MAI DAKI (2) Hausa Novels By Hafsat Sodangi.docx

Author :  Hafsat C Sodangi Category :  KDP NOVELS

Chapter   4 / 5

9K to 12K   out of 13.9K words

tare da na yi wani kuzari ba.

Shi kenan ta faru ta kare wai an yi wa

mai dami daya sata. Aurena ya mutu a kan

karatuna gashikuma karatun yana nema ya gagara.

In ba wani ikon Allah ba. Dare ya yi

nisa bacci ya ce bai san idona ba sai juyi

nake yi a kan 'yar katifar tawa.

Zamana da Ishak ya rinka dawo mun a

raina rashin yanci na walawa da

mu'amalla da fargaba a kowanne lokaci.

Kamar ba aure ba. In ban da ma zuciya

banga abinda zai sa har sakin da yayi mun

ya daga mun hankali ba.

Matsalar daya ce, Babana da yaja ya

tsaya akan ba zan koma Makaranta ba.

65

Ba dai a gianshi ba. Idan na auri wani

mijin yaga zai bar ni na koma Makaranta

to wannan a tsakanın mu.

Haka kawai naji zuciyata tana bani

shawarar zuwa birnin kudu nayi Azumin

Ramadan a can.

Don haka tun kafin Babana ya fita na

sanar da shi, na kuma yi sa'a bai hana ni

ba.

Ya ce,"Yaushe ki ke son tafiya? Na

ce, "Ko zuwa nan da kwanaki uku." Ya ce,

To." Ya shiga daki ya fito ya ce, To ungo

rike kiyi kudin mota sai kiyi manejin su.

Na ce, Lah, Baba ai fna da kudi, ya ce

eh karbi dai ki kara. Nayi godiya. Umma

ta shiga kokarin hada mun kayan tsaraba

irin su omo, sabulun wanka, sabulun

wanki, sugar, maggi da dai sauransu tunda

Su karkara ne.

Shiryawa nayi don zuwa kasuwa saboda

SIyayyar da zan yi na tafiya.

66

Kwalliya sosai nayi ban kuma san

dalilina na yin hakan ba. Doguwar riga na

saka mai fadi sai dai girmanta yabi jikina

saboda santsi da laushinta.

Hannunta shima mai matukar fadi ne

amma ya tsinke a daidai wuyar hannun.

Rigar ribi biyu ce samanta bulu ce mai

shara-shara da ake iya ganin na kasanta

wanda yake ja.

Sai adon da aka yi ana saman shima da

jan zare da kuma hannun rigar.

Na dauka jan gyale na yane kaina dashi

na saka jan takalmi da kuma karamar jaka

itama jar kala.

Na kalli kaina a madubi na tuna ranar

da Ishak ya kawo mun rigar da kuma uban

tashin hankalin da na gani a ranar.

A dalilin bakin da ya dawo ya same ni

da su wadanda suka zo daga Birnin Kudu,

kannen Babana.

Nayi saurn kawar da tunanin lshak daga

cikin raina, don gudun samun matsala, na

67

kamo hanyar fita a dakin, a zuciyata ina

addu'ar samun miji mai hali sabanin na

shi, wanda zan yi mu'amalla ta kwanciyar

hankali da shi cikin farin ciki da jin dadi.

Shi yasa kuma a yanzu ko kadan na

daina jin haushin irin sakin da Ishak ya

yimun, fatana kuma shi ne ya zamo mun

alheri.

Na fito tsakar gida Umma tana bina da

kallo. Zuwa can ta ceYanzu nan wannan

kwalliyar duk ta zuwa kasuwan ce?

Nayi murmushina ce Ta yi yawa ne

Umma?

Ta ce, "A'a je ki Allah ya tsare." Na ce,

Amin. Ina Tasi'u ya raka ni? ta ce, "Na

aike su gidan Mama Tambaya su bi min

bashina, amma sun kusa daowa ma."

Na ce, "To bari na gani ko zan gansu a

waje.

Tun ranar da na dawo gidanmu da

takardar sakin aurena ban kara leka koda

68

kofar gida ba ne ballantana nasa kafata na

fita.

