[11/20/2023, 11:24 AM] Jiddarh Aliyu 2: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love Story) Na JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 001. *RUBUTUN ƳAN TAGWAYE BIYAR KARO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* *KIN TABBATA KIN CIKA MACE? BABBAR MACE DAKE JI DA KANTA? KINA CIKIN MATAN DA SUKA SAN KANSU? WANDA SUKA SAN MUTUNCI DA DARAJAR KANSU? KO KUWA KEMA KINA CIKI SAHUN SU O’O?* *INA KUKE MANYAN MATA? WAƊANDA SUKA SHIRYA DAN GYARA JIKINSU? AURANSU? DA KUMA FARINCIKINSU?” *KUYI MAZA KU GARZAYA GUN FITACIYGA KUMA INGANTACIYAR MAI MAGANIN MATA DA MAZA DAN AMSAR NAKU KU GYARA DA KANKU WATO MEERAH HERBS WACCE TAI FICE GUN KAWO MUKU INGANTATTUN MAGUNGUNA BA TARE DA ALGUS BA.* Mun gwada mun gani 💯 Mun gani mun shaida 💯 Anyi mun gani 💯 MAGANIN SANYI MAGANIN NONO MAGANIN HIPS MAGANIN SLIMMING MAGANIN NANKARWA GYARAN AMARE GYARAN MAIJEGO MALLAKAR MIJI KO MATA SUBULU DA SCRUB MAYUKA NA GYARAN JIKI TURAREN WUTA MATSI MAGANIN NI'IMA MAGANIN TSUMI INFECTION FLUSHER DA DAI SAURANSU…..Uwar gida, Amarya, Budurwa, Saurayi, Ango, Mai gida? Duk mai kuke jira? Kuyi maza ku garzaya Meerah herbs maganin dake ingantace 💯 08142800199 07068558096 _________________________ Taƙure take can ƙarshen gado ta sunne kanta tsakanin guiwayoyinta biyu. Wani irin kuka take yi wanda sautinsa baya fita sosai a dalili dusashewa da muryata tayi. Jikinta lulluɓe da lafayya pink and white colour ƙafafuwanta ɗauke da lalle na salatif maroon color sai ɗan baƙi kaɗan da aka bi gefe da gefen ƙafafuwan nata dashi. Bata taɓa tsammani ko hasashe ƙaddarar ta za ta kawo ta izuwa wannan mataki ba. Ko kuma matsayi da yau ta riske kanta a ciki. Abu ne da ta kasa yarda da faruwarsa, take ganinsa tamkar a mafalkinta, ga wasu tarin tambayoyi da ke ta shawagi a cikin ƙwaƙwalwarta. Shin miyasa mahaifinta ya kasa yarda da cewa wannan aure da ya zama sila kuma jagora haɓakawa ba abu mai yiwuwa bane? Ta rantse ta kuma sake maida rantsuwa koda sama da ƙasa za ta haɗe ba za ta taɓa karɓa AB (Abba Bashir )a matsayin mijin aurenta ba. Wannan ai abin kunya ne babba a gareta kai har ma dashi kansa AB ɗin. Ta ya za su tashi a gida ɗaya uba ɗaya sannan kuma uwa ɗaya ce ta raine su, ta tarbiyyarta dasu da kalar tarbiyya ɗaya sai kawai ta wayi gari ta tsinci kanta a gidansa kuma a matsayin matar aurensa. Haba Wannan kwamacala ba da ita za a yi ta ba. Dole ta nemowa kanta mafita. Ko za ta iya haƙura da komai ban da zama da AB a matsayin mijinta. Aure tsakani ta dashi ya haramta duk da addini Musulunci bai haramta ba amma ita ta haramtawa kanta shi. Tun sanda ƙanwar mahaifinta ta shigo da ita wannan gida kuma cikin wannan ɗaki ta zaunar da ta ƙara yi mata nasiha ta fita, tawagar ƙawayeta 'yan rakkiyar amarya ke bata baki amma kuma tamkar suna zugata ne. Ita kaɗai za ta iya misalta adadin raɗaɗin da take ji a ƙahon zuciyarta. "Haba Sady-B(Sadiya Bashir)wannan kukan naki ya yi yawa tun gida ki ke ta wannan kukan, da kuka zai iya sauya miki ƙaddararki da ya sauya ta daga safe zuwa dare nan. Sai dai kash! bakin alƙalami ya riga da ya bushe dole ki rungume ƙaddararki. AB shine mijin da ƙaddararki ta zaɓar miki. Ɗaya daga cikin ƙawaye nata ta faɗa da sigar son ta rarrashe ta ko Allah zai sa ta daina wannan kukan na fitar hankali. "Ba za ki taɓa fahimtar hali da nake ciki ba Maryam Abdallah, taya Daddy yake tunani zan samu farin ciki a gun mutumin da nake masa kallo a matsayin ɗan uwana wanda uba ɗaya ya haife mu. Wallahi-tallahi Daddy ya tafka babban kuskure ya zantar da hukunci cikin fushi ba tare da la'akari da irin abinda fushin nasa zai haifar ba. Ban yarda da wannan aure ba, ba kuma zan taɓa amincewa dashi ba. Idan har Ya Abba yaƙi kawo ƙarshen wannan bahagon aure to ni nan da kaina zan kawo ƙarshensa, ban damu da tsinuwa da Daddy yake ikirarin zai min ba. Har Maryam Abdallah ta buɗe baki da zimmar sake magana suka ji shigowar ango tare da abokansa. Tun sanda suka shigo ɗakin shi da abokansa bai kalli gun da amarya tasa take ba, yana tunani taya zai iya kallon ƙanwarsa Sadiya Bashir a matsayin matar aurensa. Miyasa ƙaddara za ta zo musu ta wannan siga duk da yaso ya danne zuciyarsa ya yiwa Daddynsa biyayya wanda ya kasance duniyarsa, kamar yadda ya saba yi masa a can baya, sai dai shigowar da ya yi yanzu ya kuma hango Sadiya a taƙure sai ya ji wani irin kololon baƙin ciki ya dunƙule masa a maƙoshinsa. Ya yi kuka har sai da hawaye idanuwansa suka ƙafe ya dawo kukan zuci wanda har yanzu yake kan yi. Wannan wacce irin baƙar ƙaddara ce ta yiwa rayuwarsa shigar kutsu. Tabo kafaɗarsa da Al-Ameen ya yi ya dawo dashi daga duniyar nema da lallube da ya afka. Yayin da Al-Ameen ya ci-gaba da faɗin "AB ga ƙanwarka nan Sadiya a yau matsayin ta ya haura wanda kasanta dashi a can baya, kada ku yi la'akari da alaƙar ku ta can baya ku yi duba izuwa da wannan da a yanzu ku ke kai. Dukkanku kusan halaye juna kuma kusan like and dislikes ɗin junanku tun da already kun tashi a karkashin inuwa guda ne, sai kuma gashi Ubangiji masani sirrikan fili da na boye ya sake kawo ku wani mataki na daban wanda ku dukkanku ba ku taɓa tunani riskar kanku a cikinsa ba. Koda kuwa a mafalki ne, tun anan ya kamata kusan cewa ƙudurar Ubangiji tana da yawa sannan shi kaɗai yasan hikimar da yasa aure ya kasance a tsakanin ku. Har Al-Ameen ya dasa aya a zance sa babu wata kalma guda ɗaya kwakwara da AB zai buga ƙirji ya ce ya ji, domin hankalinsa ga baki ɗaya ya ta'allaka ne ga tunani makomar rayuwarsa ta nan gaba, domin duk abunda ya faru dashi kafin zuwan wannan rana shafin vasiline ne a bisa wacce zai tunƙara anan gaba. Kusan kowanne daga cikin abokansa su biyar ba wanda bai tofa albarkacin bakinsa ba, domin sun san ta yadda auren abokin nasu da ƙanwarsa ya kasance abu ne wanda kafin hankali da tunani su karɓe sa za a sha gwagwarmaya. Abdulkarim Safana ne ya rufe musu da addu'a kana abokan ango suka sallame ƙawaye amarya da sallama mai tsoka, daga abokan ango har ƙawaye amarya basu sami damar taɓa barkwanci a tsakaninsu ba kamar yadda aka saba ya yi kawo amarya ɗakinta, a wannan karon su kansu abokan ango da ƙawaye amarya aure ne da ya zo musu very complicated. Bayan AB ya yi musu rakkiya zuwa farfajiyar gida idan suka yi parking motacin su kana ya dawo sai da ya rurrufe kofofi tare da kashe bulbs ɗin dake kunne kana ya wuce ɗakinsa ya yi wanka, ya saka fararen pajamas ƙafarsa sanye da flip flops sai da ya biya ta main parlor ya ɗauki leda da ya baro kan centre table kana ya wuce ɗakin amaryarsa. Bakinsa dauke da sallama ya tura ƙofa yayin da shigowarsa tsakiyar ɗakin ya yi daidai da fitowar Sadiya daga maɓoyarta cikin curtain ƙaifaffiyar wuƙa dake riƙe da hannunta ta dabawa AB da dukkan ƙarfinta a daidai gefen cikinsa, kamar daga sama ya ji shigar wuƙa a cikinsa zaro wuƙar da Sadiya tayi ya haddasa wa AB saki rikitaccen ihu cikin tsanani azaba ya dafe gun da ta caka yayin da jini ya dinga zuba kamar an buɗe famfo. "Ka yi haƙuri Ya Abba banso haka ta kasance tsakanin mu ba sai dai banida wani zaɓi da ya wuce wannan. Na tabbata koda duniya za ta taro akanka ba za ka taɓa warware wannan baƙin auren naka dake kaina ba. A dalili tsanani biyayyar da ka ke yiwa Daddy za ka zaɓi ka dawwama a baƙin ciki, muddin Daddy zai kasance a farin ciki. Ni kuma bani da ƙarfin imani da zan iya irin wannan biyayya taka, kasancewar ina so na rayuwa cikin farin ciki, kamar kowacce mace dake ɗakin aure. Wannan buri nawa tuni ya bi ruwa gani ba zan taɓa samun cikar muradina ba na yanke shawara gara na kashe ka idan yaso nima a kashe ni, a lokaci Daddy zai farga ya gane babban kuskure da ya tafka. Sadiya tayi magana cikin muryar kuka dake bayyanar da irin tsanani baƙin ciki da take ciki, sannu a hankali AB ya sulale ƙasa ya zube guiwayoyinsa kan tiles da kyar ya iya buɗe bakinsa saboda irin raɗaɗi da yake ji cikinsa na masa "Miyasa za ki yi haka Sadiya miyasa ki ka zaɓi wannan gurguwar hanya domin dawo da farin ciki da ki ke hasashen kin rasa?" Ita ma Sadiya zubewa tayi gabansa tana wani irin gunji kuka na fitar hayyaci "Bani da zaɓi ne Ya Abba na gwammace na kare rayuwata a gidan kaso da na rayu da igiyar aurenka. Babu wani babban mugun abu a wurina da yawuce wannan aure naka. Kasa magana Abba ya yi saboda jini da ya soma bugar dashi, a hankali ya kai kwance, har zuwa lokaci Sadiya tana durƙushe a gabansa tana kallo yadda ransa ke fita daga gangar jikinsa, sai kuma wani irin tsoro ya fara shigarta tai sauri jefar da wuƙar hannunta, tayi kansa tana jijjiga shi gami da kiran sunansa "Ya Abba ka tashi dan girman Allah ka tashi kada ka mutu Ya Abba, wayyo Allah na shiga uku na kashe sa Ya Abbaaaaa! Ta ƙarashe magana cikin sauti mai amon gaske. Can kuma ta miƙe ga baki ɗaya ta gama fita hayyacinta ta ɗora hannu aka sai ta kai bango gabas ta dawo na yamma tana gunji kuka. Sai kuma ta nufi wayarta dake kan bedside drawer tayi dialling number best friend ɗinsa Abdulkarim Safana. A lokaci har Abdulkarim ya yi shirin kwanciya bacci sai dai bai kai da yi bacci ba, kira nata ya shigo wayarsa nan take ya ji wani irin mashahurin faduwar gaba jikinsa ya ɗauki rawa ya ji wani kalar sanyi-sanyi yana huda kasusuwan jikinsa, da kyar ya tattaru jarumtarsa ya furta "Hello Sadiya lafiya ki ke kira na a daidai wannan lokacin?? "Na kashe shi wallahi na kashe shi. "Wa ki ka kashe Sadiya Dan Allah ki faɗa min wa ki ka kashe? Yayin da Sadiya sai maimaita kalmar ta kashe shi take yi, hakan kuwa ba ƙaramin tashin hankali Abdulkarim ya shiga ba, ya wutsillo daga gado yana ture duvet daidai Sadiya tana hanging up abu na farko da ya fara shi ne ɗaukar car key ɗinsa ko takalma bai tsaya sakawa ƙafafunsa ba, ya fice da wani kalar sauri kamar zai tashi sama tun kafin ya ƙarasa parking lot ya shiga kwaɗawa maigadi kira "Malam Habu! Malam Habu zo ka buɗe min gate. Sadiya tana kyalla ido taga yadda jini jikin AB yake kwance male-male akan tiles ta ƙara tsorata sai lokaci wata irin nadama ta soma shigarta, tsoron irin hukunci da zai biyo kanta ya shige ta, ƙwaƙwalwarta ta fara mata refreshing irin hukunci da ake zantarwa da duk wanda ya yi kisan kai shima kashe shi za a yi "tabbas kashe ni za a yi ko Daddy ba zai taɓa bari na a raye ba kawai ki gudu Sadiya ki gudu ki tseratar da rayuwarki wani bangare na zuciyarta ya umarce ta, ba tare da ɓata lokaci ba ta ɗauki lafayyarta da ta cire dake ajiye a gefen gado bata tsaya naɗa ta ba ta lulluɓa ta kawai a jikinta dama wayarta na riƙe a hannunta, da gudu ta fice daga ɗakin, har ta kai main parlor sai ta tuna da dole tana buƙatar kuɗi, ɗakinsa ta shiga wallet ɗinsa da wayarsa na ajiye akan bedside drawer jikinta sai faman kakkarwa yake ta buɗe wallet ɗin gaba ɗaya kuɗaɗen dake ciki ta kwashe ta fice da gudu. Idan Allah ya taimake ta maigadi yana ɗakinsa cikin sanɗa ta zare sakata dake jikin ƙofa, ta yanka da gudu ceton rai tana dab da isa titi ta hango motar Abdulkarim Safana kasancewar tsakani gidansu zuwa titi akwai tazara sosai kuma sabuwar unguwa ce babu mutane sosai. Da sauri ta laɓe jikin gini wani gida da ba a ƙarasa gininsa ba, har sai da taga ya wuce kana ta fito ta ci-gaba da tafiya mai haɗe da gudu-gudu. Uban horn ɗin da Abdulkarim Safana ke dannawa ya yi nasarar tashe da maigadi dama yana ciki mutane masu nauyi bacci, a tsorace ya dauko adda cikin sanɗa ya fito daga ɗakinsa, zuciyarsa cike da tu'ajjabin waye yake musu horn ciki silasili dare. Ƙaramar ƙofar da ya gani a buɗe ya haifar masa da matsanancin faɗuwar gaba alhali yasan kafin ya kwanta sai da ya rufe ta. Abdulkarim yana gani zai ɓata masa lokaci ya buɗe murfin mota ya fito ta ƙaramar ƙofa dake buɗe ya shigo yaga maigadi tsaye ya dafe da kofa da hannunsa sai wuƙi-wuƙi yake da idanuwa a fusace ya daka mishi tsawa kasancewar Abdulkarim Safana ba bako bane a wurinsa ya hanzarta buɗe masa gate, kana ya Abdulkarim ya shigo da mota sai dab da entrance ɗin gidan ya yi parking ya fice da gudu ya tura ƙofar shiga main parlor. Da gudu ya haura sama firstly ɗakin Ab ya fara buɗewa yaga ba kowa a ciki dole ya dawo na Sadiya buɗe ƙofarsa ke da wuya ya hango amininsa kwance cikin jini "Innalillahi wa'inna illahim raji'um! Kalma ta farko da Abdulkarim ya fara furtawa kafin ya isa ga gawar Ab, ga baki ɗaya Abdulkarim ya ruɗe ya rasa ta ina zai fara jikinsa ko'ina rawa yake wannan shine karonsa na farko da ya fara gani gawa ido da ido. Zubewa ya yi gefen Ab ya sa wani irin kuka mai ban tausayi da taɓa zuciya, kafin ya kai hannunsa ya taɓa kafaɗar Ab ciki rikitatciya murya ya kira sunansa "Ab! Ab!Abba Dan Allah ka tashi karka yi min haka Abba Dan Allah kada ka mutu, kasani mutuwarka za ta taɓa zukata da dama ka tashi Abbaaaaa! Sai kuma ya tashi a rikice zuwa farfajiyar gida ya kwallawa maigadi kira wanda tun shigowar Abdulkarim jikinshi ya bashi babu lafiya, shiyasa kasa komawa daƙinsa ya yi tsaye jugun! Da gudunsa ya zo suka ciccibe Abba zuwa mota duk da dukkansu biyu sun gama amincewa da Ab ya mutu saboda ko jikinsa ya yi wani irin sanyi ga kuma uban jini jikinsa da ya yi kace-kace a ɗakin. Maigadi da ya gaza haƙuri sai da ya tambaya gari ya haka ta faru duka bai fi two hours da rabuwarsu ace har an kashe shi waye yai masa wannan aika-aikar. "Amaryarsa ce. Abinda kaɗai Abdulkarim Safana ya iya furtawa maigadi shima gudu kada ya bar shi cikin tunani kaitsaye softcare private hospital ya nufa duk da yana da tabbaci Abba ya riga da ya mutu amma don ya kara tabbatarwa ya kawo shi asibiti. Bayan an shigar dashi ɗaki duba marasa lafiya likitoci suka ce dole sai an kira 'yan sanda saboda murder case ne sai lokaci Abdulkarim ya yi tunani ya kira Daddy domin bai ga amfani boye masa ba. Alhaji Bashir yana kwance akan katafaren gadon sa da ke bedroom ɗinsa a gefensa maidakinsa ce Hajiya Mariya bacci suke cikin kwanciyar hankali, can cikin bacci nasu suka ji ring ɗin ɗaya daga wayoyin Alhaji Bashir, kusan su dukka a tare suka falka. Alhaji Bashir mutum ne da baya taɓa nisanta da wayarsa a cewarsa waya tafi amfani a cikin dare domin wani zai iya shiga matsala ya kuma nemi taimakon ka, hakazalika kai ma za ka iya shiga matsala shiyasa koda yaushe wayoyinsa suna ajiye kusa dashi. Ya zabura da sauri ya tashi zaune ya tabbata koma waye ya kira sa a irin wannan lokaci ba lafiya ba. Yana miƙa hannunsa ya dauko wayar kiran yana tsinkewa sai kawai ya ji wani irin faɗuwar gaba, har sai da ya kai da furta "Hasbunallahu wal-imaal wakil! A bayyane. "Lafiya Alhaji? Hajiya Mariya ta faɗa tana kallon mijinta da fuskarsa ta fara jiƙewa da gumi tamkar babu Ac a ɗakin, yana daukar wayar wani kira na sake shigowa, "Abdulkarim! Ya faɗa a bayyane sai kuma ya yi gaggawar receiving "Assalamu alaikum Abdulkar...... "Daddy ka zo yanzu-yanzu nan Softcare private hospital Allah ya yiwa AB rasuwa. "Innalillahi wa'inna illahim raji'um! Abdulkarim me ka ke cewa ne? "Daddy Abba ya rasu Abba ya mutu Sadiya ta kashe mana Abba. Tsanani shock da Daddy ya shiga jikinsa ya ɗauki rawa bai san sanda wayar dake maƙale a kunnensa ta zame ta faɗo, firgici da tashin hankali gami da razanarwa suka taro lokaci guda suka yi masa dirar makiya, yadda yake ta maimaita "innalillahi wa'inna illahim raji'um! Yasa ita ma Hajiya Mariya jikinta ya shiga kakkarwa da kyar ta iya haɗa kalmar "la....fi....ya...Alha...ji?? Shiru Daddy ya yi yayin da bugawar zuciyarsa ya tsananta sai da ya sauka daga gado kafin ya iya furta "Allah ya yiwa Abba rasuwa kuma 'yarki ce ta kashe shi. "Innalillahi wa'inna illahim raji'um! Na shiga uku ni Mariya wannan wacce irin masifa ce? Sadiya ce za ta yi kisan kai kuma ta rasa wanda za ta kashe sai ɗan uwata yayanta, mijinta Ya Allah kada ka jarabce mu da wannan baƙar ƙaddara. Nan take Hajiya Mariya ta rikice da wani irin kuka tana sambatu Alhaji Bashir ya ɗauki key ɗin mota ya fice da sauri Hajiya Mariya ta sauko daga gado ta bishi a baya sai da ta kai ƙofar fita ta tuna da bata suturta jikinta ba gashi kuma kayan bacci ne take sanye dasu. Duk girman jikinta haka ta kwasa da gudu ta shiga bedroom ɗinta ta sako hijabinta na sallah, koda ta fito compound har Daddy ya jawo mota tsananin tashin hankali da suke ciki ba zai misaltu ba. Koda suka iso Softcare kowanne su zuciyarsa na dab da bugawa. Zuwan Daddy yasa likitoci suka dukufa duba Abba duk da suma suna da tabbaci ya riga da ya mutu, kawai dai za su duba shine saboda yana aikinsu. Sadiya tana isowa bakin titi mutum na farko da ta fara kira Hafiz Sale shine wanda za ta aura a kuma wurin ɗaurin aure nasu ne rashe ya juye da mujiya ƙaddara ta faɗa mata igiyar aure ta ratse tsakaninta da yayanta. Sai da ta jeranta masa kira yafi goma kafin ta samu ya yi picking cikin dassashiyar murya ya kira sunanta saboda kwata-kwata babu alamar bacci a idanuwansa ya kasa karɓar ƙaddarar rasa ta da ya yi kwatsam sai ga kiranta ya shigo wayarsa. "Hafeez Dan Allah ka zo ka taimake ni ina cikin tashin hankali idan ba ka taimaka min ba, bansan ina na nufa ba. "Subhanalillah! Sadiya meke faruwa ne ki natsu ki yi min bayani? "Maganar nan ba za ta yiyuwa a waya ba. "Shi kenan kina ina gani nan zuwa. "Ina tsaye a bakin titi gidan Ya Abba dan Allah Hafeez karka bata lokaci domin komai zai iya faruwa. Kusan ten minutes da yi wayarsu sai gashi ya zo, jikin Sadiya yana rawa ta buɗe mota ta shiga, Hafeez Sale ya ja motar da gudu ya halba kan titi sai da suka yi tafiya da nisa kafin ya juya ya kalleta da idanuwansa da suka soye ya ce "faɗa min dalili da yasa ki ka fito gidan mijinki a darenku na farko ki ka rasa wanda za ki nemi taimakon sai ni?? Wasu zafafan hawaye ne suka wanke mata kumatu ta kasa magana saboda batasan yadda Hafeez Sale zai karɓi al'amarin ba. #Love Story 2023/2024 #Jiddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya [11/21/2023, 6:46 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 002. *RUBUTUN ƳAN TAGWAYE BIYAR KARO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* *KIN TABBATA KIN CIKA MACE? BABBAR MACE DAKE JI DA KANTA? KINA CIKIN MATAN DA SUKA SAN KANSU? WANDA SUKA SAN MUTUNCI DA DARAJAR KANSU? KO KUWA KEMA KINA CIKI SAHUN SU O’O?* *INA KUKE MANYAN MATA? WAƊANDA SUKA SHIRYA DAN GYARA JIKINSU? AURANSU? DA KUMA FARINCIKINSU?” *KUYI MAZA KU GARZAYA GUN FITACIYGA KUMA INGANTACIYAR MAI MAGANIN MATA DA MAZA DAN AMSAR NAKU KU GYARA DA KANKU WATO MEERAH HERBS WACCE TAI FICE GUN KAWO MUKU INGANTATTUN MAGUNGUNA BA TARE DA ALGUS BA.* Mun gwada mun gani 💯 Mun gani mun shaida 💯 Anyi mun gani 💯 MAGANIN SANYI MAGANIN NONO MAGANIN HIPS MAGANIN SLIMMING MAGANIN NANKARWA GYARAN AMARE GYARAN MAIJEGO MALLAKAR MIJI KO MATA SUBULU DA SCRUB MAYUKA NA GYARAN JIKI TURAREN WUTA MATSI MAGANIN NI'IMA MAGANIN TSUMI INFECTION FLUSHER DA DAI SAURANSU…..Uwar gida, Amarya, Budurwa, Saurayi, Ango, Mai gida? Duk mai kuke jira? Kuyi maza ku garzaya Meerah herbs maganin dake ingantace 💯 08142800199 07068558096 Banda tsananin bugawa babu abunda zuciyarta keyi hoton cakawa yaya Abba wuƙa da tayi ya kasa barin gilma mata cikin idanuwanta har, lokacin kuma ta kasa yiwa Hafeez bayani da ya gaji da tuƙi ya gangara gefen titi yayi parking motar tare da kasheta duka. A hasale ya juyo yana faɗin."kiyi min bayani Sadiya kinbar zuciyata acikin tashin hankali da tunani ki faɗamin ina mijinki da kika fito cikin wannan dare?""na kashe sa Hafeez!" kalmomin da suka fito da kyar daga bakinta kallonta yake with so much shock acikin fuskarsa tamkar da wani yare tayi masa magana "Na kashesa Hafeez da gaske bazan iya rayuwar aure da yaya Abba ba. Zan iya mutuwa idan muna zaune a gida daya dashi ba zai iya jure hakan ba. Wallahi zuciyata bazata iya jurewa ba, ban taɓa yi masa soyayyar aure ba, baya ga ta yan uwantaka wanda nake hangosa a matsayin yayana wanda muke uba ɗaya dashi na rasa Meyasa Daddy yayi tunanin haɗamu aure dashi. Lokaci ɗaya Daddy ya rusa dangantakar dake tsakanina da yaya Abba."ta ƙarasa maganar cikin shesshekar kuka dan ko kaɗan bata hango shock din dake kwance cikin fuskar Hafeez sale ba. Hafeez ya haɗiye wasu busassu miyau a hankalinsa ya yi mugun tashi "Sadiya kin fara shaye-shaye ne daman?"Hafeez ya faɗa cikin rawar murya, girgiza masa kai kurum ta shiga yi ga baki ɗaya abirkice take. Tasan labarin mutuwar Yaya AB ya riga ya zagaye duk wanda yake da alaƙa dashi "kisan kai ki kayi akan wani banza tunani naki."Hafeez ya faɗa sounding so very harsh duk da ya fahimci ko kaɗan bata cikin natsuwarta lokacin jin yake kamar ya kwaɗawa Sadiya mari kifa kansa yayi jikin sitiyarin mota yana ambaton Allah a ransa yama rasa kalar tunanin da ya kamata yayi a wannan lokacin Sun fi minti goma a haka babu mai magana a cikinsu sai shesshekar kukan Sadiya dake tashi a motar mai ciked a danasanin abinda ta aikata tare da hango makomar rayuwarta, ta tabbatar itama kasheta za ayi tada motar Hafeez yayi batareda ya sake yiwa Sadiya magana ba, ya harbata kan titi bai tsaya da ita ko'ina ba sai cikin harabar Bon hotel ya kashe mota Sadiya ta ɗago rinannun idanuwnta tana ƙarewa harabar wurin kallo, duk da bata cikin natsuwarta ta gane hotel ne Hafeez ya kawota wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi. Tunda take a rayuwarta ƙafarta bata taɓa tako cikin hotel ba tun tana budurwa, ballantana yanzu da aure akanta ace ta shigo hotel da tsohon saurayinta ganin bata motsa daga inda take ba sai bin Hafeez ɗin take da kallo cike da gajiya a muryarsa yake faɗin."muje mu kama ɗaki Sadiya mu samu mafita kinga yanzu dare yayi ban san inda zan ajeki ba bayaga nan, Jiki sabule ta balle marfin motar tabi bayansa har zuwa cikin reception ɗin Ya kama masu ɗakin da zasu sauka su tattauna dan yasan babu maganar su kwanta suyi bacci daga ita har shi. Tana tsaye tana kallonsa har ya dawo da key a hannunsa ya kalleta yana faɗin suje babu musu tabi bayansa cikin wani irin sanyi jiki da kansa ya buɗe ɗakin ya shiga sa'anan tabi bayansa ciki da parlor ne ta nemi kujera mai cin mutum ɗaya ta sulale ta zauna tana jin tsoro da tashin hankali na cika zuciyarta lokaci ɗaya. Dafe kansa Hafeez yayi da duka hannunsa biyu ya rasa ma wane kalar tunani zaiyi tabbas mata duka ragaggen tunani ne dasu idan banda hauka taya zatayi kisan kai bancin tasan itama kasheta za ayi. "Sadiya ya zama dole gobe kije ki gurfana agaban iyayenki ki nemi gafarar su bamu da tabbas akan AB ɗin ya mutu ko yana raye. A wani irin razane take faɗin."Na koma kace Daddy ya yankani Nima?"meyasa baka fahimta saboda son da nake yi maka na kasa karɓar yaya Abba a matsayin mijina, na kasa karɓar ƙaddarar zama gidansa, idan har soyayyar da kake min da gaske ne bai kamata kace na koma gidanmu cikin wannan yanayin ba Hafeez."baki buɗe Hafeez ke kallonta to me kike so nayi?"so kike na gudu dake muje wani wurin muyi aure ko yaya?"ke idan zaki iya barin iyayenki ni bazan iya barin nawa iyayen ba. kallonsa kawai sadiya keyi a wannan lokacin tana mamakin kalaman dake fitowa daga bakin Hafeez din. "ke kin san dole idan aka wayi gari akaji mutuwar AB acikin garin Kano dole a shiga nemanki so ki ke ki jamin masifa Sadiya ina zaman zamana."na faɗa maki gobe da safe zan kai ki gaban iyayenki ko ki hau adaidaita sahu ki tafi da kanki kar ma aganmu a tare a ɗauka da haɗin bakina kika kashesa. Ki tashi ki shiga ciki ki barmin parlorn, kallon Hafeez take tamkar bashi ba duk yabi ya sauya shin ina soyayyar da yake ikirarin yana yimata? "Sadiya ki daina yimin irin wannan kallon. miƙewa Sadiya tayi ta nufi cikin bedroom ɗin gefen bed ta zauna ta dafe kanta tana tunanin makomar rayuwarta mai cike da na sani tasan 'yan gidansu yanzu sun tsaneta duka kannenta da iyayenta, duk akan Abba Bashir."tun farko ban amince da wannan auren ba Daddy meyesa kazo ka lalata komai sadiiya ta ƙarasa maganar tana danna kanta ciki pillow ta saki wani irin kuka mai girgiza zuciya da ruhi. Daga Daddy har Hajiya mariya wacce yaranta suke kira mami tsaye suke a bakin emagency suna ganin yadda likitoci ke kai da kawo, batareda an masu bayanin wane hali Abban yake ciki ba saboda tashin hankali suna wurin a tsaye har qarfe huɗu na a asuba, sauro kuwa duk ya gama canye naman jikinsu dan basu mabi ta kansa ba tashin hankali bai sa sunji cizon da yake masu ba. Hawaye na zuba a idanu Mami tana addu'ar Allah ya tashi kafaɗun Abba, idan suka rasa Abba batasan wane hali zasu shiga ba. wani babban likita ne ya fito daga ɗakin da Abba ,yake ciki da sauri Alh Bashir ya nufesa cikin sauri da rawar murya yake faɗin."likita ya jikin nasa?"girgiza kai matashin likitan yayi yace su samesa a office ga baki ɗaya har Abdulkarim da yake tare dasu suka bi likitan kowa jikinsa a mugun sanyayye, bayani likita yayi masu wanda da kyar da taimakon Allah Abba,ya tsira da rayuwarsa sai dai yaji mugun rauni acikinsa sun masa allurar bacci daga Daddy har Mami wata irin ajiyar zuciya suka shiga saukewa a boye shima Abdulkarim sai lokacin ya samu ya dawo cikin natsuwarsa banda tsinewa Sadiya babu abunda yake a aransa Abdulkarim ya kalli Daddy yana faɗin."suje gida kafin washe gari zai zauna da Abba ɗin, suna mota Mami taga kiran siyama ya shigo a wayarta daman ta fito da ita ne koda wani zai kira acikinsu, lokacin karfe biyar da rabi na asuba mami ta dauka cike da ƙarfin hali tana ƙoƙarin ɓoye damuwarta."Mami ina kika je keda Daddy?"meya faru?"Siyama duk ta ruɗe. "gamu nan kan hanya siyama da haka mami ta katse wayar har suka kai gida daga Mami har Daddy kowa da abunda ke cin zuciyarsa gashi har lokacin likita bai basu damar ganin yaron nasu ba, zaune suka tarar da Siyama a parlorn da kayan bacci riga da wando masu kauri ajikinta tana ganin iyayen nata ta nufosu tana tambayarsu lafiya.?"mami ce tayi ƙarfin halin faɗin.yayansu ne babu lafiya Amman da sauki siyama ta dafe kirji zuciyarta na bugawa take faɗin."meya samu yayanmu Mami?"nan take Siyama ta ruɗe "Na faɗa maki da sauki. Dama Daddy ko tsayawa baiyi ba ya nufi bangarensa kai tsaye yana tunanin hukuncin da zai yankewa Sadiya wannan lokacin, ba dai shi zata wulaƙanta ta tozarta ba."ina Aydah?"kema mami kin san tana can buɗe da baki tana baccin musamman yanzu da ba sallah zatayi ba. "To kije kiyi shirye-shirye sallah da kin gama ki tasheta kuzo mu haɗu kitchen mu haɗa breakfast na kaiwa yayanku."da haka mami itama ta nufi bangarenta suna gama sallah daga Mami har ya'yan nata kai tsaye kitchen suka nufa suka fara shirye shiryen dora breakfast da yar aikinsu a gefe. Aydah sai turo baki take ganin an katse mata baccinta daman yan biki tun Jiya kowa ya kama gabansa daman babu wanda ya faɗawa Aydah Ab na hospital har suka gama break fast kowa ya nufi ɗakinsa dan yin wanka tun kafin su wuce Mami ta kalli Aydah dan tasan tana iya komawa bacci dan tasan halinta da shegen son bacci "karki koma baccin asara wanka za kiyi ki fito muje asibiti. Sai lokacin Aydah ta dawo gaban Mami duk a tsorace take "Mami waye babu lafiya?" Ta faɗa tana ƙoƙarin fashewa Mami da kuka, Mami ta sakar mata da harara tana faɗin."kefa dadina dake sakarya ce. "To Mami waye babu lafiya?" Aydah ta faɗa hawaye sun cika idanuwanta lokaci ɗaya dama ita ce mai rauni acikinsu kuma ita ce autar Mami. "Yayanku ne. Kuka Aydah ta fashe dashi lokaci ɗaya duk tabi ta rikicewa Mami tana faɗin "meya same sa Mami? Duk Aydah ta rude ta fita hayyacinta daman duk cikin kannen Ab yafi shaƙuwa da ita tasu kuma tafi zuwa ɗaya idan kana son kaga bacin ran Ab a gidan to ka taɓa masa Aydah, komai Aydah ta samu yayansu shima komai ya samu na Aydah ne, haka Siyama da Sadiya ke jin haushinsa Mami tayi tai masa faɗa tace ya daina nuna bambanci a tsakani kannensa haka zai cewa mami ya daina gobe kuma ya ci-gaba. Aydah na wanka tana kuka duk tabi ta firgice tana ta tunanin wane irin ciwo ne zai kwantar da yayansu daren Jiya daren angwancinsa cikinsu daga Mami har Daddy babu wanda ya faɗa masu asalin meya samu Abba ɗin. Siyama ta daɗe da shiryawa tana zaune tana jiran fitowar Mami takun stairs taji ta dauka Mami ce sai taga Aydah ce ta fito sanye da hijab har kasa kallonta kawai siyama keyi har ta ƙaraso tana tambayar mami bata fito ba ?"Siyama ta tallabe cheeks ɗinta cike da matsananciyar damuwa dauke a fuskarta take faɗin."Nima ita nake jira. Juyawa Aydah tayi ta koma sama dan duba Mami idan ta shirya ga baki ɗaya ta ƙagu ta ganta asibiti wurin yayansu da Mami taci karo saura kaɗan su bugu Mami taja da baya a tsawace ta ce "wai meyasa bakida natsuwa ne ko kaɗan kina tafiya sharaf -sharaf bakya duba gabanki, Ko yaushe baki tafiya a natse. Mami ta faɗa tamkar zata rufe Aydah da duka. Baki Aydah ta turo tana bai wa Mami haƙuri ta juya ta koma parlorn, Mami ta ja tsaki tabi bayanta daman Daddy yana fitowa masallaci asibitin ya koma ,Mami ce take tuƙasu a mota har zuwa asibitin daidai su Mami suna fita lokacin kuma Hafeez ya ƙaraso da sadiya a ƙofar gidansu. #Love Story 2023/2024 #Jiddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only Zaki biya ta wannan account ɗin👇🏻 0020428430 Ishaq Fatima A GTBank KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k [11/22/2023, 3:17 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love Story) JEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU 003. #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye novels *RUBUTUN ƳAN TAGWAYE ZANGO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* PAID BOOK *KIN TABBATA KIN CIKA MACE? BABBAR MACE DAKE JI DA KANTA? KINA CIKIN MATAN DA SUKA SAN KANSU? WANDA SUKA SAN MUTUNCI DA DARAJAR KANSU? KO KUWA KEMA KINA CIKI SAHUN SU O’O?* *INA KUKE MANYAN MATA? WAƊANDA SUKA SHIRYA DAN GYARA JIKINSU? AURANSU? DA KUMA FARINCIKINSU?” *KUYI MAZA KU GARZAYA GUN FITACIYGA KUMA INGANTACIYAR MAI MAGANIN MATA DA MAZA DAN AMSAR NAKU KU GYARA DA KANKU WATO MEERAH HERBS WACCE TAI FICE GUN KAWO MUKU INGANTATTUN MAGUNGUNA BA TARE DA ALGUS BA.* Mun gwada mun gani 💯 Mun gani mun shaida 💯 Anyi mun gani 💯 MAGANIN SANYI MAGANIN NONO MAGANIN HIPS MAGANIN SLIMMING MAGANIN NANKARWA GYARAN AMARE GYARAN MAIJEGO MALLAKAR MIJI KO MATA SUBULU DA SCRUB MAYUKA NA GYARAN JIKI TURAREN WUTA MATSI MAGANIN NI'IMA MAGANIN TSUMI INFECTION FLUSHER DA DAI SAURANSU…..Uwar gida, Amarya, Budurwa, Saurayi, Ango, Mai gida? Duk mai kuke jira? Kuyi maza ku garzaya Meerah herbs maganin dake ingantace 💯 08142800199 07068558096 Hafeez Sale ya yi parking motar ba tare da ya kashe ta ba ya mayar da ganinsa kan fuskar Sadiya wacce tayi wani irin zuru-zuru idanuwanta sun kode laɓɓanta sun bushe kallo ɗaya za ka yi mata ka fahimci a firgice take. "Ki shiga gida Sadiya idan Allah yasa ƙura ta lafa zan nemi ki. Amma Dan Allah Sadiya karki ambaci sunana a matsayin wanda ya ba ki mafaka, kin dai san bansan yaushe kika shiryar da wannan shiri naki ba. Ƙarfaffiyar ajiyar zuciya Sadiya tayi zuciyarta tana bugawa da ƙarfin gaske ta kalli Hafeez yayin da idanuwanta da basa gajiya da kuka suka fara ambaliya kwalla "Dan Allah Hafeez ka mai dani hotel ɗin wallahi ina tsoron haɗuwa ta da Daddy Hafeez kasan yadda mahaifina yake da zafi sh.... "Dakata mana Sadiya! Hafeez ya katse ta da sauri fuskarsa ta bayyanar da ɓaci ransa a fili "Ya kike so ki jefa rayuwata a matsala?" Kisan kai fa kikayi Sadiya sannan kuma kike so na cigaba da baki wurin ɓoya? Gaskiya ba zan iya ba Sadiya ki fita min kawai daga mota, ko taimakonki da nayi jiya na kai ki hotel nayi nadamar sa. Oya fita tun kafin wani ido ya ganni tare dake masifar da kika jawowa kanki ta shafe ni. "Hafeez Dan Allah... "Dallah malama fita! Nace ki fita min daga mota. Cikin tsawa da hargowa Hafeez ya yi mata magana, Hafeez ɗin da ta sani mai sanyi hali da rashin son haniya halinsa sak! na Ya Abba, amma yau shine yake buga mata tsawa da ihu irin wannan. Gani ta kasa fita sai kallonsa take ga baki ɗaya hawaye sun gama wanke mata fuska. A mugun fusace Hafeez Sale ya ɓalle murfin mota ya fito ransa a ɓace ya ɓalle wa Sadiya murfi tun kafin ya kai da magana ta fito da sauri tana kallonsa ya ja motarsa da gudu sai da ya ɓacewa ganinta kafin ta durƙushe wurin ta saki kuka mai taɓa zuciya, ta dau lokaci a wurin tana kuka kafin ta miƙe ta kwakwasa ƙaramar ƙofa maigadi ya buɗe mata yadda ya ganta sai da ya ja da baya hakan da ya yi, ya ƙara linka tashin hankali da Sadiya take ciki shikenan kowa ya gama sani ta'asar da tayi shikenan ta zama abin tsoro da gudu a cikin mutane. Tun da masoyinta ya gujeta wanda ta hakikance dashi take ikirarin shine rayuwarta to kowa ma zai iya gudunta. Mamaki da maigadi ke yi me ya kawo ta gida ita da jiya-jiya nan aka kaita ɗakin miji shine za ta dako wannan uban sammako "A'ah ikon Allah Halimatu! ke ce a tafe da sanyi safiya nan? Allah yasa lafiya to shi kuwa ango naki yana ina da yabarki kika fito ke kaɗai? Gashi kuma kin taki rashin sa'a ga baki ɗaya mutane gidanan sun fita hatta da Alhaji yana dawowa daga masallaci ya fice, da alama Halimatu akwai abinda ke faruwa a gidanan. Naga fuskar Alhaji kamar wanda aka yiwa mutuwa, to ko mutuwar aka yi muku tun da kema ga ki kin zo da taki fuskar tashin hankali gashi kuma kina hawaye? To amma da mutuwa ce aka yi ai bai kamata Alhaji ya ɓoye min ba ko ladar jana'iza na samu. Dukka maganganu da maigadi ke yi yana ƙara linka tashin hankali da Sadiya take ciki ne ji da tayi babu kowa yasa ta nufar cikin gida da wani irin sauri, maigadi ya bi ta da kallo baki buɗe "Ikon Allah to ko me ta zo yi ne oho! Wannan garsakeƙƙiya ba za a ce tana tsoron namiji ba sai dai in kuwa bata da cikakkiyar lafiya. Maigida ya yi magana a bayyane kana ya koma ɗakinsa zuciyarsa cike da tu'ajjabin dalili zuwan nata. Mami tayi parking motarta wurin da aka tanada domin yi parking a hospital ɗin, ta wuce gaba Siyama da Aydah suna bin ta a baya hannayensu riƙe da food basket. Mami ta tura ƙofar ɗakin Daddy da Abdulkarim Safana suna zaune akan plastic chair gaban gadon da AB yake suna kallon hawa da saukar numfashinsa. Mami da Siyama ne kaɗai suka yi sallama banda Aydah wacce tana hango AB kwance cikinsa naɗe da bandage ta fara kuka. "Ina kwana Alhaji ya jikin nasa?" Mami ta faɗa sa'ili da ta iso kusa da Daddy. "Al-hamdullilah! Daddy ya faɗa muryarsa bata fita sosai. "Ina kwana Mami?" "Lafiya ƙalau Abdulkarim ya jikin abokin naka?" "Jiki Al-hamdullilah sai dai har yanzu bai falka ba. "Zai falka da izini Ubangiji. Mami tayi magana da damuwa akan fuskarta. Siyama ta matso ta gaida Daddy da Abdulkarim tare da tambayar jikin AB Aydah na can rakuɓe jikin ƙofa tana kuka, shesshakar kukanta ne ya jawo hankalinsu izuwa gareta, murmusawa Daddy ya yi tun faruwar al'amari sai yanzu fuskarsa ta saki har ya sami yi murmushi, da hannu ya fito Aydah tare da faɗin "Zo nan Mamana! Da gudu ta zo ta faɗa jikin Daddy ta saki kuka a hankali Daddy ya dinga bubbuga gadon bayanta "ya isa haka ki daina kuka Mamana ki yi masa addu'a kin ji?? Aydah ta gyaɗa kai gami da barin jikin Daddy "Oya share hawaye mana. Abdulkarim ya faɗa yana kallon fuskar Aydah. Tasa gefen hijab ɗinta ta goge fuskarta "Yau kam akwai aiki kuka sai mun gaji dashi mun nemo auduga mu toshe kunnayen mu. Mami tayi magana tana kallon Aydah wacce ta nufi kusa da AB tai tsaye tana kallon fuskarsa ma'aɓociya kyau da kwarjini. Sai misali ƙarfe 11:15am AB ya falka bakinsa ɗauke da sallati kusan dukkan su a tare suka tashi tare da nufo wurinsa kowanne yana kokari yi masa sannu, kafin Daddy ya kama hannunshi ya riƙe gam! Yana kallon fuskarsa "Sannu Abba ya ka ke ji jiki naka??" "Al-hamdullilah Daddy! "ma-sha-Allah! Bara a kira likita ya zo ya duba ka ya gani idan babu wata matsala Abdulkarim kira likita. Abdulkarim ya amsawa Daddy tare da ficewa da sauri. Jim kaɗan sai ga Abdulkarim ya dawo tare da likita da wata nurse dake biye dasu hannunta dauke da ɗan ƙaramin tray silver mai ɗauke da tarkace kwalaben allurai da syringe A firgice Aydah ta ɗago tare da bin matashin likitan da kallo yana sanye da farar long sleeve shirt haɗe da baƙin wando ya ɗaura lab coat akai wuyansa na saƙale da Stethoscope, duk duniya babu abinda ke sauri haifar mata da tsoro irin allura ta tsani allura ko syringe bata so gani. Sai da likita ya fara duba bugun numfashin AB kafin ya miƙa hannu ya ɗauki bottle ɗin allura ya fasa kwalbar tare da ɓare syringe ya zuƙo ruwan da sauri Aydah ta runtse idanuwanta jikinta ya ɗauki rawa, zufa ya tsatsafo mata akan goshinta da ƙananu gashi yake kwance lub-lub. A hankali ta ɗan buɗe idonta guda daidai lokaci da likita ya ɗauki auduga wacce ya jiƙa ta daga ruwan spirit ya kama tsintsiyar hannun AB sake runtse idon nata tayi ta, hawaye masu zafin gaske suka fito daga kwarmin idanuwanta. Tambayoyi da ta ji likita yana ma AB yasata buɗe idanunta. Bayan fitar likitan Daddy da Abdulkarim suka taimakawa AB ya tashe zaune mami ta saka masa pillow a bayansa. Abdulkarim ya taimaka masa ya yi brush da alwala sai lokaci ya sami damar yi sallar asuba, sai da Daddy yaga Abba ya ɗan sha tea kana ya nufi gida ya yi wanka bayan fitar Daddy shima Abdulkarim ya yi musu sallama, aka bar Mami da girls ɗinta Aydah tana manne da AB ko nan da can bata kusa ba kuma lokaci zuwa lokaci sai ta tambaye shi ya aka yi ya ji ciwo me ya same shi ina Yaya Sadiya ko batasan cewa bashi da lafiya ba. Tambayoyi dai ga su nan birjik take masa sai dai ko guda daga ciki ya kasa amsa mata daga ƙarshe ma da yaga tana so ta matsa mishi sai kawai ya lumsashe idanuwansa tamkar ya yi bacci dole ta kyaleshi. Kaitsaye Sadiya ta wuce ɗakinta ta faɗa kan gado tare da yi rub da ciki cigaba rera kukanta nadama babu kalar wacce bata yi ba. A hankali Daddy yake driving tun jiya zuciyarsa take cike da mamaki ta ya aka yi ɓoyayyen sirrinsa ya fito fili, kuma bai tashi bayyana ba sai a ranar daurin auren 'yayansa. Sirri ne da aka yi haƙa rami karkashin ƙasa aka binne daga shi sai marigayi matarsa Maryam suka san dashi wacce duk duniya ta ɗauki cewa ita ce ta haifi Abba hatta da iyayenta basu san cewa Abba ba jikansu bane. Ta ya aka yi wannan sirri ya bayyana? A ina Alhaji Bello Madawaki ya sami wannan ɓoyayyen sirri? Ina son Abba tamkar raina ba zan taɓa barin fitar wannan sirri ya shafi gobensa ba. Zan iya kokarina naga na kare masa martabarsa, ita kuma Sadiya tabbas sai ta fuskanci hukunci abinda tayi ba zan kyaleta ba duk da kuwa ta kasance 'yar cikina. Da wannan zance zuci Daddy ya iso gida yana fitowa daga mota, maigadi yana ƙarasowa "Sannu da zuwa Alhaji. "Yawwa Balmo. "Ai Alhaji bayan kun fita sai ga Halimatu amarya ta zo fuskarta a kumbure idanuwa duk a kode alamar tasha kuka har ta gode Allah, babu kalar tam..... Kafin Balmo ya ƙarasa magana Daddy ya nufi cikin gida da mugun sauri har wani uban tuntuɓe ya ci da interlock amma ko a jikinsa muradina ya yi ido biyu da Sadiya, rai ɓace Daddy ya tura ƙofar ɗakin Sadiya wacce har zuwa lokaci tana kwance rub da ciki yadda Daddy ya tura ƙofar da ƙarfi yai sanadi da ta zubura ta tashi zaune, idanuwanta suka bayyanar da tsanani tsorata da tayi, cikinta yai wani kalar ƙugi musamman da idanunta suka sauka akan fuskar Daddy wacce ke ɗaure tamau. Sadiya bata ƙara shiga bala'in tashin hankali ba sai da taga irin mugun kallo da Daddy yake bin ta dashi, zance ta gudu bai ma taso ba idan ma tace za ta gudu to ta je ina? Sai kawai ta sakko daga gado ta zo ta zube guiwayoyinta biyu agaban Daddy ta sadda kanta ƙasa tare da fashewa da mahaukacin kuka "Ka hukunta ni Daddy Dan Allah ka hukunta ni daidai da laifin da na aikata ban cancanci afuwanka ba saboda I really really disappointed you Daddy ban kasan yarinya tagari ba nayi tarnishing image ɗin gidanan na jawowa zuri'arka bad record Daddy ka yi min duk abunda ka ga dama... Muryarta yai wani kalar sarƙewa duk maganganu dake fita daga bakinta tamkar tana ƙara gayyato wa Daddy fushi da takaicinta ne, idanuwansa sun ƙara rinewa yasa hannunsa ɗaya ya cakume wuyanta ya yi dragging nashi ya ɗauke ta da gigitatcen mari na fitar hankali wata irin razanannayar ƙara ta saki sa'ili Daddy ya sake wanka mata wani mari, ba iya mari guda ko biyu ba maruka ya ci-gaba da ɗauke tasu har sai da ji da ganinta suka ɗauke hanci da bakinta na zubda jini fuskarta da ta fara hayewa Daddya ya duba "meyasa za ki nemi salwantar min da rayuwar yaro? Me ki ka fi Abba dashi da ba za ki iya rayuwar aure dashi ba? Shin ban cancanci a matsayina na mahaifinki ki fidda ni kunya a idon jama'a ba? Ɗan uwanki bai cancanci ki sadaukar masa da farin cikin ki ba? Meyasa Sadiya meyasa za ki nemi kashe Abba? Ya ƙarashe magana da wani irin mugun fushi a muryarsa, ya sake ta ta zube ƙasa wanwar numfashinta sai ya yi sama ya dawo ƙasa, ko kaɗan Daddy bai damu da hali da take ciki ba ya fito da wayarsa ya yi dialling number CP (Commissioner of police) tare da faɗa masa ya tura masa da yaransa su zo gidansa ga suspect ɗin da suke nema, da yake tun da sassafe Daddy ya kira shi ya sanarda shi komai sai dai ya ɓoye masa bai faɗa masa cewa Sadiya 'yarsa bace. A fusace Daddy ya rufe Sadiya a ɗakin nata ya dawo downstairs parlor ya kai gwaro ya kai mari, shi kaɗai ne zai iya iya bayyana hali da yake ciki. After twenty minutes ya ji ƙarar jiniyar motar 'yan sanda ya koma ɗaki ya jawo Sadiya kamar kayan wanki sai gunji kuka take yi. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [11/23/2023, 5:57 PM] Jiddarh Aliyu 2: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #team tagwaye novels 004. *RUBUTUN ƳAN TAGWAYE BIYAR KARO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* *KIN TABBATA KIN CIKA MACE? BABBAR MACE DAKE JI DA KANTA? KINA CIKIN MATAN DA SUKA SAN KANSU? WANDA SUKA SAN MUTUNCI DA DARAJAR KANSU? KO KUWA KEMA KINA CIKI SAHUN SU O’O?* *INA KUKE MANYAN MATA? WAƊANDA SUKA SHIRYA DAN GYARA JIKINSU? AURANSU? DA KUMA FARINCIKINSU?” *KUYI MAZA KU GARZAYA GUN FITACIYGA KUMA INGANTACIYAR MAI MAGANIN MATA DA MAZA DAN AMSAR NAKU KU GYARA DA KANKU WATO MEERAH HERBS WACCE TAI FICE GUN KAWO MUKU INGANTATTUN MAGUNGUNA BA TARE DA ALGUS BA.* Mun gwada mun gani 💯 Mun gani mun shaida 💯 Anyi mun gani 💯 MAGANIN SANYI MAGANIN NONO MAGANIN HIPS MAGANIN SLIMMING MAGANIN NANKARWA GYARAN AMARE GYARAN MAIJEGO MALLAKAR MIJI KO MATA SUBULU DA SCRUB MAYUKA NA GYARAN JIKI TURAREN WUTA MATSI MAGANIN NI'IMA MAGANIN TSUMI INFECTION FLUSHER DA DAI SAURANSU…..Uwar gida, Amarya, Budurwa, Saurayi, Ango, Mai gida? Duk mai kuke jira? Kuyi maza ku garzaya Meerah herbs maganin dake ingantace 💯 08142800199 07068558096 _______________________ Wuraren sha biyu na rana Mami ta kalli su Siyama tace su tashi su wuce gida ta juya kan AB da Aydah ke gwadawa wani abu a wayarsa sai murmushi yake yi Abba me za a haɗo maka na lunch?" Ya rausayar da kai yana faɗin "Mami komai ma kika yi zanci. murmushi jin daɗi Mami ta yi ganin yadda ya sake lokaci ɗaya. "Yayanmu dan Allah ka faɗawa Mami ta barni a wurinka. Aydah ta faɗa murya kasa-kasa ta yadda Mami, ba za ta ji ba shima murya can ciki yake faɗin."kuje tare dai nasan damuna za ki yi da surutu kuma anjima akwai islamiyya tun da ba ki samu zuwa ta safe ba. Lokaci ɗaya Aydah ta wani haɗe rai tayi folding hands ɗinta akan ƙirjinta shi dai murmushi kawai ya yi yana ɗauke kansa tunda ya yi haka tasan ya gama magana kuma ba zai ƙara fadar komai ba. Baki buɗe Mami ke kallonta tana faɗin."ko adaidaita za ki nema mu yi tafiyar mu? Ta ɗan kalli gefen AB ganin ya ma rufe idanuwansa tamkar za ta yiwa Mami kuka cikin sanyin murya ta ce "Dan Allah Mami ki barni anan tare dashi sai ku tafi da yaya Siyama. Da sauri Siyama tace "Nima Mami zan zauna nasan abunda take yiwa gudu dan kar a shiga kitchen tare da ita. "Yaushe na faɗa miki haka yayanmu ka yiwa yaya Siyama magana ta daina sakamin ido a lamurranna ta daina bana so. A hankali Abba ya buɗe idanuwansa yana kallonsu kafin ya kalli Aydah yana faɗin."Tashi ku tafi bana son rigima. Ai yana faɗar haka ta miƙe ta nufi kofa a mugun fusace. daman Mami ta daɗe da fita ganin ta fita yasa Siyama ta juya tana yiwa yaya Abba, sai anjima daman wani kallo yayi mata wanda ta riga tasan me yake nufi ganin Mami ta nufi gidan yaya Abba, da mota yasa Siyama dake zaune a front seat faɗin."Mami yaya Sadiya zamu dauko ne?" shiru Mami ta yiwa Siyama ko magana bata son yi har suka iso ƙofar gidan Ab mami bata furta uffan ba. A bakin gate ta yi parking ta kalli Siyama tana faɗin."taje ta shiga ta kira mata Sadiya kai tsaye Siyama ta fice daga motar a bakin gate ta tsaya tana knocking ta ƙaramar kofa a tsorace maigadi ke faɗin."wanene dan har lokacin daren jiya bai daina gilma masa cikin idanunsa yadda aka dauki mai gidansa rai a hannun Allah kwana ya yi yana zagayawa a banɗaki ya tsinewa Sadiya Kwando-kwando a wannan daren. Ya buɗe ƙofar yana kallon Siyama wanda duk a tsorace yake haushi sosai Siyama ta ji tamkar bai ganeta ba "malam Barau ka buɗemin ƙofa mana. "Babu fa kowa a gidan Hajiya. Da mamaki Siyama ke faɗin."matar gidan nake maka magana. "Ai matar gidan tun jiya da ta cakawa maigidan nan wuƙa aciki bata kwana gidan nan ba. Wani irin bugawa ƙirjin Siyama ya shiga yi jin kalaman Barau maigadi wato kenan sanadin yaya Sadiya yaya Abba ya kwanta gadon asibiti, yadda Mami taga Siyama ta nufo su babu wata natsuwa a tattare da ita yasa ta tsaya tana kallonta shiga kawai tayi cikin motar har hawaye sun cika mata idanuwa cikin rawar murya ta ce."Mami ashe dama yaya Sadiya ita ce silar kwanciyar yaya Abba, a gadon asibiti ? Siyama ta ƙarasa maganar cikin rawar murya batare da Mami ta bata amsar tambayarta ba take faɗin "ya a kayi kika tsaya wajen maigadi ba ki shiga cikin gidan ba? Anan Siyama tasake faɗawa Mami, abunda taji abakin maigadi na cewa yaya Sadiya bata kwana a gida ba kai tsaye Mami ta yiwa motar key batare da ta ƙara bin takan Aydah da Siyama ba dake mai da zance cike da mamakin yar uwar tasu. Wanda ko a mafarki ko a gaske basu taɓa tunanin zata aikatawa yayansu haka ba. Har suka isa gida jikin Mami sanyayye maigadi ta fara tambaya ko Sadiya tazo gida ?"anan ya tabbatar mata da tazo sai dai kuma bata jima ba motar police tazo ta tafi da ita wani irin tashin hankali Mami ta ji ya cika zuciyarta still tana kallon motar Daddy, da har lokacin tana cikin compound cike da ƙarfin hali Mami ta sake kallon maigadi tana tambayarsa Alhaji yana nan lokaci da aka tafi da Sadiya? Ya tabbatar mata da yana nan. kai tsaye Mami cikin gidan ta nufa lokaci ɗaya jikinta ya yi mugun sanyi tasan Daddy ,da zuciya idan aka bata masa rai babu wanda ya isa ya tankwasa shi ko kaɗan hukuncin da Daddy ,ya ɗauka bai yi ba duk da tasan Sadiya bata kyauta ba tana bukatar a hukunta ta Amma bata hanyar miƙa ta hannun hukuma ba, tun da ma an samu abun yazo da sauki ta kalli su Siyama da har lokacin jikinsu ke a sanyayye tana faɗin."su fara yin breakfast sai su tashi su taimakawa Huwaila da girkin rana. Daman mutanen gidan indai ranakkun weekend ne basu cika yin breakfast da wuri ba sai idan sun san suna zuwa islamiyyar safe. Wacce ba kullum suke zuwan ta safe ba sun fi zuwa da yamma, ta samu Daddy a katafaren parlornsa ya yi wanka still yana sanye da jallabiyya ajikinsa ya yi nisa cikin tunanin da yake Mami ta shigo dauke da sallama a bakinta ya amsa sallamar batare da ya kalleta ba. zama ta yi a gefensa Mami ta rasa ta inda zata yiwa Daddy zancen Sadiya cike da ƙarfin hali Mami tace "Alhaji Amma kamar hukuncin da ka daukarwa Sadiya sai nake ganin kamar bai yi ba kar ayi ta yawo damu a gari. Wani kallo Daddy ya yi mata A matuƙar harzuƙe yake faɗin."Ita abunda ta yi ta kyauta? Sadiya ƙaramar Yarinya ce ko me?"shekarar Sadiya 25 a duniya shine kike kiranta ƙaramar Yarinya?"ki daina batamin rai dan Allah. Idan kin san ba magana mai muhimmanci zaki faɗa ba ki tashi ki fita ki barni da damuwar da nake aciki. Ran Mami ya gama ɓaci akan hukuncin da Daddy ,ya dauka tasan tana ƙaunar Abba, fiye da 'ya'yan da ta haifa da cikinta ita kanta bata ji daɗin yadda Daddy, ya yanke hukunci haɗa yaran nata aure ba. musamman Sadiya da tayi gadon kafiya a wajen mahaifinta. kai tsaye Mami parlorn tabari ta wuce ɗakinta sai kai da kawo take a tsakiyar ɗakinta da gaske Daddy yana ƙoƙarin jawo masu abunda ba zai iya gyarawa anan gaba ba, duk wanda ya ji yadda Sadiya ta yi a daren aurenta ba zai yarda ya aureta ba ko kaɗan bata so maganar nan ta kai wurin yan sanda ba. Tafiso su da suka bata komai su warware komai, mutum na farko da ya faɗo mata a wannan lokacin shine Abba, Amma kuma da kunya ta kira Abba ta shaida masa Daddy ya miƙa Sadiya a hannun hukuma mutum na ƙarshe da yazo mata wannan lokacin shine Abdulkarim za tayi magana dashi su tattauna da Abban, ko za a iya samun mafita da sallama Abdulkarim ya daga kiran Mami, ya gaisheta ta amsa shiru ya ɗan biyo na wani lokaci kafin Mami ta soma yiwa Abdulkarim bayani abunda ke faruwa, shima Abdulkarim ɗin shiru yayi yana ta nazarin maganganun Mami kafin yace mata Abba yanzu ya samu bacci idan ya tashi za su tattauna godiya Mami ta yi masa gamida sauke wayar. Wannan ƙaron driver Mami ta haɗa da Siyama da kuma Aydah su suka je asibiti kaiwa Ab abincin rana suma basu jima ba Ab ya uzura musu akan su kira driver ya mayar dasu gida lokacin islamiyya ya yi kusa shiru Aydah ta yi tare da bata rai sosai da alamar ko kaɗan zancen bai mata daɗi ba tasan haka yayan nasu yake ko kaɗan baya son ayi fashin islamiyya ko biki suke basa fashin zuwa islamiyya. Bayan isowar driver Siyama kawai ce ta yiwa Ab sallama daman Aydah tafiyarta ta yi ko kallon gefen da yake bata sake yi ba yasan fushi ta yi bayan tafiyarsu Abdulkarim dake zaune akan sofa ɗin dake girke acikin ɗakin kallon AB yayi da ya rufe idanunsa ɗan gyaran murya ya yi da yasa AB buɗe manyan fararen idanuwansa yana kallon Abdulkarim "Da tun farko wannan yarinyar Siyama ya aura maka ba wannan shashashar mahaukaciyar yarinyar ba. Wani kallo AB ya riƙa yi masa, murya a shaƙe ya ce "ka manta cewa Siyama tana da wanda take so very soon za a sa musu rana ko Sadiya da aka auramin kasan yadda igiyoyin aurenta sukayi min tsaye akai? "To ba ga Aydah ba amma wannan Sadiya tun farko ni dai bata kwanta min a rai ba ta cika rawar kai. "What! Aydah fa kace? "Kwarai kuwa Aydah. "Duka-duka yaushe aka haifi Aydah da har za a aura min ita? She's just 15-16yrs fa. "Koma jaririya ce gara ita sau duba da Sadiya. "Wallahi gara in dawwama da auren Sadiya da in auri yarinyar da nike mata wanka na canja mata diaper. Yadda AB ya yi maganar ya kusan saka Abdulkarim dariya sai dai bai yi dariyar ba, lokaci ɗaya AB ya juya masa baya alamar dai kwata-kwata bayason maganar. Da yamma da Daddy, ya shigo cike da ƙarfin hali Abba ke faɗin."Amma Daddy sai nake ganin kamar kai Sadiya cell bashine mafita ba ka yi hakuri Daddy duk da nasan bata kyauta ba ƙaddara ce da kuma sharrin zuciya ayi mata alfarma acikin alfarmominka Daddy, indai ta nine na yafewa Sadiya duniya da lahira. AB ya karasa maganar da respect a muryarsa kallon da yaga Daddy na yi masa ne yasa ya yi saurin saukar da kansa ƙasa."idan ba a hukuntata ba taya kake so ta karɓi laifinta? "Amma Daddy macce fa ba dace ace ta shiga irin wannan wurin ba. murmushi mai ciwo Daddy ya yi kafin yace."idan ba a hukunta ta ba ba zata gane kuskurenta ba ka bar 'yar banza ta kwana a ƙarkame gobe ko da kuɗi aka bata akace ta nunawa wani wuƙa bama ta caka masa ba za tayi ba. A razane Abba, ke faɗin."Ta yaya za ta kwana a irin wannan wajen Daddy ai sai ta kwaso cuta. A fusace Daddy ya dube shi "Ka daina magana haka Abba, na rantse Sadiya sai ta kwana a hannu hukuma sai tayi nadama sai ta azabtu ko ina yin belinta. Jin rantsuwar da Daddy ya yi jiki a sanyayye Abba ya yi shiru bai ƙara faɗar komai ba, koda magarib da Mami tazo tana jiran Abba ya yi mata maganar Sadiya sai dai Abban bai ce komai ba har lokacin tafiyarta gida ya yi tasan Abba da miskilanci ba zai mata magana ba haka Mami ta dawo gida jiki a sanyayye kuma har lokacin Daddy bai yi mata izinin tafiya police station ba. Wasa-wasa sai da Sadiya ta yi sati guda a cell aka fito da ita ga baki ɗaya kamanninta sun canja tamkar ba Sadiya Bashir ba 'yar gayu da kwalisa duk wannan gayun babu shi, shima a ɓangaren Abba, yana samu sauƙi sosai har ciwon ya fara ƙamewa saboda irin maganguna da yake sha, daga Mami har Daddy babu mai amsa gaisuwarta haka ma ƙannenta da take hango tsanarta acikin idanuwansu har lokacin kuma babu wanda yake yi mata maganar AB ko yayane tana son taji wani hali yake ciki sai dai bataga fuskar tambayar kowa ba a gidan, a bakin Huwaila mai aiki ne ma taji ai yaya AB yana asibiti. Satinsa biyu aka bashi sallama kai tsaye gida aka dawo dashi daga Siyama har Aydah tamkar zasu mayar da AB ciki dan ganin ya samu sauƙi sosai a kuma daren Abba,ya haɗa dukka 'ya'yan nasa Tun kafin Daddy yayi magana zuciyar Mami ta shiga bugawa tana ta addu'ar Allah yasa abunda Daddy zai yanke mai sauƙi ne. Kai tsaye Daddy ya miƙawa Abba takarda da biro fuskarsa babu walwala balle wani annuri yace."Abba ka rubutawa Sadiya takardar saki yanzu ka bani umarni nake baka ba shawara ba. Babu wanda kalaman Daddy basu girgiza shi ba ,cikin rawar murya Abba ke faɗin."Amma Daddy.! Saurin ɗaga masa hannu Daddy ya yi "Abba ko kaima za ka bi bayan Sadiya ne kamar yadda ta zama shaiɗaniyya cikin 'ya'yana kaima haka zaka zama?Da sauri Abba ya girgiza kai hukunci Daddy bai wai ya masa wani irin tsauri bane sai dai yana gani kamar Daddy ya yi gaggawa kaman yadda ya yi gaggawa haɗa auran nasu bayan yasan dole su sami rauni zuciya kafin su karbi junansu a matsayin mata da miji. A maimakon ya yi farin ciki da wannan sakin sai ya samu kansa cikin tashin hankali da muguwar fargaba sai da ya haɗiye wasu busassu miyau kana ya ɗora hannunsa a takardar cikin minti ɗaya ya gama rubutun Daddy ya ƙarbi takardar ya duba ya kalli Sadiya ya miƙa mata takardar fuskar Daddy tamkar hadari wasu irin hawaye masu zafin gaske suka balle acikin idanuwanta sai da Daddy ya daka mata tsawa sa'annan ta karɓi takardar babu inda baya rawa cikin jikinta. Ya kalleta ido cikin ido yace "Wata biyu na baki ki fitar da miji ba za ki yimin zawarci acikin gidana ba. Parlorn tsit ya yi banda shesshekar kukan Sadiya babu abunda ke tashi cikin parlorn , Daddy ya kalli Mami yana faɗin "in-sha-Allah nan da sati guda zan nemo wa Abba matar da ta dace dashi muddin ina raye Abba ba zai taɓa wulaƙanta ba. Abba zai taɓa kukan rashin iyayensa ba. #love story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #kurman Allo. *💃🏻PROMO PROMO PROMO*💃🏻 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jeeddah Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Yanzu 1800 Hudu 1600 - 1400 Uku 1200 - 1000 Biyu 1000 - 800 Ɗaya 500 - 400 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k Promo zai kare zuwa wani satin, garzaya kisai naki🙌🏻💃🏻 ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 [11/24/2023, 3:12 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful love Story) NA JEEDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love Strory #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 005. *RUBUTUN ƳAN TAGWAYE BIYAR KARO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* *KIN TABBATA KIN CIKA MACE? BABBAR MACE DAKE JI DA KANTA? KINA CIKIN MATAN DA SUKA SAN KANSU? WANDA SUKA SAN MUTUNCI DA DARAJAR KANSU? KO KUWA KEMA KINA CIKI SAHUN SU O’O?* *INA KUKE MANYAN MATA? WAƊANDA SUKA SHIRYA DAN GYARA JIKINSU? AURANSU? DA KUMA FARINCIKINSU?” *KUYI MAZA KU GARZAYA GUN FITACIYGA KUMA INGANTACIYAR MAI MAGANIN MATA DA MAZA DAN AMSAR NAKU KU GYARA DA KANKU WATO MEERAH HERBS WACCE TAI FICE GUN KAWO MUKU INGANTATTUN MAGUNGUNA BA TARE DA ALGUS BA.