MAI DAKI (2) Hausa Novels By Hafsat Sodangi.docx

Author :  Hafsat C Sodangi Category :  KDP NOVELS

Chapter   3 / 5

6K to 9K   out of 13.9K words

ba.

Abulkhairi ya matso, "Mama tashi."

Yasa hannu yana girgiza ni ban motsa ba.

44

Ya fita ya dawo da robar swan ya kama

ni zai daga ni na fizge hannuna na koma

na sake kwanciya.

Shima fita yayi bai sake ce mun komai

ba. Na sake fashewa da wani sabon kukan,

babu irin tunanin da bai zo mun raina ba.

Ya zama dole na hemi mafita abinda

kawai zuciyata take kara jaddada mun

kenan.

A hankali sai na samu sauki na ci gaba

da hidimomina, sai dai idona har yanzu bai

washe ba. Zazzabi sosai ne ya kama

Abulkhairi wanda yasa Ishak ya sauke mu

a asibiti don ganin Likita.

Muna zaune muna bin layi a sashen

yara sai kawai naga Sadiya Tanimu cikin

mamaki na rike baki ina kare mata kallo

sanye take da fararen kaya na jinya wato

Nurse na ce, Sadiya kada dai ki ce mun kin

zama Nurse?

45

Ta ce, a'a haba ce miki aka yi abin babu

wuya, ina dai shirin zama wannan ita ce

shekarata ta farko.

Na ce, Au to koda dai naji. Ta ce, ai

shekara biyu kenan rabon da muga juna

kin tuna?

Sai lokacin ne na tuna zuwanta na

karshe wajena da abin da ya faru

tsakaninta da Ishak. Na dan yi murmushi

na ce haka ne fa ba mu sake haduwa ba.

Ta sunkuya daidai inda Abulkhairi yake

ta mika mishi hannu tare da cewa "Hi

handsome ya ka ke? Ya ce, Salamu

alaikum Babana yake cewa.

Ta ce, To ko kuwa ya ce, Eh to ce to ka

gani kenan akwai 'bambanci. Ta mike ta

gyara tsayuwarta ta ce, yaron ki ya mun

kyau gashi da wayo na ce baki yi aure ba?

Ta ce, Eh to muna kan hanya na ce to

Allah ya ba da na kwarai. Ta kara zuba

mun ido tana kallona ta ce, Kin san wani

abu ne?

46

Mijinki exacthy mijin Sister ta shi yasa

abinda ya yi mun bai bani haushi ba. Idan

ya tashi dukanta itama sai idonta ya bar

jini, na ce kai! Sadiya kenan baki da dama

ce miki nayi dukana yayi jini ya taru mun

a ido? Ni ciwon ido nayi.

Ta dan tabe baki kamar dai yadda ta

saba ta ce, Oho dai ni na gaya miki nasan

maza irin su. Abu daya za ki yi ki taimaki

kanki ki koma Makaranta shi kanshi

wataran idan aka ce ya buge ki ba zai fara

ba.

Shi yasa wani lokaci ma ko son tunanin

aure bana yi saboda irin wannan tauye

hakkin.

Ai ba haka aka ce ayi auren ba. Ban ce

wa Sadiya komai ba amma dai ina ganin

shawararta zan bi to ta ina? Ni dai nasan

ba karamin yaki za a yi da Ishak ya bar ni

na koma Makaranta ba.

Sai da muka gama ganin Likita sannan

na kira shi a waya yazo ya kai mu gida.

47

Muna zaune da dadare bayan mun gama

cin abinci na kwashe kanukan duk da

faduwar da gabana yake yi.

Ban fasa yi mishi maganar ba cikin

hanzari kuma ya dakatar da ni irna so in

tabbatar miki da komawarki Makaranta ba

zai taba yiwuwa ba.

Nayi shiru zuwa wani lokaci na ce kayi

hakuri ka gaya mun sharuddanka na yin

karatuna ba zan kaucewa dokarka ba, ka

ji?

Na tambaye shi ya mike ya zauna ya

zuba mun ido, Kina son yin karatu? Cikin

sauri ya ce, To ga zabi zan baki.