Hakan ne yasa ni tsayuwa a kofar gidan

ina bin layin da kallo, ina kuma wasu yan

tunane-tunane a raina.

Na irin yadda unguwar ta canza gaba

daya tun daga lokacin aurena shekaru

hudu da suka wuce zuwa yau dinnan.

Karab! Sai kawai muka yi ido hudu da

Abdussamad wanda daga ganin irin kallon

da yake yi mun na gane ya dade yana

kallona bá tare da na ganshi ba.

Sauri nayi na sunkuyar da kaina ga

barin kallonshi, sai dai hakan bai hana ni

ganin canjin da ya samu ba.

Ya kara tsawo yayi haske sosai sannan

yayi 'yar kiba daidai ba mai yawa ba.

Wacce ta sanya shi ya yi kwarjini, ba

kadan ba. In da da hali to da na fasa. fitan

da nayi niyya.

69

Sai dai zai yi mun wata fassara haka

nan dole na gayawa Umma abinda ya hana

ni fita tunda har mun yi sallama.

Wuce shi nayi, nayi tafiyata bayan nayi

iyakacin kokari na ganin tsananin kallon

da yake yi mun bai harde ni na fadi ba.

Tafiya nake yi ina tunani a raina nasan

Abdussamad ya ji maganar mutuwar

aurena.

Don kuwa a unguwarmu kaf babu

wanda bai ji ba. Wani babban shagon saida

kaya na shiga saboda daukan hankalina da

shagon yayı.

Rabon da wani abu ya kawo ni kasuwa

tun kafin aurena da Ishak, don kuwa shi

baya ba ni kudin komai kawowa yake yi.

Wani dan saurayi ne ya karaso inda

nake tsaye saboda girman shagon yasa na

kasa fahimtar inda zan dosa.

Barka da zuwa Hajiya, me ki ke so?

Lokacin ne na fara kallon yadda aka

kakkasa shagon gefen takalma da

70

jakunkuna daban, haka na leshi haka na

atamfa, haka na material da kuma shadda.

Na dawo da kallona ga yaron saboda

kada na bata mishi lokaci, duk da akwai

masu sayar da kaya a shagon irin shi masu

yawa na ce atamfa.

Ya ce, "Babba ko karama?" na ce,

"Kanana za ka bani guda hudu." Ya ce,

To ga wuri zauna bari naje na kawo

miki."

Na zauna a kan kujerar da ya bani ina

kallon mu'amallar kasuwanci yadda take

tafiya a shagon da irin mutanen da suke

shiga suke fita.

Yaron ya dawo rike da atamfofi guda

hudu na duba na ce, "Sun yi." Na mika

mishi wata na ce ya karo mun irinta guda

daya.

A raina kuma ina tunanin wadanda zan

baiwa. Kakata Baba Ladi da kishiyoyinta

guda biyu, sai matan Yayun Babana biyu.

71

Sai kuma kanwar Babana. Ya dawo na

tambaye shi kudin ya fada, nasa hannu a

cikin jakata na mika mishi yayi godiya

yana saka mun a babbar jakar su ta shagon

mai dauke da suna da adireshin shagon.

Yana kuma tambayata ko za ki duba

gefen mu na takalma ne? kamar naki sai

kuma na bishi ina dubawa.

Wani takalmi yayi matukar daukan hankalina, na dauke shi ina dubawa na

tambaye shi kudin ya fada mun.

Na mayar na ajiye yana gaya mun ai da

kin dauüka Hajiya "zai matukar yi miki

kyau, saukinshi na fada miki, in kin duba

da kyau. za ki gane asalin takalmi ne dan

Italy.

Na ce, Eh na sani wani lokaci nazo na

saya amma ba yau ba."

Na fito daga shagon don ci gaba da

Siyan abubuwan da nake bukata na káina.

"Hajiya! Hajiya!! "

72

Nayi maza na waiwaya saboda wani

mutum da yayi mun alama da cewa ana

kirana.

Yaron da nayi sayayya a shagonsu ne

"Lafiya? na tambaye shi. "Ki zo in ji

Maigidana."

Na. ce, Maigidanka kuma?" ya ce, Eh.

gabana ne ya y1 mummunan faduwa.

