Kundin Kaddarata Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Huguma Category :  Complete Novels

Chapter   115 / 120

342K to 345K   out of 359.7K words

tunaninta,naquda take haiqan saidai haihuwa tawi zuwa,tun biyu na dare har gari ya waye haihuwa bata zo ba,daga gefan almustaphan ya kira wayarta yafi a qirga saidai ba amsa,saboda sun baro wayar a gida,ya kira su'ad tace bata sani ba,bata gama bashi cikakkiyar amsa ba ma ta kashe wayarta,yayita kira switchoff,take hankalinsa ya tashi,sai sannan yayi dana sanin me yasa ko baba uwani baisa an kawo ba?,kai tsaye ya kira asibitin nan suka shaida masa tana nan tun daren jiya,ranshi ya baci hankalinsa ya tashi,fada ya hauyi kan me yasa basu shaida masa ba?,sannan ya za'ayi su barta tun jiya har yanzu wayewar gari tana naquda har ta kusa cinye awanni da aqa'idar likitoci ba'a so ta gama su bata haihu ba,haquri suka shiga bashi,bai sauraresu ba ya katse layin ya soma tattara ya nasa ya nasa ba tare da ya kammala abinda ya kaishi ba,hankalinsa gaba daya yayo dubai,jinsa yake kaman yayi tsuntsuwa ya ganshi a can.

        Qarfe hudu na yamma ya iso dubai,kai tsaye ya yiwa drivan umarni ya wuce da shi asibitin,kai tsaye ya wuce dakin da take,kwance take saman gadon,kallo daya zaka mata kasan cewa ta jigata qwarai,duk sanyin dake dakin bai hanata gumi ba,muryarshi kawai taji ta daga kanta taba dubanshi,tuni ya ajjiye jakar dake hannunsa ya qarasa inda take,nurses din dake dakin suka fice daya bayan daya,tafin hannunta ya laluba ya sanya nashi hannun ciki,hannunsa saman kanta yana shafawa a hankali,baki daya zuciyarsa ta karye
"Baby......sannu baby" ya fada idanunsa cikin nata,ga mamakinsa murmushi ta sakar masa a wahalce
"Ka dawo?"
"Eh...." Maganar tasa ta katse sanda ta furta
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil!" Cikin madaukakin sauti ta soma murqususu cikin matsanancin ciwon da ya taso gadan gadan,tamkar dama jiran zuwan almustaphan yake,yanayin yadda yaga tanayi ya sanyashi sake dubata da kanshi,nan ya tabbatar haihuwar ce,nurses din da suka fita ya kirawo don su taimaka masa,din bashi da qwarin gwiwar da zai iya karbar haihuwar shi kadai,yana riqe da ita yana gaya mata addu'o'i tana maimaitawa cikin wahala,a qalla mintuna goma kafin jaririyar ta samu isowa duniya,kukanta ya karade ilahirin dakin baki daya har zuwa waje,basu gama tantance komai ba ta sake wani yunqurin,wani sabon kukan ya sake karade dakin suka hadu suka cika ilahirin dakin zuwa harabar dakunan da kukansu,nurses din ne suka dauke yaran yayin da baki daya hankalinsa ya raja'a a kanta,gumin da ya mata sharkaf ya soma goge mata yana jero mata sannu babu qaqqautawa,dubanshi take yadda ya rude baki daya,kukan yaran na yawo cikin kwanyarta,tasbihi take wa ubangijin talikai,yau gata a karo na biyu ta sake samun diyoyi,diyoyin da suka fito daga tsatsonta,kasa dauke idanunata tayi daga shiyyar da yaran suke sankda nurses suka gama rabasu,kukansu suke sosai suna wutsil wutsil da qafafu da hannyensu,sakayau a yanzu take jinta kamar sun fita da duk wani ciwo dake damunta.

       Cikin mintuna qalilan nurses din suka soma gyara yaran,shi kuma ya gyara ta da kanshi a wani daki daban,komai ya kammala,aka maidata zuwa wani dakin ita da yaran baki daya.

