Author : Hafsat C Sodangi Category : KDP NOVELS
/>
turamen zannuwa masu kyau sosai na bata
guda biyu.
22
Na hada da kayayyakin su turare
sabulu da omo da hijabai tare da kudi ma
dan auki na ce, Yaya to ga wannan tunda
ban san haka tafiyar taki zata zo mana ba.
Ta ce, na gode miki Hauwa'u ki kuma
yi ta hakuri kin gane ko? Na ce, eh. Na
dauko Naira dubu biyu na ce mata wannan
ki siya ma Rukayya sweet a hanya ki ce
mata in ji ni.
Tayi murmushi abinda yasa na fahimci
hakan yayi mata dadi ba kadan ba. Ta ce,
zan gaya mata.
Kicin na wuce don nayi girkin dare, don
ba zan jira sai Yaya ta tafi ba, 1tama tana
shirin kayanta.
Da daddare ina daki ina jin su da Ishak
fama yake yi da ita. Amma ko sauraronshi
bata yi, wasu irin maganganu take yi mishi
masu zafin gaske.
Hakuriyake bata amma bata
sauraronshi. Kayi kokari itama ka koreta
sai kuma ka san nayi. Amma ina tabbatar
23
maka zuwa gidanka na daina yi, idan har
ba taitayinka ka shiga ka kama kanka ba,
Ni dai bacci ya dauke ni ni na sake
farkawa na jiyo su na gyara kwanciyata
ban bude ido ba sai da aka yi kiran sallah.
Yaya na samu har tayi wanka ta gama
shiri cikin sauri na ajiye mata tunda ni har
yanzu sallah ta bata daidaita ba.
Wani lokaci ina ganin alama. Ta ce, kai
ni Hauwa'u wani kari zan yi, na ce yi
hakuri Yaya ki karya, ta ce to.
Ina zaune a gefen ta ina shayar da
Abulkhairi ta kalle ni, "Hauwa'u. Na ce,
Na'am Yaya. Kada kijewa iyayenki a
haka da wannan idon ki bari sai ya
washe." Na ce, To.
Tafiya Yaya tayi bata dauki ko
kwandalar da lshak ya bata ba. Duk kuma
alama ne na tsananin fushin da tayi da shi.
Gidan yayi mun wani iri don dama-
dama Abulkhairi yana rage mun 'yar
24
damuwa. Wunin ranar kuma Ishak bai
leka ko ma ba.
Na gama abincin rana na dauko na
kawo mishi dakinshi ya ce, kai mun falo
gani nan zuwa.
Bai fito ba sai da ya yi wanka yayi
sallah ya gama cin abincin shi ya shigo
dakin ya same ni ina bai wa Abulkhairi
nono.
Ya zauna a gefen gadon yana kallonmu.
Na gama ba shi nono na mika mishi shi ya
karbe shi. Yana dan mishi 'yan wasanni.
A raina na ce Ya iya wasa da danshi
kuma kana ganin irin yadda yake tafiyar
da yaron zaka gane yana da muhimmanci a
wurinshi.
Da ni ne kawai ko kuma na ce da
matanshi bai iya mu'amalla ba. Ya dago
kanshi ya kalle ni muka hada ido kadaran-
kadahan fuskarshi.
Na sunkuyar da kaina. "Me yasa idan
na ce miki bana son abu ba kya bari?
25
Kinga abinda hakan yaja mun Yaya ta tafi
tana fushi da ni abin da bai taba faruwa ba.
To kada kiyi tunanin hakan zai sa na
sassauta daga kan ra'ayina na bana son
mu'amallarki da ita.
Nayi shiru zuwa wani dan lokaci na ce,
To amma menene dalilinka na hana ni
mu'amalla da mutane da ka ke yi?
A ciki har da yan uwana? Kana ganin
idan kayi mun hakan kayi mun adalc1?
Kada ka manta kafin aurena dą kai ina da
kyakkyawar m:'amalla tsakanina da 'yan
uwana a yanzu ko inda suke ba ka barina
naje?
"Ba hana ki mu' amalla da su nake yi
ba. A yanzu kin yi kuruciya, ki fahimci
abubuwan da nake kokarin fahimtar da ke,
don haka ba zan Zauna yin wannan
bayánin ba a yanzu."