Na ce, Ina ce na baka kudinka? Na

tambaye shi saboda tunanin da yazo mun

raina.

Ya ce, Eh ban san dai dalilin kiran naki

ba, ki dai taimaka din kizo tunda kin gani

nima dan aike ne."

Juyowa nayi na biyo bayan yaron nan

zuwa shagon su.

Mutumin yana zaune a can wani

kebantaccen wuri da aka tanada a shagon,

amma daga wurin kana iya ganin duk wani

abinda ake yi a cikin shagon.

Kammalallen mutum mai kwarjini mai

matsakaicin hasken fata da tsawo. Kamalar

73

shi ce tasa na dan rusuna a lokacin da zan

gaishe shi.

"Lafiya yanmata, kiyi hakuri fa naga

kamar kin dan damu ina fata ban takura ki

ba ko?"

A lokacin ne naji na dan sake saboda

tunane-tunanen da nake tayi a zuciyata, na

game da kiran Wata alfarma nake nema

kiyi mun."

Na ce, Kamar ta me fa? ya ce Lambar

wayarki za ki taimaka ki bani.

Nayi shiru saboda yadda abin ya yi mun

wani iri. Don Allah. Lafuzzan shi da ya yi

amfani da su suka hana ni bijirewa bukatar

tashi.

Don kuwa ban san mu'amalla ta roko a

tsakanin mace da namiji ba.

Yayi godiya na juyo na wuce, yaron

nan yana ta harkokinshi ya ce sai anjima

Hajiya, na ce Yauwa.

Ban wani dade a kasuwar ba na gama

siyayyata na kamo hanyar dawowa gida.

74

Sabanin dazu da Abdussamad yake

tsaye a kofar gidansu a yanzu tsaye yake a

kofar namu gidan, hannayenshi duka

biyun zube cikin aljihunshi.

Babu yadda zan yi na shiga gidan ba

tare da ya katdce hanya ba. Ban san me zan

ce mishi ba, hakanne yasa naja na tsaya

don ya fahimci ina da bukatar shi din ya

kauce mun a hanya.

Ban ga alamar yana da niyyar yin hakan

ba, na daga ido na kalle shi shima ni yake

kallo kuri kamar bai taba ganina ba.

Ban ce mishi komai ba amma sai nayi

nufin rabawa ta gefe na wuce. Ya sake

tarewa.

Hakan yasa na fahimei neman magana

yake yi, don haka na juya kallona ga wasu

yara can gaba da mu da ke guje-guje suna

wasan ojiyo jiyo.

Dama nasan wata rana zata zo, ranar

da zan fuskance ki gani ga ki don na gaya

75

miki cewa a wancan lokacin zabin da ki ka

yin kuskure babba ki ka tabka.

To gashi ko lokaci mai tsawo ashe ba za

a yi ba ranar zata zo. Mata irinku masu

kwadayi da kallon kyalkyalin mota a mafi

akasarin lokuta abin da ke faruwa da su

kenan.

Ba zan mance bakin cikin da ki ka sa ni

ba, bakin cikin da da kyar na samu ya bar

ni, bakin cikin da ya yi mun sanadin

abubuwa masu yawa.

To amma na gode Allah ko ba komai

kema yanzu gashi nan kin gani ya gama

cin amfaninki ya kore ki ya mayar da ke

tokumbo 'yar kwatano."

Ganin da nayi Abdussamad ba shi da

niyyar tsayawa da maganganun banzan da

yake ta jero mun yasa ni dakatar da shi

cikin sauri.

Na ce, Kayi kuskure da ka dauka

tokumbo bata da daraja, don kuwa akwai

wata tokumbon da ta fi sabuwa daraja.

76



Misali, Tokumbon mota kirar America

da kuma Tokumbon mota kirar China kaga

kamar yadda kwarin su ba ya zama daya

haka ko da suke na hannu farashinsu ba

daya ba ne.

Kuma ka godewa Allah da ya taimake

ka ya rufa maka asiri da a lokacin ba ka

tunkare ni da wata magana ba.

