Author : Hafsat C Sodangi Category : KDP NOVELS
MAI DAKI.... (2)
NA
HAJ. HAFSAT C. SODANGI
(Mrs. Yunus Abdullahi Dabai)
1
SADAUKARWA
Sadaukarwar littafin ta Iyayena ce,
Alhaji Chindo Muhammad Sodangi da
Hajiya Fatima Musa Sodangi, Ubangj
ya saka muku da alheri ya kuma kara
muku lafiya amin.
TUKUICI
Tukuicin littafin naki ne;
Khadija Chindo Sodangi (Mrs Nasiru
Idiris)
JINJINA
Jinjinar littafin taki ce Amarya ba kya
laifi (Maman Umar) Zuhuriyya Ibrahim
(Mrs Lawal Chindo Sodangi), Ubangiji
ya raya Umar da Imani.
FATAN ALHERI GARE KU
Fatima Abdulkadir Kazaure
Hafsat Iliyasu Unguwar Rimi
3
Khadija Usman Nasarawa
Nafisatu Ibrahim Muhammad
Fatima Ahmad Shehu Kaduna
Maryam Muhammad Gusau, Zamfara
Umaima Abubakar Umar
Maijidda Uba Magaji
Na gode, Ubangiji ya saka da alheri
amin.
KUNA RAINA
Hajiya Maryam (Mami) Dan Hassan
Hajiya Jamila Ibrahim Na-Bature
Hajiya A' isha Balarabe (Jazan)
Ubangiji ya bar zumunci amin.
4
Littattafan SODANGI:
Uwar Miji
Naga Ta Kaina
Rabon Kwado...
Cikar Alkawari
Wayyo Duniya
Yi wa Wani...
Abu Naka...
Mata Ma su Duniya
Nufin Allah
Kifi Na Ganinka...
Daga Kin Gaskiya..
Da Kamar Wuya...
Mai Uwa..
Duk Daya...
Mata Da Kicin Dinsu
Wacece Ni?
Wata Fuskar...
Mijin Ta ce
Garin Banza..
Ga ni Gare ka
5
Biyan Bukatar Rai
Shamaki
Hattara
Mata Masu Duniya
Kyautataa
Ayi Dai Mu Gani...
Tabbataccen Al'amari
In Kunne Yaji..
Halin Rayuwa
Mai Daki..
Littattafan ba sa nufin yi da wani ko
habaici ga kowa sai dai an rubuta su ne
don fadakarwa da nishadantarwa, ana
neman afuwa ga duk wanda yaga wani abu
yayi kamar 'abinda ya shafe shi, ba da shi
ake ba dace ne kawai.
6
MAI DAKI...2
W ahala dai irin wacce nayi ta ranar
ta wuce a zauna fada. Babu wani
na makwabta da zan tuntuba don ba ma
zan iya mikewa ba balle na ka1 ga zuwa
wani wuri.
Na kai awa biyu kafin ciwon ya sake ni,
na kokarta na ja jikina na hau kan
doguwar kujera na kwanta.
Wasu hawaye ma su dumi suna bin
kuncina. Ban kai mintina goma a haka ba
sai ga shi ya shigo ko kallonshi ban yi ba
balle nayi mishi sannu.
4Ya ya akwai matsala ne? ban ce mishi
komai ba, kukana kawai nake yi.
Ganin haka yasa shi ya ajiye ledar da ya
zo da ita ya wuce ni ya shiga dakinshi. Bai
fito ba haka nan nima ban tashi don yin
sallar Magriba da Isha'i da ban yi ba har
wajen karfe goma na dare.
Ya fito falon yana kalloa "Na tambaye
ki ko kina da matsala ne kin yi mun shiru,
7
amma kin zauna kina kuka wai ke wane
irin hali ne da ke ne?"
Ya kalli ledar abincin da ya ajiye a kasa
yayi tsaki. "Idan ba za ki ci abincin nan ba
wuce kije ki kwanta.