Ya dauki Abulkhairi ya fita da shi. Na
bishi da ido har ya gama fita a dakin nayi
ajiyar Zuciya a hankali,
27
Ban je gida ba sai bayan sati guda cif da
tafiyar Yaya. Ina zaune a gaban Ummana
farin cikinta bai misaltuwa. Su Tasi'u
kuwa sai kokarin a ba su Abulkhair su
dauke su.
Umma ta hana har Yaya Auwalu ma ya
baro kasuwarshi da wurwuri da nayi mishi
waya na gaya mishi muna gida.
Shi ma Ishak bai zo daukata ba har
Babana ya dawo daga aikinshi ya same
mu. Muka hadu muna ta hira gwanin dadi.
Ishak bai zo ba sai karfe shida na
yamma, kirana yayi a waya ya sanar dani
isowarshi ban kuma nemi ya shigo ba don
nasan ko na nema ba samu zan yi ba.
Na shiga daki muna sallama da Umma
na ce, Ni Umma kina ganin za ki iya yin
wata sana'a kuwa ta cikin gida'?
Ta ce, Eh to me zai hana sai na gwada
na gani. Hannu nasa a cikin Jakata na ciro
mata kudin da na tanada wanda na tara a
lokacin bikin sunan Abulkhairi.
27
Na mika mata gaba daya na ce, Ga su
nan ki gwada muga abinda Allah zai yi. Ta
ce, Ke ko a ina ki ka samu kudi haka?
Ban tsaya yi mata wani bayani ba goya
Abulkhairi kawai nayi na fito muka tafi.
Abubuwan Ishak sun dan ragu,
musamman da yake ya kan dawo gida a
yanzu da dan wuri ko don Abulkhairi.
Sai dai duk da haka ranar da abin nashi
ya motsa sai ya kai sha daya na dare.
Kullum naga yanda Ishak yake tafiyar da
yaron mamakinshi yana kama ni.
Menene hujjarshi na har a yanzu da na
fara haihuwa da shi bai yi tunanin ya gaya
mun komai game da labarin 'ya'yanshi ba?
Wani lokaci sai naji kamar nayi mishi
magana amma sai naga to ma menene na
hanzari ne bari dai na kyale shi naga
iyakacin gudun ruwanshi.
Yau kuwa da ya dawo aiki da wuri
zaune muke duka a falon yayin da
28
Abulkhairi yake kwance kan Cinyarshi
yana barci.
Ya dauko wayar shi ya daddanna ya
fara magana na kuma gane da Yaya ne don
haka na nemi ya bani wayar na gaisheta.
Muna gaisawa ina tambayarta abubuwa
da gangan na ce Yaya ya su Rukayya? Ina
ganin irin kallon da Ishak ya watso mun
wanda ban san ma'anar shi ba.
Yaya ta ce, Tana nan lafiya gata nan ma
a kusa da ni na ce bata mu gaisa, yarinyar
ta fara gaishe ni cikin muryarta mai sany
ta ce mun, Ina Baba karami?
Nayi murmushi na kuma san Yaya ce ta
sa ta ta tambaya. Na ce Baba karami yana
nan lafiya Rukayya, to ai ba ki tambayi
Baba babba ba?
Ta ce, To ina Baba babba? Na ce gashi
nan bari na baki ku gaisa. Na mika mishi
wayar har yanzu kallona yake yi.
Ban zauna ba' wuce shi nayi na shiga
daki na zauna. Sai dai a madadin naji
29
dadin abinda nayin wani gululun bakin
ciki ne ya tokare mun kirii.
Ishak ya raina ni yana yi mun wani
gani-gani to amma babu laifi.
Da kanshi ya shigo dakin yazo ya
gyarawa Abulkhairi wurin kwanciya, ya ce
zan samu wuri kuwa a nan? Na ce me zai
hana idan kana bukata na gyara yanayin
kwanciyata shima ya kwanta yana
fuskantata.
Juyawa nayi na fuskanci bango da nufin
na kaucewa kallonshi nayi bacci sai dai
abin ya gagara.