Sai kiyi wanda ki ka fi so, babu matsala

duka zan yi miki. Za ki zauna ne kiyi

zaman aure shi kadai ba tare da kin yi

karatu ba ko kuwa za ki bar zaman aurenki

ki koma karatu?

Gabana ya yi mummunan faduwa, na

dago kai na kalli Ishak da ya zuba mun ido

yana kallona.

48

Wacce irin tambaya ce wannan? Ishak yana nufin kenan idan har zan zauna da shi ba zan koma Makaranta ba, haka zan yi ta zama dashi da halayenshi?

Ya raba ni da "yan uwana, ya raba ni da kowa haka nan kankanin abu idan nayi ya rufe ni da duka tamfar an aiko shi.

Amma hakan bai ishe shi ba ya tsare ni da irin wadannan tambayoyin saboda rainin hankali.

Ina son aurena duk da irin abubuwan da nake fuskanta, to amma idan na zabi auren nashi ai zai ga kamar naji tsoro na kuma ba da kaina ban kuma san abinda zai biyo bayan hakan ba.

Haka nan shi idan ya matsu da auren ai sai ya bar ni na ci gaba da karatuna saboda nima na samu mafita kan matsalolina, kenan dama ce ta zo mun.

Ya ce, Ke fa nake jira. Wanne ki ka zaba? Na ce, "Karatu. Ya ce, "To babu laifi. Ya koma ya kwanta.

49

Na hau gado na kwanta a raina ina

tunanin babu mamaki nima nan da yan

watanni kadan na koma na ci gaba da

makarantata.

ldan na gama kuwa na tafi na zama

Nurse har yanzu ban canza buri ba. A haka

barci ya dauke ni.

Da sassafe na shiga dakin Ishak don na

gaishe shi ya gama amsawa na mike don

fara shirin abin karyawa.

Ya ce, Zo. Na dawo na sake zama

Ungo wannan. Na karba, takarda ce ina

jiran ya yi mun bayanin wanda zai zo ya

karba ko wani abu makamancin hakan.

Sai na ji ya ce, "Zabin ki ne nakaratu

don haka kije kiyi na sauwake miki." Bai

jira amsawata ba ya juya ya fita a daki.

Ina zaune a wurin kwakkwaran motsi

na kasa yi, sauwakewa saki kenan ko me?

Sai dai har a yanzu ban bude takardar

na ga abin da ke cikinta ba. Ya sake

shigowa dakin ya ganni a inda nake zaune

50

ya ce Kije "gida kiyi musu bayanin komai".

Na mike na dawo dakina na dauki hijab

da Jakata nasa hannu na dauki Abulkhairi

da har yanzu yake barci na saba shi a

kafadata na fito falo zan wuce ya ce, Zo

Hauwa'u.

Nadawo ya ce, "Sauke shi. Nayi

sokoko ina kallonshi ya sake cewa "Sauke

min shi. A lokacin da ki ka yi zabin da ki

ka yin ba ki kalle shi ba, yi kawai ki ka yi

ba tare da kin yi tunanin wasu abubuwa

masu grma za su biyo baya ba.

Abulkhairi dana ne ni ke da cikakken

iko a kanshi, don haka ajiye mun shi.

A hankali ya mike har inda nake yazo

syasa hannu ya dauke shi a kafadata ya

shimfide shi tare da dan jijjiga shi a

hankali ganin yana kokarin farkawa na

dawo gida cikin wani yanayi da baya

kwatantuwa.

51

Umma tana ganina ta ce "Lafiya ki ka

bugo irin wannan sammakon haka? Ina

yaron?"

Na ce, Yana tare da Babanshi. To lafiya

dai ko? Ta sake tambayata na ce, Eh Baba

nake son gani.

Ta ce, Ikon Allah, to ai yanzu ya tafi sai

dai ko ki yi sammakon zuwa da safe, ko

kuma ki dawo da yamma.

Neman wuri nayi na zauna ba tare da na

ce mata komai ba. Ta sake bina da kallo ta

tashi ta kawo mun abin karyawa ta ce, To

ga shi nan ki karya ko?"