        Zaune take saman gadon sosai tana jingine da bango,murmushi ne sosai kan fuskarta wanda har sai da ya sanya haqoranta bayyana,idanunta taf da qwalla sanda almustapha yake nufota dauke da daya daga cikin jariran wadda ke nannade cikin wasu irin kayan sanyi masu azabar kyau set da abun daukansu,gabanta ya qaraso shima idanunsa cike da qwalla yana dubanta tare da duban babyn,miqa mata ita yayi sai ta dauke idanunta qwallar data cika mata idanu tana gangaro mata saidai har yau murmushin dake kan fuskarta bai bace ba,da hanzari ua sake matsarta ya kama hannunta yana matsawa cikin rauni da rawar muryar da bata taba ji daga gareshi ba yace
"Kada kice zaki ji kunya babe....karbi diyarki ki gani in dauko miki dayar....duniyarmu ce baby duniyarmu....daga ni sai ke sai su karbi ki gani", ya qarashe maganar yana dora mata yarinyar saman cinyarta,tuni ta sanya hannu ta karbeta,cikin sakanni qalilan qaunar data ke musu taji ta soma ninkuwa cikin zuciyarta,sak jinin gidan baba prof,kana dubanta ko makaho ya shafa yasan jikar mutanen gwambe ce,photocopy na almustapha,sake komawa yayi ya dauko dayar ya dawo saman gadon ya zauna sosai kusa da ita yana bude mata fuskarta
" kalli usaina baby.....ba wadda ta miki kara?"ya fafa yana sakin dariya wadda ke qunshe da zallar farinciki,jinsa yake yau kaf duniya babu dan adam din da ya kaishi farinciki,ba wanda kuma ya kaishi sa'ar zuwa duniya,itakam murmushi kawai take bakinta ya gaza furta komai,Allah kenan,buwayi gagara misali,cikin rayuwarta kaf bata taba kawowa kanta haihuwa bama bare kuma aje ga haihuwar 'yan biyu,dai gashi a yau,Allah yayi mata kyautar da bata taba hasashenta ba,haqiqa Allah mai tsananin karamci ne,sosai almustaphan ya dinga sumbatu wanda tasan na tsantsar farinciki ne tana dubanshi tana dariya,ita din ma jinta take saman wata duniya ta farinciki tana yawo,ta kasa dauke idanunta daga yaram,ba don yaranta bane,amma zata iya cewa bata taba ganin jarirai masu ban sha'awa irinsu ba,sam ya mance da ya wanu kira gida ya fada sai data tuna mishi,a sannan ne ya dauko wayarshi,ummi ce mutum ta farko da ya soma kira,danda yake gaya mata tsaye ta miqe tana kabbara,bata qarasa jin zancan ba ta rankaya falon baba,saidai kash kafin ta isa tuni anty maamaa ta rigata kai labarin,wanda ta jishi je sanda take shigowa wajen ummi,a take baban ya mata kyautar kudi masu tsoka,ta dinga ma ummi dariya tana cewa saidai a tara a gaba,itama dariyan ta dinga tace rabonki ne,duk yadda baban yaso sakaya farincikinsa abun yaci tura,haka shima ya dauki waya ya dinga kiran abokai da 'yan uwa yana sanar musu,cikin lokaci qanqani labarin haihuwar ya karade kowanne sakaye,tsakanin baba da malam sai aka rasa wanda za'a yiwa murna,amira kuwa da anty dije kukan farinciki suka sanya,ta dinga kiran almustaphan tana roqonshi zata taho yace sam,sai ta saka kuka,tana so ace cikin dangi itace mutum ta farko data fara daukan yaran,abu daya ne ya saka mata haquri hoton yaran da ya dauka ya tura mata ta email adress dinta,don shi baya watsapp.

      Da kanshi ua sallami matarshi bayan ya tabbatar da cewa komai lafiya suka kama hanya zuwa gida,yana bayan motar shi da ita,baki daya yaran na hannunshi ya hana mata ko daya,ji yake idan ya rufe idanu zaiga kamar mafarki kamar almara,ashe duk arziqinka duk dukiyarka,duk farincikin da kake taqama kana ciki bai gama kammaluwa ba matuqar baka samu diyoyin da zaka alaqanta da jininka ba,ashe zallar farincikin da zata fadeshi sai randa ka ganka dauke da zuriya taka ta kanka.

