Author : Takori Category : Complete Novels
Guinea duba ta da bata da lafiya.
Haka Yayar shi Sayluba ma ya je Tahoa sabida sada zumunci da ita.
A wannan hutun ne aka kawo mata Fajur, hutu, zata zauna har sai ta haihu, a bakin Fajur ta ji wani labari da ya gigitata, wai Mamma Jalan ma cikin ta ya tsufa.
A gigice Amani ta kira Mamma tana son tabbbatar da abinda ta ji daga kanwar tata, Haj. Jalan ta rasa inda zata tsoma ran ta don kunya sai ta hau Amani da fada tana cewa ni abokiyar wasanki ce ko Amani? Don kin ga tsayin mu daya girman mu daya ko? Shikyasa kika maida ni saar ki. A shekaru na ai na wuce haihuwa yanzu, ki zauna Fajur tana gaya miki abinda bazai yiwu ba.
Ita kuwa Fajur tayi rantsuwa ta maya cewa cikin Mamma yanzu yafi nata girma, kuma kusan kullum sai ta je asibiti awo.
Amani sai ta kira Alhaji da kan sa.
Daddy da gaske ne? mamma zata baima su Fajur kanne?
Hawayen farin ciki suka tsirgowa Alhaji Usman Faskari na godiya ga Allah. Ya ce da gaske ne Tafisu, da gaske ne!
Uwa sai ta saka kuka don dadi.
A halin farin ciki dana bakin ciki duka, Uwar su Alhaji ta fi gane ta yi kuka.
Amani har katon Sa da rago tasa aka kayar, ta rabar da shi sadaqa ga bayin gidan ta, tana mai taya Daddyn ta godiya ga Allah, da adduar ita da Mamma Jalan duka, Allah ya sauke su lafiya cikin koshin lafiya.
**** **** ****
EPILOGUE