Duk da ban ci komai ba na fito daga

gida ban ji wani alamar yunwa a tare da ni

ba.

Ina kallon Umma tana ta harkokinta da

yaran da suke zuwa siyan kaya da kuma su

Tasi'u. Itama ta Iura ta gane ba zan yi

magana ba ta rabu da ni.

52

Sai dai a duk lokacin da nayi nufin

kallon inda take sai naga itama ni take

kallo. Zuciyata tana ta kaiwa da komowa.

Ban taba tunanin zabin da nayin zai

zamo haka ba. To me Ishak yake nufi

kenan?

Babana bai dawo gida ba sai wajen

Karfe biyar na yamma, yadda dai ya saba

dawowa kenan. Yana ganina ya ce, "A'a

Hauwa'u ce yau a gidan? To ina abokin

nawa?

Na ce mishi Yana gida Baba. Na

durkusa na gaishe shi. Ban yi mishi wata

magana ba sai da ya ci abincin shi ya samu

nutsuwa sannan na mika mishi takardar da

Ishak ya bani wacce har a yanzu din nan

ban iya budeta naga abinda ke cikinta ba.

Cikin nutsuwa ya budeta ya fara

karantawa. Babana duk da yake Masinja a

Banki ya iya karatu da rubutu daidai

gwargwado.

53

Inna lillahi wa inna ilaihir-raji'un.

Abin da ya biyo bayan karatun nash1

kenan.

Yayi shiru na kusan mintina biyar

sannan ya ce, Ikon Allah! Me ki ka yi

mishi da zafi haka Hauwa'u da yayi nufin

yanke miki irin wannan hukunci mai

tsanani? Ba zai yi miki saki daya ko biyu

ba sai ya yi miki uku gaba daya."

Na dafe kirji da sauri na ce "Uku Baba?

Yau na shiga uku! Tuni na fashe da kuka.

Mikewa nayi cikin sauri da nufin fitowa

a gidan na koma gidan Ishak. Babana ya

ce Ina za ki je? Na ce, "Baba zan dauko

Abulkhairi ne. "

Ya ce, "Dawo kawai Hauwa'u, ba shi

ya karbe shi ba? Na ce, "Eh Baba ai cewa

ya yi nazo nay1 muku bayani ne kafin na

koma na karbe shi."

Ya ce, "A'a bar mishi danshi kawai kiyi

hakuri. Wata rana za ki ga kamar ba ayi

ba, ki daure ki zama Jaruma ki yawaita

54

addu'a, Ubangiji yayi miki zabin miji

nagari da zai zamo miki alheri fiye da

wannan da ku ka rabu."

Cikin sanyin jiki na koma dakin Umma

na hau kan shimfidar na sake zama. Ita

kuwa tana ta harkokinta na kokarin ganin

ta karasa abincin daren da take yi.

Ban taba sanin haka abin zai zamo ba,

yanzu duk wannan zaman da muka yi da

kuma hakurin da na rinka yi a haka auren

zai kare?

Lallai Ishak ya wuce sanina, don

kuwaban taba zaton zai yi mun hakan ba.

Ko da ya bani zabi kuma na dauka karkari

ya yi mun saki daya ne ba uku ringis ba.

Hakan ya yi ne don ya nuna mun dama

can ni ce na damu da zaman ba shi ba.

Auwalu ne da kanshi ya shiga dakina na

da ya tsaftace shi ya gyare shi tsaf ya sayo

sabuwar katifa waya takwas da zanin gado

da filo guda daya ya ajiye ya shimfida leda

55

a tsakar dakin don na dan ji dadin zama a

ciki.

Kwanaki biyun da nayi a gida ba masu

sauki ba ne ko kadan don kuwa kwtaa-

kwata bana barci.

Babu abin da yafi damuna irin kwace

Abulkhairi da Ishak yayi da dai a ce yayi

mun sakin ne sai ya bar ni na taho da dana

to da abin ya zamo mai dan sauki a

wurina.

Shi kenan shima yanzu nasan yana

Kaduna wurin Yaya tare da su Anas da

Rukayya.

Ina zaune ne a gida amma ko tsakar

gida ba fitowa nake yi ba ballantana naa

taya Umma wan1 aikin gida.