Na mike a hankali tare da rike gefen
cikina da ke mun wani irin ciwo na lallaba
a hankali na hau kan gadona na kwanta.
Wata kila yanayina da ya gani ne yasa
shi biyo ni dakin. Hauwa'u menene
damuwarki? Ina kuka na ce "Umma nake
so ka kira mun. 99 Ya ce, "Umma kuma? A
wane dalilin zan yi hakan?
Na ce, Ba ni da lafiya ne. nayi mishi
bayanin abinda ya faru da baya nan da
kuma ciwon da gefen cikina yake yi mun.
Fita yayi zuwa dakinshi ya dauko
mukulli ya sa hannu ya dauke ni zuwa
wurin motar shi, muka tafi asibiti.
Likita na duba ni ya ce haihuwa ce, duk
da akwai sauran kusan sati uku kafin
(E.d.d) dina ya cika. Nakuda kamar za a yi
8
kamar ba za a yi ba shiru ka ke ji kamar an
shuka dusa.
Har gari ya waye ya leko dakin yana
shaida mun zai je kiran Umma, don shi ma
ya je ya shirya yayi wanka na ce To.
Umma ce tazo ta tsaya a asibitin. Da
kyar da taimakon Allah da na Likitoci na
haihu wajen karfe uku na rana na samu
santalelen yaro, jajir da shi.
Ba mu dawo gida ba sai washegari
saboda hutu da suka ce na samu da kuma
dalilin zubar jinin da nayi
Umma ta nemi Ishak ya bar ni na koma
gida don yin jego bai yarda ba, don haka
dakina aka mayar da ni.
Mutanen unguwar mu sun zo mun
barka ba kadan ba, har ma da wadanda
ban sani ba. Sanin halin Ishak da nayi ne
yasa da aka fara maganar kawo mai yi
mun wanka na ce su bari a tuntube shi
tukunna.
9
Ilai kuwa sai cewa yayi Yayarshi ce
zata zo. Bayan kwana biyu kuwa sai gata
ta iso.
Mata mai saukin kai ni kuma nayi sabo
da ita ne ta yawan wayar da suke yi da
Ishak ta ce a bani mu gaisa.
Suna sosai aka yi ta bangarena iyayena
da 'yan uwana sun yi mun irin nasu
kokarin, sun kuma yi mun gata ta wajen
zuwa dubani da jariri.
Haka nan yan uwan lshak suma sun zo
ba kadan ba. Don haka bikin suna mai
gamsarwa sosai aka yi. Yaro kuma yaci
sunan Baban Ishak wato Abdullahi, amma
an yi mishi lakani da Abulkhairi.
Abinci kala-kala aka yi ta kawowa da
aka yi odar su babu kuma wanda zai ce bai
gamsu ba. Yaya ce da kanta ta tashi
washegarin sunan tunda asuba ta fara aikin
tsabtace gidan.
Kafin takwas na safiya kuwa tamfar ma
ba a yi komai a cikin shi ba.
10
Mu kuwa tuni mun yi wanka daga ni
har jarii Abulkhairi. Ta shigo har cikin
dakin da nake zaune ta fara karyawa muna
dan hira tana tambayata "Kin ga kayan
naku kuwa?
Na dan yi murmushi. Ta ce Hauwa'uu
kenan, hala ke ba kya halin naku ne na
zamani? Na ce, Yaya meye halin
zamani?
Ta ce, Rashin kunya mana wai ku nan
a dole kun waye? Yaya ce da kanta ta
ware mun kayan da Ishak yayi mana.
Kaya ne sosai ba wai masu dumbin
yawa ba, amma dai masu daraja ne kwarai
baran ma na jaririn wanda tamfar ba a
kasar nan aka yi sayayyar ba.
Ta bangaren gidanmu ma babu laifi ga
kuma alherin da na samu wurin mutane,
Momin Hindu ma ta yi wa Abulkhairi
sayayya ma kyau.