Don kuwa da jinyar bakin cikin da kayi

ka warke da kyar da har yanzu kana yi

bata kare ba, don kuwa babu abinda zan yi

da kai ko a da can ballantana a yanzu da

aka yi iska asirin kaza ya budu."

Naja mishi wani dan banzan tsaki

sannan na ce Da ka ke cewa naga mota

nabi kyalkyali kudi banza ne?

Kaima kayi mana kaga kenan har a

yanzu kai din ba tsarata ba ne. Na raba ta

gefenshi na wuce na shiga zauren

gidanmu.

77

Na dan tsaya sai da na dan ji nutsuwa

saboda barin da jikina yake yi sannan na

shiga gida.

Ban so haka ya shiga tsakanina da

Abdussamad ba, amma ko ma dai menene

shi ya fara.

Sammako nayi don kuwa karfe goma na

safiya na isa tasha tare da rakiyar Yaya

Auwalu.

Karfe uku daidai kuwa muna tasha.

Sammani shi ne yaron wan Babana da

yazo daukana a tasha.

Saboda dama tun da motarmu ta tashi a

tasha nayi waya na sanar da su zuwana.

Saurayi ne da zai kai shekaru ashirin ko

zuwa da biyu. Ba karamar karba na samu

ba daga wurin Kakata Baba Ladi da sauran

kishiyoyinta ba.

Baba Jummai da Baba Iya da kuma

sauran matan gidan baki daya.

78

Babana mutum ne mai dangi, don kuwa

maza ne da su sOsai haka nan yawancinsu

daga mai mata b1yu sai mai uku ko hudu.

Da wuya matuka kaga mai mata daya

sai dai ko yaro. Haka nan 'ya'ya ne da su

masu dumbin yawa.

Wasu daga cikinsu suna zaune ne a

cikin gidan da iyalinsu, yayin da wasu da

suka sanmu hali sun yi nasu a waje sun tare.

Don haka gidan su Babana babban gida

ne na gandu.

Kakata Baba Ladi ita ce mata ta biyu a

wurin mijinta, Dattijuwa ce da a kalla ta

doshi shekaru tamanin a duniya, amma

saboda irin kirar karfi da Allah ya yi mata

har yanzu din nan da karfinta.

Uwargidanta ta dade da rasuwa, haka

nan ma Maigidan gaba daya don kuwa mu

ba mu ma san shi ba.

Kafin nayi wanka na ce zan rama

sallolina da aka biyo ni tuni kwanukan

79

abinci sun kusa cika tsakiyar dakin Baba

Ladi.

Na idar da sallah itama tana miko mun

furar da ta dama mun da hannunta, tana

cewa "Fara shan wannan ki warware yan

hanjinki tukunna."

Na ce, To. Ina shan furata tana

tambayata labarin Ummana da 'yan uwana

ina gaya mata.

Ta ce, Ikon Allah! Ashe ke kuma

wannan aure naki haka ya kasance? Na ce,

Eh Baba Ladi ki taya ni da addu'a hakan

ya zamo mun alheri.

Ta ce, To amin hakan ne kam yafi

amma wai! Alamar tana jinjina abin

mutuwar aure ai ba karamin al'amari ba

ne.

To shi ina dan naki yake? Na ce, Ya

karbe shi. Ta fara zata yi magana na ce

Baba Ladi bar maganar Ishak bana so.

80

Ta kalle ni ta ce, To na bari 'yar, nan,

maganar dai kam babu dadi. Na ce, Yauwa

ashe kin gane kenan.

Na jawo kwanon kwadon zogalen da na

gani ya bani sha'awa saboda wadatar kuli-

kuli da su tumatur a ciki na fara ci.

Ta ce, "To ba kin gama idda ba har

yanzu ba ki fara zawarwa ba ne? na ce, Na

fara to ina suke? Na ce suna nan.

Na mike na fito saboda a yanzu babu

abinda na tsana irin naji ana kirana

bazawara.

Da alama hirarmu da Baba Ladi ba za ta

rinka yin tsawo ba.

Dakin Baba Jummai na shiga duk da

mutanen gidan sun zo mun gaisa nayi

nufin kuma na zaga su gaba dayansu.

Baba Jummai jika take yi da ni sosai.