Idan har nasa kafata a waje to kuwa

wanka zan yi ko wani uzuri ko kuma

alwala.

Ko abinci Tasi'u ne ko kuma Sabi'u

suke kawo mun na kasa sakewa ko kadan

naji dadin zuciyata.

56

Itama Umma harkokinta take yi ba tare

da ta saurare ni ba don kuwa har a yau

dinnan bata ce mun komai a kan maganar

ba ballantana ta tambaye ni abinda ya hada

ni da Ishak yayi abinda yayin.

Ranar da na wayi gari kwanana bakwai

a gidan ranar ne dan aika ya yi sallama ya

dire mun akwatunana wadanda su ne kadai

abinda na mallaka a gidan Ishak.

Komai na same shi ne a can ya kuma

miko mun zungureriyar envelop ya ce in ji

Ishak din.

Na koma daki na zauna na bude wata

'yar gajeriyar wasika ce, ga abinda ya ce:

Hauwa 'u,

ts Ina fata kina nan lafiya?,

Ga kayanki a bayar a kawo miki, don

nasan kina da bukatarsu. Wannan kudin

kuma kiyi amfani da su wajen ganin kin

koma Makaranta tunda na gane hakan

yana da matukar muhimmanci a

57



rayuwarki, tunda ki ka zabe shi a kan

aurenmu.

Ina so ki.san zan zamo mai taimako

kwarai ta fannin karatun naki a duk sanda

ki ka bukaci nayi hakan.

Ina miki fatan alheri. Abulkhairi yana

gaida Mamanshi.

Na gode.

Na bude daya envelop din, rafa ce ta

dubu daddaya guda daya.

Na mayar a ajiye na fara duba kayana,

duk wani abu da na mallaka a idanshi ya

saka mun a cikin akwatuna set daya mai

shida.

Sai saitin Encholac guda daya mai uku.

Na jawo babbanalbum dina wanda

hotunan Abulkhairi ne kadai a ciki na

bude hotonshi na karshe na fara gani

wanda aka yi mishi shi a ranar da ya cika

shekaru biyu a duniya.

58

Nasa hannu na shafa fuskarshi da ke

murmushi a hoton ko sai yaushe zan sake

ganinshi, sai Allah.

Hawaye suka yi ta zubo mun. Ya zama

dolena wartsake na fuskanci al'amuran da

ke gabana.

Ba zai yiwu nayi ta zama cikin kunci

don kawai Ishak ya sake ni ba. Rayuwata

yanzu ne take farkon ganiyarta, tunda ko a

bana shekaru ashirin da daya ne da ni,

auren kuwa shekaru hudu.

Wartsakewa nayi na fito tsakar gida na

fara taya Umma hidimar gidan da kuma

harkokinta na saye da sayarwa.

Irin su bayar da abu idan an zo siye,

karbar kudi da kuma bayar da canji, muna

kuma yan hirarrakinmu.

Su Tasi'u ma ganin na dan soma

wartsakewa murna suka rinka y1. Bini-bini

Su zo su zauna a inda nake suna yi mun

magana.

59

Babana yana dawowa da yamma sai da

ya gama cin abinci sannan naje na same

shi.

Na sake gaishe shi sannan na kawo

mishi batun bukatata na son komawa

Makaranta, don ganin na ci gaba da

karatuna.

Shiru yayi yana kallona, kallon da yake

yi mun shi ne yasa ni ta kara shiga

taitayina tun kafin naji abinda zai ce.

Ke! Kina cikin hayyacinki kuwa?

Anya wani abu vai shiga kwakwalwarkii

ba?

Idan ma kin kaso aurenki ne don ki

koma Makaranta, to ki kwaan da sanin

hakan ba zai yiwu ba, shashashar yarinyar

kawai, wacce ta ke nema ta mayar da

kanta wata ir1.

Tun kafin ki gama Iddah har kin fara

kokarin neman abin yi saboda ke addinin

ba damuwa ki ka yi da shi ba ko? Tashi ki

bani guri na sha iska."

60

Idan na ce ban shiga mawuyacin hali ba

ma to nayi karya. Duniyar tayi mun wata

iri.