        Daidai sanda suka nufi gidan su'ad na tsaye tsakar dakinta tana amsawa wayar da suke da mahaifiyarta
"Nifa gaskiya su'ad na soma sarewa,kinga tsantsar farinciki da doki da professor yake ciki sanda ya kira mahaifinki kamar ranar aka soma haifa masa jikoki,anya kuwa su'ad ba muyi kuskure ba?,ina da yaqinin Allah kadai yasan dukiyar da zasu samu su kuma mallaka tun suna qananunsu,wanda dukkan abinda suka samu zai koma fa hannun mahaifiyarsu ne" qatuwar ajiyar zuciya ta saki
"Bama wannan ba momy,wallahi na tabbatar na shiha uku,duk wani soyayya da tattali da adalci da almustapha ke qoqarin gwadamin ina da yaqinin sai ta ragu,tun cikin bai fito duniya ba kinga abinda yake?,ina ga ya fito sannan kuma twince mommy?,shi yasa nake tunani anya ba zamu sake plan ba?,na nemi dalilin haihuwa nima ko don na sake janyo hankalinshi zuwa gareni baki daya?"
"Dqlla can rufewa mutane baki,ke ta soyayyarsa ma kadai kike,soyayyar vanza,ana miki maganar kudi abokan tafiya qare magana,so nake fa ki zama cikin jerin attajiran da duniya ke lissafinsu kaman yadda a yanzu mijin naki yake,ke kadai ce fa 'yata ke daya na mallaka,saboda haka ina so naga kinyi shaharar da ko d'a namijin da yayi shekara arba'in yana gwagwarmaya baiyita ba"
"To yanzu ya za'a yi momy?"
"Cikin satin nan kisan yadda zakiyi kizo nan mu warwareta"
"An gama" ta fada tana katse wayar saboda motsi da taji kaman ana shigowa,a hankali ta tako ta fito zuwa falon,almustapha ne riqe da baby daya,wata mace mawociyarsu 'yar asalin qasar saudiyya dauke da dayan,fuskarta a washe tana tana yaba kyawu da girman yaran cikin harshen larabci,duk da bata fahimtar me take fada amma daga yanayin matar tasan tana yabawa ne da yadda yaran suke,idanu ta zuba musu tana karantar fuskar almustapha wanda bata san da dawowarshi ba saibyanzu,tunda sukayi magana ya tambayeta sumayya tace bata sani ba bai kuma kira ba hakanan bata bi ta kanshi ha itama,iya tsahon zamanta da shi bata taba ganinshi cikin wannan hali na matsanancin farinciki ba, saidai ba wanda ya kula da ita a cikinsu saboda tana daga bayan labule ne har suka shige.

      Yana fitowa daga dakin ya lura da ita,fuskarshi sake yake dubanta,bacin rai da take dannewa ya taso yafi qarfinta,sai kawai kuka ya qwace mata,sai ta juya da gudu gudu ta koma ciki,tausayinta ne ya sauko masa lokaci guda,yana tunanin rashin samun tata haihuwar shi ya motsa mata,wanda hakan zai iya faruwa ga kowacce mace,kowanne lokaci kuma yanayin kan iya motsuwa cikin zuciyarki har ki kasa controlling din kanki,sai ya rufa mata baya,samunta yayi kuwa zaune saman kujera tana buge buge da hannunta,dama ace dama ace ce fal cikin zuciyarta,zata so a ce itace ta samu wannan yaran ba sumayya ba,wai shin me ya hanata tsayawa ko guda daya ta samu ne?,ba shakka tana ji a jikinta lokaci yayi da zata tashi ta dawowa da kanta dama ta samun haihuwa a gareta,a tausashe ya zauna gefanta yana riqeta,baison idan wani abu ya sameta ta dinga irin wannan acting din dake nuna zallar rashin yarda da qaddara,cikin taushi ya soma ce mata
"Am sorry dear....ba kuka zakiyi ba,addu'a zakiyi Allah ya kawo mana,komai a duniya yana da lokaci sannan komai yai farko yana da qarshe banda ikon Allah,matuqar kina da rabo ta babu makawa sai kin haifa kema"
"Ko bani da rabo wallahi sai na yishi,sai na haihu nima" tsauri maganar tayi masa,haqiqa ba qaramin illa da tasiri dabi'un yahudawa marasa tauhidi suka yiwa su'ad din ha,saidai yana da burin sosai wajen ganin ta daidaitu,duk da hakan ma alhamdulillah,ya rabata da shigar banza ya sata tsaida sallah,koda kuwa zata yita ne bayan wucewar lokacinta
"Subhanallah,kiyi istigfari,babu bawan da yafi qarfin QADDARA,saidai addu'a na maida MUMMUNAR QADDARA ta koma zuwa KYAKKYAWA,ki roqi Allah sai ya kawo komai a sauqaqe,ba wayonki ko dabararki ba,ita kanta ada can an taba kiranta juya,an fidda mata rai zata haihu,amma a yanzu gashi ke ya faru?" Cikin hikima yake gaya kata kalaman kwantar da hankali,saidai jinsu take kaman busat sarewq,abu daya ne ya dan kwantar mata da hankali,kasancewa da yayi tare da ita duk da ba ranarta bace,da kuma yadda yake lallashinta,saidai ba shakka cikin satin nan zata san yadda zata wuce america don bazata juri rasa cika burin data qudurtawa ranta ba.