Zaman da nake yi da Yaya ba karamin
dadi yake yi mun ba, don kuwa 'tuni na
11
manta da irin zaman Kadaicin da na ke yi
da Ishak.
Duk da dai yanzu shima ya daina yin
dare Sannan duk da jarirantakar Baba
tunda shi abinda yake kiranshi kenan, yana
daukanshi ya kwanta da shi a dakinshi.
Ko kuma idan ya ji shi yana kuka ko
wani rikici za ka ga yana zaryar tambayar
abinda ke damunshi ko da dai ba dani yake
yi ba, hakan yana yi mun dadi a raina.
Da sassafe Yaya take juye mun ruwan
wanka wanda nake yi da tawul kafin na
gama na fito kuwa ta yi wa Abulkhairi.
Muna gama karyawa zata fara shirin
dora mana abincin rana idan kuwa ta gama
aikace-aikacenta to zama muke yi muna
kallon mu muna kuma hira.
Ga ta da kirki da raha da kuma saukin
kai, abin ya kan daure mun kai har nake
tunanin a raina tamfar ba ciki daya suka
fito da Ishak ba.
12
Shi ma idan ya dawo don kuwa yanzu
baya dadewa saboda yana zama hira da
Yayarshi, to sai ya kai karfe goma basu
kwanta ba suna hirar yan uwa da kumna
wasu al'amuransu can.
Zaman jegon da nayi mai cike da
nutsuwa da kwanciyar hankali shi ne yasa
kafin muyi kwanaki arba'in mun yi
bumbum gwanin sha'awa.
Babu abinda a yanzu nake tunawa
hankalina ya tashi irin na tuna watarana
dole Yaya ta tafi, hakan ne yasa muna hira
nayi nufin gwada yi mata tayin zama.
Ta kalle ni tayi murmushi ta ce, "Haba
Hauwa'u, koda ba ni da miji ai akwai
harkoki da nake yi a can na sana'o'i, ga
kuma yara."
Na ce, Yaya ai sun girma. Ta ce, Eh to
sun girma amma Rukayya fa? Na ce
wacece Rukayya? Ta ce, "A'a ba ki san
Rukayyar ba kuma yau? Yarinyar Isiyaku
mana.
13
Abin kawai sai ya dibibice mun har na
rasa waye ma Isiyaku. Ita kuwa maganarta
ta ci gaba da yi wacce ko fahimta bana yi
saboda ganewan da nayi Ishak take nufi.
Ai tun da uwarta ta dawo da ita tana
shan nono watanninta goma ta ajiyeta tare
da dan uwanta sai kawai naje na debo su
na zo nake rike da su.
Ba karamar dauriya nayi ba lokacin da
na cewa Yaya to amma Yaya ita me yasa
tayi hakan?
Ta ce, To halin su na yara mana daga
ita har shi din wanda rashin hakuri yasa
suka yi rabuwar da bata dace ba.
Ai shi Isiyaku ma naga ya canza gaba
daya yanzu kamar ba shi ba, duk wasu
abubuwan da yake yi a da can ya daina su.
Don ko matar da ya sake aura bayan
uwar su Rukayya ai bata zauna ba don ita
kam ma ai bata haihu da shi ba.
Ke dai kiyi hakuri da abin da za kigani
Wanda ba zai yi miki dadi ba, don shi
14
aure ba ka samun shi yadda kayi zaton
shi."
Maganar da Y aya tayi ya haifar mun da
wani abu a cikin raina mai ciwon gaske.
Bai taba gaya mun zancen auren da yayi
har guda biyu ba da kuma 'ya'ya.
Menene nufinshi nayin hakan? Yana
tunanin wataran ba zan sani ba ne ko kuwa
nima bal shirya zama da ni zuwa ranar da
zan sani ba ne?
Abinda ya tsaya mun a rai kenan. Babu
wata mata da zata iya zama da Ishak idan
har ba hakurinta ne ya kai inda ya kai ba.
