na zama a yau din nan

to da bazarta ne. Ina rokonki daki

taimake ni ki zauna lafiya da ita.

Zan iya yin hakuri idan ki ka saba

mun, amma ina da gajen hakuri ta

fannin sabawa mahaifiyata.

Sai abu na biyu, nasan kin ga yara

to ina so ki san ko ni da nake ubansuu

Hajiya bata yardar mun ta bani

yancin shiga harkarsu ba.

ldan kin ga wani abu da suka yi

miki da bai yi miki dadi ba, to na

roke ki da kiyi hakuri, idan kuma kin

20

ga ba za ki iya ba to ki jira ni na dawo

ko menene a lokacin sai ki fada mun.

Ina yi miki wannan maganar ne

saboda ni nasan kan gidana, na kuma

san matsalar da ke cikin shi. Ina so ki

taimake ni na samu nutsuwar da nake

bukata a cikin gidana."

Na yarda da duk abubuwan da

mijina ya gaya mun da kanshi ya

kuma roke ni a kai ina kuma iyakacin

kokarina wajen ganin na biya mishi

bukatunshi.

Gara nake shirya mishi kullum mai

dadi, daga cikin littafin girkina a

kullum kuma bai gajiya wajen yaba

mun.

Haka nan baya gajiya da yabon

kwalliyata, don kuwa kullum a cikinta

nake safe da yamma, matukar yana

gidan.

21

lna son mijina ina kuma son zama

da shi. Zama nake yi na yanci da

walwala. A yanzu ne kuma na gane

me ake nufi da zaman aure.

Zama na hakika ba mai cike da

kunci ba. Zama na sanin hakki da

yancin dan Adam.

A yanzu ne nasan so nasan abinda

kalmar take nufi don abinda nake ji a

game da Ahmad.

Shima burinshi a kullum bai wuce

na ganin ya faranta mun ba. Da

matukar wuya ya dawo gida ba tare

da ya riko mun wani abu ba, wanda

zan yi amfani da shi don kaina ba don

shi ko wani ba.

Iyayena kuwa yana mutunta su

tamfar nashi. To abinda nake so

kenan na kuma samu, zan kuma

jurewa zama da ya' yanshi da

22

mahaifiyarshi kamar yadda ya ce, don

na tabbatar mishi matsayin shi a

wurina.

Watana biyu cif, Ahmad ya ce na

shirya a kai ni gida wuni. Cikin doki

ranar na kama shiri. Tsaraba sosai

yayi mun wanda zan tafi dashi tamfar

wacce take nesa.

Nayi sallama a kofar dakin Hajiya

na shiga a gefe na durkusa na gaya

mata zuwana gida.

Ta ce, Eh mijin naki yazo ya gaya

mun. Allah ya kiyaye hanya, ki gaida

manyan naki. Na fito na shiga mota.

Bala direba ya tuka muka tafi.

Babu wanda bai yi murna da ganina

ba.

Umma ta ce, "Haka fa Allah ke

lamarinsa, ki duba ki gani wannan

auren naki nutsuwarshi ma daban. "

23

Wajen karfe uku Ahmad ya kira ni

a waya. Na dauka "Yaushe ki ke

shirin zuwa gida ne?

Na ce, "Ina ce wai ko za ka bari ne

na yi sallar Magriba tukuna daidai

lokacin dawowarka kenan."

Ya ce, "To abincina fa? Ko zan

zauna da yunwa ne yau tunda nayi

karambanin yi miki gwaninta?

Nayi maza na ce, "A'a yallabai

mu tafi." Ban iya tsayawa jiran

Babana ba na kama shiri.

Tasi'u ne yake ta magana yana

cewa, Zai bini yaje yaga gidana,

Umma ta ce, Aa a wane dalili ka

bari dai a kai ku wani lokacin." Ba

tare da wata fargaba ba na ce a hada

musukayansu shi da Sabi'u.

Wurin Hajiya muka fara shiga, na

gaisheta. Su Tasi'u ma haka, na mike

24

zan fito ta ce mun, "Zo mana. Na

dawo na sake tsugunnawa ta ce, Su

waye wadannan?

Tana nuna su da baki, na ce

Kannena ne. ziradat ta leko daga cikin

dakinsu ta kalli su Tasi'u ta ce, Wai!

Sannan ta kwashe da dariya.

Ta ce, Lallai kuwa. Na tashi bayan

ta bani umarnin tafiya, na dawo

sashena amma ina jin wani abu a

raina maras dadi.

Muka shigo falona sannan na kara

bin yaran da kallo wadanda tuni suka

bi lafiyar kujera suka zauna. Ni nasan

mu ba masu kudi ba ne.

Amma daidai gwargwado Umma

tana iyakacin tawajen ganin ta

tsaftace danta babu kazanta a tare da

shi.

25

Tsarguwar da nayi ita ce tasa na

leka na kira Bala direba na ba shi

kudi na ce ya sayo mun kaya daidai

nasu Tasi'u set bibbiyu wadanda zan

yi musu amfani da shi.

Aikina na fara yi gadan-gadan

saboda kada na makara. Abinci mai

kyau sosai nayi mishi. Sai da na gama

sannan nayi wa su Tasi'u wanka na

saka musu sababbin kayansu nima

nayi wankan nayi alwala, sannan nayi

kwalliyata.

Ka'idar Ahmad shi ne, yana

dawowa zai shiga wurin

Mahaifiyarshi, idan aka yi sallar

Magriba ya dawo zai shiga suyi hira.

Daga sallar Isha'i ne zai shigo

wajena, don haka yau ma hakan ya yi.

Yana ganin su Tasi'u ya sai

murmushi.

26

"A'a'a, ke ki ce yau muna da

manyan baki a gidan nan, amma ba ki

sanar dani ba, ai da na shigo da kayan

tsaraba. To yanzu me ki ka ba su na

saukan baki?"

Na bude baki zan yi magana ya ce,

"A'a bar su kawai su bani amsa.

Suka fara lissafa mishi abubuwan da

suka ci tun da suka zo.

Sai da suka gama ya ce, "Ba ta ba

ku sweet ba, ba ta ba ku Ice Cream ba

kenan kun ga bata iya karbar baki

ba."

Ya jawo wayarshi daga aljihu ya

kira Bala direba ya ba shi kudi ya ce

yaje ya siyo mishi Ice Cream da

candy.

Sannan ya kalleni, "To baiwar

Allah ya ya ki ka samu gida? Nayi

murmushi har cikin zuciyata na ce

27

"Lafiya lau yallabai, kowa yana

gaisheka tare da godiya mai yawa, sai

dai ban ga Baba ba saboda gudun

kadana makara."

Ya mike ya nufi hanyar sashen shi

ina bin shi har muka shiga. Ya tsaya a

bedroom din shi yana tube kayanshi,

ni kuma na wuce bayangida ina hada

mishi ruwan wanka a kwarmi.

Ya ce, Ki koma wurinki kawai

saboda yaran nan na ce to. Ban dawo

ba sai da na ajiye mishi dukkan abin

1 / 6