      Maqota biyu da suke da su wadanda ba yarenta ba saidai 'yan uwantaka ta muslunci da tsananin kirki da suke da shi,wanda batasan suna da shi ba sai yanzun da haihuwar 'yan biyu dake da farinjini suka sa tasan hakan,suna kula da ita sosai,akai akai suke leqota da kalar abinci da kulawa da sukewa maijego,akwai mai tayata zama guda daya daya samu wanda ta kasance mutuwar qasar ghana ce,zaman sana'a yasa take zaune a qasar,sai ta kasancewa sumayya tamkar yar uwa,sosai matar ke kula da ita,tana da qoqari da zafin nama qwarai,babu abinda sumayyan ta nema ta rasa,hatta da shi mai gayya mai aikin idan ya fita sha daya,biyat na yammaci ya dawo gida,koda yashe burinsa ya ganshi tare da su,a haka ma idanun su'ad yasa ya dan rage wasu abubuwa tare da danne daukinsa,don har ga Allah tausayinta yake ji,yasan cewa rashin haihuwa babbar damuwa ce dakan iya zamewa wasu matan ciwo cikin zukatansu,abinda bai sani ba shine ta soma girbar abinda ta shuka ne ba tare da shi karan kanshi ya sani ba,wani tsananin son hauhuwa ne ya mata mugun kamu cikin kwanakin da basu haza hudu ba,sosai walwala da kuzarinta ya ragu,kishin yaran da uwarsu baki daya ya gallabeta,ko sau daya tak bata taba kusantar dakin sumayya ba bare tace zata ga yaran,wani abu ke tokare mata wuya duk sanda taji sautin kukansu,ji take kaman ta kaudasu ko ta samu hutu.

       Daga daya bangaren kuma tuni ummi ta gama duk wani shirinta na zuwan yaran da mamarsu,kwana biyu taji shiru hakan ne yasa ta tuntubeshi,sai yace 'yar matsala ce aka samu wajen siyan ticket,tuni ta baroshi,wanne matsala ce za'a samu wajen siyan ticket kawai?,shi kansa yasan qaryar bata hadu ba saboda ba sabonshi bace,ko kadan ne kawai baya son su tafi su barshi,baya jin zaman garin zai yiwu gareshi idan suka tafi din,shi a son ranshi duk maison zuwa cikin gidan nasu zai siya masa ticket,wanda bai da visa zai masa suzo suga yaran,sam bazaiyiwu ba ummi ta gaya masa,su a wajensu tamkar haihuwar fari ne,saboda haka dole ya kawo 'yar mutane a kula da ita sosai,sannan itama tana da yan uwa tana son zama cikinsu ai,shikam baiga wacce kulawa akeson bata ba bayan wanda take samu nan daga wajensa,yana kallonta take saka towel cikin tafasasheshen ruwa ta gasa kanta sosai,ta fito taci abinciccika masu gina jiki,ga magungunan da yasa zasuyi mata matuqar amfani a jiki da take sha,hakan ya sanya hatta da ruwan nono ta samu wadatacce,kana kallonsu zaka san kulawa kam sun sameta,daga ita har yaran kai kace sunfi kwanaki hudu da haihuwar,warshe dai haquri ya baiwa ummi yace suna tahowa.