Mace maras hakuri kuwa to babu inda
aurenta zai kai da Ishak. Babu ko tantama
abubuwan da yake yi ne sura ga ba za su
lamunta ba.
Kenan halin shi ne ba kuma zai daina
ba.Tunda ai an ce hali zanen dutse.
Taimako daya zan yiwa kaina shine na
tsaya tsayin daka na ga na koma
15
Makaranta kamar yadda tun farko va
alkawarta.
Gaba daya hirar ta daina mun dadi don
haka sallama nayi wa Yaya na shiga daki
na kwanta ba don nayi barci ba.
Don kuwa wane ni! Ina jin dawowarshi
ko motsawa ban yi ba ballantana naje yi
mishi sannu. Yau sun kai sha daya suna
hirarsu ina jinsu.
Sai a yanzu ne na gane ai dama can idan
suna irin wadannan hirarrakin suna yawan
ambaton sunan Rukayya da Anas da alama
shi ne babban. Ban san lokacin da barci ya
dauke ni ba.
Da safe kuwa da na tashi bin Ishak da
kallo na rinka yi ina kara jinjina hali irin
nashi.
Shiri sosai muka wayi gari yau muna yi
saboda gobe ne zamu yi fitan arba'in.
Yaya ce da kanta ta bada lissafin abinda za
a siyo mata na yin sadaka.
16
Tayi
funkasau
da
fanke.
Ta
bi
makwabta
gaba
daya
ta
rarraba
nima
ta
bayar
da
na
gidanmu
aka
kai.
Washegari
kuwa
ta
kama
Asabar
kwalliya
sosai
nayi
ta
burgewa
da
nufin
Zuwa
gidanmu
sai
Yaya
ta
ce
a'a
ba
haka
ake
yi
ba
nabi
makwabtana
mu
gaisa
saboda
hidimar
da
suka
yi
suma
suji
dadi.
Ina
kallon
Ishak
in
ba
don
ban
taba
jin
yayi
musu
da
Yaya
na
tabbata
da
ya
hana,
don
kuwa
tana
fada
naga
yanayin
fuskarshi
ta
canza.
Yana
zaune
rike
da
Abulkhairi
a
hannunshi
wanda
ya
zama
tamfar
dan
wata
uku
ba
shi
da
niyyar
miko
mun
shi,
ni
kuma
ban
ce
ba
ni
shi
ba,
na
gaji
da
jira
na
kama
hanyar
fita
tare
da
yi
ma
Yaya
sai
na
dawo.
Ta
ce,Yau
ji
mun
yarinya
za
ki
tafi
ne
ki
bar
yaron
a
gida
ki
kai
musu
kanki?
Na
dawo
da
baya
ta
kalle
shi.
17
"To kai kuma bata shi mana. Ya miko
mun yaron na kara gyara mishi ruhuwa na
juya zan fita ya ce Ke zo nan. Na dawo
na ce, "Ga ni."
"Tafi ki cire gyalen nan ki dauko hijab
na ce, "To". Har da na dauko hijabin ma
abin bai yi mishi ba sai da ya ce na goya
yaron duk kuwa da shi ma yasan a iyakar
unguwarmu zan tsaya, ban ki ba nayi
yadda yace.
Gidansu Hindu na fara shiga muma
sosai Momi tayi yadda dama can take yi
mun. Tasa hannu ta karbi Abulkhairi tana
rike dashi tana yaba yaron.
Ni dai duk kunyar Momi ta baibaye m,
ko nuna mun alamar ta san abin da Ishak
ya yi musu bata yi.
Na ce, Momi ina Hindu? Ta ce, Tana
wanka yanzu.zata fito. Muna zaune kuwa
sai gata, tsalle tayi ta rungume ni Maman
Abulkhairi!
18
Na ture ta na ce, Ban son wulakanci,
Momi ta ce, A to gaya mata dai mara
kunya. Ta karbi yaron ta zuba mishi ido
can ta ce, Gaskiya Momi mu ma ta karo
mana baby dubi yaron nan kamar na sace.