Nayi ta kokarin ganin na sake jikina

nayi hidimar gabana amma abin ya gagara.

Don kuwa ko na dan manta kuma na

dan lokaci ne sai naji kamar wani abu ya

muntsini zuciyata.

Ko da ba wani jin dadin zama da shak

nake yi ba sai na fahimci dakina shi ne

cikakken 'yancina.

Sai nake ganin kamar na rasa komai

babu Abulkhairi wanda a kullum kewarshi

take sanyanına rasa sukuni.

Tsananta wa kana aikace-aikace da

nayi sai yake debe mun kewar zaman

tunane-tunane wadanda ba za su amfane ni

da komai ba.

Kullum na idar da sallar asuba sai

kawai na fito tsakar gida na wanke ta kwal

na wanke mana bayan gida na ciccika

randunan ruwa.

61



Nayi wanke-wanke nayi wanki sannan

na dora abin karyawa.

Yaya Auwalu da kanshi sai da ya ce,

aikin ya yi yawa na rage. Murmushi kawai

nayi ban ce mishi komai ba.

Idan nayi wanka sai na dora mana

abincin rana nayi na dare, Umma kuwa

tana harkar kasuwancinta wanda kullum

kara bunkasa yake yi.

Yanzu gidan ba a rashi kamar da. Dan

albashin Babanmu da kuma sana ar Umma

wani karin rufin asiri ne a gare mu baki

daya.

Ga Yaya Auwalu da a yanzu saukin

abubuwan da ya samu na gida yasa yake

ajiye mana hatsi a maimakon kullum a yi

ta awo.

Don kuwa a yanzu shima oga ne na

kanshi duk da dai ba rabuwa yayi da

maigidan nashi ba.

Duk da hakan dan kankanin lokaci ne

kawai sai na zube nayi baki. Ganewan da

62

nayi in ba matukar hankali nayi ba zan

canza gaba daya yasa nayi tsaye don ganin

na kula da kaina ta wurin cima da kuma

gyaran jiki.

Iddahta ta cika ne ana gab da fara

Azumin watan Ramadana mai albarka, bai

fi saura sati uku ba.

Zuciyata sai kaiwa da komowa take yi

akan na sake samun Babana a kan

maganar Makarantata.

Babu mamaki a yanzu tunda na gama

Iddah ya yarda amma ina matukar jin tsoro

don kuwa wani abu makamancin wancan

bai taba faruwa tsakanina da shi ba.

Ina zaune a kan shimfidar tabarmar da

nayi a tsakar gida ina taya Umma kullin

gishiri.

Yayin da take gete tana lissafin kudin

cinikinta na ce Umma ko za ki taimake ni

ne ki B yi.siwa Babanmu maganar

Makarantata tunda a yanzu babu wani

nauyi a kaina.

63

Ta ce, "A wane dalili?"

Nayi shiru ina tunanin abinda zan fada

mata don gamsar da ita zamana a haka ba

shi da wani amfani."

Sai ta ce, "Kina so né na taimaka miki

ki bijirewa maganarshi? In yaso kenan

nima sai nasa ran wata rana zai kafa doka-

ki taimaka a karya dokar ko?

To ba zan iya ba. Babanku burinshi a

yanzu na ki samu miji ne kiyi wani auren,

ki zauna a dakinki cikin rufin asiri.

Yanzu da da ba daya ba ne. da da yake

burin ganin kin yi karatu to ya wuce.

Yanzu ke ba yarinya karama ba ce,

koda ba ki da yawan shekaru a kanki

yanzu kuwa burinshi bai wuce na ganin

kin zauna a dakinki kin nutsu kin samu

mijinki da zai kula da al'amuranki ya

kuma tausaya miki.

Ba wanda zai nemi wulakanta ki ko

tozarta ki ba, karatu ga budurwa ba dole ba

ne ballantana ga bazawara.

64

Wani irin faduwar gaba naji da Umma

ta kira ni Bazawara.

Nan da nan sai maganganun Umma

suka zamo tamfar fami a zuciyata, nayi

wunin ranar ba

3 / 5