       Sai ana ya gobe zasu cika kwanaki bakwai sannan ya siya musu ticket har da shi da su'ad zasu tafi,dakin su'ad ya fara zuwa,ya taddata zaune tana latse latsen waya,sam sumayya bata gaya mishi bata taba zuwa taga yaran ba,shima kuma bai taba kawo ba zata shiga din ba,gefanta ya samu ya zauna yana fuskantar fuskarshi a sake sosai,kai ta daga ta dubeshi,as usal bata iya sannu da zuwa ba ko gaisuwa
"Baki gajiya da danna waya?" Ya tambaya yana daukar remote ya rage saitin kidan dake tashi a tv
"Idan ban danna ba me kake so nayi?" Ta tambayeshi cikin yanayin bacin rai,idanu ya zuba mata yana karantar yanayinta,sai kuma ya hadiye ya dauke kanshi daga fuskarta yaba bata amsa
"Karatun qur'ani,istigfari da sauransu"
"K'nnnnn" ta ce a taqaice,tun daga ranar zuciyarta da shaidan suke gaya mata ta gama burge almustapha fa,yanzu ba sonta yake ba ba kuma qaunarta yake ba,yaranshi da uwarsu su kadai yake so da qauna,bayan babu wani abu da yayi mata wanda ke nuna haman,illa ma lallashinta da yake saboda yana tunanin rashin samun nata yaran na kanta ke damunta
"Gobe zamu shiga nigeria,su ummi sun matsa sai mun dawo a yi suna a can kowa yaga yara"qafafunta ta miqe ranta na baci
"wannan ku ta shafa sai kun dawo" idanunsa ya qanqance yana dubanta,wati mai hali bai fasa halinsa,duk yadda yake tattali da rarrashinta wato shi din banza ne baisan ciwon kanshi ba?
"Kamar yaya fa?" Ta tambayeta yana son qarin bayani
"Ai suma su ummin tsabar gulma ce,babu gidan uban da zani,wato nake inje aji dadin nuna ni gani ban haihu ba wata tazo bayan bayana ta haihu ko?,to bazanje ba,dama an dade ana ruwa qasa na tsotsewa,muna fukin auren ma duk ha sune sila ba sabida kai an tsaneka ba'a sonka" cikin tsananin bacin rai ya daka mata tsawa,nunata yake da yatsa cikin bacin rai
"Hey idiot.....Kar ki soma kuskuren fadin maganar banza kan mahaifana,ki kintsa bakinki kada furucinka ya jawo miki nadama......iyayena sun fiye komai da komai da na mallaka nake da shi,su din wasu abubuwane masu daraja da babu kamarsu,kudi ko qarfin iko basu isa su baka su ba.....ban gaya miki zamu nijeria ba wai don ina neman shawararki ba,umarni nake baki kaman yadda wadanda suka isa da ni suka bani umarni nabi,kema dole kibi umarni na don na isa da ke" ya miqe yana niyyar ficewa ranshi a bace
"To wallahi ba inda zani daga nan nima gidanmu zan wuce ai ina da gidan uba...." Waiwayowa yayi yana mata wani kallo daya sanyata rusuna ba tare data shirya ba
"Really?,....ok,indai haka ne idan kinje kada ki sake ki dawomin gida kinji ko?,ruwanki kije nigeria ruwanki kije ameria amma ki zauna acan,kada qafarki ta dawo gidan muhammad almustapha" yana kaiwa nan ya wuce yana mai buga qofar cikin fushi,kanta ta dafe,tabbas bata da wata mafita,zai iya aikata dukkan abinda yace din,saidai ta gama rayawa ranta abinda zatayi,zuwa gida babu fashi.

          Da sallama bakinsa ya shiga dakin sanda take gaban sif tana fidda kayansu tana shiryawa cikin akwati,yaran na kwance cikin gadonsu suna bacci hankalinsu kwance,cukin tsafta da qamshi,a qunshe suke cikin kayan baby masu taushi pink,yanayin muryarshi kawai taji ta saki abinda take ta waiwayo tana dubanshi,duk sanda taji muryarshi haka tasan ranshi a bace yake koda yayi yu qurin boye mata,bai dubeta ba har ya isa gaban gadon yaran ya bude dan net din dake matsayin qofa ya zura kanshi,kissing kowannesu yayi yana lumshe idanunshi,qamshinsu da kyan da suka yi suna ratsashi,kaso hamsin cikin dari na bacin ranshi take ya kwaranye,sai da ya gama duddubasu sannan ya sake rufesu,ya waiwayo suka hada idanu da sumayya,kusan tare suka sakarwa juna murmushi,qare mata kallo yake yana takowa inda take tsaye,rigar jikinta ta kamata ta fidda surarta qarara,ga na shanunta fa suka cika sun zauna das jikinta har wani qyalli suke,hankalinshu bai kwanta ba sai da yasanyata cikin jikinsa ya dora hannayenshi saman qirjinta yana yawo da shi yana lumshe ido
"Me kike a tsaye...ke da na gaya miki bacci nakeso kiyi?" A tausashe tace
"Na gaji noor,kuma gobe zamu wuce kaga dole na hada mana kayan da zamuyi amfani da su ko?" Kai ya kada
"noo,kada mi wahalar da kanki,babu wani abu da zaku dauka a nan,akwai komai can an tanada" mamaki ya kasheta,kada dai ya gaya mata ya sake wata siyayyar ne bayan wadda yayi a nan,bakinta ta bude da niyyar magana,saidai ba bata dama ba ya hade bakin nasu waje daya ya soma aika mata da saqo.

      Da qyar ta qwaci kanta gajin yana yunqurin wuce makadi da rawa tana maida numfashi,da baya ta soma ja ya dinga binta idanunsa kafe a nata yana dariya
"Me na tsorata haka babe?"Kai ta langabe
"jego fa nake noor...ni

115 / 120