Ta kalle ni tana balla goronta ta cc, To ke

kin je in kashe aurenki, ga 1azan naki duk

sun kare sai kawai kiyi zamanki a nan

muyi ta lallabawa.

81

Nayi dariya na ce mata, Kada ki damu,

kwanan nan zan ballo miki wani darjeje ki

sha gara har ki ture.

Ta ce, Wayyo yan nan gamu nan dai.

Daga nan dakin ta hudunsu na shiga Baba

Iyalele kafin na gama zaga gidan Magriba

tayi.

Don haka daga nan alwala nayi na wuce

dakin Baba Ladi don yin sallar Magriba.

Harkokina nake yi cikin walwala da

sakewa ga iyayena maza kowa ya fita

kasuwa ko gona ya dawo zaka ji ana ina

"Hauwa Kulu?

Kowa da irin tsabar da yake riko mun.

Da safe kuwa to zan yiwa Baba Ladi aikin

gyaran wurinta na tsabtace shi.

Na cika mata randunan ruwanta na

kuma wanke mata kayanta na sakawa.

Haka ma sauran abokan zaman nata.

Matan gidan kuwa zaka ji suna ina Kulu

take ta taya mu kaza...ina jin Baba Iya

82

rannan tana korafin basa barina ina hutawa

amma ni kam ko a jikina.

Sammani kuwa babu inda bai zaga dani

ba a cikin gari, gidajen yan uwa na waje

da kuma yan kananan kauyukan da yake

kai kwan kaji.

Kafin na cika sati biyu sai kawai aka

fara sallama wai ana kirana zance. Wasu

ko sunana ba su sani ba sai ka ji yaro ya

shigo wai ana sallama da bakuwa.

Haushi ya kama ni ba kadan ba, ban san

yadda aka yi naja wa dan aikan wani dan

banzan tsaki ba na ce, Je ka ka ce ba zan

zo ba, kada kuma su dame ni.

Baba Jummai ta rarumo muciyar tukin

tuwonsu ta nufo ni wai zata fasa mun kai.

Inna Hadiza matar kanin Babana ta ce,

Haba Baba, ai sai ki nakasata. 1Ta ce, To ba

shi kenan ba magana sai1 ta kare.

Ja'irar yarinya kowa yayi sallama ta yi

tsaki kin kaso auren naki ne ki zo ki zaune

wa mutaneki rinka jawo musu

83

maganganun mutane da ba a iyar musu sai

sun tanka?

Ina ce gayar gidan Malam Akawu

kwanaki da aurenta ya mutu washegarin da

ta gama lddarta aka daura mata aure da

mijin da ko ganinshi bata taba yi ba

saboda ta san darajar iyayenta.

To ki raba ni da wannan rashin

mutuncin da ki ke yi wa mutane, idan ba

so ki ke nasa iyayenki su nemo miki miji a

garin nan su aurar da ke ba.

Tsit nayi jikina a sanyaye kuma na

shiga daki na kwanta don nasan zata rina.

An kama azumin watan Ramadan ne

ranar Jumma'a saboda ganin watan da aka

yi a daren Alhamis.

Don haka wayewar garin sai ta zamo

daban. Yau aikin duk na azumi ne masu

surfe suna yi masu daka suna yi.

Nima ba a bar ni a baya ba, sai dai

sabanin yadda nayi zato ba a je ko ina ba

84

na ajiye tambayar saboda bororon da

hannuna ya fara yi sai na koma tankade.

Ranar da aka yi ukun azumi tashi nayi

da nufin yin abinda zan yi buda baki da shi

da kaina.

Alele da kuma soyayyiyar doya da

miyar kwai don kuwa su kunu kawai suke

yi sai abincin gida.

Baba dan Juma ne ya ba da kudin da

aka yi mun cefanen kayan da babu a gida.

Zama nayi nai abincina mai rai da lafiya

na bi 'yan tsofaffin na basu sannan nayi

alwala na zauna ina jiran a kira sallah.

Wayata ta fára kara kamar ba zan dauka

ba, saboda magana ma wahala take yi

mun.

Don kuwa ba karamin jin azumin nake

yi ba. Na yi sallama daidai na

4 / 5