An kai kamar awa daya bayan nan sa1
naji ya kira sunana ban amsa ba har ya
sake tare da dan daga murya.
Na amsa ya cé, juyo muyi magana. Na
juyo ina fuskantarshi. Ba tun yau ba naso
na zaunar da ke don muyi wasu yan
maganganu sai dai ban samu lokaci ba.
Nasan babu mamaki kin ji wadansu
maganganu daga wurin Yaya. Na ce kamar
30
Don kuwa yadinan shadda bandir biyu
ya saya da atamfofi da kuma wasu
kananan abubuwan amfani iri-iri.
Nima koda nake da kayan amfani ya
karo mun da kuma Abulkhairi da yake na
fara bashi abincin gongoni.
Muna zaune a falo ana gobe zai tafi rike
yake da abokiyar hirar tashi Jarida na ce ni
haka zamu zauna ne a gidan nan idan ka
tafi dagani sai Abulkhairi?
Ya duake Jaridar a fuskarshi ya kalle ni
Ban gane ba? Na sake maimaita mishi
tambayar ya ce, Eh to menene?
Na ce, Ba zan iya ba ne ina jin tsoro.
Kuma nayi tunanin kai da kanka zaka
fahimci hakan ba tare da nayi maka
magana ba.
Sai naga ba ka yi ma wannan tunanin
ba. Kuma ai ya kamata ka fahimta. da
kanka cewa ko ba na tsoron zaman ni
kadai ma ai ba1 yi tsari ka tafi ka bar ni
33
daga ni sai yaro mai watanni biyar a cikin
gida irin wannan ba.
Ko mutanen gari ne suka fahimci baka
nan ai.. To naji ya isa haka. Na ja bakina
nayi shiru shima ya ci gaba da karatunshi.
Abulkhairi yayi bacci na mike na shiga
daki na shimfide shi na fito falon na sake
zama lokacin ne ya kalle ni.
To menene ra'ayinki na ce ni bani da
wani ra'ayi idan a kan wannan ne. tunani
yazo mun a cikin raina.
Mutumin da bai yarda da mu'amallar
matarshi da kowa ba ba shi da kyakkyawar
mu'amalla ko kankani da makwabtanshi
balle da mutanen waje.
Ban taba ganin mutum irin Ishak ba.
Naja bakina nayi shiru ni dai kawai nasan
ba zai tafi ya bar ni a gida ni kadai sai
Abulkhairi ba.
Na sake tashi don zuwa kwanciya tunda
dare ya soma yi na kwanta har na fara
34
bacci sai naji yana tashina na bude ido ki
shirya kayanki mu tafi tare, na ce to.
Kayan Abulkhairi nafi diba tunda shi
yaro ne sai na dauki nawa guda hudu ban
da na jikina.
Sai 'yan tarkacen amfani, tunda dai ya
ce kwana uku zai yi. Tafiya sosai muka yi
don kuwa cikin awowi hudu sai ga mu a
Kaduna gidan Yaya.
Murna sosai tayi tana rike da
Abulkhairi da itama take cewa Baba tana
ta shafa shi tare da yaba girmanshi ta ce,
Ikon Allah! Wato yaron nan da magajinshi
ya ke kama?
Ishak ya dan yi murmushi ya ce, Nima
lokaci-lokaci sai naga kamar hakan. ta ce,
Ai babu ko wai a ciki, to Allah yasa ka
gaji halinshi.
Ta kalle ni yau ga Hauwa'u a gidan
Yaya, nayi murmushi muka sake gaisawa
na ce, Yaya ban ga yara ba ta ce eh sun tafi
35
Makaranta. Tafiyar taku babu sanarwa
babu komai?
Ya ce, Eh ban sa rän yinta ba a yanzu
nima, ta dauro ne kawai tunda kin ga
hutun kwanaki uku kawai na dauko duk da
kwanakin sati sai su zama biyar.
Ta ce, Eh hakan yayi kyau zaka wuce
Kaciya kenan? Ya ce, Eh su Abulkhairi za
su gida kenan. Ya ce, A'a su a nan zan bar
Su.
Ta ce, Saboda me? Bai bata amsa ba sai
dai daga ni har ita bin shi da ido muka yi.