Hindu ce ta ce, na jirata ta shirya ta raka
ni gidajen da za ni, har cikin raina hakan
yayi mun dadi, don kuwa wasu da yawa
ban ma san su ba.
Muka fito daga dakin Momi ta miko
mun leda mai shake da turaruka na dakin
da na jiki da kuma magunguna ta ce Hindu
ta rike mun.
Godiya sosai nayi mata muka fito, mun
fito kofar gida kenan sai kawai muka yi
ido hudu da Ishak yana tsaye a kofar
gidanmu ya zuba hannayea aljihun
wandon jeans din da yake sanye da shi.
Kamar yadda na dake haka Hindu ma
muka wuce muka shiga wani gidan.
19
Alheri sosai 'yan unguwar mu suka yi
mun na kuma kudura a raina ba zan sake
zama ba na mu'amalla da su ba.
A kofar gida Hindu ta tsaya ta miko
mun Abulkhairi alamar ba za ta shiga
gidanmu ba.
Ni ma ban ce ta shiga ba, nayi mata
godiya na kawo alheri cikin wanda na
samu na bata ta ki karba nayi rantsuwa na
ce ai sai ta karba, hakan ne yasa ta karba.
Na shigo gida Ishak yana zaune a kan
kujera one sitter Yaya bata dakin alamar
tana kicin ko ta shiga bandaki.
Ban ce mishi komai ba nayi wucewata
daki. Na ajiye kayan da ke hannuna na
kwance goyon Abulkhairi na ajiye shi a
kan gado kenan na juyo na ganshi tsaye a
kaina.
Yanayin shi yasa ni ja da baya. "Ban ce
miki bana so kina mu'amalla da wadannan
mutanen ba iye? Keta dokata da ki ka yi
20
bata ishe ki ba shi ne ki ka je ki ka bata
dana tana goyawa?"
Bude baki nayi da nufin yin magana
kawai Ishak ya dauke ni da marin da sai
da na kifa a kan dressing mirrow
Ihuna da Yaya taji ne yasa ta tahowa da
sauri. Ta kama salati ganin da tayi har
bakina ya fashe, kuka nake yi sosai itama
Yayan haka tana cewa.
"Ashe baka bari ba Isiyaku, to yaushe
kuma? lye na ce maka sai yaushe kenan?
Wannan yarınya menene aibunta'?
Ya tsaya zai fara yi mata bayani ta
dakatar dashi ta ce, Bana son ji. Na kuma
fahimci zamana a gidanka ne ya isheka
dama kuma nayi abinda ya kawo ni
magana ta kare."
Wucewa Ishak ya yi ya fita ni kuma
naje na wanke bakina da ke ta fitar da jini
saboda buguwar da nayi kan madubi
hakan har idona na gefen d na fadi ya tara
jini.
21
Ita kuwa har yanzu Yaya kuka take yi
saboda cin zali yarinya na jego? Wane irin
hali ne wannan?
Har da rokon Yaya da na zauna nayi ta
yi bata fasa shirin ta ba. Ta rantse akan
gobe zata tafi. Ba dukana da Ishak yayi ba
ne damuwata, tafiyar Yaya ne.
Don kuwa nasan tana barin gidan zamu
koma zamanmu na baya. Na durkusa a
gabanta na ce "Yaya don Allah kiyi hakuri
ki zauna ko sati biyu ki kara kin ji?"
Ta zuba mun ido. Zuwa can ta ce
"Aiya! Abinda dan uwana yayi miki bai
6ata miki rai ba, don na dan faranta mata
sai na ce eh Yaya."
Ta ce, Ikon Allah kenan yanayin wanda
yafi haka. Kin ga kuwa ba zan tsaya sai an
yi kafin na tafi ba ko? Babu yadda na iya
da ita don haka na shiga daki na dauko