Hajiya Baba kamar yadda naji yaron
suna kiranta mata ce mai matukar
mu'amalla da mutane sabanin kanin nata.
Tun da muka shiga gida kafar yara bata
dauke ba haka nan babu abinda bata
siyarwa na amfanin gida.
Don haka tana da rufin asirinta daidai
ita, don kuwa kaninta a tsaye yake akan
al 'amuranta tunda gidan da take ciki ma a
36
yanzu nashi ne, shi ne kuma ya biya mata
ta sauke farali.
Su Rukayya ba su dawo ba sai wajen
karfe biyu da rabi. Na bi yarinyar da kallo
lokacin da ta durkusa tana gaishe ni
Ba za ta fi shekaru shida ba, ya yanta
kuma takwas ta juya tana gaida Babanta ya
miko mata hannu alamar ta karasa inda
yake ta kwanta a jikinshi yana mata 'yan
tambayoyi.
Sai da ta gama ba shi amsa ya ce, To ba.
ki tambayi kaninki ba gashi can je ki ki
dauke shi, ta taho inda nake zaune tasa
hannu ta dauki Abulkhairi da ke zaune
yana wasa.
Duk da sanin da nayi ba wani iyawa
zata yi da shi ba, ban hanata ba. Ishak ne
dai da yaga zata tima shi a kasa ya zabura
ya karbe shi.
Sosai na sake da yarinyar saboda
yanayinta na nutsuwa don kuwa tafi
37
wanta, tana yawan zuwa inda nake saboda
Abulkhairi, ba na kuma hanata daukanshi.
Washegari da sassafe Ishak ya wuce
garinsu na sake a gidan Yaya sosai har
kicin tare muke shiga ina kuma tayata
sayar da kayanta.
Muna cin abincin rana take tambayata
ni Hauwa'u ya mijin naki dai komai lafiya
ko?
Na ce lafiya kalau Yaya. Babu wata
matsala? Na ce ko kadan. Ta ce, To ai shi
kenan tunda kin fadi haka, alama ne na ke
din mata ce mai hakuri to sai ki kara a kan
na da.
Bakunta mai matukar dadi muka yi har
Ishak ya dawo washegari na roke shi ya
kai ni na yi wa yara siyayya bai ki ba.
Siyayya sosai nayi musu dangin kayan
sakawa kayan wasa da kuma na kwalama.
Murna sosai Rukayya ta rinka yi sannan
na ce muje studio aka yi mata hoto da
Abulkhairi wait and take.
38
Na bata nata nima na dauki kwafi daya,
hoton yayi matukar kyau hakan ne yas
Ishak cewa a wanke musu baba, duk da
dai ba tsayawa karba zamu yi ba a baiwa
Yaya.
Ni kaina bakuntar tayi mun kadan,
amma haka muka taho gida washegari
muka bar su cikin kewa Rukayya kuwa
tana ta kukan a bar mata Abulkhairinta.
A yanzu da Abulkhairi yayi wayo kuma
nake ganin canji daga wurin Ishak alamar
ya dan fara sassautowa daga tsamin
halinshi, sai nake ta kwadayin komawata
Makaranta.
Tun da dai yaron yay1 wayo a watanni
goman da yayi ne a duniya yake gudunshi
ko ina.
Samun Ishak nayi cikin dabara na yi
mishi maganar Makarantata tun da ni dai
babban burina kenan. Na ce, Don Allah ka
bar ni na koma ko ba ka yarda nayi aiki ba
ni bani da matsala.
39
Amma burina dai yin karatun ne kawai
zai amfane mu ba ki daya. Karatuna ba zai
taba zama maka mätsala ba.
Bai ce mun komai ba har na yi
maganganuna na gaji nayi shiru. Sai ma
gyara kwanciyar shi da ya yi ya juya baya.
A haka muka ci gaba da zama sana'ar
da Ummana ta fara yi sai ya bunkasa ba
kadan ba itama dai kayan gidan ne dangin
man gyada, maggi, kalanzir har da su
kuli-kuli.
Kai komai yanzu sayarwa take yi, kuma
sana'a ce mai albarka ta rufin asiri. Ba na
ko damuwa don ban bata kudi ba yanzu
tunda nasan bata rasawa.
nrbRasuwa aka yi a unguwarmu kuma
Ishak ne da kanshi yazo yake gaya mun,
na kuma roke shi ina son yi musu
ta'aziyya ya ce to.
Don haka da na gama ayyukana sai ma
rike hannun 'Abulkhairi muka fita na rufe
gidan.
40
A gidan ta'aziyyar naga Hindu da
Mominta muka fito tare don komawa gida
Hindu tana rike da hannun Abulkhairi tana
gaya mun ta samu admission a (Ahmadu
Bello University) da ke Zariya.
Murna sosai nayi mata ta ce ke dai
Maman Abulkhairi har yanzu shiru. Nayi
murmushi ban ce mata komai ba.
Muka yi sallama da Momi na mika
hannu zan karbi Abulkhairi ta ce, a'a bar
mun shi kawai zan turo Abubakar ya dawo
da shi.
Na ce to, ba don raina ya so ba sai don
kada suyi zaton wani abu sannan kuma shi
da ai ba a rowarshi.
Na dawo gida sai dai gaba daya
hankalina yana wurin Abulkhairi, har
karfe shida a yanzu da Ishek bai cika yin
dare ba ina tsoron ya dawo yaga danshi
baya gida ban san abinda zan ce mishi ya
fahimce ni ba.
41
Ina jin taba kofa na zabura na mike
cikin sauri na bude kofar, Abubakar ne
rike da Abulkhairi sai dai an makara, don
kuwa shima Ishak din gyaran parking yake
yi.
Jikina a sanyaye na fara kokarin rufe
kofar tunda shi ta cikin gareji zai biyo. Ina
shiga daki shima ya shigo.
Abulkhairi ya falla a guje ya tafi don yi1
mishi oyoyo din da ya saba. Yana
daukanshi ya shigar dashi cikin daki ya
kulle ya dawo.
Me na gaya miki a kan mutanen nan
iye? Na fara ja da baya saboda matsowar
da yake yi da kuma abinda na gani a
idonshi na tashin hankali.
Ni kuma a yanzu babu abinda nake
tsoro irin dukan Ishak, sai dai ban tsira ba.
Duka sosai ya lakada mun ya tara mun jini
a ido.
Kwana nayi ina kuka, haka nan
Abulkhairi duk da kin barin shi yazu
42
gurina da yayi ya shiga dakinshi da shi ya
rufe kofa.
Na fara gajiya da irin wadannan
abubuwan har gashi yaro ya fara fahimtar
wasu abubuwa ya tayaka kuka.
Da kyar na lallaba da asuba na shiga
bayangida na gaggasa jikina, har da
fuskata na dawo alwala nayi sallah.
Lokacin ne shima ya bude kofa ya fito
don zuwa Masallaci.
Har da gari ya waye bai bar Abulkhairi
yazo wajena ba, da kanshi ya ba shi abin
karyawa ya yi mishi wanka ya sa shi a
mota ya tafi da shi, ban san inda suka tafi
ba.
Ko girki ban iya yi ba sai tea da na
wuni sha saboda mummunan ciwon daa
jikina yake yi mun, ba su dawo ba sai
karfe hudu na yamma.
Yana sake Abulkhairi dakina ya nufo a
guje. Ina kwance gwalandin magana yana
43
tambayata wai Babanshi ne ya dake ni to
nayi hakuri kin ji Mama.
Ban ce mishi komai ba amma duk
kokarin hana hawayena zuba da nake yi
bai fasa gangarowa ba.
Ya shigo dakin ya rike hannun
Abulkhairi yaja shi suka sake fita, na ci
gaba da kukana.
Idan na bari Ishak yana yi mun irin
wannan dukan wanda jinýa take biyo
bayanshi anya zan kai labari kuwa?
Ya sake shigowa dakin rike da leda a
hannunshi ya zauna a kan stool din gaban
dressing mirrow yana ciro abubuwan cikin
ledar.
Robar abincin ne na take away sai
gasasshiyar kaza sai magunguna. Tashi
kici abinci.ban ce mishi komai ba, amma
ban iya daina kallonshi