* Mun gwada mun gani 💯 Mun gani mun shaida 💯 Anyi mun gani 💯 MAGANIN SANYI MAGANIN NONO MAGANIN HIPS MAGANIN SLIMMING MAGANIN NANKARWA GYARAN AMARE GYARAN MAIJEGO MALLAKAR MIJI KO MATA SUBULU DA SCRUB MAYUKA NA GYARAN JIKI TURAREN WUTA MATSI MAGANIN NI'IMA MAGANIN TSUMI INFECTION FLUSHER DA DAI SAURANSU…..Uwar gida, Amarya, Budurwa, Saurayi, Ango, Mai gida? Duk mai kuke jira? Kuyi maza ku garzaya Meerah herbs maganin dake ingantace 💯 08142800199 07068558096 A tsorace AB ya ɗago idanunsa ya kalli Daddy zuciyarshi tana wani kalar bugawa sai da ya maida kanshi ƙasa kafin ya ce "Ka gafarce ni Daddy ba wai inaso bijrewa umarninka bane ko kaɗan bana fatar zuwan ranar da ni Abba za ka bani umarni na bijire maka. Kawai dai ina rokon alfarma da ka janye zance neman min aure, a halin yanzu na fi so na ƙarashe rayuwata babu aure. "Zance banza kenan Abba taya ina raye tare da shaƙar numfashi a duniya na barka, babu aure? Burina shine ka yi aure Abba ka haifa min jikoki shiyasa a lokaci da Alhaji Bello Madawaki ya fasa aura maka 'yarsa Rumaisa a bisa hujja da kai kanka bakasan da wanzuwar ta ba. A lokaci raina ya ɓaci kalar ɓaci da bai taɓa yi ba, shiyasa idanuwana suka rufe ruff ba tare da na yi duba da irin abunda zai je ya komu ba na aura maka 'yar uwarka wacce nake gani na isa da ita amma ta watsa min ƙasa a ido. Abba bansan waye ya bankaɗo daɗaɗɗen sirri da na ɓoye tsawon shekaru wanda daga ni sai margayiya Maryam muka san dashi. Abba kai ba shege bane ɗan gaba da fatiha kamar yadda mahaifin Rumaisa ya faɗa ba. Ina da cikakken yaƙini akan cewa ta hanyar aure aka same ka sai dai babban takaicina da ya kasance bansan komai ba akan iyayenka ba. Kuma banida wata gamsasshiyar hujja da zan faɗa maka akan dalili da yasa ka kasance ɗana. Kuma banaso ka sake yi min wata tambaya akan asali iyayenka domin kafin na mallake ka, ka zama ɗana sai da na cika wasu sharuddan koda ace yau iyayenka na asali suka bayyana, ba zan taɓa basu kai ba, domin kai ɗin rayuwata ne Abba ina sonka fiye da 'ya'ya da na haifa. Daddy ya ƙarashe magana tare da ƙoƙarin hanawa hawayen cikin idanuwansa zubowa. Kowacce kalma dake fita daga bakin Daddy tana shiga jikin Abba tare da kassara masa dukkan wani ƙudurinsa saboda haka ba zai iya ja-in-ja da Daddy ba. Tun sanda AB ya baro Parlorn Daddy ya dawo ɓangarensa ya kwanta akan sofa tunani ya yi masa yawa, zuciyarsa tana cike da alhini abunda zai faru dashi anan gaba. Ƙarar wayarsa dake kan centre table ce ta dawo dashi daga natsuwarsa da ta kaurace masa suna Rumaisa Madawaki ya gani, sai da gabansa ya faɗi yana matuƙar ƙaunar Rumaisa ita ce mace ta farko da ya fara soyayya da ita, sai kuma ga wannan ƙaddarar ta raba su. Sai da ta jera masa kira huɗu ana biyar ya yi picking, yana ɗaura wayar a kunnensa tun kafin ya yi magana ya ji shesshakar kukan Rumaisa bata yi magana ba sai faman gunji kukanta take yi, shi kuma bashi da kuzari da zai iya rarrashinta, shi kansa yana bukatar wanda zai rarrashe shi. Tsawon lokaci suka dauka a haka ita tana kuka shi kuma yana sauraren kukan nata, daga bisani ya kashe wayar tare da blocking dukkan numbers ɗin Rumaisa, saboda komai ya zo ƙarshe a tsakaninsu, soyayyarsu ta zama tarihi dukkan alƙawarruka da suka yiwa junansu sun bi ruwa, saboda haka bai ga amfani ci-gaba da ajiye numbernta a wayarsa ba. Bayan fitar su AB daga parlorn Daddy Mami ta kalli Daddy a natse cikin sanyi murya gami da mutuwar jiki ta ce "Alhaji nima da za ka ɗauki shawara ta da nace ka haƙura da zance nemawa Abba aure da kayi haƙuri ka ɗan jinkirta zuwa wani ɗan lokaci. Musamman idan ka yi duba da hali da yake ciki. "Kin ga Mariya ki yi min shiru ki adana shawararki banaso idan ma shawara kike so badawa ki ba 'yarki domin idan lokaci da na ɗiba mata ya cika ba tare da ta kawo mijin aure ba tabbas za ta sha mamakin kalar hukunci da zan yanke akanta. "Amm.... "Ya isa Mariya na gama magana karki dawo min da hannu agogo baya. Ba yadda Mami ta iya dole ta ja bakinta ta tsuke duk da a can ƙasan zuciyarta tana jin zafin abinda Daddy ya aikata taya zai dauƙo ɗan wasu, wasu ma da bai da cikakken sani akansu ka mayar dashi naka sannan kuma ka ɓoye hakan ba tare da ka sanar da makusantan ka ba. Wato nufinsa koda mutuwa yayi Abba zai yi gadonsa ita kam wannan fallasuwar sirrin nasa gaba ta kaita da haka kawai za a cuce ta a dauko ɗan shege a gauraya shi da 'ya'yan halas. Da shikenan Abba zai mamaye dukiyar da batasa ba. Murmushin gefen baki tayi tare da miƙewa ta koma nata parlor. Tun sanda Sadiya ta baro Parlorn Daddy take kwance a ɗakinta tana kuka ta rasa dalili da yasa take jin ƙunci can ƙasan zuciyarta, duk lokaci ta dubi takardar sakinta da Daddy ya damƙa mata a hannu sai sautin kukanta ya daɗa ƙaruwa. Siyama ce ta turo ƙofa ta shigo ta daɗe tsaye rungume da hannuwanta a ƙirji tana kallon Sadiya dake rare kuka kafin ta girgiza kai tare da sauke hannayenta, ta taka a hankali ta nemi kusa da ita ta zauna cikin sanyi murya ta kira sunanta "Yaya Sadiya! Sadiya bata iya amsawa ba saboda kukan da take yi kawai dai ta ɗago ta kalli Siyama, kana ta sake maida kanta ta cigaba da kukanta, a wurinta yin kuka shi kaɗai ne mafita da yai mata saura. "Ni wannan kukan naki yaya Sadiya na rasa da wane suna zan kira shi kukan farin ciki, kukan rashin cimma buri ko kuma kukan raini wayau? Cike da madaukakin mamaki Sadiya ta ɗago tana kallon Siyama da farko batada niyar kulata koda kuwa ta zo ne da zimmar rarrashinta, amma kuma wannan furunci da tayi yasa ta haɗiye kukanta har ta kai da furta "Me kike nufi Siyama??" "Abinda nake nufi ki ware guda daga cikin dalillai dana lissafa da yake da nasaba da wannan kukan da kike yi. "Bai zama dole sai nayi abinda kike so ba Siyama na fahimci dukkanku gidanan bakwa tausaya min yaya Abba shi kaɗai ne damuwarku. "Dole mu ɗura damuwar mu akan yaya Abba domin ya cancanci a tausaya masa saɓani ke ɗin da nake ji haushi da takaicinki yaya Sadiya, ina tabbatar miki da cewa kin yi baƙar asara na rasa gwarzo kuma jarumin namiji irin Ya Abba, ba kuma za ki san da ingancin magana ta ba sai ana gaba. Wallahi yaya Sadiya sai kin yi nadamar abinda kika yiwa Ya Abba sai ki yi danasani tozarta Daddy da kika yi. Siyama tana ƙarashe magana ta tashi ta fice abinta ta bar Sadiya da rusar kuka. Sannu a hankali Aidah ta kama handle ɗin ƙofar parlorn AB lokaci da Aidah ta shigo parlorn ta hango shi kwance wasu hawaye masu mugun ɗumi ke ta sintiri akan tattausan kumatunsa da wani kalan sauri Aidah ta isa gabanshi ta zube guiwayoyinta abu na farko da ta fara yi shine ɗaura tafin hannunta akan kamatunsa ta shiga goge masa hawaye tun sanda ta zube a gabansa natsuwarsa ta dawo jikinsa bai yi yunƙuri hana ta goge masa hawaye ba, sai ma kallon innocent face ɗinta yake idan aka cire Daddy to Aidah ita ce mutum ta biyu dake bala'in sonshi ko rashin lafiya yake yi Aidah ta dinga kuka kenan har sai ya sami sauki. Shiyasa sometime idan yana rashin lafiya yake ɓoyewa, ko kaɗan bata so ta ganshi cikin damuwa yanzu nan za ta rikice. AB yana gani ta fara kuka ya zabura ya tashi zaune ya yi ƙoƙari ɓoye damuwarsa ta hanyar, kama hannayenta ta miƙe tsaye kusa dashi ya zaunar da ita kafin ya kai da yi magana har ta riga shi "Ya Abba kuka kake yi ko wuri yana maka ciwo ne na kira Daddy ya maida ka asibiti?" Ta yi magana tana kama t-shirt ɗin jikinsa ta ɗage ta sama tana kallon gun da Sadiya ta caka masa wuƙa, sai dai wurin har ya fara baƙi-baƙi alamar warkewa hannunta ta kai ta shafa tabon dinkin da aka yi masa yadda take lailaya fatar cikinsa ya ji tsigar jikinsa ta mimmiƙe babu shiri ya ture hannunta tare da gyara rigarsa ada fiye da wannan yana shiga tsakaninsa da Aidah bai taɓa ji komai ba. Sai gashi yau da yasan babu wata alaƙa ta jini a tsakaninsu tana taɓa shi ya fara ji feeling shi kan har gobe kallo su Aidah yake a matsayin ƙannansa na jini. Idan ma ya ce ya sauya masu matsayi ina yaga wasu da zai bugi kirji yace 'yan uwansa ne shi kan iyayensa sun cuce shi da sun san cewa basa farin ciki haifarsa miyasa tun yana gudan jini ba su zubar dashi ba, gashi nan sun haife shi sun jifar dashi sun barshi da fuskanta ƙalubale irin daban-daban. "Ya Abba please talk to me. Muryar Aidah ya tsikayi a dodon kunnensa cikin shagwaɓar nan nata da ya zama jini jikinta. "I'm fine Baby Aidah kawai dai ina cikin damuwa na rashin sani su waye iyayena taya aka yi na zo hannun Daddy jefar dani suka yi ya tsinta ko kuma a gidan marayu ya yi adopting ɗina??" Baby Aidah ina so nasan amsoshin waɗannan tambayoyi sai dai kuma Daddy ya yi min gargaɗi akan kada na sake yi mishi zancensu kuma ba zan iya take umarnin Daddy ba. Sai da Aidah ta sauke numfashi kafin ta gyara zamanta ƙugunta ya ƙara mannewa dana AB "Ya Abba ka yi haƙuri ka ɗaure ka cire duk wata damuwa aranka Allah yana sane da hali da kake ciki a sannu zai warware maka dukka damuwarka, wannan abin zai zo ya wuce kamar ba a yi ba. "Haka ne Baby Aidah in-sha-Allah zan yi kokari na bi shawararki. "Thank you Yaya Abbana tashi mu tafi sport field mu yi wasa kwana biyu nayi missing buga wasa dakai, yaya Siyama bata iya komai ba a table tennis. Murmushi ya yi wanda bai wuce iya fatar bakinsa ba yasan Aidah tana yi haka domin ta kawar masa da damuwar da yake ciki, shiyasa bai mata musu ba ya ce ta je ta canza kaya ta sami shi a field, da gudu ta fice Siyama ta biyo ta zuwa field ɗin suna wasa tana musu tafi da sowa yayin da ihunsu ya kai kunne Sadiya da sauri ta taso daga kan gado ta nufi window ta leƙa ta hango yadda AB yake ta zabgar fara'a ga walwala akan fuskarsa, tun ba a je ko'ina ba farin ciki da walwalarsa sun fara dawowa jikinsa saɓani ita da take ji wani kalar ƙunci haɗe da baƙin ciki yana nuƙurƙusar zuciyarta. Sai da aka fara kiran sallar magarib kana suka dawo cikin gida. A washegari Daddy ya umarci AB ya koma bakin aikinsa wanda shine ceo na Kamfanin Daddy na siyarda motoci moon light Automobile industry, ba wai iya motoci kamfani yake siyarwa ba, suna sai da cars accessories da kuma abubuwan gyaranta Moon light Automobile industry kamfani ne da ya shahara saboda haɗin gwiwa ne da kamfanin whitepaper Automotive industry Germany, shiyasa motoci da suke kamfani suka fita daban da na sauran kamfanoni. Kaitsaye AB ya wuce ofishin sa dake hawa na huɗu secretary shi ta shigo ta kawo mishi schedule ɗinsa na yau ya duba firstly yana da meeting da employees na kamfani kana akwai online meeting da zai yi da whitepaper Automotive industry throughout bai huta ba saboda akwai sabuwar mota da kamfanonin nasu za su yi lunching sai around ten na dare ya dawo gida. #Love story 2023/2024 #Jiddah Aliyu #Asmy b Aliyu #team tagwaye novels #kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [11/25/2023, 8:27 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye Novels 006. Assalamu Alaikum Hajiyata kinada labarin kayan Egypt da muke kawowa kuwa to in baki saniba matso kusa kiji Ainam stockpile mun kawo muku kaya na gani na fada na gayu wainda sai wance da wance ake gani dasu ba kano made bane kunsan a koda yaushe burinmu mu kawo muku unique abu.Available ne ba jira zakiyi akawo ba muna bada sari muna kuma aikawa koina,duk abinda kike bukata hajiyata ki latsoni kawai wa.me/2348146766440 Ko baki siyaba yanzu kiyi saving number ta murika ganin status din juna Nagode jikinsa ga baki ɗaya ya yi masa nauyi tamkar wanda aka yiwa duka. Yana tura ƙofar parlornsa idanuwansa suka sauka akan fuskar Aydah dake zaune a ƙasa ta jingina bayanta ga soofa bacci ya ɗauke ta. Sai da ya ƙare mata kallo kana ya girgiza kai ya aje briefcase ɗinsa akan centre table kusa da wasu luxury warmers dake aje akan centre table ɗin ya nufi tv dake aiki wacce yake da tabbaci Aydah ce ta kunna ta ya rage volume, ya wuce ɗaki ya yi fresh up ya dawo parlor jikinsa sanye da pajamas sky blue in color ya zauna akan soofa da take jingine ya ɗan bubbuga kafaɗarta gami da kiran sunanta "Baby Aydah! Baby Aydah! Na dawo tashi ki je ki kwanta. A hankali ta ware matsakaitan idanuwanta akan fuskarsa da sauri ta gyara zamanta tana mutsitsika idanuwanta da bayan hannunta "lah! Ya Abba yaushe ka dawo?? "Yanzu nan. "Ka ci abinci? "A'ah amma zan ci. "Ga shi nan akan centre table na ajiye maka bari na zuba maka. "Dare ya yi Baby Aidah ki tashi mu je na raka ki idan na dawo daga raka ki zan zuba da kaina. "Shikenan. Ta faɗa da sanyi muryarta miƙewa AB ya yi ya miƙa mata hannayensa ta kama ta tashi tsaye suka fito compound ɗin gidan suna tafiya side by side, Aydah ta ɗaga kanta sama taga yadda taurari suka yiwa sama ƙawaiya gwani sha'awa ta dawo da ganinta kan AB "Ya Abba ɗaga kanka sama kaga yadda taurari nan suka haskaka sararin samaniya. Ba tare da ya tanka mata ba ya ɗaga kansa sama ya daɗe kafin ya dawo da ganinsa kanta yana faɗin "Tsalki ya tabbata ga Ubangiji da ya halicci sama ya ƙawata ta da taurari. Murmushi Aidah tayi tana gyaɗa kai kafin ta sake maida ganinta sama da sauri tayi pointing yatsanta akan wasu taurari guda uku da suka ware kansu sai dai ta tsakiyar su tafi haske "Ya Abba duba ka ga wadancan taurari guda uku. Idanuwansa ya kai gun da take nuna wa "Na gani. "Me ka gani?? "Taurari guda uku sai dai ta tsakiya ta fi su haske. "Ina nufi me ka fahimta akan taurarin?? "Bani da ilimin taurari. Ya yi magana yana kallonta tare da sakar mata murmushi saboda yasan shirmenta ne ya motsa. "Waɗancan taurari guda biyu ka ɗauke su a matsayin Yaya Sadiya da aunty Rumaisa. "Uhm! To ita kuma wancan guda ɗaya mai haske a matsayin wa zan ɗauke ta?? Yayi magana yana siririyar dariya dama yasan za a yi haka. Tsayawa tayi tare da fuskanta shi tana kwaɓe fuska gami da cuno baki gaba. "Ki faɗamin mana wacece mai haske nan?? Cikin shagwaɓaɓbiyar murya ta ce "Ka canka mana. "Kinsan ni ba kwararre bane a canka kawai ki faɗamin. Cikin zallan shagwaɓa take buga ƙafafuwanta akan interlock "Dan Allah ya Abba ka canka ina ji a jikina a wannan karo za ka canka daidai. "Ke dai in za ki faɗamin ki faɗa kawai idan kuma ba za ki faɗa ba shikenan sai da safe. Murmushi tayi haɗe da juyawa tana faɗin "Sai da safe Ya Abba. Har tayi taku biyu zuwa uku sai kuma ta juyo da sauri ta kira sunansa har shima ya juya saboda dauriya kawai yake yi amma yunwa yake ji kamar hanji cikinsa zai tsinke "Ya Abba ka biyo ni bashi amsar tambayar ka nayi maka alƙawari wata rana zan gayamaka wacce wancan tauraruwar da tafi yaya Sadiya da aunty Rumaisa haske. Bata jira ya yi magana ba ta buɗe ƙofar shiga main parlor da kallo ya bi ta dashi yana wani kalar murmushi. A washegari kasancewar Aydah tana da test na biology shiyasa bata jira AB ya tashi daga bacci ba ta wuce school. *ALHAJI BELLO MADAWAKI MANSION* Rumaisa tana kwance a ɗakinta tun daga ranar da aka fasa aurenta da AB ta daina fita ga baki ɗaya ta yi wata irin rama, kullum cikin kuka take musamman yanzu abin nata ya ƙara tsananta a dalili blocking ɗinta da AB ya yi, tana son AB fiye da komai shi ne rayuwarta rasa shi a gareta ba ƙaramin nakasu ne a rayuwarta ba. Mahaifinta ya kasa fahimtar irin ɗimbin son da take wa AB bata damu da rashin asalinsa ba. A haka take sonsa idan har bata aurensa bata ji za ta iya aure a rayuwarta. Mahaifiyarta ta turo ƙofar ɗakin nata ta shigo duk sallama da take yi Rumaisa bata amsa ba saboda tayi zurfi a tunani AB da irin soyayyar da suka shimfiɗa a can baya, kusa da cikinta Hajiya Nafisa ta zauna tare da ɗora hannunta akan sumarta a hankali take shafa sumar kan Rumaisa kafin cikin sanyi murya ta kira sunanta "Rumaisa! Firgigit Rumaisa tayi kamar wacce aka tasa ta hanyar watsa mata ruwan sanyi "Na'am Ammi. "Rumaisa har sai yaushe za ki daina wannan koke-koke naki?" Sanin Kanki ne Rumaisa mahaifinki ba zai taɓa aura miki Abba ba to don me da ba za ki cire shi daga zuciyarki ba? Babu kalar rokon da ban masa ba akan ya haƙura ya aura miki zaɓin ranki ko don wanzuwar farin cikinki amma ya yi biris dani jiya da dare har cewa ya yi idan na sake masa maganar Abba a gidanan zai yi mummunan saɓa min. Mahaifinki mutum ne mai matuƙar zafin kai da kafuwa wanda maganar fatar baki ba za ta iya canza masa ra'ayin sa ba. Saboda haka dan Allah ki cire damuwa aranki ki dawo da walwalarki nayi magana da yayarki Shema'u gobe za ki tafi Abuja wurinta ki kwana biyu watakila ki fi samu sakewa a can duba da nayi da irin shaƙuwar dake tsakanin ku. Har Ammi ta dasa aya a zancenta Rumaisa tana sharar hawaye kafin cikin dusashewa murya ta ce "Ammi ba zan iya nisanta da AB ba idan na tafi Abuja hakan yana nufi zan daina ganinsa kwata-kwata zuciyata ba za ta iya jure hakan ba. A halin yanzu ma zuciyata zafi take min Ammi zuciyata za ta buga taɓa ki ji Ammi watakila mutuwar zan yi soyayyar AB za ta kashe ni. Ta ƙarasa magana tare da ɗora hannun Ammi a ƙirjinta sosai Ammi ta firgita da jin yadda zuciyar 'yarta ke bugawa, da wani irin mugun ƙarfi da sauri ta jawo Rumaisa zuwa jikinta ta rungume ta wani irin tausayinta take ji ita kanta shaida ce akan irin zazzafar soyayyar da take wa Abba Bashir. Sadiya ta ɗauki wayarta dake aje a gefenta ta sake gwada kiran numbern Hafeez Sale a karo na ba adadi, tun ranar da ya dawo da ita gida idan ta kira wayarsa bata samu da alama ya yi blocking ɗinta. Tayi kuka har ta gaji tana son Hafeez Sale tamkar rai da numfashinta rabuwa dashi wani al'amari ne da zuciya da gangar jikinta ba za su iya ɗauka ba. Duk wanda ya san Sadiya ada a yanzu idan ya ganta da matuƙar wahala ya gane ta saboda ta rame ta yi baƙi sai ta yini guda curr batare da taci abinci ba tun Mami tana shareta har ta dawo rarrashinta kuma har izuwa wannan lokaci idan ta gaida Daddy baya amsawa hakazalika Siyama da Aydah basu shiga sabgarta. Cikinta da ke mata mugun ƙugin yunwa yasa ta fitowa ta shiga kitchen ta haɗa tea ta fito main parlor ta zauna, a hankali take sipping tea ɗinta AB ya turo ƙofa ya shigo bakinsa ɗauke da sallama, ta ɗago idanuwansu suka sarƙe tun faruwar wannan al'amari take wasan ɓoya dashi, kunyar haɗuwa dashi take ji. Sannu a hankali take bin jikinsa da kallo ya yi masifar yiwa idanuwanta kyau yana sanye cikin black blue color suit ya ɗura white necktie wanda ya yiwa three knot style ƙafarsa sanye da black men loafers sosai shigar tayi masa kyau ga ƙamshin turarensa da ya gama cika mata hanci. Kasa yi masa magana tayi shiyasa ta yi sauri sadda kanta ƙasa shima ya ɗauke kai tamkar bai ganta ba ya wuce dining area.sosai jikin sadiya yayi wani irin sanyi tamkar ba yayanta ba da tasani Acan baya sai wani shasshareta yake.lokaci ɗaya idanunta suka cicciko da kwallah gashi tunda ta dawo gidan babu wanda yayi mata maganar komawa makaranta tana shakkar tambayar daddy,dan har lokacin idan ta gaishesa baya amsa mata.ta qara kallon cikin dinning area din,yaya Abba ,kawai ne zaune a wurin har lokacin yana sipping Black coffee da wayarsa a hannu yana daddanata.qarfin hali tayi ta miqe tsaye ta nufi cikin dinning area din xuciyarta na wani irin bugawa tsaye tayi dan nesa dashi ko kallon wurin da take bai yadda yayi ba.xuciyar sadiya lokaci ɗaya ta kara qaryewa cike da qarfin hali take faɗin ."dan Allah yayanmu kayi hakuri wallahi sharrin shaidan ne."ta qarasa maganar cikin rawar murya nan ma dai AB.tamkar tana magana da dutsi haka yayi mata banza daman AB.badai miskilanci ba ,zata qara buɗe baki tayi magana ya dire cup tea din hannunsa ya bar cikin dinning area din da wata irin sassarfa da kallo ta bisa tana jin wata irin faduwar gaba wanda bata taɓa jinsa akan yayan nata ba.har dare abunda yayan nata yayi mata ya kasa barinta da irin yadda ya shareta tamkar bai taɓa saninta ba a duniya.kusan qarfe tara ta shigo dakin Mami ta sameta kan sallaya da carbi a hannunta akan doguwar soofa ta xauna tana jiran Mami ta gama azkar.jin tayi an turo kofar Sukayi ido biyu da AB.sai da gabanta ya fadi suna haɗa ido yayi saurin dauke idonsa cikin nata.sanye yake cikin cooffe brown din jallabiyya da tayi matuqar haske farar fatarsa. Shi bai juya ba shi bai shigoba still yana riqe da handling din kofar. Cikin rawar murya sadiya ta gaishesa babu yabo babu fallasa ya amsa ya juya Yabar kofar na Mami batareda ya jira mamin tagama ba.bayan Mami tagama sallah ta kalli sadiya da ta zama (Absent minded)sai da Mami ta kira sunanta fitgigit ta fado duniyar tunanin da ta tafi sai yanzu ta qara tabbatarwa watau yayanta yafi hafeez class da wani irin quality ashe idonta rufewa yayi?"gaskiyyar siyama ne da Take fadin zatayi na dama lokacin da bata da amfani ,to idan bazakiyi magana ba tashi kibarmin daki."Mami ta faɗa a mugun fusace da alamar sadiyar ta kaita bango cikin rawar murya sadiya ke faɗin."daman Mami akan maganar yaya Abba ne,da kuma maganar komawa school Dina nagaji da zaman.kuma yaya Abba,sai wani shareni yakeyi cikin gidan nan tamkar wata makiyarsa idan ina a wuri baya zama.shi bai san ƙaddara bane?"har hakuri na basa fa.maganar Abba,mu ajeta a gefe can tsakaninku lokacin da kuka bata ban sani ba,maganar karatu bana da iko akan karatunki kije ki samu daddy."hawaye lokaci ɗaya suka cika idon sadiya tana faɗin."to Mami kiyi masa maganar komawar tawa makaranta.idan dai ke zakiyi masa kije kiyi masa babu ruwana ki daina sakani a lamurranki sadiya."ganin dai da gaske Mami bazata saka baki ba yasa tabar dakin na Mami,a parlor ta tarar da AB Shida Aidah tana riqe da wayarsa tana bangalar Daria shi kuma sai murmushi yake wani irin kunci taji ya cika mata xuciya daga Aidah har AB babu wanda yabi takanta juyawa tayi ta koma sama tana jin idonta na cika da hawaye lokaci ɗaya. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [11/26/2023, 3:44 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novel's *RUBUTUN ƳAN TAGWAYE ZANGO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* PAID BOOK 007. *MOON LIGHT AUTOMOBILE INDUSTRY* AB yana zaune a office ɗinsa yana duba wasu car design da whitepaper Automotive industry suka tura masa yana selected ɗin wanda suke buƙata a kamfani nasu, secretary shi ce ta shigo tare da sanar dashi yana da baƙuwa amma ta duba bata da appointment dashi. Sai da ya kwaɓe fuska kafin ya tambaye sunanta "Rumaisa Madawaki! Secretary tasa ta faɗa. "Let her in. Ya yi magana kaman mai ciwon haƙora jim kaɗan da fitar secretary tasa Rumaisa Madawaki ta turo ƙofa tashigo tana sanye da turkish Abaya maroon in color tayi rolling da veil ɗin rigar sosai rigar ta karɓi fatar jikinta kasancewar fara duk da fari nata ta ɗan sirka shi da mayukan nan na zamani shiyasa skin ɗinta ya yi wani ɓauuu farinta har ci idanuwa yake. Tun kafin ta ƙaraso AB ya fara shigar ƙamshin turarenta a hankali ta tako yayin da idanuwansu suka sarƙe sosai ya hango ramar da tayi, nan take ya ji zuciyarsa ta karye amma sai ya yi kokari basarwa baya so ta silarsa su dawo da hannun agogo baya. Sai da ta iso gaban desk ɗinsa ta tsaya tare da rungume hannuwanta a ƙirji kallo-kallo suke wa juna shine ya fara janye ganinsa, gami da kawar da kansa gefe ɗaya. "Ban taɓa tsammani akwai wani dalili da zai zama sanadi rabuwar mu a faɗin duniya nan. Abba idan kai ka shirya haƙura da soyayyarta ni kan yanzu ma na ɗaura ɗamarar yaƙi da duk wanda zai kawo min cikass a soyayyarka. Ta ƙarasa magana tare da zama akan kujerar dake gaban desk ɗin tana kuma facing ɗinsa, ɗan bazawari murmushi AB ya yi shi kaɗai yasan irin raɗaɗi da yake ciki na soyayyarta sai dai bai ga amfani soyayyar ba tun da ba za ta kai su da mallakar juna a karkashin inuwar aure. "Ka haƙura dani ko Abba? Tayi magana hawaye na fitowa daga kwarmin idanunta. Sai da ya ɗan wargaza Sumar kansa kafin cikin raunatatciya murya ya ce "Ba zan taɓa iya daina sonki ba Rumaisa sai dai ya zama mana dole da haƙura da juna, duk wata soyayya da muke wa junan mu bata da wani amfani tun da mahaifinki ba zai iya mallaka min ke a matsayin matata, ta sunnah ba. "AB idan har da gaske ba ka haƙura dani ba to ka bani wani ɗan lokaci in-sha-Allah zan daidaita al'amurranan zan nemi hanyar da Dad zai amince da aurenmu. "Idan ma nace na jira ki Rumaisa ni kuma nawa mahaifin ya zan yi dashi domin na daukar masa alƙawari nisanta daga gare ki. "Wacce irin magana ce kake faɗa Abba? Ko dai dama ba ka ji soyayyata kwatankwacin yadda nake jin taka?" Rumaisa ta faɗa cikin muryar kuka. "Ba haka bane Rumaisa ke kanki shaida ce akan matsananci son da nake miki you're my first love how do you think zan daina sonki faratt ɗaya?? "Dole nayi wannan tunani Abba saboda hali da ka nuna min ka daina picking calls ɗina daga ƙarshe ma sai blocking ɗina ka yi, Abba wallahi ba zan iya rayuwa idan babu kai. Ka bani haɗin kai mu yi yaƙi kwatar soyayyarmu. Da girar ido ɗage yake kallonta yana ɗan shasshafa kwatatce sajensa, kafin ya ce "Rumaisa bana so mu yi abunda zai saɓa ra'ayin iyayenmu, mu yi haƙuri mu bi su yadda suke so a rayuwa ba komai kake so kuma ka same shi ba. After all this time Daddy yana ƙoƙarin ganin ya faranta min saboda haka ba zan iya abunda zai ɓata mishi rai ba. "Nima ban ce ka yi abunda za ka ɓata wa mahaifinka ba kawai i want my love back ka dawo da soyayyar da kake min Abba ka ɗaukar min alƙawari za ka jirani har zuwa lokaci da Dad ɗina zai amince da aurenmu. Girgiza kai ya yi tare da faɗin "hakan ba zai yiwuwa ba Rumaisa mu haƙura da juna kawai. "Ba zan iya ba Abba idan ban same ka ba mutuwa zan yi wallahi zuciyana zai buga.. Ta ƙarashe magana tare da saukowa daga kujera ta durƙusa on her knees ta haɗe hannayenta guri ɗaya cikin muryar kuka take faɗin "Dan girman Allah Abba karka bar ni rabuwa da kai zai iya cutar dani ka tausayawa rayuwata. Da wani kalan sauri AB ya taso ya kama kafanɗunta ya tashe ta tsaye hakan ya bata damar faɗawa ƙirjinsa hugging ɗinta ya yi tana kuka yana rarrashinta da daddaɗan maganganu hakan yasa ta daina kuka, ya ja ta zuwa kan ɗaya daga cikin cushion ɗin da ke cikin ofishin nasa ya ci-gaba da rarrashinta da kalaman soyayya masu sanyayya zuciya. "Da gaske nake yi AB idan babu kai ba zan iya rayuwa ba dan Allah karka sake juya min baya. Ka duba yadda na lalace tun daga ranar da aka fasa auren mu har kawo yau ɗinan rabon da na zauna naci abincin kirki iyakacina nasha tea shima sai naga yunwa za ta min illah nake ɗan kurɓawa sama-sama. Rumaisa ta faɗa tana ɗauke hawaye da suka sake silalo mata a kumatu. Sai lokaci da tai wannan magana AB ya ƙare mata kallon tsaf da gaske kuwa ta rame irin muguwar rama nan wacce da an ganka sai an tambaya ba za a shaida kana ciki damuwa, da sauri ya miƙe tare da nufar desk ya ɗauke car key gami da wayoyinsa yana faɗin "Tashi mu je mu ci abinci dama lokaci tashi na lunch ya yi. Rumaisa tayi murmushi tare da miƙewa ta ɗauki handbag ɗinta yana gaba tana bin sa a baya yayin da AB ke ci-gaba da faɗin "Daga yau duk abunda zai faru Rumaisa kada ki sake bari kanki da yunwa ina sonki sosai ba zan iya jurewa ba idan wani abu ya same ki. Ya ƙarashe magana daidai suna isowa parking lot kowanne su ya shiga motarsa suka fice daga kamfani. Alhaji Sanusi dake tsaye jikin window ofishinsa idanuwansa akan AB da Rumaisa wani kololon baƙin ciki ne ya dunƙule masa a kahon zuciya a fusace ya baro jikin window ɗin ya ɗauki wayarsa ya yi dialling numbern abokin ci mushe sa "Alhaji Umar kaga abinda naga ni kuwa?? "Me ka gani Alhajin Allah? Alhaji Umar ya faɗa har yana haɗawa da wata 'yar bazawarar dariya. "Alh Umar wannan shegen yaro tsintatce yanzu nan naga ya fita daga kamfani tare da 'yar gidan Bello madawaki?" "What?? "Wallahi nake gayamaka ai na zaci ka ga fitar su hankalina ya yi mugun tashi Alh Umar kada waɗannan shegun yara su mayar mana da aiki baya. "in-sha-Allah hakan ba za ta taɓa faruwa ba bari nayi gaggawar kiran Alh Bello madawaki na ƙara rura wutar al'amari. "Haka nake so mutumina. Alh Sanusi ya faɗa tare da hanging up yana saki murmushin mugunta, alƙawari ne ya ɗaukar wa kansa ba zai taɓa bari Alhaji Bashir da shegen ɗansa AB su sake farin ciki a rayuwarsa, shekaru 15 da kafa wannan kamfani shine silar hasassa shi duk wani cigaban kamfani shine ya kawo shi burinsa a ce yafi kowa damawa a wannan kamfani a matsayin sa na ƙani Alhaji Bashir da suke uwa ɗaya amma abin takaici sai da ya gama shan wahala kamfani ya haɓaka ya zama lamba ɗaya, Alhaji Bashir ya ɗauki babban matsayin da yake hari ya ba wa ɗansa AB duk da haka ya danne zuciyarsa ya cigaba da aiki a kamfani daga hawan AB kujerar CEO (Chief Executive officer) shegen yaro nan ya dinga bincike da bin diddigi shige da fice kuɗaɗen Kamfani har yai nasarar gano irin almudahana da suka dinga yi shi da financial director, AB bai bar su ba har sai da suka dawowa da kamfani kuɗaɗen da suka sata wannan abin da yai musu shine silar da yasa account ɗinsu yai ƙasa har yau basu farfaɗo ba. Sannan kuma ya bi ya tare gaba ya tare musu baya duk wani motsinsu akan idanuwanshi. Wannan shine silar da ya haifar da zazzafar ƙiyayya tsakanin AB dasu Alh Sanusi daga wannan lokaci suka shiga bincike hanyar da za su kawo ƙarshen AB a kamfani. Alh Sanusi ya yi nisa da tunani ƙarar buɗe ƙofa da Alh Umar ya yi ya dawo dashi natsuwarsa ba tare da ya ƙarasa tunano irin gada zare da suka ɗannawa AB da mahaifinsa. *GUSTO RESTAURANT* AB da Rumaisa suna fita kai tsaye Gusto restaurant suka nufa AB yana gaba tana bin sa a baya AB ya zaɓi Gusto restaurant a dalili ya yaba da daɗin abincinsu ga kuma wurin babu haniya, bayan an kawo musu menu kowanne su ya zaɓi abunda yake so yaci koda suka kammala ci abinci ƙarfe 3:00pm AB yana duba wristwatch ɗinsa sai da gabansa ya faɗi kasancewa da Rumaisa ya manta da Aydah da ya yiwa alƙawari zai je ya yi picking ɗinta a school agaggauce ya sha ruwa ko ta kai juice ɗin da aka kawo masa bai bi ba ya miƙe tare da kallon Rumaisa yana faɗin "Habibty I have to go bansan cewa lokaci ya tafi sosai har haka ba. Cike da zallan mamaki ta dire spoon ɗin hannunta ta ɗago "Habibi ina za ka tafi kake wannan saurin?? "Zan je nayi picking Aydah a school kinga lokaci ya tafi sosai sai mu yi waya. Yana ƙarashe magana bai jira jin ta bakinta ba ya nufar entrance ɗin fita da sauri ta bishi da kallo wannan hali na AB dangane da irin wannan kulawar da yake ba wa ƙannansa yana bala'in ƙona mata rai duk wani abu da ya shafe su sai ya dinga wani rawar ƙafa more especially wannan brat girl Aydah, yanzu da tasan babu alaƙa ta jini a tsakanin shi da Aydah sai ta wani irin mugun kishi ya lulluɓe ciki da wajen zuciyarta, tsabar takaici sai ture abinci tayi ba don ta ƙoshi ba ta ɗauki handbag ɗinta a fusace ta bar restaurant ɗin. *CRESCENT INTERNATIONAL SCHOOL* Tun kafin AB ya yi parking ya hango Aydah tana ta faman kumbure fuska murmushi ya yi yasan yau sai sun yi daru da ita Aydah ba dai rigima ba har ta siyarwa tana dashi. Sai da ya yi mata horn kusan sau uku kafin ta nufo wurinsa duk da yasan ta ganshi tun ma kafin ya yi parking ita a dole fushi tayi fushi, tana zuwa buɗe backseat ta jefa backpack ɗinta kana ta zagaya ta buɗe front seat ta zauna, lulu eyes ɗinsa ya watsa mata yana sakar mata da tsadadden murmushinsa. Turo baki tayi gami da kauda fuska tana ci-gaba da kumbure-kumburenta cike da tsokana ya fara yi mata waƙar da yake mata sanda tana yarinya muddin yana so saka ta kuka a wancan lokaci ita yake mata "Aididi, Aididin ya Abba mai majina a hanci tayi k.... "Ya Abbaaaaa! Please stop that horrible song of yours na tsani wannan waƙa bana sonta. Aydah ta faɗa tamkar cikin muryar kuka, yadda ta kwabe fuska yai masifar ba wa AB dariya sosai ya dinga yi mata dariya ita kuma ta ƙara hasale wa sai kawai ta kwaɓar da seat ta kwanta tare da lumshe idanuwanta "okay I'm sorry my little baby gayamin me kike so na siya miki kafin mu isa gida?" Taƙi ta tanka masa sai rarrashinta yake tai biris dashi "Shikenan tun da ba za ki kula ni ba nima nayi fushi daga yau mun bata karki sake yi min magana. Ya yi magana shima yana turo baki kaman ita. Aydah tana ji abunda ya faɗa tai sauri tashi daga kwance da take ta mayar da seat ɗin daidai fuskarta ya bayyanar da irin razanarwa da tayi na ji furuncinsa zuciyarta har wani kalar bugawa yake yi ba abunda ke sauri tayar mata da hankali irin Ya Abba ya ce ya yi fushi da ita "Ya Abba dan Allah karka yi fushi dani. Tayi magana yayin da idanuwanta suka cicciko da ƙwalla, a natse AB ya juyo ya kalleta yaga yadda take danne hawayenta murmushi ya sakar mata yana faɗin "who touch my Baby?? "Ya Abba ne. Ya faɗa sounding so childishness har wani kalar turo ƙaramin bakinta take yi wanda hakan ya daɗa ƙarawa fuskarta kyau, a daidai wani super store ya tsaya ya siya mata tarkace chocolate da biscuits, a bakin gate ya ajiye ta bai shiga gida ba yana kara jaddada mata ta tabbata taje islamiyya idan ya bincika bata je ba zai yi fushi da ita. Hakan yasa tana shiga gida ta wuce bathroom tayi wanka ta shirya cikin uniform ɗinta na islamiyya da yake Siyama bata dawo daga school ba dole ita kaɗai za ta tafi ko abinci bata tsaya ci ba ta fice direban dake kai su school ya kaita. #Love Story 2023)2024 #Jiddah Aliyu #Asmy b Aliyu #team tagwaye Novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [11/27/2023, 10:24 AM] Jiddarh Aliyu 2: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love Story #Gwagwarmaya #Team tagwaye novels *RUBUTUN ƳAN TAGWAYE ZANGO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* PAID BOOK 008. (FLASH BACK) Alhaji Bashir Shamaki shi kaɗai mahaifiyarsa ta haifa tare da mahaifinsa tun yana da ƙaranci shekaru Allah ya yiwa mahaifinsa rasuwa sai dai yana da 'yan uwan su uku da suka haɗa uba ɗaya biyu mata namiji guda. Bayan rasuwar mahaifinsa, mahaifiyarsa ta sake aure idan ta haifi yara biyu Sanusi da Jamila. Matar Alhaji Bashir ta fari maryam ta rasu wacce duniya ta shaida ita ce ta haifi AB bayan rasuwarta ne ya auro Mariya ita kuma ta haifa masa yara uku Sadiya ita ce babba mai shekaru 25 a duniya Sadiya kyakkyawa ce sai dai ba irin matsananci kyau ɗinan ba tana da matsakaici tsayi, ga ta da jiki sosai 'yar lukuta ce kiwon parlor. Sai Siyama ita kuma tana shekara 22 Siyama da Sadiya tsayin su zai iya zuwa ɗaya sai dai Siyama bata yi jikin Sadiya ba, kuma kusan kamanunsu ɗaya sai dai Sadiya tafi Siyama hasken fata, dukkansu suna karatu ne a skyline university Sadiya tana shekarar ƙarshe yayin da Siyama yanzu ne farkon shigarta, sai auta kuma shalelen Ya Abba Aydah tana da shekaru 15 saura watanni uku ta cika shekara 16 tana SS two a crescent International school. Aydah duk ta fi su Sadiya kyawo nesa ba kusa ba, sai dai su nuna mata hasken fata saboda ita fatar jikinta chocolate color ce, bata jiki ko kaɗan gata gajera 'yar firitt da ita har yanzu da ta kai SS two ƙirjinta da kaɗan ya wuce na mai kirge dangi, su kan hips a bar ma maganar su, Aydah tana da wata irin baiwa ta ƙwaƙwalwa bala'in gifted ce komai aka faɗa mata ya zauna akanta, gata da bala'in shiga rai da wuya Aydah ta zauna a wurin ba ka ji kana sonta ba saboda talktive ce ta ƙarshen lissafi bata da saurin fushi sai dai akwai saurin kuka da shagwaɓa wannan kuma ya samu asali ne daga raino da Ya Abba ya yi mata. Duk girman laifi idan Aydah tayi indai Ya Abba yana nan ba a isa a dake ta ba. Muhammad Bashir shamaki shi ne cikakken sunansa amma an fi saninsa da Abba schoolmate ɗinsa suna kiransa da AB saboda su saukakawa kansu fadar Abba Bashir ɗin. Abba matashi ne mai jini a jiki shekarun sa na haihuwa ba za su wuce 37 ba zuwa dai 38 Abba dogo ne sosai tsawonsa yasa har wani ɗan rankwafa ya yi yana da girman jiki don ba za a kira shi da ramamen ba. Yana da round face mai ɗauke da dogon hanci, Abba yana da wasu irin idanuwa masu masifar ɗaukar hankali gasu manya ne sosai eyes ball ɗinsa gray color ne, laɓɓansa pink kamar yana shafa lipstick sumar kansa baƙa wulik da ita, sajensa da ya bari mai haɗe da gejeren gemin ya ƙara ƙawata fuskarsa, Abba kyakkyawa ne ajin farko fatar jikinsa fara ce mai silke da ja, ja, tun kafin yasan cewa ba Daddy bane ya haife shi ya sha tambayar Daddy shi da wa ya yi kama domin Kwata-kwata ba abinda ya ɗebo daga kamanu Daddy ɓalle kuma Maryam saboda yana da hotunata sometime har saka hotonta gaba yake yi yana kallo ko zai ga idan ya ɗebo kamaninta. mutane sun sha tambayarsa ko shi half-caste ne(ruwa biyu) wannan tambayar har gobe ana masa ita Abba Yayi karatunsa tun daga primary har izuwa secondary school anan gida kano bayan ya kammala sakandare ne Daddy ya samar masa da gurɓin karatu a Kyiv national economic university ukraine ya karanci fannin ilimin kasuwanci da tattalin arziki anan ya yi degree sa har zuwa masters kana ya dawo gida Nigeria idan Daddy ya bashi matsayin CEO (Chief Executive officer) na kamfaninsa. Abba yana farko-farko dawowarsa Nigeria ya haɗu da Rumaisa Bello madawaki suka ƙula alaƙa ta soyayya wacce har takai su matakin aure wanda a ranar ɗaurin aurensu ne ɓoyayyen sirri da Daddy ya ɓoye akan Abba ya bayyana wanda shi ne silar da yasa mahaifin Rumaisa ya ce ba zai haɗa zuri'a da shege marar asali ba. Shi kuma Daddy saboda baƙin ciki da fushin zuciya anan take a wuri ya aurawa AB Sadiya. (FLASH BACK END) Koda AB ya dawo gida dare ya yi sosai ya tarar da abincinsa Aydah ta kawo masa da ya yi arba da warmers ɗin sai da ya yi murmushi saboda cikinsa a cike yake, ya kuma san gobe akwai rigima tsakaninsa da ita. A gajiye ya wuce bedroom ɗinsa ya yi wanka boxer kaɗai ya saka ya bi lafiyar gado. *MASAURATAR KUDU* Wata kyakkyawar mota ce kirar Mercedes Benz GLS 2023 fara tass da ita, ta shigo zuwa cikin masauratar daidai wurin da aka tanada domin parking mamallaki motar ya nufa ya yi parking da sauri murfin gefen direba ya buɗe wani matashin saurayi ya fito wanda da ganinsa kasan direba ne, ya buɗe backseat ƙafarsa ɗaya da ke sanye cikin takalmin sarauta halfcover ya fara sauke ta kan interlock, sai da ya kusan share 60 seconds kana ya zuro guda ɗaya nan ma sai da ya ɓata lokaci kafin ya fito da gangar jikinsa ya subhanalillah! Tsalki ya tabbata ga Ubangiji da ya halicci wannan kyakkyawar sura duk da shekarunsa sun tafi amma hakan bai ɓoye komai ba na daga kyau halittar da Ubangiji yai masa at least shekarunsa na haihuwa za su kai 52 l swear za ka zaci bai wuce 40yrs ba wani irin kyau gare shi mai fizgar hankali, gashi fari tass kaman ka taɓa skin ɗinsa jini ya fita. Jikinsa sanye da shadda milk in color dinkin babbar riga kansa ɗauke da rawani wanda ya yi matching da shaddar jikinsa. Alhaji Aliyu Mustapha na uku kenan ƙani ga Sarkin Kudu Alhaji Mahmood Mustapha na uku. Cike da izza mai ɗauke da zallan ƙasaita ya shiga takawa zuwa ainihin cikin faɗar ta mai martaba sarkin kudu faɗawa na hango shi suka fara zuba masa kirari yayin da bayi sai zubewa ƙasa suke yi suna kwasar gaisuwa ko kallo basu isheshi ba ballantana su saka ran zai amsa musu, fuskar nan tashi a maturƙe as usual. Faɗar a cike take da 'yan majalisar Sarki, irin su waziri, ciroma, wambai Galadima, jakadan Sarki da dai sauransu yana zuwa ya isa gaban sarki dake zaune akan kujerar sa ta mulki yasha naɗi da alkibba sai da ya zube ya kwashi gaisuwa kana ya nemi wurin ya zauna. Kallo ɗaya za ka yiwa mai martaba ka gano tsanani kamanin shi da Alhaji Aliyu. Sai da sarki ya ƙare masa kallo kana ya yi gyaran murya cikin izza irin ta sarakuna da suka amsa sunansu mai martaba ya ce "Aliyu mun aika maka saƙo muna so ganinka tun kwana biyu da suka gabata amma ba ka amsa kiran mu ba sai yau da ka ga dama, shin ko za mu iya sani dalilinka na yin hakan?" Shima Alh Aliyu sai da ya gama shan ƙamshinsa irin na wanda jini sarauta ya gama ratsa shi kafin ya amsa wa mai martaba da cewa "Allah ya taimaki mai martaba Amma kasan da cewa tun inada ƙanunun shekaru bana da ra'ayin mulki, saurata kwata-kwata bata gabana. A fusace mai martaba ke faɗin."wannan karon ba zan saurari uzurin da kake kawomin ba Aliyu nacewa baka son sarauta, kamanta sauratar gadonka ce jininka na zagaye da ita, wannan karon na rantse bazan saurari uzurinka ba kaje kawai ka fara shiri domin na saka sunanka a cikin jerin mutane goma da masaurata za ta yi bikin naɗin sauratarsu. Tashi ka tafi nagama magana. Aliyu ya sadda kansa ƙasa yana bai wa yayansa haƙuri "Allah ya jada ranka ya ƙara ma lafiya da nisan kwana Allah ya huci zuciyarka." Daga haka Aliyu ya miƙe tsaye ya fito daga cikin fadar wanda fadawa sai zuba masa kirarin da suka saba yi masa suke ko kallonsu bai yi ba shi wannan kirarin ma ciwon kai yake sakasa to ina ga ranar da yake mulki yasan sai ya kwanta gadon asibiti. Daga nan ɓangaren mahaifiyarsa ya wuce kai tsaye bayi mata tun daga kofar da zata sadaka da babban ɓangaren mai babban ɗaki bayi mata birjik ne ke kai da komawa kowa yana hidima bayyanar Aliyu a wajen yasa suka shiga zubewa gabansa suna miƙa gaisuwa ko kallo basu ishesa ba kai tsaye parlorn da mahaifiyarsa ke ganawa da 'ya'yanta ya nufa, wannan karon bai sameta zaune a Parlon ba kamar yadda ta saba zama ya kalli amintacciyar baiwarta ya faɗa mata tayi masa magana da mahaifiyarsa, ko minti goma bata yi ba ta dawo ta faɗa masa tana zuwa anan ta shiga hidima dashi ta cika gabansa da 'ya'yan itatuwa cima dai mai rai da lafiya irinta gidan sarauta kusan mintina goma sha biyar da zamansa sai ga mahaifiyarsa ta fito cikin babbar shigar alfarma wuyanta da hannayenta sun sha ado da gold tun kafin ta bayyana cikin parlorn ƙamshi ya gama cika ko'ina gami da zagaye ko'ina acikin Parlon,wannan ƙamshin mahaifiyarsa ce kawai mamallakiyyarsa, bayi biyu ne a bayanta tana shiga suka rufo mata ƙofar suka juya suka koma ganin bayyanar mahaifiyarsa cikin Parlon yasa ya miƙe tsaye har ta ƙaraso ta zauna bai zauna ba sai da ta zauna ya durƙusa gafda kafafunta yana gaisheta ta amsa cike da kulawa tana nazarta yanayin yaron nata. Kusan shekaru talatin harda doriyya haka yaron nata yake tun kafin ma yayi aure idan zata iya tunawa tun da ya dawo daga karatu, a haka kullum fuskarsa take babu kalar tambayar da bata yiwa Aliyu ba a lokacin sai dai yace mata babu komai idan tace rashin walwala yaron nata bai hanata sukuni za tayi karya. Jin mahaifiyarsa tayi shiru yasa ya ɗago ya kalleta cikin natsuwa yadda ta haɗe rai yasa gabansa yayi mummuna faɗuwa cikin wani irin yanayi yace "ummah.!" "Mai sabon birnin. ta kira sa da sunan da take kiransa dashi yana jin yadda muryarta ke shaking A razane yake kallon fuskar mahaifiyar tasa yadda ta koma lokaci ɗaya "ba zan gaji da tambayarka ba meke faruwa da rayuwarka? Nasan akwai abunda kake boyemin tsawon shekaru talatin ko ka kashe wani rai ne da ka hana kanka walwala da farin ciki kamar yadda sauran al'umma keyi?" Girgiza kai ya shiga yi ba tare da ya kalli mahaifiyar tasa ba ,cike da karfin hali ya furta "Dama wajen mai martaba na fito akan maganar naɗin sauratana ta Sarkin sabon birnin kudu. Ki saka baki ummah,da gaske bazan iya daukar wannan nauyin ba duk yadda zan yi masa bayani ya kasa fahimta ta. Aliyu ya ƙarasa maganar da respect a muryarsa, yana kallon yadda mahaifiyarsa ke karkaɗa ƙafa sunfi minti biyar a haka ba tare da kowa ya sake faɗar wata kalma ba. Cike da izza mai babban ɗaki ke faɗin."tashi ka tafi naka gidan Allah ya bamu alkhairi. Jin haka yasa ya ɗan kalli mahaifiyarsa bai ƙara cewa komai ba ya miƙe tsaye yai mata sai da safe dama acikin gidan nasu aka yanki wani fili akayi masa gini irin na sarauta acewar mahaifin su mai martaba Sarki Mustapha na uku yafi son 'ya'yansa maza ko sunyi aure su zauna a tare dashi tunda akwai filaye manyya yanka kawai za a yi ayi masu ginin gida irin na sarauta. Duk da a ɓangaren Aliyu shi ba haka yaso ba Ko kaɗan baya sha'awar komai na rayuwar sarauta, sam bashi da ra'ayi hakan ba haka tsarin rayuwar da ya tsarawa kansa yake ba. Babu ranar da ba zai tuna ta ba ita ɗin ta zama jinin jikinsa duk iya ƙokarin sa na gani ya nemo ta har yau ɗinan ya kasa samun ta ko sai yaushe zai sake tozali da ita?? Tambayar da yake yiwa kansa koda yaushe kenan. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [11/28/2023, 3:51 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love Story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 009 *RUBUTUN YAN TAGWAYE BIYAR KARO NA BIYU.TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* *ALH BASHIR MANSION* Yau tunda tayi sallar asuba bata koma bacci ba ita ta taya Mami da yan aiki suka haɗa break fast. dama kuma Mami bata yiwa ƴa'ya ta horon rashin son aiki ba. Duk da tana da masu aiki bai sa ta sakankance da cewa yan aikin zasu riƙa yi mata komai ba. Sai ga 'ya'yan nata duka sun biyota da iya girki da son shiga kitchen idan ka cire Aydah acikinsu harta AB tun baida wayau yana taya Mami shiga kitchen indai yana a gida babu makaranta. Aydah ga ta mace sai dai bata aiki da rashin motsa jiki, idan kaji masifar mami a gidan na rashin son aiki to da Aydah ce, indai AB baya gida to sai ta shiga kitchen haka Siyama za tayi rantsuwa ba zata barsu da aiki ba ta taso ko ɓarar magi ne da yanka wani ganye tayi, haka zasu ta faɗa su ce yaya Abba, ya sangarta ta tana yiwa mutane yadda taga dama da anyi magana zai fara faɗin Aydah ai Yarinya ce duka-duka nawa take?" idan yana gida a ranakun weekend baya fita tasan a weekend idan ta dawo islamiyya dole ta shiga kitchen ta riƙa wani aikin. To watarana idan tana jin halin nata dama da driver ya sauke ta in har bada Siyama suka tafi ba, ta balcony take bi zuwa ɓangaren AB A can za ta je tayi kwanciyarta a parlornsa tana buga game da wayarsa watarana har bacci take ,sai angama zata shiga cikin gidan taje ta ɗibi abinci taci. Kuma daga Sadiya har Siyama babu mai magana tun da sun san yaya Abba, yana gidan baya dukansu baya zaginsu fushinsa shine punishment ɗinsu ,su kuma Allah ya ɗora musu azababben ƙaunarsa ko kaɗan basa so suga yayan nasu na fushi dasu. A kitchen tayi tsaye ta haɗa tea ta zuba soyayyen chips acikin plate ta shiga break fast ɗin da sauri kar mami ta ganta tsaye tana cin abinci tayi faɗa tasan driver sai ya fara sauke Aydah kafin ya sauketa ita kuma tana da lecture karfe 8 daidai tasan shirin Aydah idan ma aka bibbiya yanzun za ta yi wanka kafin ta shirya ta ɓata mata lokaci gara kawai ya fara ajeta Idan ya dawo ya kai ta tun da dama ita Aydah ta saba da shiririta tana gamawa Ta wuce kai tsaye ɗakinta ta shirya cikin doguwar rigar Atamfa da ɗan ƙaramin mayafinta ta dauki kayan karatunta ta fito ta samu Mami a parlor ta mata sallama, da mamaki Mami ke faɗin."batare zaku tafi da Siyama ba?" "Mami Siyama bacci take maybe batada lecture din safe. "To ita Aydah fa??" "Mami ya fara saukeni kin san shirin Aydah inada lecture ƙarfe 8. "Amman dai zaku wahalar dashi. Bata tanka Mami ba ta juya tana faɗawa Mami sai ta dawo."Mami ta bita da addu'ar Allah ya tsare hanya, sai da ta shiga ɓangaren mahaifinta ta gaishesa babu yabo babu fallasa ya amsa jiki sanyayye ta fito dama duk wata yana tura masu kuɗi a account ɗinsu, dashi suke cira suyi hidimomin makaranta da kuma lalurorinsu na yau da kullum. karfe 7:30 da rabi na safe Aydah ta fito cikin shirin zuwa school sanye cikin uniform ɗinta, Mami ta kalleta tana faɗin."Sarkin shiririta sai yanzu kika gama shirin ?" Tun asuba, ban san ubanme kike ba yanzu ko gama break fast ɗinki wani babban aiki ne sai ki kama jiki ki je ki yi kafin driver ya dawo yaje ya sauke Sadiya." Tamkar Aydah zata yi kuka take faɗin "shi ne kuma tace ya tafi Mami bancin tasan nima zani makarantar salon ta saka nayi latti. Wani kallo kawai Mami ,tayi mata "ai ke senior student ce bakya gudun latti. Mami ta ƙarashe magana tana dalla mata harara, maimakon ta nufi dinning area sai kawai ta wuce parlorn daddy tana kumbure-kumbure da turo baki ta zauna kusa ga Daddy ta gaishesa cike da kulawa ya amsa yana tambayar "me akayiwa shalelen Ya Abba?" Hawaye har sun cika idonta cike da shagwaɓa tace masa "yaya Sadiya ce tasa driver a gaba suka yi ficewarsu bancin tasan nima zan je. Ta ƙarasa magana tana wani matso ƙwalla. "ke mamana shirinki ne sai hamdala yanzu ki je ki faɗawa Yayanku sai ya kai ki. miƙewa tayi ta nufi ɓangaren AB a hankali ta tura ƙofar shiga Parlorn wani irin sanyi ne ke tashi acikin Parlon, baya cikin parlorn Amma ya kunna ac ta rasa soyayyar yaya Abba ,da son sanyi komai sanyi da ake sai ya kunna AC kuma tana mamakin yadda baya mura, kai tsaye master bedroom ɗinsa ta nufa jikin ƙofar ta tsaya tayi knocking har kusan sau biyu jin shiru yasa ta tura kanta akwai duhu a ɗakin. Haka ya saukar da duka labulayya. Da hannunta ta riƙa lalubar switch ɗin bulb ta kunna haske ya gauraye ko'ina. Hangosa tayi kwance cikin italyn bed ɗinsa ya dunkunkune kansa cikin duvet, kai tsaye kan bed ɗin ta nufa ko fuskarsa ba a gani ɗan ɗaga duvet ɗin tayi tana kiran sunansa, can cikin bacci yake jin muryar Aydah a tsakiyar kansa ɗan buɗe idanunsa yayi masu cike da bacci yana kallon fuskarta, ta wani marairaice fuska tana kallonshi "Aydah menene?" Ya faɗa da Muryar bacci nan Aydah ta faɗa masa yadda Sadiya tayi mata gashi lokaci yana ta tafiya. "je ki parlor ki jira ni na saka kaya. miƙewa tayi ta koma parlor mintina biyar ya fito da jallabiyya ajikinsa da car key sai da suna hanya ya tambayeta tayi break fast? tace ita batajin yunwa, faɗa ya dinga yi mata ita dai tayi shiru a hanyar dawo daga kai ta makaranta kiran Rumaisa ya shigo wayarsa, ɗauka yayi yasa a speaker ta gaishesa tana tamabayarsa yau tayi mafarkinsa shiyasa ma ta kirasa dan tashinta kenan ko kan bed bata sakko ba. Tana jin sautin murmushinsa ta cikin wayar bai dai ce komai ba ,tasan halin miskilancinsa sai ita ce tace "ba ka tambaya wane kalar mafarki bane.?" "ina tuki Rumaisa idan na isa gida i will call you back." Da mamaki a muryarta take tambayar inda yaje da safe nan? dan tasan idan zai fita office yana kai 9. "Aydah na sauke a school ina hanyar komawa gida ya faɗa sounding so very free cikin muryarsa abu taji yana tsaya mata a wuya dakyar ta iya furta "driver ba zai kai ta school ba sai kaine za ka kaita.?" Banza ya yi mata tamkar bai ji tambayarta ta ba, ta fara sakawa shaƙuwarsa da Aydah alamar tambaya ta fara jin tsoron kulawar da AB yake yiwa Aydah ɗin. Yana nufin ma idan sunyi aure haka zai rika yi mata?"katse kiran tayi ba tare da ta ƙara furta komai ba. ƙarfe biyu Sadiya tana tashi daga lecture ma'aikatar su Hafeez Sale ta wuce kai tsay office ɗinsa ta wuce sai da sakatariyar Hafeez ta shiga ta faɗa masa ya sha mamakin nacin da Sadiya keyi masa shi tun da tayi aure ta fita ransa baya sha'awar aurenta yanzu. Idan ya auri bazawara yace me?" Yasan mahaifinsa da mahaifiyarsa ma Ba zasu taɓa yarda ya auri Sadiya ba a yanzu ba. tun da ta shigo cikin katafaren office ɗin nasa take binsa da kallo kona sakan ɗaya bata ɗauke kanta akansa ba tana mamakin kalar son da take yi masa tamkar ba Hafeez ɗinta ba duk yabi ya canja mata. Bai mata tayi zama ba sai ita ce ta nemi wurin ta zauna, da tulin files agabansa yana dubawa cikin natsuwa. Sai da ta kira sunansa cikin raunin murya sannan ya ɗago kansa yana kallonta ido cikin ido. "Sadiya Meya kawoki office ɗina?" kina matsayin matar wani so kike ki ja min bala'i ne?" a raunane take faɗin."meyasa baka daga kirana koda sau daya ba kaji dalilin kiran?"karshe ma sai ka buge da blocking ɗina ina soyayyar shekaru huɗu da muke yiwa junanmu. "Soyayya !"soyayyah!"daga ranar da kika auri wani na bani ba na tsinke wannan soyayyar acikin zuciyata Sadiya, ban taɓa yaudararki ba hasalima kece kika yaudareni. kallonsa take tana mamakin kalamansa ,wani murmushin Sadiya tayi tare da faɗin "idan nace maka na kashe aurena saboda soyayyarka Hafeez za ka yarda?"idan nace maka naki yiwa mahaifina biyayyar da ya keso nayi masa na zaman aure da yaya AB za ka yarda babu auren yaya AB akaina yanzu Hafeez ka daina shunning din soyayyata ko kwana ɗaya ban yi ba a gidan Ya AB ba kai ɗin nan shaida ne, idan da gaske kana sona mahaifina ya bani nan da sati biyu na fito da miji aure zai min. fashewa da dariya Hafeez ya yi yana buga desk da yatsa yake nuna kansa a fusace yace "Ni kike tunanin zan auri ragin wani ?" kin rainawa kanki wayau Sadiya ba zan ɓoye miki ba ba zan iya aurenki ba koda iyayena za su yarda ke kin san kishina, ma ba zai barni na aureki ba wallahi. wannan karon hawaye ke gudu sosai acikin fuskarta tana jin yadda zuciyarta ke wani irin bugawa ga wani irin zafi -zafi da zuciyarta taji tana yi mata. Ƙofa ya nuna mata yana faɗin "Allah ya sadamu da alkhairi. Sadiya miƙewa tsaye tayi ta nufi ƙofa bata ƙara waiwayen Hafeez Sale ba tana jin yadda yaja wani dogon tsaki adaidaita sahu kawai ta tare ba tare da tayi masa bayanin inda za taje ba. Sosai jikinta ke mugun rawa kalaman Hafeez ta ke ji cikin kunnuwanta haɗe kai tayi da gwiwa ta shiga rera kukan bakin ciki murya dan sahu taji yana bata haƙuri kafin ya tambayeta wacce unguwar zai kaita dakyar ta faɗa masa har ƙofar gida ya sauketa ko canji bata tsaya karɓa ba ta shiga gida, wannan ƙaron Aydah ce kaɗai a parlon zaune akan rug da uniform ajikinta wanda tunda ta dawo bata cire ba shinkafa da miya ce agabanta cikin plate da littafi a hannunta ,jin shigowar mutum cikin parlorn yasa tayi saurin tura Novel ɗin karkashin kujera ,dan kakaf gidansu babu wanda yasan tana karatun hausa novels ita ma wajen yar class ɗinsu take karbowa mai suna Zulaiha Kasim, tun basa bata sha'awa har ita ma ta fara karantawa tasan idan Mami, ta ganta da littafan soyayya a gidanta kasheta za ta yi hakama yaya Abba, mafi yawanci tafi karatunta da dare idan ta shiga ɗaki ta sakawa ƙofarta key, wannan karon ta kasa haƙura da karantawa sai da dare saboda daɗin da labarin yayi mata da kanta ta bai wa Zulaiha kuɗi ta siyomata daga na daya har na 4 kuma wai littafin yafi shekara goma Amma yadda Zulaiha ke zuzuta haɗuwarsa littafin sunansa wai (Tattalin so)har bata so ko na minti ɗaya ta daina karatun sai dai ganin yadda yaya Sadiya ta shigo a firgice kamar bata cikin natsuwarta yasa ta mayar da hankalinta sosai wajen yar uwartata da alamar idanuwa Sadiya a rufe suke ko sanin zaman Aydah ba ta yi a Parlon ba da gudu ta nufi stairs da kallo Kurum Aydah take bin ta har ta bacewa ganinta ɗan taɓe baki Aydah ta yi tana faɗin."duk bake kika jawo wa kanki abunda da ya sameki ba da yanzu kina gidan yaya Abba, hankalinki a kwance ana riritaki ana tattalinki kamar yadda yaya Aliyu na cikin littafin tattalin so yake yiwa zeee ,har hango fuskar Aliyu take kamar yaya Abbanta amma ta nacewa wannan Hafeez ɗin da bata san da me ya fi yaya Abba, dashi ba. Yayanta ya fi Hafeez komai da komai ba ma za a haɗa su ba Jawo novel ɗinta ta yi ta cigaba da karantawa abincin da ta keci har ya yi sanyi ya sandare tana gama cin abinci har ɗaki ta samu Mami ta marairaicewa Mami ,tamkar da gaske tace kanta na ciwo dakyar idan za ta iya zuwa islamiyya za ta je ta sha magani ta kwanta, mami ta bita da addu'ar Allah ya sawwake, tana shiga ɗaki ta sakawa ƙofarta key ta faɗa kan dan kyakkyawan gadonta tayi ruf da ciki ta cigaba da karatun ta... #Love story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [11/29/2023, 5:28 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love Story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye novels 10... *RUBUTUN ƳAN TAGWAYE ZANGO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* PAID BOOK #Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye novels *MASARAUTAR KUDU* Masarauta ce mai ɗimbin tarihi duk wani jinin sarautar da ya fito daga masarautar za kaga yasha bamban da normal mutane. Jinin masauratar suna da wata irin izza, taƙama, ƙasaita, za ka ga duk wanda ya fito daga wannan masauratar ɗabi'un da halayensa ba kamar na sauran mutane ba, ga su da girman kai da ɗagawa wayayyu ne suna da ilimin boko dana addini kuma gasu da wani irin kyau na ban mamaki da matuƙar wahala ka ga mummuna cikinsu sai dai abinda ba a rasa ba saboda mutum ɗan tara ne bai cika goma ba. Allah ya yi musu arziki sarauta da kuɗi gasu da mulki ga kuma tarin dukiya da Allah subhanahu wata'ala ya albarkace su da ita. A halin yanzu mai martaba sarkin kudu Mahmood Mustapha na uku shi ke mulkar wannan daula shine a matsayin sarkin kudu mahaifinsa Margayi Alhaji Usman Mustapha na uku shine Sarki bayan ya rasu aka naɗa ɗansa Mahmood Mustapha na uku. Sarki Mahmood su shidda mahaifiyarsu ta haifa wacce suke kira da mai babban ɗaki wato ita ce uwargidan sarki Usman, mai martaba sarki Usman ya mutu ya bar mata huɗu da sadaka uku tare da tarin 'ya'ya arba'in da bakwai a halin yanzu talatin da tara ke raye takwas daga ciki sun rasu. Kafin Sarki Usman ya rasu kan zuri'arsa a haɗe yake sai ya rasu ne aka fara samun rabuwar kawunan su wannan kuma ya samu asali ne daga wurin matarsa ta biyu Hajiya Kilishi, a dalili sarautar Sarkin sabon birnin kudu da margayi Sarki Usman ya bai wa Aliyu tun yana da rai kasancewar Aliyu shine ɗansa na shidda a ganinsu bai cancanci wannan sarautar ba tun da akwai na sama dashi. Wannan sarauta da sarki Usman ya ba wa Aliyu ita ce silar haddasa ƙiyayya tsakani yaran mai babban ɗaki da yaran Kilishi. Shi kuma Sarki Usman ya yi hakan ne a dalili fahimtar da ya yi Aliyu baya da ra'ayi sarauta ko kaɗan idan aka ɗora masa nauyi mulkin jama'a dole ya fara saka sarautar aransa. Dama shi Aliyu abarsa da kasuwanci domin kusan dukkan kamfanonin su shi ke kula dasu. Alh Aliyu yana baro bangaren mai babban ɗaki ya wuce gidansa kaitsaye ɓangaren sa ya shiga yana shiga katafaren parlorn sa ya nemi ɗaya daga cikin royal cushion da suka daɗa ƙawata parlornsa ya zauna, ya cire rawani kansa ya ajiye kusa dashi ya tsani rawani sai dai doka ce ga duk wani jini masarautar ya saka naɗi kafin ya shiga faɗa, shiyasa yanzu ma da zai shiga faɗa ya saka ba don haka ba da ba abinda zai haɗa shi da rawani. Hajiya Safiya ce ta turo ƙofa ta shigo cikin parlorn, ta hango mijn nata ya lafe jikin cushion idanunsa rufe tasan ba bacci yake yi ba kawai dai damuwar nan ce da ya ɗorawa kansa tasaka shi cikin irin wannan yanayi. Tambayar duniya nan idan za ka yi masa zai amsa maka ne da ba komai rana da baya ji so magana sai ya yi banza da mutum. Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta nemi dab da ƙugunshi ta zauna tana matuƙar son mijinta irin son da fatar baki ba za ta iya faɗarsa ba, sai dai ta misalta. "Abbu! Ta kira shi da sunan da yaransa ke kira shi dashi, dama a wasu lokuta haka take kiransa dashi. Bai matso ba balle ta sa ran ya ji kira da tai masa sake lankwasa muryarta ta yi ta koma kiransa "Abbu! A hankali ya ɗage idonsa guda ya kalleta na 'yan wasu daƙiƙu kafin ya maida idonsa ya rufe, ya yi hakan ne don tasan ba bacci yake ba balle ta dame shi da kira. Sanin hali yafi sani kuma tasan halinsa fiye da yadda tasan yunwa cikinta muddin ba shi yaso yin magana ba duk nacinka dole ka kyaleshi don ba tanka ka zai yi ba. "Abbu har sai zuwa yaushe zan daina gani wannan damuwar akan fuskarka? Dan Allah Abbu ka faɗa min idan ni ce ba ka jin daɗin zama dani ko ina maka wani abu da ba ka so wallahi a shirye nake da na gyara. Shiru ya yi alamar ba tanka mata ba "A matsayina na matarka makusanciyarka ina da damar da zan san damuwarka idan ina da hali taimakawa Abbu sai na taimaka ma idan babu kuma sai na tayaka da addu'a. Ni da kai abu ɗaya ne damuwarka nima tawa ce hakazalika farin cikinka shine nawa matuƙar kana cikin damuwa ba yadda za a yi na kasance cikin walwala. Har ta kai ƙarshen zance ta idanunsa suna a rufe "Safiya ina buƙatar hutawa za ki iya tafiya. Ya yi magana still idanunsa na rufe. "Amma Abb.. "Safiya please. Yai sauri katse mata hanzari a wannan karo ya buɗe idanuwansa suka fara canza launi, jikinta a sanyayye ta miƙe ta baro ɓangaren nasa, ba tun yau ba take ayyana cewa gangar jikinsa ta aura ruhinshi yana wani gun daban. *RUMAISA MADAWAKI* Rumaisa ta fito daga cikin gida jikinta sanye da straight gown na lace pitch in color gaban rigar har zuwa ƙasanta an mata beads work, sosai shigar tai mata kyau hannunta riƙe da purse ɗinta wacce tayi match da heel ɗin ƙafarta ɗayan hannunta ke ɗauke da car key ɗinta. Fitar nan da za ta yi za ta je gyaran gashi da body waxing da take zuwa duk ƙarshen wata yadda take tafiya tamkar wacce bata kashi sai wani yatsine fuska take yi ga idanuwanta ta lulluɓe su da sunglass. Ta shiga motarta tare da yi reverse ta fito da ita daga parking lot kana ta daidai motar ta ja ta zuwa gate wanda tuni maigadi ya buɗe mata. Kai tsaye Aj beauty palace and spa ta nufa dama can ake mata duk wani gyaran jiki, tana shiga wurin ta haɗu da old friend ɗinta Aneesa Baffa wacce suka yi karatun sakandare tare tun daga lokaci basu sake haɗuwa ba sai yau da suka haɗu a Aj beauty palace and spa. Aneesa Baffa kyakkyawar matashiyar budurwa wacce ke ji da naira saboda mahaifinta Alhaji Baffa ya mutu yabar musu tarin dukiya wannan yasa ta fara business ɗinta tana da manya-manyan boutiques na siyar da expensive clothes na mata da maza har ma dana yara Aneesa Baffa she's independent woman wacce ke cin kashin kanta sai dai har yanzu bata yi katari da namiji da take gani ya dace da ita ba duk da tana da farin jini wurin maza. Cike da wayewa ta mata da idanuwansu suka gama buɗewa suka rungume juna ita da Rumaisa daga nan hira ta barke a tsakanin su daga nan suka yi exchange ɗin contact, da yake ita Aneesa har an kammala mata abunda ta zo yi saboda haka suka yi sallama tare da alƙawari kai wa junansu ziyara. *ALH BASHIR MANSION* Sosai Sadiya ke rera kuka kaman ba gobe Allah na tuba ko uwarta da ubanta suka mutu iya kukan da za ta yi kenan, wani kololon abu take ji ya danne mata zuciya saboda tsanani kukan da take yi she can't even breathe sai wani irin sheɗewa take yi tasha baƙar wahala kafin ta samu numfashinta ya daidaita a jikinta, she didn't think Hafeez would break her heart like this ta ɗauki soyayya da yarda ta bashi sai gashi ya barta da dafi a ƙahon zuciya, wani kalan mahaukaci so take mishi shiyasa ta kasa karɓa Ya Abba a matsayin mijinta sai gashi tayi biyu babu ta rasa Ya Abba shi kuma Hafeez Sale ya guje ta. *AYDAH* Hankali kwance take karanta novel ɗinta duk gun da ya yi mata daɗi sai tai wani lumsashe idanu, tana rausayar da kai kiran sallah magarib ya tashe ta ba don ranta ya so ba ta ajiye littafin sai lokaci ta cire uniform ɗin jikinta ta ɗaura light pink towel ɗin ta ta shiga wanka agaggauce ta fito ta zura plain cotton gown mai gajeren hannu tayi sallah bata tashi ba sai tayi sallah isha kana ta fito main parlor, babu kowa sai mai aikinsu da ta hango a dining area tana arranging table, saboda haka ta wuce ɗakin Siyama tana tura ƙofa Siyama was busy with her laptop turo ƙofar ɗakin nata da Aydah tayi yasa ta ɗagowa Aydah ta ƙaraso ta zauna kusa da ita "me kike yi ne yaya Siyam?" "Ina ruwanki da abunda nake yi? Siyama ta faɗa tana mayar da idanuwanta kan laptop ɗin. Sai da Aydah ta galla mata harara a fakaice ta wani turo baki tare da leƙa screen ɗin laptop ɗin ita a dole sai ta ga abunda Siyama take yi cikin sauri Siyama ta janye laptop ɗin tana faɗin "what's wrong with you? "I just want to see what you are doing in the laptop ko haramun ne don na ga abinda kike yi? Wani kallo Siyama ta wulga mata sosai iskanci Aydah ke sauri hasala ta kalli yadda tai mata magana kaman wata sa'anta "Get up and get out of my room before naci ƙarniyarki. Miƙewa Aydah ta yi tana gunguni ƙasa-ƙasa magana ne take mayar mata, rai ɓace Siyama ta kalleta taga sai da take da ɗan mitsitsi bakinta ko ba tambaya ba tasan maganganu banza ne take faɗa mata "Why don't you respect me, Aydah?, I am your sister ina gaba dake you have to respect me. "Haba dallah Yaya Siyam sai faɗa kike kina nanata wa sai kace wasu shekaru kika bani masu yawa. "Iyeee! Aydah yau kuma iskancin naki akaina ya dira? Kallo sama da ƙasa Aydah ta yi mata hakan ya ƙara harzuƙa Siyama ta zabura ta miƙe tsaye da zimmar idan ta kama Aydah sau ta yabawa aya zaƙinta, Aydah tana ganin yadda ta miƙe ɗinan da gaske za ta iya dukanta saboda haka ta juya da gudu ta buɗe ƙofa ta fita, ita ma Siyama da rashin haƙuri ta biyo ta da gudu suka sakko ƙasa dai-dai Sadiya tana fitowa kitchen hannunta riƙe da mug ta haɗo tea, ta gaji da kukanta na rashin dalili ta fito yunwar da ta dinga naniƙar hanjinta yasa ta fitowa babu shiri sai dai ta rasa appetite babu ɗanɗano ko kaɗan a bakinta wani ɗaci-ɗaci ma yake mata shiyasa ta yi deciding ta sha tea. Sai kuma ga waɗannan rigimammun siblings ɗin nata da basa gajiya da rigima, Aydah da ta zo da gudu bata lura da Sadiya ba tai bala'in bangaje ta mug ɗin hannunta ya subuce ya faɗi kan marbles ya tarwatse tea ɗin ya zuba a ƙafarta, duk dai bai da zafi sosai hakan bai hanawa Sadiya tsandara ihu tana kira ƙafarta sai tsalle take Siyama ta nufe ta, tana ƙoƙari kamata Aydah tana gani yadda jikin Sadiya ke motsawa sai kawai abin ya bata dariya ta fashe da dariyar harda su riqa ciki .a fusace su dukka biyu Sadiya, Siyama suka yi kanta ta sake kwasa da gudu ta fice zuwa compound tana dariya abinta, a bayyane ta ce "Cabdijam! Wallahi yaya Sadiya buhun banza ce dallah kalli yadda naman jikinta ke rawa dama za ta ɗauki shawara ta fara rage fat. Ta ƙarashe magana tare da kwatanta yadda Sadiyar ke tsalle sai kawai ta sake sheƙewa da dariya. Motar Ya Abba da ta hango yana shigowa ta nufi wurinsa tana ƙoƙarin haɗiye dariyarta saboda tasan halinsa ba kasafai yake son dariya ba. "Sannu da dawowa Ya Abba! Ta faɗa sa'ili da ya fito briefcase ɗinsa ta karɓa ya sakar mata yana faɗin "Me kike yi a waje Aydah?" "Yaya Sadiya da yaya Siyama ne za su yi min duka shine na gudu waje. Sai da ya ƙare mata kallo kafin ya furta "Hauka suke yi da za su yi miki taron dangi? Ban da mugunta me za su daka anan? Sai dai in kasusuwan ki za su karya. Ya ƙarashe magana yana nuna jikinta cunno baki tayi "A'ah! Ya Abba bangane ba wannan yabo ne ko zagi? Murmushi mai sauti ya yi tare da dungure mata goshi "bansani ba. Ya yi magana tare da nufar flat ɗinsa tayi tsaye tare da bin sa da ido tana kallon yadda yake tafiya cike da izza da ƙasaita a zuciyarta tace "Anya kuwa Ya Abba ɗinan ba daga royal family ya fito ba? OMG! ji tafiya irin na hamshaƙai sarakuna. Tuni AB ya yi gaba yabar ta tsaye tana sambatunta na shirme yana dab da isa entrance ɗin flat ɗinsa ta kwasa da gudu ta cimmasa tana "Ya aka yi yau yaya Abba ka yi saurin dawowa?" Bai bata amsa ba har sai da suka shiga parlornsa ya ce "Ko na koma ne? "Ni na isa na ce ka koma. Ya ajiye wayoyinsa kan centre table yana faɗin "Ki jira ni zan yi wanka. Ya ƙarasa magana gami da karɓar briefcase ɗinsa dake hannunta ya nufi master bedroom ɗinsa "A fito lafiya! Aydah ta faɗa tana mai zaunawa akan cushion. #Love Story 2023/2024 #Jiddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye Novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [11/30/2023, 1:53 PM] Jiddarh Aliyu 2: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye novels 011. Daya daga cikin wayoyinsa ta ɗauka wacce ta kasance ita ce babba iphone 14 pro max, ba ta tasha wahala wajen cire code saboda sunanta ne, yawanci dukka pics ɗin dake ciki nata ne, ta shiga nan ta fita nan sai kace ta bashi ajiya a wayar ne. Text message ya shigo daga habibty, ɗan ƙaramin tsaki taja tare da buɗe text ɗin "Habibi ka buɗe Data na tura maka pics ɗin kitso da aka yi min yau ka gani ko ya yi kyau. "Mtss! Aikin banza tsabar iskanci hatta da kitso tayi sai ta nuna masa. Aydah ta yi magana a bayyane sai kawai ta buɗe Data ɗin jim kaɗan sai ga pics ɗin sun shigo kusan guda biyar wanda har sun buɗe "mtsss! Ta sake jan tsaki har yafi na farko a dalili kitso da aka yiwa Rumaisa na attachment ne irin gana waving ɗinan ƙanana ya sauka har gadon bayanta, tsabar ɗaukar magana irin na Aydah sai kawai ta yi tagging guda daga cikin pics ɗin ta rubuta "Bai yi kyau ba ko kaɗan saboda ba da ainihin gashinki kika yi ba sai da kika haɗa da gashin doki kuma Allah ya la'anci mai ƙara gashi. Sai kawai ta tura mata tana gani text ɗin ya tafi ta kashe Data ɗin ta ci-gaba da sabgar gabanta. AB ya fito sanye da farar jallabiya sai zabga ƙamshi yake ya dubi Aydah ya ce "tashi mu tafi yunwa nake ji tun breakfast ban sake saka komai a cikina ba. Aydah ta tashi da sauri suka nufo flat ɗin Mami koda suka shigo hatta da Mami jiraye take da ita ganinta tare da AB yasa dole suka shafa mata lafiya saboda sun san in har yana wurin ba dakuwa za ta yi ba. Bayan sun kammala ci abinci AB ya wuce parlorn Daddy saboda tun a kamfani Daddy yace yana so su tattauna magana mai muhimmanci. Bayan ya yi sallama Daddy ya amsa masa kana ya ɗan runsuna ya gaida Daddy, ya nemi wurin ya zauna yana faɗin. "Daddy ka ce za mu yi magana. AB ya yi magana yana kallon Daddy wanda hankalinsa ke kan akwatin talabijin yana kallon news. Sai kawai Daddy ya tattaro hankalinsa ya mayar kan AB "Abba dangane da zance aurenka ne nayi magana da Alhaji Habibu Bichi akwai 'yarsa da ta kammala karatun ta na pharmacy yarinya ce mai cike da nagarta ka shirya gobe idan Allah ya kai mu ka je ku dai-daita bana so al'amari ya dauki dogon lokaci. Wani irin gumi ne ya karyowa AB a jiki ya kasa furta uffan sai bin Daddy da idanu yake yi, da Daddy ya ji ya yi shiru bai ce komai ba ya kuma san halinsa da kawaici da matuƙar wahala yai mishi musu saboda haka ya umurce shi da ya tashi ya tafi amma ya tabbata gobe ya je sun gana da yarinyar. AB ya baro parlorn Daddy tamkar zai rusa ihu, meyasa Daddy zai kafe lallai-lallai sai ya yi masa aure? Shi ba wani mummuna abu yake yi ba da zai sa Daddy ya matsawa kansa. Tun sanda aka fasa aurensa da Rumaisa aure ya gama fice masa arai Rumaisa ita ce zaɓinsa ita ce mace da yake ganin zai iya zama da ita a karkashin inuwar aure. Da wannan tunani ya dawo bangarensa ya cire jallabiya jikinsa ya hau gado ya kwanta ba don yana ji bacci ba sai don yana ji kaman kwanciya zai iya sassauta mishi halin da yake ciki a koda yaushe yana ƙoƙarin danne damuwar da yake ciki don gani ya farantawa Daddy yasani muddin ya bari damuwar da yake ciki tai tasiri za ta shafi makusantan shi da dama abunda baya fatan faruwarsa shiyasa yake pretending as yana cikin farin ciki alhali azahirance ne kawai amma badilinsa abu ba haka bane. Yana so sanin wani abu da ya danganci asalin iyayensa komai ƙanƙatarsa amma babu hali yin hakan saboda Daddy ya gargaɗe sa akan zancensu. Daren rana AB bai yi bacci ba sai tufka da warwara yake. Shiyasa washe gari ya tashi da wani irin azababben migraine headache, adaddafe ya je sallar asuba yana dawowa ya sake kwantawa sai lokaci ya sami bacci. Yau trouble maker Aydah an auna arziki ta shirya da wuri, yau su dukka uku za su fita Siyama da Sadiya dukkansu biyu lectures ɗin safe suke da. A parking lot suka rutsa Aydah kowane su da kalan muguntar da yai mata Sadiya ta fara kai mata rankwashi yayin da Siyama ta sakar mata mugun dundu saboda azaba sai da Aydah ta fasa ihu ido ya raina fata har ta isa school tana matsar idanuwa sai tsokana amma babu juriya. Sai misali ƙarfe 11:00am AB ya falka zuwa lokaci ciwon kai ya ragu sosai agaggauce ya yi wanka ya shirya ko breakfast bai tsaya yi ba ya wuce kamfani saboda yana da meeting da team members (employees) wannan meeting ɗin har da Daddy zai yi attending ƙarfe 11:40am dukkansu sun hallara a conference hall dake cikin kamfanin bayan AB ya gabatar da sabuwar motar da za su kawo bayan dogon bayani da ya ɗauke shi tsawon awannin yana yiwa team members dangane da mota ɗin wani abin burgewa kamfanin su shine kamfani na biyu da zai fara shigowa da irinta a Nigeria, cike da kwarewa ya kammala jawabin nasa, sannan ya zauna nan take hall ɗin ya kaure da tafi da sowa. Daddy sai gyaɗa kai yake yi cike da alfahari kasancewarsa mahaifi ga AB idan ka cire mutane biyu Alh Sanusi da Alh Umar dake ciki hall ɗin kowanne team member za ka hango fuskarsa lulluɓe da farin ciki domin nasarar kamfani nasarar su ce dukka. Bayan an watse daga meeting ɗin a jigace AB ya wuce ofishinsa wani irin jiri ke ɗibarsa bai daɗe da zama ba ya ji muryar Secretary shi Skyler a dai-dai ƙofar shigowa ofishinsa da alama akwai wanda take sa'in-sa dashi, da ƙarfi aka banko ƙofar ofis ɗin nasa ya ɗago yana dafe da forhead ɗinsa "Madam! Madam, I told you that you're not allowed because you do not have an appointment with him, Come back and wait. Lemme ask him first if he wants to meet you. Duk maganganu da secretary Skyler ke yiwa Rumaisa bai sa ta tsaya ba har sai da ta iso tsakiyar ofishin ɗin na AB alama AB ya yiwa Skyler da hannu ta juya tare da rufu ƙofa ta koma baki aikinta cike da jin haushin Rumaisa. "What's all this Abba? Na ce menene wannan miyasa za ka yi min wulaƙanci irin wannan? if you really want to break up with me, you should not follow this way Abba. Sai da ta fesar da wani kalan iska mai zafi daga bakinta muryarta yana rawa ta cigaba da faɗin "I know all this time I was the only one who loved you and you didn't love me ba ka sona Abba ina yaudara kaina ne kawai. Ta ƙarasa magana hawaye yana bin kumatunta Abba bai ce komai ba sai komawa ya yi jikin kujera ya jinginar da bayansa tare da lumshe idanuwansa yana ji yadda kansa ke wani irin sara mishi kwata-kwata bai san abunda take magana akai ba kuma ko za su kai gobe ba zai iya buɗe bakinsa ya tambaye ta ba. Da ta gaji da masifarta ta nemi kujera ta zauna sun ɗauki tsawon lokaci ba wanda ya yi magana Rumaisa tasan waye AB ciki da wajensa, shiyasa ta saukar da fushinta cikin sanyi murya kaman za ta yi kuka ta ce "Please Abba, talk to me, why did you humiliate me? Na je na ɓata lokaci aka yi min kitso da body waxing don dai kawai na burgeka ka soni ni kaɗai amma ka rasa kalma da za ka jefe ni da ita sai wannan. Ta nuna masa wayarta duk da azababben ciwon kan da yake ji hakan bai hana shi bi text message ɗin ya karata take ya gane ko aiki waye. "Idan ma baka so ina ƙara gashi sai ka faɗa min ta siga mai daɗi sai na daina duk abunda ba ka so Abba duk son da nake masa wallahi zan daina. Rumaisa ta faɗa tana wani langwaɓar da kai. "Rumaisa ki tafi gida za mu yi waya, Ya faɗa kamar mai ciwon haƙora. "Abb... "Please go!! Yai sauri tarar numfashinta ba tare da ta sake magana ba ta tashi ta nufi ƙofar fita tana sharar hawaye tana fita ya sauke naunnayar numfashi. *MASARAUTAR KUDU* Alh Aliyu na uku yana gani Hajiya Safiya ta fita ya miƙe ya nufi master bedroom ɗinsa kai tsaye wardrobe ɗinsa ya nufa bangaren da ya ajiye safe ɗinsa ya saka lambobin sirri (code) ya buɗe safe ɗin yana ɗauke da muhimman takardun sa wasu hotuna ya ɗauko ya nufi gefen gadonsa ya zauna hoton farko ya fara ƙurawa idanu na wata kyakkyawar baturiya tana tsaye jikin wata bishiya wacce samanta ke ɗauke da furanni ja da fari tana sanye ne da half blouse pattern gown red in colour rigar da kaɗan ta wuce gwiwoyinta, gashin kanta ya sauka har gadon bayanta, mace ce kyakkyawar gaske wacce kallo ɗaya za ka yi mata ka tabbatar da kyawon nata yakai maƙura. Ya ɓata lokaci sosai yana kallonta yana sauke numfashi a jere kafin ya aje hoton gefensa, idanuwansa suka sauka akan wanda suke tare manne da juna akan gadon asibiti da kyakkyawan Baby sun saka shi tsakiyar hannayensu tare da rungume shi, Baby yana naɗe cikin farin baby shawl fuskarsa ce kaɗai a buɗe. Alh Aliyu bai ankara ba ya ji wani abu mai ɗan ɗumi-ɗumi yana bin tattausan kumatunsa, bai damu da sai ya goge su ba ya rungume hoton a ƙirjinsa ya ɗauki lokaci mai tsawo a haka sai da ya ji wayarsa tana ringing kana ya tashi ya mayar da hotunan cikin safe ɗin, sannan ya ɗauki wayarsa dake ta faman ruri. *ALH BASHIR MANSION* Misali ƙarfe 4:15pm AB ya baro kamfani duk da yana da tarin muhimman ayyuka da ya dace ace ya kammala su kafin tashinsa sai dai ya zama mishi dole ya bar ayyukan duk da irin muhimmanci su agare shi, saboda yana so ya je ya haɗu da yarinyar da Daddynsa ya nema masa bedroom ɗinsa ya wuce ya cire kayan jikinsa ya ɗaura brown towel ya shiga wanka, bai wani ɓata lokaci a wurin wanka ba ya fito saboda har yanzu yana fama da migraine headache sai ma ji yanzu ya daɗa ƙaruwa fiye da ɗazu da safe. Ya shirya cikin farar shadda tasha aiki da zare blue shiyasa ya saka hula blue da blue color sandal irin wanda ake sakaɗa yatsa sosai takalmin suka yiwa fararen ƙafafuwansa kyau, duk da baya ciki yanayi mai daɗi hakan bai hana masa feshe jikinsa da tsadaddun turarunkansa, dama ƙamshi ya zame masa jiki ma'aɓoci so turare ne. Kai tsaye parking lot ya wuce ya shiga motarsa tuni maigadi ya wangale masa gate koda ya isa gidan Alh Habib Bichi ƙarfe 5:44pm bayan ya yi parking motarsa ya aika maigadi ya sanar wa da Mufeeda zuwansa. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/1/2023, 6:53 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye novels *RUBUTUN ƳAN TAGWAYE ZANGO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* PAID BOOK 012. Tsaye yake cikin compound ɗin gidansu Mufeeda, ya jingina bayansa da mota ya harɗe hannayensa akan ƙirjinsa yana ƙarewa harabar wurin kallo. ma'aikata ne maza ke ta kai da kawo, har kuma zuwa lokacin zuwaciyarsa taki amanna da yarinyar da Daddy ya keso ya aura wani irin ƙunci yake ji a can ƙasan zuciyarsa duk yadda zai yiwa Daddyn nasa bayani yasan bazai fahimta ba. "Salamu Alaikum amincin Allah ya tabbata akan wannan kyakkyawar halittar. Bai san yayi zurfi duniyar tunanin da ya shiga ba sai da ya ji wata murya mai sanyi tana yimasa sallama, kallonta ya yi na sakan biyu babu laifi tana da kyau ƙamshinta ga baki ɗaya ya gama cika wurin amsa sallamarta ya yi cikin sanyin murya kallonsa kurum take still da murmushi akan fuskarta. "Da fatan banyi laifi ba dana barka kana jira? Mufeeda ta faɗa da wata irin murya mai jan hankalin duk wani ɗa namiji dama Mufeeda ba dai iya tsara zance ba da tattausan kalamai, murmushi ya kirkira yana shafa beard ɗinsa " mu ƙarasa daga ciki. mufeeda ta faɗa tana juyawa ta fara tafiya cikin takonta mai jan hankali duk da yadda take tafiyar a hankali dan su jera da AB haka bai sa ya cimmata ba. Tana mamakin izzarsa tamkar wanda ya haɗa jini da sarauta Sai murmushi take saki ita ɗaya koda mahaifinta ya yi mata zance duk da tana jin labarin AB ɗin kuma tana kallon yadda ake ɗora business din kamfanin mahaifinsa a jaridar daily trust ana saka daidai kun hotunan sa bata taɓa tunanin haɗuwarsa yafi haka ba a fili ba. A parlor baƙi aka yi masa masauki aka cika gabansa da cima kala-kala babu abunda yaci acikin abubuwan da aka aje masa bottle water kawai ya dauka ya sha rabi ya aje Mufeeda ta ɗan saci kallonsa suna haɗa ido tayi saurin sadda kanta ƙasa ta shiga wasa da yatsun hannunta murya can ciki ta kara gaishesa. Ya amsa yana tamabayarta mutanen gidan ta amsa da suna Lafiya, shiru ne ya ƙara ratsawa a tsakanin su har na kusan mintina goma shi ba magana ya iyayi mai tsayi ba bai san me zai ce ba Ko Rumaisa idan ya je zancen wurinta rabin hirar duka ita take masa, wani wurin ya tanka ta wani wurin yayi murmushi, haka dai ya daure ya yi rabin awa a gidansu Mufeeda duk a takure yake ta kaisa har wurin mama suka gaisa har bakin mota ta rakasa tana ta ƙoƙarin ya sake da ita sunyi musayar lambar waya a tsakaninsu kafin ya shige motar tana tsaye tana kallonsa har ya fita daga cikin get ɗin gidansu. Bai shiga cikin gida ba sai bayan sallar isha Mami da siyama kawai ne a parlor ya zauna kujerar da Mami take mai zaman cin mutum biyu yana gaisheta ta amsa tana kallon yadda ya yi wani irin zuru-zuru "Kwanan nan baka son cin abinci Abba, ina ganin yadda ka ke zuba abincin watarana ma ba ka tsayawa cinsa musamman da safe haka ka ke tafiya office, wannan miskilancin naka ba ƙaramin haushi yake bani ba matar ka ta shiga uku ,za ka kasheta da ranta idan Allah ya zuba mata surutu tamkar Aku. Bai san lokaci da ya saki murmushi ba, bai dai ce komai ba Dariya Siyama tayi tana faɗin "wallahi yayanmu da gaskiyar Mami, wacce za ta zauna a matsayin matarka idan ba miskila bace ta shiga 9 Bama uku ba. Duk yadda Hindu ke nacin na bata lambar yaya Abbanmu su rika gaisawa kin bata nayi dan nasan halin kayana har tagaji da naci ta kyaleni. Wani irin kallo AB ya shiga aikawa Siyama dashi ta danne dariya dake cinta ta ɓoye fuskarta cikin kujera. "Siyama je ki haɗomin cooffe. Siyama ta mike tsaye ta nufi kitchen dan cika umarnin yayan nata. Mami ta mayar da hankalinta sosai wurin AB tana faɗin "Ya ku kayi da Mufeeda ɗin? Nasan halin ka idan baka son yarinyar nan tun wuri ka faɗawa Daddy, karka bata mata lokaci. Mami tamkar tasan maganar da ya keso su yi kenan ya tattauna da wani ya rasa dawa ya kamata ya yi maganar. "Na je Mami. Sai kuma ya sassauta murya ya ci-gaba da faɗin "Mami Amma kina ganin Daddy,ba zai haƙura da maganar auren nan ba har zuwa gaba?" Ko ke ki yi masa magana. Da sauri Mami ta shiga girgiza kai tana faɗin "Ni zan zauna maka da matar ne?" kawai ka je ka samu Daddyn ka ce baka ra'ayi sai a fasa. Ɗan fito da ido ya yi yana gami da faɗin."Ni ai bance ban ra'ayinta ba ganin na ke me Daddy ke yiwa saurin lallai sai nayi aure a yanzun. Mami ta taɓe baki ta ce "Ka daina sakani a matsalarku da ku ka gama maganar da Daddy ai ba ku sakoni aciki ba. Ɗan shiru Abba ya yi yana kallon Mami kafin yace "Mami ni fa yanzun mun gama daidaita kanmu da Rumaisa har office ta sameni ta bani hakuri. Wannan karon baki buɗe Mami ke kallonsa cike da takaici take faɗin."Duk irin tozarcin da mahaifinta ya yi mana aranar daurin aurenka shine har ka manta Abba?" Yadda Mami ta fusata yasa illahirin jikinsa ya yi sanyi ya yi da nasanin faɗawa Mami, zancensa da Rumaisa, ƙarshema Mami bata saurari haƙurin da yake bata ba ta tsallakesa ta bar masa parlor Siyama ta haɗo masa cooffe ga baki ɗaya yanayin sa ya canja har tambayarsa Siyama tayi yace babu komai. Ya kalleta yace ta kira masa Aydah juyawa tayi ta nufi stairs tana riƙe handling ɗin ƙofar za ta tura ta ji sa a rufe Siyama ta shiga buga kofar tana faɗin."Wannan wane irin iskancine za ki riƙa rufe kofa kamar wata marar gaskiya. Dama Aydah najin ana buga ƙofa da sauri ta mayar da sabon Novel ɗin da take karatu ta mayar dashi cikin bag ɗinta na islamiyya fuska a murtuƙe ta zo ta cire key tana kallon Siyama da ranta ya gama ɓaci. "ubanwa kike rufewa ƙofa sai kace wacce bata da gaskiya. Ɗan buɗe idanu Aydah tayi akan Siyama tana faɗin."To wai ke yaya Siyama ina ruwanki ƙofar ɗakin ki ko nawa. Ta faɗa tana wani haɗe rai , ƙwafa Siyama tayi aranta tana faɗin ranar da bata zuwa makaranta sai ta shiga ɗakin Aydah ta bincika me take ita ɗaya a daki dan ga baki ɗaya jikinta ya gama bata bata da gaskiya ko zaman parlor ta rage yi ,dama tunda yaya Abba ya saka mata kayan kallo a ɗakinta ta daina bi a parlor duk magarib sai anji 'yan matan gidan na rigimar canja channel dama ita Aydah drama da take kallo a zee word tun 7 na dare har 10 babu kuma wanda ya isa ya canja channel ita kuma Sadiya star life, Siyama ce mai Kallon African magic idan suka hasala Mami sai duka ta kashe kayan kallo tace kowa ya tashi ya koma ɗakinsa ya yi karatu ko kuma ta mayar tashar (Sunnah Tv) ta ce duk ubanda ba zai iya kalla ba ya bar mata parlor AB yana saka mata nata a ɗakinta aka samu zaman lafiya daman ita ce rigimammiya. "Idan Kin ga dama ki je yayanmu na parlor yana jiranki. Daga haka Siyama ta juya tabar ƙofar ɗakin na Aydah da yar bingilar rigar baccinta wacce ta sauka dai-dai gwiwoyinta ta nufi cikin parlor sai manyan kalaban dake reto a tsakiyyar bayanta, ta zauna kusa garesa yana shan cooffe yana waya da Rumaisa jin ta kusa dashi yasa ya katse wayar ba tare da yayiwa Rumaisa sallama ba. Yau jin kansa yayi wani iri da Aydah ta zauna da kayan bacci agabansa bai san meyasa ba sai ya ji kansa wani iri watakila hakan yana da nasaba da ya ji ba Mami da Daddy ne suka kawo sa a duniya ba kenan su Aydah ba muharammansa bane."Yayanmu ina wuni duk yau bamu haɗu ba. Aydah ta faɗa tana kallonsa maimakon ya amsa ta sai ya tamƙe fuska ya shiga faɗin "Yaushe na fara wasa dake a gidan nan?" Gaban Aydah na faɗuwa take kallon fuskarsa?' His sounds so pissed off tuni hawaye suka cika idanunta abun da ya tsana kenan ganin hawayenta, duk da haka bai fasa mata faɗa ba "Yaushe ki ka yi girman daukar min waya ki yiwa babba rashin kunya irin tarbiyyar da akayi miki kenan?" Tuni Aydah ta gano laifinta cikin rawar murya hawaye na zubo mata take basa haƙuri Amma ina ko kallonta bai yi ba yabar mata parlor rai a bace kife kanta tayi da hannun kujera ta shiga rera kuka, a haka Sadiya ta sameta ta tsaya akanta ta kira sunanta banza Aydah tayi mata ɗan tabe baki Sadiya tayi ta wucewarta kitchen bata ƙara bin takan Aydah ba. Daman rashin kunyarta ba zai bari a shiga sabgarta ba koda tana cikin damuwa. lokaci dinner da aka haɗu cikin dinning area AB yana zaune gefen Daddy, suna cin abinci dare babu Aydah babu alamarta babu kuma wanda yabi takanta. Sai Daddy ne ya dakatar da cin abincin da yake da mamaki yake tambayar ina Aydah ko tayi bacci ne?" Mami ta taɓe baki tana faɗin "baƙin halin ta keji ban san acikinsu da wa tayi faɗa ba. Mami,ta kare maganar tana kallon tsakanin Sadiya da Siyama kusan tare suka haɗa baki da ita akan su babu abunda suka yimata, tamkar babu AB daman a wurin ake magana abincinsa yake ci cikin natsuwa Daddy ya kalli Siyama ya bata umurnin taje ta kira Aydah. Babu jimawa Siyama, ta dawo Aydah tana bayanta da taci kuka har ta ƙoshi idanu sun mata luhu-luhu har lokacin rigar bacci ce ajikinta kallonta kurum Daddy yake har ta ƙaraso cikin rawar murya ta tare da hawayen dake son zubo mata Daddy ya amsa cike da kulawa he still looking at her "bakida lafiya ne?" Sai lokacin hawaye suka shiga zubo mata AB nagama cin abincinsa dama ko takan drama Aydah bai bi ba yayiwa iyayen nasa sai da safe da wani kalan kallo Sadiya take binsa dashi tana jin wani irin sauyi da zuciyarta ta samu game da yayan nata. Ganin yadda Aydah tabi AB da kallo yasa Daddy ya saki murmushinsu na manya watau faɗan tsakaninta ne ita da yayanta, bayan wucewar AB Daddy ya mayar da hankalinsa sosai akan Aydah yana faɗin "Da alamar kunyi faɗa ke da yayanki kuma nasan kece ba ki da gaskiya mamana. Cikin rawar murya Aydah ta ce "Dan Allah Daddy, ka basa haƙuri nasan nice bani da gaskiya ni wallahi ba zan iya jure fushin yayanmu ba. Daddy ya daga kai ya mata umurnin tagama cin abinci taje ta basa haƙuri ,abincin turasa kawai take ba tare da tasan ɗan ɗanonsa ba duk lokacin da ta tuna fuskar AB irin yadda ya fusata sai taji hankalinta ya sake tashi idan yayan nata yana fushi da ita har rashin lafiya take ita ma Sadiya AB na barin cikin dinning area ɗin tabar wurin haka kurum take ganin wurin yayi mata fili na ban mamaki ta rasa meke faruwa da ita akan yaya Abba, ko muryarsa taji a parlor suna magana da Aydah wani irin faɗuwar gaba take ji ranar kuma da basu haɗu ba jin take kamar bata da lafiya duk yadda take son dawo da kusancin su kamar yadda suke ada yaƙi bata dama ya rufe kowacce hanya gaisuwarta ma sai yaga dama yake amsawa yau a baƙin ƙofar parlor ta tsaya tana knocking tunda tasan ita mai laifi ce, jin shiru yasa ta shiga Parlor kai tsaye da sallama a bakinta ga mamakinta yana zaune acikin Parlon yana kallon (tvc news)da remote a hannunsa Amma ko kallon ƙofar bai yi ba ballantana tasa ran zai amsa dama tun kafin ta ƙaraso cikin parlor ya kashe Tv ya nufi master bedroom ɗinsa haɗe kanta tayi da ƙofar parlor ta fashe da kuka mai sosa rai... #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye Novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/2/2023, 4:48 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) Na JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye *RUBUTUN ƳAN TAGWAYE ZANGO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* 013. https://www.tiktok.com/@maims_kiddies "Lallai Dr irin wannan kyau haka tamkar kunzo daga ƙasar UK? Gaskiya kayan jikin su Hanan sunyi matukar kyau, amma dai ba'a ƙasar nan kuka siya ba?" Cikin dariya Dr Aisha tace. "A ƙasar nan muka siya, sai dai kamar yadda kika ce ɗin haka ne, duk wannan kayan da kika gani a jikin yaran nan na ƙasar UK ne da *@Maims_kiddie* take sai da su a cikin Nigeria, muma a wajanta muka siya kuma ba tare da munje inda take ba, kayan na gani a Instagram account ɗin ta na *KIDS THRIFTY/OKRIKA STORE.* Kayane masu kyau da kwari daki bari kenan malam Khadija dan tun da na fara siyan kayan yara a wajanta shikenan na dena ganin kyawun na ko'ina. Kema/kuma zaku iya nemanta a Instagram link ɗin dake sama. Za kuma ku iya samunta a WhatsApp ta wannan link ɗin dake ƙasa. Ko lambar wayarta. https://Wa.me//08101378616 Siyama ta turo kofar room ɗin Sadiya ganinta zaune a bakin gado daga ita sai towel ajikinta da alamar ko wanka batayi ba. Sai wayar hannunta da take famar dannawa da mamaki Siyama ke faɗin."Daman yaya Sadiya ba yanzu za ki tafi school ba?" Dan Allah karki sakani latti yau wanda zai ɗauke mu lecture yana da zafi ko minti ɗaya ka kara bai zai bar ka ka shigar masa aji ba. "Ni nace ki jirani Siyama ku yi tafiyanku kawai sai zuwa anjima zan tafi. Jin haka yasa Siyama ta juya tabar ɗakin da sauri yar ajiyar zuciya Sadiya ta sauke tasan ita ma tana da lecture ƙarfe takwas na safiyar yau Amma tafiso tayi asarar ta in har zata saka Abba Bashir cikin kwayar idanunta jiya kwana tayi da tunaninsa manne da zuciyarta kowanne juyi da take cikin baccinta shine mutum na farko dake faɗo mata arai ta kudurta aranta yau komai zai faru sai AB ya sauketa a makaranta. Siyama tana sauka a kasan stairs ta samu Aydah goye da schoolbag ɗinta ga tea da Huwaila mai aiki ta kawo mata da wainar kwai a sama ko taɓawa batayi ba ."wato dan ki ɓatamin lokaci ko breakfast ɗin baki fara yi ba salon ki jamin masifa. Siyama ta faɗa rai a ɓace maimakon Aydah ta tankata kamar yadda ta saba miƙewa tsaye tayi ta nufi ƙofar ficewa daga parlon ba tare da ta ko kalli gun da Siyama take ba wani irin ƙwafa Siyama tayi tabi bayanta Aranta take faɗin."Ai gara ma da suka samu matsala da yaya Abban,ya rufe masu bakin rashin kunya na kwana biyu Aydah aka fara saukewa sa'annan aka wuce da Siyama. Daga shi sai mami ne zaune cikin dining area suna breakfast har yayi shirin zuwa office cikin ruwan tokan italyn suit wanda sukayi matuƙar karbarsa suka fito da ainahin kyawonsa a sarari ƙamshinsa ga baki ɗaya ya gama gauraye parlorn, da shirinta na zuwa makaranta ta fito cikin Parlor har cikin parlorn ta taka tamkar mai tausayin ƙasa ga sauyin bugun zuciyarta da ya sauya nan take ganin ƴaƴanta zaune cikin dining area ɗin yana breakfast, taja kujerar gafda shi ta zauna ta kalli Mami ,ta gaisheta Mami ta amsa tana faɗin."daman bata fita ba?" ta amsawa Mamin da sai karfe goma take da lecture,ta wutsiyar ido take kallon AB yadda ya yi kamar bai san tana wurin ba."Yayanmu ina kwana, Sadiya ta faɗa a natse ba yadda ya iya dole ya amsa mata kodan saboda Sadiya ɗin jinin Daddy ce da kuma Mami ,ya ture plate ɗin gabansa ya zari tissue ya goge bakinsa ya mike tsaye kitchen ya nufa ya wanko bakinsa ya dawo ya kalli Mami yana faɗin."Mami na fita. A natse Mami ke masa addu'ar Allah ya bada sa'a ya amsa da Ameen,da sauri Sadiya ta miƙe tsaye ta marairaice fuska tana faɗin "yaya Abba, ka ɗan saukeni makarantar mana. Juyawa yayi batare da yace komai ba jin haka ta juya ita ma tabi bayansa da sauri binsu kurum mami tayi da kallo acan ƙasan ranta sai taji duk babu dadi da Daddy bai yi gaggawa ba akan yaran nan da yanzu suna ƙarƙashin innuwar aure, yadda ta lura da Sadiya kamar ta fara saukowa shi Abba ɗin ne ma kamar har yanzu bai sauko ba, Tana tsaye ajikin motarsa tana jiran ya fito daga part ɗinsa bai jima ba ya fito dauke da briefcase ɗinsa wani irin yanayin take ji game da yayan nata bata san Meyasa tayi gajen haƙuri ba da yanzu tana ƙarƙashin kulawar Abba Bashir, bata san Meyasa ta biyewa son zuciyarta ba da gaske yanzu tana son zaman aure tare da yayan nata sai yanzu take hango wani irin quality da attributes akan yayan nata har ya buɗe mota ya shiga Sadiya ta tafi duniyar tunani sai da ta ji wani irin gigitatcen horn da ya ratsa har tsakiyyar kwanyar kanta shi ya dawo da ita hankalinta da sauri ta buɗe front seat ta yiwa kanta masauki gami da rufo ƙofar a hankali maigadi ya buɗe masu get suka fice daga gidan Kai tsaye hanyar makarantarsu ya ɗauke kan motarsa banda kira'ar (Ahmad sulaiman )dake tashi cikin motar cikin suratul bakara ba kyajin komai a motar, wayarsa ce ta soma ringing ya rage volume haka ya rage gudun motar yasa wayar a speaker dama kuma ɗabi'arsa ce in har yana tuki zai yi wuya ya dauki waya sai dai ya barta a speaker."Habibi ina kwana.! "Rumaisa! Ya faɗa cikin muryar jan hankali wani irin dokawa kirjin Sadiya ya yi jin wata macce ta kira yaya Abbanta da Habibi, nan take farin cikin dake cikin fuskarta ya ɓace bat."Ya ki ke?"Lafiya lau ya maganar fitar mu zuwa anjima karka shanyani dan Allah nasan halinka wallahi ina buƙatar yin shopping yau kayan shafana sun kare. Ta ƙarashe maganar cikin muryar shagwaɓa mai dauke da wani irin shauƙi "Bayan la'asar yayi maki?"yeah! "Owk idan zan shigo zan kiraki. Daga haka ya sauke wayar har ya kai Sadiya makaranta ranta a ɓace yake ko kallonta bai yi ba balle ya gane yanayin da ta shiga. a ranar kakaf Sadiya bata shiga lectures ɗin dake gareta ba yanayin yadda Yaya Abba, ke waya da Rumaisa ya yi mugun daga hankalin ta ƙarfe biyu nayi ta biyo Siyama zuwa gida tana jin kamar zazzaɓi zai rufeta tambayar farko da Siyama tayi mata ita ce."Bakida Lafiya ne yaya Sadiya? "kaina ke ciwo. Sadiya ta faɗa gami da dauke kanta tana mayarwa kan titi inda ababen hawa ke kai da kawo. A hankali Siyama tace "Allah ya sauwakke. A parlor suka sami Mami tare da Aydah ita ma ta dawo da nata zazzaɓi, har Siyama da Sadiya suka tausayawa little sis ɗin tasu ganin yadda ta rame lokaci ɗaya. Sun san idan yaya Abba,yayi fushi da ita duk cikinsu ita ce marar juriyar daukar fushinsa yanzu nan zata kwanta ciwo."Mami jikinta da zafi sosai kuma ba a kira family doctor ba ya dubata?" Sadiya ta faɗa da damuwa sosai a fuskarta, "kin manta baya gari sai dai idan za ki yi sallah ki ci abinci sai ku je asibiti da driver a duba ta ɗin. Mami ta faɗa tana shafar kalabar kan Aydah. Da sauri Aydah ta buɗe idanunta da suka kada suka canja kala "Ni bana son ta kaini wata asibiti yayamu nake so yazo ya kaini."ta karasa maganar cike da zallan rigima. "auuhhhh Allah? kin manta fushi yaya keyi dake?" Banza Aydah ta yiwa Siyama ta koma ta kwanta cike da damuwa Sadiya ke faɗin."To ke Mami ki kirasa ya kai ta mana kin san shima yanzu zai rikice idan ya ji ance bata da lafiya. Acan ƙasan ran sadiya kuwa har addu'a take fitar da zai yi da budurwarsa ya watse. Mami dai bata kara cewa komai ba daman Siyama, ta daɗe da wucewarta ɗaki dan zafi take ji tana buƙatar watsa ruwa yau garin an zuba rana sai kusan ƙarfe 3 Abba, ya shigo gidan ko kaɗan baya ƙaunar zafi kai tsaye part ɗinsa ya nufa ya rage kayan jikinsa ya yi wanka. Ya shirya cikin ƙanunun kaya marar nauyi yayi matuƙar kyau acikinsu kana ya wuce cikin gida mami ce a parlor da Siyama tana danna waya da kayan shan iska ajikinta ga baki ɗaya cinyoyinta a waje suke kallo ɗaya ya yi mata ya dauke kai, mami tana kallonsa ya gaisheta ta amsa tana tambayarsa ya aiki?"ya amsa da Al-hamdullilah, Siyama ce ta kawo masa abincin rana cikin parlor ,ya kalleta in a serious note yake faɗin."Daga yau kar ki ƙara zama da waɗannan kayan acikin parlon gidan nan. ɗaga kai kurum ta yi ta juya tabar cikin parlorn Mami tace ta fadawa Aydah ta fito idan ya gama cin abinci ya kai ta asibiti A natse Abba ke cin abincinsa yana tambayar mamin me kuma ya sami Aydan? "Tun da ta dawo school take kwance zazzaɓi ne kawai sai dai kasan halinta da mugun raki. Murmushi ya yiwa mami yasan gaskiya ta faɗa kuma yasan ciwon yana da alaƙa da fushin da yake da ita Siyama ta leƙa ɗakin Aydah duk wannan uban zafin harda su lullube jiki da duvet ta kira sunanta tana faɗin "ki taso yaya Abba, ya dawo ya kai ki kiga likita. Jin an ambaci yayanta ta cire duvet ɗin jikinta da sauri duk da jirin da take ji dan komai taki yadda taci haka ta nufi toilet ta wanko bakinta hijab ɗinta na sallah ta ɗora akan rigarta tun daga kan stairs yake kallon yadda take layi tamkar zata faɗi ita ma ta zuba idanunta acikin nasa tai wani marairaice masa har kusa dashi taje ta zauna tana gaishesa ya amsa yana tambayarta ya jikin."ta amsa da sauki ,hannunsa ya kai a forehand ɗinta saboda zafi ya yi saurin janye hannunsa, "kin ci abinci?" Da sauri ta girgiza kanta yayin da hawaye na taruwa acikin idanunta "Na zuba miki za ki iyaci?" Ɗaga masa kai ta yi da sauri wani irin daɗi na lulluɓeta ,da kansa ya miƙe tsaye ya nufi cikin dining area din ya zubo mata white rice kaɗan da stew a sama da naman rago. ya dawo ya miƙa mata ta fara cin shinkafar a hankali badan tana jin daɗinta ba kaɗan taci tace ta koshi Abba ,ya miƙe tsaye yana kallonta ya ce."su je taga doctor ta marairaice masa tamkar zata yi kuka."banda allura yayanmu. Wani kallo ya yi mata kana ya miƙe tsaye ya kalli watch ɗin dake hannunsa bai fi minti ashirin ba a kira sallar la'asar yace ta jirasa kai tsaye stairs ya nufa har zuwa ɗakin Mami, sai da aka basa izinin shiga ya shiga da sallama a bakin ƙofa ya tsaya yana faɗawa Mami za su je asibiti , mami ta faɗa masa babu komai acikinta ya samu ko tea tasha Ya faɗawa Mami ,ai ya zuba mata abinci taci ƙadan. Mami ta hararesa tana cewa "Daman ciwon nata na gulma ne. Ya ware ido yana faɗin."Da gaske take Mami ba ki ji jikinta ba akwai zafi sosai. Mami ta taɓe baki tana faɗin."Duk ba iskanci bane ka bi ka sangartata. Murmushi Kurum ya yi yabar ɗakin na Mami kusan cin karo suka yi da Sadiya da sauri ya ja da baya Ta gaishesa ya amsa ya wani dauke kai ya soma sauka akan stairs da ido ta bisa har ya ɓacewa ganinta. Tun kafin su isa inda file ɗin duka yan gidan yake ya yi waya da Dr Musa akan suna hanya yasa a fitar da file ɗin Aydah zai dubata bata da lafiya. Dr.musa yana ta yiwa Aydah tambayoyi tana basa amsa har ya gama rubutun da yake a takarda ya miƙawa AB yana masa bayanin drugs din da za a siya mata ne ya faɗa masa sai sunyi mata allura tun kafin azo kan allurar ta fara hawaye AB ya dauke kansa bai ma san tanayi ba har nurse ta kawo allurar da za ayi mata guda biyu, tunda Dr Musa ya fara haɗa allura ta fashe da kukan da yasa Abba yimata tsawa gyara ayi miki kina ɓatamin lokaci, Abba ya faɗa yana yimata tsawa ta buɗe hannunta tana miƙawa Dr Musa dake yimata Dariyar tsoron allura a baya za a yi miki da sauri ta kalli AB kusan minti goma Aydah taki tsayawa ayi mata allura ganin tana ta ɓata masa lokaci har anyi kiran sallah ,yasa ya wani fisgota ya matseta cikin jikinsa tsit tayi har aka gama duka biyun bata san anyi ba har kuma lokacin hawaye take cikin tsokana doctor Musa ke faɗin."ke gaki kin zama yanmata amma kina tsoron allura ita dai batace komai ba ta nufi ƙofa ta fice daga office ɗin AB ya tsaya yana yiwa doctor Musa godiya kafin yabi bayan Aydah acan bakin motarsa ya cimmata tana kuka ko kallonta bai yi ba ya shiga mota dole ta buɗe ta shiga ya tsaya ya siya mata drugs "za ki sha rufaidah?"daga masa kai tayi still fuskarta na cikin hijab furar rufaidah ya siya mata har roba biyu da gasassar kaza ita ma biyu duk kayan jinya ne Yasan Aydah dason cin nama kamar me a haka suka isa gida da kansa ya bata drugs ,ya sumbaci goshinta a hankali ya furta."get well soon little sis fita zan yi me kike so nazo miki dashi?"ice cream ta faɗa cikin sanyi murya ,daga mata hannu yayi alamar bye-bye Sadiya dake laɓe a ƙofar kitchen tana kallonsu jin tayi wani abu na tsaya mata dai-dai tsakiyar ƙirjinta musamman yadda taga Aydah tabi yayan nasu da kallo tana binsa da murmushin da ta kasa gane ma'anarsa. #love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #team tagwaye novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/3/2023, 2:56 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love Story #Gwagwarmaya #Team tagwaye novels *RUBUTUN ƳAN TAGWAYE ZANGO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* PAID BOOK 014. https://www.tiktok.com/@maims_kiddies "Lallai Dr irin wannan kyau haka tamkar kunzo daga ƙasar UK? Gaskiya kayan jikin su Hanan sunyi matukar kyau, amma dai ba'a ƙasar nan kuka siya ba?" Cikin dariya Dr Aisha tace. "A ƙasar nan muka siya, sai dai kamar yadda kika ce ɗin haka ne, duk wannan kayan da kika gani a jikin yaran nan na ƙasar UK ne da *@Maims_kiddie* take sai da su a cikin Nigeria, muma a wajanta muka siya kuma ba tare da munje inda take ba, kayan na gani a Instagram account ɗin ta na *KIDS THRIFTY/OKRIKA STORE.* Kayane masu kyau da kwari daki bari kenan malam Khadija dan tun da na fara siyan kayan yara a wajanta shikenan na dena ganin kyawun na ko'ina. Kema/kuma zaku iya nemanta a Instagram link ɗin dake sama. Za kuma ku iya samunta a WhatsApp ta wannan link ɗin dake ƙasa. Ko lambar wayarta. https://Wa.me//08101378616 Da mamaki take ta kallon Aydah ganin yadda ta samu sauƙi lokaci ɗaya farin cikinta da walwalarta suka dawo. Acan wani ɓangaren na zuciyar Sadiya yake faɗa mata ko dai Aydah ta faɗa son yaya Abbane?? Da sauri wata zuciyar ta kwaɓeta da ba hakanan bane shaƙuwa ce kawai,a shekarun Aydah ai ba za ta san menene ma soyayya ba. A zahirance jin tayi ƙafafunta sunyi mata wani irin nauyi na ban mamaki haka ta ja ƙafafunta ta fito daga kitchen ɗin tana ta kallon Aydah dake ta shan furarta a hankali cikin natsuwa da nishadi da sauri ta dauke kanta akan ƙanwarta ta, ta nufi stairs. Shopping Rumaisa ta yi sosai sai wurin biya kuɗi ne AB ya bada card ɗinsa aka cire kuɗin a hanyar dawowarsu ne take faɗa masa mahaifinta baya gari da ya dawo zata zauna dashi ta fahimtar dashi ƙofar gida kawai ya ajeta batare da ya shiga ciki ba ya juya kan motar zuwa gida yana isa ana kiran sallar magarib parking motar kawai ya yi kana ya yi alwallah ya shiga masallacin dake cikin unguwarsu bashi ya shigo gida ba sai bayan sallar isha kai tsaye cikin gida ya nufa dukkansu suna zaune a parlor ya kai kallonsa gurin Aydah dake kwance cikin doguwar kujera cike da kulawa ya ce "Ya jikin naki zafin sa ya sauka?" Ɗaga masa kai tayi alamar "eh! "kinci abinci kin sha magani?" nan ma amsa masa tayi kai tsaye parlorn Daddy ya nufa da respect ya gaishe da Daddy dan tun safe basu haɗu ba ya amsa cike da kulawa kafin ya ɗora da faɗin."hope kun samu fahimtar juna da Mufeeda?" Na faɗa maka bana son aurenku ya ɗauki dogon lokaci ko ɗazu muna tare da Alhaji Habib ,yadda yake zancenka da alamar yar tasa tayi amanna dakai ta karbeka a matsayin mijin aurenta. Ina son ka saki jikinka Abba insha Allahu wannan auren alkhairi ne zan ƙara maka sati ɗaya kafin ku ƙara shaƙuwa da yarinyar daga nan zan tura a nemar maka aurenta. Tun sanda Daddy, ya fara yi masa zancen auren Mufeeda komai ya kwace masa har suka gama cin abincin dare ya kasa maida walwalarsa Sadiya sai nazarta yanayinsa take bai jima tare dasu ba ya koma ɓangarensa sai bayan wucewarsa ne Daddy ke yiwa Mami zancen yar gidan Alhaji Habib, Mami tayi Allah ya sanya Alkhairi hakama sauran ƙannen nasa Siyama da Aydah sosai suke farin ciki da auren yayan nasu banda Sadiya da ta ji komai ya fice mata arai a daren ranar ba ƙaramin kokuwa Sadiya ta dinga yi da numafashinta ba har ma da zuciyarta. Wai yaya Abbane zai yi aure sai ta samu kanta da wani irin kishinsa na ban mamaki wanda bata taɓa jin kalarsa ba ,da alamar iyayenta sun riga sun haramta zaman aure a tsakaninsu, tasan ta yi laifi ta kuma amshi laifinta da hannu bibbiyu kuma ai saki daya ne yaya Abban ya yi mata ko yanzu yace ya mayar da ita za su ci-gaba da zaman aurensu. Har ƙarfe goma na safe Sadiya tana dunƙule a ɗaki cikin duvet dare ɗaya ta fice daga hayyacinta ta yi wani irin zuru-zuru duk akan zancen auren Abba Bashir da Daddy yasa a gaba yau ta yi sa'a bata da lecture ko ɗaya haka kuma ranar jumu'a ne, sosai Mami ,tasha mamaki har ƙarfe goma da kusan rabi na safe bata ga wurgawar Sadiya cikin parkon ba. Bayan Daddy ya wuce office kai tsaye ta nufi ɗakin Sadiya tsayawa ta yi kanta tana kiran sunanta a hankali ta buɗe idanunta da suka canja kala, alamar dai babu wani wadatatccen bacci acikin su "Ke lafiya meya faru? Sadiya ta miƙe zaune a hankali tana sakin 'yar ƙaramar miƙa a hankali tare da faɗin. "Mami ina kwana?" Mami ta amsa da "lafiya lau! Mami dai sai kallonta take kafin ta juya tana faɗin."Tun da lafiyarki ƙalau ai shike nan, daga haka Mami ta fice daga ɗakin tana son ta yi zancen aurenta da yaya Abba da Mami sai dai bata san ta inda zata fara ba. shi ma a ɓangaren yaya Abba, yaƙi bata fuska ta tsaya tayi doguwar magana dashi duk wata hanyar da zata yi magana mai tsayi dashi ya tosheta. A haka kwanaki suka riƙa gudu Sadiya tana ta ƙunci ita ɗaya kullum tunanin yayan nata manne a zuciyarta satin da aka kai kayan auren yaya Abba har zazzaɓi tayi ita ɗaya ke jinyar zuciyarta. Sai washe gari Alh Sanusi yasan cewa 'yar gidan Alh Habeeb bichi ce Abba zai aura ranar Assabar ce ƙarfe takwas na safe ya fice daga gidansa cikin tashin hankali ko karin kumallo bai yi ba yana tuƙi yana tsinewa yayansa dan ko maganar auren Abba ɗin bata taɓa haɗasa dashi ba. Wani murmushin takaici yayi takwas da mintuna ya tsayar da motarsa a get ɗin gidan Alh Habeeb bichi da mamaki maigadi ya leiƙo ta ƙaramar ƙofa yana ƙarewa motar kallo da ta zama baƙuwa a wajensa, A fusace Alh Sanusi ya sauke glass yana kumfar baki "Malam baka san aikin ka bane ?" Ka tsaya kana wani kallo na kamar tsohon maye, kalaman Alh Sanusi ba ƙaramin konawa maigadi rai suka yi ba shima a kufule ya ce "malam lafiya ban taba ganin koda fuskar ka ba ballatana motar da kazo da ita wurin wa kazo da sanyi safiya haka? wurin maigidan nazo ko banyi matsayin da zanzo wurinsa ba?" Wani kallo maigadi ya yi masa kafin yace "Ni babu wanda ya sanar dani zuwanka da safen nan kuma maigida yanzu haka bacci yake. Rai bace Alh Sanusi ya fito daga motarsa tuni maigadi ya mayar da kofar ya rufe haka Alh Sanusi ya rika dukan get tamkar wani zautatce yana zagin maigadi yana kiransa matsiyaci talaka tamkar a mafarki maman Mufeeda dake kitchen taji ana buga get da ƙarfi da sauri ta fito kitchen tana kallon mai aikinta Lanto tana faɗin ta je taga ina maigadi ya shiga baya jin ana buga ƙofa ne da ladabi Lanto ta juya ta yi hanyar ficewa daga parlon ,a kan benci ta samu Mudi mai gadi ya ƙure volume ɗin redio da mamaki tace "Mudi baka jin ana buga get ne? Wani kallo ya yi mata ya dauke kansa, rai a ɓace ta nufi get ta buɗe karamar kofa suka yi ido huɗu da Alh Sanusi da ransa ya gama ɓaci da ladabi Lanto ta gaishesa tana tambayarsa wurin wa yazo? Ya faɗa mata wurin maigidan yazo maigadi yai masa wulaƙanci ya zagesa ya rufe masa ƙofa Lanto tace ya shigo daga ciki zata je ta faɗawa Hajiyar gidan. Har cikin compound Lanto ta shigo da Alh Sanusi dake famar dokawa maigadi harara da yake kare da dan redionsa a kunne tamkar bai san da zamansu ba ,a lokacin Alh Sanusi jin yake tamkar ya je ya kwaɗawa maigadi mari da mamaki maman Mufeeda ke kallon Lanto dake kora mata zancen yadda maigadi ya yiwa bakon Alhaji koda ta tarar da Alhaji Habeeb ya tashi daga bacci sai dai da alamar bai daɗe da tashi ba. Tambayar da ya fara yi mata shine wa ke ta buga get haka bugun ne ya tashesa daga bacci tace masa shine dalilin da ya kawota ta faɗa masa yana da bako a waje maigadi ne ya hanasa shigowa shine ya rika buga get Alh Habeeb dai yana ta juya kalmar bako aransa da safiyar nan, Daman akwai jallabiyya ajikinsa casual slippers kawai ya saka wa ƙafarsa ya bi ta cikin balcony, zuwa cikin compound Alh Sanusi na hango fitowarsa ya washe haƙora tun kafin ya ƙaraso gun sa ya taresa ya saukar da kai ya basa hannu with respect suka yi musabaha, Sanusi kaine da safen nan haka? Allah yasa lafiya?" Alh Habeeb ya ƙarasa zancen yana kallon Alh. Sanusi dake famar shafa kansa "wallahi kuwa Alh wata magana ce mai muhimmanci nazo muyi da kai. "To mu ƙarasa daga ciki har cikin balcony ya kai sa wurin akwai kujeru acikinsa suka zauna suka ƙara gaisawa kafin Alh Sanusi ya nisa yana faɗin."Ashe yar wajenka ce zata auri Abba Alh? murmushi Alh Habeeb ya yi yana faɗin "kaima dai Sanusi da son zance kake kar dai ka ce min ba ka da labari zance aure nasu? Wasu yawun baƙin ciki Alh Sanusi ya haɗe yana faɗin "Aini wallahi yaya Bashir ya bani mamaki ace ya rasa wanda zai cuta sai kai. Da mamaki Alh Habeeb ke kallon fuskar Alh Sanusi dan ko kaɗan bai dago zancen nasa ba "Sanusi wacce irin magana kake faɗa haka? Ban gane ba. "Ai ba zaka gane ba Alh Habeeb yaya ya faɗa ma dalilin fasa auren Abba na farko?" Ɗan shiru Alh Habeeb,ya yi kafin yace "kasan lokacin da aka yi auren bana gari so yace matsala aka samu ba a ma daura auren ba. Alh Sanusi ya riƙe baki yana ƙara gyara zama ya ce "waton dai aminci ya yi wuya yanzu a wannan duniyar, nan take Alh Sanusi ya fara bai wa Alh Habeeb labari akan rashin yiyuwar auren Abba ,na farko har Alh Bashir ya aura masa Sadiya yar wajensa yanzun ma haka sun rabu ta dalilin daren aurensu na farko ta caka masa wuka. Sosai Alh Habeeb ya tsorata da lamarin jikinsa lokaci ɗaya ya yi sanyi ransa yai masifaffen ɓaci akan ha'intarsa da Alh bashir ya yi ai ba irin wannan maganar ake ɓoyewa ba wato shiyasa ya rika yi masa zarya a office yana son a saka auren Abban da Mufeeda da wuri ,ta yadda ba zai ɗauki lokaci ba yasan yaron ma shege ne bai da uba bai da asali azo a kakkabawa 'yarsa ko 'yarsa ta rasa mijin aure ba zata auri marar asali tsintatce ba. Haka dai Alh Sanusi ya baro gidan ransa fess! Da yake ranar Assabar ne ana hutun ƙarshen mako ba a fita aiki Alh Habeeb yana gama karin kumallo ya ɗauki motarsa sai gidan Alh Bashir wanda sosai Alh Bashir ya yi mamakin ganin aminin nasa har parlorn sa suka ƙarasa sama-sama suka gaisa ganin yadda fuskar Alh Habeeb take a mugun murtuƙe sai da ya daga hankalin Daddy A natse Alh Habeeb ke faɗin."Dama Alh Bashir Abba ,ba ɗan cikin ka bane?" kuma da gaske shege ne ba kai ka haifesa ba?" A razane Daddy ke kallon Alh Habeeb jin irin kalaman da yake jifar Abba dasu. Rai a ɓace Daddy ke fadin "Habibu kana cikin right mind ɗinka kuwa?" Shi ma Alh Habeeb a hasale ya katse sa ta hanyar faɗin "Da hankali na Bashir ka amsa min tambayar da nayi maka a farko. "Abba ɗana ne sai dai bani bane biological father ɗinsa he's adopted child by me and I love him more than my own childrens. murmushin takaici Alh Habeeb ya yi yana huci yake faɗin "Amma gaskiya Alh Bashir ba kada cikkaken hankali ta ya za ka yi adopting ɗa ba kasan ta wacce hanya siga aka samar dashi ba. Ka garwaye shi cikin 'ya'yanka na halak gudan jininka har kana kirari ka fi sonshi fiye da 'ya'yan da ka haifa. Wannan wane irin sakalci ne? "Alh Habeeb ka faɗamin inda aka haramta adoption? "Babu inda aka haramta adoption Alh Bashir sai dai ya haramta ta hanyar da kai ka yi shi meyasa ka ɓoyewa duniya sahihiyar gaskiya akan Abba?" "Saboda bana kallonsa a matsayin adopted child face ɗan da na haifa da jini jikina. "Amma ina fatar kasan da cewa Abba bayada gadonka? "Na sani mana tun da ni ba jahili bane. "To da ace wannan sirri bai fito ba ta Allah ta kasance da kai kuma shikenan sai Abba ya ci gadonka? "Alh Habeeb ka daina yi min kallo jahili mutum tun-tuni na rubuta (wasiyya) na ware kason Abba a cikin dukiya ta. Sosai Alh Habeeb yasa dariya mai cike da zallan takaici kafin ya kalli Alh Bashir a shaƙeƙe ya ce "Yarka taƙi zaman aure dashi ni kuma kake son kakkabawa tawa 'ya lallai Bashir baka da ta ido wallahi, to kasani ko dukka dukiyarka kabar wasiyya a ba wa Abba aure tsakanin sa da 'yata ba zai yiwu ba wallahi. A je can a samu wata shegiyar a aura masa ba dai 'yata ba. Alh Habeeb yana gama faɗar haka ya kakkaɓe babbar rigarsa yabar parlon a mugun fusace karo suka ci da Mami, wacce ko takan gaisuwarta bai bi ba sai da gabanta ya fadi ganin yadda Alh Habeeb ɗin ya fito a parlon maigidan nata da sauri ta faɗa parlorn Daddy ta isko shi dafe da ƙirjinsa yana ta kokuwa da numfashinsa Mami ta kwala ihu tayi kansa a guje tana kiran sunansa ta kama shi ga baki ɗaya Daddy sai zufa yake haɗawa jikinsa na wata irin kakkarwa da dukkan ƙarfinta Mami ta shiga kiran 'ya'yanta kusan a guje suka shigo parlon na Daddyn nasu ganin halin da mahaifinsu yake ciki duk suka yi kansa a guje ,a ruɗe Mami ta ce a kira mata Abba duk ƙarfin zuciya irin na mami wannan karon hawaye ke fita acikin fuskarta. #love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/4/2023, 8:35 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye novels *LAST FREE PAGE.* *RUBUTUN ƳAN TAGWAYE ZANGO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* PAID BOOK 015.. Siyama ce ta kwasa da gudu ta nufi part ɗin AB yana zaune a parlor da laptop a gabansa online meeting suke yi da Kamfani whitepaper Automotive industry Germany tare da haɗin gwiwar kamfanin Two stars Automobile industry wanda suma suna da hannun jari da whitepaper yanzu kuma suna buƙatar ƙula yarjejeniyar kasuwanci da kamfani su AB saboda kusan duk wasu sababbin motoci a tare kamfani na whitepaper ke turo musu. Yadda Siyama ta turo ƙofa da ƙarfi ya jawo hankali AB zuwa gare ta sai uban haki take "Ya Abba kazo Daddy ba shi da lafiya dakyar yake iya numfashi. Siyama tayi magana cikin harɗewa harshe, duk da hankali Abba ya yi mugun tashi sai dai ba za ka taɓa fahimtar hakan ba, saboda a natse ya kalli team members da suke meeting ɗin ya faɗa musu uzurinsa kana suka yiwa Daddy fatan samun lafiya ya rufe laptop ɗin. Ya nufi ƙofar fita cikin tafiyarsa ta natsuwa tuni Siyama ta wuce shi hali da yaga Daddy aciki ya yi masifar ɗaga masa hankali, da taimakon direban gidan suka ka kai Daddy cikin mota AB bai tsaya jiran su Mami su fito ba ya umurce direban da ya ja mota su tafi. Koda Mami da girls ɗinta suka fito su AB sun wuce sai Aydah ce ta koma ciki gida ta daukowa Mami makullin mota hankali tashe Mami ta iso farfajiyar International private hospital wanda shine asibiti da suke da file. Su Mami basu sha wahala gani AB da direba dake safa da marwa a ƙofar ɗakin da aka shigar da Daddy. Dukkansu tsaye suka yi cirko-cirko Aydah sarkin kuka gaba ɗaya fuskarta ta kwabe da hawaye da majina. *KIM'S AUTOMOBILE INDUSTRY LAGOS* Kyakkyawar matashiyar budurwa ce ta fito daga ofishinta dake hawa na biyu jikinta sanye da california pink gown wacce ta bayyanar da sirri kyawonta, hannunta ɗauke da wasu tarin files kaitsaye elevator ta hau wanda zai kaita hawa na biyar idan ofishin Chairman na kamfani yake. Sai da ta tsaya suka gaisa da ASM na Kamfani (Assistant stage manage) da shima ya fito daga office ɗin Chairman, sun ɓata almost a ten good minutes suna tattaunawa dangane da sababbin motoci da wani ƙaramin kamfani ke so. Sai da tayi using da key card ɗinta kana ƙofar ta buɗe ta shiga wani irin ni'imatatcen sanyi mai ɗauke da tsadadden ƙamshin turarensa ya lulluɓeta har batasan sanda ta lumsashe ƙanana idanuwanta kafin ta buɗe su ta ci-gaba da takawa har izuwa gaban desk ɗinsa ya juya mata baya iya gadon bayansa take iya gani sai kuma fararen hannayensa da ya haɗe su guri guda, cikin sanyi muryata ta furta "Welcome back Abbu! Sai da ya kusan share 60 seconds kafin ya juyo da kujerar izuwa gareta fuskarsa a haɗe as usual Alhaji Aliyu Usman Mustapha na uku kenan Chairman of Kim's Automobile industry. "Anaal ina raguwar 'yan uwanki ne da na ganki ke kaɗai ko su ba su sami sako neman su da nake ba? I have some important issue to discuss it with you. "Abbu all of them are not in the company tun sanda ka yi tafiya suka daina zuwa I am the only one who takes care of the company. Ta ƙarasa maganar kaman za ta sa kuka irin wahala ta yi mata yawa. Sosai ran Alhaji Aliyu ya ɓace ya rasa gane me ke damun Zeeyad da Zaheed da basan so maida hankali akan aikinsu, Anaal da take macce ma ta fi su maida hankali, a fusace ya furta "kira su a waya ki faɗa masu ina so ganinsu nan da ten minutes a conference hall, muna da meeting na gaggawa don ba zan ci-gaba da zuba musu ido suna yiwa kamfani riƙo sakainiyar kashi. Ran Anaal ya yi fari tass! Cike da zumuɗi ta yi dialling numbern Zaheed kuma tsabar mugunta sai ta saka wayar a speaker "real disturber ya aka yi ne?" "Yaya Abbu ya ce na sanarda kai yana so ganinka nan da ten minutes a conference hall. "Ke banaso karya ko Abbu zai dawo sai next week saboda haka ki je ki cigaba da aikin gabanki agogo sarkin aiki. "I swear to God Abbu ya dawo. "What! Yaushe ya dawo? "Yesterday night! "To dan ƙaniyarki me ya hana ki faɗamin tun jiya ɗin? "Yaya Zaheed na saka wayan a speaker duk abunda kake faɗa Abbu yana ji ka kuma san baya so kalaman rashin ɗa'a. Ai kuwa da sauri Zaheed ya yi hanging up. Ta kira Zeeyad koda kiranta ya shigo yana sharar bacci abinsa dakyar ma ya yi picking call ɗinta cikin muryar bacci ya fara zazzaga mata masifa, sai da ya yi mai isarsa kafin ta sanarda shi saƙon Abbu, a firgice ya ture duvet ɗin jikinsa ya faɗa bathroom da gudu. Anaal sai faman ƙunshe dariyarta take yi dakyar ta saita kanta cike da respect ta miƙawa Abbu files ɗin hannunta "Abbu ga files ɗin kula yarjejeniyar kasuwanci da kamfanoni dake da sha'awar motocin mu. Sai kuma ɗayan file ɗin na mr Anthony ne yana so Kamfani ta bashi motoci ɗari zai yi half payment saboda kamfaninsa yana fuskantar financial crisis yana so ya farfaɗo. Sai kuma wannan file ɗin kamfani whitepaper Automotive Germany suna buƙatar saka hannun jari a kamfanin mu amma fa haɗin gwiwa ne da kamfani moonlight dake Kano. Abbu idan za ka tuna na taɓa ba ka labari wannan kamfani ɗin da yadda suka yi shura wajen kawo latest cars and car accessories ko lokaci da Mercedes Benz C43-four door ta fito sun ri ga mu shigowa da ita nayi following Instagram handle na Chief Executive officer na kamfani Abba Bashir Abbu jiya-jiya nan ya ɗora the upcoming 2024 model C63 bai kamata mu jinkirta accepting offer ɗinsu ba. Saboda idan muka haɗa gwiwa dasu za mu ƙaru dasu duk faɗin arewacin Najeriya sune lamba ta ɗaya wajen shigowa da sababbin motoci, kaman yadda kamfanin mu ya cire tuta a kudancin Najeriya. Har Anaal ta dasa aya a dogon sharhinta Abbu bai tofa uffan ba hakazalika bai katse ta ba. Gani ta kai ƙarshen zance nata ya ɗan murmusa cike da izzarsa da jini sarauta da ya gama ratsa jikinsa yace "Ki haɗa mana zama dasu amma ki tabbata su ne za su zo ba mune za mu je musu ba. "Okay Abbu! Anaal ta faɗa cike da farin ciki saboda tun lokaci da ta yi following ɗin Abba Bashir a Instagram ta ji yana burge ta musamman yadda yake hardworking tana so taga mutum ya ɗauki aikinsa da muhimmanci ba kaman stupid twins cousin ɗinta ba da abinda suka iya sai lalaci da shegen son jiki tsiya ko ita da take ta mace ta fi su. Da fice daga office ɗin tana ƙoƙari shiga elevator sai ga Zaheed, mugun kallo ya wulga mata ya yi ƙwafa kana ya wuce office ɗin Abbu. Bayan sun fito daga meeting wanda kusan rabinsa faɗa ne Abbu ya dinga yiwa twins akan rashin maida hankali da suke yiwa kamfani. Abbu yana ficewa daga hall ɗin cikin sauri Anaal ta kwashe wayoyinta, da nufi ta gudu domin ta tabbata idan twins suka rutsa ta za ta ji jiki. Da sauri ta kutsa cikin ayarin team members da suke ƙoƙari fita daga hall ɗin, karaf ta ji an riƙe mata hannu a tsorace ta sauke ƙanana idanuwanta akan fuskar Zeeyad ɗayan hannunta ta ji an sake kamawa tana juya wa taga Zaheed suna haɗa idanu ya kashe idonsa ɗaya yana mata murmushi mugunta "Meye haka? Me nayi da za ku wani rirriƙe ni kaman wata ɓarauniya? "Anaal abunda ke ɗinan ki ka yi mana gwada ɓarauniya dake. Kinsan tun jiya Abbu ya dawo meyasa ba ki sanar mana ba? Zaheed ya yi magana yana zare mata idanuwansa. Ta sheƙe da dariya tana faɗin "Akan me zan sanar daku, wato kun manta yadda ku ka barni da aiki ni kaɗai. Zeeyad ya mitsine mata fatar hannu yana faɗin "ai kuwa jikinki ne zai gayamiki ba dai taƙamar mugunta ba. Shi ma Zaheed mitsine ta ya yi sai ihu take tare da neman agaji dakyar ta samu suka sake ta farar fatar hannunta tayi shatin farce su ga Anaal da ɗan neman raki sai yarfe hannaye take tana hawaye, yayin da su kuma sai dariya suke mata kafin kuma suka dawo rarrashinta har da yi mata alƙawari kai ta shopping sai ga Anaal tana dariya. *INTERNATIONAL PRIVATE HOSPITAL KANO* Da taimakon likitoci numfashin Daddy ya daidaita kana aka yi masa fixing drip mai ɗauke da allurai saboda jininsa ne ya yi mugun hawa a lokaci da su Mami suka shiga ɗakin da aka kwatar da Daddy yana kwance magashiyam hannunsa na dama manne da drip yayin da numfashinsa na hawa da sauka alamar bacci yake yi. Jikin Mami a sanyayye ta ja plastic chair ta zauna a gefen gadonsa daidai fuskarsa Siyama da Sadiya kowacce ta ja kujera ta zauna tallaɓe da kumatu suna kallon mahaifin nasu. Aydah ce kaɗai ta kasa zama sai ta koma daidai fuskarsa Daddy ta tai tsaye lokaci zuwa lokaci take goge hawaye da bayan hannunta. Lokaci da likita ke sanar da AB makasudin ciwo Daddy sai da girgiza domin iya saninsa Daddy ba shi da cutar hawan jini, baya kuma ciki wata damuwa da za ta haddasa wa jininsa muguwar hawa, domin likitan ya faɗa masa jinin Daddy ya yi matuƙar hawa kusan 140 jikinsa a mace ya dawo ɗakin da Daddy yake ya nemi kusa da Aydah ya tsaya shi ma ya bi sahun su na kallon hawa da saukar numfashin Daddy da suke yi. Cikin sanyi murya Mami ta kira sunan AB "Abba! "Na'am Mami! "Halan me likita ya ce yana damunsa ne?" Sai da AB ya ja ƙarfaffiyar ajiyar zuciya kafin ya ce "Bai ce komai ba Mami. "A'ah! Kaman ya Abba?" ya kamata musan musababbin faruwar wannan ciwo nasa saboda na ci karo da Alh Habeeb bichi ya fito daga parlornsa kuma ga dukkan alamu ransa a ɓace yake domin ko tsayawa bai yi ba muka gaisa ina ƙarasa shiga parlorn na tarar da Alhaji yana fizgar numfashi. Ciki kaɗuwa AB yake kallon Mami sai kuma ya yi sauri kawar da fuskarsa tare da ƙoƙarin saita natsuwarsa. "Mami kada mu yi gaggawar yanke hukunci mu jira sakamakon bincike da likitoci suka yi, sune suke da hurumin yanke hukunci abinda ke damunsa. AB ya faɗa da so kawar ma Mami da zarginta. Jim kaɗan AB ya umarce Mami dasu koma gida saboda sun baro gida ba kowa Aydah bataso ta bi su Mami ba sai da AB ya yi mata tsawa kana ta fice tana sharar hawaye. Bayan tafiyarsu Mami AB ya tsunduma kogin tunani idan har lissafin sa ya tafi daidai Alh Habeeb Bichi ya zo ne akan zancen aurensa da 'yarsa Mufeeda watakila shima ya sami labari akan rashin asalinsa. Lumshe idanuwansa ya yi can ƙasan zuciyarsa yake ji wani irin tuƙuƙi baƙin ciki, shiyasa ya ce da Daddy ya jingine zance aurensa a gefe a halin da yake ciki zai iya riƙe kansa har ƙarshen rayuwarsa ba tare da aure ba. Kwata-kwata aure ya fice masa arai ƙanwarsa ma ta kasa zama dashi wa Daddy yake tunani iyayenta za su karɓe shi a yadda yake. AB bai ankara ba ya ji zafafan hawaye na bin kumatunsa. Sai dab da magarib Mami da girls ɗinta suka dawo ɗauke da luxury warmers zuwa lokaci Daddy ya farfaɗo sai dai babu ƙarfi ko misƙala-zarrati a jikinsa yini guda har ya yi rama. Ya jiki suka yi masa kafin kowacce su ta nemawa kanta wurin zama ganinsu yasa AB ya fice zuwa masallaci saboda azhar da la'asar dukka a ɗaki ya yi su nan da can bai matsa ba yana tare da Daddy. Ana kammala sallah AB ya dawo shi ya taimaka wa Daddy ya yi alwala kana ya yi sallah anan AB yabar su Mami ya tafi gida ya ɗebo abubuwan buƙatarsa misali ƙarfe 10:15pm Daddy ya umarci Mami da tashi su tafi gida ba don ransu yaso ba suka baro asibitin especially Aydah. Bayan tafiyarsu Mami Daddy ya kalli AB dake Istigifari da counter ɗin dake maƙale da yatsansa gyaran muryar da Daddy ya yi yasa shi ɗagowa ya yada ganinsa kan fuskar Daddy "Ka yi haƙuri Abba zancen aurenka da Mufeeda babu shi Alh Habeeb ya ce ba zai ba ka 'yarsa ba, duk da nayi iya ƙoƙarina na gani na ɓoye asalin kai waye amma abin yaci tura bansan daga ina ne ake fitar da wannan ɓoyayye sirri ba. Dogon numfashi AB ya ja kana ya fesar kafin cikin raunatatciya murya ya ce "Daddy ka daina matsanta wa kanka akaina gashi nan silar wannan mutumin har jininka ya yi muguwar hawa, sai ɓoyewa su Mami asalin ciwon naka nayi domin banaso su ma su shiga damuwa kaman yadda ka ke ciki. Daddy wallahi zan iya riƙe kaina in-sha-Allahu ba ka taɓa kama ni da wani mummunan kaba'ira ba. Saboda haka dan Allah ka haƙura da zance aure nan. Guntun murmushi Daddy ya yi wanda bai wuce iya fatar bakinsa ba shi kaɗai zai iya faɗar halin da yake ciki babban burinsa a duniya yaga Abba ya yi aure sai gashi ya kasa samun cikar burinsa. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/10/2023, 10:04 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful love story) NA ASMY B ALIYU & JEEDDAH ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye novels 016. *RUBUTUN ƳAN *TAGWAYE BIYAR KARO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* *KIN TABBATA KIN CIKA MACE? BABBAR MACE DAKE JI DA KANTA? KINA CIKIN MATAN DA SUKA SAN KANSU? WANDA SUKA SAN MUTUNCI DA DARAJAR KANSU? KO KUWA KEMA KINA CIKI SAHUN SU O’O?* *INA KUKE MANYAN MATA? WAƊANDA SUKA SHIRYA DAN GYARA JIKINSU? AURANSU? DA KUMA FARINCIKINSU?” *KUYI MAZA KU GARZAYA GUN FITACIYGA KUMA INGANTACIYAR MAI MAGANIN MATA DA MAZA DAN AMSAR NAKU KU GYARA DA KANKU WATO MEERAH HERBS WACCE TAI FICE GUN KAWO MUKU INGANTATTUN MAGUNGUNA BA TARE DA ALGUS BA.* Mun gwada mun gani 💯 Mun gani mun shaida 💯 Anyi mun gani 💯 MAGANIN SANYI MAGANIN NONO MAGANIN HIPS MAGANIN SLIMMING MAGANIN NANKARWA GYARAN AMARE GYARAN MAIJEGO MALLAKAR MIJI KO MATA SUBULU DA SCRUB MAYUKA NA GYARAN JIKI TURAREN WUTA MATSI MAGANIN NI'IMA MAGANIN TSUMI INFECTION FLUSHER DA DAI SAURANSU…..Uwar gida, Amarya, Budurwa, Saurayi, Ango, Mai gida? Duk mai kuke jira? Kuyi maza ku garzaya Meerah herbs maganin dake ingantace 💯 08142800199 07068558096 Musamman idan ya tuna da abinda Sadiya ta yiwa Abba sai ya ji zuciyarsa ta ƙara tsinke wa. A natse Daddy yake kallon kyakkyawar fuskar Abba wani irin ƙaunarsa ke bin jini da ɓargon jikinsa "Abba matuƙar ina numfashi a duniya sai naga aurenka domin shine burina kaɗai a duniya. "Amma Dad.... "Karka ce komai Abba domin na gama yanke wa kaina shawara acikin 'ya'ya da na haifa uku mata don ɗaya ta kasa yi min biyayya ta zauna da kai hakan baya nufi raguwar biyun za su bijere min, saboda haka a karo na biyu zan sake aura maka ɗaya daga cikin ƙannanka. A firgice Abba ya ɗago manyan idanuwansa yana kallon Daddy babu komai cikin idanuwan nasa face tsoro gami da fargabar a wannan karo bai kuma san da wa Daddy zai haɗa shi ba. Sai dai hasashen sa yafi karkata akan Siyama duk da tana da baiko wani akanta, ko kaɗan bai kawo Aydah a lissafin sa ba. Dukka maganganu da Daddy ya cigaba da yi ba wanda AB ya sake fahimta a dalili zuciyarsa ta bar gangar jikinsa. Satin Daddy ɗaya a hospital aka sallame shi zuwa lokaci jikinsa ya yi kyau sosai, yayin da shi kuma AB ya shiga ruɗani da zance zuci haɗe da neman mafita. *MOONLIGHT AUTOMOBILE INDUSTRY KANO* AB yana zaune a office ɗinsa damuwa tayi mishi katutu tun sanda Daddy ya yi masa zance sake haɗa shi aure da ɗaya daga cikin ƙannan shi ya rasa sukuni da walwala, kullum yana ciki tunani, Abdulkarim Safana ya turo ƙofar office ɗin na AB ya shigo har ya iso gaban desk ɗinsa bai ma sani ba a dalili ya yi nisa a tunani, Abdulkarim ya yi tsaye yana ƙarewa kyakkyawar fuskarsa kallo ko bai tambaya ba yasan abokinsa yana cikin tsanani damuwa domin har wata rama ya yi, Abdulkarim ya sauke naunnayar ajiyar zuciya ya ja kujera ya zauna ƙarar ja kujera da ya yi ya dawo da natsuwar AB ya sauke ganinsa akan fuskar Abdulkarim sai da ya furzar da zazzafar iska daga bakinsa, kana ya goge fuskarsa da tafukan hannayensa cikin kasalalliyar murya ya furta "Ak ya ake ciki ne??" Ya ƙarashe magana tare da miƙawa Abdulkarim hannu suka yi musabaha. "Me ke damunka ne AB? "Abubuwa da yawa don bana ce guda ɗaya ba. "AB duk abunda yake damunka addu'a ya dace ka yi ba wai ka tsananta wa kanka tunani ba kowacce matsala tana da hanyoyin magance wa. "Ak bana tunani nawa matsaloli suna da hanyar magancewa. "Kar ka ce haka AB domin bawa baya fita rai da rahamar Ubangiji. "Haka ne kuma. AB ya faɗa a gajarce kana ya tashi daga kan kujerar sa ya taka zuwa ga window ɗin office ɗin nasa ya zuge gilashi yana kallon farfajiyar kamfani nasu, shima Abdulkarim ya miƙe ya iso kusa da shi ya tsaya "AB ka faɗamin damuwarka watakila ina da shawarar da zan taimaka ma da ita. Ba tare da AB ya kalle shi ba yake faɗin "Ak Daddy ya sake bijiro min da zance aure. "AB aure shine cikar kamala da mutuncinka aure zai ƙara ɗaga darajar ka a idon al'umma haka zalika za ka habbaka sunnar ma'aiki Sallallahu alaihi Wasallam! A ganina wannan ba abin damuwa bane. Girgiza kai AB ya yi tare da maida gilashi window ɗin ya juya a natse ya nufi ɗaya daga cikin cushion ɗin da ke office ɗin nasa ya zauna ya daga idanuwansa ya kalli Abdulkarim tare da faɗin "Ak zance Mufeeda babu shi saboda labarin rashin asalina ya riske mahaifinta. "Inna wa'inna illahim raji'um! Ni kam wane munafiki ne yake yaɗa wannan al'amari?" "Wannan ita ce tambayar da ni kaina banida gamsasshiyar amsarta. Wannan ba shine asalin damuwata ba Ak domin nima na yanke wa kaina shawara koda ina da rabon yi aure ko anan gaba ne duk wacce zan aura zan sanar da ita asali wane ne ni. AB ya faɗa cikin wata kalar murya mai cike da rauni. Sai da Abdulkarim ya ja gwaron numfashi ya sauke kafin ya dako cikin mutuwar jiki ya zauna akan hannu kujerar da AB yake zaune akai, kana ya ɗan rungumo kafaɗarsa yana ɗan bubbuga gefen kafaɗar tasa alama dake nuni da rarrashi. "Ka yi haƙuri AB kowanne ɗan adam da kake gani yana rayuwarsa tana tafiya ne a bisa zanen ƙaddararsa, duk yadda mu kai da nuna maka ƙauna ba mu isa mu sauya ma ƙaddara ba. Don Allah ka saki ranka ka dawo da walwalarka ka karɓi, wannan ƙaddara da hannu bibbiyu. Kasani AB cikar imani mumini shine yarda da ƙaddara mai kyau ko kuma akasinta, kasancewarka adopted child ba yana nufi kai ɗin ba ka da cikekken asali ba. Kawai dai mutane suna jahiltar adoption ne amma a ƙasashen turawa yadda ɗa da ya tashi a gaban iyayensa yake da 'yanci haka zalika shima adopted child yake da 'yanci kuma ba za ka ga ana goranta masa ba. Sannan idan ka yi duba da yadda naka iyaye suke sonka AB ƙannanka suke matuƙar ƙaunarka ban ga dalili da zai sa ka jefa kanka a damuwa ba. Tun sanda Abdulkarim ya fara magana AB ya ɗago da idanuwansa yana kallonsa har ya dasa aya bai dauke ganinsa daga kan fuskarsa ba tamkar yana karantar wani abu akan fuskar tasa ne. Dukkansu suka yi shiru na wani ɗan lokaci kafin AB ya kawo karshen shiru nasu ta hanyar faɗin "Dole na shiga damuwa Ak Daddy yana so ya sake haɗa ni aure da ɗaya daga cikin yara nan, ni kuma har ga ba zan iya rayuwar aure da ko ɗayar su, kana gani dai yadda ta kare tsakanina da Sadiya ita da ma ta gama mallakar hankalin kanta. Siyama kuma tana da wanda take so ita Aydah a ma jinginar da zancenta a gefe ba ma za a saka ta a jeri mata ba. Cike da gundarin mamaki Abdulkarim yake kallon AB kasa cigaba da ɓoye mamaki nasa ya yi har sai da ya kai da furta "Kana matuƙar bani mamaki AB. "Na me fa?? "A duk sanda ka furta iri-irin waɗannan maganganu akan Aydah. "Ya kamata kai daina mamaki Ak saboda hakikanin gaskiya nake faɗa Aydah bata cikin jerin mata a wurina. "Ni kuma sai nake gani Aydah ita kaɗai ce yarinyar da ta dace da kai kada ka yi la'akari da ƙarancin shekarunta ka yi duba izuwa ga tsanani shaƙuwa da juna da ku ka yi duk idan aka ce akwai shaƙuwa tabbas so zai iya shigowa cik.... "Dallah ya isa Ak! Na sha faɗa maka Aydah tamkar 'yar da na haifa nake kallonta kashi, fitsarinta ba kalan wanda ban ci ba ni na raine ta da hannaye nan nawa babu abinda bansan ni ba a jikinta sai kawai na aureta haba Wannan kwamacala ba dani ba wallahi. "Mtsss! Duk wanda ya ji kana fadar ba abunda ba kasani ba a jikinta zai fassara ka ta wani fanni na daban kasan komai na jikin Aydah sanda tana yarinya ba yanzu da ta balaga ba ko kana nufi har yanzu kai ke mata wanka?" Sai da AB ya ture hannayen Abdulkarim daga kafaɗarsa ya miƙe a mugun fusace ya nufi ƙofar fita Abdulkarim ya miƙe ya biyo shi a baya sosai AB yake ji ɓacin rai yana lulluɓe shi, ya rasa dalilin da yasa a duk sanda Abdulkarim ya danganta aure tsakaninsa da Aydah yake wani irin baƙin ciki ya danne masa zuciya, da ya aure Aydah gwada ya ƙare rayuwarsa kaf babu aure me zai tsinta a jikinta. "Ya ka yi shiru ka bani amsa mana har yanzu kai ke mata wanka kaman yadda ka saba faɗa. "Ba bambanci a wurina domin duk mace da kasan jikinta tun tana jinjira don wasu 'yan ƙananu abubuwa sun fito mata a ƙirji ba zai zama bakon abu a gareni ba, saboda nasan lokaci da bata dasu. "Maganar banza kake yi AB wannan bai isa ya zama kwakwarar hujja da za ka haramta kanka aurenta ba. "Dan Allah Ak mu bar wannan zance wallahi yana ƙara linka min sa ɓacin rai. "Shikenan! Abdulkarim ya faɗa daga nan motar Abdulkarim suka shiga kowanne su yunwa yake ji don haka suka wuce Gusto restaurants. *MASARAUTAR KUDU* "Umma ki yi wani abu akai kaman yadda kike yi a shekarun baya na hana naɗa Aliyu a matsayin sarkin sabon birnin kudu. Umma sarautar nan ko kaɗan bata dace da Aliyu ba da ni ta dace. Alhaji Hashim ya yi magana yana kallon Hajiya Kilishi dake kishigiɗe akan wata lallausar carpet cike da izza da taƙama take jujjuya yatsun hannunta da suka sha ado da zobunan gold, ta ɗauki dogon lokaci tana jujjuya yatsun nata kafin ta buɗe bakinta cikin wata irin izza ta furta "Ciroma! "Na'am Allah ya ƙara wadata ki da lafiya gami da nisan kwana. "Amin! Ina son ka sani Ciroma na fika shiga tashin hankali sa'ilin da labarin naɗin sarautar Aliyu ya riske ni. Bani da wani buri a duniya sama da naga na kawo ƙarshen mai babban ɗaki da 'ya'yanta wannan makirar mata da kake gani Hashim na share tsawon shekaru masu yawan gaske ina shanye baƙin cikinta. Tun lokaci da takawa yake raye nake nuƙurƙusar baƙin ciki har kawo yau ɗinan ba abinda ya sauya. Hajiya Kilishi ta kasa cigaba da magana wani irin fushi da ɓacin rai ne sosai suka bayyana karara akan fuskarta da babu burbushi imani balle tausayi, sai da ta furzar da iska daga bakinta ta tashi daga kishigiɗa da ta yi ta kalli Hashim kallo idon cikin ido ta yadda zai iya hango tsanani fushi da take ciki "Ban taɓa sanya ko nuna gajiyawa domin cimma daɗen burina Hashim kai sauratar sabon birnin ita ce damuwarka ni kuma ga baki ɗaya sarautar kudu nake so ta dawo karkashin iko da mallaka ta. Wani irin washe haƙora Hashim ya yi ya ƙara gyara zaman shi tare da ƙara ƙasƙantar da kai, "Allah ya ƙara miki lafiya acikin mu wa kike wa sha'awar wannan babban matsayi?" "Ahmadu! Nan take annurin kan fuskar Hashim ya gushe wani irin mashi ya ji ya dakar mishi zuciya, duk da haka sai ya yi ƙoƙarin danne abunda yake ji yana taso masa a ƙahon zuciya "Ranki shi dade Ahmadu fa kika ce?" "Kwarai kuwa Ahmadu. Ta faɗa kanta tsaye domin ƙara tabbatar mishi da nufin ta. "Ranki ya dade Ahmadu fa kwata-kwata baya da sha'awar mulki shiyasa tasu ta zo ɗaya da Aliyu, kuma bana tunani Ahmadu yana da experience akan yadda ake gudanar da mulki ki tsaya ki yi nazari ranki ya dade kada ki yi gaggawar yanke hukunci amma Ahmadu ba zai iya sarauta ba. Ina ma laifin ki zaɓi Yusuf ko Abubakar ko kuma ni ɗinan domin duk acikinsu ni kaɗai nake da experience akan gidan sarauta, kuma ni ne babba. "Ciroma ina so kasani bana yanke hukunci ba tare da lissafi na ya faɗa daidai ba, duk abunda zan yi a bisa jagoranci natsu da hankali nake yi sa. Ahmadu shi ne lissafi na ya faɗa akansa, ka janye ƙudurinka akan masauratar kudu domin sarautar sabon birnin kudu ita ce ta fi dacewa da kai anan gaba za ka fahimci manufa ta. "Amma ranki ya daɗe.... "Ya isa Ciroma! Tai sauri tarar numfashin sa da kakkausar murya. "Ka fara shiri gobe da safe za mu kai ziyara a akan tudu. "Tohm! Ranki ya daɗe. Ya faɗa zuciyarsa na mishi zafi "Na barki lafiya. Ya miƙe tare da baro katafaren parlorn nata. *FLAT ƊIN MAI BABBAN ƊAKI* Mai babban ɗaki tana hakince a parlornta tare da bayi haɗu biyu suna mata massage ɗin yatsun ƙafafunta yayin da biyu ke yanka mata 'ya'yan itatuwa (fruits) amintatciyar jakadiyar ta ce ta shigo ta zube a gabanta ta sadda kanta ƙasa cikin tsanani girmamawa ta furta "Allah ya ƙara miki lafiya yanzu nan magatakarda ya dawo da sakon da kika ce na aika wa da sarkin sabon birnin. magatakarda ya tabbatar min jiya sarkin sabon birnin ya koma Lagos. Shiru mai babban ɗaki tayi tana nazarin kalaman jakadiya bi da bi wani irin ɓaci rai ne ya bayyana akan fuskar mai babban ɗaki miyasa a duk sanda tai gini Aliyu yake rusa shi? Miyasa duk acikin 'ya'yanta shi ne yafi bata matsala, bata da buri da ya wuce taga ya hau karagar mulkin sabon birnin kudu a duk sanda ta kusa cimma burin ta sai Aliyu ya wargaza mata shi. Tabbas da akwai wani ɓoyayye al'amari a tattare dashi dole ta matsanta bincike domin gano abunda Aliyu ya dau shekaru yana ɓoye mata ta gaji da wannan kurman allon nasa. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/10/2023, 10:15 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love Story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 017. *RUBUTUN ƳAN TAGWAYE BIYAR KARO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* *KIN TABBATA KIN CIKA MACE? BABBAR MACE DAKE JI DA KANTA? KINA CIKIN MATAN DA SUKA SAN KANSU? WANDA SUKA SAN MUTUNCI DA DARAJAR KANSU? KO KUWA KEMA KINA CIKI SAHUN SU O’O?* *INA KUKE MANYAN MATA? WAƊANDA SUKA SHIRYA DAN GYARA JIKINSU? AURANSU? DA KUMA FARINCIKINSU?” *KUYI MAZA KU GARZAYA GUN FITACIYGA KUMA INGANTACIYAR MAI MAGANIN MATA DA MAZA DAN AMSAR NAKU KU GYARA DA KANKU WATO MEERAH HERBS WACCE TAI FICE GUN KAWO MUKU INGANTATTUN MAGUNGUNA BA TARE DA ALGUS BA.* Mun gwada mun gani 💯 Mun gani mun shaida 💯 Anyi mun gani 💯 MAGANIN SANYI MAGANIN NONO MAGANIN HIPS MAGANIN SLIMMING MAGANIN NANKARWA GYARAN AMARE GYARAN MAIJEGO MALLAKAR MIJI KO MATA SUBULU DA SCRUB MAYUKA NA GYARAN JIKI TURAREN WUTA MATSI MAGANIN NI'IMA MAGANIN TSUMI INFECTION FLUSHER DA DAI SAURANSU…..Uwar gida, Amarya, Budurwa, Saurayi, Ango, Mai gida? Duk mai kuke jira? Kuyi maza ku garzaya Meerah herbs maganin dake ingantace 💯 08142800199 07068558096 Tun ranar da Alh Habeeb Bichi ya baro gidan Alh Bashir ya kira Mufeeda ya sanar da ita zance aure tsakaninta da AB babu shi. Tun daga wannan ranar har kawo yau Mufeeda tana cikin ƙunci saboda ta kamu da soyayyar AB atunani ta za ta iya fatattakar soyayyar tasa a farat ɗaya kaman yadda ta shiga zuciyarta a tashin farko, sai dai haƙar ta ya kasa cimma ruwa kullum soyayyarsa ya ƙara habbaka take a zuciyata. Sannu-sannu damuwa ta fara yi mata yawa farin ciki gami da walwalarta suka bar jikinta. Bata da aiki sai na tunanin AB. Yanzu ma tana kwance ne a ɗakinta hoton AB take kallo wanda a shafin sa na Instagram ta same shi zooming ɗin hoton tayi ta yadda fuskarsa ta fito ɓaro-baro gray eyes ball ɗinsa yana ɗaya daga cikin abinda take bala'in so a tare dashi sai kuma pink lips ɗinsa ga kuma kwatatce sajensa mai haɗe da ɗan matashin beard ɗinsa da ya ƙara ƙawata fuskarsa. Wasu hawaye ne suka silalo daga kwarmin idanunta suka gangaro suka saukar mata a gefen wuyanta. Lokaci da Abbanta ya zaunar da ita yake faɗa mata zance aure ta da AB ya rushe dan kawai ya kasance adopted child ba shi da asali ba a san su waye biological parents ɗinsa ba, har ga Allah ita bata ɗauki wannan a matsayin ƙarfaffiyar hujjar da zai sa ya hanata aurensa ba. Domin Abba Bashir yana da nagarta da ko'ina za a iya bashi mata ya aura rashin asalinsa bai dame ta ba. Da farko ta yi tunani ba za ta shiga damuwa ba, a dalilin mahaifinta shi ne ya zaɓar mata AB ta kuma yi masa biyayya tare da karɓa zaɓin nasa da hannu bibbiyu yanzu kuma shine ya dawo da kansa ya ce ya fasa ta zaci cewa tun anan wuri za ta manta da Abba Bashir sai gashi ɗan taliki nan ya hana mata ci abinci ya kuma hana mata bacci, ga baki ɗaya ya yi awon gaba da farin cikinta. Batasan cewa soyayyar AB ta mata mummunan kamu ba har haka ba. Ƙanwarta wacce ke bi mata Jalila ta turo ƙofar ɗakinta ta shigo dawowar Jalila kenan daga school tana karatu a BUK ta shigo ɗakin na Mufeeda ne da zimmar ta saka wayarta charging a dalilin charger ɗinta ya lalace, tana gani halin da yayarta ta, take ciki tayi tsaye turus! Ta daɗe tana kallonta kafin ta tako a hankali kamar mai sanɗa ta zauna daf da Mufeeda sai da ta fara leƙa screen ɗin wayar Mufeeda ta ga picture ɗin da take kallo, kana maida ganinta akan hawaye da Mufeeda batasan suna zuba daga idanuwanta ta sauke numfashi ta kai hannunta ta fincike wayar da Mufeeda ta yiwa wani kalar riƙo tamkar rayuwarta ce aciki. "Yaya Mufeeda kar dai ki ce min kin kamu da soyayyar guy din nan??" Sai da Mufeeda ta tashi zaune ta jefa pillow a bayanta ta jingina gadon bayanta, ta ja wata 'yar siririyar majina ta koma cikin ƙoƙon kanta cikin rauni murya ta furta "Ga alama kin gani azahiri miye na tambaya. "Cab! Amma kuwa kina da aiki yaya Mufeeda domin sanin kanki ne Abba yanka ɗaya ne da matuƙar wahala ya sauya kalamansa. Don haka tun wuri ki gaggauta yaƙi da yaudararriyar zuciyarki, ki yaƙe ta, ta raba ki da son abinda ba za ki taɓa samu ba. Ba abinda maganganu Jalila suka ƙara wa Mufeeda face fushi da ɓacin rai don haka sai da ta baro fizge wayarta daga hannun Jalila ɗin kafin cikin ɓacin rai ta ce "Lokaci da na fara son AB bai yi shawara da kowa ba daga ciki kuwa har Abban da kike tsorata ni akansa, kuma ina so kisani Jalila ita soyayya da kike gani wata aba ce wacce bata neman shawara ko yarjewa, haka zalika bata neman izni kutsa wa a cikin zuciyar ɗan adam. Jalila soyayya halitta ce da Allah subhanahu wata'ala ya halicce ta sannan ya dasa ta a duk wata halitta zuciya mai rai. Soyayya wani sashe ne mai matuƙar wahalar da ruhi gami da gangar jiki kalmar so yana da sauƙi faɗa fiye da kowacce kalma sai dai ma'anar sa ta fi kowacce kalma raunata ruhi da gangar jiki. Ba lallai bane ki fahimci kurman allo da nake miki ba saboda ba ki taɓa riskar kanki a koramar so ba. Kyakkyawar numfashi Jalila ta ja tare da saukewa cike da sanyi jikinta ta dafa kafaɗar Mufeeda "ki yi haƙuri idan furunci nayi ya ɓata miki rai bana nufi na ƙara miki damuwa kawai dai ina ƙoƙari tunatar dake kaman abunda kika manta akan Abban mu zan fi kowa farin ciki idan kika sami cikar muradinki. "Addu'a ya kamata ki tayani da ita idan har akwai alkhairi a tarayya ta da AB Allah ya karkato da hankalin Abban mu idan kuma akasin hakan ne Allah ya musanya min da mafi alkhairi. "Shi kenan yaya Mufeeda Allah ya zaɓi miki mafi alkhairi. "Amin! Mufeeda ta faɗa tana mai sauka daga gado ta shiga bathroom Jalila kuma ta saka wayarta a charging ta fice zuwa babban parlorn gidan. *ALH BASHIR MANSION* AB yana dawowa daga office ya wuce bangaren sa ya yi wanka koda ya fito daga wanka ana kiran sallar magarib agurguje ya shirya cikin silk jallabiya brown in color ya fesa turare kaɗan, ya wuce masallaci bayan an gama sallar isha ya shigo gida kaitsaye ɓangaren Mami ya nufa a babban parlor ya tarar da Sadiya da Siyama kowacce tana sabgar gabanta, Sadiya tana rubutun project ɗinta a laptop yayin da Siyama take chat da Saleem fiancé ɗinta sai uban murmushi take zabgawa alamar hirar da suke yi tayi mata mugun daɗi. Ƙamshin perfume ɗinsa ya ankarar dasu wanzuwar sa a cikin parlor, kusan a tare suka ɗago "Ya Abba ina wuni? Sadiya ta faɗa cikin rawar murya banza ya yi mata "Ya Abba barka da dare? Siyama ta gaida shi ba tare da la'akari da ƙin amsawa Sadiya da ya yi ba. "Siyam ya karatu? "Al-hamdullilah Ya Abba! "Ina Baby Aydah? Da sauri Siyama taso ta matso daf da yaya Abba ta yi ƙasa da muryar kamar munafuka "Yaya Abba wallahi ina zargi Aydah da akwai abunda take aikata wa a ɓoye duk bin kwakwafi na, na kasa gano mene ne. Da zarar ta dawo daga islamiyya za ta ƙunshe kanta a ɗaki hatta da abinci ta rage ci haka zalika ta daina fitowa a babban parlor. "Uhm! Tun yaushe ta fara wannan halaya? AB ya yi magana cikin ƙaramin sauti. "Za kai three weeks. "Three weeks! Meyasa tun lokaci ba ki faɗamin ba? "Ya Abba na zaci za ta daina ne yanzu ma naga abun nata ya ta'azzara sosai. "Je ki kira min ita. Da sauri Siyama ta nufi mattakalar bene zuciyarta cike da murna yau za su sha kallo, tana murɗa handle ɗin ƙofar ɗakin Aydah ta ji shi a ƙargame da sauri ta sakko daga bene sai da tazo kusa da Ya Abba sannan ta yi magana "Ya Abba ɗakinta a rufe yake. "Je ki yi mata knocking ki faɗa mata ni nake so ganinta. Har Siyama ta juya sai kuma ya dakatar da ita "Siyama! Yi zaman ki kawai bara na je da kaina idan ma tana ɓoye wani abu ne zan gani da idanuna. Hakan da ya faɗa ba ƙaramin daɗi Siyama ta ji ba tana da yaƙini dole ya kamata da laifi musamman ɗazu taga sanda Aydah ɗin ta fito da wayar Mami tana ɓoyewa batasan cewa ta ganta ba, tasan Ya Abba baya so tana riƙe waya a cewarsa har yanzu bata yi girman da za ta riƙe waya ba. Don haka yanzu idan ya kamata da wayar Mami mai hana shi yai mata duka sai Allah. Duk abunda ke wakana tsakani AB da Siyama Sadiya ta tattara hankali da natsuwarta kacokan akan su yanzu ma da ya juya ya haura bene, ta bishi da kallo a hankali yake knocking ƙofar ɗakin Aydah, tun yanayi a sannu har ya dawo yi da ɗan ƙarfi Aydah wacce tayi nisa a karatun littafin secret relationship na Asmy b Aliyu sosai take enjoying littafin ba ƙaramin tausayin Jiddah ya kamata na gani yadda ta kamu da zazzafar soyayya Junaid Dikko alhali shi kuma baya ji sonta a zuciyarsa. "Aydahhh! Me kike yi a ɗaki zo buɗe ƙofar nan tun kafin ranki ya ɓaci. Kaman daga saman ta ji muryar ya Abba a kausashe. Wani kalan wutsillowa ta yi daga gado ta faɗo ƙasa "Na shiga uku! Kaman muryar Ya Abba nake ji. Aydah ta faɗa cikin zare idanuwa kafin ta gama tu'ajjabi ta sake ji ya kira sunanta a fusace "Aydah kina ji na fa. "Na'am! Ya Abba gani nan zuwa. Ta faɗa cikin harɗewa harshe ta tashi da sauri ta ɗaga pillow dake kwance akai ta ɓoye wayar ɗayan wayar Mami da ta dauko, sai dai ta daidaita natsuwarta kafin ta nufi ƙofar ta buɗe idanuwanta suka sarƙe da na Ya Abba wanda yai bala'in haɗe fuska "Ya Ab...ba! Yadda ta furta sunansa da kuma yadda idanuwanta suka firfito wannan kaɗai ya isa ya tabbatar mishi da bata da gaskiya, tun tana yarinya idan tai laifi ta ƙwayar idanuwanta yake ganewa "Me kike yi ke kaɗai ƙunshe a ɗaki ba sannan kuma ba kallo kike yi ba saboda ban ji ƙarar sauti tv ba?" "Uhm! Uhm! Ya Abba headache ke damu na. Ta gama kame-kamenta ta da kyar ta lallaɓo wannan karya ta faɗa kallon da yake bin ta dashi duk sai ta ji ta tsargu ta shiga cukuɗaɗɗiyar kalabar kanta wacce tsabar tsofa har ta fara tsife kanta da yake gashinta yana da tsatsin mayar da ganinsa ya yi kan gashin nata, take ya ɓata fuska cike da ba da umarni ya ce "Ban yarda dake ba Aydah ki faɗa min gaskiyar abinda kike yi idan kuma kika sake na bincika da kaina na gano ki to ki kuka da kanki. Idanuwanta suka cicciko da hawaye ta wani langwaɓar da kai ita dole sai ta bashi tausayi cikin muryar so ya kuka take faɗin."Ya Abba game ne nake yi da wayar Mami. Wani kalan ajiyar zuciya ya yi kafin ya ture ta ya wuce cikin ɗakin nata ya ɗinga dube-dube can idanunsa suka kai ga pillow da tashi ya ɗauke shi ya ciro wayar Mami, ya ɗan jujjuya ta sai kuma ya mayar da ganinsa akan fuskarta "Wato saboda game shiyasa kika zaɓi ki dinga rufe kanki a ɗaki ko? Wai ke ga ki mayyar games. "Ya Abba I'm sorry! Tayi magana tare da kama fatun kunnenta biyu. "Wannan shine kashedi na ƙarshe da zan miki akan ki daina daukar wa Mami waya saboda ba sana'arki bace kin ji ko?" "Tohm! Ta faɗa cikin ƙaramin sauti "Dama kina ji magana da watakila na runtse idanu na siya miki tab ki ta buga game tun da kin dawo mayyar sa. Sauri ta ƙaraso gabansa ta shiga zuba mishi taɓara tana wani bubbuga ƙafafuwanta akan marbles hakan ya haifar wa da ilahirin jikinta motsawa 'yan matasan boobs ɗinta sai rawa suke yi ta jikin 'yar fingilalliyar half gown ɗin jikinta wacce ko santala-santala cinyoyinta bata rufe da sauri AB ya kauda fuskarsa yayin da Aydah sai zuba shagwaɓar take yi har tana ƙoƙari kama mishi hannu ya yi sauri ja da baya cikin kakkausar murya ya ce "Baby Aydah banaso rigima idan kina min wannan taɓarar sai ki sa na fasa. "Na daina Ya Abba Allah na daina. "To shi kenan ki canza kayan jikinki ki sakko ƙasa mu yi dinner. Yana ƙarashe magana ya nufi ƙofar fita ba tare da ya sake kallonta ba. #Love story 2023/2024 #Jeedah Aliyu #Asmy b Aliyu #team tagwaye novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/11/2023, 10:04 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 018.. *RUBUTUN ƳAN TAGWAYE BIYAR KARO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* *KIN TABBATA KIN CIKA MACE? BABBAR MACE DAKE JI DA KANTA? KINA CIKIN MATAN DA SUKA SAN KANSU? WANDA SUKA SAN MUTUNCI DA DARAJAR KANSU? KO KUWA KEMA KINA CIKI SAHUN SU O’O?* *INA KUKE MANYAN MATA? WAƊANDA SUKA SHIRYA DAN GYARA JIKINSU? AURANSU? DA KUMA FARINCIKINSU?”* *KUYI MAZA KU GARZAYA GUN FITACIYGA KUMA INGANTACIYAR MAI MAGANIN MATA DA MAZA DAN AMSAR NAKU KU GYARA DA KANKU WATO MEERAH HERBS WACCE TAI FICE GUN KAWO MUKU INGANTATTUN MAGUNGUNA BA TARE DA ALGUS BA.* Mun gwada mun gani 💯 Mun gani mun shaida 💯 Anyi mun gani 💯 MAGANIN SANYI MAGANIN NONO MAGANIN HIPS MAGANIN SLIMMING MAGANIN NANKARWA GYARAN AMARE GYARAN MAIJEGO MALLAKAR MIJI KO MATA SUBULU DA SCRUB MAYUKA NA GYARAN JIKI TURAREN WUTA MATSI MAGANIN NI'IMA MAGANIN TSUMI INFECTION FLUSHER DA DAI SAURANSU…..Uwar gida, Amarya, Budurwa, Saurayi, Ango, Mai gida? Duk mai kuke jira? Kuyi maza ku garzaya Meerah herbs maganin dake ingantace 💯 08142800199 07068558096 Agurguje ta canza rigar jikinta zuwa bubu na material hularta a hannu ta fito da ɗan gudunta ta sakko ƙasa yadda ta fito tana fara'a yasa Siyama ta ɓata rai wato ƙararta da ta yi wurin Ya Abba ta tsalleke shi. Yau su uku suka ci abinci Sadiya, AB da Aydah, Siyama taci abinci da yamma lis da ta dawo daga school Mami kuma azumi ta yi a parlonta dake sama ta yi buɗa baki tuni Sadiya ta ƙoshi amma ta kasa tashi ba ƙaramin daɗi take ji idan tana kallon kyakkyawar fuskarsa ba. AB ya ture plate ɗin gabansa ya kalli Aydah wacce ke tsotsar ƙashin miya "Aydah! "Na'am! "Ki shirya gobe da yamma na kai ki saloon a wanke miki kai ayi miki kitso Allah na gaji da ganinki da wannan ƙazantar dake kanki. Ya ƙarashe maganae yana ya mutsa fuska irin da gaske kyakyamin ta yake ji. Kafin Aydah ta yi magana Sadiya ta rigata ta hanyar cewa "Gaskiya Ya Abba ka rage sangarta Aydah she's mature enough and she can take care of herself haba hatta da kitso ace kaine za ka kaita sai kace wata yarinyar goye. "Mtss! Ya ja dogon tsaki tare da miƙewa ya ture kujera ya nufi ƙofar fita Aydah ta kalli Sadiya taga yadda ta bi shi da kallo har idanuwanta sun kawo ƙwalla ta fashe da dariya, hakan ya fusata Sadiya ta tashi rai ɓace ta tsike Aydah da wawan mari har sai da Aydah ta faɗo ƙasa ta takarkare ta tsandara mahaukacin ihu wanda yasa Siyama ta jefar da wayarta ta kwaso da gudu ta shigo dining area ɗin ta sauke idanunta akan fuskar Sadiya wacce ke cika tana batsewa Siyama ta sunkuya ta ɗago da Aydah wacce ta saki baki sai kuka take yi tana kiran wayyo Allah idonta yaya Sadiya ta fasa mata ido. "Wannan ya zama miki na farko kuma na ƙarshe da za ki sake yi min dariya 'yar iska yarinya kawai wacce ta gama raina mutane. AB har ya gama ficewa daga entrance ɗin part ɗin Mami ya ji ihun Aydah a rikice ya dawo daidai furunci Sadiya yana faɗawa kunnensa dukkan su basu lura da shigowarsa dining area ɗin ba yana zuwa ba tare da ka-ce-na-ce ba ya ɗauke Sadiya da lafiyayyen mari tana ɗagowa buɗe da baki ya sake dallawa ɗayan kumatunta cikin tsanani fushi da ɓacin rai ya nuna ta da yatsa cikin kakkausar murya ya ce "Daga yau daga yanzun nan da nake tsaye a gabanki idan kika kara taɓa lafiyar Aydah acikin gidan nan wallahi tallahi sai na baki mugun mamaki,with shock Sadiya ke kallon Abba,tana ganin yadda jikinsa ke wani irin rawa saboda tsananin ɓacin rai. marin da ya mata bai ɓata mata rai ba kamar yadda ransa ya ɓaci akan marin Aydah da ta yi zuciyarta ta fara kokonto akan yayan nasu akan kulawar da yake baiwa Aydah fiye dasu. "Hayaniyar me nakeji anan?" Mami ta faɗa tana tsaye akan stairs dan hayaniyarsu yasata fitowa Siyama da Aydah suka yi tsuru-tsuru saboda ɓacin rai AB ko kallon wurin Mami, bai yi ba ya juya a mugun fusace ya fice daga Parlon ita ma Sadiya ta juya ta nufi nata ɗakin cike da shakku da wani irin tsoro dake cika zuciyarta. Sai lokacin Siyama ta korawa Mami abunda ya faru. Mami tabi Aydah kawai da mugun kallo ta juya ta koma sama. Da dare sai dai AB ya kira siyama a waya ta kai masa coffee a part ɗinsa har lokacin bai gama fushin da ya dauka da Sadiya ba dama kuma tara mata yake yi. Har zuwa washegari bai huce daga fushin da ya yi ba, shiyasa ko breakfast bai fito ba. Sai da Daddy ya tambaya me aka yi masa da bai fito ba? Mami tace "kannensa ne suka ɓata masa rai kai ma kasan ba zai zo ba Siyama ta zuba masa ta kai masa. Daddy ya juya kan Aydah da take zaune a wurin tana juya spoon ɗin a hannunta ɗan murmushi Daddy ya yi yana faɗin."mamana meyasa kike tsokanar yayunki bancin kin san yayanki baya da haƙuri a wannan ɓangaren?" Hawaye suka fara sauka a fuskar Aydah cikin shesshekar kukan ta ."Daddy ban mata komai ba kawai ta mareni.! Mami ta wani daka mata tsawa tana faɗin."tashi ki bar gabana kar na kwada maki mari, da sauri Aydah ta mike tsaye tana ture plate ɗin gabanta cikin banbamin faɗa Mami ke faɗin."Ba dole ta yiwa mutane rashin kunya ba duk yabi ya sangarta yarinya ya lalata ta bata respecting ɗin kowa. Na sha faɗawa Abba ba so ɗaya ba biyu ba wannan ba gata bane macce ce gidan wani zata tafi wallahi wahala za tayi. Da zarar ya buɗe baki sai ka ji ya ce ba zai taɓa bari ta wahala ba, haka zalika babu shegen da ya isa ya wulakanta masa kanwa. Ai zamu dai gani mu je zuwa. Mami ta ƙarashe magana a mugun fusace wani murmushi mai sautin gaske Daddy ya yi shi dai bai ce komai ba sai yanzu wani tunani ya shiga kansa meyasa tun farko bai aurawa Abba, Aydah ba? Tun da har akwai irin wannan muguwar shaƙuwar a tsakaninsu yasan ba zai taɓa kin amincewa ba wata irin shaƙuwa ce dake tsakanin Abba da Aydah tun tana ƙarama yake nuna mata matsananciyar ƙauna ya sha canja mata school don kawai ta yi laifi an hukunta ta, ko bata mata rai akayi shi kenan ba za ta ƙara zuwa ba school ɗin ba. Babu irin faɗan da bai yi masa ba akan wannan canje-canjen makarantar da yake mata har yanzu da take secondary school haka suke kullum yana sintiri zuwa makarantarsu Aydah sulhu da malaman makaranta. Kamar yadda ya saba yana gama shirin fita office cikin shigar suit maroon in colour sai da ya tsaya a mota ya aje briefcase ɗinsa ya nufi cikin gida Mami da Sadiya kaɗai ya tarar cikin dining area ɗin. Ita ma Sadiya saboda ta saka yayan nata a ido ta fito cikin dining area ɗin fuskarsa a tamke ya ja kujera ya zauna daf ta Mami yana gaisheta cike da respect ta amsa. Cikin rawar murya Sadiya ta gaishesa ko kallon inda take bai yi ba ballantana tasa ran zai amsa Mami dai bata ce komai ba tana ta sipping ruwan lipton ɗinta da Sadiyar ta haɗa mata, Sadiya ta dawo gabansa tana ƙoƙarin ɗaukar cup ta haɗa masa tea ya yi saurin daukar wani ya shiga haɗawa, tuni idanu Sadiya suka cika da hawaye juyawa kawai tayi tabar cikin dinning area ɗin. Mintuna goma sha biyar kacal ya yi cikin dining area ɗin ya yiwa Mami sallama ta bisa da addu'ar Allah ya tsare hanya. Mami tana tsaye da 'yar aiki tana yi mata list ɗin abubuwan da zata siyo mata a kasuwa tana gama rubuta mata tabar kitchen ɗin tana ƙara jaddada mata da ta yi sauri rana ta yi sosai. Kai tsaye ɗakin Sadiya ta nufa kwance ta sameta kan doguwar sofa ta yi ruf da ciki ganin mami a ɗakinta yasa ta yi saurin goge hawayen da har lokacin basu daina zuba mata ba ta tashi zaune haka sai kawai ta tsince kanta da kasa kallon mami. "meke damunki?"kukan me kika zauna kina yiwa mutane haka?" Wasu hawaye suka kara zubowa akan kumatun Sadiya. Cikin shesshekar kuka ta shiga faɗin."Mami bakya ganin yadda yaya Abba ke avoiding ɗina acikin gidan nan yana kula kowa banda ni duk ya bi ya tsaneni shi bai san tsautsayi bane? Ko Allah ana yiwa laifi ya yafe balle mutum ɗan adam. Ban san Me yake so nayi da zai fahimci nayi kuskure ba na kuma yi nadama biye wa ruɗin zuciyata da nayi, jiya akan Aydah tayi min rashin kunya na mareta sau biyu Mami ya mareni abunda bai taɓa yi ba sakawa wani hannu a cikinmu duk girman laifin da za muyi masa iyakacinsa ya ɗauki fushi damu." Sadiya ta ƙarasa maganar tana rufe fuskarta da tafukkan hannayenta kana ta ci-gaba da rera kukanta a hankali. "Duk bake kika jefa kanki cikin wannan masifar ba saboda taurin kai irin naki da yanzu ba kina zaune can gidanki lafiya lau ba. Kika mannewa wannan gantalalle yaro gashi kin kashe aurenki saboda shi har kuma yanzu ya kasa fitowa ayi maganar aurenku. Shawarata na karshe dake ki daina shiga sabgar Aydah a gidan nan musamman idan kin san yayan naku yana gida. "Mami ko ita keda laifi bamu ba baya gani rufe idonsa yake da anyi magana sai yace yarinya ce 'yar ss 2 ɗin ce?" Yarinya saboda ya daure mata shiyasa ta rainamu wallahi ko gobe ta sake yi min rashin kunya ba raga mata zan yi ba. Mami dai tayi ƙwafa tabar mata room ɗin kawai saboda duk abinda zata ta faɗa ba fahimta za ya yi ba. Da yamma Mami ta ce 'yanmatan nata su shirya a fita shopping dasu kaman yadda ta sabar musu duk ƙarshen wata tana fita dasu shopping su siye abubuwan da suke bukata. Siyama ta kalli Mami a natse ta ce "mami dan Allah dan Annabi yau ki bar Aydah ta dauko bra ta fara sakawa nawa fa take dauka mami ko sun mata yawa sai ta saka." Aydah ta wani zaro ido lokaci ɗaya kuma ta haɗe rai tana faɗin."Yaushe na daukar maki bra na saka yaya Siyam saboda sharri ni yaushe ma bra ɗinki zata tsaya ajikina saboda gir..... kafin ta karasa mami ta kaiwa bakin bugu da sauri Aydah ta riƙe bakinta tana jin tamkar ba bakin nata bane saboda mugun azabar da taji "Bana hanaki yi musu rashin kunya ba?" karyama tai miki kenan? Mami ta faɗa a fusace, da sauri Aydah ta miƙe tsaye still tana riƙe da bakinta hawayen azaba na feso mata bata kara koda minti ɗaya ba a wajen tabar cikin parlorn tana fashewa da kukan tabara Sosai Sadiya da Siyama suka ji daɗin abunda Mami tayi mata. Kowa ya fito cikin shirin sa a parlor har lokacin Aydah bata fito ba Mami ta nufi ɗakinta a kwance ta sameta tana shesshekar kuka har lokaci sai kace wacce aka kwakulewa idanuwa. Jin muryar Mami yasa ta miƙe a razane Mami na bin ta da kallo ta ce "ubanwa kika mayar sa'arki da zai tsaya jiranki?" Cikin sautin kuka Aydah ta ce."Tare da yayanmu zan je. Ganin Mami tayo kanta a mugun fusace yasa ta saukowa daga kan bed ɗin ta ɗauki hijab ta nufi ƙofa Ko kallon su Sadiya ba tayi ba ta nufi hanyar barin parlorn Siyama ce ta karbarwa Mami,tukin daman sun iya Driving kuma suna da motocinsu sai dai anyi wata biyu da yaya Abba,ya yi seizing ɗin keys ɗinsu kafin aurensa da Sadiya suke masa magiya ya mayar musu da key ɗin amma yaƙi. Duka kuma saboda Aydah ta faɗa masa yadda suke mata wulakanci musamman idan suka tashi fita sai wannan yace bazai dauketa ba wannan ma haka. Shima saboda tafiya school aka basu motocin akwai ranar da suka je biki babu wanda ya dawo da Ayda acikinsu bikin na familyn Mami ne wai acewarsu ta yi masu rashin kunya shine suka saka ta shiga adaidaita shi kuma ya ji haushi ya kwace. Har magana Mami tayi masa yace zai basu amma ba yanzu ba sai ya gama hora su ta yadda next time ba za su ƙi ɗaukar Aydah ba, dama kuma shi Daddy babu ruwansa bai shiga sabgarsu duk irin hukuncin da zai yi masu bai cewa uffan. Dama Aydah bata yadda ta zauna baya wajen Mami ba frontseat ta buɗe ta shiga sai dai fuskar nan a ɗaure kuma babu wanda ya kulata acikinsu har suka tsaya cikin parking lot na kantin da suke yin shopping ɗinsu, dama Siyama na gama parking Aydah ta balle marfin motar ta nufi entrance ɗin shiga wajen babu wanda ta jira acikinsu tana zuwa ta ɗauki shopping cart tayi shigewarta cikin mall ɗin. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/11/2023, 10:22 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love Story #gwagwarmaya #Team tagwaye novels 019.. *RUBUTUN YA'N TAGWAYE BIYAR KARO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* *KIN TABBATA KIN CIKA MACE? BABBAR MACE DAKE JI DA KANTA? KINA CIKIN MATAN DA SUKA SAN KANSU? WANDA SUKA SAN MUTUNCI DA DARAJAR KANSU? KO KUWA KEMA KINA CIKI SAHUN SU O’O?* *INA KUKE MANYAN MATA? WAƊANDA SUKA SHIRYA DAN GYARA JIKINSU? AURANSU? DA KUMA FARINCIKINSU?”* *KUYI MAZA KU GARZAYA GUN FITACIYGA KUMA INGANTACIYAR MAI MAGANIN MATA DA MAZA DAN AMSAR NAKU KU GYARA DA KANKU WATO MEERAH HERBS WACCE TAI FICE GUN KAWO MUKU INGANTATTUN MAGUNGUNA BA TARE DA ALGUS BA.* Mun gwada mun gani 💯 Mun gani mun shaida 💯 Anyi mun gani 💯 MAGANIN SANYI MAGANIN NONO MAGANIN HIPS MAGANIN SLIMMING MAGANIN NANKARWA GYARAN AMARE GYARAN MAIJEGO MALLAKAR MIJI KO MATA SUBULU DA SCRUB MAYUKA NA GYARAN JIKI TURAREN WUTA MATSI MAGANIN NI'IMA MAGANIN TSUMI INFECTION FLUSHER DA DAI SAURANSU…..Uwar gida, Amarya, Budurwa, Saurayi, Ango, Mai gida? Duk mai kuke jira? Kuyi maza ku garzaya Meerah herbs maganin dake ingantace 💯 08142800199 07068558096 Aydah ta dinga jido kayan kwalliya kamar wacce za ta buɗe shagon makeup alhali ko powder bata damu da ta shafa ba, da Aydah ta yi wanka iyakanci ta shafa turare amma ko mai bata shafawa, idan ka ga tasha mai to ga bazara (hunturu) ne shima don kada skin ɗinta ya bushe amma ba don haka ba, ba abinda zai haɗa ta dashi. Siyama ce ta iso kusa da ita ta leƙa kayan dake ciki cart ɗin Siyama batasan sanda ta zare idanuwa gami da faɗin "Aydah me za ki yi da wannan tulin kayan kwalliya ke da ba makeup kike yi ba?" Tura cart ɗin ta Aydah ta yi ta wuce Siyama ba tare da ta kula ta ba, saurin bin bayanta Siyama ta yi "Magana nake dake Aydah ki faɗamin me za ki yi da kayan kwalliya ko don salon almubabzaranci? A shawarce ki ɗauke abinda kika saba dauka a kowanne wata amma wannan powder lipstick, mascara da sauransu ba amfani da za su yi miki asalima Mami ba za ta biya kuɗi wannan tarkace da kika ɗiba ba, don tasan ba amfani za ki yi dasu ba. "Yaya Siyam kowa yana da 'yanci zabar abinda yake so nima a wannan karo kayan kwalliya nake so. Siyama ta fashe da dariya tasan saboda Mami ta bugewa Aydah baki shine ta sauke fushinta ta hanyar daukar abubuwan da za su mata amfani ba. "Aydah ke fa ba baƙuwa ta bace nasanki sarai fushi kike yi doke miki bakin da Mami ta yi shine kika kwashe waɗannan kayan... "Yaya Siyam ki kyaleni dan Allah kar nayi magana kuma ace na yi miki rashin kunya. "Shi kenan naga ta yadda Mami za ta biya kudaden wannan tarkacen. Siyama ta ƙarashe magana tare da nuna cart ɗin da bakinta ta wuce abinta, ta bar Aydah tana gunguni kowanne su ya zo da kayayyaki da ya ɗiba da aka zo kan na Aydah da mamaki Mami take kallon ta, tai sauri kauda fuska tamkar bata lura da kallon da Mami take mata ba. Mami ta haɗiye mamakinta ta ciro ATM ɗin ta ta miƙa aka cire kuɗin. Akan hanyar su na zuwa gida Siyama da Sadiya suka dinga korafi dangane da ɓannata kuɗi da Mami ta yi akan abubuwan da Aydah ta dauka ita dai Mami ta na jin su ta yi biris dasu kaman yadda Aydah ta yi musu. Tun kafin Siyama ta iso parking lot suka hango ya Abba tsaye ya jingina bayansa ga jikin motarsa ya wani harɗe ƙafafuwansa yana amsa waya. Sadiya tana kallonsa sau ɗaya sai da ta ji matsananci faɗuwar gaba, tai sauri janye idanunta akansa ganinsu da ya yi ya saka shi ƙarashe maganar da yake yi agaggauce kowacce su ta fito tare da ɗaukar ledar shopping ɗinta. Walking majestically ya nufo su "Sannu da hanya Mami! "Yawwa Abbati ina fatar da ka dawo ka ci abinci? Mami ta yi magana gami da kallon cikin idanunsa, yai sauri sadda kai ƙasa yana sosa ƙeya "Na dai sha fresh milk Mami. "Abba ka daina wasa da abinci kwana biyu nan bana gane kanka kwata-kwata ba ka son cin abinci, idan ba ka gyara ba za mu sami matsala dakai. Mami ta ƙarashe maganar tare da nufar entrance ba tare da ta tsaya jin ban haƙuri da AB yake yi ba. Kusan su dukka uku suka gaida shi ya amsawa Siyama, Sadiya kuma kaman dai koda yaushe bai amsa ba ya yada idanuwansa akan baby face ɗin Aydah yana faɗin "Baby miƙawa Siyama kayan hannunki ki zo mu tafi yamma ta yi banaso mu yi dare sosai. "Ya Abba bari na shiga na canza kayan jikina. Sanin halinta da ya yi da saka fingilallu riguna yasa shi cewa "Oya ki yi sauri karki ɓata min lokaci. Da gudunta ta wuce cikin gida Siyama kuma ta karasa rurrufe kofofin mota ta bi bayan Aydah, aka bar Abba da Sadiya kallo guda yai mata ya kauda fuska sai ma fito da wayarsa ya yi daga gaban aljihun black in colour shadda dake jikinsa wacce ta ƙara fito da farar fatarsa da kuma kyawonsa kansa ba hula sumar kansa ta kwanta lub-lub kaman ta jariri sabuwar haihuwa. Sadiya ta sauke wani lafiyayyen numfashi tai wani kalan langwaɓar da kai tare da marairaice murya tamkar za ta sa kuka ta ce "I'm sorry, Ya Abba, please forgive me, you know I'm not happy at all the way you're treating me kowanne ɗan adam yana kuskure idan kuma ya tuba ya gane kuskurensa afuwa ake masa ba nuna masa tsana da tsangwama ba. Cike da ƙosawa da zancenta ya ja guntun tsaki ya bi ta gefenta ya buɗe motarsa ya shiga, cikin rauni zuciya Sadiya ta bi shi da kallo tana ji wani irin kuka yana zuwa mata duk iya ƙokarinta na hanawa hawayen ta zuba hakan bai samu ba domin kuwa kuka mai ƙarfi ya subuce mata tasaki ledar hannunta kayan ciki suka tarwatse ita kuma ta zube guiwayoyinta kan interlock ta fashe da raunatatce kuka. Abba ya fesar da wata zazzafar iska daga bakinsa har yau yana mamaki irin ƙiyayyar da Sadiya ta nuna masa wacce har ta kaita da yunkuri ɗaukar ransa, duba da irin shaƙuwa da kyautatawa da ya dinga mata tun daga yarinta har zuwa girmanta, bai zaci cewa ko bakin bindiga aka ɗora mata aka aka ce ta caka masa wuƙa ko aɗauki ranta za ta zaɓi ta sadaukar da rayuwarta akansa sai dai kashh! Hasashen sa ne yake bashi hakan. A duk lokaci da ya tuna wancan daren sai ya ji wani irin ƙunci da takaici Sadiya don ba zai ce tsana ba domin kuwa har yanzu yana ji ƙaunarta a matsayin ƙanwarsa. Sai dai zuciyarsa ta kasa yi mata afuwa ta kasa goge hoton abunda ta aikata masa a zuciya da idanuwansa. Aydah ta wuce ɗakinta da gudunta tana zuwa ta jefa ledar shopping ɗinta akan bed, jikinta har wani kalan rawa yake yi duk da bata so kitso da Ya Abba yake ikirarin za ai mata amma tana mararin fita dashi duk wani abu da ya shafi yaya Abba ko ya dangance shi tana daukarsa da matuƙar muhimmanci. Fitted gown ta ciro na wani black and gold ɗin lace ta cire kayan jikinta ta maye gurbin su da gown ɗin. Kayan da shigo dasu ta ciro powder haɗe da man lebe ta shafa powder akan kyakkyawar fuskarta lips ɗinta sai ƙyali suke a a dalilin man lebe da ta shafe su dashi. Turare kusan kala uku ta fesa, ta zari ƙaramin veil ɗinta gold in colour takalmin ƙafarta ma gold ne ya subhanalillah! Ba ƙaramin fitinanne kyau ta yi ba cike da farin ciki ta fice tana fitowa ta hango Sadiya tsugunne tana rusar kuka tun daga gun da Aydah take ta ji sautin kukan nata, taɓe baki ta yi a zuciyarta kissima watakila wani mari Ya Abba ya sake zuzzuba mata. Aydah ta so ta wuce ta ba tare da ta kula ta ba amma abinka da jini ɗaya ba wasa bane, sai ta tsaya musamman yadda taga Sadiyar take shasshekar kuka, ta jikin mirror mota yaya Abba ya hangon ta tsaye kusa da Sadiya tun kafin ta kai da yi mata magana ya danna mata mahaukacin horn dole ta haɗiye kalamanta ta nufi wurinsa da sauri, ta buɗe front seat ta zauna ƙamshin turarenta ya mamaye ƙofufin hancinsa sai da suka fice daga gidan kana ya dawo ganinsa akan fuskarta sosai ta yi masa kyau "Babyn yaya Abba yau kwalliya aka yi?" Murmushi ta yi tana ƙara jefa idanunta acikin nasa tana mai gyaɗa kanta "To amma miyasa ba ki shafa ƙwalli ba? Wani kalan cunno baki ta yi muryarta cike da shagwaɓa take faɗin "Banso kwalli Ya Abba zafi yake min ya dinga sakani hawaye dole. Ɗan ƙaramin murmushi ya yi "Ki ɗaure ki dinga sakawa yana miki kyau sosai. "Ni dai banaso. "To ni inaso ko ba za ki saka saboda yaya Abbanki ba?" Sosai ta washe fararen ƙanana haƙoranta masu ɗauke da siririyar wushirya dimple ɗinta na kunce ɗaya ya lotsa ta ƙara narke masa "Zan saka amma ba koda yaushe ba. Ta yi magana cike da zallan shagwaɓa. "Gaskiya Aydah ki rage ƙazanta kina mace amma ace bakyso kitso, kwali, kwalliya na rasa asalin ƙiyayyar ki da triple k ɗinan. Dariya Aydah ta yi tana bubbuga ƙafafunta akan carpet ɗin da ke wurin ajiye ƙafafuwa a mota "Ni wallahi ba ƙazama bace ina wanka sau uku a yini idan da akwai zafi har sau huɗu nake yi. Ta yi magana tana ɗaga yatsunta huɗu. Taɓe baki ya yi yana faɗin "Miye amfani wankan da babu kwalliya. "Yaya Abba saboda wannan korafin naka yau dai na runtse ido da muka je shopping na dauko kayan kwalliya ba ga gansu ba masu yawa. "Iyeee! 'yanmata yaya Abba dai kwana nan za a ƙaro wulaƙanci. Kusan a tare suka sa dariya sai hira suke abinsu har suka iso Aj beauty palace and spa da sauri Aydah ta kalle shi "yaya Abba ina ne nan? "Saloon ne haɗe da wurin gyaran jiki anan yake yiwa Rumaisa kitso da gyaran jiki na yaba da kwarewarsu fiye da wancan da muke zuwa. Turo baki ta yi ba tare da ta yi magana ba ta ɓalle murfin mota ta fito da kanshi ya yi musu bayani abubuwan da yake buƙata ai mata daga ciki har da pedicure da manicure sannan ya baro shagon ya nufi wuri da suka saba haɗuwa da Rumaisa sai dai su haɗu a keɓaɓɓen wuri ba dai a gidan su Rumaisa ɗin ba duk da irin kakkausar gargaɗin da mahaifin nata ya yi mata akan ta rabu da AB ɗin. Sai dai gargaɗin nasa ya kasa tasiri akanta kamar ma ya ce ta ƙara linƙaya a kogin soyayyar Abba ne. Duk wayewar gari sai sonsa da ƙaunarsa sun daɗa ƙaruwa a farfajiyar zuciyarta. Wuri ne can a ƙarshen gari a wani gidan gona Daddy wuri ne da ake kiwon kaji, kifi, dabbobin mu na gida da na kasashen ketare ga itatuwan fruits sosai wuri ke da wata irin ni'ima wacce ke haifar da natsuwa da kwanciyar hankali. Kusa da motarta ya yi Parking motarsa tuni ɗaya daga cikin ma'aikatan gidan gonar ya kai musu red plastic chairs a gidin bishiyar mangwaro wanda dama anan suka saba zama. Abba ya fito daga motarsa gami da maida ƙofa ya rufe, ya taka a hankali cikin natsuwa ya kai hannunsa ya buɗe side ɗin da Rumaisa take suna haɗa idanuwa suka sakar wa junansu da ƙayatattce murmushi "Ka ɓata almost 15 minutes a bisa lokaci da muka saba haɗuwa halan ka haɗu da traffic jams?? Sai da ya rufe mata murfin motarta ya juya tare da nufar wurin zamansu sai da zauna kana ya bata amsar tambayarta "Baby Aydah na kai Aj beauty palace and spa za a yi mata gyaran gashi. "Baby Aydah! she repeated the name with so much of jealous all over her face. Yayin da shi kuma ko kaɗan bai lura da yanayi da take ciki ba. "Habibi na fara kokwanto akanka da wannan yarinyar ka faɗamin gaskiyar abinda yake a tsakanin ka da ita? Da shock yake kallon fuskar Rumaisa wacce sai cika da batsewa take yi ita kaɗai tasan irin mugun tsanar da ta yiwa shaƙuwar Abba da Aydah tun kafin ma tasan babu alaƙa ta jini a tsakanin su balle yanzu da tasan igiyar aure za ta iya shiga tsakaninsu. Sai abinda tsanar ta ƙara linkawa a zuciyarta, zazzafan kishin yarinya nan take ji marar misaltuwa balle har a faɗin adadin sa. Domin Abba ya kore zargi haɗin da hasashen fassarar kalamin Rumaisa sai ya furta "Ban fahimcin idan wannan tambayar taki ta dosa ba Rumaisa ki daina nuku-nuku ki fito fili ki faɗamin manufar ki. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/12/2023, 10:20 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love Story #Gwagwarmaya #Team tagwaye novels 020.. *RUNBUTUN ƳAN TAGWAYE BIYAR KARO NA BIYU.* *TAFIYAR BIYU TAFI ƊAYA* *KIN TABBATA KIN CIKA MACE? BABBAR MACE DAKE JI DA KANTA? KINA CIKIN MATAN DA SUKA SAN KANSU? WANDA SUKA SAN MUTUNCI DA DARAJAR KANSU? KO KUWA KEMA KINA CIKI SAHUN SU O’O?* *INA KUKE MANYAN MATA? WAƊANDA SUKA SHIRYA DAN GYARA JIKINSU? AURANSU? DA KUMA FARINCIKINSU?”* *KUYI MAZA KU GARZAYA GUN FITACIYGA KUMA INGANTACIYAR MAI MAGANIN MATA DA MAZA DAN AMSAR NAKU KU GYARA DA KANKU WATO MEERAH HERBS WACCE TAI FICE GUN KAWO MUKU INGANTATTUN MAGUNGUNA BA TARE DA ALGUS BA.* Mun gwada mun gani 💯 Mun gani mun shaida 💯 Anyi mun gani 💯 MAGANIN SANYI MAGANIN NONO MAGANIN HIPS MAGANIN SLIMMING MAGANIN NANKARWA GYARAN AMARE GYARAN MAIJEGO MALLAKAR MIJI KO MATA SUBULU DA SCRUB MAYUKA NA GYARAN JIKI TURAREN WUTA MATSI MAGANIN NI'IMA MAGANIN TSUMI INFECTION FLUSHER DA DAI SAURANSU…..Uwar gida, Amarya, Budurwa, Saurayi, Ango, Mai gida? Duk mai kuke jira? Kuyi maza ku garzaya Meerah herbs maganin dake ingantace 💯 08142800199 07068558096 Wani jahilin kallo ta wulga masa shi kansa a yanzu haushinsa take ji ankai stage ɗin da ba za ta iya cigaba da sarrafa tsananin kishin Aydah da take ji. Ba ƙaramin takaici ke kamata ba a duk sanda ya kira Aydah da suna Baby ga bakinsa ya kware da iya kiran Baby Aydah, har wani lankwasa harafin Baby yake yi cike da salon jan hankali wanda shi kam baisan dashi ba watakila kunnen Rumaisa ne yake ji mata hakan. "Abba karka ka raina min da hankali mana idan da can babu soyayya a tsakaninka da ita a yanzu fa? Nan take ran Abba ya yi mugun ɓacin da duk duniya idan da akwai abinda yake saurin haifar masa da matsanancin fushi shi ne a danganta shi da kalmar aure ko soyayya da Aydah yanzu nan sai ka ga ya fusata irin fushin da baya misaltuwa. "Wannan wacce irin maganar banza ce Rumaisa? Don kawai kina sha'awar ki ɓata min rai shine kika bijiro min da wannan zance. "A'ah! Abba duk mai cikakken hankali zai fahimci yadda kake nuna tattali da kulawarka akan yarinya nan ya zarce ƙa'ida ta wa da ƙanwa. Haba sai kace ita kaɗai ce ƙanwarka naga dai su uku ne har ma da wacce aka yi maka auren huce haushi wannan nake nufi wacce taso ta datse numfashinka, ban da ma rashin zuciya irin naka Abba me za ka yi da zuri'ar da suka yi yunkuri kawo ƙarsh..... Abba bai bari Rumaisa ta kai ƙarshen zancenta ba ya wanke mata kumatunta da kyakkyawan mari wanda sai da jinta da ganinta suka ɓace na wani lokaci. "How dare you Rumaisa! Ke har kin isa ki zagi family da suka inganta min rayuwa suka mayar dani ɗa kaman kowa, na zama abin sha'awa har ke ɗinan kika yi kwaɗayi haɗa zuri'a dani. Rumaisa ni ba butulu bane mai manta alkhairi duk da ba su kasance biological parents ɗina ba hakan ba zai sa na zuba ido ina kallo a furta mummunan kalma akansu. Har gobe su ɗin nake kallo a matsayin iyayena banida kamar su a duk faɗin duniya nan, inason su ina ƙaunarsu, sune komai nawa idan har bakinki zai ci-gaba da faɗar kwatankwacin irin wadannan zafafan maganganu akansu, dan Allah kowa ya kama gabansa dama can ke ce kika nacewa alaƙarmu. Cike da wani kalan tashin hankali Rumaisa take dafe da kuncin ta tana kallon AB ba kalmar da ta fi ƙona mata rai irin cewar da ya yi ita ce ta nacewa alaƙarsu, ta ji zafin kalmar nan fiye da marin da ya yi mata. "Wannan shine kashedi na dake na ƙarshe karki kuskure ki sake danganta aure ko soyayya a tsakanina da Aydah domin har gaba da abada babu wannan alaƙar a tsakanin mu. Daga haka ya juya ransa a ɓace ya shiga motarsa ya ja ta da ƙarfi ta bishi da kallo har zuwa lokaci hannunta yana kan fuskarta gun da ya mara, bata taɓa sani Abba yana da zafin rai har haka ba iya sani da tai mishi mutum ne mai sanyi hali da haƙuri ba kasafai ake gane fushinsa ko ɓacin ransa ba. Ita kanta tasan ta kaishi bango ne shiyasa har ya ɗauki hukunci makamanci wannan akanta. Jiki a sabule ta shiga motarta ta nufi gida, zuciyarta a cukude ta wuce ɗakinta ta faɗa kan gado idan Allah ya taimake ta ammi bata cikin main parlor ɗin, balle taga yadda idanunta suka yi jajir ga kuma shatin kyawawan zara-zaran yatsun Abba biyar shimfiɗe akan tattausan farin kumatunta, sai lokaci tasami damar sakin ɗan marayan kuka. Sai da Abba ya yi tafiya mai nisa kafin ya gangara gefen titi ya yi parking ya kifa kansa akan steering wheel, wani irin zafi haɗe da raɗaɗi can ƙasan zuciyarsa ke masa at least ya share 20 minutes wuri da taimakon addu'ar da yake furtawa acikin zuciyarsa ya sami sassauci abunda yake ji har ya iya ɗaukar water bottle ɗin da ke cikin motar duk da basu da sanyi a haka ya ɓalle murfin ya kafa a bakinsa a bottle ɗin sai da ya sha fiye da rabin ruwan kafin ya maida murfin ya rufe tare da mayar da su gun da ya ɗauko su. Ya ja dogon numfashi ya sauke ya sake ja wani ya sauke sai da ya yi hakan kusan sau huɗu sannan ya ji natsuwarsa tana dawo masa a hankali a jikinsa tuni duhun magariba ya yi wanda ke nuni da an kammala sallar magarib ya yiwa motar key cikin tuki natsuwa ya haura kan titi a wani masallaci ya tsaya ya yi sallar magariba da isha sannan ya nufo Aj beauty palace and spa ya ɗauki Aydah wacce yake tunani tun-tuni an kammala mata shi kaɗai take jira, ai kuwa hasashen ya tabbatar gaskiya domin kuwa a taƙure ya iskota zaune sai faman rarraba idanuwa take yi tana neman gun da zai ɓullo, tana arba dashi ta taso da sauri ta nufe shi tana ɓaɓɓata fuska kaman za ta yi kuka "You took long time Yaya Abba da ba ka zo yanzu ba Allah har zan fara musu kuka. Ta ƙarashe magana cikin zallan tabarar nan da ta saba masa. "I'm sorry Baby na tsaya nayi sallah ne. Ya yi magana yana mai shafa kumatunta ya je ya biya su kuɗin aikinsu kana suka wuce wurin mota tun yana reverse ta fara cewa "Ya Abba duba kitso na( shuku) aka yi min ya yi kyau sai dai yaya Abba akwai zafi Allah kaman kaina zai cire? Ta faɗa tana wani kalan matso ƙwallan shagwaɓa. Bai kula ta ba har sai da ya daidaita motar akan titi ya dawo da ganinsa akan kitson kanta da bata maida ɗan ƙwalinta da ta cire ba "Wow! Kitso nan ya yi kyau sosai kin ga ma kuwa uhm! Uhm? Sai kawai ya dinga uhm! Me ma zai ce can kuma cike da zolaya ya ke faɗin "Aididin yaya Abba mai majina a hanci ta yi kashi a wando. Aydah ta fashe da kukan da babu hawaye tana faɗin."Yaya Abba! Yaya Abba! Ni ka daina banaso na girma bana kashi a wando kalli hancina ka gani babu majina! Yadda ta dinga zuba mishi rigima kala daban-daban hakan ya mantar dashi damuwar da Rumaisa ta haifar mishi da ita kafin su iso gida ya tsaya ya siya mata tsire ita da Siyama yasan suna sonshi sosai ƙarfe 9:00pm daidai suka iso gida shi ya wuce a ɓangaren sa ita kuma ta shigo da ledar tsirenta a hannu da wani irin fara'a shimfiɗe akan fuskarta gashi kitso da aka yi mata ya ƙara haskaka fuskar nata goshinta sai ƙyali yake, sanin batayi magarib ba yasa ta wuce ɗakinta direct wanka tayi dan duk ƙanunun gashi sun manne mata cikin wuya, harda alwala ta haɗo ta a lokaci ɗaya ta gabatar da sallar magarib da ishai, tana gamawa ta dauko doguwar rigar bacci ta saka ajikinta Kai tsaye parlor ta wuce,ta miƙawa Siyama ledar tsirenta har kusan ƙarfe goma sha ɗaya ta kai a parlor tana zaune tana taya su yaya Sadiya dake kallon wani movie a tashar (African magic epic )duka hankalinsu yana kan movie ɗin daidai lokacin da AB ya shigo cikin parlor dan bai ci abincin dare ba ya shigo yasha coffee kafin ya kwanta dan har jin yake cikinsa na wani kalar nadewa, daidai lokacin da idonsa ya hasko masa macce da namiji kwance akan gado suna romance ɗin juna hankali tashe yake kallon ƙannen nasa ganin duka hankalinsu ya tattara ga akwatin talabijin musamman Aydah wani kalar faɗuwa gabansa ya yi da sauri ya je ya kashe kayan kallon duka sai lokacin suka bisa da kallo dukkansu su uku. Siyama ta mike tsaye tana zaro idanuwa hakama Sadiya da Aydah kowacce ta yi wuƙi-wuƙi mugun kallon da Abba, ke jefa masu yasa Siyama ta fara kame-kame sai ita Sadiya ta wani kalan daure fuska "Yaushe ku ka fara kallan tashar nan a gidan nan?" Abba ya faɗa rai ɓace tuni ita dai Aydah idanunta suka fara cika da kwallah cike da ƙarfin hali Siyama ta ce."Dan Allah yayanmu ka yi haƙuri wallahi koda na shigo Parlor nan na tarar da yaya Sadiya da Aydah suna kalla. Rasa ma abun faɗa ya yi duk yafi ji takaicin yadda Aydah ta tattara hankalinta akan Tv. Su yasan shekarunsu ya kai su kalla ita fa?" jin yaki cewa komai dukansu suka juya suka nufi stairs ita ma Aydah tana kallonsa ta juya tabi bayansu ganin yadda fuskarsa ta zama lokaci ɗaya tsoron yi masa magana take kar yayi mata ihu. Kitchen ya nufa ya haɗa coffee ɗinsa ya dawo cikin parlorn yana sha still kallon da ya sami ƙannen nasa nayi yana gilma masa cikin idanuwansa gobe zai yi waya da office ɗin Dstv acire masa duk wata tashar da ake haska ire-iren wa'yannan movies ɗin. Aydah har ta yi shirin kwanciya taji an turo ƙofar ɗakin nata da sauri ta kara danna kanta cikin pillow dan duk a tunaninta yaya Abba ne ya biyo ta yayi mata faɗa sai ta ji muryar Sadiya akanta buɗe idanu ta yi tana kallon yayarta ta, fuska a haɗe Sadiya ke faɗin."Daga yau idan kinga muna kallar irin wannan movie ɗin a parlor karki ƙara zuwa ki zauna a ɗakinki ko ranki ya ɓaci kema gulmace ta kawoki nasan saboda ke yaya Abba ya wani kashe kayan kallo. Bancin yasan mun isa muda muke zuwa jami'a danke yayi karki kara zuwa gashi nan kin ja mana a banza a wofi ba za mu sami damar ƙarasa kallan movie ɗin ba. Sadiya ta ƙarasa magana sounding so pissed up tana bar wa Aydah ɗakin. Sai mita take ita kaɗai yaya Abba, ya shiga hakkinsu kuma yayi ne saboda Aydah ita da take ƙarama a daren Sadiya bata kwanta ba sai da tai downloading movie ɗin akan laptop ɗinta ta kalli abunta hankali a kwance acan kasan ranta tana mamakin yayan nasu gashi dai yana da class yana da wayewa sai ya yi ta wasu abubuwan yan ƙauye kenan da har yanzu tana da aurensa akanta haka zai riƙa kallonta ya wuce bancin da ranta da lafiyarta. Ranar Saturday misalin ƙarfe goma na safe Daddy ya ɗauki wayarsa ya kira layin Abba ,bata jima tana ringing ba Abba ya ɗauki wayar Daddy ya faɗa masa ya samesa a parlor yanzu. Ya amsawa da Daddy da to gashi nan zuwa daga shi sai boxer ajikinsa ya nemi jallabiyya ya saka ya nufi part ɗin iyayen nasa da sallama ya shigo Parlor Mami ta amsa tana kallonsa ya samu wuri ya zauna kasan rug Daddy ya buɗe wata envelope ya ciro card ɗaya aciki ya kalli Mami ya mika mata da murmushi cikin fuskarsa gaban Mami banda faɗuwa babu abunda yake tun kafin tasan mene ne aciki taji iskar parlor nayi mata kaɗan wani irin tashin hankali ta ji yana zagaye zuciyarta still Mami taki kallon card ɗin dake hannunta da mamaki Daddy ki faɗin."ki duba mana Mariya. AB ya ɗago yana kallon Mami ganin yanayinta ya canja sai da zuciyarsa tayi wani tsalle daga cikin ƙirjinsa a hankali Mami ta ɗora fuskarta saman rubutun dake cikin card ɗin. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/12/2023, 10:43 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye novels 021. Wani irin expression ne kwance a acikin fuskar Mami ta karanta rubutun ya kai sau goma tama kasa fahimtar komai sakin card ɗin kawai ta yi a ƙasa daga Daddy, har Abba bin card ɗin suka yi da kallo. Daddy bai damu da shock ɗin dake cikin fuskar Mami ba, a hankali ya dauki card ɗin ya miƙawa Abba tun kafin ya karɓi card ɗin daga hannun Daddy, ya ji wani irin sanyi na shiga cikin jikinsa cike da ƙarfin hali AB ya karɓi card ɗin hannun Daddy ya ɗora fuskarsa akan rubutun in a second ya daga kai yana kallon Daddy, da shi ma Daddyn shi yake kallo cikin tsananin tsoro gami da firgitarwa AB ke kallon daddy yana girgiza kai da rawar murya yake faɗin."Daddy card ɗin daurin aure nagani amman ban fahimci sunan dake jikin invitation card ɗin ba. Ka yi min bayani sosai Daddy. AB ya faɗa muryarsa na karyewa a hankali addu'a yake Allah yasa Daddy yace ba wacce ya gani jikin invitation card ɗin bace zai haɗasa aure da ita addu'a yake Allah yasa idanunsa kurum ne suka gano masa hakan. Tun kafin Daddy ya yi magana Mami ta miƙe tsaye hankalinta a matuƙar tashe ta kalli tsakiyar idanuwan Daddy sannan ta ce "Wannan karon tunaninka bai faɗa maka daidai ba aure fa za ka yiwa Aydah kuma da yayanta Abba duka-duka shekarun Aydar nawa suke a duniya? Wannan karon kayi kuskure Alhaji ka canja shawara." Wani kallo Daddy ya shiga aikawa Mami yana faɗin."Akwai haramci acikin Aurensu? ko shekarun Aydah ne suka zama haramta na yi mata aure a wannan lokacin?" ban amince ki fadawa kowa cikin 'ya'yanki ba har sai bayan ɗaurin aure. Za ki iya tafiya umurni nake bayarwa ba shawara ba muddin na isa da gidana abi yadda nake so na kuma tsara. Mami kawai ta juya tabar Parlon Daddy ya dawo da dubansa akan AB yana kallon yadda ya zama wani iri tun lokacin da Daddy ,da Mami suka fara musayar yawu ya ji duniyarsa na juya masa. "Abba ina fatar za ka ƙara yi min biyayya a karo na biyu ka karɓi zaɓin da na yi maka?" "Amman Daddy Aydah fa?" Ya faɗa a wani irin birkice ? murmushi kurum Daddy ya yi tare da yiwa AB izinin tafiya yana ƙara faɗa masa date ɗin da ya saka na daurin aurensu babu fashi. Haka ya nufi ɓangarensa ko ganin gabansa baya yi, ko aurensa da Sadiya da aka daura bai daga masa hankali ba kamar wannan ba. Fatansa kawai ya zama mafarki ne ya zama cikin mafarki Daddy ya faɗa masa haka a birkice Mami ta fito parlorn Daddy kai tsaye ɗakinta ta wuce harda su sakawa ƙofar ta key. Sai safa da marwa take acikin ɗakin ga baki ɗaya ta haɗa gumi ita tasan duk duniya babu mai canja wannan ra'ayin na Daddy tunda yace haka zata kasance, ko auren Sadiya da Abba bai ɗaga mata hankali ba kamar wannan auren . Da sauri ta isa bakin gado ta zauna ta jawo wayarta ta shiga dialling lambar ƙanwarta Safeena ita ma dake aure cikin garin Kano a unguwar jambolo. bugu ɗaya Safeena ta dauka tana gaishe da yayarta tana faɗin."kamar kin san inata so na kiraki zuwa anjima kaɗan zan shigo idan yara suka tafi islamiyya. "Safeena me zai hana ki taho yanzu wallahi ina cikin tashin hankali Alh Bashir so kawai yake ya zautar dani. Safeena jin muryar yayarta kawai ya daga mata hankali tace mata to bari kawai ta taho sai mai'aiki ta kula dasu kuma maimoon ma tana gida wacce 'yarta ce ta biyu kuma sa'an Aydah sai yayanta Jameel sai kannensa guda biyu da macce da namiji ƙannen maimoon da mai shekara biyar da kuma shekara bakwai macce ce ƙaramar su. Mami zamanta ta yi a ɗaki dan bata son ko kaɗan 'ya'yan nata su fahimci damuwar da take ciki musamman Aydah yanzu zata kama damunta da tambayar mami baki da lafiya ne." Siyama na kwance a parlor tana karanta English novel dake cikin wayarta ta ji muryar small Aunt ɗinsu, ta miƙe tsaye cike da murna ta rungume ta tana yimata sannu da zuwa ta amsa tana tambayar su Aydah? ta faɗa mata Sadiya ta shiga school Aydah kuma yanzu tabar Parlorn, kai tsaye ɗakin Mami Aunty Safeena ta nufa ita kuma Siyama ta juya kitchen dan kawowa Aunty nata abun motsa baki duk da tasan daga gida take. Mami jin tayi ana knocking sai da ta tambayi wanene Aunty Safeena tace ita ce sa'annan Mami tazo ta buɗe ƙofar dama tana shigowa ta mayar da ƙofar ta rufe, ganin yadda mami ta zama lokaci ɗaya yasa aunty Safeena ta cire mayafin jikinta ta aje ƙaramar handbag ɗinta ta zauna gefen Mami tana kallonta har zata buɗe baki tayi magana taji ana knocking ɗin ƙofar sai da Mami ta tambayi waye?"Siyama ta amsa da ita ce, Aunty Safeena taje ta buɗe ƙofar da karamin tray Siyama ta shigo ta aje akan rug ɗin dake tsakiyar ɗakin na Mami. Aunty Safeena nayi mata sannu Mami ta kalli Siyama tana faɗin."kar fa ku sakarwa mai aiki kitchen ɗin dukkanku, ku tayata har Aydah. Siyama ta amsawa Mami da to Ta fice daga dakin."Safeena kin san me Bashir ke son ƙara yi a wannan karon?" Mami ta faɗa cike da wani irin bakon yanayi a muryarta. Ita dai Safeena kallon yayarta ta kawai take tun kafin ta sanarda da ita abunda ke faruwa ita ma ta fara ta jin hankalinta ya tashi zuciyarta na bugawa."Aure zai haɗa tsakani Aydah da Abba.!" Ita ma Safeena kalmar ba ƙaramin razanata tayi ba ta shiga maimaita Aure da mamaki Safeena ta ce "Mijin nan naki kuwa yana cikin right mind ɗinsa kuwa?"duka -duka nawa Aydah take? Ni Ko kaɗan kin san banji daɗin hukuncin da ya yanke ba tun a auren Sadiya, sai gashi tun kafin su kwana a gidan abubuwa suka cabe."!still bai daddara ba yanzu kuma za ya ƙara haɗa wani auren. To wallahi yaya karki yadda wannan karon ke ma sanyin ki ya yi yawa haka kawai sai ki zuba masa ido yana ta yankewa 'ya'yanki hukunci kema fa kina da hakki dasu. Duka-duka nawa Aydah take? yarinyar dako matakin secondary school bata fita ba. Mami na girgiza kai tana sakin murmushin takaici a hankali "wai sai kace baki san taurin kan Bashir bane?"kin manta waye shi babu wanda ya isa yasa ya canja masa ra'ayi. "To shi abban meya ce?"me zai ce fa kin san kawaicinsa ai bazai iya cewa A'ah ba. Amma hakikanin gaskiya banaso haɗin nan ke kisan akwai alƙawari da muka yi na ƙara ƙarfafa zumunci tsakanin Jameel da Aydah. "Ban manta ba yaya shi kansa Jameel ɗin a koda yaushe yana min zance Aydah ni ce nake taka masa birki na ce ya ƙara haƙuri ta kammala karatun secondary school sai ya bayyana mata sirri zuciyarsa. "Meye mafita Safeena ga baki ɗaya kaina ya kwance?" "To ko dai za ki gwada kira Abban ne cikin sirri ki faɗa masa ya faɗawa Daddy abar maganar nan ko duba da ƙarancin shekarun Aydah." Mami ta girgiza kai tare da faɗin "Sam ba zan iya ba saboda nasan irin girmama zance Alhaji da Abba ke yi ko wuta ya ce yaro nan ya faɗa wallahi ko second ɗaya ba zai ƙara ba zai faɗa ciki. Shiru kawai Aunty Safeena tayi tana jinjina ƙarfin hali irin na mijin yayartata. "Ni dai yaya ga shawara ko za ki yiwa Daddy maganar kawai ya yi haƙuri Abban ya mayar da Sadiya ɗakinta na tabbata idan ya je wa Bashir da wannan zance zai karɓe shi ko ba komai Sadiya ƙosasshiyar budurwa ce saɓani Aydah da take kwaila ko nonuwan kirki basu gama fita a ƙirjinta ba. Shiru Mami tayi tana juya maganar Safeena cikin ranta ɗan ajiyar zuciya ta sauke "Zan gwada wannan shawarar amma kin san taurin kan Sadiya kamar na mahaifinta idan kuma taki yarda fa?" aka koma gidan jiya. Dariya kawai Aunty Safeena ta yi tare da faɗin."Tun da ta kwana a cell ai ko a mafarki ba za ta ƙara wannan kuskuren ba. Idan kuma ba mu sami haɗin kai Sadiya ba sai ki zaunar da Aydah ki nuna mata illar da auren da Abba zai haifar mata kinsan ta da rigima take za ta bijirewa buƙatar mahaifin nata domin ya gujewa abinda zai biyo baya take zai janye kudirin sa. Sai da Mami ta saki dariyar takaici kafin ta ɗora da faɗin "Lallai Safeena kina da sauran sani akan Aydah, ai nan da kike ganinta ko ranta za ta iya bayar wa akan Abba, ƙauna da shaƙuwar dake tsakaninsu ta zarce na misalta miki ita atake. "Cabdijam! To kuwa Sadiyar nan ita ya dace za mu lallaɓa. Da haka mami da ƙanwarta, ta suka yanke shawarar za tayi wa Daddy, maganar ko a mayar da auren Sadiya da Abba ne a karo na biyu kamar zai fi musu sauki akan a haɗa Abba da Aydah. Har bayan ishaai Abba yana can gidansa a kwance wani irin ciwo ƙirjinsa yake da kyar ya lalubi wayarsa ya kira layin abokinsa Abdulkarim bata jima ba tana ringing ya daga jin muryar AB kurum yasan babu lafiya cike da kulawa Abdulkarim ke faɗin."Are you owk AB.?" Sai can kuma ya bude ido yana salati cikin minti ashirin ya nufi gidan AB ɗin a ƙofar gidan yabar motarsa ya yi knocking maigadi yazo ya buɗe masa a tsaitsaye ya amsa gaisuwar da maigadi ke yi masa ya tura ƙofar parlorn yana addu'ar Allah yasa a buɗe take. Ya yi sa'a a buɗe take kai tsaye upstairs ya nufa kusan ɗakuna 3 ne a sama bai san wannne daga ciki AB yake ciki ba ya buɗe na farko baya ciki yana buɗe na biyu ya hango fitila a kunne kamar hasken rana. Ya ƙarasa da saurinsa ya Abba hango kwance akan bed ya rufe har kansa da duvet muryar Abdulkarim ya ji akansa yana kiran sunansa jin shiru yasa ya ya ye duvet ɗin. Ganin he is shivering ya fara salati yana faɗin."ba kada lafiya ne AB? Ɗaga masa kai kurum ya iya yi da sauri Abdulkarim ya ɗauki remote ɗin AC ya kashe duka yana faɗin."kana rashin lafiya still kana zaune cikin AC kodai za muje asibiti ne?" Da sauri AB ya girgiza kansa tare da lumshe idanuwansa har na kusan minti biyu "To wai kai haka za ka ci-gaba da zama ba za ka tashi muje asibiti ba?" Cikin rawar murya AB ke faɗin."ai ba ciwon asibiti bane wannan yafi ƙarfin asibiti." Da mamaki Abdulkarim ke cewa "To ciwon menene?" shiru AB ya yi ga zazzaɓi na cinsa idan kuma ya tuna kalaman Daddy da inviting card ɗin da ya gani na aurensa da yarinyar nan wacce ko a mafarki bai taɓa tunanin za ta zo a matsayin matarsa ba sai ya ji zazzaɓin ya ƙara lullubesa tun da Daddy ya faɗa masa aurensa da Aydah babu fashi ya ji duniyarsa ta tsaya cak!"jin ya yi kamar an ɗauki dutsi mai nauyi an ɗora masa aka. Gani yaƙi cewa komai yasa Abdulkarim yace "kasan ba zan barka cikin wannan yanayin ba dole muje na kai ka asibiti kar kace min a'ah. Da haka Abdulkarim ya riƙe sa zuwa mota ga wani irin zafi da jikinsa ya yi. Bayan likita ya gama duba shi ya yi masa fixing drip, kafin ya bar ɗakin ya dube Abba cike da kulawa ya ce "Abba wacce irin damuwa ce ka jefa kanka ciki? Gashi nan har jininka ya hau. Kauda fuska Abba ya yi da barin kallon likitan shi kaɗai ne zai iya misalta adadin raɗaɗin da yake ji a ciki da wajen zuciyarsa. "Ni fa wannan al'amari ya fara ɗaure min kai Abba haka kwanaki Alhaji ya yi jinya same case with you blood pressure Dan Allah ku dinga saka dangana a zuciyarku, duk abunda ka ga ya faru da ɗan adam muƙadarri ne daga Allah subhanahu wata'ala mu 'yan adam ba mu isa mu canza ƙaddarar mu ba. Burina na zama soja tun daga yarinta nake da wannan buri ko a mafalki ban taɓa hango kaina a matsayin likita ba. Amma sai gashi Allah ya mayar dani likita da nayi imani da babu mai yi sai Allah sai gashi a yanzu ina alfaharin kasantuwa ta a matsayin likita, tuni na manta da wancan buri nawa. Nasan kasani Abba yarda da ƙaddara yana cikin rukunan imani ɗan adam ya yi imani da ƙaddararsa mai kyau ko kuma marar kyau shiga damuwa ko tsananta tunani ba zai taɓa canzawa bawa ƙaddararsa ba. Sai ma ya daɗa jefa mutum a mugun yanayi, a matsayina, na family doctor ɗinku ina shawartar ka da ka cire damuwa aranka ka miƙawa Ubangijin talikai lamarin ka in-sha-Allahu za ka ga ribar hakan. Ka kwanta ka yi bacci domin kana buƙatar hutu zuwa anjima idan jikin naka ya yi kyau sai mu sallame ka, ka tafi gida. Likitan ya ƙarasa magana tare da ɗan bubbuga gefen kafaɗar Abba sannan ya fi ce. Abdulkarim ya ja kujera ya kai saiti da fuskar Abba yake, ya zauna bai ce dashi uffan ba sai faman kallon fuskar Abban yake yi wacce har ta fara bayyanar da rama, Abba ya yi ƙoƙarin buɗe bakinsa ya yiwa Abdulkarim magana cikin sauri Abdulkarim ɗin ya girgiza masa kai tare da ɗora yatsansa akan lips ɗin Abba "shhh! you don't have to talk and just sleep like the doctor said you need to rest. Sai kawai AB ya lumsashe idanuwansa babu jimawa bacci ya ɗauke shi, cike da zallan tausayinsa Abdulkarim ya kama hannunsa wanda bai da drip ya haɗe cikin nasa. *MADAWAKI MANSION* "Mommy gani. Rumaisa ta faɗa sa'ili da ta shigo ɗakin mahaifiyarta Hajiya Jamila. "Ne me wuri ki zauna za mu yi magana. Sai da Rumaisa ta sauke ajiyar zuciya kafin ta nemi sofa dake girke a ɗakin ta zauna kallon da Hajiya Jamila ke mata yasa duk sai ta ji ta tsargu babu shiri ta sadda kanta ƙasa zuciyarta tana mata wani irin bugawa "Rumaisa! "Na'am mommy! "Meke damunki ne? Kwana biyu nan na kasa gane kanki kin daina ci abinci walwalarki ta ragu, kullum kina ƙunshe a ɗaki kamar wata marainiya marar gata oya tell me what's really bothering you. Remember I'm your mother and I should know your worries idan ina da maganin damuwar taki sai na taimaka miki. Rumaisa tana ji waɗannan maganganu sun fito daga bakin mahaifiyarta sai kawai ta ji zuciyarta ta karye ta zube guiwayoyinta ƙasa ta rushe da matsanancin kuka cikin muryar kuka take faɗin "Mommy, I love him so much, I can't live without him, he is the love of my life ba zan iya jure rashin sa ba, ki taimake ni Mommy soyayyar Abba Bashir za ta kashe ni. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/13/2023, 10:30 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #love Story #Gwagwarmaya #Team tagwaye novels 022. *AREWA BOOK*: jeeddah3256 Da gundarin mamaki Hajiya Jamila ke kallon Rumaisa wacce ke wani irin gunji kuka kaman ranta zai fita wani kalan tausayin 'yarta ta ya dirar mata a ƙahon zuciya, tun farko ba ta so Alh Bello madawaki ya rushe auren Rumaisa da Abba ba. Domin Abba yaro ne mai cike da nagarta wanda kowacce uwa za ta so ta haɗa zuri'a dashi har ga Allah ita tana so Abba da 'yarta, kawai dai Alh Bello ya fi ƙarfinta ne. Amma a wannan karan ba za ta yarda sanadin son zuciyarsa 'yarta ta cutu ba. Duka 'ya'ya nawa ne da ita da za ta bari ya salwantar mata da rayuwar guda daga cikinsu musamman ma Rumaisa da take yiwa wata irin ƙauna kasancewar ta Auta. Dukka yaranta uku Raliya ita ce babba ta yi aure tana zaune a Abuja har da albarka yara guda biyu mace da namiji sai Safwan shi kuma yana karatunsa a Cyprus. Hajiya Jamila mace ce mai azabar son 'ya'ya sai kace magge ita idan akan yaranta ne ba abunda ba za ta iya aikatawa ba. Saboda haka rai ɓace ta baro wajen zamanta ta kama kafaɗun Rumaisa ta miƙar da ita tsaye da sauri Rumaisa ta faɗa ƙirjinta, ta ƙara sakin kuka mai ƙarfi har da wani sheɗewa take yi ta kama hannun Ammi ta ɗora a saitin da zuciyarta take, wani irin bugawa zuciyarta ta ke yi wanda ya zarce ƙa'ida wani irin ɓacin rai ne ya lulluɓe Ammi dole ta yi gaggawar ɗaukar mataki, ta nemowa 'yarta muradin zuciyarta. Cikin sigar rarrashe Ammi take shafar gadon bayanta "that's enough, and stop crying, I don't want you to cry I'll try to get to you what you want ba dai Abba ne kaɗai damuwanki ba?" Rumaisa ta yi nodding head "To karki damu matuƙar ina numfashi sai kin zama matar Abba. Sai ga Rumaisa ta washe haƙora tana dariya Ammi tana riƙe da hannunta suka fito zuwa dining room da kanta ta dinga feeding Rumaisa just like a baby. *KIM'S AUTOMOBILE INDUSTRY LAGOS* Yana zaune a office ɗinsa ya saka laptop ɗinsa a gaba yana kallon samfurin wasu motoci da za su iso nan da 30 days a kamfaninsu, dake Cotonou so yake ya gama settled ɗin abubuwa na wannan kamfani kafin ya wuce Cotonou ɗin a can ma ya tabbata zai tarar da ayyuka masu yawan gaske. Yawan aiki ko kaɗan baya damu Alh Aliyu na Uku a rayuwarsa ba abinda ya fi so da ƙauna irin ya yi keeping kansa busy akan harkokin kasuwancin sa. Ko kaɗan baya da sha'awar gidan sarauta da ita kanta sarauta he's always want to achieve his goal to be the most popular number one business tycoon hakan kuma ba zai taɓa samuwa ba idan har bai janye jikinsa daga gidan sarauta ba. Shiyasa koda yaushe yake gudun masaurata a wasu lokutan shi yake ƙiƙƙira tafiya don kawai ya yi nesa da masarautar kudu. Burinsa ace yana da ɗa namiji wanda zai dinga taimaka masa ya tabbatar da yana da yaro namiji dole zai zama jajirtatce kaman shi. Daga baya da ya zauna ya yi nazari sai yaga dacewar ya jawo 'yarsa ta fari a kasuwancin nasa ita ma za ta iya wannan ne ya bashi damar sanya Anaal ta karanci fannin ilimin kasuwanci tun daga sanda ta kammala karatunta, ta fara tayashi da wasu abubuwa sai gashi cikin ƙanƙani lokaci kwarewar Anaal ta kai matakin da bai taɓa zata ba. Yarinyar tana da wata irin baiwa ta ban mamaki ga ta dai ƙaramar yarinya she's just twenty-five years amma tana da wani irin business talent tamkar dai shi. Shiyasa bai taɓa kukan rashin haifar ɗa namiji ba. Anaal ce ta fito daga office ɗinta jikinta sanye da Palazzo haɗe da string blouse ta ɗora ƙatuwar farar jacket wacce ta sauko har zuwa ga guiwayoyinta, saboda yau garin na Lagos an tashi da wani irin mashahurin sanyi ga baki ɗaya ta rufe maɓallai(bottoms) ɗin rigar wanda hakan ne ya rufe ainihin shigar jikinta, ta yi rolling da scarf black in colour takalmin ƙafafuwanta sneakers ne baƙaƙe sosai shigar tai bala'in yi mata kyau. Direct office ɗin Zaheed ta nufa yana zaune akan kujararsa jikinsa sanye da dark blue ɗin long sleeve shirt tare da black chino jeans ya ɗora cardigan sweater mai gajeren hannu akan rigar tasa kunnensa manne da waya tana zuwa a fusace ta jefa masa file ɗin hannunta kallon sama da kasa ya yi mata kafin ya cire wayar daga kunnensa "real disturber ya aka yi ne?" Ya yi magana yana ƙunshe dariyarsa "whats wrong with you bro Zaheed? almost a week ace ba ka ƙarasa aikin wannan file ɗin ba. Me kike so na ce da Abbu idan ya nemi na tura masa da bayanai dake cikin file ɗin?" Miƙewa ya yi iso gabanta ya shammace ta sai ji ta yi ya kama waist ɗinta ya yi sama da ita kaman yadda ake ɗaga yara ƙanana ya zaunar da ita kan desk ɗinsa ya yi tsaye gabanta kafin kuma ya kama kunnen sa dukka biyu "No! No! Ƙarka ma fara yau kam ko kaine shugaban masu magiya na duk duniya ba zan karasa maka aiki nan ba. "Anaal please. "No! Na ce a'ah. "I swear this weekend I will take you to the beach and I will buy you everything you want. "I am tired of the bribes you guys are giving me and leaving me with a lot of work na gaji da tarkace shopping ɗin da ku ke yi min jiya ma sai da na kai wasu kayayyaki orphanage kuma ni ba mahaukaciya bace da zan bari ka dauke ni ka kai beach cikin wannan uban sanyi salon mura ya kama ni I'm not stupid like you think I know what I'm doing saboda haka ka bani wuri na wuce na baro lot of work a office ɗina. Da sauri ya mayar da ita zaune ya ƙara langwaɓar da kai ya ci-gaba da yi mata magiya har sai da ta amince ɗin za ta ƙarasa masa aiki cike da farin ciki ya sumbace forehead ɗinta ta kai mishi duka a shoulder "lazybones. Ta furta tana dalla masa harara "Hey don't call me that. Zaheed ya faɗa yana ya mutsa fuska. "Me yasa? "Saboda I'm not lazy kawai dai dan na faɗa soyayya ne gardin soyayya yake hana ni aiki ke ma kinsan ada ba haka nake fa don duk lazineess ɗina na fi Zeeyad. "Hi guys whats going on here me kuke shirya wa ne da ba ku nemi ni ba tsabar ga ku one soul in two bodies ko? Zeeyad ya yi magana tun kafin ya ƙaraso cikin office ɗin. Jikinsa sanye da exactly irin kayan jikin Zaheed. A lokaci guda Zaheed da Anaal suka sheƙe da dariya har suna tafawa. "Ba wani abu mai muhimmanci bane kaman dai yadda kai da shi ku ka saba yi min magiya tun muna nursery school na yi muku rubutu yanzu ma da muke age of twenty-five ba ku canza ba you guys duk ranar da na juya muku baya basan ya rayuwarku za ta kasance ba. Anaal ta ƙarashe magana tare da sheƙewa da dariya. Zeeyad ya dungure mata goshi yana faɗin "dallah rufe mana baki! Haka kawai da ranmu da lafiya mu mayar da kanmu agogo ba mu da hutu sai aiki mu ba irinki bane muna bukatar mu more ƙuruciyar mu. "Faɗa mata dai bro ko ɗan saurayi nan bata dashi kuma ko last month da muka je birnin kudu sai da mai babban ɗaki ta yi zancen aurenta naga yadda za ta yi aure babu miji. "Ya kamata ki sassauta wa kanki Anaal kalli nan. Ya nuna mata screen ɗin wayarsa hoton wani friend ɗinsu ta gani. "Na gani sai aka yi yaya? Ameer Abdallah Sambo ne inkiya AA Sambo. "Ashe kin shaida shi. "Ta ya za a yi na gasa shaida shi wannan baƙi mayye mai naci tsiya. "Kinsan dai yadda guy nan ya mutu akanki dan Allah ki bashi dama Anaal. Sai da ta ture shi kana ta diro ƙasa tana faɗin "Bai min yi ba. Da sauri Zeeyad ya sha gabanta "Haba Anaal! wallahi guy nan ya haɗu matuƙar haɗuwa. "Kai ka aure shi mana. Ta faɗa tare da harararsa. Zaro idanuwa Zeeyad ya yi yayin da Zaheed ya sheƙe da dariya. "Haba dallah! An gayamiki ni gay ne da za ki ce na aure namiji ɗan uwana. "To naga ka wani zakalkale ne sai koɗa sa kake yi na zaci ko you had a huge crush on him ka ga sai ka aure abinka ko Zaheed? Ta ƙarashe magana tana kallon Zaheed dake ta kyakyalar dariya ƙeta. "Za su dace sosai da juna wa yaga ango da amarya. Zaheed ya faɗa yana ƙara sheƙewa da dariya Anaal tana tayashi. Sosai ran Zeeyad ya ɓaci don bai ga dalili da za su dinga masa wannan mummunan wasan ba. A fusace ya bar musu office ɗin dama sun saba haɗe masa kai. *International private hospital* Drip ɗin jikin AB yana ƙarewa aka sake jona mishi wani sai da ya sha ledar ruwa huɗu kafin likitan ya sallame shi tare yi masa gargaɗin ya dinga sha maganinsa on time. Abdulkarim yaso daga asibiti su wuce gidan iyayen AB a ganinsa acan zai fi samun kyakkyawar kulawa fiye da gidansa tun da a gidan nasa shi kaɗai ne acan kuma ga iyayensa da kannensa, amma AB ya kafe da lallai-lallai shi gidansa zai kai sa ba don zuciyar Abdulkarim taso haka ba sai don bashi da yarda zai yi. Sai da yaga shigar AB bathroom zai yi wanka sannan ya fita ya nemo musu abinci da za su ci saboda yunwa yake ji shima AB dole yana bukatar abinci. AB yana tsaye agaban shower ruwa na sauka akan naked body ɗinsa ya cije lips ɗinsa kafin ya kai hannu ya wargaza jiƙaƙƙiyar sumar kansa tare da lumsashe idanuwansa shi kan yaga ta kansa daga wannan sai wannan yanzu fissibillahi ta ya zai iya karɓar Aydah a matsayin matar aurensa, Sadiya ma da ta kasance cikakkiyar budurwa bai ji zai iya rayuwar aure da ita ba, balle wannan 'yar mitsiyaya yarinya wacce ya rena da hannunsa. A bayyane cikin wata irin raunatatciya murya ya furta "Don't do this to me, Daddy, I can't accept Aydah as my wife yarinya nan fa nine na raine ta ba zan iya ba Daddy. Ya ƙarashe magana wani irin kuka yana subuce mishi sai kawai ya zube guiwayoyinsa kan tiles ya cigaba da kukansa wanda sautin sa ya gama cika bathroom ɗin. Dawowar Abdulkarim kenan ya ji kamar kukan AB a bathroom a tsorace ya ajiye ledar takeaway ɗin da ya yi musu akan bedside drawer ya nufi ƙofar bathroom ɗin ya baza kunnuwansa yana so ya tabbatar da gaske kukan AB ne yake ji ko kuma kunnuwanshi ne ke yaudarar sa domin sani da ya yiwa Abba jarumi ne abunda zai iya saka shi kuka ba ƙaramin abu bane. Wani kalan zaro idanuwa ya yi yadda ya ji shesshakar kukan nasa ya daɗa ƙaruwa bai tsaya wani dogon tunani ba ya buɗe ƙofar ya shiga idanunsa suka yi masa tozali da AB durƙushe yana kuka, zuciyar Abdulkarim ta yi mugun bugawa da ƙarfi da sauri ya nufi hanger dake bathroom ɗin wacce ke dauke da towels haɗe da bathrobe ya zari bathrobe ɗaya ya ƙarasa wurinsa sai da ya kashe shower ɗin kafin ya nufi bayansa ya saka masa rigar ba tare da ya kalle nakedness ɗinsa ba. AB ya ɗago jajaye idanuwansa ya kalli Abdulkarim sai kawai ya sake fashewa da kuka Abdulkarim ya kama shi tare da miƙar da shi tsaye sai kawai ya faɗa jikin Abdulkarim cikin muryar kuka yake faɗin "I can't marry her. I can't see her as my wife. If Daddy marries Aydah to me, I swear to God my heart will stop beating and I will die. Ak ba zan iya ba dan Allah ka sanarwa da Daddy Aydah she is like a daughter to me, I can't live a married life with her. Zuciyana ba za ta iya jure wannan abin kunya ba. Ya ƙarashe magana yana goga fuskarsa a shoulder ɗin Abdulkarim tsanani shock ɗin da Abdulkarim ya shiga ya hana mishi furta uffan sai kawai ya raba jikinsa da na AB kana ya riƙo hannunsa suka fito a gefen gado Abdulkarim ya yi musu masauki ya ɗauki longtime yana maimata maganganu AB ajiyar zuciya ya yi ta yafi sau ashirin kafin ya shiga rarrashin abokin nasa har ya ci nasarar shawo kansa ya daina kukan "AB yaushe Daddy ya yanke wannan hukuncin?" Abdulkarim ya tambaya tare da tsare AB da idanunsa yana jiran ya amsar da zai basa. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/13/2023, 10:46 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye novels 023.. *AREWA BOOK* :jeddah3256 Kusan sau uku yana buɗe bakinsa dan zimmar ya yiwa Abdulkarim bayani sai yaji komai nasa ya tsaya ya kasa buɗe bakin nasa ya yi magana dan wata irin kunyar yin maganar yake ji duk lokacin da ya tuna da Daddy zai aura masa Aydah sai zuciyarsa ta shiga dokawa da wani irin karfi tamkar zata fito daga ƙirjinsa shi dai har lokacin Abdulkarim kallon AB kurum yake kwantawa ya yi akan bed ɗin tare da runtse idanuwanshi gam! Ya ɗauki lokaci a haka kafin kuma ya tashi zaune ya koma ya dafe kansa da dukkan hannunsa biyu ya yi shiru har na kusan mintina biyar. Abdulkarim da ransa ya soma ɓaci ya miƙe tsaye yana mayar da wayoyinsa cikin aljihun wandonsa yana faɗin."ni zan wuce sai da safe, da sauri AB ya kallesa cikin sanyin murya yake faɗin."na dauka nan zaka kwana ae." wani banzan kallo Abdukarim ke yiwa Abban, "na kwana nayi maka uban me sau nawa ina tambayarka meye damuwarka kaki buɗe baki kayi min bayani."dama ni kaɗai ne na damu da damuwarka bance kuma dole sai ka faɗamin ba Allah ya yaye ma abunda ke damunka. Ya faɗa sounding so fed up yana nufar ƙofar fita. Ganin da gaske tafiya zai yi cike da karfin hali AB ya kira sunan Abdulkarim. Dakatawa yayi Amma dai bai juyo ba gani yaƙi juyowa cikin sarkewar harshe yake faɗin."Daddy aure zai haɗani da Aydah wani satin mai zuwa har ya fitar da card na daurin aure. Ya ƙarasa magana da wani irin rauni a muryarsa. With so much shock Abdulkarim ya juyo dukansa, ya nufi AB ɗin ya zauna gefen bed yana faɗin."kace min da wasa kake yi AB?" wani kallo AB ɗin ya yi masa jin irin maganar rainin hankalin da yake yi masa."Na taɓa yi maka kalar wannan wasar?" shine sanadin ciwona gara in mutu da in auri Aydah , yarinyar da na raina da hannu na shin idan ma mun yi auren me zan cira ajikinta."meyasa Daddy yake yanke irin wannan hukuncin batare da wani dogon tunani ba baya duba abunda zai iya faruwa a gaba. "I know my self ko nan da shekara goma zan iya rike kaina batare da macce ba ,ban san taya zan fahimtar da Daddy ba." Ya ƙarasa maganar da wata irin rawar murya duk yadda Abdulkarim yaso hana kansa yin dariya ganin halin da abokin nasa yake ciki sai da ya ɗan dara. Kallonsa kawai AB yake zuciyarsa na tafarfasa dama yasan idan Abdukarim ya ji wannan zance ya samu abun tsokanarsa kenan gashi nan tun kafin aje ko'ina dariya yake yi masa. On a serious note Abdulkarim ke faɗin."yanzu ne za ka fuskanci reality ɗinka AB wai kai baka san irin waya'nnan cwt 16 din ba sun fi daɗin sha'ani ba? A ko'ina ƙwaƙwalwarsu fresh sai abunda ka koyar dasu ka bai wa Aydah shekara ɗaya kaga yadda za ta zama ka koya mata training ɗinka. Da sauri AB ya katsesa "Na koya mata me?" ka daina bata min rai Ak kana nufin me kenan, Aydah fa?" Ak ya juya ido yana faɗin."Yes it's her ba matarka bace. Da sauri AB ya dunƙule hannunsa zai kai wa Abdulkarim wanin irin punch da sauri Ak ya janye yana zaro ido yana faɗin."Haba Angon Aydah Bashir what's the meaning of this manner?" owk na yarda ƙanwarka ce ko bayan an kai maka ita a gidanka rainonta za ka ci-gaba da yi right?" Da sauri AB ya haɗe ransa yana jin zuciyarsa na ci-gaba da tafarfasa irin maganganun da Abdulkarim ɗin ke zubawa. Nasan za ka iya rike kanka har na shekara goma kuma ka ci-gaba da zama tare da Aydah kaga sai ka ci-gaba da shan lemi ɗinka. Tun da Allah yasa baby Aydah ce ka aura. Abdukarim ya karashe magana tare da fashewa da dariyar shakiyanci yana ficewa daga ɗakin ganin yadda AB ya fusata sosai. Ranar tun da Aydah ta dawo daga school ba taga AB ba duk tabi ta damu tana dawowa daga school ta nufi ɗakin Mami ,ko uniform ɗin jikinta bata cire ba take tambayar "mami ina yaya Abba.?" Mami yin tayi kamar bata ji me take faɗa ba. Sai da ta ƙara maimaita tambayar a fusace Mami ke faɗin."Abba yarone da za ki zo ki tsareni da tambayar ina yake." Tamkar zata yi kuka take faɗin "tun Jiya fa Mami ban ji alamarsa a gidan nan ba kuma ba tafiya ya yi ba. Cike da gajiya da zancen Mami tace "Ki fitar min daga ɗaki bana son fitina. Juyawa Aydah ta yi ta fice daga ɗakin har tayi shirin islamiyya ranta a ɓace yake dama kuma ba tayi gigin ɗaukar wayar Mami ba da ta kira yaya Abba. Sai da ta dawo bayan magarib ta shiga ɗakin siyama ta sameta tana waya ta zauna kan soofa tana jiran tagama wayar, Siyama tana ganin Aydah ta yi mata zaune yasata sallama da wanda take wayar, ta kalli Aydah ganin yadda ta yi fuskar tausayi lokaci ɗaya dama kuma idan ta yi haka da akwai abunda takeso a wurin Siyama ɗin."Dama yaya Siyama yayanmu za ki kira min a waya tun jiya fa ban gansa ba kodai ya yi tafiya ne bai sanar mana ba? Ba tare da Siyama ta ce komai ba ta yi dialling number AB har ta katse bai ɗaga ba nan ta sake kira tana shiga ya katse ya kirata ta dauka ta gaishesa da cool voice nasa ya amsa cike da kulawa Siyama ke fadin."Yayanmu mura kake naji muryarka wani iri....! ai kafin ya bata amsa Aydah ta fisge wayar ta nufi ƙofa Siyama ta bi da ta da kallo baki buɗe har Aydah ta fice daga ɗakin direct ɗakinta ta shiga harda su sakawa ƙofar key, dan tasan Siyama tana iya biyo bayanta."cikin sanyin muryarta ta kira sunansa "yaya Abba! "Baby Aydah ya kike?" Ya faɗa da murya marar amo cikin rawar murya Aydah ta ce."Yayanmu bakada lafiya ne?" ina ka shiga tun jiya?" Yana jin yadda muryarta take ɗan rawa yasan za ta iya fashe masa da kuka. Shiru yayi na kusan sakan goma. Kafin yace "Ina hanyar dawowa kafin na shigo ki haɗamin coffee ki soya min egg. shima kawai ya faɗa ne badan wai yana jin yunwa ba. Da farin ciki Aydah ta katse wayar ta koma ɗakin Siyama ta aje mata wayarta akan mirror dan taji kamar motsin ruwa a toilet ɗinta kai tsaye kitchen ta nufa cikin minti goma ta gama haɗawa yayan nata coffee ta zuba cikin flask ta soya masa wainar kwai ta juyeta cikin plate tana zaune a parlor tana jiran shigowar yayan nasu har kusan minti goma da zamanta,ta ji horn ɗin motarsa. kai tsaye part ɗinsa ya nufa Daidai kuma lokacin kiran Rumaisa ya shigo a wayarsa tun daren jiya take ta kiransa a waya yaki ya daga har yau ɗin. ɗagawa ya yi a dakile ya furta "Hello! hankali tashe take faɗin."meya samu wayarka ina ta kiranka tun daren jiya baka ɗagawa?" "Ba komai! Ya faɗa a takaice sai kawai ta kara bashi haƙuri akan yadda ta fusata sa ranar da suka haɗu dan ta yi tunanin ko shine yasa yaki daga wayarta. "Yanzu nan na shigo gida Rumaisa idan nayi wanka na huta zan Kiraki." Ɗan shiru ta yi tana sauraresa cikin sanyin murya take faɗin."karka sa nai ta jira ka je kuma ba ka kira ba. "Insha Allah zan kira. Da haka ya katse wayar kai tsaye master bedroom ɗinsa ya wuce yana rage kayan jikinsa. A hankali ta aje ƙaramin tray ɗin da ta riƙo akan center table ɗin dake cikin parlorn kai tsaye bedroom ɗinsa ta nufa tana buɗe kofar tayi ido huɗu da AB just his short and singlet da sauri Aydah ta nufesa gaba ki ɗaya AB ya ruɗe ganin Aydah ta samesa a haka ba zai iya tuna lokaci na karshe da ta gansa a haka ba. A tsawace yake faɗin "me na faɗa maki kafin ki shigowa mutum a ɗaki Aydah?" tsayawa tayi cak.! tana kallon yanayin yayan nata jin taki magana yasa yace ta fita ta jirasa a parlor juyawa kawai tayi ta fita tamkar za tayi kuka ganin irin tsawar da ya yi mata ita ta ma manta da bayaso a rika shigar masa ɗaki babu sallama. Zama ya yi gefen gado ya dafe kansa da yake jin yana masa ciwo har lokacin yafi minti biyar a haka kafin ya tashi dakyar ya nufi cikin closet nasa jallabiyya ya ciro marar nauyi ya saka ajikinsa kai tsaye parlorn ya nufa har lokacin fuskar Aydah a haɗe tamkar ba a taɓa halittar murmushi acikin fuskarta ba. Zama ya yi yana kallon yadda ta wani folding hands ɗinta akan ƙirjinta ta wani kwabe baki da alamar kiris take jira ta fashe masa da kuka. Ya zauna gafda ita ya riƙo hannunta murya kasa-kasa yake faɗin."waya tabamin baby ne.?" cike da tabara ta nunasa da hannunta wanda yasa ya ware mata manyan fararen idanunsa, wanda yasa dole sai da ta saki murmushi har kumatunta suka lotsa ya dauki coffee ɗinsa yana sha a hankali batare da ya taɓa wainar kwan dake cikin plate ba. "Yayanmu baka ci wainar kwan ba." Ya ɗan kalleta kafin yace bana jin daɗin cikina barni kawai nasha coffee ɗin har kusan 9 Aydah na bangaren AB sai da yaga ta fara masa gyangyadi yace ta tashi ta je ta kwanta ta haɗa kayan ta koma cikin gida Mami sai bin ta kawai take da kallo bata dai ce komai ba ganin ta nufi stairs yasa Mami tace "abincin fa?" Ta murza ido tana faɗin."Mami bacci nake ji na koshi" Da haka Mami ta dauke kanta dama Sadiya tunda taga Aydah ta shigo Parlon ta ji wani abu ya tsaya mata a wuya, har aranta ta fara tsanar alaƙar Aydah da Yaya Abba. Tasan idan sune suka je part ɗinsa da yanzu ya korosu yace su tafi zai yi aiki. Amma Aydah sai tayi kusan awa biyu a part ɗinsa ba zai ce ta tashi ta tafi ba. Ganin dai babu kowa a parlorn Sadiya ta yi gyaran murya tana kallon Mami zuciyarta na ɗan bugawa ta saukar da kanta kasa dan bata san yadda Mami zata karbi zancenta ba "Mami dama maganar aurena da yaya Abba ne dan Allah Mami, ina son ki kara bai wa Daddy, haƙuri akan abunda ya faru wallahi nayi nadama kuma hakan ba zai ƙara faruwa ba. Na yarda na haƙura yaya Abba ya mayar dani ɗakina mu yi zaman aure na har abada."! Sadiya ta ƙarasa magana kanta a ƙasa Mami kallon Sadiya kawai take. Tamkar mai son gano abunda ke cikin zuciyarta wani murmushin takaici Mami, ta yi tana faɗin."To Allah yasa Daddy naku ya yarda. Cike da zallar farin ciki Sadiya ke faɗin."zai ma yarda Mami kinga zai dawo yana amsa gaisuwata daidai kamar kowa Mami. Da haka Sadiya tabar Parlon zuwa ɗakinta cike da tsananin farin ciki tamkar an dauke mata dukkan damuwarta Tasan idan Daddy yaji wannan zancen zai yi matuƙar farin ciki da haka ,sai murmushi take ita ɗaya a ɗaki tamkar wata wacce ta zauce ba ƙaramar rahama Allah yake sonta da ita ba da ta dawo hankalinta lokaci ɗaya. Samun miji irin yaya Abba a wannan zamanin ai sai an tuno har ta hango yadda yayanata zai rika sarrafata akan gadon aurensu yana kasheta da salon soyayyarsa. Mami tafi minti biyar zaune a Parlon na Daddy sai ta ji damuwarta ta ragu saboda yadda Sadiya ta zo mata da wannan zance kamar dai tasan abunda suke shirya wa, ta rasa ta inda za ta fara yi masa bayani, cike da karfin hali ta dubi Daddy ta ce "Alhaji ɗazun nan Sadiya ta sameni da wani zance ta faɗamin na ƙara baka haƙuri kuma tana neman alfarmar a mayar da aurenta da Abba....."! Wani tsinannen kallo Daddy ya rika yimata cike da takaici yake faɗin."mariya!" jin yadda ya kira sunanta har tsakiyar kanta kafin yace."Aure ya haramta tsakanin Sadiya da Abba har abada kin manta ƙanwarta zai aure yanzu. Ai tayi wasa da damarta har abada kuma damar ta ri ga tafi ta barta karma na kara jin wannan zancen. Duk yadda Mami ta so fahimtar da Daddy kin saurareta ya yi kamar ma rigima yaso zamar masu acikin daren. cike da zafin zuciya Mami ta baro bangaren na Daddy ta koma nata #Love story 2023/2024 #jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #team tagwaye Novels #kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/15/2023, 10:35 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye Novels 024. *AREWA BOOK:* Jeddah3256 *MASARAUTAR KUDU* Tun daga ranar da Kilishi ta bayyanar wa Ciroma da ainihin buri da muradinta ta ya ye masa natsuwa da kwanciyar hankali. Kullum burinsa da fafutukarsa, haɗe da faɗin tashinsa sun ta'allaka ne a nema da lallube mafita wacce yake kyautata zaton za ta kaishi ga cimma muradin sa. To amma wani babban abin takaici har yau ɗinan da ya tashi tsakiyar yana shawagi daga bangon gabas zuwa na yamma bacci ya kauracewa ganinsa duk da wannan ba shi bane karo na farko da ya tsinci kansa a cikin irin wannan yanayi ba. Kusan duk daren Allah sai ya tashi tare da matsanta wa ƙwaƙwalwarsa da ta nemo masa saukaƙkiyar hanya da zai bi ba tare da wani ko wata ya farga da takunsa. Burinsa ya sami mafitar da za ta sada shi da daɗe muradinsa. Matuƙar zai sami biyan bukata bai damu da ko mutane nawa za su cutu ba. Matarsa kuma amaryarsa Hajiya Umaima ce ta juya domin gyara kwanciyar ta sai kawai ta yi tozali da mijinta dake sarƙe da hannaye a ƙirji yadda yake safa da marwa yafi kama da mace mai naƙuda. "Allah ya taimake Ciroma kuma sarki gobe a masarautar birnin kudu wacce damuwa ce ta saukar maka haka wacce ta hana ka more dare wanda Allah subhanahu wata'ala ya sanya don ya zamo wa bayinsa mahuta (hutu)?" Hajiya Umaima ta ƙarasa magana tare da sakkowa daga kan gado ta nufa wurin Ciroma wanda yake gani ga baki ɗaya duniya ta yi masa juyi ɗan mangwaro wani kyakkyawan numfashi Ciroma ya fesar kafin ya juya ya fuskanci Umaima cikin wata rikitatciya murya ya ce "Umaima dole kin ganni a haka domin abubuwa suna neman kwace min duk wani buri nawa yana neman subuce min, wani abin takaici ina ji ina gani Umaima zan rasa cikar burina. Sai da umaima ta fesar da wata kalar iska daga bakinta kafin ta ce "Allah ya ƙara wa Ciroma lafiya tun farko na zo maka da shawarwari masu kyau da inganci amma sai wannan munafukar matar taka wacce ba ka taɓa gani laifinta sai ta hana ka bin shawarar tawa to wallahi kasani Ciroma matuƙar ba za ka bi hanyar da nake so ɗora ka ba har abada burinka ba zai taɓa cika ba. Hatta da wannan sarautar ta Ciroma da ka gama rainawa wata rana kana ji kana gani za ta gaggare ka, Allah ya ri ga ya haɗa ka da uwar da bata so cigaban ka, ka duba ka gani kaine babba a wurinta amma a koda yaushe ƙannanka take ɗorawa akan komai, kai ta mayar da kai saniyar ware kai da banza da babu duk ɗaya. Amma ka gafarce ni idan na faɗi maganar da ba daidai ba. Raina mugun ɓaci yake a duk sanda na tuna da irin abunda Hajiya Kilishi take maka. Wani zazzafan iskar Ciroma ya fara furzar wa tare da dunƙule hannunsa na dama ya naushin tafin hannunsa na hagu, wani irin takaici da baƙin ciki yake ji yana taso masa tun daga yarinta yake fuskantar nuna bambanci da mahaifiyarsa Hajiya Kilishi ke nuna wa a tsakaninsa da 'yan uwansa, sau dama ya sha tambayar ta idan akwai laifin da yai mata wanda shi baisan dashi ba ta yi haƙuri ta yafe masa. A duk lokaci da ya yi mata magana kwatankwacin wannan da zarar ta buɗe bakinta sai dai ka ji ta ce dashi "Ciroma wasu abubuwa da muke gani suna jingine ne a matsayin Kurman allo domin ba kowa ke da basirar iya fahimtar su cikin saukaƙkiyar hausa ba balle har ya fassara su zuwa ga harshe mafi sauƙin fahimta. Wadannan kalaman nata masu cike da murɗaɗdiyar ma'ana da ƙwaƙwalwarsa ta kasa fahimtar ma'anar su. "Umaima ba wai naƙi shawararki bane kawai dai ina duba da gobena ne kada garin gyaran gira aransa ido. "Ranka ya dade wannan al'amari fa za a iya aikatawa daga baya sai a nemi yafiyar ubangiji ai Allah gafuru raheem ne. Amma wallahi ina tabbatar maka idan ka ci-gaba da biye wa tsohuwar matarka za ci kasuwa a watse a bar ka da kuturun jaki. Ba tare da Ciroma ya yi magana ba ya nufi gadonsa ya zauna ya deep breath kana ya yafito umaima da hannunsa "Zo ki zauna Umaima ki yi min ƙarin haske domin a shirye nake tsaf da na bi kowacce irin hanya za a ɗora ni matuƙar dai zan sami biyan buƙatata. Da sassarfa Umaima ta zo ta zauna kusa dashi ta dinga warware masa zare da abawa. "Amma Umaima kina gani shigo da jakadiyar Umma a wannan tafiyar zai haifar mana da ɗa marar ido ba? "Ranka ya dade kafin na shigo da ita cikin wannan al'amari sai da na toshe duk wata kafa da za ta iya zama barazana a gare ka sannan kuma komai na duniya yana da sanadi ka sa aranka jakadiya ita ce mattakalar nasarar ka ta farko. "Na yarda dake Umaima na kuma damƙa miki wuka da nama idan har muka yi nasara a wannan tafiya Allah ne kaɗai yasan adadin kyaututtukan da za ki mallaka daga gareni. "Godiya nake Ciroma Allah yabar min kai. "Amin! Amaryata. Yanzu daga ina za mu fara?" "Ka bani ɗan lokaci ƙanƙani zan yi magana da jakadiya duk yadda muka yi da ita za ka ji daga gare ni. "Shi kenan! Ciroma ya faɗa zuciyarsa cike da muradin mallakar masauratar kudu. *Washegari* (Part ɗin mai Babban ɗaki) Mai babban ɗaki tana zaune a cikin ɗakin baccinta ranta a ɓace yake al'amari Aliyu ya fara kaita bango jakadiya ce ta buɗe ƙofa ta shigo bakinta ɗauke da sallama tana zuba ta zube a gaban mai babban ɗaki "Ranki ya dade gani na amsa kira. Shiru mai babban ɗaki ta yi na ɗan takaitaccen lokaci kafin cikin izza ta yada ganinta akan jakadiya wacce ke durƙushe tana jiran umarni "Jakadiya na kira ki ne dangane da naɗin sarautar Aliyu gashi lokaci sai daɗa karatowa yake amma babu wani shiri da Aliyu ya yi kuma ko na nemi shi a waya bana samun shi. Shin kin aikatar da aikin da na saka ki?" "Ranki ya dade ɗazu cikin hukuncin Ubangiji cikin dabara na dinga bugun cikin Magaji ƙarami ya tabbatar min da Sarkin sabon birni yana ikko (Lagos) babu wata kasar turawa da ya je a lokaci da muke tattauna wannan maganar da Magaji ƙarami zuciyata har wani zafi take min miyasa Sarkin sabon birni yake so ya watsa miki ƙasa a ido? Bayan yasan 'yan baƙin ciki da masu son gani bayansa burinsu kenan yabar sarauta da masarauta. Ajiyar zuciya mai babban ɗaki ta sauke wani irin nauyi take ji ƙirjinta ya yi mata har sai yaushe Aliyu zai san muhimmanci da sauratar nan take da a wurinsa bata taɓa gani jinin sarauta dake gudun sarauta irin Aliyu ba. "Jakadiya dauko ɗaya daga cikin wayoyina ki kira Anaal. "An gama! Allah ya ƙara miki lafiya da nisan kwana mai amfani. Jakadiya ta yi magana tare da miƙewa ta dauko wayar, ta yi dialling numbern Anaal har ta tsinke Anaal ba ta ɗaga ba. "Allah ya ƙarawa uwar magajin masaurata nan Lafia na kira Anaal amma cikin rashin dace ba ta ɗaga ba. "Ki aika ɗaya daga cikin bayi su kira min sarkin fada akwai tattaunawa da za mu yi dashi. Sannan ki faɗawa Rahane ta tabbata magaji ƙarami ya ci karin kumallon sa. "An gama Ranki ya dade faɗa taki cikawa ta mu makiyanki fadawanki balbela ba ki yi farin banza ba, ki yi naki ki yi na wasu baya goya marayu Allahu ya haskaka kabarin Sarki Usman na Uku. "Amin jakadiya! Mai babban ɗaki ta faɗa cikin wata irin izza da taƙama kafin ta kishigiɗa tare da lulawa duniyar tunani. *ALH BASHIR MANSION* "Ya aka yi Sadiya ba ki tafi school ba ko yau ba ki da lectures ne?" Mami ta yi magana tana kallon Sadiya ta shigo mata ɗakin bacci. Sai da Sadiya ta gaida Mami kafin ta nemi gefen gado kusa da ƙafafuwan Mami ta zauna cikin sanyi murya ta ce "Bana jin daɗi jikina shiyasa ban je ba. Cike da kulawa Mami ta tashi zaune ta kai hannunta gefen wuyan Sadiya ta tattaba "Subhanalillah! Gashi nan jikin ki har ya yi zafi kin sha magani kuwa?" "Eh! Na sha. Mami dama zuwa na yi na tambaya ko kin yi maganar komawa ta gidan yayanmu da Daddy?" Mami ta yi ajiyar zuciya yayin da damuwar da take ƙoƙarin ɓoyewa ta bayyana akan fuskarta "Sadiya Daddynku bai amince ba. "Innalillahi wa'inna illahim raji'um! Mami saboda me? Sadiya ta yi maganar a ruɗe ga wani irin bugawa da zuciyarta ke mata da ƙarfin gaske tuni har idanuwanta sun cicciko da ƙwalla. "Saboda Aydah yake so ya haɗa da shi nan da one week za a ɗaura aure har ya buga invitation card kuma wannan maganar banaso ta fita ta tsaya iya tsakanina dake. Duk yadda Sadiya taso ta hanawa kanta kuka kasa wa ta yi domin kukan zuwa maka yake ba tare da ka shirya wa zuwan nasa ba, da sauri Mami ta jawo ta zuwa cikin jikinta tana shafa gadon bayanta "Sadiya dama kina so Abba ko kuma daga baya ne kika fara son nasa?" "Nima bansan yaushe ne ba Mami zan iya cewa dake kawai wayuwar gari nayi na tsince kaina dumu-dumu a cikin matsananciyar soyayyarsa. Mami ki taimake ni ki yi wani abu akai ki hana faruwar aure nan da Aydah dukka Aydah guda nawa ce da za a yi mata aure. Wallahi ko kaɗan bata dace da yayanmu ba. "Sadiya ba irin maganar da ban gayawa Daddynku ba amma kwata-kwata yaƙi ya saurare ni me ƙato kaman Abba zai tsinta a jikin 'yar mitsiyaya yarinya irin Aydah fisabillahi me ya hau kan Daddynku ya yi wannan bahagon tunani. Mami ta ƙarashe magana cike da wani irin takaici. Sadiya ta karawa kukanta sauti bata taɓa sanin soyayyar da take yiwa Abba Bashir ta yi girman haka ba sai da ta ji Mami ta furta aurensa da Aydah wannan wacce irin ƙaddara ce take so ta yiwa rayuwarta shigar kutsu jiya-jiya nan ta gama ganin hotunan auren Hafiz Sale suna trending a social media, duk da bata da sauran feelings akansa amma sai da ta ji haushi sai ta ji burinta na son komawa gidan Abba ya karu ko ba komai za ta nuna wa Hafiz Sale ita ma fa ta daina sonshi ko shi kansa Hafiz ɗin yasan Yaya Abba yafi shi nesa ba kusa ba. Ba ma za a hadu su ba. Rarrashin duniya nan Mami ta yiwa Sadiya amma ta kasa daina kuka daga ƙarshe ma tashi ta yi ta fice daga ɗakin na Mami ta koma nata, ta rufe ƙofa da key ta zube anan bakin ƙofar ta cigaba da rusa kuka, ta dauki lokaci yashe a bakin ƙofa kafin ta koma kan gado. Sai yau tasan zafi da ciwo idan ka rasa abinda kake so ashe duk son da take yiwa Hafiz Sale na karya ne ashe yaya Abba shi ne ainihin wanda zuciyarta ta daɗe da ginawa fada. Sannu a hankali take jin tsanar Aydah yana darsuwa a zuciyata yadda take ji raɗaɗi a cikin zuciyarta komai za ta iya aikatawa matuƙar Abba zai zama mallakinta. AB yana zaune a parlorn sa hannunsa riƙe da mug ɗin coffee saboda yanayi jikinsa yasa yau ya haƙura da zuwa kamfani duk da yasan akwai tarin ayyukan dake jiraye dashi, ba ya jin ƙarfin jikinsa ko kaɗan, tun jiya zuwa yau coffee kawai yake ta durawa cikinsa. A dalilin rasa appetite da ya yi bakinsa har wani ɗaci-ɗaci yake masa coffee kaɗai yake iya sha shima ba don wai yana ji daɗinsa ba. Sai da aka yi kiran sallar azhar sannan ya tashi daga parlorn ya wuce master bedroom ɗinsa ya sako jallabiya ya tafi masallaci, bayan ya dawo daga masallaci ya tsaya bakin gate yana magana da maigadi daidai direban da ya ɗauko Aydah daga school ya yi horn maigadi ya buɗe masa gate Aydah tana fitowa daga mota ta hango AB tsaye, ta ɗaga masa hannu tana dariya shima hannu ya ɗaga mata har ta juya da zimmar ta shiga gida sai kuma ta fasa tana mamaki me ya dawo da yayanta gida yanzu ko kuma dai yau bai je office bane. Sai ta nufi gate wurinsa yana gani ta nufo wurinsa ya yi mata alama da hannu ta wuce ciki gida maƙe kafaɗa ta yi tare da bubbuga ƙafafunta akan interlock girgiza kansa ya yi zuciyarsa tana kisimamai yanzu wannan yarinya da ba a gama raino ba ita ce nan da sati mai zuwa za ta zama matarsa. Wani irin ɓacin rai ya ji yana kanainaye masa zuciya sai da ya ja deep breath kafin ya cira ƙafafuwansa ya fara tafiya ita tana tunkuro shi tana dariya shi kuma yana mata murmushi yaƙe don bai ga laifin da Aydah tai mishi ba da zai sauya mata ko ya tsane ta da alamar bata ma san waina da ake toyawa ba. Da yadda take da ɗan banza surutu nan da tuni ta tambaye shi akan gaskiyar al'amarin. Sadiya tana kwance kamar wacce aka mintsina ta tashi ta nufi window ɗakinta dake facing compound ta buɗe idanuwanta suka sauka akan AB da Aydah yadda taga AB yana yiwa Aydah murmushi ya haddasa wa zuciyarta mugun bugawa har bata san sanda ta dafe ƙirjinta da dukkan hannayenta, idanunta suka firfito wani irin kishi taji ya lulluɓe ta. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/15/2023, 10:35 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWA BOOK*:Jeddah3256 #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye novels 025. A hankali ta sulale ta zauna dabas akan marbles tana jin yadda take fitar da numfashi da wani irin sauri da sauri tamkar numfashin nata zai tsaya ga baki ɗaya. Dunkule hannayenta tayi duka ta shiga gogasu akan marbales ɗin "noo no way!" ta shiga furtawa da dukkan karfinta tamkar mai cutar jinnu haka ta koma cikin ɗakin,watsi ta shiga yi da kayan ɗakin tana sakin wani irin razanannen ihu. Daidai lokacin da AB da Aydah suka shigo cikin parlor dukansu suka kalli junansu kowanne da fuskar mamakin ta ina ihun ke fitowa daidai ita ma lokaci Mami, ta fito daga nata ɗakin jin kamar ihun Sadiya ganin yadda mami ta fito a hargitse yasa AB ya nufi stairs da sassarfa Aydah na biye a bayansa Da dukkan karfinta Mami ta shiga kiran sunan Sadiya tana buga kofar hankali a mugun tashe. Abba ya ƙaraso yana tambayar mami "me ya samu Sadiyar.?" Ita dai Mami duk a ruɗe take, Aydah ma tazo ta tsaya jikin kofar tana kwalawa Sadiya kira da damuwa Mami,ta kalli AB dake tsaye a wurin tana faɗin."Abba ko za ka gwada kiranta?" da haka mami ta bashi wuri yazo ya tsaya gaban kofar yana buga ƙofar Sadiya jin muryarsa yasa ta kalli kofar da sauri."zo ki buɗemin kofa. Abba ya faɗa da sanyin muryarsa da sauri Sadiya ta nufi ƙofa ta cire key. A hankali suke bin ɗakin nata da kallo yadda ta hargitsa shi kayanta dake jere a gaban mirror dressing duk ta farfasa su. Hankali tashe Abba ya kai dubansa kan hannunta dake fitar da jini sosai da sauri ya ƙaraso cikin ɗakin yana riƙe hannun sosai a rikice yake faɗin."kin fara shaye-shaye ne?"You are bleeding for god sake sadiya.!" Rudewar da yayi lokaci ɗaya yasa Sadiya ta rungumesa sosai cikin jikinta yadda ta rikesa sosai yasa yaji yanayinsa ya fara canjawa dan ba irin wannan kalar rungumar suka saba yi masa ba duka kannen nasa yau sai ya jita is different akan wacce suka saba yi masa duk kokarinsa na son fisge Sadiya daga jikinsa ya kasa tamkar ma ta mance da Mami da Aydah a wajen a fusace yace "meye haka sadiya?" Ta kwantar da kanta cikin ƙirjinsa tana shaƙar sanyayye ƙamshin turarensa da take bala'in so tun ba yanzu ba tun yana matsayin yayanta uba ɗaya, murya a harɗe take faɗin."Dan Allah Yayanmu ka yafe min ko zanga daidai a rayuwata tun da wannan abun ya faru tsakani na da kai nayi bankwana da duk wani farin ciki da walwalata. Daddy har yanzun bai sakarmin fuska hakama kai nagane kuskure na wallahi a shirye nake da na koma gidanka muyi zaman aure na har abada. Ɗagota ya yi cikin jikinsa arikice yake faɗin."In dai nine na yafe maki Sadiya. Aydah ta miƙo masa ɗan ƙaramin first aid box shi ya yi mata dressing hannun, Aydah itakuma ta fara tattara ɗakin da Sadiya tagama hargitsa shi har lokacin Sadiya taki barin Abba yabar ɗakin nata dama Mami tun lokacin da taga Sadiya ta rungume Abba, tabar masu ɗakin ganin dai Sadiya ta dawo natsuwarta AB yabar room ɗin ga baki ɗaya ya fice daga part ɗin yana mamakin sudden change ɗinta. Wuraren ƙarfe 3 na rana Mami ta fito da shirin fita da car key a hannunta haka ma Sadiya Aydah kawai ce a parlor tana kallo tana cin abincinta a har yanzu uniform ne ajikinta Ta kalli Sadiya da Mami, lokaci ɗaya ganin kamar fita za su yi da sauri ta cewa Mami "zan bi ku dan Allah. Tun kafin Mamin tayi magana da sauri Sadiya tace "A'ah ki yi zamanki ke da za ki je islamiyya. Lokaci ɗaya Aydah ta haɗe rai tana kallon Mami take faɗin."Yau fa Mami babu abunda zan yi a islamiyya hardar ma sai gobe zan bayar dan Allah Mami na canja kaya na bi ku."Mami tayi gaba tana faɗin."kafin na dawo ki tabbatar kina islamiyya." Daga haka Mami ta juya ta nufi kofa Sadiya tabi bayanta a hankali Aydah ta ture plate ɗin jelop ɗin shinkafar dake gabanta tafi minti biyar a haka kafin ta miƙe ta kai sauran abincin kitchen. Kai tsaye ɗakinta ta wuce tana tsinewa halin yaya Sadiya aranta tasan da bata yi magana ba da tsab Mami za taje da ita. Har AB ya koma part ɗinsa yana mamakin wannan hali da Sadiya ta tsira, tunawa da maganarta akan a shirye take a ƙara mayar da aurensu ba ƙaramin tsaya masa arai ya yi ba da ya tuna haka sai ya ji gabansa ya wani irin faduwa. Gashi har lokacin ya kasa sanar da Rumaisa akan auren da Daddy zai haɗasa da Aydah wannan karon kuma bai san taya zata dauki al'amarin ba. Har yanzu bai cire ransa ba akan mafarki ne yake, so yake kawai ya tashi yaga cewa mafarki ne da gaske. Mami na driving zasu je gidan Aunty Safeena. Sadiya ta kalli Mami cikin fuskar damuwa ta ce."Anya Mami kina ganin zai amince ya mayar dani ɗakina cikin sauki?" "Zai iya amma idan kika ci-gaba da yimasa dabaruku na mata na kissa shi da kansa zai je wa Daddynku da zancen zai mayar dake ya haƙura da auren Aydah. Shiru Sadiya ta yi tana kwantar da kanta cikin seat ɗin mota tana fatar Allah ya karbi addu'arta yasa zancen Mami ya zama gaskiya da tasan sai tafi kowacce macce sa'a a duniya samun mijin aure irin Abba Bashir ai ba ƙaramin sa'a bane a arayuwa, tana jin yadda moment ɗin rungumesa da ta yi yana zauna mata acikin zuciyarta wani irin azababben son yayan nata ke shiga lungu da sako dake cikin zuciyarta. Sosai Aunty Safeena ta yi murnar ganin yayarta ta Sadiya ta zauna cikin kujerun da suka ƙawata parlor tana gaishe da small mum ɗinta. "Aunty Safeena ban ji hayaniyar su Malika ba.? "Sun tafi islamiyya maimoon kuma tana gidan Hajiya. Aunty safeena ta zauna tana kallon Mami "Yaya hop Daddyn Siyama ya amince?" Wani gwaron numfashi Mami ta sauke tana faɗin."ai na faɗa maki da kyar idan zai yarda kin manta taurin kansa, shiyasa ma yanzu na taho da Sadiya ɗin anan mu san wace shawara kuma ya kamata mu yi. Mami ta baiwa Aunty Safeena labarin abunda ya faru tsakanin Abban, da Sadiya Aunty Safeena ta juya kan Sadiya tana faɗin ."kinga kalar taurin kai irin na ubanki abunda ya jawo maki kou?"da yanzu kina gidan Abba hankalinki a kwance sosai naji takaicin raba wannan auren naki da Abba, yanzu tunda kin san ciwon kanki kin dawo right sense ɗinki sai ki yi ƙoƙari cikin kwana shidda kafin Daddyn naku ya kara maimaita wani kuskuren duk yadda za ki yi, ki dakatar da aurensa da Aydah ya zama kece zaki kara zama matarsa a karo na biyu. Da haka suka kai karshen maganar, koda suka koma gida dab da magarib kowanne ya shige ɗakinsa dan yin sallah basu haɗu ba sai bayan ishai da suka fito cin abincin dare. Har lokacin Aydah kumbure-kumburen fuska take ,duk fushinta akan Mami taki fita da ita ne. Da Sadiya taga har an kusa kammala cin abincin na dare bata ga bullowar yayan nasu ba ta zuba masa komai da komai cikin tray ta nufi bangarensa Siyama, dai sai bin yayarta ta kurum take da kallo ganin wai yaya Abba ne, za ta kaiwa abinci yau. Sai da ta yi knocking ƙofar parlor aka bata izinin shiga ta aje tray ta ɗan buɗe kofar sa'annan ta ɗauki tray ta shige cikin parlor yana zaune cikin parlor yana aiki da laptop ɗinsa kallo ɗaya ya yi mata ya ɗauke kai Allah yasa ma jallabiyya ce ajikinsa tun da ya dawo sallar ishaai bai cire ba dan yasan Aydah za ta iya fado masa ko wane lokaci. Bin Sadiya kawai yake da kallo har ta aje tray ɗin da ta shigo dashi akan center table ga mamakin sa Sadiya ta yiwa kanta mazauni gaf da shi tana dan leƙa cikin laptop ɗin cike da kulawa ta ce "yayanmu aiki kake ashe? kowa ya fito cin abincin dare banda kai shiyasa na ɗibar maka na kawo ma. "Thanks! kawai ya iya faɗa mata ya mayar da hankalinsa kan laptop ɗinsa ya ci-gaba da aiki cikin kwarewa ita dai Sadiya tallabe cheeks ɗinta tayi da hannuwanta duka biyu tana kallon yadda yake aiki cikin kwarewa, a gefe ɗaya kuma ƙamshin turaren Sadiyar ya dami AB sosai. Sai Allah-Allah kawai yake ta tafi har kusan minti goma yaga batada alamar zata tafi ya ture laptop ɗin gabansa yana kallonta yana faɗin."ki tafi sai da safe aiki nake. Yadda ya faɗa babu alamar wasa saman fuskarsa yasa gabanta ya shiga faɗuwa ,cikin sanyin murya da kwantar da kai take faɗin."Yaya magana nakeso muyi shiyasa nakeso na jiraka har ka gama aiki naka muyi maganar ta yadda bazan takuraka ba." Wani numfashi ya sauke cike da gajiya a muryarsa yake faɗin "ina jinki" har ta buɗe baki za tayi magana taji ana knocking ƙofar parlor lokaci ɗaya mood ɗin Sadiya ya canja. kai tsaye AB ya bada izinin shigowa ,ran Sadiya ya yi mummunan ɓaci ganin wacce ta turo ƙofar sanye take cikin rigar bacci wacce da kaɗan ta wuce gwiwarta sai hular net da ta saka akanta ,tunda ta shigo take kallon Sadiya da yayanta. Ta cire takalmin ta ƙaraso cikin parlor tana kallon Sadiya take faɗin."Yaya Sadiya yaci abincin?" banza Sadiya ta yi mata karshema miƙewa tayi tsaye tabar parlorn a ɓoye AB ya saki wata irin ajiyar zuciya harga Allah ya ji daɗin zuwan Aydah dan da bai san yadda zai yi da Sadiya ba. Aydah ta nufi wurin tray ɗin tana buɗe abincin da Sadiya ta zubo masa ta haɗe rai tana kallon AB da ya ci-gaba da aikinsa a laptop "yayanmu ai ba kaci komai ba fa. "Idan na gama zanci ya faɗa batare da ya kara kallonta ba. jin haka yasa taje ta zauna kusa dashi ta dauki dayar wayarsa tana game, knocking suka ji a ƙofar shigowa sai da ya bada izini Siyama ta shigo Parlor da dogon hijab har kasa dan har tayi shirin kwanciyya ta saka kayan bacci Mami ta tasota wai taje ta kira Aydah a part ɗin Yayansu Allah ya gani yau agajiye ta dawo makaranta bacci ne sosai a idanunta ,a bakin ƙofa Siyama ta tsaya ta gaishe da AB ya amsa yana kallonta kafin ta mayar da kallonta kan Aydah tana faɗin."ki je Mami na nemanki daga haka Siyama ta yiwa yayan nasu sai da safe ta wucewarta ,Aydah ta miƙe tsaye har lokacin wayar AB na hannunta take faɗin."yayanmu na je da wayarka dan Allah da safe kafin na tafi school sai na shigo na kawo maka" Hannu ya miƙa mata alamar ta basa wayar, miƙa masa tayi tana wani turo baki haka ta fice daga part ɗin nasa kamar zata tashi sama kallo ya bita dashi yana sakin murmushi a hankali zuwa ya yi ya sakawa ƙofarsa key, a tsaye tasamu Mami na jiranta kallo ɗaya ta yiwa fuskar Mami ta ji gabanta yayi mummunan faɗuwa tsayawa tayi batare da ta ƙaraso ba A tsawace Mami ke faɗin."sai ki ƙaraso nan! jiki na rawa Aydah ta ƙaraso Mami ta turata cikin ɗaki ta rufe ƙofa cikin masifa Mami take faɗin "Na lura kwanan nan kina wani shigewa Abba, naga alamar bakida hankali ko kaɗan kalli shigar da kika je masa dashi tarbiyyar da na baki kenan Zulaiha?" Mami ta faɗa a tsawace tana kiran sunanta na ainihi da sauri Aydah ta shiga girgiza kai hawaye har sun taru a idonta "uban me kike zuwa yi part ɗinsa da dare?" daga yau idan na ƙara ganin ƙafarki a part ɗin Abba wallahi-tallahi sai na karyaki a gidan nan, na riga da na faɗamaki bani na haifi Abba ba ba daddynku ya haifesa ba so ba muharraminki bane da za ki rika shige masa koda yaushe. Haka kika ga yayunki nayi masa?" Hawaye na sauka a idon Aydah take girgiza kanta "Na riga na faɗa maki duk namijin daba muharraminka ba ka yadda ko hannunka ya riƙa za ki iya yin ciki ko so kike kiyi cikin?" nan ma Aydah ta shiga girgiza kai hawayen idonta suka kasa tsayawa. "To ki shiga hankalinki a gidan nan wuce ki je ki kwanta wawuya kawai...!" da haka ta fice daga ɗakin na Mami sai lokacin ta ji kukan gaske na taho mata ita ta kasa fahimtar duka maganganun Mami bata san me Mami ke nufi ba meyasa ɗazun da yaya Sadiya ta rungumesa ba ta yi mata faɗa ba sai ita.? haka ta kwanta ta rika rusa kuka tamkar wacce aka yankawa naman jiki. #Love story2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye Novels #kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/17/2023, 9:48 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*:Jeddah3256 Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 026. Kukan da Aydah take yi ya haifar mata da headache gashi ta kasa bacci sai wurare ƙarfe 3:00am ta sami bacci, shiyasa duk knocking ɗin da Siyama take mata da asuba tashi ta yi sallah ba ta ji ba. Shiru-shiru har lokaci tafiyar ta school ya wuce bata tashi ba misali ƙarfe 8:00am Siyama da Sadiya sune zaune a dining Area kowacce ta yi shirin tafiya school kuma dukkanninsu lectures ɗin safe suke da. Siyama ce ta kalli Sadiya ta ce "Yaya Sadiya har yanzu Aydah fa bata fito ba kuma a ka'idar tafiyarta school 7:30am ne gashi har 8:00 ya yi. "Mtss! Da kike gayamin me kike so nayi mata? Cike da mamaki Siyama take kallon Sadiya gani yadda yanayin ta ya canza nan take, gudun kada abin ya koma musu faɗa sai kawai cikin sanyi murya Siyama ta furta "Babu ni da nake da abun yi mata bari na je na duba ta ko ba komai she's my little sister and I love her the way she is idan ma wani abu tai miki kike nuna wannan bad attitude akanta idan Aydah ce kin yi a banza don ba fahimta za ta yi ba. Ba kuma shi zai hana gobe ta sake yi miki laifin da ta yi miki ba watakila ma yafi na farko. Siyama tana ƙarashe magana ta miƙe batare da ta tsaya jin kalar amsar da Sadiyar za ta bata ba ta haura bene yayin da Sadiya ta bi ta da faɗar "Idan kuwa ta ci-gaba da shige min hanci da kududduni dukan masifa zan mata a gidanan ba abinda za a yi wallahi. Ai duk ku ke ɓata ta tana yiwa mutane sangarta banza da wofi ni karyata zan yi. Sadiya tana cikin wannan mita Mami ta sauko ƙasa tana tambayar ita da wa da sassafe nan? Kai tsaye ta bata labari abunda ya faru guntun tsaki Mami ta ja can ƙasan zuciyarta cike yake da fargaba da alama Aydah za ta bata matsala, sai yanzu take regretting barin shaƙuwa mai ƙarfi ta shiga tsakaninta da Abba. Yadda ta shaƙuwa dashi ko ita da ta haife ta bata shaƙu da ita haka ba, tun da ta haife ta kulawa da ita kacokan ya koma kan Abba iyakancinta da ita idan ta yi kuka ya kawo ta ta bata nono, sannu-sannu ma sai ta daina shan nono sai madara hakan yasa Abba ya tattare kayanta ta koma part ɗinsa hatta da wankin kayanta shi ke mata ya goge ya shirya mata su a gun da ya ware mata a closet ɗinsa. Mami tana cikin wannan tunani Abba ya shigo cikin brown suit ɗin da suka yi masifar yi masa kyau sai dai ya ɗan yi rama a fuska a dalili rashin lafiyar da ya yi ga kuma damuwar da kullum ƙara yawa take masa ya rasa tudun dafawa. "Ina kwana Mami?" Ya faɗa sa'ili da ya iso dab da ita yana mai ɗan runsuna wa. "Lafiya ƙalau! Mami ta amsa fuskarta ba yabo ba fallasa yayin da AB ya ja kujera ya zauna batare da ya lura da yanayi da Mami ta amsa masa gaisuwa ba. "Ina kwana yayanmu?" Sadiya ta faɗa tana fari da idanuwa "lafiya! Ya Amsa mata a takaice ta taso da sauri ta zari plate ta yi masa serving har ta ajiye masa plate ɗin a gabansa bai ɗago ya kalleta ba hankalinsa naga wayarsa da yake operating. Siyama ta ɗinga yiwa Aydah heavy knock can cikin bacci Aydah ta ji knocking ɗin sannu a hankali ta ɗan buɗe idanuwanta kanta ya yi mata mummunan sarawa tai sauri dafe forhead ɗinta, ta ɗauki daƙiƙu a haka kafin ta ƙarashe ware idanunta dukka, cike da kasala ta tashi zaune still hannunta na kan goshinta ta ya ye duvet ɗin jikinta tare da ture shi gefe ɗaya ta zura ƙafafuwanta ƙasa ta sauka daga gadon, tana tafe dizzy na ɗibarta a haka ta isa ga ƙofar ta cire key "Subhanalillah! Daman ba ki da lafiya Aydah shi ne kika kunshe a ɗaki batare da kin faɗawa kowa ba? So kike ki kashe kanki ko me?" Zazzafan numfashi Aydah ta fesar wanda iskarsa ya sauka a fuskar Siyama da sauri ta kama ta suka koma ciki ɗakin ta zaunar da Aydah a gefen gado sannan ta ce "wait for me here while I make warm water for you to take a bath za ki ji ƙarfin jikinki. Aydah ta gyaɗa kai Siyama ta wuce bathroom ta haɗa mata ruwan tana nan har Aydah ta fito daga wanka sosai kuwa ta ji daɗin jikin nata sai dai still kanta bai daina ciwo ba wannan kuma ya danganta ne da uban kukan da ta ci a daren jiya. Ta goge jikinta da hand towel as usual bata shafa mai ba roll on da turare kaɗai ta shafa ta zura plain cotton gown bata saka hula ba, ta kalli Siyama dake kitsa mata gadonta cikin sanyi murya ta furta "Nagode Yaya Siyam! Harararta kawai Siyama ta yi ta kama hannunta "mu je ki yi breakfast kin ga saboda ke har na yi latti. Da sauri Aydah ta rungume Siyama tana faɗin "I love you Yaya Siyama! "Uhm! Kafin zuwa anjima ki ce you hate me ba. 'Yar dariya Aydah ta yi cikin shagwaɓe murya ta ce "Kai yaya Siyam. "Kai Aydah! Siyama ta faɗa tana kwaikwayar muryarta sai kawai suka yi dariya footsteps ɗinsu yasa Sadiya ta ɗaga kai ta kalle su gani Aydah ya ɓata mata mood ɗinta, har sai da ta ja guntun tsaki sai a kunne AB ya kalleta a fakaice sai kuma ya maida ganinsa akan abincinsa. Mami da ke zaune a parlor tana waya da ƙawarta Hajiya Zeena ta yada ganinta akan jikin Aydah tana ganinta sanye da personal clothe ba da school uniform ba, ta ɓata fuska ta ba wa Hajiya Zeena uzurinta tare da faɗin za ta kirata later on. Kusan a tare Siyama da Aydah suka gaida yayan nasu cike da kulawa ya dire spoon ɗin hannunsa ya ɗago yana kallon Aydah ganinta sanye cikin kayan gida yasa shi ɗan zare idonsa "Baby me ya faru na ganki sanye da kayan gida school ɗin fa?" Da wani irin takaici Sadiya take kallon AB musamman yanda ya yi magana with so much caring ga sexy eyes ɗinsa dukka akan Aydah har wani kalan tuƙuƙi take ji yana taso mata a zuciya. "Yaya Abba I'm sick. Aydah ta faɗa cikin shagwaɓaɓbiyar muryarta har wani langwaɓar da kai take yi. "Subhanalillah! Me ke damunki?" "Headache and dizzy. "Zo nan ki zauna kina jin jiri shi ne za ki tsaya salon ya yarsar dake na shiga uku. Ba wai iya Sadiya ba hatta Mami sai da ta ɗan zare idonta sai kuma ta tuna da irin yanda Abba ɗin ya damu da Aydah indai akanta ne fiye da hakan ma zai iya. Aydah ta kalli hannunsa fari sol da ya miƙa mata da nufi ta ɗora nata hannu kamar wacce ta tsorota da gani hannun nasa tai sauri kallon cikin parlor gun da Mami take wani mugun kallo Mami ta wulga mata tai sauri janye idanunta daga kan Mamin ɗin. Direction ɗin da take kallo AB ya bi da idanunsa duk abinda Mami tai yi mata akan idonsa sai kawai ya yi murmushin takaici saboda ba ƙaramin zafi ya ji ba aganinsa koda Daddy bai bijiro da zance aure tsakaninsa da Aydah ba ita ɗin tamkar wani tsagi ne na jikinsa, ko zai cutar da kowa a duniya nan ban da Aydah. Aydah ta zagaya ta zauna kujerar dake kusa dashi tasa ƙafarta ta ɗan tabo ƙafarsa hakan yasa ya kalle ta tai ƙasa da murya "Yaya Abba ka yi haƙuri da naki kama hannunka Mami ce ke hararata. Murmushi ne ya subuce mishi a zuciyarsa yana ayyana idan ma Mami ta faɗi wani abu akansa, bakin Aydah ba zai shiru ba tsaf za ta kwashe ta faɗa masa. Siyama ta kalli Sadiya ta ce "Yaya Sadiya tashi mu tafi ko kin fasa zuwa school ɗin ne? naga kin saka wa da ƙanwa gaba kina kallo sai ka ce yau kika fara ganin su. Rai ɓace Sadiya ta tashi ta ture kujerar da tashi akai da ƙarfi a fusace ta wuce ɗakinta ta dauko handbag da takardun ta suka fi ce. AB bai damu da Kasancewar Mami a parlor ba ya zuba wa Aydah abinci ta ci sai da ya bata magani tasha ya umurce da ta je ta kwanta sannan ya yiwa Mami sallama, zuciyar Mami na tafarfasa ta ce dashi "idan ka dawo ka same ni akwai maganar da za mu tattauna. "Okay! Ita ce kalma da kurum AB ya iya furtawa Mami ya fi ce abinsa saboda ya gama fahimtar inda kurman allonta ya dosa. *MASARAUTAR KUDU* Jakadiyar Kilishi ce ta fito daga ɓangaren Kilishi sai da ta duba lugun da saƙo na farfajiyar gidan bata ga idanuwa kowa akanta ba. Dukka bayi da fadawa dake farfajiyar sabgar gabansu suke yi, sai kawai ta yi wuff ta bi ta ƙofar baya da ba kasafai ake amfani da ita a gidan na sarauta ba sai in za a gudanar da wani al'amari dake buƙatar sirri. Da fitar ta ta hango motar Ciroma a gefen hanya da saurin gaske ta isa ga motar wacce tun kafin ta ƙaraso aka bude mata seat ɗin baya, jikinta na rawa ta faɗa cikin motar ta maida murfi ta rufe sai da Ciroma ya ja motar kafin Fulani Umaima ta juya ta kalli Jakadiya tana faɗin "Allah yasa ba wanda ya gamki Jakadiya sanda kike tahowa kinsan al'amari nan yana bukatar zallan sirri?" "Allah ya taimake ki ina taka tsantsan da dukkan abinda ya shafe ku da izinin mai sammai bakwai ba wanda ya ganni. "To madallah. "Jakadiya yanzu ina muka nufa?" Tambayar da Ciroma ya jefo mata kenan. "Ranka ya dade birnin gwari. "Birnin gwari kuma Jakadiya?" "Kwarai kuwa Allah ya ƙara ma lafiya muddin muna so aiki sha yanzu magani take dole sai mun je birnin gwari wurin boka mai Gunduleliya, domin shine ainihin bokan da ke yiwa uwargijiyata Kilishi aiki kuma tun da muke dashi bai taɓa aiki bai ci ba shiyasa uwargijiyata ta riƙe shi tamau ya zama abin dogaro da tinƙaho ta(wa'iyazubillah Allah ya tsare mana imanin mu) "To amma Jakadiya kina gani ba Zai fallasa asirin mu a wurin Umma ba kasancewar sa bokanta?" "Ranka ya dade mai Gunduleliya hatsabibin boka ne mai abin mamaki shi a tsarinsa ba abinda ya fi so yake kuma maraba dashi irin butulci da cin amana, ai na gayawa Fulani Umaima sai da na fara zuwa na nemo izzin zuwanku a wurinsa kuma nan take ya amince har ya yi farin ciki marar iyaka. "Idan kuwa haka ne Jakadiya mai Gunduleliya shine bangon da zan jingina bayana akansa shine mutumin da zai tsallakar dani ramin da Umma ta haƙa min na kasa tsallake wa shi ne zai kaini da mattakalar nasara. "Wannan haka yake ranka ya dade. Jakadiya ta tabbatar mishi da hasashen sa. Tafiya ce wacce ta ɗauke su tsawon kilomita 252.1km bima'ana 3 hours 33 minutes duk irin mugun gudu da Ciroma ke shararrawa dajin Allah ne falau suka dinga ɗiba har suka iso wata duhu mai sarƙaƙƙiya anan Jakadiya ta umarce su da su yi parking domin iya nan mota take iya zuwa suka ci-gaba da tafiya a ƙafa ga Fulani Umaima da kiba ba ta wasa ba sai nishi da haki take yi daga ƙarshe sai Ciroma ne ya kama ta rabin nauyinta yana ga kafaɗarsa suna tafe yana ƙorafi wata tafiya shi kadai zai zo ba za ta sake biyo shi ba. Ashe tsugunne bata ƙare musu ba saboda ɗan uban Kogi da suka cimma wanda sai sun shiga kwalele an tsallakar dasu, zuwa lokaci ita kanta Fulani Umaima ta gama kisimawa ranta babu uban da zai sake dawowa da ita wannan baƙin daji. Ana tsallakar dasu ba su wuce yi tafiyar mintuna 20 ba suka fara hango wani tafkeken fili mai ɗauke da farin yashi sol har wani ɗaukar ido yake lokaci da suka fara tattaki akansa sai ƙafafuwansu sun lotse a cikinsa kamar masu tafiya cikin ruwa. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo [12/17/2023, 9:57 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*:Jeddah3256 Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 027. Suna fita daga cikin yashi ɗin suka cimma wani gidan kara mai ɗauke da bukkoki uku ga baki ɗaya jikin karan a bi shi da kawuna dabbobin daji a mabanbanta wurare daban-daban ga wani arne wari bunsurai dake tashi Fulani Umaima ta toshe hancinta, Allah ya sanar mata ko kaɗan bata so wari awakai yana mugun ɗaga mata hankali. Can idanuwanta suka yi mata tozali da wasu tirka-tirka bunsurai sun kai su goma kowanne gemin shi na ja da ƙasa ga su da wanɗansu dakwa-dakwan idanuwa. Yadda taga idanuwan bunsurai kafe akanta ya haifar mata da matsanancin faɗuwar gaba da sauri ta kauda fuskarta wani basamuden ƙato ne baƙi wulik dashi ya nufo su yana sanye da ɗan wani ja da baƙin walki ɗaure da ƙugunsa jikinsa duk maiƙo yana tafe uban tumbin sa na rawa sai kace 'ya'ya arba'in ne a cikin nasa mummuna baƙar fuskarsa a haɗe cikin muryarsa mai kama da kukan kwaɗi yake faɗin "Shugabana mai Gundulelliya yana muku barka da isowa daularsa, daular dake cike da biyan buƙata kafin kun isa zuwa gare shi ka'idar wannan daula sai kun fara ciyar da hidimansa abinci, ga kwado can kuna gani kowanne ku ya ɗebo ciyawa ku ciyar dasu cikin ƙauna. Wani kalan zare idanuwa Fulani Umaima ta yi cikin kaɗuwa take kallonsa kana ta haɗiye wasu busassu miyau cike da tausayin kanta ta yada ganinta akan bunsurai nan masu abin mamaki, bata ankara ba ta ji Ciroma ya cukume hannunta daman can yasanta da tsoron awakai ballantana waɗannan da suka sha bambanta da ire-iren wanda ta saba gani, cike da tsoro ta ɗebe ciyawa ta miƙa musu atare suka farmaki ciyawar tamkar za su haɗa da hannunta, bayan sun gama cinyar dasu kana suka wuce zuwa ainihin bukkar da mai Gundulelliya yake. Suna arba dashi hatta da Ciroma sai da gabansa ya faɗi saboda wasu sassan jikinsa dukka babu su ƙafarsa ɗaya a gundule take haka ma kunnensa guda, dukka yatsun hannunsa goma babu ko ɗaya rabin leɓɓenshi ya cire, haka zalika hancinsa astagfirllah ga baki ɗaya bashi da kyau gani siffarsa ta tashi daga ta ɗan adam zuwa wani mashahurin dodo. Tsabar hatsabibbancin sa zigidir yake sai wani ɗan ganye da ya ɗaura a ƙugunsa wanda bai kare komai na daga tsiraici sa ba, yana zaune gaban kaskon wuta dake ci bal-bal baƙin hayaƙi na fita daga cikin wutar. "Ciroma barka da zuwa. "Barka dai. Ciroma ya faɗa cikin harɗewa harshe. "Ga wuri ku zauna. Duk wannan maganar da yake yi idanunsa suna rufe ruff har sai da su Ciroma suka zauna kana ya buɗe idanunsa wanda gara ma ya bar su a rufe su saboda irin abin razanarwa dake cikinsu. "Ciroma ba za ka taɓa mulkin koda sabon birnin kudu ne ballantana karagar mulkin kudu har ka mutu ka komawa mahaliccinka ba za ka taɓa hawanta ba. Wani irin gumi ne ya karyo wa Ciroma a fuskarsa yasa gefen babbar rigar jikinsa ya goge fuskar tasa cikin kaɗuwa ya kalli mai Gundulelliya muryarsa tana rawa yake faɗin "Yanzu babu wani taimakon da za a iya yi min?" Mai Gundulelliya ya sheƙe da dariya marar daɗi tsawon lokaci ya ɗauka yana sheƙa dariya kafin ya tsaya kaman anyi ruwan sama an dauke ya wani kalan turɓune mummunar fuskarsa ya ce "Ai tun da ka zo nan Ciroma buƙatar ka ta gama biya lallai za ka yi mulkin kudu za ka shimfiɗa mulki na zalunci amma kasani taurarinka basu da haske ko kaɗan wanda hakan yana nufi akwai wani kurman allo a tattare da kai. Wani kalan washe haƙora Ciroma ya yi shi ko kaɗan bai damu da zancen ƙarshe da mai Gundulelliya ya yi masa, a ganinsa da zarar ya sami biyan buƙata ya zama sarkin Kudu bashi da wata damuwa a doron duniya. Yayin da mai Gundulelliya ya ɗebo wasu fararen ruwa kal a wata kwarya suna tafarfasa ya zuba ciki wata batta da aka yi ta da fatar damisa. "Wannan ruwa shi za ka dinga ciyar da sarki Mahmood har na tsawon kwana bakwai idan bai tsallake rana ko ɗaya ba yana shan su tabbas zai mutu idan ya tsallake koda kwana ɗaya ne ba su shiga cikinsa ba zai kwanta matsananciyar jinya, kai kuma za ka hau karagar mulkin kudu. Godiya Ciroma ya shiga yi kana ya fito da damin kuɗi ya ajiye a gaban bokan sannan suka yi masa sallama. Cike da farin ciki suka koma masarautar kudu. *MOONLIGHT AUTOMOBILE INDUSTRY KANO* AB yana zaune acikin katafaren office ɗinsa ga tulin files a gabansa ya kasa duba ko ɗaya ba sosai damuwa ta yi masa yawa. Yanata ƙoƙarin ya gane me Mami take nufi da akan alaƙarsa da Aydah duk iya tunaninsa ya kasa fahimtar kurman Allon na Mami. Gefe ɗaya ga Sadiya da yanzu ke rawar ƙafa akansa ko kaɗan bayason yadda take wani shisshige masa. Idan kuma ya tuna aurensa da Aydah nan da kwanakin biyar masu zuwa sai ya ji damuwarsa ta ƙara yawa. ƙarfe biyu na rana kiran Mami ya shigo a wayarsa har lokacin yana zaune cikin office ɗin nan da can bai gusa ba hatta da sallar azhar a office ɗin ya yi ta. Bai kawo komai aransa ba daga kiran nata da sallama ya amsa wayar tare da gaisheta da respect ta amsa tana faɗin."idan baka da aiki sosai a office ka je ka dauko Sadiya a makaranta ta kira ni akan na yiwa driver magana ya je ya daukota ni kuma na aiki driver gidan ƙawata Hajiya Zeena. amsawa Mami kurum ya yi da to ya fi minti goma sha biyar kafin ya fice daga office ɗin yana rike da car key a hannunsa sai da ya karaso faculty ɗin su Sadiya sannan ya kirata a waya. Ba jimawa ta ƙaraso a hankali take takowa cikin wata irin izza da yanga tana ta sakawa Mami da albarka na wannan dabarar da ta yi duk dan tasa ya fasa auren Aydah. Buɗe gaban motar ta yi ta shige ta rufo kofar wata irin natsuwa ta ji yana saukar mata musamman da ta ji ƙamshinsa da ya gama cika motar ya haɗe da sanyi AC. Ta kallesa ido cikin ido ta wani rausayar da kai gefe ɗaya ta ce "Barka da rana yayanmu. Babu yabo babu fallasa ya yiwa motar key da wani irin gudu ya ja ta zuciyarsa banda tafarfasa babu abunda take duk wannan bai damu Sadiya ba tun da tana tare dashi a gefe tasan wuyarta ta koma gidansa ya shiga hannunta sai yadda ta juyasa duk wannan zafin kan nashi da ɗaɗɗaure fuska da yake mata zai kau. Yana cikin wannan yanayin kiran Rumaisa ya shigo a wayarsa ɗaga kiran yayi tare da sakawa a speaker cikin sanyin murya da shagwaba Rumaisa ke faɗin."habeebi yau za ka zo ɗin? pls karkace nooo wallahi ba zan iya jurewa ba kwana nawa ban ganka ba kuma ka ƙi bani damar da zan zo na ganka. Ta ƙarasa maganar da salon shagwaɓar dake kara narke da zuciyar AB bai san lokacin da ya saki wani irin murmushi rabin damuwar da ya ji ya shiga sai ya ji ta yaye ina driving other half idan na sauka zan kiraki. "Kasan ina sonka kou?"cikin wata irin natsuwa ya ce."na sani. "Ka kula da kanka. Ta faɗa cike da kulawa a muryarta."Insha Allah! Ya faɗa yana katse kiran, a lokacin kar kuso ku hango Sadiya yadda fuskarta ta kumbura idanunta suka Kada suka canja kala lokaci ɗaya. Watau ita haukan banza take ita da Mami akwai ƙura a kasa har yanzu yaya Abba ,yana tareda Rumaisa kenan?"kuma tasan tsananin soyayyar dake tsakanin yayan nata da Rumaisa, ko kaɗan Abba bai lura da yanayin da Sadiyar ta shiga ba ƙofar gida taga ya yi parking batare da ya kalleta ba yana jiran kawai ta fitar masa a mota ya kama gabansa. Ita ma tana ganin haka tasan ba shiga zai yi buɗe marfin motar ta yi ta fice daga motar. Mami kawai take son gani a wannan lokaci idan kuma ta tuna yadda yaya Abba ,yake yiwa Rumaisa magana cikin natsuwa sai ta tambaye kanta dama ashe haka ya iya soyayya da tattalin macce har haka duk wannan uban izza nasa da shan ƙamshin nasa. Wani irin fitinannen kishin Rumaisa yazo ya danne mata zuciya fiye da wanda take ji akan Aydah. Babu ko sallama haka ta faɗa ɗakin Mami tana kiranta da dukkan ƙarfinta tana jan numfashi tana fitarwa Mami dake tsaye gefen wardrobe tana gyara kayanta ta bi Sadiya da kallo yadda ta shigo mata agigice."ke Lafiya?" Wani zazzafan numfashi Sadiya ta shiga ja tana fitarwa ta yi hakan kusan sau ukku kafin ta samu wasu irin warm tear's suka dinga fitowa acikin idanunta."ke Lafiya me Abban ya yi maki kuma?" Mami ta faɗa da rawar murya tana kallon Sadiya da take sharar hawaye ta dawo abin tausayi lokaci ɗaya. "Mami ashe yaya Abba har yanzu yana tare da Rumaisan nan da yabi ya nacewa wacce aka wulaƙanta shi akanta?" "Mami muna hanya ta kirasa baki ga yadda take lankwasa masa murya ba shi kuma sai wani tarairayarta yake. Mami idan Yaya Abba,ya cigaba da kula Rumaisa zuciyata bugawa zata yi nayi kuskure Mami laifina ne laifina ne wallahi. Ta faɗa wani irin kuka mai haɗe da kishi na kwace mata "Da yanzu ina gidan yaya Abba, hankalina kwance mai yasa wannan kalar ƙaddarar zata sameni?" Ta faɗa muryarta na karyewa a hankali. Tsaki Mami tayi tana faɗin."an faɗa miki ko mahaifinki ya yarda Abba ya nemi auren yarinyar nan a karo na biyu ni zan yadda ne?"ai ta riga da ta rasa shi har abada.!"idan haka bata kasance ba kice ba Mariya bane suna na. So kima daina wannan banzan tunanin ina nan ina jiransa zan basa umurni nima kamar yadda mahaifinku ya basa, zan basa umurnin ya janye auren Aydah a dawo da auren akanki ,cikin rawar murya Sadiya ke faɗin."to Mami idan kuma yaki amincewa fa?"kin san irin biyayyar da yake yiwa daddy fa. Wani kallo Mami ta yiwa Sadiya ganin haka Sadiya ta ɗauki jakarta da mayafinta ta nufi nata ɗakin. Sai bayan magarib ya hauro upstairs ɗakin Aydah ya fara leƙawa tana kwance akan rug da tulin text books a gabanta ɗagowa ta yi tana kallonsa, cikin sanyin murya ta gaishesa kallonta kawai yake yana mamakin yadda tayi sanyi har haka da adane da ta gansa zata bar duk abunda take ta zo ta kama hannunsa ko ta shige jikinsa."har yanzu ciwon kan ne?"ta girgiza kai tana faɗin ."yayi sauki kallonta ya yi na kusan sakan biyu kafin ya juya yabar kofar ɗakin da ido ta bisa. Knocking ya yi a ƙofar ɗakin Mami sai da ta basa izinin shiga sa'annan ya shiga ya samu Mami zaune agefen bed tana danna wayarta Ta amsa sallamarsa ta dauke kanta shigowa ya yi cikin ɗakin ya zauna akan soofa ya saukar da kansa ƙasa yana son jin Mami me za tace gyaran murya ta yi kafin ta aje wayar hannunta."kana jina Abba?" Ɗan ɗagowa ya yi ya kalli Mami kafin yace "I' ina jinki Mami . "Yaushe ka fara take maganar iyayenka?" Mamakin furucin Mami yake har ya kasa cewa komai kurum ya kalleta ya sadda kai bai daice komai ba dan bai san me tambayarta ke nufi ba "Dama har yanzu kana tare da yarinyar nan Rumaisa mu ka mayar yan iska kenan." Wannan karon Mami ta faɗa da ɓacin rai cikin muryarta. "ku yi haƙuri Mami tun lokaci ta rika bina tana bani haƙuri kuma wallahi ba laifinta bane laifin mahaifinta ne. Da baki buɗe Mami ke kallon Abba tana mamakin yaushe har ya yi baki haka yana kare budurwarsa agabanta. "A haka kake so a kai maka Aydah kana cigaba da kula tsohuwar budurwarka? Ya Rasa me zai ce da Mami wani ƙwafa Mami ta yi tana faɗin."dama kiran da na yi maka ka je ka samu Daddynku ka faɗa masa ka amince a mayar da aurenka da Sadiya auren naka ma da sadiya zaifi akan Aydah. Tun da ni na basa shawara yaki dauka kai sai ka je ka gwada taka sa'ar. kallo Mami kawai yake rasa ma abunda zai ce mata ya yi jin yayi shiru Mami ta ce "Ko hakan bai yi maka ba Abba na ga ba kace komai ba?" da sauri AB ya girgiza kansa yana faɗin."shikenan Mami I will talk to him."Mami ta tabe baki tana faɗin."better!"za ka iya tafiya. jiki a sabule ya baro ɗakin Mami ko gabansa baya gani a wannan lokacin maganganun Mami ,yake ta faman juyawa aransa ya ma kasa fahimtar me wannan kurman Allon nata ke nufi shi dai yasan har abada ba zai yadda ya kara auren Sadiya ba. koda Daddy ya yarda shi ba zai yi shiru ba a wannan lokacin gara ya auri Aydah da dai ya auri Sadiya yarinyar da ta yi yunƙuri raba sa da rayuwarsa me zai yi da ita daman kuma yasan shine guarding angel ɗin Aydah ga baki ɗaya Mami ta bata masa mood ɗin fita ya je yaga Rumaisa ko kaɗan baya son Rumaisa ta fahimci damuwar da yake ciki har aka kira ishaai yana jin ana sallah a masallaci ya kasa zuwa. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #team tagwaye novels #Kurmam Allo. [12/18/2023, 10:15 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*: Jeddah 3256 Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 028. AB da yaga wanki hula zai kaishi dare ga rashin mafita sannan kuma ga na sallah ya tashi adaddafe ya shiga bathroom ɗinsa ya dauro alwala ya fita masallaci duk da yana da tabbacin zuwa yanzu an dade da gama sallah. Kawai dai ba zai iya sallah a cikin gida ba, bayan ya gama sallah ya nufo gida har zuwa lokacin ya kasa tsayar da zuciyarsa a wuri ɗaya sai ya ji kamar ya amince da auren Sadiya sai kuma wata zuciya ta kwaɓe shi, ta kisimamai gara auren Aydah sau million da Sadiya idan ya aure Aydah da matuƙar wahala ya sami matsala daga gare ta. Hakan ma zai bashi damar sake neman the love of his life Rumaisa zai fake da ƙanƙatar Aydah ya aure zaɓin zuciyarsa. Da wannan tunani ya tsaya bakin gate wurin Balmo maigadi ya karbi waɗansu takardu da ɗazu aka aiko masa dasu ya ce aba wa Balmo ɗin ya ajiye masa. karɓa takardun kawai ya yi ya nufi bangaren Daddy, domin akwai tattaunawar data shafi kamfani za su yi tun sanda AB ya shigo har ya zauna idanuwan Daddy suna zube akansa. Bayan ya gaida Daddy ya nemi kasa rug carpet ya zauna tare da miƙa masa takardun hannunsa "Daddy idan ka sami lokaci ka duba wannan yarjejeniyar kasuwanci ne da kamfanin kim's ke son ƙullawa damu har sun nemi zama na musamman dani a kamfaninsu dake Lagos ina tunani gobe ko jibi zan tafi Lagos ɗin. Har AB ya kai ƙarshen maganarsa Daddy yana kallonsa sai da Daddy ya sauke naunnayar ajiyar zuciya kafin ya furta "Bashir me ke damunka?" ga baki ɗaya ka bi ka rame Bashir ina hango tsanani damuwa cikin idanuwanka idan ka ɓoye min wa kake dashi da yafi ni ko kana da wanda ya fi ni Bashir?" AB ya girgiza kansa duk sai ya ji zuciyarsa babu daɗi, tun da har ya ji Daddy ya kira sunansa na aihini wanda ba zai iya tuna when last da Daddy ya kira sa dashi ba. Cikin sanyi murya tare da sadda kai ƙasa AB yake faɗin "Daddy dangane da zance.... "Auren ka da zan yi maka ko Abba? Daddy ya yi sauri katse masa hanzari "Eh! Daddy! AB ya furta da sanyayyar muryarsa mai cike da respect. "Abba bakason Aydah ne?" "A'ah! Daddy ba haka nake nufi ba ai Aydah ƙanwata ce ba zan taɓa ƙin ta ba. "To idan ba sonta ne ba za ka yi ba Abba menene ya haddasa maka shiga damuwa? AB ya yi shiru yana wassafa ta yadda zai furtawa Daddy zance a mayar da aurensa da Sadiya, ganin shiru nasa yana neman ya yi yawa yasa Daddy ya dafa kafaɗarsa cikin kwatar da murya yake faɗin "Abba ni fa mahaifinka ne babu zance ɓoye-ɓoye atsakanin mu, ka buɗe baki ka faɗamin hakikanin gaskiyar abunda yake ranka. Karka damu zan fahimci ka. Wani kalan numfashi AB ya fesar gabansa na wani irin bugawa ya ce "Daddy na ce me zai hana ka janye aurena da Aydah ka mayar akan Sadiya tun da yanzu mun gama fahimtar juna. Sadiya ta yi nadamar abinda ta yi har ta roke ni gafara na kuma yafe mata Daddy let bygone be bygones. Tun da ya fara magana Daddy yake karantar yanayinsa ga baki ɗaya, kafin ya ja numfashi tare da saukewa "Mariya ce ta kimtsa maka wannan maganar ko Abba?" Daddy ya tambaya duk da yana da tabbacin wannan maganar ba daga Abban take ba amma domin ya tabbatar tare da kawar masa da kokwanto shine ya tambaya. Nan take Abba ya ruɗe ya shiga kame-kame "Ka yi haƙuri Daddy idan ranka ya ɓaci Mami tana gani is too early a yiwa Aydah aure zai zama kamar an shiga hakkin ta ne, kuma ni banaso na yi abunda zai cutar da Ayd... "shut up, I told you to shut up before I get angry with you Abba yaushe har lalacewa ta ya kai na zantar da hukunci a gidana Mariya ta tashe shi? Kai kuma da yake shashasha ne har ka aminta da zancenta, to bari ka ji muddin na isa dakai kuma har yanzu kana kallona a matsayi mahaifi aure tsakaninka da Aydah babu fashi. "Daddy I'm sorry please forgive me zan yi duk abinda ka umarce ni kasani har duniya ta nade bani da wani mahaifi sama da kai burina a koda yaushe na kasance ɗa mai biyayya ga iyayensa shine ma dalili da yasa na amsawa Mami bukatar ta. "Daga yau banaso ka sake zuwa min da zancen Sadiya aure a tsakaninku ya haramta saboda kai mijin ƙanwarta ne. Tashi ka tafi sai da safe. Batare da AB ya sake cewa komai ba ya tashi jiki sabule har ya kai kofa ya kama handle da nufi buɗe ƙofa Daddy ya dakatar dashi "Ka ɗaga tafiyarka zuwa Lagos sai bayan ɗaurin aurenka, kuma ka tabbata ka raba invitation cards ɗin da na ba ka. "To! Daddy. AB ya faɗa tare da buɗe ƙofa ya fita ya nufi ɓangarensa yana tafe yana haɗa hanya baisan har sai yaushe ne zai fita daga matsalolin rayuwa ba?" kullum daga wannan sai wancan, al'amurran sa sai daɗa taɓarɓarewa suke yi tun daga ranar da yasan Daddy da Umminsa ba su bane suka haife sa ba ya yi bankwana da farin ciki walwalarsa ta koma ƙunci, damuwa ta mamaye dukkan jin daɗinsa, baƙin ciki ya maye gurbin farin cikinsa. Yana tura ƙofar parlornsa idanunsa suka hasko masa Sadiya zaune ta harɗe hannuwanta a ƙirji ta yiwa ƙofar shigowa kur da idanunta, tana dubi ta inda zai bullo. Ganinta a zaune cikin parlornsa ya haifar masa da wani kalan baƙin ciki ya rasa ya ake so ya yi da rayuwarsa. Rai ɓace ya tako zuwa tsakiyar parlorn ganinsa da ta yi yasa ta miƙewa tsaye jikinta har wani rawa yake yi ita kaɗai tasan irin azbtuwa da take yi da soyayyar yayan nata, soyayyarsa tana neman ta kaita a wani mataki mai matuƙar wahalar fassara wa. Kafin ta yi magana ya rigata ta hanyar furta "Me kika shigo yi a bangarena ke miyasa ba ki da tunani da baki san right time da ya dace ki shigo part ɗina ba?? "Ka yi hakuri yaya Abba na kasa samun natsuwar zuciya, idanuwana kai kaɗai suke da bukatar gani ruhi... "Will you shut up! Ya katse ta a hassale ransa na masa ƙuna ya cigaba da faɗin "Ya kamata ki iya gano wa Sadiya babu so irin wanda kike marari a tsakanin mu ban taɓa miki wani kallo na daban sama da na ƙawata wacce mu ke uba ɗaya, kuma bana tunani sauyawar hakan koda anan gaba. A shawarce ki yi gaggawa cire ni daga zuciyarki domin ƙanwarki Aydah nake so kuma ita zan aura, saboda haka ki fitar min a parlor banaso gani ki ko kaɗan Sadiya. Ya ƙarashe magana yana wani kalan huci. Mutuwar tsaye Sadiya ta yi tare da runtse idanunta maganganun sa sun yi mata nauyi a zuciya sai faman fizgar numfashinta take yi a hankali ta shiga buɗe idanun nata akan kyakkyawar fuskarsa da take hana mata sukuni hawaye kawai ke zuba daga idanunta cikin rawar murya ta ce "zuciyata ba za ta iya jurar rabuwa da kai ba yaya Abba. "Ni kuma zuciyata tana ga Aydah. "Uhm! Yayanmu kawai faɗa kake yi domin kana gani ta hakan ne kaɗai za ka iya ƙonamin rai, amma ni nasan babu Aydah a zuciyarka Rumaisa madawaki kake so ba Aydah ba. "Tun da kin san da haka me zai hana ki shafa min lafiya ki fita daga sabga ta dan Allah. Ya ƙarashe magana tare da haɗe hannayensa wuri guda Abba mutum ne bayaso tashin hankali ko kaɗan, shiyasa yake ta lallaɓa Sadiya. "Ba zan iya ba yayanmu da ace za a bani dama a rayuwata na canza abubuwa, bazan yi kasa a gwiwa ba wurin ganin na zabe ka a matsayin mai sarautar zuciyata. kasan irin son da nake maka kuwa? Banta ba tunanin zan so wani ɗa namiji kamar yadda nake son ka ba yaya Abba. Daga Aydah har Rumaisa ba wacce za ta iya ba ka farin ciki koda rabin kwatakwacin wanda ni ɗinan na tanadar maka dashi, yayanmu wallahi zan jiyar da kai daɗi irin wanda babu macce da ta isa ta jiyar da kai shi a shimfiɗarka zan koyi kalolin sarrafa namiji a shimfida duk don saboda kai zan zame maka tamkar sex machine ka juya ni da duk kalolin styles ɗin da kake so ba zan maka ƙorafi ba ko na nuna gajiyawa ba. Cikin kaɗuwa AB yake kallon Sadiya ya ma rasa me zai mata domin ta shammace shi matuƙa bai taɓa tunani fitar waɗannan manya-manyan kalamai daga bakinta ba. Ya kasa yarda ƙanwarsa Sadiya ce tsaye a gabansa tana ikirarin cewa za ta sarrafa shi a shimfiɗa wannan wane irin lalatatcen zamani ne Allah ya kawo mu, yanzu kamar Sadiya as her age tasan yadda ake jiyar da ɗa namiji daɗi. Zuciyarsa sai bugawa take yi har ta zarce ƙa'ida wani deep breath ya ja yayin da tsikar jikinsa ta mimmiƙe a hankali yake furta "Hasbunallahu wal-imaal wakil! Ya furta ya fi a kirga kafin ya ji natsuwarsa ta fara dawowa a jikinsa idanuwansa dake ciki da wani irin fushi da ɓacin rai ya sauke akanta kafin cikin tsawa da hargowa ya ce "Na godewa Allah da ya bayyana min da ko ke wacece Sadiya, nagode Allah da nuna min asalin halayar ki ko kaɗan ba ki cancanci natsetse namiji kamata ba. Na tsare mutuncin kaina ban taɓa ketare iyakokin Ubangiji ba. Shiyasa Allah ya kawo ƙarshen aurena dake ki sani ko daga ni sai ke kaɗai muka rage a duniya ba zan taɓa aurenki ba. Ki yi gaggawar barmin parlor kafin na yi miki wulaƙanci da ko kare ba zai ci ba. Da sauri ta matsa kusa dashi sautin kukanta ya ƙaru "yayanmu dan Allah ka fahimci inda kalamai na suka dosa wallahi-azim abunda kake tunani ba shi bane ba.. "Don't take my quietness for granted Sadiya just do what I say get out of my setting room, I don't want to see your feet ever again in my apartment. Da sauri ta zube guiwayoyinta gabansa tana gunji kuka "Yayanmu karka yi min haka wallahi kaine rayuwata idan na rasa ka komai zai iya faruwa dani a wannan duniyar da muke ciki sonka zai iya jefa ni a cikin mayuwaci hali, koda za ka datse numfashina amma ba zan fasa furta maka kalmar ina sonka ba inason kasan wani abu guda ɗaya, duk halin da zan shiga ko za ka shiga ba zai sa na daina maka irin son da nake maka ba. "Mtss! To shi kenan tun da ba za ki fata min a parlor ba ga ki nan gashi ki yi ta zama har a busa ƙaho, banza heartless. Ya ƙarashe magana tare da nufar master bedroom ɗinsa a fusace ya datse ƙofar da key, ƙirjinsa na masa wani irin zafi ajiyar zuciya ya sauke ta ya fi a kirga ga baki ɗaya rayuwarsa ta dawo abar tausayi duk ya ta'allaka wannan masifar da yake ciki akan mahaifiyarsa data haife data jifar miyasa ma ta haife shi ba ta zubar dashi ba tun da ya zama unwanted child kamata ya yi ta kashe shi tun yana ciki da yanzu duk bai haɗu da waɗannan masifun ba. Duk dauriyarsa sai da ya zubar da hawaye sannu-sannu yake rera kukansa mai ƙaramin sauti kansa ya dau zafi ji yake tamkar zai yi hauka, baki ɗaya abubuwa sun kwace masa ya rasa ina zai jefa kansa ya ji daɗi duniya ta yi masa ɗaurin goro ji yake kamar ya tashi ya haɗa kayan sa sai dai a waye gari a nemi sa arasa, sai kuma idan ya tuna da tafiyarsa za ta cutar da mutane da yawa musamman Daddy da Aydah sai ya ji jikinsa ya yi bala'in sanyi kwarin gwiwarsa ya fice. Daren rana gaba ɗaya ya raya shi ne yana miƙa kukansa a wurin Ubangiji sammai bakwai, da safe kaitsaye ya wuce office batare da ya shiga ɓangaren Mami ba. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/18/2023, 10:31 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*: Jeddah 3256 #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 29.. Sosai Mami tasha mamakin fitar da Abba ya yi office batareda ya shigo bangarensu ya gaisheta kamar yadda ya saba. jiya da tunani da fargaba ta kwana dan ko a fuska Daddy bai nuna mata sun yi maganar da Abba akan mayar da aurensa da Sadiya. ga baki ɗaya cikin damuwa take da zullumi tasan mijin nata koda ya yi magana da Abban ,da matuƙar wahala ya faɗa mata shima Daddy a daren ranar yana kallon yadda mami take sai mutsu-mutsu kurum take ita ɗaya. Juya mata baya kawai Daddy ya yi ya ci-gaba da baccin sa cikin natsuwa. A can kuma kasan ransa damuwa ce sosai yana mamakin yadda son kan matar tasa ya yi yawa da alama ita abunda Sadiya ta yiwa Abba bai dame ta ba, domin da ya dame ta ba za ta bijiro masa da zance a mayar da aurensu, duk mutumin da ya nemi ya salwanta maka rayuwa abin gudu ne. Har Daddy ya yi shirin fita office bai kula Mami ba haka zalika magana kwakwara ba ta shiga tsakanin su ba. A haka ya yi mata sallama ya fice daga gidan acikin dinning area Siyama ta samu mami kana kallon yanayinta kasan tana cikin damuwa "Mami wai bakida lafiya ne kwanan nan sai nake ta ganinki wani iri?" Siyama ta faɗa da muryar damuwa yadda ta yi maganar itama ya nuna ta nuna damuwarta sosai akan lamarin mahaifiyar ta ta. Mami ta kalleta tana faɗin."ke kaɗai za ki shiga makaranta ne ina Sadiya ne? "Mami yau banda lecture zan dai je wanki kaine yaya Sadiya kuma ban sanar mata ba tun da kika ga ta kai haka tana bacci ba fita zata yi ba. Mami ta sauke ajiyar zuciya tana faɗin ."Allah ya tsare hanya. Siyama ta amsa da "Ameen! Ficewa ta yi daga parlorn tana gyara veil ɗin abayar da tayi rolling kanta dashi. Mami kitchen ta shige tana faɗawa mai aikinta idan ta gama gyara kayan miyan ta fito da wake ta gyara sai tayi musu awara tun da ta iya, Aydah tanata maganar ayi masu awara,mai aikin ta amsa da to Mami ce tsaye a ƙofar ɗakin Sadiya tana ɗan buga ƙofar gami da kiran sunanta shiru ta ji da haka ta juya ta nufi nata ɗakin wayarta ta ɗauka dake kan mirror dressing tayi dialling lambar Abba, ga mamakinta wayarsa a kashe bata yi wani mamaki ba dan tasan halin Abban, zai iya aikata fiye da haka wani murmushin takaici Mami ta saki ta lura yaron nan so yake ya yi wasa da hankalinta daga shi har mai daure masa wato Daddy, wannan karon sai ta nuna masu ainihin wacece ita wallahi ko zata yi yawo a tsirara Abba ba zai auri Aydah ba. kusan ƙarfe goma sha biyu har da rabi Sadiya ta fito daga ɗakinta cikin shirinta na zuwa makaranta kallo ɗaya zaka yiwa idanunta kasan tasha kuka har ta godewa Allah saboda kumburar da suka yi dan haka ta boye kwayar idanunta cikin glass ɗin frada ta yadda ba za ka iya kallon kwayar idonta kai tsaye, Mami ta sama a ɗaki tun da daga sama har ƙasa Mami ke kallonta cire baƙin glass ɗin da ta mannawa, suna haɗa ido da Mami sai da ta wani kalar zaro ido a rude take faɗin "ke me ya samu idanunki haka?"rasa ma me zata cewa Mami tayi dan ko kaɗan bata son tuna baƙaƙen maganganun da AB ya faɗa mata daren jiya dan hauka ne kawai bata yi ba."mami zan shiga makaranta idan na dawo zamu yi magana. "Kina cikin wannan yanayin kike maganar wata makaranta. "Mami pls! Sadiya ta faɗa da rauni a muryarta da gaske ko magana bataso yi saboda yadda kanta ke wani irin ciwo, Mami ta tako zuwa gabanta da car key ɗin motarta ta miƙa mata tana faɗin."ki je da mota na da dare zan yi magana da Daddynku shine ya haifar min ku ko Abba,wata nawa da ya kwace keys ɗin motarku ya kamata ya ba ku abinku haka tunda bada kuɗinsa aka siya ba. Na gaji da ganin ya'yana suna gantali acikin adaidaita sahu sai kace wasu marar gata. Ita dai Sadiya juyawa kawai ta yi ta fice daga ɗakin na Mami tun a hanya ta yi dialling lambar ƙawarta saratu wacce suka mayar da sunanta (sarah )yar asalin jahar taraba ce Sarah irin mutanen nan ne wayayyu gaske wanda suke da wani irin freedom suna cikin 'ya'yan da idan suka zo karatu wani gari suke yin fatali da tarbiyyar da iyayensu suka ɗora su akai, wanda a tunaninsu idan basa gaban iyayensu duk ta'asar da suke son yi zasu iya yi batare da duba da me gobensu za ta haifar musu ba. Sarah babu kalar kayan mayen da bata sha haka ma maza tana hurda dasu sosai. Babu yarda AB bai yi da Sadiya ba akan ta daina ƙawance da Sarah da yake tun fil'azal Sadiya kunne ƙashi ne da ita sai tayi fatali da umarnin yayan nata. "Sarah kina hostel ko kin fita gantali ki?"Sadiya ta faɗa bayan Sarah ta daga wayar "Ina hostel sai zuwa anjima kaɗan zan fita saboda ina da appointment da wani ɗan majalisa me ya faru na ji muryarki wani irin?" "Gani nan ƙarasowa maganar ba zai yiwu a waya ba. Da haka ta katse kiran. Ta mayar da hankalinta sosai akan driving tana kissima da tana ganin Rumaisa yanzu akan titi zata iya bin takanta da mota saboda yadda ta tsaneta. Tun da ta shigo cikin ɗakin bata cewa Sarah komai ba kwanciya kawai ta yi akan bed ɗin dake cikin ɗakin. Tana fitar da numfashi da sauri da sauri wani irin kunci take jin kanta a ciki ga baki ɗaya duniyar ta yi mata zafi, jin har lokacin taki magana yasa Sarah ta zo ta zauna gafda ita tana ƙarewa yanayinta kallo a hankali Sadiya ta miƙe zaune ta saka bayanta kan pillow sai lokacin ta cire glass ɗin da ya mamaye rabin fuskarta idonta cikin na Sarah da take kallon fuskarta harma da idanunta. cikin rawar murya Sarah ke faɗin."ke lafiyarki kuwa?"Kinga idanunki! "Ina cikin matsananciyar damuwa Sarah ki bani shawara na tabbata ƙwaƙwalwata tana gafda tabuwa. Ta karasa maganar muryarta na wani irin hardewa, anan kuma ta soma bai wa Sarah labarin mutuwar aurenta dan koda wasa bata taɓa gayawa ƙawayen nata wai sun yi divorce ita da yaya Abba. Cike da tashin hankali Sarah ke faɗin."kuma mahaifin naku ya rasa wacce zai aura masa sai autarku wannan 'yar mitsiyaya yarinya yaushe za ta iya ɗaukar ƙato irin yaya Abba? inama laifin Siyama, kai gaskiya Daddyn nan naku bai yi ba Sady-B ni yanzu nama rasa wane kalar tunani zan yi ya kamata dai ki fara samun bacci dan yanzu baki da natsuwar da zamu yi magana. Duk wanda ya kalle ki zai san you're suffer from depression dole sai kin ɗan sami bacci ko da kaɗan ne da haka sarah ta dauko wata bag ta zuge bag ɗin ta fitar da wata kwalba ta kalli Sadiya da murmushi cikin fuskarta tana faɗin "yanzu dai ki shanye duka wannan haɗin Insha Allahu baƙaƙen maganganun da Abba ,ya faɗa maki tuni zasu fice miki akai ke baza ki masan wannan na musamman bane yana da dandano sai kin shanyesa dukka. Lokaci ɗaya yanayin fuskar Sadiya ya canja tana girgizawa Sarah kai take faɗin."banda wannan. Wata dariya Sarah ta saki tana faɗin."ki sha na yau kawai Sady-B ni na faɗa miki damuwar nan zata rage dan Allah ki sha. Da haka Sarah ta kwance marfin batare da dogon tunani ba ta kai sa daidai bakin Sadiya dakyar Sadiya ta buɗe bakint tana fara sha ta wani irin ya mutse fuska da sauri ta janye kwalbar daga bakinta tana girgizawa Sarah kai haka tana jin kanta na wani irin juyawa lokaci ɗaya. Sarah ta dinga yi mata dabara har ta shanye dukka ta dauki bottle water ta miƙa mata ta sha rabi anan ta baje tsakiyar ɗakin ta koma ta kishingiɗa tana jin yadda kanta yayi wani mugun nauyi babu shiri ta lumshe idanunta. Gefe Sarah ta koma tana ta lura da yanayin ƙawarta ta har na kusan minti goma sha biyu kafin bacci mai nauyin gaske ya Sadiya. murmushi Sarah ta yi tana faɗin."idan kika farka ke da kanki za ki nemi ƙari wani. ƙarfe biyu AB ya fita restaurant yaci abinci saboda yadda hanjin cikinsa ke haɗewa wuri ɗaya babu abunda ke cikin cikinsa, tun safe yana gamawa ya koma office bai bar office ba sai karfe biyar tilas gida ya koma dan yin wanka yana ta tunanin zuwa wurin Rumaisa da yamma, ya kamata ya faɗa mata hukuncin da Daddy ya yanke ganin kwanakin nata matsowa. Bai shiga da motarsa cikin gida ba a waje yabarta dan ko kaɗan baya son haɗuwa da mami. Har ya shige ɓangarensa bai haɗu da kowa ba kayan jikinsa ya cire yayi wanka. Yana cikin shiryawa ne ya ji ana buga masa door bell dan buɗe idonsa yayi da mamaki jallabiyya ya nema ya saka ajikinsa dan ko creams ɗinsa bai gama shafawa ba ya saka (casual slippers)a ƙafarsa ya nufi kofa yana buɗe kofar idonsa cikin na Siyama da murmushi a fuskarta ta gaishesa ya kalli tray ɗin dake hannunta "Sannu da dawowa yayanmu ya office?" Mami ta ce a kawo maka lunch, da haka ta isa kan dinning ɗin dake cikin parlorn ta aje masa. Sosai yayi mamakin yadda Mami tasan ya shigo gidan, bai san da cewa Mami magana ta yi da Balmo maigadi akan idan Abba ,ya dawo kai tsaye ya kirata a waya haka ko aka yi yana ganin dawowarsa ya kira Mamin a wayar har yana ce mata bai shigo da motar na kila zai ƙara fita ne. murmushi kawai Mami ta yi watau Abba ya mayar da ita yar iska a lokacin suna zaune da Siyama a parlor Mami ta mata umurnin ta zuba abincin ta kai masa acan bangarensa. Yana tsaye a bakin ƙofa har Siyama ta aje ta dawo. "Ki jira ni" Ya ce da Siyama yana barin bakin ƙofar ɗakinsa ya wuce ya buɗe bedside drawer ya ciro keys ɗin motarta ita da Sadiya, tun da ya miƙa mata take kallonsa da murna take faɗin."mungode sosai yayanmu amman ka jawa babynka kunne ta daina yimana rashin kunya. "Ai bama sai na ja mata kunne ba ita ma motarta na zuwa kwanan nan. Ɗan buɗe ido ta yi tana kallon yayan nasu sai dai ba tace komai ba ta juya tare da ficewa daga part ɗin tana murmushi tasan wasa yake wane mahaukacine zai siyawa Aydah mota, daman ko kallon abincin da Siyama ta aje bai yi ba ya koma master bedroom ɗinsa ya ci-gaba da shiryawa yana gama shiryawa ya fice daga gidan sai da ya fito gidan ya sauke wata irin ajiyar zuciya sosai Mami ,tasha mamakin Abba yadda ya mayar da ita wata shashasha ya ƙara ficewa batare da ya shigo ba. Yana driving ya yi dialling lambar Rumaisa tamkar jiran kiran nasa take ta dauka agagauce cikin muryar kuka take faɗin."wallahi ka daina sona habeebi. "Ina hanya. Ya faɗa tare da saurin katse mata hanzari duk sai haka sai da take furta "Da gaske kake yi Habibi? "ko na koma ne?" Da sauri tace "A'ah sai ka ƙaraso. Da haka ya sauke wayar wannan karon kuma bai san ta yaya Rumaisa zata karbi wannan al'amarin ba. ƙofar gidansu Rumaisa ya yi parking motarsa ya kirata a waya bai fi minti goma ba da kiran nata sai ga ta, ta buɗe ƙaramar ƙofar dake haɗe da gate ɗin gidansu tun kafin ta karaso ya sauke glass ɗin motar riga da skirt ne ajikinta na Atamfa sun yi mata kyau sosai sai dan karamin veil ɗin da ta ɗora kan kafaɗarta light make up ne akan fuskarta wanda ya kara fito da asalin kyawunta ta yi masa kyau ba kaɗan ba. Kallonsa kawai take cin karo da fuskarsa kawai da ta yi yanzu duk wani haushinsa da take ji tun jiya ya ɓace daga zuciyarta. Tana mamakin yadda bata iya fushi dashi, fitowa ya yi daga motar yana ci-gaba da kallonta ƙasa-ƙasa kamar yadda ita ma take kallonsa girar ta dukka biyu ta dage."kayi kyau sosai Habibina! Ta faɗa a hankali ,kafin ta kuma ta cigaba da ƙarewa kayan jikinsa kallo na tsanake baƙin yadin filtex ne ajikinsa sai links da aka yiwa hannuwan wani sanyayyen murmushi ya sakar mata irin mai shiga jiki yana shafa sumar kansa mai kama da ta labarawan asali murya can ciki ya ce "Ban kai ki ba habibty. "Zagina kake yi. Buɗe mata manyan fararen idanunsa yayi ,camera wayarta ta saita ta shiga daukarsa pics tana faɗin "kai ba zaka gane kyan da kayi bane. Bai ce da ita komai ba iyankacin sa ya yi murmushi dawowa tayi daf dashi ta shiga daukarsu video duk da bai yi dariya ba Amman a hakan ya yi mata kyau sosai. Ya girgiza kai ya rasa soyayyar Rumaisa da son hotuna. Idan kaga hotonsa to Rumaisa ce ta tilasta masa yinsa. "Mu shiga daga ciki wai meyasa kake parking motar ka a waje?." Ta faɗa da yanayin marar daɗi a muryarta, kin manta Daddy.. Da sauri ta katsesa tana faɗin."baya gari fa ta karɓe car key ɗin motarsa ta shiga ɓangaren driver ta tada motar ta doshi get ɗin gidansu tana yiwa maigadi horn sai da ya leƙo ganin Rumaisa ce ya buɗe gate ɗin da wani irin kallo ta bisa ganin yadda yasata take ta danna masa horn sai kace wani kurma gyara parking motar tayi. Har lokacin tana mamakin AB da yaki shigowa ,tana kawowa wurin maigadi ta yi masa wani shegen kallo ta fice daga gate ɗin a tsaye ta samu AB yana jiranta ƙarasawa tayi wurinsa tana faɗin."kaga na shiga mota kaki shiga kuma ka zo ka yi tsaye anan mu karasa aciki mana. Kallonta yake da wani yanayi dake kwance cikin idanunsa mai cike da zallar ƙaunarta bin bayanta ya yi har zuwa parlorn da suka saba zama duk lokacin da yazo gidan. Kayan motsa baki ta aje masa agabansa ta dauki glass cup ta zuba masa lemu.. #Love story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/19/2023, 11:07 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*:3256 Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 030. "Habeebi!" Rumaisa ta kirasa cikin sanyi murya ganin yanayinsa ba haka ta saba ganinsa ba, sai da ta ƙarewa masa kallo ta sauke numfashi kafin ta ce "meke damunka ne kwanan nan?"duk ka zama wani iri. murmushin iya fatar baki ya yi mata yana shafa beard ɗinsa yana kallon yadda take wani bin jikinsa da kallonsa tamkar mai neman wani abu a jikin sa tana kallon yadda idanunsa suka fada duk girmansu sai da suka shige "ka rame bakada natsuwa tare da kai ka daina boyemin damuwarka. Rumaisa ta faɗa da wani yanayi a muryarta da tasa zuciyarsa wani irin dokawa. "Zan kara yimaki laifi Rumaisa amman karki manta a kowanne yanayi sonki ne manne a zuciyata karki dauka da son raina zan yi miki wannan laifin ina sonki!"inason ki Rumaisa wallahi ke ce macce ta farko da zuciyata ta fara so da ƙauna. Yadda yake ta maimaita yana sonta yana kara narkar mata zuciya har ya fara daga mata hankali kamar wani abu mai girma zai gifta a tsakaninsu. "Zan dauki kowanne irin laifin da za kayi min banda.... Tun kafin ta karasa ya katseta dan yasan me zata faɗa."Daddy ya yanke shawarar auramin Aydah a karo na biyu nan da jibi.!" Shi kansa yadda ya faɗi kalamar cikin da sauri yasha mamaki yana kallon yanayin Rumaisa da ya canja lokaci ɗaya, tamkar bata fahimce me yake nufi ba. Ganin yadda ta zama lokaci ɗaya yasa ya dawo kusa da ita hannunta ya kama ya damƙe cikin nasa yana ganin yadda idanunta suka cicciko da kwallah lokaci ɗaya, "Ki sani Rumaisa aurena da Aydah ba zai canja alakarmu ba Rumaisa idan mahaifinki ya amince dani bayan aurena da Aydah zan aureki saboda ke ce zaɓin zuciyata. Kalamansa banda ƙona mata rai babu abunda suke cikin tsanani ɓacin rai ta ce "ka aureni a ina? Na haƙura Bashir da gaske na haƙura da kai. Ta faɗa cikin fita hayacinta.wasu irin hawaye ne ke fita akan fuskarta tana jin yadda jikinta ya dauki wani kalar dumi kamar zazzaɓi zai rufeta lokaci ɗaya.babu abunda zai canja Rumaisa."meyasa kike shakkar soyayyar da nake yimaki,aure zakayi meyayi saura a tsakanin mu kuma auren da Aydah Wani irin murmushi take saki wanda bai da alaƙa da farin ciki "Daga ranar da ka haɗa gado da wata macce daga ranar zan daina sonka.! Ba zan boye maka ba ina da kishin da Ni kaina ban san kalarsa ba musamman akan ka Bashir. Tun kafin ma hakan ya faru na faɗa maka kar ya faru kaga na canja ka ce dan me?" Kallonta yake yana juya Kalamanta aransa, kina nufin da ƙanwar tawa zan haɗa gado Aydah ce fa? Ya faɗa a hassale hakikanin gaskiya Rumaisa ta fara harzuƙa shi akan me za ta ce ya haɗa gado da Aydah, sai kace bashi da ƙwaƙwalwa a kokon kansa, maganganun ta su yi matuƙar yi masa muni. Rumaisa ta kalle shi a lalace ta ce "Wannan ɓangaren bai da yare"! Ni dai na hakur.... Tun kafin ta ƙarasa ya fisgota cikin jikinsa abunda bai taɓa faruwa ba a tsakaninsu tana jikinsa tana jin yadda ƙirjinsa ke wani irin bugawa sosai ta rungumesa hawayenta na sauka kan ƙirjinsa "Zan iya mutuwa habibty idan kika sake cewa na haɗa gado da Aydah she's like a daughter to me babu wannan zance a tsakanin mu na amincewa Daddy da aurenta ne saboda ba zan iya masa musu ba Rumaisa dukka Aydah nawa take da za ki yi wannan kalar tunanin me ma ta sani acikin rayuwar aure? ki kwantar da hankalin ki Rumaisa babu abunda zai canja ni naki ne na har abada Aydah kawai zata cigaba da zama a karkashin kulawata da ta girma ta mallaki hankali kanta ni kaina zan samu mata mijin da ya dace da ita zan rabu da ita cikin sauki batare da Daddy ya ji zafina ba. Ita ma Aydah a matsayin yaya take kallona na kuma tabbata har abada ba za ta canza min wannan matsayin ba. Na maki alƙawarin babu abunda zai canja matsayin Aydah a zuciyata. Ɗagowa ta yi daga cikin jikinsa tana dan ja da baya kusancinsu yasa take jin wani iri kalamansa kuma ba karamin sanyayya mata zuciya suka yi ba tasan halin AB baya magana biyu kuma tasan babu abunda zai cira ajikin Aydah yarinyar da ma nonuwa basu gama tsayawa a kirjinta ba me za ya yi da ita amma sanin da ta yiwa butulci irin na ɗa namiji sai kawai ta ce "Habibi na yarda da kai ɗari bisa ɗari amma inaso kauda duk wani kokwanto da zai zo min anan gaba Habibi me zai hana ka rantse da Alqur'ani ta hakan ne kaɗai zan ƙara yarda da kai ɗin nawa ne ni kaɗai. Wani malalaci murmushi ya yi yana faɗin "Habibty ba ki yarda dani ba. "No Habibi wallahi na yarda da kai the only problem ku maza ba ku da tabbas yanayin ku tamkar na hawainiya ne koda yaushe kuna iya canza kala. "Habibty da kin yarda dani da ba za ki nemi na rantse da Alqur'ani ba ki tuna Rumaisa Alqur'ani ba abin wasa bane. "Ai shiyasa na ce ka rantse dashi idan har ka amince ka yi rantsuwa dashi ni kuma zan nemi hanyar da zan sa Abbana ya amince da aurenmu, yanzu zaɓi ya rage naka kuma ta wannan hanyar ce zan ƙara tabbatar da ni kaɗai ce a zuciyarka. Duk yadda AB yaso Rumaisa ta janye zance rantsuwa da Alqur'ani amma ta kafe lallai idan da gaske yana sonta dole sai ya yi abinda take so daga karshe baram-baram suka rabu a fusace ya yi mata sallama ya koma gida. Sai dab da magarib Sadiya ta tashi daga naunnaye baccin da ya ɗauke ta a ɗakin Sarah da kyar ta iya tashi zaune wani irin azababben ciwon kai take ji a hankali ta dafe goshinta tare da runtse jajjayen idanuwanta da suka mata dankaran nauyi ta dauki ten minutes a haka kafin ta yada ganinta a cikin ɗakin Sarah bata nan room mate ɗinta kaɗai ta gani kwance a nata gado tana chatting da wayarta Sadiya ta ja deep breath tare da sauke wa ta kalli Esha cikin nauyin harshe ta kira sunanta "Esha! Da hanzari Esha ta waiga gafen da Sadiya take cikin fara'a ta ce "Ah! Sadi-B kin falka? "Uhm! Ina Sarah? "Ai kuwa Sarah ta daɗe da fita ita ce ma ta bani gadinki da tuntuni na fita kin ga babu daɗi kina bacci mufi ce mu barki ke kaɗai a kwance. "Nagode Esha! Ni zan wuce gida idan Sarah ta dawo ki ce ta kira ni dan Allah tun da ta fita gantalinta nasan ko na kira ta ba zan same taba, ta kashe wayarta. "Shi kenan zan faɗa mata ki gaida min da Siyama. "Za ta ji! Sadiya ta faɗa a takaice tare da ɗaukar handbag ɗinta, ta fice Esha ta bi ta da kallo tana murmushi sai kuma ta taɓe baki ta maida ganinta kan wayarta, Sadiya tana tafe dizzy yana ɗibar ta adaddafe ta isa wurin da ta yi parking mota da wata irin kasala ta ja motar sai da iso gida abinda ya faru da ita ya fara dawo mata da sauri ta dauki robar ruwan faro dake cikin motar ta wanke fuskarta tare da gogewa da mayafin jikinta dole ta mayar da baƙin gilashinta ta rufe mota ta nufi cikin gida kafin ta tura ƙofar main parlor sai da ta ƙara daidaita natsuwarta musanman da take jin damuwarta ta ragu daga kashi sittin a cikin ɗari. Idan Allah ya taimake ta mai aikinsu kaɗai ta tarar a parlor ita ma tana ƙoƙarin arranging throw pillows ɗin kujerun da yaran Aunty Safeena da ta zo dasu suka wargaza su wanda basu daɗe da tafiya shine Mami tasaka kimtsa parlor ɗin. Kallo ɗaya Sadiya ta yiwa Huwaila mai aiki ta haura upstairs da gudunta tana zuwa ta cire kayan jikinta da suka yi wani kalan uban squeezing ta faɗa bathroom ta yi wanka. *MASARAUTAR KUDU* Yau kusan kwana uku da Ciroma ya dawo daga wurin boka mai Gundulelliya, damuwa tana neman tayi masa yawa saboda ya rasa ta wacce hanya zai bi ya ciyar da sarki Mahmoud ruwan da bokan ya bashi gashi zuciyarsa ta kasa haƙuri da muradinsa. Gashi kuma lokaci da sarki Mahmoud ya ɗiba na naɗin sarauta da za a gudanar a masarautar ta kudu sai daɗa karatowa yake yi. Hankalin sa ya ƙara tashi saboda baya so wa'adin da Sarki Mahmood ya ɗiba ya cika ba tare da ya aiwatar da shirin sa ba. Sai kwatsam! Wata shawara ta faɗo masa da ya nemi Galadima duk basa shiri da junansu, domin idan ya ce zai yi wannan tafiyar shi kadai to kuwa ba zai taɓa cimma gaci ba. Ƙasanwar burinsu ɗaya da Galadima naso sarautar sarkin sabon birnin to kuma da ya sami damar mulkar kudu ga baki ɗayanta sai yaga dacewar ya shigo da Galadima cikin tafiyarsa idan Allah yasa, burinsa ya cika shi kuma zai naɗa shi a matsayin sarkin sabon Birni. Da wannan shawara ya nemi ganawar sirri da Galadima a wani gidan gonarsa duk da ya kwana da sani irin 'yar tsamar dake tsakaninsu. Galadima ƙani ne ga margayi sarki Usman Mustapha na uku shi ne ƙarami a cikin 'ya'yansa bayan rasuwar sarki Usman Galadima yaso a bashi sarautar kudu duba da manyan fada suka yi da ƙananu shekarun sa ba zai iya riƙe babbar karagar mulki irin wannan a bisa duba da cancantar Mahmood da kuma yawan shekaru da Mahmood yafi dasu tare da goyon gogewa akan sha'anin sarauta sai suka bashi wannan sarautar daga baya da Galadima yaga sarautar Kudu ta subuce masa sai ya dawo kan sauratar sabon birnin kudu anan bai yi nasarar samun ta saboda Aliyu, mai martaba sarki Usman ya ba wa ita tun kafin ya bar duniya, a tunaninsa tun da sarki Usman ya rasu manyan fada za su jagoranci a basa sarautar duba da ya girme wa Aliyu nan ma bai yi nasarar ba saboda yadda Ciroma ya hana mishi rawar gaban hantsi. Da farko Galadima bai so amsa kirar nasa ba saboda yana tsoro idan ba wani makirci ne ya haɗa mishi saboda ya kwana da sani makirci irin na Ciroma. Daga baya kuma sai yaga dacewar ya je ɗin dama tsakanin su shege ne yasan makwanci shege, kowanne su mugun kai ne. Bayan Galadima ya iso gidan gonar ta Ciroma sai ya hango shi zaune a cikin wata rumfar hutawa, fuskarsa a murtuƙe ya isa wajensa ko sallama bai masa ba ya shiga faɗin "kai makiri uban makirar mai fuska biyu me kake nema gare ni da za ka aiki amintaccen bawanka da suna kana so ganina?" Sai da Ciroma ya yi murmushi mai cike da zallan mulki yaƙara lafewa a jikin kujarar da yake zaune akai "Kai fa cikakken musulmi ne Galadima duk ka kasance mai sabawa Allah bai kamata a matsayina na musulmi ka kasa yi min sallama baya kuma kasan irin tarin albarkar dake cikin sallama. "Ko zan yi sallama Ciroma ba ka cikin jerin mutane da zan iya yiwa ita saboda haka ka yi gaggawa zuwa ga gundarin dalili da yasa ka nemi ganina a wuri irin wannan. "Galadima alkhairai nake nemanka ba da sharri ba kai kasan wanene ni da ina nemanka da mummunan abu ba zan nemi ganinka a wurin da ya kasance mallaki na. "Mtss! Ni fa Ciroma idan za ka kwana dubu kana faɗa min magana indai daga bakinka ta fito ba zan taɓa aminta da ita ba, muradina ka faɗa min meyasa kake nema na?" "Da fari ka nemi wuri ka zauna domin muhimmancin maganar da zan yi da kai ta wuce a yi ta a tsaye. Wani kallo kama raina min da wayau Galadima ya watsawa Ciroma, kafin kuma ya ja kujera ya zauna rai ɓace ya yi haka ne domin ya kai Ciroma ƙarshe. "Galadima na zauna nayi nazari kuma na zurfafa bincike kafin Allah yasa nayi gamdakatar da saukaƙkiyar hanya da za mu bi domin cikar burukan mu. Daga ni har kai Galadima baƙin jinin mu ɗaya Allah ya jarabce mu da son mulki amma tsabar baƙin jini da muke dashi har yau mun kasa cimma burukan mu... "Dan Allah Ciroma ka tafi kaitsaye ga gundarin manufarka kai kasani banaso nuku-nuku duk abinda za a yi na fi so a tafi straight to the point. "Dadina da kai Galadima gaggawa kuma ka sani aikin shaiɗan ce kuma idan ba ka iya kama barowa ba sai barowa ya kama ka, ka tsaya na yi maka bayani daki-daki kafin na zarce zuwa ga ainihin manufa ta. Kyakkyawar ajiyar zuciya Galadima ya sauke kana ya tattaro hankali da natsuwarsa zuwa kan Ciroma, nan take Ciroma ya kwararo masa manufar sa "idan Allah yasa sarki Mahmood ya mutu ni kuma zan sami damar ɗane karagar mulkin kudu, daga nan zan tsige Aliyu daga sarautar sa kai kuma na naɗa ka a matsayin sabon sarkin sabon birnin kudu, ina fatar za ka bani haɗin kai mu haɗa karfe da ƙarfi mu kwace abinda ya kasance mallakin mu dukka su biyu babu wanda ya cancanta da sauratar da aka basa, to gara ma Mahmood yana da sha'awar mulki ba kaman Aliyu ba ka ga shi Aliyu tsige sa ba zai min wahala ba. Amma ya ka ga wannan dabarar tawa sannan kuma ka amince mu yi wannan tafiyar a tare ko kuwa har yanzu kana da sauran wani kokwanto akaina. A karo na biyu da Galadima ya sake sauke ajiyar zuciya ya gyara zaman babbar rigarsa kana ya ce "Ban ji ka faɗi ta inda zan iya ba da tawa gudummawa acikin wannan tafiyar ba?" Ciroma ya saki ja'irin murmushi cike da farin ciki yadda ya yi nasarar shawo kan Galadima duk tun farko yana da yakini ba zai sha wahala wajen saka shi ya aminta da manufar sa. "Galadima na duba na hango kai kaɗai ne mutumin da zai iya aiwatar da aikin boka batare da an sami kuskure ko wata matsala ba. Murmushin kaima raina min da hankali Galadima ya yi tare da kallon Ciroma a shaƙeƙe kafin ya furta "lallai Ciroma kai ɗin cikakken marar lissafi ne in banda kana mahaukaci ta ya har kake tunani ni Galadima zan amince da wannan mummunan manufa ta ka watau nufinka kura da shan bugu gardi da kwace kuɗi. "Haba Galadima miyasa kake da gaggawa ka tsaya na buga maka lissafi da nayi domin ban taɓa haɗa lissafi batare da ya tafi daidai ba. "Sai kuma gashi a wannan karo bai tafi a daidai ba asalima ka faɗi a lissafin naka. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/19/2023, 11:14 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*:3256 Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 031. Sai da Ciroma ya yi kyakkyawan murmushi kafin ya zarce da faɗin "Duk wanda ke cikin masarautar kudu kama daga manya har zuwa yara kowa ya shaida irin matsananciyar ƙauna dake tsakaninka da Fulani Ƙarama ƙauna ce wacce ku ka gina ta a bisa yarda da aminci amma kwatsam! Mahaifinta ya datse wannan zazzafar ƙaunar taku ya aurar da ita ga sarki Mahmood a cewarsa bai kamata sarki irin Mahmood ya zauna da mata ɗaya ba. Duk da a wancan lokaci sarki Mahmood baya ƙaunar Hafsatu amma saboda irin girman Wambai da yake gani yasa aminta da aure Hafsatu ba don yana sonta ba. A dalilin wannan babban rashi da ka yi sai ya haifar maka da matsananciyar damuwa wanda har sai da ka bar masaurata daga baya ne ka dawo daga nan sai kuka kula haramtacciyar alaka wacce ba kowa ne yasan da ita ba sai ire-iren mu masu bacci da ido ɗaya. "Ka ga Ciroma nagaji da saurare abinda na daɗe da saninsa ka faɗamin sabon abu ko kuma na tashi na ƙara gaba Idan kai ba ka da abin yi ni ina dashi. "Galadima da wannan damar za mu yi amfani ka ɗorawa Fulani Ƙarama alhakin aiwatar mana da wannan aiki kasancewar ta matar sarki Mahmood, na kuma tabbata za ta bi kowacce Irin hanya ce domin mu cimma burin mu saboda irin ƙaunar da take maka. Shiru Galadima ya yi tare da zurfafa nazari da tunanin sa take ya aminta da wannan shawara bai baro gidan gonar Ciroma ba sai da ya basa assurance akan tabbatuwa kudirin su. Bayan kwana biyu Galadima ya haɗu da Fulani Ƙarama inda ya bijiro mata da bukatarsa haɗe da kwaɗaita mata abubuwa da dama. Daman can bata so sarki Mahmood shiyasa bai wani sha wahala wurin shawo kanta ba. *ALH BASHIR MANSION* Sanin da AB ya yi Mami tana jiraye dashi sai ya ƙirkira 'yar boya a tsakaninsu da sassafe zai fice zuwa kamfani ba kuma zai dawo ba sai karfe goma dare, kusan kwanaki uku kenan da ya daina shiga part ɗinta, hakan da ya yi ba ƙaramin tunzira ta ya yi ba Sadiya kuma duk sanda ta fita school tana kammala lectures za ta wuce hostel wurin Sarah ta dirka mata kayan maye tayi tatul sannan ta kwanta tasha bacci abinta da zarar ta falka sai ta ji kanta wasai bata da wata damuwa sai dai a can ƙasan zuciyarta soyayyar AB ce a danƙare sai daɗa hauhawa take, ba za ta dawo gida ba sai magarib dama AB ne mai tsawata musu shi kuma yanzu damuwarsa kaɗai ta isheshi, wannan ya kara bata cikakken freedom da yake shi Daddy ba zama yake yi ba a wasu lokuta yana kai har karfe goma kafin ya dawo gida Mami ce kuma ko kaɗan bata so abinda zai ɓata wa Sadiya rai duk acikin su uku da ta haifa Sadiya ita ce mafi soyuwa a zuciyarta. Yau kam Mami tasha alwashi koda AB zai kai ɗayan dare sai ta yi magana dashi domin ta ji a ina zance su ya kwana shiyasa ta zo ta zauna a main parlor ta kasa ta tsare ƙarfe 10:08pm daidai AB ya tsayar da motarsa a parking lot, ya fito tare da rufe murfin motar ransa a ɓace yake a dalili yadda cikin ƙanƙani lokaci Rumaisa take so ta susuta shi yanzu akan hanyar sa ta zuwa gida ya kira ta sai da ya jerenta mata 7 miscall kafin ta yi picking daga ƙarshe ma baram-baram suka rabu kusan kwana uku kenan tana wahalar da ruhi da gangar jikinsa ko ya yi niyar ya haƙura da ita sai zuciyarsa ta ƙi ba shi haɗin kai yana matuƙar ƙaunar Rumaisa shiyasa yake ta haƙuri yana bibbiyarta. Balmo maigadi yana gani dawowar sa ya kira Mami a waya da kanta ta zura hijab ta nufi bangaren AB a lokacin yana zaune a parlornsa yana waya da Abdulkarim yana faɗa masa irin abubuwan dake faruwa tsakaninsa da Rumaisa sai dai ya boya bai faɗa masa hakikanin gaskiya abunda Rumaisa ɗin ke so ya yi mata, ya ji an turo ƙofa gami da shigowa kaitsaye da fari ya yi tunani ko Aydah ce shiyasa ya yi saurin waigawa sai kawai ya tozali da fuskar Mami wacce babu annuri ko kaɗan akanta "ina so magana da kai ka zo ka same ni a ɓangarena karka ɓata min lokaci ka ji ko?" Mami ta faɗa cikin muryar dake nuna tana cikin fushi, da sauri AB ya yi sallama da Abdulkarim ta hanyar bashi uzurinsa. A zaune ya tarar da Mami a main parlor sai wani girgiza ƙafa take tare da yin ƙwafa. "Mami gani. AB ya faɗa ya nemi kujera ya zauna ya wani sadda kai ƙasa. "Abba yaushe raini ya shiga tsakanina da kai?" Da sauri AB ya ɗago ya kalleta sai kuma ya sake maida kansa ƙasa "Ki yi haƙuri Mami. "Rufe min baki karka sake ka ƙara furta min kalmar haƙuri. "Wallahi Mami na yiwa Daddy magana kamar yadda kika umarce ni amma sai ya fatattake ni tare da ƙin amincewa. A halin yanzu bansan ya zan yi ba Mami. Wani mugun kallo Mami ta wulga masa gani take yi ya ma zo mata da raini hankali shi fa ke aure nan ba Daddy zai yi masa zaman aure ba idan ya kafe lallai-lallai Sadiya yake so ba Aydah ba duk taurin kan Daddy dole ya janye kudirin sa, saboda haka a mugun hassale ta daka masa razananniyar tsawa "dallah dakata Abba! Daman duk yadda aka yi da jaki sai ya ci kara kuma tsintatciyar magge har abada bata magge ɗan tsintuwa ba zai taɓa zama ɗa ba idan ba ka yi min butulci ba Abba ai ba ka cika tsintaccen ba. Wani irin zabura AB ya yi tare da miƙewa tsaye idanunsa suka firfito jikinsa ya dauki rawa tsigar jikinsa ta mimmiƙe, a rikice yake ambaton Allah, gumi ya karyo masa a sassan jikinsa sai kallo fuskar Mami yake yi ya kasa yarda waɗannan zafafan maganganu daga bakinta suke fitowa, yayin da Mami idanuwanta suka rufe ruff cikin ɗaga murya ta cigaba da faɗin "Ka duba irin wahala da na dinga yi da kai tun kafin na haihu a duniya na fara rainonka naci kashi da fitsarinka ga ka da ɗan banza kukan tsiya sai dare ya raba tsakiya kake tashi ka dinga tsala fitinanne kukanka, haka zan tashi idanuwana cike da bacci na saɓa ka a baya na dinga safa da marwa bana bango gabas bana na yamma hankali da natsuwa ta ba za su dawo jikina ba har ka yi bacci. Hatta da uwar da ta haife ni a wancan lokaci sai da ta nuna min kuskuren ƙauna da soyayyar da nake maka ashe tun a wancan lokaci ta hango min zuwan wannan rana. To bari ka ji daga Sadiyar da kake gudu kana nuna mata zallan ƙiyayya da Aydar da kake ƙauna ni ce nan na haife su kuma su duka biyu na haramta maka su. Kai ba ma abin alfaharin ka bane yarinya mai cikakken asali irin Sadiya 'yar halak gaba da baya ta nuna tana son irinka marar asali wanda babu tabbacin ta tsalkakkiyar hanya aka same ka, amma tsabar butulci irin na ɗan adam za ka nuna ba ka sonta. Yadda Mami take magana tare da ɗaga murya ga baki ɗaya muryata, ta cika gidan hakan yasa su Sadiya firfitowa daga dakunan su. Kowanne da kalar mamakinsa yayin da AB ya zube guiwayoyinsa a gabanta ya idonsa suka Kada suka canja kala lokaci ɗaya, yayin da Mami ta cigaba da kare masa tanadi da gudu Siyama ta zo ta rungume shi ta fashe da kuka gani haka yasa ita ma Aydah ta zo ta haɗe su duka shi da Siyama ta ƙamƙame tasa kukan da ya fi na Siyama. Tsaye Sadiya ta yi tare da harɗe hannunta akan kirjinta tana kallonsu ita kuma Mami baki buɗe take kallonsu wata irin tsawa Mami ta yi masu "baza ku tashi ko koma ɗakin ku ba sai ranku ya ɓaci" Tamkar tunzurasu take musamman Aydah da take jin haushin Mami a fusace Mami ta yo kansu Siyama ta fara fisgowa kafin ta yi kan Aydah kara manne masa Aydah ta yi kamar zata koma jikinsa cikin kuka Aydah ke faɗin."Mami yayanmu ne fa?"a hasale Mami ta fisgota ta kaiwa fuskarta mari. Marin AB ya ji yana tabasa wurare da dama dake cikin zuciyarsa idan ya ci-gaba da zama anan zuciyarsa za ta iya bugawa nan take da kyar ya miƙe tsaye yana jin yadda kafafunsa suka yi masa wani irin nauyi harma da nauyin da yake ji acikin zuciyarsa. A nan Tsakiyar Parlorn Aydah ta zube ta haɗe kai da gwiwa ta shiga raira kuka mai ban tausayi, a hankali Siyama ta miƙe tsaye tana ta goge hawayen da suka kasa tsayawa acikin idanuwanta kallon mami da Sadiya take ta kasa gasgata duk maganganun da ta ji suna fitowa daga bakin Mami, watau shiyasa Mami da Sadiya suka canja lokaci ɗaya kenan Daddynsu aure zai haɗa yaya Abba da Aydah samun kanta ta yi da tsintar kanta cikin farin ciki sosai ta taya uwarta murna samun miji irin yaya Abba a wannan lokacin ba ƙaramar sa'a bane a rayuwa."Mami duk abunda yaya Sadiya ta yiwa yaya Abba baki gani ba ta tashi kashesa a daren aurensu saboda irin ƙiyayyar da take masa yanzu a karo na biyu bayan sun rabu kuma kikeso ya kara aurenta?"da gaske kece kuwa Mami.!"me naji kina faɗawa yaya Abba dan tsintuwa kike kiransa marar asali marar gata haba mami yaushe zuciyarki ta zama haka?" ke yafi dacewa ki bada goyon bayan auren nan shine kike bin bayan yaya Sadiya da sai yanzu ne take da tasani nakin amincewa da auren yaya Abba, nasàni mami koda can baya soyayyar yaya Sadiya daban ne a zuciyarki." Sai ta kalli gefen Sadiya dake mata wani shegen kallo jin take kamar ta karaso ta rufeta da duka "baki ji kunya ba yaya Sadiya? Duk wanda ya furta maka Kalmar ƙi da safe sai kuma ya dawo yamma ya furta ma ta so karya yake sai har da wata manufa shimfiɗe a ƙasan zuciyarsa, ke ɗinan har abada ba za ki taɓa zama cikin mutanen kirki ba. Ke kanki kin san yaya Abba yafi karfin ajinki wallahi kuma insha-Allahu Aydah ce matar aurensa uwar 'ya'yansa sai dai ki haɗe zuciya ki mutu.!" "Siyama! Mami ta kirata a hargitse tana wani daka mata tsawa Siyama ko kallon Mami bata yi ba ta ƙarasa wajen Aydah da har yanzu kanta yana cikin cinyoyinta maganganunsu ta ji suna ƙoƙarin fasa mata kai ta rasa me maganganunsu ke nufi. Ta daga Aydah ta rikata suka nufi stairs daga Mami har Sadiya bin su suka yi da kallo."Mami kina jin yaran nan fa idan ba ki yi da gaske ba su za su bamu matsala wallahi."ji yadda suka je cikin jikinsa tamkar wani ubansu Mami ki yi wani abu akai jibi ne ɗaurin Aure wallahi-tallahi idan ban auri yayanmu ba zuciyata za ta iya tarwatsewa ina sonsa ina sonsa Mami."! Sadiya ta faɗa da wani yanayi a muryarta Mami ko fahimtar ta bata yi ga baki ɗaya hankalinta a tashe yake dole zuwa gobe ta yi wani abu kara Abba yabar rayuwarsu na har abada ya koma wani wurin ya cigaba da rayuwa da ta barsa ya auri Aydah. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye Novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/20/2023, 10:56 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*: Jeddah 3256 #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 032. Tana jikin Siyama har lokacin kuma kukan take ta kasa gasgata Mami ce take fadawa yaya Abba waya'annan baƙaƙen kalaman wanda ko a cikin mafarki bata taɓa hasaso Mami zata iya fadarsu ba. Cikin rawar murya Aydah ke faɗin."Da gaske ne yaya Siyam Daddy zai haɗa aurena da yaya Abba?"cikin fita hayyacinta take yin maganar. Siyama dai banda tafasa babu abunda zuciyarta ke yi shafa kan Aydah take a hankali cikin kwantar da murya ta ce "ki yi shiru Aydah babu abunda zai faru da wasa Mami ke yi maki. Shiru Aydah tayi Amman acan ƙasan ranta tsoro da fargaba ga kuma damuwa su suka taru suka yi mata yawa, jin take kamar ta je yanzu ta samu yayan nasu taga wane hali yake ciki. ita ma a bangaren Siyama tunanin da take ta yi kenan jawo wayarta ta yi ta shiga dialling lambarsa har ta katse bai ɗaga ba kara kira tayi nan ma bai daga ba sai da ta jera masa kira kusan goma a na ma ƙarshen da ta kira aka faɗa mata a kashe wayar take a wannan daren AB kasa bacci ya yi duk inda ya juya kalaman Mami ke yi masa ihu cikin kunne da gaske rashin asali bala'i ne gaskiyar Mami ne da tace me Sadiya zata yi dashi. Wani irin ciwo ne kwance can a ƙasan zuciyarsa wanda ba zai faɗuwa ba, tun a daren ranar yaso barin rayuwar gidan Daddy Bashir na har abada da zarar ya tuna Daddy da aydah sai jikinsa ya yi wani kalar sanyi na ban mamaki. Aydah za ta fi kowa shiga tashin hankalin rashinsa a kusa da ita, bai san meyasa zuciyarsa bata son abunda zai taɓa Aydah ba komai kankantarsa. washegari suna gama sallar Asuba, Siyama ta koma ta kwanta dan sai 2 zata fita lecture saɓanin Aydah da ta ɗora kanta akan bed ɗin ta yi nisa cikin tunani, dan jiya tare da Siyama suka kwana ɗaki ɗaya, lokaci ɗaya idanunta suka cicciko da ƙwalla ga kanta da take jin yana mata wani irin ciwo kamar zai fashe. Yaya Abba kawai take tunani a wannan lokacin Da gaske tana son ta je ta gansa sai dai tana tsoron mami, kasa daurewa ta yi daga ƙarshe sai da ta tabbatar baccin Siyama ya yi nisa sosai ta fice daga ɗakin da sauri take saukowa kan stairs banda faduwa babu abunda gabanta ke yi ko takalma babu a ƙafarta saboda kar ta saka ƙararsu ya fito da Mami ta kitchen tabi zuwa bangaren yaya Abba, tana addu'a Allah yasa ƙofar parlorn sa abude take. Ta kama handling ɗin tana murdawa ta ji ya buɗe wata ajiyar zuciya ta sauke ta shige cikin parlor ta mayar da kofar ta rufe a hankali babu wadataccen haske a parlor duk da haka idanunta basu kasa hasko mata yayan nata dake tsakiyar rug ya tattare jikinsa wuri ɗaya. Sai da gabanta ya fadi ganin irin kalar kwanciyar da ya yi tasan idan ya yi irin wannan kwanciyar to baya da lafiya a haka ta nufesa da sauri ta kai hannunta saman fuskarsa jin wani irin zafi yasa ta janye hannunta da sauri hannu tasa tana bubbugasa tana kiran sunansa. Sama -sama ya rika jin muryar Aydah akansa da sauri ya buɗe idonsa saboda ciwon kan da ya kwana dashi yasa idanunsa suka yi masa wani irin nauyi sai ƙoƙarin miƙewa zaune yake yana kallonta da mamaki, yana tashi zaune da kyar ta faɗa cikin jikinsa ta fashe masa da wani irin kuka mai taɓa zuciya da ruhi, cikin kuka take faɗin."Yayanmu baka da lafiya mu je asibiti kar wani abu ya sameka wai meyasa kake son zama da ciwo dan Allah."Runtse idonsa ya yi zuciyarsa na wani irin bugawa yana jin yadda hawayen Aydah ke sauka cikin ƙirjinsa shiru ya yi yana jin yadda take shesshekar kuka. "Babyn yaya Abba?'"ya faɗa cike da ƙarfin hali dagowa ta yi tana kallonsa ya ware mata manyan idonsa yasa ɗayan hannunsa yana tare hawayen idanunta "wai waya faɗa maki budurwa tana kuka?"yasan kalmar data tsana kenan a kirata da budurwa ai kuwa ta haɗe rai sosai ta turo masa bakinta ganin haka sai da ya saki murmushi, to na ji har yanzu ke baby ce kije ki yi shirin zuwa school zan fito na kaiki idan na saukeki sai na karasa clinic a dubani."a hankali ta saki murmushi ta miƙe tsaye tana faɗin."na kawo breakfast muyi anan yayanmu?"dan shiru yayi yasan da yace a'ah itama tana iya cewa bazata ci ba, gyada mata kai kurum ya yi da farin ciki Aydah ta juya ta koma part ɗinsu kai tsaye ɗakinta ta koma wanka tayi ta saka uniform ɗinta tana ta addu'a kar su haɗu da Mami har ta wuce makaranta sosai take jin haushin Mami, a kitchen ta samu huwaila mai aiki tana soya doya, Aydah ta tambayeta ta soya wata bayan wannan ta nuna mata cooler ta wanko plate ta saka masu ita da yayan nata anan ta haɗa masu tea cup biyu sai da taje ta fara kai tea lokacin bai parlor ta koma ta dauko plate ɗin soyayyar doyar, zama ta yi a parlor tana jiran yaya Abba har na kusan minti goma tana ta kallon tea ɗin kar ya huce. Master bedroom ɗinsa ta nufa tsayawa tayi a bakin ƙofar tana knocking sai da aka bata izinin shiga ta shiga tsaye yake a bakin mirror dressing shima yana shiryawa ya yi wanka cikin ruwan tokan japaness suit da suka yi masa kyau suka fito da kwarjininsa sosai sai dai duk wanda ya kalli fuskarsa yasan baya cikin natsuwarsa a bakin ƙofa ta tsaya tana ganin yadda gadonsa ya yi wani irin suqeezing ƙarasawa ta yi tana gyara masa gadon a ɗakin ya barta ya koma parlor ita ma bata jima ba ta fito tare suka yi breakfast ƙarfin hali kawai yake dan wani irin zazzaɓi yake ji da ciwon kai ko yawan magana baya son yi suna gamawa za ta koma ta mayar da kayan tana ƙoƙarin shiga ɗakinta suka ci karo da Mami, kallonta Mami take tun daga sama har kasa saukar da kanta ta yi tana gaishe da Mami."batare da Mami ta amsa ba take tamabayarta daga ina take dan ta ji kamar ƙamshin turaren Abba tare da Aydah, daga kitchen da haka ta juya ta shige ɗakinta tsaye tayi cikin ɗakin kamar zata yi kuka duk bata ji daɗin fitowar Mami ba kar ta hanata shiga motar yayan nasu. Kamar Mami ta san abunda take shiryawa zamanta tayi cikin parlor dan har kitchen ta samu Huwaila tana tambayar yaushe Aydah ta tashi?"nan ta faɗa mata tun ɗazu har tayi break fast ita da Yaya Abba, sosai ran Mami ya ɓaci daman tayi mamakin da taga Aydah da uniform karfe bakwai na safe ita da bata shiryawa da wuri zama ta ci-gaba dayi a parlor tana so taga ta inda Aydah za ta fito. *KIM'S AUTOMOBILE INDUSTRY LAGOS* "Good morning Abbu! "Morning my princess ya zance ganawar mu da CEO na Kamfanin moonlight tun kafin na yi tafiya zuwa Cotonou ya dace ace mun haɗu dashi anya kuwa kamfaninsu yana so kula wannan yarjejeniya ɗin?" Sai da Anaal ta sauke numfashi kafin ta ja kujerar dake gaban desk ɗin Alhaji Aliyu na uku ta zauna tukun kafin ta ɗora da faɗin "Daddy ko jiya na kira shi sai kawo min uzurinsa har ya yi insisting da a dage zaman har zuwa na wani ɗan lokaci, saboda ɗaurin aurensa da za a yi ranar juma'a ɗinan ta jibi. Har Alhaji Aliyu na Uku ya buɗe baki da zimmar magana kira ya shigo cikin ɗaya daga cikin wayoyinsa da yake wayar ya kebe ta ne saboda family and friends ya ɗauki wayar tare da duba sunan mai kira nasa magaji ƙarami ya gani sai kawai ya maida wayar batare da ya dauka ba ya ƙara gyara zamansa ya kalli Anaal ya ce "To shikenan babu damuwa tun da shine ya bukaci hakan. Sai dangane da Hamdallah motors dake garin Kaduna jiya na amsa kira Chairman na kamfani yana buƙatar manyan motoci sababbin samfur ki yiwa Zeeyad magana ya tura masa waɗanda muke da shi kuma Zaheed ki faɗa masa ya kira mr obina ya faɗa masa wa'adin da ya nema mu yi masa lamuni ya cika ya tura mana da kuɗaɗen mu ko kuma na haɗa shi da lawyer mu. Wayarsa ce ta sake ringing a wannan karon daga Gimbiya Zainaba ce ta kira shi wacce daga sarki Mahmood sai ita da sauri ya yi picking call ɗinta saboda yasan ita bata kiransa sai da kwakkwara dalili "Aminci Allah ya tabbata a gare ki yaya Gimbiyar Kudu lafiya! "Wa'alaikum salaam! Tare da kai sarkin sabon birnin! "Yaya Gimbiya ya na ji muryarki wani irin Allah yasa dai lafiya?" "Babu lafiya Aliyu yau da safe muka tashi da wani mummunan al'amari mai martaba Mahmood ne ya tashi da wani mummunan rashin lafiya ko ɗan yatsansa baya iya ɗagawa gashi nan kwance magashim! "Innalillahi wa'inna illahim raji'um! in-sha-Allahu gani nan zuwa sannan yaya Gimbiya ku kwantar wa mai babban ɗaki da hankali kinsan tana da hawan jini dole sai ku yi ƙoƙari wajen kwantar da hankali. "Uhm! Kamar ka manta da jaruntar mahaifiyarka, duk yadda ta shiga tashin hankali ba zai taɓa nunawa akan fuskarta ba. A halin yanzu ita ce ma ke kwantar wa da iyalinsa da hankali musamman Fulani ƙarama, sumanta biyu a lokaci guda ta dawo abar tausayi. "Subhanalillah! Lallai al'amarin ba mai daɗi bane in-sha-Allahu nan da five hours za mu iso. "To shikenan Allah ya tsare ya kawo ku lafiya Aliyu. Daga haka ya kashe wayar yana mai dafe goshinsa yana sauki numfashi da sauri Anaal ta taso ta zagaya wurinsa ga baki ɗaya jikinta ya yi sanyi cikin mutuwar jiki ta ce "Abbu me ya faru ne a masaurata?" Sai da ya ƙara sauke numfashi kafin ya ciro kai ya kalli fuskarta muryarsa a sanyayye ya furta "Mai martaba ne. "Subhanalillah! "Ki je maza ki faɗawa Zaheed ya siya mana ticket ta online su shirya gaba dayanku za mu wuce tare. Amma kada ki faɗawa musu mahaifin su ne bashi da lafiya ki ce dasu mai babban ɗaki ce banaso su tashi hankalinsu. "To Abbu! Ta faɗa da sanyi murya kana ta nufi kofar fita da sauri ta isa office ɗin Zaheed, cikin sa'a ta tarar dasu duka suna wani aiki a laptop ɗin Zaheed sai da ta tattara natsuwarta wuri ɗaya kafin ta isar musu da sakon Abbu. Dukansu jikinsu ya yi sanyi nan take Zaheed ya siya musu ticket ɗin Jirginsu zai tashi ƙarfe biyun rana, saboda haka dukansu suka tashi daga office gida suka wuce suna jira time ɗin tafiyarsu ya yi ƙarfe 1:40pm suka isa airport. *ALH BASHIR MANSION* A hankali Aydah ta sake leƙo da kanta ta jikin ƙofar ɗakinta taga still Mami ta nan zaune wannan shine karo na hudu kenan da Aydah tana leƙowa. Wani irin abu ta ji ya tokare mata maƙoshi har ga Allah tana bukatar yaya Abba ya kaita school she wants to bws with him this morning tana so ta sake bashi haƙuri akan abunda jiya Mami ta yi mishi, Mami da ta gaji da zama ta miƙe ta nufi ɗakin Aydah ta jikin ƙofar Aydah ta hango ta tai sauri maida ƙofar ɗakinta, ta murza key, tana ji Mami tana knocking tare da kiran sunanta amma ta yi biris da Mami ta gaji da dukan ƙofar ta yi ƙwafa tare da nufar ɗakinta dake upstairs. Aydah tana ji sawun tafiyar Mami ta buɗe ƙofa a hankali cikin sanɗa ta fito tana fita ta buɗe ƙofar fita daga main parlor ta kwasa da gudu ta nufi bangaren AB daidai ya fito suka ci karo sai da kanta ya bugi jikinsa ta yi baya ta yi tangal-tangal za ta faɗi daman can ba wani jikin kirki ne da ita ba ya yi sauri taro ta, ta hanyar kamo hannunta fisga ɗaya yai mata sai gata kwance cikin jikinsa. Sai kawai ta ƙanƙame shi tana shaƙar ƙamshin daddaɗan turarensa wanda yake saukar mata da wani kalan natsuwa. A hankali ya ciro ta daga jikinsa amma sai ta ƙara komawa jikin nasa "yaya Abba barni na ci-gaba da shaƙar ƙamshinka har a busa ƙaho. Duk da yana cikin damuwa hakan bai hana masa dariyar shirmenta ba, da yake ya saba da wannan halin nata na shaƙar ƙamshinsa ciki ma yanzu ta rage yi masa haka ada yana tsakiyar baccinsa zai ji hancinta tana shinshinar sa kamar magge, shiyasa a wasu lokuta yake kiranta da maggen yaya Abba. "Kin ga Babyn yaya Abba bana so shirme school fa za ki tafi ko so kike ki makara garin wannan childishness ɗin naki yi latti a yi miki duka?" Yana magana ne tare da sake ciro ta daga jikinsa ya kama hannunta suka nufi parking lot "Yaya Abba ka ga yadda yau ɗinan ka yi wani irin nau'in kyau na musamman?" Bai bata amsa ba sai da ya shiga mota ya yi warming ɗinta kana ya fita daga parking lot ɗin, Balmo maigadi ya buɗe masa gate. "Yaya Abba ko ba ka yarda da ka yi kyau bane sai magana nake yi ka yi shiru? Ta yi magana cikin shagwaɓaɓbiyar murya tana wani turo baki. "Baby me kike so nace?" "Ka yi haƙuri yaya Abba about yesterday night daga ni har yaya Siyam ba mu ji daɗi abinda Mami ta yi maka ba ka ɗauki shi a matsayin kuskure da sharrin zuciya saboda Mami tana ƙaunar ka sosai wannan so-called daughter ɗinta ne ke so haddasa fitina a tsakanin ku. Amma kowa zai iya bada shaida akan kyawawan halaye Mami. Ɗan ƙaramin murmushi ya yi wanda ya tsaya iya laɓɓansa, sai da ya kalli innocent face ɗinta kana ya yi concentrate tukinsa. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/20/2023, 11:03 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*:Jeddah3256 Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 033. Ganin yanayinsa wannan karon sai suka zauna zaman shiru daman kuma ita ce mai masa surutun yau bata dame sa da surutu ba ta kwantar da kanta cikin seat ɗin motar ta kurawa titi kawai ido, dan kallon gefenta ya yi ta taimaka masa ma a haka da tayi shiru dan yana son ya ji shiru acikin kan nasa na ɗan wani lokaci har suka karasa bakin gate ɗin makarantarsu. Yana gama parking motar ya dauko wallet ɗinsa ya ciri 2k aciki ya miƙa mata girgiza kai ta dan yi tana faɗin."Akwai kuɗi a tare dani. Harararta ya yi ya buɗe hannunta ya saka mata kuɗin, murmushi ta yi sosai ta karaso gafda fuskarsa har suna jin numfashin juna ta sumbaci gefen fuskarsa a hankali ta furta "i love you Yayana."murmushi ya yi mata da haka ta balle marfin motar ta rufe masa tana daga masa hannu. Shima hannun ya daga mata har lokacin murmushin cikin fuskarta bai bace ba baya son wannan murmushin ya ɓace daga fuskarta har lokacin da numfashinta zai tsaya yana son kannen nasa da dukkan zuciya da ruhinsa ta yadda baki ba zai iya misalta shi ba, acan ƙasan ransa Aydah tana da wani matsayi mai girma a zuciyarsa wanda ba zai faɗu ba. Haka ya ja motarsa ya ƙarasa office wannan ranar ma cikin tunani da damuwa yayi ta kusan ƙarfe goma sha biyu na rana aka tura kofar office ɗin nasa yana kwance cikin couch ɗin dake cikin office ɗin nasa da mamaki yake kallon mutumin da ya shigo office din nasa. Kallonsa kawai Daddy yake yana ganin yadda yaron nasa ya yi wani irin zuru-zuru gaba ɗaya jiya bai saka shi a idanunsa ba da gaske yaga yaron nasa ya yi wata irin rama wacce za ka ganta kwance cikin idanunsa. Idan ka yi masa farin sani kuwa za ka tabbatar akwai damuwa sosai a tattare dashi. miƙewa tsaye AB ya yi kai tsaye ya nufi Daddy, yana ƙoƙarin wadata fuskarsa da murmushi yake faɗin."Daddy meyasa baka kirani a waya ba na sameka a office ɗinka ai ba ma sai ka zo ba. "Menene asalin damuwarka Abba?" Daddy ya faɗa yana kafesa da idanun dake kassara duk wani tunanin AB. Cikin rawar murya AB ke faɗin. "Daddy duk meya kawo wannan maganar? Yadda yake magana za ka san baya cikin hayyacinsa kuma a rude yake, Daddy ya nemi wuri ya zauna ya ɗora kafa daya akan ɗaya yana girgizasu a hankali."shi dai AB yana tsaye a wurin tamkar wanda aka dasa banda faduwar gaba babu abunda yake ji a wannan lokacin."Baka rasa ci da sha ba kana da gata kana da iyaye da yan uwa a zagaye dakai kashe kanka kake so ka yi ne?" Wannan karon Daddy ya faɗa da ɗan ɗaga murya, zama Abba ya yi gefen Daddy yana riko duka hannayensa biyu bai san taya zai soma yiwa daddy bayani ba. Idan kuma ya faɗa masa asalin damuwarsa bai san tayaya zai dauki al'amarin ba kenan karar Mami zai kai wurin mahaifinsa kararta zai kai da bai yiwa kansa adalci ba maccen da ta shekara talatin tana hidima dashi bai kamata ya ji haushinta ba koda na minti ɗaya ne, koda kuwa yayyanka naman jikinsa take a kullum."Ko kuma hukuncin da na yanke akanka ne yai maka nauyi!" Daddy ya faɗa da raunin muryar da ta dawo da AB duniyar tunanin da ya faɗa da sauri AB ya shiga girgiza kai yana faɗin."Har abada dadydy baza ka yanke hukunci akaina naki karbarsa ba komai nauyinsa zan karba da hannu bibbiyu nayi maka biyayya Daddy. "Yanzu ka tashi mu je gida na soke zuwanka zuwa office har na sati biyu ka huta. Wani irin fargaba da tashin hankali zuciyarsa ta kara shiga lokaci ɗaya, komawarsa gida shine babban tashin hankalinsa a yanzu yana gujewa duk wani abu da zai haɗasa da Mami, wannan umurnin da Daddy ya basa ko kaɗan bai masa daɗi ba. Ga matsalar Sadiya a gefe dake son ta zamar masa matsala cikin rayuwarsa har yau kalamanta basu daina yi masa yawo cikin kunnuwansa ba sun samu wurin zama sosai a ƙasan zuciyarsa. Har yau bai daina mamakin kalaman Sadiya ba. Kananan shekarunta bai ci ace ta san wa'yannan manyan kalaman ba ko Rumaisa da ta girmeta bai taɓa tunanin ita da suka kwashe shekaru biyar a tare irin waya'annan kalaman basu taɓa haɗasu ba. Duk kuwa budewar idon Rumaisa da wayewarta wacce tayi karatunta na degree a abroad. Bai san wanda ya canja duniyar ƙanwarsa ba lokaci ɗaya. Ya dauki car key ya dauki suite jacket ɗinsa da ya cire ya sargafeta akan hanger ya saka ya kwashi wayoyinsa da car key ɗinsa har lokacin Daddy na tsaye yana jiransa. A tare suka fito suka nufi cikin parking lot da kansa AB ya buɗewa Daddy bayan motar, mai makon haka Daddy ya mayarda kofar ya rufe ya buɗe frontseat ya shiga murmushi kawai AB ya yi ganin baturen Daddyn nasa a gaban mota har lokacin da ya shiga motar murmushi bai bace cikin fuskarsa ba, "Za ku cigaba da zama wancan gidan ne ko kuna bukatar canji? Daddy ya yi maganar batare da ya kalli gefen da AB yake ba hasalima hankalinsa na kan titi, Daddy ina ganin kawai mu zauna acan tunda ko kwana bamu yi ba ranar. Ya karasa magana da raunin murya, Daddy ya numfasa yana faɗin."naji ra'anyinka sauran Mamana idan tana bukatar a canja kayan daki za a canja. Duk lokacin da Daddy ya dauko masa zancen aurensa da Aydah jin yake duniyarsa na birkicewa wannan karon har cikin gida ya bi Daddy dauke da briefcase ɗinsa bai yi gigin zuwa bangarensa ba dan kauda duk wani zargin da Daddy zai yi masa Sadiya kaɗai ce a parlor har lokacin kayan bacci ne ajikinta cikin sanyin murya take yiwa Daddy sannu da zuwa tana mamakin dawowarsu a irin wannan lokacin haka ta tsayar da fuskarta cikinta AB wanda bai yadda da ya kalli gefenta ba zuciyarta wani irin bugawa take da sauri da sauri sosai ya yi mata kyau yanayin shigarsa yasa ta ji yana neman dagula duk wani lissafi nata, zuciyarta ta ji tana matsewa wuri ɗaya cikin rawar murya Sadiya ke faɗin."Ina kwana yaya Abba.!" bai kalleta ba ya amsa saboda Daddy dake tsaye har lokacin, Daddy ya juya ya amshi briefcase ɗinsa yana faɗin "ka je ka huta na rabin awa lokacin sallah ya matso ka fito mu shiga masallaci a tare idan mun fito mu yi lunch, a tare ɗagawa Daddy kai Kurum ya yi ya juya yana barin cikin parlor da wani irin taku da Sadiya ke jinsa har cikin gangar jikinta da duka ruhinta. Sosai Mami ke kallon mai gidan nata bai saba dawowa gida da tsakiyar rana ba, sai dai har ya gama rage kayan jikinsa bai yiwa Mami bayanin ko kalma dayya ba har kuma lokacin Mami na tsaye tana kallonsa ya juya yana kallonta."Mariya daga yau na dakatar da Aydah daga zuwa makaranta abarsa zuwa wani satin zan faɗawa Abba, sai ya je ya yiwa shugabar makarantar bayani. numfashin Mami kusan tsayawa yaso ya yi na wucin gadi jin abunda Daddy ya faɗa. Da gaske dai wannan auren sai Daddy ya kullasa ko hankalinsa zai kwanta ya kamata fa tasan abu yi gashi lokaci yana ta tafiya. fuska babu yabo babu fallasa Mami ta ce."Insha Allah! juyawa tayi tabar cikin bedroom ɗin da wani irin kallo Daddy ya bita dashi tana fita shima ya nufi cikin bathroom. *MADAWAKI MANSION* "Kashe kanki ki keso yi Rumaisa akan kankanuwar damuwar da bata taka kara ta karya ba wai shin baki yadda dani bane ?"cikin wani irin rawar murya idonta na cika da kwallah take faɗin "Na yadda dake Ammi auren da zai yi shine babban damuwata Ammi idan ya auri yarinyar nan zuciyata za ta iya bugawa. Ta faɗa da wani zafi mai dauke da yanayin kishi cikin muryarta. "ke fa dadina dake sakarya ce akan wannan yaron bakida control ko kaɗan ki bari mu gama maganin wannan matsalar kafin mu dawo kanta. Yanzu ki fito ki ci abincinki ko na saka zuwaira ta kawo maki a daki?"cikin sanyin murya Rumaisa ta ce "Bara na watsa ruwa zan fito yanzu shafa kanta Ammi ta yi tana barin ɗakin, Allah ya gani tana son yaranta bata haɗa ƙaunarsu da kowa ba a duniya, dole ta nemo aminiyarta zulai a waya kafin Abban Rumaisa ya dawo daga kasar Thailand so take komai ya daidaita bata son tashin hankalin yaran nata ko kankani bayan fitowarta daga ɓangaren Rumaisa nata ɓangaren ta nufa cikin bedroom ɗinta ta ƙarasa ta ɗauki wayarta ta shiga kiran aminiyarta Hajiya zulai har ta katse bata dauka ba ɗan tsaki Ammi taja ta rasa meyasa zulai bata baiwa wayarta muhimmanci ka yi ta kira bata dauka, tana cikin wannan tunanin Hajiya zulai ta kira ɗagawa ta yi "afuwan hajjaju na saka wayar a caji kin san yanayin unguwarmu ba a samu wutar lantarki ko minti biyar ba tayi ba da dawowa na saka caji. batare da Ammi ta saurari surutun da Hajiya zulai ke yi mata ba tace "kina jina Hajiya zulai?" "Eh! Ina jinki" Zuwa bayan la'asar zan fito da driver zamu biyo ta gidanki za ki rakani wurin malamin nan naki naga aikinsa yana kyau. Wannan karon ma wani aiki zai yi min, da farin ciki sosai a muryar Hajiya zulai take faɗawa Ammi sai ta ƙaraso ta san ita ma za ta samu kasonta daman kwana biyu aljihunta yayi kasa tunda Allah ya haɗata da miji ɗan iska. Da haka suka yi sallama kowanne su ya sauke wayar. *MASARAUTAR KUDU* Bayan jirgin dasu Alh Aliyu na uku ya yi landing direbansa ne ya zo ya yi picking nasu daga airport direct masauratar suka yo, sai da suka shigo cikin masarautar sannan Alh Aliyu ya ciro wayarsa ya kira yaya Gimbiya ta faɗawa mishi mai martaba yana kwance ne a babban asibitin masarauta har kawo yanzu babu wani takamaiman labari daga likitoci da ke kansa. Kaitsaye ya umurci direba da ya sauke su a kingdom specialist hospital a bangare vip suka nufa domin anan ne mai martaba yake kwance cikin hali rayuwa ko mutuwa bai san inda kansa yake ba numfashi dake fita daga gangar jikinsa ta jikin na'urar da aka saka masa zai ba ka tabbacin yana raye. A babban parlor dake vip suka tarar dasu yaya Gimbiya, Magaji ƙarami, wambai, Galadima, Ciroma, har ma da madaki sai kuma Fulani babba ita kuma Fulani karama tana can ɗakin da aka kwatar da ita har yanzu bata gama dawowa hayyacinta ba. Idan ka ga yadda Galadima da Ciroma suka tashi hankulansu ba za ka taɓa zargin suna da sa hannu a kwanciyar sarki ba. Walking majestically Alh Aliyu ya iso wajen su cikin izzar nan da ta gama zagaye jinin jikinsa ya yi musu sallama tare da tambayar mai jiki. Ciroma ne ya bashi amsa da cewa "Ba za mu iya fadar yanayin jikin nasa kaitsaye ba domin har yanzu ba mu ji daga bakin likitoci ba. Mu dai ga sai gayyato manyan likitoci suke yi daga wajen masarauta yanzu kuma Yarima babba ya iso daga Abuja yana nan ciki tare da tawagar likitocin. Naunnayar numfashi Alh Aliyu na uku ya sauke kafin ya nemi kusa da yaya Gimbiya ya zauna Zaheed da Zeeyad suka nufi Magaji ƙarami suna neman karin bayani a wurinsa domin yanzu sun gama fahimtar abunda ke faruwa. Suna nan zaune har yamma ta yi sallah kawai ke tashe dasu sai lokacin yarima babba ya fito daga ɗakin da mai martaba yake ya yi musu bayani takamaiman abinda ke damunsa, jininsa ne ya hau sosai shine ya haifar masa da collapse ɗin da ya yi daman ya dawo daga sallar asuba ne yana fitowa daga masallaci ya yanke jiki ya faɗi. Wani kalan kallo yaya Gimbiya ke watsawa Yarima babba kafin ta tashi a fusace tana faɗin "Anya kuwa Yarima babba kai da tawagar abokan aikinka kunsan aikin ku kuwa? Saboda duk mai cikakken hankali ya dubi mai martaba zai fahimci jifarsa ne aka yi babu wani hawan jini da yake da. "Haba! Yaya Gimbiya ya za ki ce haka Shekara ta nawa ina wannan aiki sai akan mahaifina ne zai faɗi fake results?" "To idan ma ba ka taɓa faɗa ba a wannan karo ka faɗa ba daidai ba. Wannan aikin magauta da mahassada ne masu son gani bayan mai martaba. Ta ƙarashe magana tana sharar hawaye da gefen mayafin tsadaddiyar Abayar dake jikinta. Da sauri Yarima babba ya isa kusa da ita yana faɗin "This is not a worry since we have already found out what is wrong with him if he continues to receive the medicines and doses that will be given to him immediately he will get back to his normal health. A sheƙeƙe Yaya Gimbiya ke kallonsa kafin ta ja siririn tsaki rai bace ta ce. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/22/2023, 11:29 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*:Jeddah 3256 Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 034. *MASARAUTAR KUDU* "Dallah! Yarima babba ka rufe mana baki ga baki ɗaya halayenka dana Ahmadu da Aliyu a koda yaushe sun sha bambam da na masarautar kudu, kun ri ga kun ɗauki ɗabi'un nasara kun ɗorawa kawunan ku. Idan zan shekara ina maka bayani ba fahimta za ka yi ba, don haka ka riƙe saninka nima na riƙe nawa, zan je na sami mai babban ɗaki ita za ta fahimci ni. Gani yadda yaya Gimbiya ta rikice da faɗa daman can ko acikinsu ita ɗin mafaɗaciya gaske ce wambai ne ya kalle ta yana faɗin "maganar Gimbiya abar dubawa ce tun da muke da mai martaba ba a taɓa binciken lafiyarsa aka tarar dashi ɗauke da matsala ta hawan jini ba. Duk da zai iya kamuwa da ita faratt ɗaya. Ke Gimbiya ki yi haƙuri mu jira zuwa wani ɗan takaitaccen lokaci idan har treatment ɗin da suke masa ba mu ga wani cigaba ba, tofa dole Yarima babba ka haƙura mu nema masa maganin gargajiya. Wannan goyon baya da Gimbiya ta samu a gun wambai ya kawo karshen ce-ce-kuce da suke yi tsakaninta da Yarima babba, ta dauki jakkarta ta koma cikin masarauta, Aliyu ya miƙe ya nufi ɗakin da mai martaba yake sosai ya kaɗu da gani hali da yake ciki shi ba matatccen ba shi ba mai rai ba domin kuwa hatta da numfashinsa da taimakon na'ura ne yake sauka shima kaɗan-kaɗan. Ya dau lokaci tsaye a gefensa kafin ya fito daga ɗakin ya kira Yarima babba suka koma gefe "Yarima idan ban ga wani cigaba ba a jikinsa nan da sati ɗaya to kasani zan dauke shi na fita dashi ƙasar waje (abroad) domin alama ce dake nuna ba za ku iya ba. "Amma ranka shi dade shi fa ciwo faratt ɗaya yake shiga sauki kuma sannu-sannu yake zuwa. "Yarima wannan damar ta sati ɗaya da na ba ku shima don ya kasance mahaifi ne agare ka da ba don haka ba, da tuni na fara cuku-cuku nema mana visa. "Shikenan ranka shi dade ai mu fatan mu duk inda za a kai shi ya sami lafiya. Daga haka Aliyu na uku ya juya Anaal ta yi sauri bin bayansa suna fitowa farfajiyar asibitin ya dube ta tare da faɗin "Koma ciki ki kira min twins. Anaal ta amsa da to kana ta koma sai gashi sun zo tare batare da ya yi magana ba ya nuna musu mota, su ma ba su yi gardama ba suka shiga. Gimbiya tana zuwa kaitsaye ta wuce bangaren mai babban ɗaki a babban parlornta ta tarar da ita ta kishingiɗa bayi biyu na durƙushe suna mata massage ɗin ƙafafuwanta hannunta riƙe da counter tana yiwa Annabi sallati. Duk da a can ƙasan zuciyarta damuwa ce shimfiɗa acikinta dangane da wannan lalura da mai martaba ya waye gari dashi amma ko kaɗan fuskarta bata bayyanar da damuwarta ba. Mai babban ɗaki macce ce jarumar gaske duk bin kwakwafin ka ba za ka taɓa fahimtar rauninta ba, bata nuna gazawar ta a fili. Duk girman al'amari idan ya tunƙaro ta ko iyalinta ta kan yi tsayin daka har ta kawar da wannan matsala. Gimbiya ta nemi wuri ta zauna yanayin ta kaɗai zai tabbatar maka da tana cikin damuwa. "Barka da hutawa ranki shi dade! "Sannu Gimbiya ya kika baro jikin ɗan uwan naki?" "Babu wani sauyi da yadda an ka kaishi sai dai abinda Ubangiji ya yi. Gimbiya ta ƙarashe magana hawaye na bin kumatunta, shiru mai babban ɗaki ta yi na wasu mintuna kafin ta ce "Ki kwatar da hankalinki Gimbiya komai da kike gani muƙadarri ne daga Allah subhanahu wata'ala, yana daga cikin rukunan imani ɗan adam ya yarda da ƙaddara mai kyau ko akasin hakan. "Ranki shi dade ni fa a nawa fahimta ciwon mai martaba bana asibiti bane duk wanda yaga yadda yini guda curr ya dawo sai ya zubda masa da hawaye, sunan kawai yana numfashi ne amma bambancin sa da matatccen kaɗan ne. "Ki sani Gimbiya babu wani ɗan adam da yasa isa ya yi nufin wani mahaluƙi da cuta face ubangiji ya yi nufin hakan koda kuwa hasashen ki ya kasance gaskiya to ki saka aranki jarabawa ce Allah ya nufi ɗan uwanki da ita domin ya gwada ƙarfin imaninsa, ki cigaba da yi masa addu'a idan yana da sauran kwana a gaba Allah ya tashi kafaɗarsa idan kuma wa'adin sa ne ya yi to ubangiji ya yi masa masauki a gidan aljanna firdausi. Ga baki ɗaya jikin Gimbiya ya yi matuƙar sanyi tana hamdallah can cikin zuciyarta da irin mahaifiyar da Allah ya basu macce mai tawakalli mai yarda da ƙaddara, lallai samun uwa kamarta babban abin alfahari ne. Kafin Gimbiya ta sake yi magana Aliyu na uku ya turo ƙofa ya shigo yayin da yaransa ke biye dashi a bayansa tun kafin ya ƙaraso bayi da ke yiwa mai babban ɗaki massage suka yi sauri tashi tsaye, kusan a tare da suka gaida shi bai ko kalli gun da suke ba ya ɗaga musu hannu da sauri suka nufi ƙofar fita, sun san da cewa idan har ya shigo bangaren mahaifiyarsa duk wata baiwa fita take yi. Ya durƙusa kusa da ita ya kwashe gaisuwa ta amsa mishi babu yabo ba fallasa kana ya nemi kusa da ita ya zauna twins da Anaal suka gaidata sai da ta ƙare musu kallo a sheƙeƙe kafin ta amsa tana mai taɓe baki. Shiru ya biyo baya kafin mai babban ɗaki ta tashi daga kishigiɗa da tayi ta kalli twins da Anaal dake zaune akan three seater sun saka Anaal a tsakiya suna kallo wani sabon samfurin mota da take nuna musu a wayarta "Yanzu kai mai sabon birnin rayuwar da ka zaɓawa Maryama kana gani ka yi daidai kenan? Yarinya ta kai muzali aure amman ka zuba mata ido sai yawon neman duniya kawai tasa a gaba. "Allah ya taimake ki har yanzu bata sami miji bane da zarar Allah ya kawo mata miji babu abinda zai hanani aurar da ita ai nima burina ta yi aure. Aliyu na uku ya yi magana cikin sanyi murya tare da sadda kansa ƙasa. "Ya dai kamata ka yiwa kanka faɗa mai sabon birnin ka kuma tuna da mutuncin mace gidan mijinta. A wannan karo yaya Gimbiya ce ta yi wannan maganar kallonta kawai ya yi ya kauda fuska bai ce da ita uffan ba. Anaal da twins suna gani an fara wannan zance suka sulale daga parlon. Ci-gaba da tattauna rashin lafiyar mai martaba suka yi yayin da yaya Gimbiya ke goyon bayan a nema masa maganin gargajiya, shi kuma Aliyu yana faɗin a fita dashi ƙasar waje zai fi. Ciroma yana gani Aliyu na Uku ya bar asibitin ya yiwa Galadima alama da idonsa suka fi ce acan gidan gona Ciroma da suka saba haɗuwa suka nufa, cike da zallan takaici Ciroma ke kallon Galadima kafin cikin fushi da fusata ya ce "A ina ne aka sami wannan kuskure shin daga gare ka ne kuma daga wurin Fulani karama cikkaken bayani nake buƙata Galadima!. Ciroma ya ƙarashe magana a tsawace, shima Galadima cikin dakakkiyar murya ya ce "Wannan ne kum bansani ba domin yadda ka yi min bayani a aiwatar da aikin haka na yi mata samun cikakkiyar amsar wannan tambayar dole sai a bakinta. *MADAWAKI MANSION* Cikin shigar alfarma Ammi ta fito ta saka bakin glass ta lulluɓe ƙwayar idonta wanda ya mamaye rabin fuskarta kai kace bata aje Rumaisa yar shekara Ashirin da bakwai ba a duniya da kuma wasu katon saurayi a gefe, cikin dinning area ta samu Rumaisa tana cin abinci a natse da waya a hannunta karar takalman da ta ji yasa ta daga kai tana baza idonta a sautin da take jin fitowarsu ta nata kallon mahaifiyarta yadda taga ta yi mata kyau sosai tamkar wata 'yar shekara talatin har lokacin da Ammi ta karaso wurin murmushi bai bar akan fuskar Rumaisa ba duk da yanayin da zuciyarta ke ciki."kin yi kyau sosai Ammi kamar baki aje kamar Yaya Safwan ba, murmushi Ammi ta yi tana ɗan shafa kan Rumaisa cike da so da kulawa take faɗin."Zan fita ba dadewa zan yi ba."Da sauri Rumaisa ta ce."Ammi ko na shirya na biki na gaji da zaman gidan nan wallahi, da sauri Ammi ke faɗin."No! ki yi zamanki yanzun nan zan dawo. Ba dan Rumaisa taso ba ta yiwa mahaifiyarta fatan sauka lafiya driver na ganin fitowar Ammi daman yana zaune tareda maigadi suna hira da sauri ya karaso yana gaisheta da Respect ta amsa nan take wani tunani ya shiga kan Ammi yafi mata sauki tayi driving da kanta akan taje da driver,kasancewar inda za taje wurin sirri ne kawai ka yi zamaka Lawi zan yi driving da kaina."Lawi ya russuna tamkar zai yi mata sujada yana mata fatan sauka lafiya da haka ta shige motar ta yi mata key kafin ta karaso tuni maigadi ya buɗe mata gate kasancewar bata da cash sosai koda ana bukatar kudi sosai wurin da za taje dan tasan kuɗi ba matsalarta bane ta tsaya gefen hanya ta ciri kudi wurin mai p.o.s tana gafda isa layin gidan Hajiya Zulai ta kirata a waya ta faɗa mata ta fito gata ta kusa karasowa dan ba zata shiga ba tasan suna iya kara bata lokaci, ko minti biyu ba tayi ba a bakin kofar gidan Hajiya Zulai ta fito ta buɗe gaban motar tana yiwa Ammi kirari a hanyarsu ta zuwa wurin Malam take baiwa Hajiya Zulai labarin matsalar Rumaisa, "in banda dan yau da neman fitina Rumaisa me za tayi da marar asali, ke kuma sai kika wani biye mata a haka zata auri mijin da bakuda tabbacin yana da asali mai kyau."Ammi na juya sitiyari cikin kwarewa take faɗin."i don't bloody care akan asalinsa in har yarinya ta za ta auresa ta dawo cikin natsuwarta ban damu da asalinsa ba tunda marikin nasa yana da kudi ba wai kananun mutane bane." Aran Hajiya Zulai tana jinjina son 'ya'ya irin na Ammi irin sune in har za ka kwantar da kanka ka nunawa 'ya'yansu soyayya za su ba ka duk abunda kake so a duniya in har baifi karfinsu ba haka kuma za su so ka su kaunaceka duk akan soyayyar da suke yiwa 'ƴa'yansu. Mutane biyu suka samu kafin su zo kan layi, sai da layi ya kawo kanta suka shiga wani babban daki da carpet kawai ne acikinsa sai tarkacen su na kayan tsibbu daga gefe suka zauna Zulai ta russuna tana gaishesa da kalar gaisuwar da ake yi masa. Itama Ammi ta yi yadda Zulai ta yi ya amsa masu da kai yana ta can doguwar casbahar hannunsa batare da ya yi magana ba. sun kwashe kusan mintuna goma a haka ya dago yana kallon tsakanin fuskar Zulai da Ammi, kamar Zulai tasan tunanin da yake da sauri ta nuna Ammi a hankali ya miƙa mata doguwar casbahar hannunsa ta rike shima ya rike gefe runtse ido ya yi yana karanto wasu kalamai na tsafi. Hakan ma sai da ya dauki wani tsawon minti goma kafin ya bude idanunsa wanda aka saka masu bakin kwalli acikin har kwallin yaso yayi masu yawa, ya zuba cikin fuskar Ammi a hankali ya shiga karantowa Ammi matsalarta da mamaki Ammi ke kallonsa ganin yadda ya karanto lokaci ɗaya batare da ta buɗe baki ta yi masa bayani ba. Ko a zuwan farko Zulai ta aiko wannan shine karo na farko da ta haɗu dashi da sauri ta daga masa kai."yanzu ya kike so ayi?" Da sauri Ammi tace "maigidana yana da kafiya sosai idan yace abu babu wanda ya isa ya canja ra'ayinsa akan abun nan ina so a saka masa son auren yaron da yarinyar mu ke so aransa ya ji duk duniya baya da natsuwa har sai yaga wannan auren ya tabbata a tsakaninsu. "bukatarki ta biya. Cikin kankanin lokaci ya buga kasa sai ga bakar laya ta bayyana ya daga layar ya miƙa mata da hannu biyu ta karba acan kasan katifa daidai wurin da yake dora kansa "har abada za ya dinga yin abunda kikeso kuma yarinyar ki za ta auri wannan yaron." Godiya Zulai da Ammi suka rika yi masa, kafin Zulai tace "To malam nawa kuɗin aiki?" "Za ku aje dubu ɗariari idan aiki ya yi za ku dawo ku bada ragowar Ammi ta balle zip diyn handbag ɗinta ta ciro rafar kuɗi na naira dubu ta aje agabansa ,da haka suka kara yi masa godiya suka fito Ammi bata samu natsuwar da take buƙata ba sai da ta shiga mota da murmushi cikin fuskar Zulai take faɗin."Kinga riba biyu kenan ga auren auta ga kuma za ki cigaba da juya mahaifinsu yadda kike so daman can juyasa kike sai dai wannan malamin yafi malamin da kika sani karfi. "Kin san har na matsu ma ya dawo saboda ga baki ɗaya a kwanakin nan Rumaisa ta firgice bata da wata natsuwa a tattare da ita har gida Ammi ta kai Zulai ta ciro dubu goma ta bata. Ta rika yiwa Ammi godiya. "Gobe wara haka angon baby kake fa?"Abdulkarim ya faɗa da muryar tsokana wani shegen kallo Ab ke yiwa Abdulkarim tun bayan la'asar yana tare da Abdulkarim idan kuma ya tuna gobe za a daura aurensa da Aydah sai ya ji komai dake zagaye dashi yana birkicewa cikin duniyarsa miƙewa tsaye ya yi yana yiwa Abdulkarim wani malalaci kallo, kafin yace "Ni na kawo kaina shiyasa za ka rika fadaymun duk wata magana da za ta fito daga bakin ka ba laifinka bane. da haka ya fice daga ɗakin na Abdulkarim yayin da Abdukarim ya bisa yana masa dariya cikin compound ɗin gidansu Abdulkarim ya dauki motarsa, a hanya ya tsaya ya yi sallar magarib batare da ya yi tunanin komai ba ya dauke kan motarsa zuwa gidansu Rumaisa wata irin kewarta ce ke zagaye dashi karfin hali kawai yake kwana biyu da bata daukar wayarsa shi kaɗai yasan irin azabar da ruhinsa ke sha, sai da ya yi parking adaidai kofar gate ɗin gidansu sa'annan ya samu kwarin gwiwar kiranta yanata addu'a wannan karon Allah yasa ta dauka. Har ta gama ring bata daga ba haka ya jera mata kira biyar bata dauki wayarsa ba. ƙarshe ya tura mata sako mai dauke da faɗin."ina kofar gidanku Rumaisa ba zan tafi ba koda zan kwana anan Dan Allah ki fito naga fuskarki koda so ɗaya ne koda daga nesa ne ki bani wannan damar. Lokacin da ya turo mata sakon tana kwance a Tsakiyar gadonta tana kallon wani American film acikin laptop ɗinta dakyar ta danne zuciyarta da duk wani abu da take ji akan AB ɗin kafin ta samu kwarin gwiwar kin daga wayarsa har na tsayin kwanaki biyu. Ganin sako yasa ta dauki wayar ta tsayar da idanunta tana ta juya sakon aranta tasan halinsa baya magana biyu da gaske zai iya kwana acikin mota har lokacin da za ta fito tana sonsa tana tsoron duk wani abu da zai taɓa lafiyarsa. ta san idan wani abu ya samesa ba zata taɓa yafewa kanta ba. Tafi minti goma tana shawara da zuciyarta akan taje ko kar taje ƙarshe dai ta mike tsaye riga da wando ne ajikinta wanda wando three quarter ne iyakarsa daidai gwiwarta doguwar bakar riga ta ɗora gamida yin rolling kanta da veill ɗin rigar ta saka flat shoe ,Ammi bata a parlor hakan yasa ta nufi kofa har zuwa wurin maigadi wanda ganinta yasa ya mike da sauri yana gaisheta bata damu da gaisuwar da yake mata ba ta nufi ƙaramar kofa ta buɗe, ganin motarsa kurum yaso ya tsayar da bugun zuciyarta tun kafin ta gansa jin take tamkar ta juya ta koma haushin kanta take ji meyesa zuciyarta keda rauni akan soyayyar Abba Bashir?"meyesa bata da juriya ne ko kaɗan hangota ya yi ta cikin madubin motar tasa ,da sauri ya buɗe marfin motar yana kallonta daga nesa ko kaɗan bai yi mamakin zata zo ba shiya ƙarasa har zuwa inda take da takunsu da Rumaisa ke ji har can kasan zuciyarta tsayawa ya yi agabanta hannayensa zube cikin kaftan ɗin dake jikinsa."bakya cin abinci ko habibty?" Ya faɗa murya can kasa bai damu da rashin amsawarta ba ya sake faɗin."kin rame sosai. Runtse idonta ta yi tana jin kalamansa na kara tafasa mata zuciya, fuska a haɗe murya a shaƙe take faɗin."mu karasa cikin gida da haka ta juya ta koma cikin gidansu yana biye da ita a bayanta har aransa yaji daɗin ganinta damuwar da yake ji ta gefenta yaji tana rage masa a hanakali, har cikin parlor da suke zama duk lokacin da yazo gidan ta jasa, sai da ta tabbatar ya zauna ta juya ta koma cikin gida da ido kurum yake bin ta yana jin wata mahaukaciyar soyayyarta na lulluɓe ruhi da duka gangar jikinsa sai yanzu yake ji idan bai auri Rumaisa ba yasan ba zai taɓa samun natsuwa ba. Jin kayrar wayarsa yasa ya fito daga ita cikin aljihun wandonsa yana bin sunan dake yawo acikin screen ɗin wayar da kallo... #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/22/2023, 11:31 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*:Jeedah3256 Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 035. Sunan Sadiya da yaga ni yasa shi taɓe baki ya maida wayar cikin aljihunsa ba wai ba zai dauki kiranta bane kawai dai bayaso ya sake yi abinda zai ɓatawa Rumaisa rai, shiyasa ya bari sai yabar gidan ya kira ta. Mai aikin su Rumaisa ce ta shigo ta ajiye wa AB drinks da ruwa mai sanyi kana ta gaida shi ya amsa batare da ya kalle ta ba. Bata daɗe da fita ba sai ga Rumaisa ta shigo ta sauya kayan jikinta zuwa plain material gown pink in colour jikinta na fidda ƙamshin turarenta mai sanyayya zuciya, bata yi makeup ba amma ta shafa powder sai ɗan man lebe da ta shafa wanda ya ƙara haskaka mata laɓɓanta. Bata ɗaura ɗan ƙwali ba sai ta rolling da ƙaramin veil da ya yi matching da rigar jikinta. Kyakkyawar ajiyar zuciya AB ya sauke ta iso ta zauna kusa da kujarar dake facing ɗinsa cikin sanyi murya ta furta "Habibi ba ka sha ruwa ba ko na zuba maka da kaina ne?" Murmushin farin ciki ne ya subuce masa ya tsare ta da rikitattun idanunsa da ke saurin narkar da da zuciyar 'ya mace "thanks love ni wannan kwalliya ma da aka yi min ta wadatar dani ya kamata na biya wannan kwalliya da tukuici mafi tsada. Wani irin daɗi ne ya yiwa Rumaisa dirar makiya ta wani langwaɓar da kai tana ji masifaffiyar soyayyarsa tana ƙara mamaye mata zuciya "Ka ji da neman maganarka Habibi domin nasan ba za ka iya bayarda kalar tukuici da nake so ba. "Habibty akwai wani tukuici sama da kyautar zuciyata ga baki ɗaya da na yi miki. Rumaisa I love you so much, Rumaisa, you are the only woman in my heart. I can't live without you soyayyarki halitta ce acikin jinina idan har na rasaki bansan ya rayuwarta za ta kasance ba. Dan Allah ki janye zance rantsuwa da Alqur'ani da kike so na yi saboda babu wata 'ya mace a zuciyata sama dake. Duk wata kalma dake fitowa daga bakinsa farin ciki take sanya Rumaisa ta adana su acan ƙasan zuciyata tare da killace su ita kanta tasan ba za ta iya rayuwa idan babu Ab acikin duniyar ta soyayya da take masa ta zarce wacce shi ɗin yake mata kawai dai shi mutum ne da bashi da juriya ta wannan fannin. Sun dauki lokaci a tare duk wani fushi da take dashi sai da ya tabbatar da ta goge shi a zuciyarta kafin ya yi mata sallama ya nufo gida. Wanka ya yi ya shirya cikin three quarter blue in colour tare da armless shirt white colour ya fito zuwa parlor sai lokacin ya tuna da kira da Sadiya ta yi masa ya dauki wayarsa ya yi dialling number ɗinta, ringing ɗaya zuwa biyu ta yi picking cikin dassashiyar murya ta furta "Yaya Abba zan mutu wallahi mutuwa zan yi dan Allah karka bari sanadin ciwon sonka na rasa rayuwata. Wallahi-tallahi idan ka aure Aydah ba zan iya cigaba da numfashi ba mutuwa zan yi domin ba zan iya jure ganinka kana amsa sunan mijin Aydah ba. Ka taimake ni yaya Abba ka ceto rayuwar ƙanwarka daga hallaka. Dafe forhead ɗinsa ya yi wani irin takaici da bakin ciki ya mamaye zuciya da sassan jikinsa ya rasa ina zai saka kansa ya sami sassauci ƙunci, baƙin ciki, damuwa sune ababe da a yanzu suka zama abokan rayuwarsa. Duk wanda ya kalle shi zai san baya ciki hayyacinsa. Sautin kukan Sadiya ne ya dawo dashi natsuwarsa ya ja numfashi yafi a kirga "Daman nasani ba za ka iya yi komai ba saboda ka tsaneni amma inaso ka sani yanzu haka akwai kwalba maganin kwari a hannuna muddin ba ka fasa auren Aydah ba, zan buɗe ne na tuttulawa cikina na gwammace na mutu na bar duniya da naga ranar daurin aurenka da ƙanwata. Da wani kalan sabon tashin hankali ya mike tsaye tun daga yarinta yasan hali Sadiya da kafiya da daurin kai duk abinda ta faɗa za ta iya aikatawa, duk cikin ƙannansa ita ce mai zafin kai. Cikin rawar murya ya ce "Sadiya kina ina ne?" Cikin shasshekar kuka ta bashi amsa da faɗin "Babu ruwanka da inda nake kawai ka zuba ido daga yanzu zuwa kowanne lokaci labarin mutuwata zai riske ka. "Sadiya please don't do this to me ya kuke so na yi da rayuwa ta ne huh?" AB ya faɗa kamar zai sa kuka. "Yaya Abba ina sonka wallahi ina bala'in masifar sonka tun da ba zan sami ka ba banga amfani rayuwata ba. "Sadiya ina gani kamar bakya cikin natsuwa da hankalinki kawai ki faɗamin inda kike yanzu nan zan zo na same ki mu magance matsala dake tsakanin mu. "Idan na faɗa maka za ka fasa auren Aydah ne?" "Duk abinda kike so shi zan yi miki Sadiya kawai ki faɗamin. Ya ƙarashe magana a tsawace. "Ina cikin balcony. Sadiya ta faɗa cikin muryar kuka. Da sauri AB ya fice direct ya wuce balcony tun kafin ya karasa cikin balcony ɗin ya hango Sadiya kwance akan grass carpet ɗin da ke lulluɓe a kasan balcony ɗin, da sauri ya isa kusa da ita ya durƙusa daidai fuskarta. "Sadiya da ikon aurena a hannuna yake da daga ke har Aydah da ba ku shigo cikin rayuwata ba, da wannan kalmar ta aure ba za ta taɓa shiga a tsakanina daku. Sadiya da kashe kai shine magani dake warware matsala da ni ne ya dace na kashe kaina ba ke ba. AB ya yi magana cikin raunin murya Sadiya ta tashi zaune idanunta sun yi jajir kaman an zuba mata barkono acikinsu, Ab ya yi mata kur da idanunsa cikin abinda bai fi 20 seconds ba ya zare idanuwa cikin kaɗuwa ya ce "me kika sha ne Sadiya?" Sadiya ta yi saurin kauda fuskarta tana mai goge zafafan hawaye dake ambaliya akan kumatunta. "Ba za ki buɗe baki ki yi min magana ba Sadiya?" Sadiya ta tashi zaune AB yaga bottle ɗin magani kwari riƙe da tafin hannunta, ya yi sauri riƙo hannunta suka shiga kokawa da kyar ya yi nasarar cire bottle ɗin daga hannunta. "Ka bani abina shine kadai hanyar da ya rage min da zan bi na huta da azabtar da ruhi da gangar jikina da soyayyarka ke yi. Ba tare da ya sake magana ba ya nufi hanyar fita daga balcony, cikin ɗaga murya Sadiya ta furta "Kaine bugun numfashina yaya Abba ba zan iya rayuwa daidai da na second ɗaya ne idan babu kai, ka ji tausai na yaya Abba ka aureni idan ka aure Aydah na rantse da Allah sai na kashe kaina. Sadiya ta ƙarasa magana tana wani irin gunji kuka mai matukar taɓa zuciya. Cak ya tsaya ya juyo gami da kallonta sai kuma ya kada kai ya fice, yana dab da isa entrance ɗin shiga bangaren sa ya tsikayi muryar Aydah tana kwalla masa kira "yayanmu! Sautin muryarta kadai da ya ji sai da gabansa ya yi wani irin bugawa tamkar wanda ke ji tsoron ta ya juya idanunsa suka sauka akanta.taji dawowarsa da mota tana tsaye a kitchen ta window ta hango dawowarsa ko yanzu ta faki idon Mami ne kawai ta fito da nufi shiga part dinsa sai ta hango shi shine ta ƙwalla masa wannan kiran, da ɗan gudunta ta iso wurinsa "yaya Abba tun safe da ka sauke school Bamu kara haɗu ba koda na dawo school har zuwa 5 na dauka ma zaka dawo kayi lunch har magarib." Ta karawa maganar tana kallonsa.na dawo baby Aydah kara fita dai nayi." Duk maganar da suke yi bai bari suka haɗa idanuwa ba sosai yake ji kunya kallonta musamman idan ya tuna da gobe warhaka ta zama matarsa. Ya tsikayi muryarta a dodon kunnensa tana faɗin "My heart tells me that there is something wrong with you. tell me Yaya Abba menene shi?" Dole ba don zuciyarsa taso ba ya haɗa ido da ita yanda ta tsare shi da kallo mai cike da tuhuma, yasa shi ɗaure fuska ya wani haɗe rai "Babu abinda yake damuna baby ki shiga gida gashi nan an fara kiran sallar ishai karki sa na rasa jam'i. Yana ƙarasa magana ya yi sauri shigewa bangarensa ta bishi da kallo har sai da ya ɓacewa ganinta sannan ta juya ta shiga cikin gidan, ashe duk abinda yake faruwa a tsakaninsu Sadiya tana laɓe jikin pillar tana kallonsu tana gani Aydah ta shiga gida, ita ma ta shiga amma sai ta wuce ɗakin Mami tana wani irin gunji kuka ta tura ƙofa, Mami tana zaune a gefen gado tana waya da Hajiya Zeena Sadiya ta shigo tana zuwa ta faɗa jikin Mami ta kara rushewa da matsanancin kuka "Mami mutuwa zan yi zuciyata za ta buga ki taimake ni ki yi gaggawar yi wani abu wanda zai dakatar da auren yaya Abba da Aydah wallahi Mami yaya Abba shine farin cikin rayuwata, ba zan iya jure rashinsa ba. "Innalillahi wa'inna illahim raji'um! Kin ji ko Hajiya Zeena? Kin ji abinda nake kan faɗa miki sai gashi kin ji da kunnenki ko?" Ajiyar zuciya Hajiya Zeena ta sauke ta cikin wayar yayin da zuciyarta ta cika da wani irin farin ciki, ta ƙudurta aranta tana gama waya da Mami za ta kira mijinta Alhaji Sanusi ƙanin Daddy ta fesa masa wannan daddaɗan labari burinsa na dab da cika. "Na ji Hajiya Mariya amma tun farko laifinki ne da kika ɓoye min irin wannan murɗaɗɗen al'amari, koda ba ki sanar dani a matsayina na ƙawarki ba, ai kya faɗamin a matsayin matar ƙanin mijinki. Da tuni mun shawo kan wannan matsala da bata girmama har haka ba. "Ki yi haƙuri Zeena ni kaina ban zaci al'amarin zai yi ƙamari har haka ba. "To dama ɗan hakki da ka raina shi ke tsone maka ido gashi nan wankin hula yana neman ya kaiki dare. "Wallahi haka ne Zeena karki so kika yanda gidana ya dawo tamkar gidan makoki, ga baki ɗaya farin cikin iyalina ya rikiɗe zuwa bakin ciki. Sadiya dake ta faman rusar kuka Mami ta dakawa rikitacciyar tsawa "ke dallah rufe min baki na yi waya duk ba ke ce kika janyo ba, sanda aka aura miki shi a bagassss! Da kin kwatar da hankalinki da yanzu kina gidansa hankalinki kwance. Tsabar daƙiƙancin ki, kika daba masa wuƙa koma waye dole ya tsane ki. Tashi daga jikina na samu nayi magana cikin natsuwa. Dole Sadiya ta tashi daga jikin Mami ta kwanta akan gado tana cigaba da kukanta, yayin da Mami ta cigaba da magana da Hajiya Zeena. "Ki kwantar da hankalinki Mariya koda Alh Bashir ya yi nasarar aurawa Abba Aydah za mu shiga mu fita mu hana masa kwanciyar hankali har sai ya sakar miki 'ya. Ai ɗaura aure ba shi bane zaman aure ba, ki sa aranki muddin kina tare dani matsalolin ki sun zo ƙarshe. Hajiya Zeena ta cigaba da kwantar wa da Mami hankali tare da ɗora ta akan mugaye shawarwari kafin suka yi sallama da zimmar gobe Hajiya Zeena za ta zo su ƙarasa magana. Mami ta koma kan Sadiya ta dinga rarrashinta da daddaɗan maganganu. *MASARAUTAR KUDU* Alh Aliyu ne zaune a dakinsa yana kallon hoton da ya zama masa jini da ɓargon jikinsa ya yi nisa sosai har bai ji ƙarar buɗe ƙofa da Hajiya Safiya ta yi ba har ta iso dab dashi bai sani ba idanunta suka sauka akan hoton kyakkyawar baturiya, wani irin bugawa ƙirjinta ya yi babu shiri ta dafe ƙirjin nata da duka hannayenta, cikin sarƙewa murya ta furta "Abbu wacece wannan da kake kallon hotonta miye alaƙar ka da ita?" Firgigit ya yi saboda kamar daga sama ya ji muryata a dodon kunnensa, da sauri ya juyar da hoton ya ɓoye fuskar wacce ke jikin hoton cike da rashin gaskiya ya kalleta sai kuma ya ɗaure fuska ba tare da ya ce da ita uffan ba ya miƙe ya shige bathroom ta bishi da kallo still tana dafe da ƙirjinta dake barazanar rabewa gida biyu. Tasan miskilanci irin na mijinta ba zai taɓa faɗa mata wacece ta jikin hoton da yake kallo ko da kuwa za ta mutu ne. Wani irin zazzafan kishi ya rufe ta har wani ɗaci-ɗaci take ji a maƙoshinta Hajiya Safiya mace ce mai ɗan bala'in zafin kishi. Tana masifar son mijinta duk da shi a wurinsa sunan sun yi aure ne kawai amma babu wata kyakkyawar fahimtar juna a tsakaninsu kullum yana busy bashi da lokacin ta ko kaɗan. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/25/2023, 12:47 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*Jedddah3256 #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 036. Shiru-shiru Hajiya Safiya tana jiran Aliyu na uku ya fito daga bathroom ya bata gamsasshiyar amsa akan baturiya da yake kallon hotonta, da taga shiru nasa yana neman ya yi yawa sai ta tashi ta nufi ƙofar bathroom ɗin ta shiga knocking tana kiran sunansa "Abbu! Lafiya kake kuwa?" Saurin kunna shower ya yi ya nuna mata wanka yake yi tuni ta fahimci manufarsa baya so magana da ita don haka sai ta juya ta fice daga ɗakin nasa, zuciyarta tana kisimamata abubuwa da dama. Duk tsawon shekaru nan da suka yi aure take fuskantar rashin kulawarsa a gareta babu wata shaƙuwa irin ta miji da mata a tsakaninsu, duk da a fannin shimfiɗarsu yana ƙoƙarin gani ya sauke hakkinta dake wuyansa. Bangare dukiyarsa ma yana hidima da ita da yaranta duk abinda suka nuna so suna bukata komai tsadarsa take yake fitar da kuɗi ya siya musu wannan abin, sai duk wadannan abubuwan da Aliyu na uku yaga ya wadata matarsa dasu a wurinta aikin banza ne domin ta rasa wani bangare na mijinta. *CIROMA DA GALADIMA* "Kwatar da hankalinka Ciroma ai abin nema ne ya samu wai mata ɗan sanda ta haifi barawo, don kawai mai martaba bai mutu lokaci guda ba hakan baya nufi da aikin mu warware ba. Ko yanzu za mu iya ƙarasa shi amma kafin sannan me zai hana ka sake komawa wajen wannan malamin naka ka faɗa masa yadda aikin naka ya kasance idan da wani taimako sai ya taimaka mana. Shiru Ciroma ya yi yana kara nazarta maganganun Galadima kafin ya nisa tare da sauke naunnayar ajiyar zuciya "maganarka abar dubawa ce Galadima gobe da sassafe mu haɗu anan sai mu dunguma ga baki ɗaya mu je wurin mai Gundulelliya ɗin gara ayi komai akan idanunka saboda mun zama partners. "Haka ne gaskiya gara mu tafi ɗin ai mai nema na tare da samu kada ma wannan ya sanyaya maka gwiwa Allah na tuba Ciroma yadda mai martaba yake kwance nan ai da matuƙar wahala ya ƙara tashi da ƙafafuwansa. "Gaskiya kam da wahala ya tashi faratt ɗaya domin kuwa mai Gundulelliya ya tabbatar min idan har bai mutu ba zai kwanta matsananciyar jinya. Ciroma ya faɗa da wani murmushin zallan mugunta akan fuskarsa. "Ai kuwa gashi nan ya kwanta domin banbancinsa da mataccen kaɗan ne. Kafin ma yasan inda yake tuni mun gama cimma burin mu. "Ni fa Galadima na kasa bari mamakin Fulani karama wannan matar cikakkiyar 'yar wasan kwaikwayo ce ka ga yadda ta bi ta birkice, sai ka ce ba da hannunta ta zubawa mijin nata guba ba. Sai kawai suka sheƙe da dariya, takon tafiya suka ji akan dry grass na tarin bishiyoyi dake zube a cikin lambu suke kusan a tare suka miƙe tsaye cikin kaɗuwa suke kallon juna kafin da sauri suka nufi gun da suka ji sautin ya ƙaru saboda wanda ya yi musu laɓe ya ɗiba da gudu ne. Hankali tashe Ciroma ya shiga kwallawa bayi dake cikin gidan gona kira ya umarce su da su bi bayan mutumin kada su bari ya sha kodai su kawo shi a raye kuma su kawo masa gawarsa. Tun mutumin yana iya gudu da dukan ƙarfin sa har ya zo ya fara jigata, kasancewar tsufa ya fara riskarsa fahimtar ya yi ba zai sha daga hannun waɗannan azzalumai ba sai ya ciro wayarsa da ya nade zantukan Galadima da Ciroma ya kira wata number ya yi magana wacce bata wuce ta mintuna uku ba ya kashe wayar, ya ƙarawa gudun nasa ya shiga wata duhuwa mai sarƙaƙƙiya ya boya a ciki yana ji maganganu bayi amma bai motsa daga inda yake ba yana kallonsu suka ƙara kwasa wa da gudu suka nusa cikin jeji, shi kuma ya fito daga maɓoyarsa ya nufi gindin wata bishiya ya haƙa rami tare da ciro wata baƙar leda cikin aljihunsa ya kashe wayarsa ya naɗe ta ciki ya binne ta cikin ramin. *ALH BASHIR MANSION* Acikin kunnensa aka kira sallar asuba, idan yace ga baki ɗaya wannan daren ya samu bacci mai daɗi ya yi karya. gaba ɗaya wannan daren yazo masa a birkice har addu'a yake Allah yasa daren ya yi ta tsayi kar gari ya waye, har lokacin da ake kokarin tada sallah acikin kunnuwansa amma sai ya tsinci kansa da kasa tashi jikinsa tamkar an ɗaɗɗaure masa shi da sassari da kyar ya yi karfin hali miƙewa tsaye yana jin yadda kansa ya yi masa wani irin nauyi saboda baccin da bai samu ya yi ba. Hakanan ya daure ya yi wanka ya dauro alwallah a gurguje ya saka jallabiya a jikinsa ya wuce zuwa masallaci lokacin har an tada sallah. kusan karfe bakwai suka fito daga masallaci shi da Daddy ya gaishe da Daddy, kallan idanunsa Daddy kurum yake wanda babu wadataccen bacci acikin su, "Bayan saukowa daga masallaci ne daurin auren kana da lokaci har na awa bakwai ka je ka samu kayi bacci ,zan jira ka zuwa karfe goma ka fito muyi break fast. Da mamaki yake kallon Daddy tun kafin ya furta Daddyn ya katsesa yana faɗin."na sani zan jiraka ka je kayi baccinka. Daddy ya faɗa yana nufar part ɗinsu shima AB ya juya zuwa nasa,kamar yadda Daddy ya umurce sa ya hau gado ya kwanta kuma cikin sa'a baccin yazo masa. ƙarfe bakwai da rabi Mami ta turo kofar ɗakin nata, kwance take cikin kyakkyawan gadonta daga ita sai towel ajikinta tayi rufda ciki tana baccinta cikin natsuwa, kallonta kawai Mami take cike da takaici ta tabbata wanka tayi niyar shiga ta buge da komawa ta kwanta dan tun jiya da Daddy ya yi mata maganar kar Aydah ta fita makaranta a yau bata faɗawa Aydah ba. Mami dai ta tsaya tanata bin Aydah da kallo tamkar mai son ta gano wani abu a jikinta wani abu taji yana tsaya mata a wuya idan kuma ta tuna wai nan da wasu awanni Aydah ɗin za a daura aurenta da Abba sai zuciyarta ta kara dagulewa ta rasa meyasa har ranta take jin bata son wannan auren ta rasa meyasa take jin babu daɗi har acan kasan zuciyarta har ga Allah akwai mugun kwaruwa acikin auren Aydah da AB to duka -duka Aydah nawa take me ma ta sani acikin rayuwar Auren saboda kawai daukar hakki da zalunci irin na mahaifinta zai ɗaura mata nauyin da shekarunta ba su isa dauka ba. Juyawa kawai Mami ta yi ta rufowa Aydah ƙofar yau ko kitchen bata leƙa ba domin ganin me Huwaila take shiryawa na break fast saboda takaicin Daddy. Kusan karfe 8 na safe ta farko a wani gigice da sauri ta zuro kafafunta daga kan bed , ɗin tamkar zata yi kuka ta nufi toilet babu wanda ya tasheta gashi har ta makara zuwa school agurguje ta watsa ruwa cikin mintuna goma kacal har uniform ta saka babu kowa a parlor lokacin da ta sauko , ɗakin Mami ta nufa kai tsaye knocking ta yi jin shiru yasa ta tura ƙofar kanta tsaye ta shiga ga mamakinta Mami na kwance akan bed sai dai ba bacci take ba, yanayin da ta samu Mami ya ɗan daga hankalinta dan ganin damuwa kwance acikin fusrkarta. "mami!"Aydah ta kira sunanta da sanyin murya "Karki dameni dan Allah ki fita ki bani waje Zulaiha!"Mami ta kira sunanta baro-baro daman kuma sunan mahaifiyar Daddy ne musamman idan tana cikin fushi haka take kiran sunan nata babu ruwanta ko a gaban Daddy ne. Ganin taki tafiya Mami ta daga kai tana kallonta ta wani daure fuska tana wani daka mata tsawa "ki je ki cire uniform tunda zaman gidan kike so karfe nawa kika sani yanzu?har zata buɗe baki ta yiwa Mami magana ganin tana shirin tasowa yasa Aydah ta fice da gudu tabar cikin ɗakin tamkar zata yi kuka Kai tsaye part din mahaifinsu ta nufa ganin bata gansa a parlor ba tasan yana master bedroom ɗinsa ya koma Bacci TV parlorn kawai ta kunna tayi kwanciyarta anan, ita ma bata daɗe ba wani baccin ya kara daukarta batare da ta yi tunanin cire uniform ba. Da mamaki sosai Alhaji Sanusi ke kallon matar tasa jin abunda take faɗa, "kin san bana son kalar wannan wasar wannan wane irin aure ne auren ma da Aydah?" wata dariya Alhaji Sanusi ya saki yana kallon matar tasa cike da takaicinsa take faɗin. "Na taɓa yimaka irin wannan wasar jiya Hajiya mariya da muka yi waya take sanar dani ta tabbatar min dacewa yau ne daurin auren Abba da Aydah. Wata irin zufa Alhaji Sanusi ya fara haɗawa ga baki ɗaya abubuwa ya ji suna neman kwabe masa duk abunda yake shiryawa baya tafiyar masa adaidai lallai wannan karon yayan nasa yayi masa ba zata kuma ya shayar dashi mamaki. meyasa ko a Company bai ji ana maganar ba.?" Wannan karon bai san kuma me yayan nasa ya shirya ba, acan kuma ɓangaren Alhaji Bashir shi kaɗai ya zauna ya yi tunani bai raba card ɗin daurin aure ga kowa ba. Musamman cikin Companyn su gudun matsala da kuma kare martabar Abba Bashir hasalima Abba kawai ya baiwa card ɗin ya rabawa friends ɗinsa, shima yasan a bangaren Abban ba wasu friends ne garesa ba sosai. miƙewa tsaye Alhaji Sanusi ya yi ya shiga kai da kawo tsakiyar parlor ɗinsa ga baki ɗaya hannayensa sargafe a bayansa. break fast ɗin da ya gama yi yanzu ya ji yana ya mutsa cikinsa da wani irin yanayi cikin fuskarsa yake kallon matar tasa dake ta kallon sa. Wani numfashi mai zafi ya fitar rai a ɓace yake faɗin."meyasa da na dawo jiya baki sanar dani ba?"kin san ko awa nawa ya rage a daura aure taya zan iya dakatar da wannan auren?" ta buɗe idanunta tana kallon mijin nata cike da takaici take faɗin."ƙarfe ɗaya na dare zan zauna parlor ina zaman jiran dawowarka tunda ni na aike ka zaman majalisa har karfe ɗayan dare aini lokacin ban ma san inda kaina yake ba. Kawai ka dauki haƙuri a daura auren. Da yanayin yadda mariya ke yimin magana kamar bata son auren nan na Abba da Aydah yanayin muryarta ya nuna kamar akwai tsanar Abba Bashir a kasan zuciyarta. Shiyasa ma nake ta sauri na gama abubuwan da zan yi na tafi gidan na sha kallo, shi dai Alhaji Sanusi car key ɗinsa kurum ya dauka ya fice daga Parlor yana kuma neman hanyar da zai dakatar da wannan auren. Fitowar Daddy kenan daga dakin baccinsa kusan karfe 9 har da mintuna goma a sama da mamaki yake kallon TV dake aiki cikin parlor kafin ya mayarda kallonsa kan Aydah dake kwance tana bacci da uniform ajikinta murmushi kurum Daddy ya yi ya karaso cikin parlor ya ɗan rage volume, zama ya yi yana canja channel zuwa channel ɗin (TVC NEWS)bai jima da zama ba Mami ta karaso cikin parlor cikin shigar alfarma bayanta Siyama ce da dan ƙaramin tray a hannunta ta ɗorasa akan side table dake cikin parlor ta gaishe da Abba,ya amsa cike da fara'a ita da Mami har lokacin idanunta na kan Aydah hannu Mami tasa da niyar ta tasheta Daddy, ya yi saurin dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu. kallonsa Mami take tana jiran karin bayani "ki kyaleta tunda bata tashi ba. cikin ƙunar rai Mami kamar jira take Daddy, ya yi magana ta sauke masa kwadon masifa "A haka kake tunanin aurar da wannan yarinyar Alhaji?" idan taje gidan auren me ma zata iya da kanta za ta ji ko da responsibilities ɗin dake kanta a matsayinta Na matar aure. shi dai Daddy kallonta kawai yake harta gama faɗanta ta zauna tana kokarin jawo ruwan dake cikin flask wanda ta dafawa Daddy ruwan lipton da suka ji citta ,da kanumfari daman a ka'idar Daddy kafin ya yi break fast sune farkon abunda yake sha. Siyama na ganin mami ta fara faɗa daman ta sulale tabar parlorn har yau tana mamakin meyasa Mami bata son auren yaya Abba, da Aydah mutane nawa ne a kauye suka yi aure batare da ma sun kai shekarun Aydah ba. harga Allah tana son Yaya Abba,ya auri autar tasu ko taga haukan da Sadiya zata yi kuma sai yanzu tasan Yaya Abban yafi dacewa da Aydah akan Sadiya, Mami ta zuba masa lipton ɗin acikin tea cup ta miƙa masa ya karba da murmushi kwance a fuskarsa yake faɗin."thank you wife. ƙara haɗe rai ta yi hayaniyar su ya tayar da Aydah ta miƙe zaune tana saukar da kanta akan iyayen nata, "Mamana kin sha bacci tana murza ido take gaisheda Daddy, ya amsa yana tamabayarta meyasa ta saka uniform banci yace ba zata je school ba yau."da sauri Mami ta karɓe zancen da faɗin "Sai kace baka san halin rigimarta ba. "Daddy yau koda na tashi asuba, bana jin daɗin jikina na rasa meke damuna ga yawan faɗuwar gaba. Murmushi kurum Daddy ya yi dole duk maccen da igiyoyin aure zasu hau kanta sai ta tsinci kanta a irin wannan yanayi. jeki ki cire uniform ki wanke baki zuwa 10 zan fito mu yi break fast kafin nan yayanku ya karaso. Nasan shima yana can yana baccin. Ɗagawa Daddy kai kurum ta yi tabar masu Parlorn da gaske bata jin Daddyn jikinta tun daga wayewar safiyar yau take jin jikinta wani irin tamkar wacce aka yiwa shegen duka. Har Daddy ya gama shan ruwan lipton Mami na zaune jin shiru har na minti biyar bai da alamar tashi ayi break fast, Mami tace "yara fa sunata jira."kuje kuyi ke da yaranki Mariya idan Abba,ya tashi zamu yi tare. Da mugun shock Mami ke kallonsa ranta banda tafasa babu Abunda yake, lallai akwai aiki babba a gabanta tun farko meyasa ta baiwa Daddy dama irin wannan?"yanzu ma Abba zai jira suyi break fast a tare kenan ma yafi 'ya'yan da ya haifa acikinsa muhimmanci Mami saboda bakin ciki kasa cewa komai tayi ta fice daga Parlor acan kasan ranta wata irin tsanar Abba ce ta fara sauka a kasan zuciyarta. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/25/2023, 12:56 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*:Jeddah3256 Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 037. Mami tana shiga main parlor ta tarar da Sadiya zaune akan kujera da kayan baccin a jikinta, ta yi tagumi idanuwanta sun yi luhu-luhu alamar tasha kuka ga kuma rashin bacci yadda idanunta suka yi jajir ya ƙara ɗagawa Mami hankali, cikin sanyi jiki ta nemi gefen Sadiyar ta zauna "Sadiya! Mami ta kira sunanta cikin mutuwar jiki da sanyi murya. "Na'am! Sadiya ta amsa da dusasshiyar muryata. "Ki yi haƙuri ki cire Abba daga zuciyarki domin na yi iya ƙoƙarina na gani ya maida ke ɗakinki amma abin ya ci tura, ga baki ɗaya na rasa kowacce irin dama. Wani naunnayar numfashi Sadiya ta sauke yayin da har hawaye sun fara bin kumatunta "Duk duniya babu wata kalma da na tsana a furta min Mami irin ace na haƙura da yaya Abba ko na cire shi daga zuciyata wannan kalmar tana kona min rai Mami anan nake ji tururin zafinta. Sadiya ta ƙarasa magana da shouting tana pointing ƙirjinta. Ko kaɗan Mami ba ta ji mamakin fitar waɗannan maganganu daga bakin Sadiya ba domin ko makaho ya kalleta zai fahimci she's depressing "Dole ki yi haƙuri Sadiya ki rungume ƙaddara ki roki Allah ya cire miki soyayyarsa nan da 'yan awannin ƙalilan Abba zai zama mijin Aydah kin kuma san ko a garin jahilai ya da ƙanwa ba za su aure namiji ɗaya ba. Wani kalan miƙewa tsaye Sadiya ta yi jikinta ko'ina rawa yake ƙwaƙwalwarta sai kimtsa mata abubuwa da dama take yi "Ƙaddara fa kika ce Mami? Wallahil-azim ba zan taɓa karɓa wannan ƙaddarar ba duk ƙaddarar da za ta ja katanga tsakanina da abin ƙaunata, ban yarda da ita ba. Ke kin yi iya naki Mami babu nasara ni ki zuba min ido ki ga ta yarda zan dawo da yaya Abba gareni. Tana ƙarasa magana ta juya a mugun fusace ta haura upstairs idanunta ga baki ɗaya sun gama rufewa, a yadda take ji zazzafar soyayyar AB kowa ma za ta iya kashewa matuƙar zai zama nata ita kaɗai. Tana zuwa ta murza kofar ɗakinta key bedside drawer ta nufa ta buɗe ta a fusace ta ciro wata bakar leda ta yi zaune darshan akan marbles ta zazzage abunda ke ciki bottle ɗin tortulin with codeine syrup ne aciki sai waɗansu tablets, ta ɓalle two tablet ta afka a bakinta kana tanata korawa da tortulin ɗin wanda bata ko tsaya yi diluting ɗinsa ba ta shiga sha tana shanye wa ta dubi jikin bango ta maka bottle ɗin ya fashe in to tiny pieces, sai kuma ta shiga fizgar sumar kanta da dukan hannayenta ta saki wani irin ihu kafin ta sulale kan marbles ta cigaba da gunji kuka wanda sautinsa baya fita sosai a dalilin dusashewar da muryata ya yi, sannu a hankali take lumshe idanuwanta da suka yi wani irin ja kamar an baɗa mata barkono, bata ɗauki dogon lokaci ba naunnayen bacci ya yi awon gaba da ita. Aydah tana shiga ɗakinta ta cire uniform ta maye gurbin su da A-shape gown na atamfar chiganvy gold ash and sky blue in colour ta haɗe kitson kanta tun wanda yaya Abba ya kaita aka yi mata ta ɗaure shi da band ta dauko hula da aka yi mata da ɗan ƙwalin atamfarta ta kifa akanta ta daidaita zaman hular kanta, ta shafa powder da man lebe sannan ta fesa turare duk abinda take yi tana yinsa ne cikin mutuwar jiki bata ji kwari a jikinta ko kaɗan yadda take ji jikinta tamkar an ɗaɗɗaure mata shi da sassari. Ga irin fargaba da faɗuwar gaba da take yi wanda ta rasa na menene, gefen gado ta zauna tana sauke numfashi ta dauki mintuna goma a haka kafin ta miƙe ta sauko ƙasa. Siyama kaɗai ta isko a dinning area ta ja kujerar dake facing ɗinta ta zauna tana faɗin "yaya Siyam me kesa faɗuwar gaba?" Yau tun da na tashi nake jin faɗuwar gaba haɗe da wani irin tsoro-tsoro. Aydah ta ƙarasa magana cikin raunatacciyar murya. "Ba dole ki ji faɗuwar gaba ba nan da ɗan wani lokaci za ki shiga jerin manyan mata. Siyama ta faɗa cikin zuciyarta a bayyane kuma sai ta ce "A duk sanda kika tsinci kanki acikin irin wannan yanayi ki yawaita ambaton Hasbunallahu wal-imaal wakil! Ko menene za ki ga Ubangiji ya kawo miki shi da sauki. "Toh! Aydan ta faɗa a takaice kana ta zare ɗaya daga cikin plates ɗin da ke kan dinning table ɗin ta zuba chips da wainar kwai sai tea da ta haɗa, Siyama tana kammala wa ta tashi ta koma cikin parlor, chips ɗin kaɗan ta tsukura ta shanye tea ɗin hatta da bakinta bata ji daɗinsa ta rasa appetite ɗinta. Ta dawo parlor wurin Siyama ta zauna kusa da ita. Sai da Daddy ya kira Ab a waya sannan ya falka daga naunnaye baccin da yake yi, cikin mutuwar jiki ya ɗauki kiran, Daddy ne ya faɗa masa shi kaɗai yake jira ya amsa da gashi nan zuwa nan da mintuna goma, da sauri ya sauko daga gado ya wuce bathroom ya yi wanka yana fitowa ya tsaya a gaban dressing mirror ya goge jikinsa da hand towel ya shafe lallausar fatar jikinsa da lotion mai ƙamshi gaske. Farar shadda ya dauka a closet ɗinsa dinkin babbar riga wacce aka yiwa aiki da baƙin zare, sai ya saka bakar hula da baƙeƙen takalma sawu ciki. Ya yi tsaye yana ƙarewa kyakkyawar fuskarsa mai cike da haiba da wani irin kwarjini na musamman, shi kansa sai da ya yaba da irin kyawo da ya yi duk da ya ɗan yi rama amma hakan bai dusashe kyakkyawar halittar da Allah subhanahu wata'ala ya yi masa ba. Ya ɗauki wayoyinsa ya fice walking majestically bangaren Daddy ya nufa ya yi sallama tare kutsa kai cikin parlorn ya tarar da Daddy da Alh Sanusi sai korafi Alh Sanusi ke yi masa a rashin sanarda shi da bai yi ba "A gaskiya yaya abinda kake yi sam ba ka kyautawa yanzu ace har yau ne ɗaurin auren Abba da Aydah bansani ba da ban ji a bakin shanu talla ba da shikenan sai dai daga baya na ji zance daurin aure ko? Kafin Daddy ya bashi amsa ya tsikayi muryar AB yana gaishe dasu ya amsa masa yayin da Alh Sanusi ko kallon gefen da AB yake bai yi ba saboda wani irin tuƙuƙi baƙin ciki ke cinsa a zuciya ji yake kamar ya taso ya shaƙewa AB wuya ba zai sake ba har sai yaga ya daina motsi. Cikin takaici da tarin baƙin ciki ya cigaba da cewa "irin wannan halin shi ke ɓata zumunci fissibillahi ina ƙaninka uwa ɗaya amma ace banida darajar da za ka sanarda ni abinda ya shafe ka, tun-tuni na gama fahimtar ba kasafai nake da amfani a wurinka ba. Na tabbata da Hajiya tana raye da ba za ka dinga nuna min irin wannan wariyar ba. Daddy ya yi sauri tarar numfashinsa yana faɗin "Ka yi haƙuri Sanusi ni ban ɓoye maka a bisa wata mummunan manufa ba na yi haka ne saboda banaso, ce-ce-kuce amma ka yi haƙuri za a kiyaye gaba. "Ai haka kake cewa koda yaushe za ka gyara amman... "Dallah ya isa haka Sanusi! Ka cika mita wallahi kamar wani tsohon dan shekara tamanin, haba na ce ka yi haƙuri an yi kuskure za a gyara amman sai mita kake yi, ko na sauko ne na zube guiwayoyina a gabanka na ba ka hakuri?" "Har ni na isa ka durƙusa min yaya kawai dai na ji ba daɗi ne da yadda ka boye min babban al'amari irin wannan, ai ka Abba daminka ne ya tsike a gindin kaba domin mai sunan Hajiya da kake gani yarinyar kirki ce za ki ji dadin zama da ita fiye da wancan sakarya da aka fara aura ma. Murmushin gefen baki AB ya yi yana sadda kansa ƙasa. "Ina fatar yaya ka sanar da Jamila da raguwar 'yan uwanka da kuka haɗa uba?"Duk su ɗin ba wani damuwa suka yi da shiga sabgogin ka ba. Amman duk da haka suma suna da hakkin su sani. Alh Sanusi ya sake faɗa duk wanda ya ji bakinsa na furta waɗannan maganganu zai zaci shi ɗin cikkaken mutumin kirki ne ba a san kuwa duk faɗi da cikar nahiyar Afirka da matuƙar wahala a sami mugun mutum irinsa. Daddy ne ya amsa mata da cewa "Na faɗa musu sai dai ita Jamila na ce ta yi zamanta ta bari sai lokacin biki ta zo ayi da Ita yanzu ɗaurin aure ne kawai za a yi. "To ai shikenan amman bari na kira Alh Umar da wasu daga cikin team members (employees) ɗinmu domin bai dace ayi daurin auren guda na Chief Executive officer na moonlight automobile ba su sani ba. Kafin Daddy ya dakatar dashi har ya yi dismiss numbern Alh Umar haka ya dinga kiran mutane yana sanarda su. Daddy ya kalli AB ya ce "Abba tashi ka shiga cikin gida ka yi breakfast sai ka faɗawa maminku ta haɗa breakfast ɗin ɗaya daga cikin yara nan su kawo mana domin daga gani wannan sarkin mita ɗin ko karin kumallo bai yi ba, ya nufo nan. Ab ya miƙe tare da amsawa da to ya fi ce. Bakinsa ɗauke da siririyar sallama ya tura kofar main parlor Siyama da Aydah ya gani zaune akan kujera ɗaya Siyama tana nuna mata waɗansu pictures a wayarta. Ƙamshin turarensa ya gauraye ko'ina a cikin parlor da sauri Aydah ta waiga ta sauke dara-dara idanunta akansa wani irin kyawo ya yiwa idanunta wanda yasa ta kasa janye ganinta akansa, shima tsintar kansa ya yi da tsare ta da manyan idanunsa, kafin cikin tafiyar tasa ta izza da zallan ƙasaita ya nufi ya soma tafiya tare da nufar dinning room, Siyama ce ta fara gaida sa ya amsa mata da ƙaramin sauti. Aydah ta taso da sauri ta nufi wurinsa tana faɗin "Yayanmu yau wannan wanka naka na juma'a ya fi na kowanne sati wankuwa ka ga kuwa wani irin bala'in kyau da ka yi Allah yayanmu kai ɗin kyakkyawa ne. Kallo ɗaya ya yi mata ya ɗauki mug ya haɗa tea Aydah ta ƙaraso ta gabansa ta tsaya tare da jingina bayanta ga dinning table guiwayoyinta suna manne da nasa ta yi folding hannayenta tana masa kallon kurilla. Duk surutun da take zuba masa ba wanda ya bata amsa saboda ganinta da ya yi yanzu nan ya tado masa da tabo abinda yake ji, yana ji wani irin abu ya tokare masa a maƙoshinsa ya kasa yarda wannan 'yar firitt ɗin yarinya ita ce nan da 'yan wasu awannin za ta zama matarsa. Ko kaɗan Aydah bata damu da shiru nasa ba saboda tasan halin yayan nata da miskilanci idan abin ya motsa har wata izza da taƙama yake yi magana ma wahala take masa sai kace jinin sarauta. Fitowar Mami kenan daga ɗakinta tun kafin ta ƙarashe saukowa daga bene ta hango su takaici ne ya lulluɓeta musamman yadda Aydah ɗin take tsaye a gabansa kusanci nasu ya yi yawa, saboda haka rai ɓace ta kira sunanta "Aydahhhhh! A tsorace Aydah ta waiga kalli Mami wacce ta yi bala'in daure fuska ranta a ɓace ta iso cikin dinning area ɗin ko gizau AB bai yi ba tea dinsa kawai yake sipping "uban me kike yi a cikin jikinsa ba nace banaso na ƙara ganin ki tare dashi ba?" Watau ke mai kunnen kashi ko? Wannan idan ban tashi tsaye akanki ba nan take wannan gabjejen kato zai kwakule ki, bace min da gani shashasha kawai ina magana kin wani tsare ni da munafukai idanuwanki. Yadda Mami ta daka mata tsawa tare da yi kanta yasa bata tsaya dogon tunani ba, balle har ta fahimci me take cewa ba ta kwasa da gudu ta fice daga dinning ɗin. "Kai kuma na dawo kanka marar kunya fitsararriya, butulu ɗan gaba da fatiha ina ƙara gargaɗin ka a karo na ƙarshe kar na sake ganinka kusa da 'yata wallahi-tallahi idan ka sake bari na ganka kusa da ita duk abinda na yi maka kai ka janyo ka ji na gayama. Da haka Mami ta juya ta nufi cikin parlor tana fadar bakaken maganganu. Duk abunda Mami take faɗa bai ɗago ya kalleta ba sai jujjuya mug ɗin hannunsa yake yi, wani abu mai nauyin gaske yake ji a maƙogwaronsa ga bugun zuciyarsa ya fara zarce ƙa'ida numfashi kuwa ya sauke yafi a kirga kafin kuma ya dawo yana ambaton Allah, ya ɗauki lokaci a haka kafin ya ji sassauci abunda yake ji ya tashi cikin tafiyarsa ta natsuwa ya shiga cikin parlor yana zuwa ya zube guiwayoyinsa gaban Mami cikin dashewar murya ya ce "Da ina da iko akan abinda kike so da ba zan miki gardama ko na musanta miki ba Mami, duk yadda ki kai da jin haushina ba zan daina yi miki kallon uwa ba. Banida wata mahaifiyar a duniya nan sama dake Mami, dukka abubuwa nan da kike aikatawa a gareni ban taɓa ji haushinki ba nasani kina yi ne domin samar mana natsuwa da kwanciyar hankali. Har ga Allah zuciyarta ta fi karkata akan zaman aure da Sadiya fiye da Aydah zan iya karɓar Sadiya a matsayin matata, ta sunnah amman ba zan iya kallon Aydah da wannan matsayin ba. Ki ma jingine zance ƙarancin shekarunta Mami ni ne nan na raine ta na ci kashi da fitsarinta duk wata kulawa da uwa za ta iya ba wa ɗanta irinsa na ba wa Aydah. To ta ya kike tunani akwai abinda zai iya shiga tsakanina da ita?" Da zan iya kallon cikin idanuwan Daddy na faɗa masa banaso aure nan Mami da na faɗa masa tuntuni, sai dai idan na aikata hakan tabbas a lokaci na cancanci a kira ni da abinda yafi butulu. Daddy ya yi min gatan da na rasa ya bani matsayi da asali ya so ni ya ƙauna ce ni sai na rasa abinda zan saka masa dashi sai bijirewa. Ba zan iya ba wallahi ba zan iya ba Mami ki gafarce ni. Yana ƙarashe magana Mami ta kalle shi da fusatattun idanuwanta ta ja dogon tsaki "mtssss! To bari ka ji na gayamaka Bashir duk abinda za ka faɗa ba shi zai sa na bar Aydah ta yi rayuwar aure da kai ba. Duk wata ƙauna da nake maka a yanzu ta rikiɗe zuwa zazzafar ƙiyayya, idan har kai ɗan halak ne ba shege ba ka tattara kayanka kafin lokaci ɗaurin aure nan ka bar gidanan. Idan Alh ya nemi ka ya rasa dole ya haƙura. Daga baya ka dawo ka bashi haƙuri a irin kaunar da yake maka nan take zai yafe maka. Idan kuma ya daidaita sai a mayar da aurenka da Sadiya domin ita ce ta fi dacewa da kai fiye da duk wata mace a duniya. Hawaye da tun ɗazu AB yake danne wa ne suka subuce masa batare da ya sake ma Mami magana ba ya miƙe ya nufi ƙofar fita ya buɗe ya fice yana tafe zuciyarsa tana kisimamai ya bar gidan kawai ta hakan ce kaɗai zai sami salama. Ya rasa me yasa zuciyarsa ta kasa dangana ta karbi Aydah ji yake idan ya aureta ga baki ɗaya daraja da mutuncinsa za su zube a idon duniya. Gudu-gudu ya isa parking lot ya shiga motarsa ya bar gidan da zimmar ya tafi kenan baya tunani zai dawo nan kusa. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/26/2023, 2:09 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*:3256 Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 038. Tuki kawai yake yi amma natsuwarsa ta gama fice wa daga gangar jikinsa ga wani azababben ciwon kai da yake ji, instead ya nufi hanyar fita daga gari kamar yadda tun farko ya kudurta aransa, sai kuma ya tsinci kansa da ka sa bin umarnin zuciyarsa sai kawai ya sauya akalar motarsa ya nufi Quarter house hotel ya kama ɗaki aka bashi key. Yana shiga ɗakin ko takalmin ƙafarsa kasa cire wa ya yi ya faɗa kan gado ya kwanta, shi kaɗai ne zai iya misalta adadin raɗaɗin da yake ji a zuciyarsa he wish Allah ya dauki ransa ko zai huta da wannan masifa. Dame zai ji da rashin asali ko kuma da rashin natsuwa da kwanciyar hankali. Daddy da ya ji shiru ba a kawo musu breakfast ba ya tashi ya wuce Master bedroom ɗinsa ya yi wanka tare da shirya wa cikin farar shadda hatta da hular kansa fara ce a cewarsa yau farar rana ce a gareshi. Ranar da zai sake cika burinsa na aurawa Abba 'yar da ya haifa ta cikinsa wacce yake da cikakken yaƙini akanta ba za taɓa watsa masa ƙasa a ido ba. Wacce yake da tabbaci za ta dawo da farin ciki ga rayuwar Abbansa za ta zame masa bango majigina. Yana kammala shirinsa ya dubi Alh Sanusi dake zaune ya yi zugun abin duniya ya taro ya yi masa yawa a wannan stage ɗin ba abinda zai iya komai ya zo masa ne a kurarren lokaci, Alh Bashir ya shammace sa amman duk da haka ba zai kyaleshi ba dole zai dauki mataki. Daddy ya ce ya taso su je bangaren Mami su yi breakfast tun da har yanzu ba a kawo musu ba ga shi lokaci sai daɗa karatowa yake yi, Daddy yana gaba Alh Sanusi yana biye dashi tun kafin ya ɗora hannunsa akan handle ya tsikayi muryar Mami lokaci da ta dakawa Aydah tsawa duk abunda ya wakana tsakanin Mami da AB tass a kunnen Daddy wani irin ɓacin rai ne ya lallube Daddy irin wanda tsawon rayuwarsa bai taɓa riskar kansa acikinsa ba. Har wani huci yake yi ya so a lokacin ya shiga parlorn ya zantar da hukunci da yake gani shine daidai sai kuma zuciyarsa ta kwaɓe sa yanke hukunci cikin fushi shi ke kawo danasani ko addini yanke hukunci cikin fushi ba abu mai kyau bane kuma an hane musulmi da aikata hakan. Sai kawai ya juya rai ɓace ya shiga motarsa Alh Sanusi wanda ransa ya yi fari kaman takarda shima ya shiga tasa mota ya bi bayan Daddy yana ji tamkar an yi masa bushara da gidan aljanna. Ganin yake komai ya zo ƙarshe. Saboda haka ya nufi gidansa zuciyarsa wasai bashi da sauran damuwa yanzu kuma sai karkata tunaninsa zuwa ga cimma muradinsa. Babban abinda ya ƙara harzuƙa Daddy ya kira duka numbers ɗin AB waya tana ringing amma bai ɗaga ba. Dole Daddy ya kira Abdulkarim ya faɗa masa hali da ake ciki daga nan ya kira amininsa Alh Abbas matawalle suka haɗu a babban masallaci da za a ɗaura aure Ab da Aydah bayan an kammala sallar juma'a dubanan mutane suka shaida ɗaurin auren Bashir da Zulaiha akan sadaki naira dubu ɗari. Sai da jama'a suka watse sa'annan Daddy ya ja Abdulkarim gefe yana tambayarsa ina yake tunani AB zai tafi tunani ya shiga yi kafin ya ce gidansa kaitsaye can suka nufa shi da Daddy maigadi ya tabbatar musu rabon Ab da zuwa gidan an kwana biyu. Duk inda Abdulkarim yake tunani za a gansa sun je, hakan ya ƙara linkawa Daddy ɓacin rai, har sun yanke shawarar komawa gida sai Abdulkarim ya tuna da Gps maps navigation ya yi sauri dauko wayarsa ya yi ya buɗe Data ya yi tracking numbern AB take ya nuna masa location ɗin da yake "Quarter house hotel! Abdulkarim ya furta a bayyane lallai Ab ya fara zama tantiri yaushe zai kawowa ransa AB zai je ya fake a hotel sau uku suna wucewa ta gaban hotel ɗin. Da sauri Abdulkarim ya dube Daddy wanda ke ta faman gyaɗa kai yana yi ƙwafa alamar da ke nuni ba iya Mami ba har AB ɗin sai ya yi mummunan saɓa musu. "Daddy na yi tracking numbernsa yana quarter house hotel. Hamdallah Daddy ya yi kana Abdulkarim ya ja mota suka nufi can. Tun sanda AB ya shiga ɗakin hotel ɗin yake kwance ya ci kuka har fuskarsa ta kumbura ta yi ja abinka da farar fata bata da juriya ko kadan. Yana nan kwance har aka gama sallar juma'a ba zai iya tuna when last da ya rasa sallar juma'a ba. Domin tun yana yaro Daddy baya bari ya yi missing ɗin sallar juma'a sai gashi yau damuwa ta hana masa zuwa. Tun kafin Abdulkarim ya ƙarasa wurin da aka tanada domin yi parking ya hango motar AB parker a wurin ya nemi wuri ya yi parking shi da Daddy suka fito direct reception suka nufa, da kyar receptionist ɗin ya faɗa musu numbern ɗakin da yake shima sai da Daddy ya faɗa masa AB ɗansa ne fushi ya yi ya baro gida sannan fa ya basu numbern ɗakin. Da yake AB bai tsaya rufe ƙofar da key ba shiyasa Daddy yana tura ƙofar ta buɗe ya yi tozali da shalelen ɗansa kwance kamar gawa numfashinsa yana fita da kyar ga jikinsa sai kakkarwa yake yi alamar zazzaɓi mai zafi ne ya rufe shi da sassarfa Daddy ya isa kan gadon ya wani rungumo sa "innalillahi wa'inna illahim raji'um! Abba buɗe idonka ga Daddynka ya zo tashi mana yarona buɗe idonka ka ji. Kaman daga sama AB yake ji muryar Daddy a dodon kunnensa, duk iya ƙokarin sa na so gani ya buɗe idanun nasa ya kasa da sauri Abdulkarim ya fice ya je reception ya nemo taimako mutane. Suka kama masa Ab saboda ga baki ɗaya Daddy ya gama rudewa ya fita hayyacinsa suka saka shi mota direct asibiti Abdulkarim ya wuce dasu suna zuwa aka karɓe shi cikin kankanin lokaci aka bashi taimakon gaggawa har drip an saka mishi sai lokacin Daddy ya fara dawowa cikin natsuwarsa gani AB numfashin AB ya zama normal. Sai misali ƙarfe 5:15pm AB ya falka da salati dauke da bakinsa wani irin nauyi yake ji a idanunsa Daddy da Abdulkarim suka taso suna masa ya jiki ya amsa cike da jin kunyar Daddy cikin dashewar murya ya ce Abdulkarim ya taimaka masa zai shiga bathroom sai da ya kama ruwa ya yi alwala a zaune ya yi sallar azhar da la'asar da ya kammala sallar kasa tashi ya yi daga wurin sai kawai ya sadda kansa ƙasa, sosai yake ji kunyar haɗa ido da Daddy a natse Daddy ya isa gaban Ab ya zauna ya kama haɓarsa ya ɗago fuskarsa cikin tattausan lafazi yake faɗin "Ba dai jikin bane Abbana?" Wani irin rauni ne ya mamaye zuciyar AB har bai san sanda ya faɗa jikin Daddy ya ƙanƙame shi ya fashe da kuka kamar ƙaramin yaro "I'm sorry for my bad attitudes Daddy ban kyauta maka ba ni ba yaron kirki bane meyasa zan butulcewa mahaifina mai ƙaunata?" Da sauri Daddy ya ciro shi daga jikinsa ya rufe masa baki da tafin hannunsa "shhh! Banaso na sake ji ka faɗin waɗannan maganganu akanka. Abba kai ɗa ne nagari abin alfahari iyaye, kai ba butulu bane. "To amman Daddy ban kyauta maka ba na saka ka kunya sanadin abinda na yi. "Ba laifinka bane Abba laifin na Mariya ne da ta kasance mace mai kafirin son zuciya a sanadin son zuciyarta tana so ta wargaza min kan iyali ta haddasa min fitina a gidana amma ba komai nasan kalar matakin da zan dauka akanta. AB ya ja deep breath ya sauke tare da kama hannun Daddy ya ce "Daddy tashi mu je ka cika burinka ka aura min Aydah idan har aurena da ita shi ne farin cikinka Daddy na shirya tsaf zan samar maka da wannan farin ciki koda kuwa ni zan rasa nawa, Daddy ina sonka fiye da komai a duniya nan you're best father in the whole world samun mahaifi kamanka a wannan zamani sai an tona a wasu lokuta ina jin zafi idan na tuna ba kai bane biological father ɗina. Amman ko a yanzu ina godiya ga Allah subhanahu wata'ala da ya bani kai I love you Daddy I love you so very much you're my world I'm nothing without you kaine komai na, na yi alkawari ba zan sake saka ka ɓacin rai ba. Wani irin kalan murmushi Daddy ke yi farin ciki marar misaltuwa ya cika masa zuciya idanunsa suka cicciko da hawaye Allah ne kaɗai yasan adadin kaunar da yake yiwa Abba jin sa yake yi tamkar wani tsagi na jikinsa. Rungume shi Daddy ya yi yana shafar gadon bayansa yana murmushi sun dauki lokaci a haka Abdulkarim dake tsaye yana kallonsu bai ankara ba ya ji hawaye na fita daga kwarmin idonsa yana ƙara girmama hikima irin ta ubangiji iyayen AB bai buɗe idanunsa da soyayyar mahaifinsa ba sai gashi Ubangiji gwanin hikima ya haɗa shi da mahaifin da yake sonshi kamar rai da numfashi. Daddy ya yi breaking hug ɗin ya ciro dabino daga gaban aljihun rigarsa ya ɓare ya cire kwallon ya saka wa AB a baki "Abba ci dabino na daurin aurenka da Aydah ne. Wani mashi Ab ya ji ya dakar masa zuciya sai da ya runtse idanunsa wani irin kunci yake ji a can ƙasan zuciyarsa sai kace ba shi bane yanzu nan ya gama ikirarin Daddy ya aura masa Aydah yanzu kuma ya ya ji tabbatuwa aure nasu sai ya ji ga baki ɗaya duniya ta yi masa nauyi akai. Da kyar ya iya saita natsuwarsa tare da danne abunda yake ji ya kirkiri murmushin dole ya yafawa kumburarriyar fuskarsa, yana tauna dabino tamkar mai cin maɗaci. Daddy ya dubi Abdulkarim ya tambaye sa likita ya amince su tafi gida da AB? Abdulkarim ya gyaɗa kai so emotional Daddy ya kama hannayen AB ya miƙe tsaye suka fice daga ɗakin. Lokaci da Hajiya Zeena ta zo Mami ta ja ta suka shige bedroom ɗinta sai da Hajiya Zeena ta ƙare mata kallo kafin ta ce "Bani mu kashe aminiyar arziki kafin na rattabo miki labari da ɗumi-ɗuminsa don ina gani bakida labari haƙar ki ta cimma ruwa. Cike da gundarin mamaki Mami ta miƙa mata tafin hannunta suka kashe Zeena ta karkace kai ta shiga faɗin "na tabbata ba ki da labari auren Abba da Aydah ya wargaje an fasa babu shi. "Haba Zeena karki yi amfani da raunina ki dinga wasa da hankalina. "Wallahi Alh Sanusi ya je min da wannan daddaɗan labari. Ta kwashe duk yadda Alh Sanusi da Alh Bashir suka ji abunda ya wakana tsakaninta da Abba ta faɗa mata ta zarce da faɗin "a gabana ya kira Alh Bashir ya tabbatar mishi Abba dai ya bar gari don sun nemi shi kaura wambai ba su ganshi ba ya yi ɓatan dabo da alama ya ɗauki shawararki. Farin ciki ya lulluɓe Mami ranta ya yi fari tass! Ga baki ɗaya ta ji matsalolin ta sun warware saboda haka suka buɗe bajakolin hira tana faɗawa Zeena yadda aka yi auren Sadiya da Abba ya lalace wanda daga Zeena har mijinta Alh Sanusi basu da wannan labarin saboda Mami da Daddy sun boye al'amarin ne a tsakaninsu ba su bar wannan maganar ta fita ba saboda kariyar mutuncin su. Sai gashi yau Mami ta feɗewa Zeena daga biri har wutsiya. Daddy ne ya yi driving ɗinsu shi da Abba zuwa gida yayin da Abdulkarim ya shiga motar Abba ɗin. A parking lot Daddy ya baro Abba da Abdulkarim suna zantawa shi kuma kansa tsaye ya yo bangaren Mami falon tsit babu kowa Sadiya tana ɗakinta tun sanda ta watsa kayan mayenta take tana kwasan bacci sai yamma lis ta falka Siyama kuma bata dawo daga school ba Aydah kuma tana dakinta tun lokacin da Mami ta daka mata tsawa ta shige dakinta ta rufe hatta da lunch yau bata yi ba. Kwance kawai take kamar wacce aka zarewa lakkar jiki, ta kasa fahimtar takamaiman abinda ke damunta. Direct Daddy ya yi ɗakin Aydah ya murɗa handle ya ji kofar a rufe sai kawai ya yi knocking da kyar ta sauko daga kan gado ta nufi jikin ƙofar ta zare key a tunaninta Siyama ce sai ta ga saɓanin tunanin nata "Sannu da zuwa Daddy! Aydah ta faɗa cikin dashewar murya yadda ta ga fuskar Daddy a haɗe babu walwala ko kaɗan a tare dashi sai tasha jinin jikinta tsoro ya cika mata zuciya. "Mu shiga daga ciki zan yi magana dake mamana. Daddy ya yi magana tare da nuna cikin ɗakin nata jiki a sabule ta juya Daddy ya jawo stool ɗin dake girke a gaban dressing mirror ya zauna dole Aydah ta nemi gefen gado ta zauna tare da sadda kanta ƙasa zuciyarta sai bugawa take mata da ƙarfi kaman za ta fasa ƙirjinta ta fado ƙasa. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/26/2023, 2:22 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*:3256 #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 39.. Sai lokacin Daddy ya kula da yanayinta yadda tayi wani irin sanyi na lokaci ɗaya, "mamana kin kuwa ci abinci?"daddy ya faɗa cike da kulawa yana kallonta da sauri ta ɗago tana kallon daddy, kafin ta girgiza kanta "To meyasa bakici abinci ba ko wani abu ke damunki."shiru Aydah tayi lokaci ɗaya tana jin maganganun da Mami ta rikayi wanda babu abinda ta fahimta aciki da kuma yadda take hantarar yaya Abba, a yanzu ko kaɗan bata jin daɗin yadda Mami ta zama lokaci ɗaya akan yaya Abba Sai dai bata san ta inda zata fara yiwa Daddy bayani ba. Dogayen fingers ɗinta ta shiga ja batare da ta furtawa Daddy komai ba."mamana ki bude baki ki yi min magana idan akwai abunda ke damunki."daga kai tayi akaro na biyu idonta na cika da ƙwalla ga zuciyarta da take tsananin bugawa, cikin rawar murya take faɗin."Daddy meyasa Mami ta canjawa yayanmu meyasa yanzu ta daina sonsa?"ta karasa maganar hawayen idanunta suka cigaba da Rolling akan fuskarta wanda ta kasa tsayar dasu. Daddy kallonta yake yana jin wani abu na taɓa mai zuciya bai san Mami tayi nisa har haka ba sai yau da kunnuwansa suka ji masa muguye kalaman da take furtawa akan Abba wanda ko a mafarki bai taɓa tunanin Mami zata yiwa Abba Bashir haka ba. "Mamana idan na daukeki daga gidan nan na kai ki gidan yayanki za ki yadda?"za ki kula dashi za ki basa farin ciki har karshen Rayuwarki?"shiru Aydah ta yi tana juya maganganun mahaifinta acikin kanta. Kafin cikin rawar murya Aydah ta ce "Daddy tayaya ?"zan zauna daga ni sai yaya Abba a gida daya, na dauka ma'aurata kawai ne suke da wannan hurumin kuma ko a islamiyya ana faɗa. Shiru Daddy ya yi yana jinjina basira irin ta yaran yanzu kenan kananun shekaru kawai ga Aydah Amman tana da hankalin sanin wasu abubuwa anzo wurin da yake son ya wayar mata da kai ya shigo da maganar da ya shigo dashi ɗakinta. Ahankali Daddy ya riƙo hannunta yana kallon yanayin ta har fahimci wani irin sanyi da tayi lokaci ɗaya . "Mamana idan na haɗa aurenki da yayanki Abba za ki yadda ki zauna dashi har ƙarshen rayuwarki za ki yadda ki karɓi biyayyar da yar uwarki ta kasa yamin karshe ta watsamin kasa a idanu?" Kallon Daddy kawai take ta kasa fahimtar me maganganunsa ke nufi Cikin sarkewar harshe Aydah ke faɗin "Daddy Aure da kuma yayanmu?" Ta faɗa da wani yanayi acikin muryarta, ga baki ɗaya ta ruɗe a lokaci ɗaya cikin rarrashi da ban baki Daddy ya fara magana."mamana ba wani ne fa za ki aura ba yayanki Abba wanda kuka tashi gida ɗaya dashi ko sau kike yabar rayuwarmu na har abada kamar yadda mahaifiyarki ke fata?" Zuciyarta na bugawa ta shiga girgiza kai."ba zan iya jure rashin yayanmu a kusa dani ba Daddy dan Allah kace kar ya tafi Daddy ka basa hakuri hakama Mami ka bata hakuri ta janye furucinta akansa. "Mamana dole Abba yabar gidan nan a yau, ba gobe ba kamar yadda malaman makarantarku ke faɗa maku muhimmanci aure a musulunci da sharuddansa nasan kin sani Mamana, shekararki goma sha biyar ko kauye yaran da basu kai ki ba ana yimasu aure kuma su zauna da mazajensu lafiya."Mamana na daura miki aure da yayanki Abba,ya fitar da kudi acikin aljihunsa ya damƙa mata cikin tafin hannunta yana faɗin."ga sadakinki nan Mamana a hannunki Allah ya baki ikon yiwa mijinki biyayya Allah yayi miki albarka wata irin nasiha Daddy ya rika yimata wanda tunda take a rayuwarta Daddy bai taɓa faɗa mata kalamai masu kashe jiki ba irin wannan hawaye kawai take ta kasa furtawa Daddynta komai to idan ma za ta furta me zata ce masa ta san ba za ta iya cewa wanda ya kawota duniya a'ah ba akan duk hukuncin da ya yanke acikin rayuwarta haka kuma har abada ba zata iya gudun auren wanda ya kwashe shekaru goma sha biyar yana hidima da rayuwarta shine uwarta shine ubanta ta kowanne fanni idan tace ba zata zauna dashi ba a matsayin miji ta cika butulu ,wannan mutane biyu sun sakata a tsakiya kowanne da muhimmancin da yake dashi a kasan zuciyarta tana ganin yadda Daddy ya sakata cikin jikinsa yana saka mata albarka wasu irin emotions ke taruwa a kasan zuciyar Aydah wanda batasan yadda zata fassara su ba,suna cikin wannan jimamin Siyama ta kira mahaifinta a waya, yana dauka ta faɗa masa tagama gyara ko'ina ana gama daura aure Daddy ya canja shawara gara ya nunawa Mami lallai a karkashin ikonsa take bata isa ta juya sa ba anan take ya yanke shawarar yau Aydah da Abba zasu tare a gidansu bikin ma a haƙura dashi tun da ba dole bane kawai zai saka malamai su yi masu addu'a da saukar Alkur'ani za'ayi sadaka kuma Allah ya sanya Albarka acikin rayuwar aurensu. Nan take ya kira Siyama lokacin tana kokarin shiga lecture na karfe biyu Yai mata umurnin ta haƙura da lecture ɗin ta wuce gidan Ƴaƴansu ta gyara masa gidansa yau Aydah zata tare, sosai Siyama tasha mamaki, kai tsaye ta cika umurnin mahaifinta nan take ta shiga cleaning clearing gidan duk da sabone komai dake ciki sabone babu abunda aka taɓa amfani dashi na gidan dan haka bata sha wahala ba."Daddy na gama komai to ki dawo gida yanzu ki zo ki taya yar uwarki shirya kayanta bayan magrib zasu wuce kallo kurum Aydah ke bin Daddy dashi har ya gama wayar da yake yi da Siyama ya kalleta yana faɗin."mamana ki jira Siyama gatanan zuwa zata tayaki shirya kayanki. Ɗagawa daddy kai kurum tayi wani irin zazzaɓi taji yana bin jinin dake yawo lungu da sako na jikinta tsoro da fargaba suka zagaye ta lokaci ɗaya komai ganinsa take tamkar a mafarki bata taɓa ganin irin wannan auren ba zan dawo bayan magarib naga kun shirya bayanan Mamana ki samu kici abinci kinji kou?"ɗagawa Daddy kai tayi acikin tana kallonsa da idanunta da suka fara canza launi ya fice daga ɗakin har kuma lokacin Daddy yana jin tashin Muryar su Mami wanda bai san dawa take hira har haka ba. Abdulkarim ya kalli AB yana kwance akan sofa tunda suka shigo Parlor yake kwance a haka babu maganar da ta haɗasa da Abdulkarim da har ya fita yayi masu oder abinci ya dawo dan yunwa yake ji sosai ko abinci rana bai samu yaci ba, agaban idanunsa Abdulkarim yaci abincinsa wanda shi ko motsawa bai yi ba da alamar bayada niyar cin abinci."wai kai bazaka ci abinci bane?"ko mai Abdulkarim ya tuna sai kuma ya saki murmushi yana faɗin."Bara na daina yimaka zancen abincin nasan duka tunaninka yana kan amaryarka kana kamanta tunanin yadda wannan daren zai zo maka kai da babynka." Abdulkarim ya faɗa yana sakin dariyar shakiyanci, tamkar da dutsi yake magana haka AB ya yi masa banza har bayan magarib suna tare ko kaɗan babu karfi a jikinsa Daddy ya kira wayar Abdulkarim yana faɗin."sun gama haɗa kayan Abban ne?"Abdulkarim ya fadawa Daddy sun gama, to ku sameni a parlor Abdulkarim ya fadawa Daddy kawai haka babu kayan da AB ya haɗa ko yace a haɗa masa bakinsa kawai zai bata daga baya abunda yake bukata sai ya dawo ya dauka idan kansa ya huce tun bayan sallar magarib da yayi wanka yama kasa saka kayan da Abdulkarim ya dauko masa zaune yake gefen bed yana dafe da kansa da yake masa wani irin ciwo tamkar bai sha magani ba. "Ka saka kayanka Daddy na jiranka shima idan taurin kai za kayi masa sai na sani."wani kallo ya yiwa Abdulkarim yana faɗin."a gabanka zan saka kayan kenan?"girarsa ɗaya Abdulkarim ya dage "To meye aciki ka juya ka saka abunka mana. Cike da izgilanci AB ya soma warware towel ɗin jikinsa da gudu Abdulkarim ya nufi kofa yana faɗin."saboda ka fara shaye-shaye za ka cire towel agabana ."Yana faɗin haka ya juya yabar cikin bedroom ɗin Bayan tafiyar Hajiya Zeena Mami na zaune a dakinta har bayan sallar magarib gidan yayi mata wani irin shiru sai lokacin ta tuna da Aydah tun safe da tayi mata faɗa bata kara ganin wurgawarta cikin gidan ba hakama Sadiya miƙewa tayi a ɗakin Sadiya ta tsaya tana knocking kofar ɗakinta jin shiru yasa ta bugawa Aydah kofa dai-dai lokacin Siyama ta buɗe kofar ɗakin tana rike da hannun Aydah da Siyama ta taimaka mata tayi wanka har kayan da za ta saka ta zabar mata tayi mata simple make up, sororo Mami ta yi tsaya tana kallon ikon Allah gabanta na bugawa dake kallon Siyama tana faɗin."Da taci wannan kwaliyyar ina za ki kaita?" "Wurin Daddy! Siyama ta faɗa tana kallon yanayin Mami ,tamkar bata fahimci me Siyama ke nufi ba. Haka Siyama da Aydah suka bar Mami a tsaye har suka fice daga ɗakin tamkar Mami ta tuna wani abu tabi bayansu a wani irin haukace, tsaye tayi a bakin kofar parlor Daddy tana kallon mutanen dake zaune acikin parlor da mugun shock kwance acikin fuskarta,Daddy ya daga kai yana kallon yanayinta ya sauke idanunsa cikin nata idon yana faɗin."ki karaso daman yanzu zan daga waya na kiraki sai gashi kin karaso. Anan bakin kofa Mami ta tsaya tana girgiza kai so take kawai taji meye dalilin wannan taron daman AB tunda ya shigo Parlor na Daddy kansa ke a ƙasa ganin bazata shigo ba Daddy ya juya kan AB da Aydah yayi masu nasiha mai taɓa zuciya da ruhi kafin Daddy ya kama hannun Aydah dana AB ya haɗe wuri ɗaya cike da wani irin raunin murya ya ce "Na baku amanar junanku dukanku ya'yana ne matsayi ɗaya kuke dashi a wurina Allah ya baku zaman lafiya kamar yadda kuka yimin biyayya Allah ya cika rayuwarku da farin ciki ya azurtaku da ya'yanda za su sakaku farin ciki Abba tashi ka dauki matarka ku tafi luggage ɗin Aydah an sakasu a mota zan yi maka transfer kuɗin lefen Aydah ta account ɗinka, miƙewa tsaye ya yi da hannun Aydah da yake cikin hannunsa har lokaci da wani kalar ɗumin da yake jin hannayen nasu ya dauka, hawaye kawai Aydah keyi tana jin zuciyarta ta yi mata wani irin mugun nauyi addu'a take Allah yasa mafarki take Allah yasa ba gaskiya bane wannan wane irin kalar ƙaddara ce da za ta yi mata shigar kutsu. Ƙasa ƙarasawa ya yi gaban Mami yana jin yadda kafafunsa suke son kasa daukarsa kallonsu Mami keyi da wani mugun yanayi kwance acikin fuskarta karasowa Mami tayi a rude AB ya daga kai yana kallonta tunda ya tashi yayi wayau bai taɓa ganinta cikin wannan yanayin ba,har za ya buɗe baki yayi magana yaji saukar mari cikin fuskarsa a haukace mami taci kwallar rigarsa tana wani irin jijjigawa tana faɗin."Ni za ka ci wa amana Abba ni za ka yaudara?"Ni za ka watsawa kasa a ido?" Mami ta ƙarashe magana tana zare ido tamkar wacce ta samu tabin hankali ta cigaba da faɗin "Sai naga yadda yarinyata za ta zauna da marar asali tsintatce, wulakntatcce irinka. Mariyaa!!!" Daddy ya kira ta da wani irin tone, wani kallo Mami ta rika aikawa ta saitinsa kafin ta mayar da kallonta kan AB "Don ubanka ka sakar min yarinya yanzu-yanzu nan! A fusace Daddy ya karaso gabanta ya wani fisgota ya bata tagwayen mari har sau biyu a kowanne kuncenta dama da hagu cikin razana da kidima Mami ke kallon mai gidan nata kusan shekarar su Ishirin da shidda da aure Daddy bai taɓa kai hannunsa jikinta ba da sunan duka sai yau kuma duk akan ɗan tsintuwa,rai ɓace Daddy ya kalli AB Cikin kakkausar murya ya ce "ja hannun matarka ku wuce sai da safe. Haka AB yabi umurnin Daddy don ba zai iya yi masa gardama ba ya rike hannun Aydah suka fice daga Parlor cike da wani irin raunin zuciyoyin su. "Ki barmin gidana yanzu Mariya ki tafi sai na nemeki. Daddy ya faɗa with angry voice wani murmushin takaici Mami tayi tana gyada kai take faɗin."gidanka dama ba zan zauna ba har sai na tabbatar da tsinannen yaron can ya sakar min 'ya in har ina numfashi Abba bai isa yayi zaman aure da 'yata ba ka rubuta haka ka aje. Mami ta juya tana barin cikin parlor tamkar wata mahaukaciya. Tun da ya bude motar ta shiga taji wani irin kuka mai cin rai na kwace mata yanayin mami kawai da ta kalla ya yi masifar birkita mata duniyarta. Shima a bangaren AB bai yi wani yunkurin hanata kuka ba shima akwai nasa ciwon da Mami ta fama masa a kasan tashi zuciyar sai dai har lokacin ya kasa jin haushin Mami ko kankani acikin zuciyarsa, har yau soyayyar da yake yimata da 'ya'yanta babu abunda ya ragu. Sai dai bai san taya zai soma rayuwar aure da yarinyar da ya raina da hannunsa ba. Yana da lokacin daidaita komai ya kamata yayi wani abu kafin komai ya ƙarasa tarwatse masa. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/27/2023, 12:50 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*: jeddah 3256 Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 040. (MASARAUTAR KUDU) Tun lokacin da aka akai mai martaba sarki Mahmood na Uku asibiti har ila yau bai motsa ko ɗan yatsansa ba abinda ya ƙara tashe hankali iyalansa da ma masarauta baki ɗaya. Sarki Mahmood adalin sarki ne mai tausayi talakawansa da jiƙansu tun sanda ya hau karagar mulkin kudu ba a taɓa yi kuka dashi ba sai dai ka ji ana yabon ayyukansa na alkhairi. Kwanciyar sa jinya ya jawo ce-ce-kuce a cikin masarauta dama wajen masaurata mutane da dama sun fi ta'allaka ciwonsa da jifa (asiri) yanzu ma Yarima babba ne da Aliyu na Uku ke tsaye a ɗakin da aka kwantar dashi kwata-kwata Aliyu na Uku bai ga wani sauki ko cigaba a jikin nasa ba saboda haka ne ya kira Yarima babba kasancewar sa babban likita da ke jagorantar kula da lafiyar mai martaba yana masa complain na rashin gani sauki a jikin na mai martaba. "Ranka ya shi dade ni ina gani kaman an yi gaggawar fita dashi waje muma yanzu mun sami cigaba sosai duk waɗansu kayan aiki da kwararru likitoci muna dasu a ƙasar mu idan ma wani abu ya shige mana duhu mu kan nemi taimakon waɗancan likitocin turawa saboda asibitin mu yana da good connection dasu, ka ba da daman a tafi dashi Alliance hospital Abuja in-sha-Allah za a dace. Har Yarima babba ya kai aya a zancensa Aliyu na Uku bai kallesa ba idanunsa suna kan mai martaba yana kallon yadda numfashinsa ke sauka ta cikin na'urar da aka makala masa. Cike da izza nan da ta gama zagaye jinin jikinsa ya ce "A shirya mana tafiya gobe bana so a sami kowanne irin tsaiko ka tabbata daga yanzu zuwa dare ka kammala duk wani shiri na tafiyar mu. Ajiyar zuciya Yarima babba ya yi saboda yasan halin ƙanin mahaifin nasa baya magana biyu amma duk da sai ya yi yunkurin ya lurar dashi na so a yi tafiyar agaggauce "Ranka shi dade wannan tafiya bata buƙatar gaggawa... "Yarima!! Ya yi sauri tarar numfashinsa tare da ɗaga masa hannu "isa bana so surutu idan ba za ka iya ba ka barmin komai a hannuna ni zan iya. "Amman.... "Please!. Tun kafin Yarima babba ya karasa faɗar abunda zai faɗa ya sake taka masa birki dole Yarima babba ya ja bakinsa ya tsuke, suna nan tsaye sai ga yaya Gimbiya tare da magaji ƙarami da first born ɗinta Marwan, dukkansu suka gaida Aliyu na Uku da Yarima babba, yayin da Yarima babba ya gaida yaya Gimbiya Aliyu na Uku ko kallon gefen da take bai yi ba. Yaya Gimbiya ta karbi ledar da suka shigo da ita daga hannun Marwan ta fito da wata robar swan mai ɗauke da ruwan rubutu tana balle murfin take faɗin "Ai daman na gayamuku wannan ciwon na mai martaba da sa hannun makiya aka yi biris da magana ta yanzu daga wurin malam na tsamiya na fito ya jadadda min asiri aka yiwa mai martaba kuma rayuwarsa ake farauta. Ta ƙarashe magana tare da nufar gadon mai martaba za ta shafa masa ruwan rubutu cikin sauri Aliyu na Uku ya tare gabanta "Miye haka yaya Gimbiya miyasa ke a koda yaushe kike so sai an yi rigima dake? Wannan abun da ke ki ƙoƙarin aikatawa ba daidai bane kowa a garinan ya sheda cewa Malam na Tsamiya malamin tsibu ne. "Dallah dakata mai sabon birnin! banaso rashin kunya ka dai san ni ba a sa'arka ce ba akwai tazarar shekaru ɗaɗɗaya har goma sha uku na ba ka don haka ka shiga hankalinka kasan da wacce kake magana. "Ikon Allah ai ke matsalata kenan da ke yaya Gimbiya bayaso gaskiya. Aliyu na Uku ya faɗa tare da kaucewa ya bata hanya don ba zai iya da masifarta ba yanzu nan sai ta goranta masa har wankin kashi da taɓa yi masa a lokacin yatinta, sosai yake mamakin halin yaya Gimbiya na faɗa masiffafiyar mai rai ce duk yaran ɗakinsu ita ce ta fita dabam ko kaɗan bata biyo halin mai babban ɗaki ba saboda mai babban ɗaki akwai ta da sanyi hali ga haƙuri da kawaici ita dai barta da izza da taƙama shi ma wannan ya samu asali da fitowarta daga jinin sarauta kana kuma ta yi aure a gidan sarauta. Yawan mutane suna cewa Yaya Gimbiya halin kakarta wanda ta haifi Sarki Usman na uku ta biyo Hajja Chogidi ita ce masiffafiyar gaske, a zamanin da tana raye an ce hatta da sarki Mustapha na Uku yana shakkar ta ba don komai ba sai masifa da faɗanta. Duk yadda Aliyu na Uku yaso ya hanawa yaya Gimbiya aiwatar da kudirin ta ta ƙi ta saurare shi dole ya zuba mata ido, ya koma gefe yana kallonta tana dab da fara shafawa mai martaba ruwan rubutun Fulani karama ta turo ƙofa ta shigo, karaf idanunta suka sauka akan yaya Gimbiya wani irin faduwa gabanta ya yi, cikin kidimewa ta furta "A'ah! Yaya Gimbiya me kike shiri aikatawa haka me za ki shafawa mai martaba?" Cak! Yaya Gimbiya ta dakatar da abunda take yi ta juya a fusace ta kalli Fulani karama "wannan wacce irin tambayar renin wayau ce kike min Fulani karama? Kin san dai ba zan taɓa yi abunda zai cutar da mai martaba ba. Fulani karama ta yi wani kici-kici da fuska ta isa wajen gadon mai martaba tana faɗin "ban ce za ki cutar da shi ba Yaya Gimbiya amma ina so na tunarda ke abinda kika manta mai martaba ya tsani duk wani abu da ya shafi tsinbace-tsinbace idan Allah ya tashe kafaɗarsa ya sami labari kin shafa masa wannan ruwan rubutu, ba zai taba yafe miki ba. Domin a koyaushe yana gargaɗin mu da mu guje ire-iren waɗannan abubuwa na haɗa ki da Allah da manzonsa kada ki shafa masa shi idan ma kina zargin asiri ne aka yi masa ki je ki roka masa sauki wurin Allah domin shi ne ya saukar da ciwo ya kuma saukar da maganinsa. Nan take kalaman Fulani karama suka yi tasiri akan yaya Gimbiya ta kasa furta uffan dole ta maida murfin robar ta rufe ta kalli Magaji ƙarami da marwan ta ce su wuce su tafi saboda bata ga amfani zamanta asibitin ba. Yadda ta fice a fusace za ka zaci za ta tashi sama ne, dukkansu suka bi ta da kallo boyayyar ajiyar zuciya Fulani karama ta sauke tana kisimawa a zuciyata dole ta nemi hanyar da za ta haɗu da Galadima ta faɗa masa irin zargin da yaya Gimbiya ta fara yi akan mai martaba gara ya yiwa tufka hanci tun kafin wankin hula bai kai su dare ba. Washegari gari da Aliyu ya je gaida mai babban ɗaki ta nuna ƙi amincewar ta akan tafiya da mai martaba Abuja ta ce su bar wa Allah ikonsa su cigaba da addu'a idan yana da raguwar kwana a gaba Allah zai tashi kafaɗarsa, kuma duk inda za su kai shi idan Allah bai nufi ya tashi ba babu abinda suka isa su yi daga ƙarshe sai haɗa kan ƴaƴan nata ta yi ta dinga yi musu nasiha mai ratsa jinin jiki tare da ƙara tunatar dasu yarda da ƙaddara yana cikin rukunan imani. Dole Aliyu na Uku ya hakura da kudirinsa. A wannan karon Ciroma da Galadima tare suka tafi wurin boka mai Gundulelliya, bayan ya gama surkulen sa da ya share mintuna yana yi, ya ɗago fuskarsa da ke fidda wani irin maiƙo ya yi musu ƙur da dakwa-dakwan idanunsa masu masifar ban tsoro da firgitarwa har sai da Ciroma da Galadima suka tsargu da irin kallon da yake musu, gashi ba kyau gani ne da fuskar tasa ba ballantana su jure kallon nasa sai da ya gaji da kallon nasu kafin ya sheƙe da wata kalan dariya wacce bata da daɗin saurare ta fi kama da kukan jaki sai ya haɗiye dariyar tasa ya wani murtuƙe fuskarsa cikin kakkausar murya ya ce "A bisa sakaci da ka yi Ciroma ya gashi nan garin sauri ka haifar da nawa bansan ya aka yi haka ta faru ba saboda sau uku kacal mai martaba ya sha ruwan sihiri da na ba ka, hakan kuma hakan yana nufi daga yanzu zuwa kowanne lokaci zai iya samun lafiya, domin kuwa 'yar uwarsa ta fara nema masa waraka yanzu haka malamin da ta je wurinsa yana kan gabbar warware mana shiri, kuma kasani Ciroma warware wannan asiri yana nufi faɗuwarka ƙasa wanwar kai da sarautar Kudu har abada. Wani irin gumi ne ya karyo wa Ciroma bai san sanda ya fincike rawani kansa ba tsananin tashin hankali marar adadi ya bayyana akan fuskarsa sai fiffita yake da rawaninsa. *ALH BASHIR MANSION* Abdulkarim ne ya zauna a mazaunin direba ya ja motar cike da rashin kwarin jiki, ba ka ji komai ackin motar sai sautin kukan Aydah. Har can cikin zuciyar AB yana so ya rarrashe ta amma rasa kwarin gwiwa yi hakan. Sai Abdulkarim ne yake bata baki a maimakon ta yi shiru sai karawa kukan nata sauti, har suka iso gidan na AB Aydah tana shesshakar kuka AB da Abdulkarim suka fito daga motar suna jiran ta fito amman ta yi zamanta sai ma sunne kanta tsakanin guiwayoyinta da ta yi AB ya buɗe murfi gefen da take cikin taushin murya ya ce "Fito mana. Aydah ta yi banza dashi ta ci-gaba da kukanta "Baby na ce ki fito mu shiga ciki ko nai tafiyata ne?" Nan ma bata tanka shi ba haƙurinsa yana gab da karewa saboda haka a tsawace ya furta "Za ki fito ne ko sai ɓalla miki mari?" A tsorace ta ciro kanta tana kallonsa da rinannau idanunta tana wani girgiza kanta, hawaye na fita daga idanunta suna sauka akan tattausan kumatunta gani ya yi za ta ɓata mishi lokaci gashi baya cikin yanayi da zai jure iyashegenta domin dab yake da ya wanke fuskarta da mari saboda haka ya sunkuya tare da tura kansa cikin motar ya dauko ta in a bridal style cikin tafiyarsa ta zallan ƙasaita ya nufi entrance ɗin gidan da ita Abdulkarim ya bisu da kallo yana murmushi sai da suka ɓacewa ganinsa sannan ya ja mota ya tafi. Yadda yake ɗauke da ita faɗaɗden ƙirjinsa ya rufe ta ruff ƙafafuwanta kaɗai ake iya gani, sai da ya kaita main parlor kana ya zaunar da ita akan two seater yana dire ta tana sake fashewa da wani sabon kuka ya yi tsaye tare da folding hannayensa a ƙirji yana kallonta kafin ya kyaɓe baki ya juya ya nufi upstairs tana Aydah tana gani zai tafi yabar ta, ta karawa kukanta sauti har tana haɗawa da kiran sunansa "Yayanmu!! Ya tsaya cak! Ba tare da ya dawo ba ya waigo yana faɗin "Baby please karki daɗa min damuwa akan wacce nake ciki ni kaina da zan sami daman irin wacce ke ɗinan kika samu da ba abinda zai hanani kuka. Yana ƙarashe magana ya juya tare da ci-gaba da tafiyarsa daman dauriyyarsa ta kare ƙarfin hali ne kawai yake yi idan kuma ya ce zai tsaya rarrashinta gaba ɗaya karfin halin nasa zai tafi Aydah ta bisa da kallo tana cigaba da shasshekar kukanta tana cikin kukan Abdulkarim ya turo ƙofa ya shigo da sallama hannunsa rike da bakar leda ya nemi kujera dake kallonta ya zauna a natse yake kallon yadda take kuka wanda ke nuni da zallan sangarta don har wani zuburo baki take yi "Haba Aydah kada ki bani mamaki mana yaya Abbanki ne kike irin wannan kukan saboda za ku zauna a gida za mu rayu da junanku na har abada, ko kin daina sonshi ne na faɗa masa ya haɗa kayan sa yabar muku gidanku daman Mami ba son aurenku take yi ba kinga shikenan sai ki koma gunta da zama shi kuma ya yi tafiyarsa wurin da ba za ki taba ganinsa ba zai yi nisan da ke da kara ganinsa har abada. Da sauri Aydah ta ɗago kodadun idanunta tana kallon Abdulkarim agaggauce ta shiga goge hawaye fuskarta da tafukan hannayenta dukka "Na daina kuka yaya Abdulkarim dan Allah ka cewa Yayanmu kar ya tafi wallahi ina sonsa idan ya tafi mutuwa zan yi. Murmushi ne ya subuce wa Abdulkarim sai ya cigaba da faɗin "idan har da gaske kina sonsa kuma bakyso ya tafi kada ki sake yi kuka, ki kwantar hankalinki ki cigaba da yi masa biyayya kaman yadda kika saba ni kuma na daukar miki alƙawari ba zan taɓa bari ya tafi yabarki ba idan ma zai tafi ɗin sai da ku tafi tare. Yanzu ki tashi ki tafi ɗakinki ga kaza mai zafi da fresh milk na kawo miki ki ci abarki sai kin ƙoshi ki kwanta ki yi bacci abinki yaya Abba ba inda zai je kuna tare ke dashi mutu karaba takalmin kaza. Aydah ta yi murmushi ta tashi tare da amsar ledar da Abdulkarim ya miƙa mata tare suka haura bene ya nuna mata ainihin dakin Sadiya ya ce "Ki shiga ɗakinki ki tabbata kin ciye kazar dukka kada ki ragewa yaya Abba kin ji?" Ta gyaɗa kanta ta tura ƙofar ɗakin wani irin ni'imataccen ƙamshin turaren wuta ya bugi hancinta bata san sanda ta lumshe idanunta ba, ta nufi gefen gado ta zauna tana mai yaye mayafin jikinta. Direct Abdulkarim ya nufi ɗakin baccin AB yana tura ƙofa ya hango shi kwance akan ya yi matashi da hannayensa idanunsa suna kafe akan pop, da alamu ya yi zurfi a tunani. Wani bala'in tausayin sa ya kanainaye wa Abdulkarim zuciya, ya furzar da iska daga bakinsa jikinsa a macce ya ɗauke pillows ɗin da Ab ya matsar dasu gefe ya nemi kusa dashi ya zauna ya daura ɗaya daga cikin pillows ɗin akan cinyoyinsa, ganinsa da ya yi cikin wannan yanayi yasa zuciyarsa ta ɓaci ko kaɗan bai ji daɗin hakan ba shi yasan ko shine a matsayin Ab dole ya shiga damuwa. Cikin taushin murya ya kira sunansa bai amsa ba Abdulkarim bai damu da rashin amsawar tasa ba ya ci-gaba da faɗin "Ka yi haƙuri abokina ka daina wannan dogon tunani bashida amfani musamman idan ka yi duba da health record ɗinka kana da blood pressure, garin wannan tunani jini naka zai iya hawa. Nasan da matuƙar wahala ace ka karbi wannan aure faratt ɗaya amman ina son ka yi haƙuri da Aydah ka cigaba da bata kulawa kaman yadda kike acan baya sa'ilin da take a matsayin ƙanwarka. Shine kadai abunda nake tunani za ka sakawa Daddy dashi. AB Daddy yana kaunarka fiye da tunani duk wani mai tunani duk yadda na kai da son na misalta adadin kaunar da yake maka na kasa. Ina rokon ka da ka daure ka ba marasa ɗa kunya. Ka saka alkhairin Daddy ya yi maka ta hanyar riƙe masa 'ya ka kyautata mata koda kuwa baka sonta. Deep breath AB tare da dauke ganinsa ya dawo dashi kan Abdulkarim cikin dashewar murya ya ce "Ba za ka gane bane Abdul abubuwan da nake fuskanta ba masu sauki bane, jinjirarar zuciyata ba za ta iya canzawa Aydah matsayi na daga ƙanwata ba. Babban abin kunya ne agareni ace 'yar da na raina wai yau ita ce a matsayin matata wallahi Abdul abunan yana kona min rai. "Abokina kada ka zama cikin mutane nan marasa godiyar Allah akan ni'imar da ya yi musu, ni ina ji a jikina Aydah alkhairi ce a rayuwarka yarinya nan tun tana cikin tsumman goyonta take sonka da kaunarka ta buɗe idanun da sonka a zuciyarta duk da soyayyar da take maka ta 'yan uwantaka ce amman ka kwatanta idan wannan soyayyar ta 'yan uwantaka za ta iya rikidewa zuwa ta mata da miji wallahi-azim duk duniya ba za ka sami mace da za ta so ka kamarta ba. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 100[12/27/2023, 12:56 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*:Jeddah3256 Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 041. Shiru AB ya yi da alamu ya shiga nazarin maganganu Abdulkarim shi kanshi shaida ne akan irin ƙaunar da Aydah take masa haka zalika shima yana ƙaunarta sai dai ba irin wancan ƙaunar ba. A gare shi ba abu mai sauki bane ya canja mata matsayi sama da wanda take dashi tun asali a wurinsa. Ya riga da ya gama tsarawa kansa mafita, mafita da yake gani ita kadai ce hanyar da za ta warware masa wannan kurman allo. "Ni dai abokina shawarata a gare ka ka yi kokari ka danne duk abunda kake ji a duk sanda ka ji damuwa ko ƙunci a zuciyarka, ka ambaci sunan Allah ka miƙa dukka al'amurran ka a gurin sa insha Allah za ka ji sassauci Allah zai kawo maka mafita ta alkhairi, sannan kuma ka yi daure ka je ka ga halin da yarinya nan take ciki ban ce sai ka kwana guri ɗaya da ita ba at least ka nuna kulawarka akanta. Abdulkarim ya dinga bashi shawarwari nagartattu kafin ya yi masa sallama ya rako shi har wurin mota suka sake yi sallama AB yana kara yi masa godiya sai da yaga fitar sa daga gidan kana ya juya cikin gida ya tsaya ya yi switch off ɗin bulbs, ya wuce bedroom ɗinsa ruwa ya ƙara watsawa jikinsa ya shirya cikin kayan baccinsa riga da wando masu tsantsi, jikinsa yana fidda ƙamshin turarensa mai sanyayya zuciya har ya kwanta sai kuma ya tuna da nasihar da abokinsa yai masa, "maganar Abdul gaskiya ce Aydah she's my little sister ba ta cancanci ya wofintar da almurranta ba duk da banaso wannan shaƙuwa da muka yi ta cigaba da wanzuwa a tsakanin mu, dole na canza mata daga yaya Abba da tasani zuwa wani yaya Abba na daban shi ne kadai hanya da zai kawo maslaha a yayin zamana da ita. Duk Wadannan zantukan AB ke yi su a bayyane, sai kawai ya sauko da ƙafafunsa kasa ya zura bedroom slippers ya fice kansa tsaye ya kama handle ɗin ƙofar ɗakinta ya murɗa kofar ta buɗe ya kutsa kansa ɗakin wadace yake da haske domin bata kashe bulb ba, ya hango ta kwance akan gado, ta kunduddune kanta da duvet yanayinta kaman na wacce ke jin tsoro ƙarar buɗe ƙofar yasa ta zabura tana wuƙi-wuƙi da idanu yadda ta zubura yai masifa bashi dariya sai kawai ya yi murmushi Aydah tana ganin shi ne ta ja numfashi tare da saukewa, cikin dashewar murya ta ce "Yayanmu kaine?" Harararta ya yi tare da zaunawa gefen gado "Bani bane. Ya bata amsa da baƙar magana cunno baki ta yi tare da faɗin "Allah ya ba ka haƙuri yayanmu. Banza ya yi tamkar bai ji me ta ce ba sai ma ya sauya akalar zance ta hanyar nuna ledar kazar da ta aje akan gadon nata yana faɗin "menene wannan a leda da kika barsa akan gado ba za ki iya kawar dashi ba kafin ki kwanta?" A shagwaɓe ta ce "kaza ce da fresh milk Yaya Abdulkarim ya kawo min. Shiru ya yi yana kallonta da girar ido ɗage can kuma ya ce "Shine tsabar lalaci ba za ki saka fridge ba za ki barshi akan gado wai Baby Aydah sai yaushe za ki daina wannan lalacin naki da son jiki?" Rau-rau ta yi idanunta kaman za ta sa mishi kuka "Ni kam yayanmu laifi me nayi maka ka daina sona tun ɗazu sai faɗa kake min har da cewa ka yi za ka doke ni. Dan Allah ka yi hakuri Yayanmu karka tsaneni a bisa laifin da bani na aikata maka ba. Ni kaina ina ji zafi irin abubuwan da Mami take maka, haka zalika da Daddy ya fara jin ra'ayina da zan faɗa masa gaskiya ƙaunarmu ba ta aure bace ta 'yan uwantaka ce, babu aure a tsakanin mu amma sai kawai Daddy ya yi gaban kansa duk da haka ban ga laifinsa ba watakila ya hango wani alkhairi a tsakanin mu wanda mu Allah bai ba mu ikon hangon sa ba. Tun sanda ta fara magana AB ya yi mata ƙur yana kallon ɗan mitsitsi bakinta dake rattabo wannan zance har ga Allah bai taɓa tunani ta iya magana mai cike da hikima irin wannan ba saboda koda yaushe,idan za ta yi masa magana babu ta kirki a ciki sai zallan wauta da shagwaɓa ashe akwai the other side of her da baisan wanzuwar sa ba a tattare da ita. Kyakkyawar ajiyar zuciya ya sauke yayin da tausai ya kama shi, ya matsa kusa da ita ya haɗe tazarar dake tsakaninsu ya ɗora hannunsa akan kitson kanta tun wanda ya kaita aka yi mata ne har yanzu bata tsife shi ba ya shiga shafa kitson a hankali cikin taushin murya ya ce "Baby daga yanzu karki sake tunani Daddy da Mami sun yi min laifi ni a wurina ba wani laifi da suka yi min dukkansu biyu iyayena ne bani da sama dasu duk abunda za su yi min ba zan taɓa canza musu wannan matsayin nasu ba. Murmushi ta yi tare da tashi zaune tana faɗin "Kuma ba za ka sake cewa za ka doke ni ba ko yayanmu?" Murmushi ya yi tare da ɗaga mata girarsa kana ya miƙa hannun ya dauki ledar kazar ya warware ta daga cikin foil paper, har yanzu da zafinta ga ƙamshin yana fita "Iyeee! Lallai Abdulkarim munafiki ne watau nufinsa ke kadai za ki cinye wannan ƙatuwar kaza to Allah ya kama ki baby tare za mu ci kazar nan. Yadda yake magana yana zare ido irin na wanda mamaki ya kama ya ba wa Aydah dariya ta dinga kyakyalawa, AB ya yi zugun yana kallonta sai da ta yi mai isarta kafin ta kalle shi tana faɗin "Yi haƙuri yayanmu nasan ba ka son dariya Allah nima ba san lokacin da ta zo min ba. "Burina kenan na ganki kina farin ciki Aydah na dinga gani walwala da dariya akan fuskarki saboda haka ki yi dariyarki yaya Abba ba zai hana ki ba domin kuwa farin ciki shi ke haifar da dariya. Bai bari ta sake magana ba ya yago cinyar kazar ya dinga bata a baki har sai da ta ce ta ƙoshi ya bata fresh milk tasha ya umurce ta ta je ta wanko bakinta, ta kwanta koda ta dawo daga bathroom ya tattare raguwar kazar ya saka mata acikin ƙaramin fridge ɗin da ke cikin bedroom ɗin nata. Har za ta hau gado ya ce ta je ta canza kaya tasaka na bacci ta buɗe ɗaya daga cikin trolley ɗinta wacce Siyama ta yi mata arranging underwears da sleeping dress ɗinta ta dauko cotton night gown irin mai taushi nan sosai ta maida zip ɗin trolley ɗin ta rufe, ta miƙa hannunta da zimmar ta yi unzipping rigarta ta kasa tayi-tayi yaƙi buɗewa daman Siyama ce ta rufe mata, shi dai AB yana kallonta a fakaice can kuma sai ta matso wurinsa tana cuno baki "Yayanmu na kasa buɗe zip ɗinan. "To me zan miki ko ni na rufe miki shi?" Ta girgiza kai "yaya Siyam ce ta rufe min kuma yanzu bata nan balle ta buɗe min ka taimaka ka buɗe min yayanmu. Sai da ya ɓalla mata harara kafin ya ce "Ai sai kin sunkunya ko kina nufi ni zan miƙewa tsaye kuma na zuge miki zip ɗin?" Da sauri ta sunkunya daidai tsayin da zai iya zuge mata zip ɗin batare da ya tashi tsaye ba, yana unzipping rigar idonsa ya sauka akan black bra dake zagaye da gadon bayanta sosai bra ɗin ta yiwa bayan nata kyau, murmushi ya yi yana faɗin "Aydah yaushe kika fara saka wannan abar? Cike da kunya Aydah ta janye jikinta ta saka night gown ɗin hannunta ta kare fuskarta ita a dole ta ji kunya "Ban taɓa sakawa ba sai yau shima yaya Siyam ce ta bani kuma fa Yayanmu har guda uku ne. Ta ƙarashe maganar tana leƙo idanunta ta jikin rigar da ke kan fuskarta. "Gaskiya dole na dau mataki akan Siyama akan me za ta ba ki bra yaushe kika yi nonuwan saka wa bra salon ta haifar miki da ciwon kirji, daga yau karki ƙara sakawa ki jira tukkuna har su kai muzalin da za ki saka musu bra ni kaina zan siya miki kala-kala. Ɓata fuska Aydah ta yi har wani bubbuga ƙafafu take tana bala'in son bra saboda dukka ƙawayenta na school suna sakawa duk cikinsu ita kadai ce bata fara sakawa ba. Duk da tana cikin ɓacin rai tana gani Siyama ta bata bra ta ji ɓacin ran nata ya ragu, shine kuma yaya Abba yake so ya hana ta sakawa alhali tana so saboda haka ta langwaɓar da kai tare da sassauta murya ta ce "Allah yayanmu sun kara girma ba kaman da ba don ka daina ganinsu shiyasa kake tunani har yanzu 'yan mitsitsi ne. Wani irin mimmiƙe wa tsigar jikinsa ya yi yana ji wani abu yana mishi tafiyar tsutsa a cikin jininsa, sai da ya yi namijin ƙoƙari kafin ya iya furta mata "To naji je ki bathroom ki canza kayan jikinki ki zo ki kwanta dare yayi sosai. Ta juya ta nufi bathroom shi kuma ya bi ta da kallo jim kaɗan ta fito sanya da rigar wacce ta saukar mata a guiwayoyinta ta hau gado ta kwanta ya ja duvet ya rufu mata, addu'o'in tsari ya yi mata, bai baro ɗakin ba har sai da yaga ta yi bacci. Sannan ya dawo dakinsa ya wuce bathroom ya dauro alwallah gaba ɗaya daren ya raya shi ne yana kai kukansa wurin Mahaliccin sa mai kowa mai komai ya ye masa damuwar da yake ciki ya daidaita masa almurarransa. Sai around 3:30am ya kwanta. *ALH BASHIR MANSION* Bayan tafiyar AB da Aydah a fusace Mami ta dawo bangarenta ta harhada kayan sawarta a ƙatuwar trolley, Siyama sai kuka take yi tana mata magiya ta yi hakuri kada ta tafi, sai ma taƙara harzuƙa Mami ta sauke quarter fushinta akanta, ta kare mata zagi tass! Har cewa tayi ita ma Siyama ɗin munafuka ce da haɗin bakinta aka yi komai, har Mami ta sauko ƙasa sai ta tuna da Sadiya tun safe rabon da ta sake sakata a idanunta. Sai kawai ta ajiye trolley ɗinta ta sake haura upstairs dakin Sadiya ta buɗe ta shiga bata ko tsaya knocking ba, abu na farko da idanunta suka fara tozali dashi Sadiya tana yashe akan marbles yadda take kwance magashiyam ya sanya gaban Mami ya yi mummunan faduwa da saurin gaske ta isa gareta ta durƙusa gefen fuskarta tana kiran sunanta gami da girgiza kafaɗarta, Sadiya kam ko motsawa bata yi ba ballantana ta amsawa Mami kira da take mata. Sai lokacin Mami taga drugs da bottles ɗin tortulin da ke zube a kusa da Sadiyar ga kuma pieces ɗin bottle ɗin da ta fasa, ko ba a faɗawa Mami ba ta gama fahimtar mummunan hali da 'yarta ta jefa rayuwarta ciki nan da nan hankali Mami ya yi mugun tashi musamman da ta fahimci babu numfashi a jikin Sadiya jikinta ya sandare, wani irin razananne ihu Mami ta kwalla Siyama dake downstairs parlor tallaɓe haɓarta ta ji ihun Mami sai da ta zubura ta mike tsaye yayin da ta ci-gaba da jin ihun na Mami, da gudu ta haura staircase sau biyu tana kuskure faduwa. Yadda Siyama taga Sadiya kwance a sandare ita ma ta fasa ihu ita kuma Mami kuka "innalillahi wa'inna illahim raji'um! Mami ba dai yaya Sadiya ta mutu bane?" "Ban sani ba Siyama amma tabbas bata numfashi gashi jikinta ya sandare yi maza ki kirawo Daddynku shikenan burinsa ya cika Sadiya ta rasa ranta akan tsinannen yaro nan marar asali. Siyama bata bi ta kan muggan maganganu da Mami take faɗa akan yaya Abba ba ta fice da gudu, a parlor ta tarar da Daddy yana waya da rigimammen ƙaninsa Alh Sanusi sai buga wuta suke yi shi a dole so yake ya nunawa Daddy kuskurensa na aurawa Abba Aydah, kamata ya yi ya maida aurensa da Sadiya amman Aydah ta yi kankanta da aure. Shigowar Siyama a ruɗe yasa Daddy ya katse kiran batare da ya yi sallama da Alh Sanusi ba. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/28/2023, 11:00 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*: Jeddah 3256 #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 42. Rudewa da gigice yasa Mami bata kwashe kwalaben dake tarwatse a Tsakiyyar room din Sadiya ba.shigowar daddy kenan idonsa bai sauka a ko'ina ba sai kan kwalaben binsu ya shigayi da kallo kamar mai son fahimtar wani abu,sai lokacin Mami ta lura da irin kallon da daddy kebin dakin dashi nan take gabanta yayi wani irin mummunan bugawa karfin halinta ta tattara tayi dauriya cike da wata irin murya take faɗin."ka kashe Yarka da hannunka ka huta kan tsintacce wanda ba'a san Asalinsa ba.!"Mami ta faɗa cikin wani irin ihu, "Wallahi Idan wani abu ya samu sadiya ka tabbata sai nayi Shari'a dakai da kai da wanda shine sanadiyar tarwatsewar duk wani farin ciki na gidan nan."meya samu yar uwarki siyama?"daddy ya faɗa yana kallon siyama da jikinta yayi balain sanyi tana jin Mami da idanunta ,sai take ganin kamar Mami tana da son kanta dayawa.meyasa Mami ta canja lokaci ɗaya,meyesa take kokarin yiwa Allah shishigi acikin kaddarar da ya zana masu. "Nima ban sani ba daddy kamar bata numfashi."siyama ta faɗa cikin wani irin raunin murya."daddy ya taka da kafafunsa ya doshi inda sadiya take akan cinyar Mami,hannu daddy ya daga da nufin yakai jikin sadiya Mami,tayi saurin rike masa hannu tana aika masa da wani irin kallo "Me kuma yayi saura karka tabamin Yarinyya wallahi kawai ka tafi Bama bukatar taimakonka.!"Runtse ido daddy yayi yana jin kalaman Mami na wani irin tafasa masa zuciya juyawa kawai yayi yabar dakin batareda yace komai ba cike da mamaki da tsoro siyama ke faɗin wai meke damunki ne Mami.?"kema ki fita!"Mami ta faɗa tana dakawa siyama tsawa."juyawa kawai siyama tayi tabar dakin..wata irin ajiyar zuciya Mami,ta shiga saukewa tanajin zuciyarta na sauka da mugun nauyin da tayi mata tun lokacin da ta fahimci irin rayuwar da sadiya ta jefa kanta taji zuciyarta tayi wani irin dokawa."firgici da tashin hankalin da ta saki ihun da ya jawo hankalin siyama ,batajin siyama kamar yadda takejin daddy idan har ya fahimci mummunar rayuwar da sadiya ta jefa kanta to tabbas ta san Daddy,zai yanke mata hukuci akan laifin data aikata.mami ta jaye sadiya daga jikinta ta jawo pillow ta ɗora mata akai miƙewa tayi tsaye kai tsaye kasa ta nufa wannan karon babu kowa a parlor kitchen ta shige ta samu huwaila na wanke-wanke tsintsiya ta dauka da parker ta koma dakin Sadiya ta tattara kwalaben da ta farfasa,karshe dai Mami dakin ta cigaba da zama wasa gaske a dakin Mami ta kwana har taga sallar asuba, Sadiya batayi koda motsi ba baccin ta take cikin natsuwa da kwanciyyar hankali da alamar kwayoyin da tasha suna da matukar ƙarfi.toilet Mami ta shige cike da bacin rai da takaicin sadiyar ruwa ta debo a bokiti kakaf ta juyesu akan sadiya wacce ke kwance akan rug,a firgice sadiya ta farka tana tunanin ta inda ruwan ke zubo mata Ido biyu tayi da Mami dake tsaye ranta a mugun ɓace mitsittsike ido sadiya ta shigayi cike da Mamakin Meya kawo Mami a dakinta."komai ta kasa tunawa rike kanta kawai tayi da yayi mata mugun nauyi.muryar Mami taji akanta tana faɗin."na baki minti goma sha biyar kiyi wanka kiyi sallah ki sameni a daki har sallolin da kika san jia baki samu kinyi ba ki tabbata kinyi su."da haka mami ta fice daga room din na sadiya.da ido sadiya ta bita."Ya rabbi!"ta faɗa can kasan ranta me take yi haka ?"badai Mami tasan abunda take sha a boye ba.?"tafi minti biyar a haka kafin ta mike dakyar da jikakken kayanta ta nufi toilet,Mami na barin dakin na sadiya ta koma kasa ta tarar da mai masu shara tana sharar parlor,murjaa kibar gyaran parlor kije ki gyara dakin Sadiya,da girmamawa murjaa ta amsawa Mami da to,koda sadiya ta fito wanka murjaa har ta fitar da rug din da ta jike da ruwa ,ta canja bedshirt ta goge ruwan da suka sauka akan marbles.kallo ɗaya sadiya tayiwa murja ta wani haɗe rai tamkar ba'a taba halittar murmushi a fuskarta ba take faɗin."ke fita zan shirya."da haka murjaa ta juya tabar dakin sai da ta rama duka sallolin da ake binta ta nufi bangaren Mami, Ta sameta gefen gado zaune kallo daya zakayi mata ka fahimci matsananciyar damuwar da Mami ke cikinta ,nan take sadiya ta sha jinin jikinta akan soofa ta zauna tana kallon Mami,kafin ta gaisheta.mami bata damu da gaisuwar da take mata ba ta kira sunanta har sau ukku."kafin tace yaushe soyayyar ɗa namiji zata saka ki lalata Rayuwarki har haka?"shiru sadiya tayi dan ko kaɗan bata fahimci me Mami ke magana akai ba."mami ban fahimceki ba soyayya kuma bani na sakawa kaina ba Allah ne ya jarabceni Mami ,ko kema kin fara gajia bazaki tayani faɗa akan abunda nakeso ba."don kazan -kazan ubanki soyayyar taci uwarta da ubanta nabi soyayyar da gudu nasa talkami masu tsini na tattake yar banza."ina maki maganar Rayuwarki kina min maganar wani shege marar asali ki shiga hankalin ki sadiya naga alamar baki da hankali bakuma san ciwon kanki ba."Yanxu uban waye ya baki Shawarar ki fara shaye-shaye sadiya kina cikin ruwan Right mind dinki kuwa?"Mami ta faɗa da wani irin sauti a Muryarta wanda uwa kaɗai ce zata fahimci wannan yanayin.gaban sadiya banda faduwa babu Abunda yake ta dafe kanta tana tunanin ya akayi Mami Tasan wannan bangaren nata.?cikin gigicewa da rudewa sadiya ta rarrafo zuwa gaban Mami ta dafe kafafunta cikin zubar hawaye da wani irin rauni a Muryar sadiya take faɗin."Mami ba halina bane wallahi na rasa yadda zanyi da rayuwata jin nake kamar na kai karshen rayuwata na huta da ina da iko da na hana zuciyata tayiwa yaya Abba irin wannan kalar soyayyar dai dai bani da iko a wannan bangaren bazan iya jayayya da kaddarata ba Mami ina sonsa ina matukar kaunarsa idan ban zauna cikin duniyarsa ba komai zai iya faruwa da rayuwata Mami ki taimakeni na samu abunda nakeso!"sadiya ta faɗa tana fashewa da wani irin kuka mai sosa rai ,a fakaice mami ta tare hawayen dake son zubo mata duk wata hanya da ya kamata tabi tayi amfani daita dan ganin Abba bai auri Aydah ba daddy ya bata komai ya rusa masu dukkan farin cikinsu sai dai idan duk duniya zata taru akanta bazata taba karbar Abba Bashir a mijin auren yarta ba ,sai ta nunawa duniya matsayin da take dauke dashi a matsayinta Na uwa."idan na kara kamaki da laifi mafi muni irin wannan Sadiya karki tuhumeni akan matakin da zan dauka akanki tashi kibani wuri."Mami ta faɗa babu walwala akan fuskarta ,jiki sabule sadiya tabar dakin Acan kasan ranta banda kunci babu abunda takeji idan kuma ta tuna da Aydah a gida ɗaya suka kwana da yaya Abba a matsayin mata da miji sai taji duniyar na birkice mata tareda wani mahaukacin kishin da takeji akan kanwar Tata. Har yaje ya siyo masu abunda zasuyi break fast dashi Aydah bata tashi daga bacci ba.yana mamakin son bacci irin nata,dole ma ya tsara yadda zasuyi rayuwa cikin gidan nan shida Aydah idan ba haka ba Dukansu zasu wahala ,musamman ita da ya riga ya gama sangartawa ko Kitchen baya bari ta shiga to mema Aydah ta iya Bancin ta dafa ruwan tea sai dafa indomi ko kuma white rice,shara Kuma baida tabbacin tanayi duk da yawancin lokutta itake share masa bangarensa jin ana jan dogon hancinta da kuma kamshin da take shaka yasa ta shiga buɗe fararen idanunta tana zubasu cikin doguwar fuskarsa da ta kara ganin ta kara mata kyau sosai."kallonta yayi yana ɗan harararta murmushi tayi tana rufe duka fuskarta da tafukkan hannunta Cikin yanayin shawagaba take faɗin."sabahool khair yayanmu."sabahool Noor baby."how was ur night?"ta langabe kai cikin rawar murya take faɗin."nayi ta mafarkin Mami tana yimin faɗa."ta faɗa kwallah na taruwa cikin idonta, Wani irin abu yaji ya tsaya masa a wuya,sai da yayi kokarin kawar da yanayin acikin ransa.ya mike tsaye hannayensa zube cikin aljihun wandonsa na jeans yake faɗin."ki shiga kiyi wanka ki wanke toilet ki gyara dakin nan tas ki fito muyi break fast sai na kira maki Mami.!"ta ɗan ji sanyi Aranta jin zai kira mata Mami, Sai dai ayukkan da ya jero mata sunyi mata yawa murjaa itake gyara mata daki ita ke mata wankin uniform da inneawears dinta ita ke wanke mata toilet ta gyara mata gado shine Yaya Abba ke zayyano mata wannan uban aikin ashe kenan bazata gama ba sai kusan la'asar tana kokarin sauke rigar bacci agabansa yayi saurin dakatar Daita yana wani haɗe rai yake faɗin."baby fa kin girma agabana zaki cire riga ?"ta ware ido akansa tana faɗin."kai yayana ne Meye aciki sau nawa ina cire riga agabanka.banda bugawa babu abunda zuciyar Abba Bashir keyi,kofa ya nufa sai kuma ta tura baki ta kira sunanta dan tsayawa yayi ya juya yana kallon yadda ta saukar da rigar baccinta sai dai ta rufe matsanan kirjinta murmushi yayi Aransa yake faɗin."baby aydah an girma.Yayanmu wannan aikin yayi min yawa gaskiyya idan nayi wanka sai ka tayani na gyara dakin hakama toilet ,ke zaki wanke toilet da kanki bari na gyara maki dakin dai ɗan murmushi tayi ta juya ta nufi cikin toilet shi kuma ya nufi kan bed din yana gyarawa rigar baccin da ta cire ya rike yana kallo da wani yanayi da yakeji har cikin ruhinsa banda kamshin turarenta babu abunda rigar keyi.basu suka karya ba sai kusan 11 duk Aydah ta canye lokacin da wankin toilet karshe ma dai kusan shine ya wanke toilet din.cike da jin haushin kanwar tasa,bai taɓa tunanin sangartawar da yake yimata zata zamar masa matsala ba irin haka sai yanzu.'da suka gama karin kumallo Ita ta wanke plate da cup da spoon din da suka bata sai korafi take yiwa yayan nata ita ta gaji bayanta ciwo yake.kan kujerar parlor yayi kwanciyarsa itama tana kwance akan 2searter tayi dialling number mami harta katse bata dauka ba haka ta rika jerawa Mami kira ba'a daga wayar tamkar zatayi kuka take kallon Abba da kwance yake idonsa a lumshe sai dai ba bacci yake ba."ta kira sunansa cikin muryar kuka buɗe idanunsa yayi yana kallonta Mami taki ta daga wayar sai kuka baki kawai ya saki yana kallonta."Yayanmu ko mu tafi can gidan ina son naganta ,ki bari zuwa anjima ki kira maybe tana aiki shiyasa bata daga ba."shiru kawai tayi har lokacin hawayenta sun kasa tsayawa samun kanta tayi da dialling lambar siyama bugu ɗaya ta dauka Cikin Muryar kuka Aydah ke faɗin."Yaya siyam Mami fa?"ɗan shiru siyama tayi jin yanayin Muryar Aydah din ,Aydah ta cigaba da faɗin."na kira Wayarta bata dauka ba Ki kai mata dan Allah."cike da karfin hali siyama ke fadin."Mami fa na bacci."dan shiru Aydah tayi da sauri siyama tace ina yayanmu ki basa."da haka Aydah ta mike tsaye ta nufi AB ta mika masa wayar fuskarta babu wata walwala sun kai minti biyu suna waya da siyama kafin ya katse kiran Sai da azzahar tayi ya dauki car key Cike da tsoro take kallonsa yin yayi kamar bai kula da yanayinta ba yace zaije ya nemo masu lunch."zan bika dan Allah yayanmu Ni tsoro nakeji." Zan tsaya masallaci nayi sallah kema ki shiga kiyi sallah kafin na dawo bai jira me zatace ba ya fice daga Parlor da ido ta bisa tana jin hawaye na sauka akan fuskarta a hankali wannan wace irin rayuwace ita bata saba zama wuri ita ɗaya ba.ko a gida tana kallon su yaya siyam,da Mami suna cire mata kewa kuma tana karatun Hausa books a wayar Mami Anya zata iya cigaba da wannan kalar rayuwar."daman shine auren."komai ta tuna sai kuma ta Turo bakinta.aranta take faɗin."Allah ya kiyaye tayi zaman aure da yanyanta bata taɓa jin matsayinsa ya canja a zuciyarta ba. #love story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye Novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/28/2023, 11:06 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*:Jeddah3256 #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 043. Baki sake Aunty Safeena ke kallon Mami bayan ta faɗa mata yadda Daddy, yaci mutuncinta kuma yasa Abba ya dauki Aydah suka fice daga gidan akan idanunta."innalillah wa'inna ilaihir Raji'un!"Gaskiya yaya Mariya Daddyn su Sadiya ya samu matsala anya ba asiri yaron nan Abba ya yi masa ba?"yanzu kamar Aydah za a haɗa da wannan zabgagen ƙato mai kama da wrestler. Wallahi yaya Mariya muddin Abba ya yi tarayya da Aydah ba abunda zai hana ya kakkarya miki kasusuwanta, za ta sha dinkin kaman kwarya yaushe Aydah take da kwari ɗaukar bajimin namiji ingarma irin Abba?" "Kema dai kya faɗa Safeena ni fa na raini Abba koda uwar rikonsa ta mutu yana da shekara biyu da watanni uku kacal a duniya, tun daga lokaci na gama tantance girman halittarsa wallahi ba ƙaramar mace ce za ta iya daukarsa a shimfiɗa ba. Ni kam na shiga uku Safeena ina matukar tausayin Aydah yarinya jikin ɗan firitt kaman ki hura ta faɗi, ba gaba ba baya. "Duk laifin Daddyn su Sadiya ne shi bashida idanuna ne ko kuma bashi da hankali ne da kamin ya yanke wannan hukuncin bai yi duba da girman Abba da ƙarancin shekarun Aydah ba. "Bari kawai Safeena Alh Bashir ya riga ya cuce ni ga Sadiya nan ta silar wannan shegen yaron tana kokarin ɓata rayuwarta a wofi. "Ai ta ma riga da ta gamawa ɓata yaya Allah na tuba me ya rage. Safeena ta faɗa da sauri tana wani kalan taɓe baki. "Yanzu Safeena menene mafita?" "Mafita ɗaya ce ki tashi mu tafi can gidan Abba ɗin ki kashe masa gargadi da kakkausar murya kar ya sake ya taɓa miki 'ya yadda nasan shi da biyayya zai ji maganarki kafin mu nemo saukaƙkiyar hanya da za mu raba Aydah dashi. Idan ba haka ba kina ji kina gani zai yaga miki 'ya a banza watakila ma ya haifar mata da yoyon fitsari. Sosai Mami ta kaɗu da jin waɗannan zantuka daga bakin Safeena ba tare da dogon tunani ba ta tashi suka fi ce Safeena ke driving Mami tana gefenta gabanta sai faɗuwa yake yi ta kasa samun natsuwa, zuciyarta sai wassafa mata take yi tun da jiya a guri ɗaya Abba da Aydah suka kwana koda bai yi mata komai ba ya tattaba mata jiki. Horn aunty Safeena ta yi maigadi ya zo ya buɗe musu gate ta nufi parking lot ta yi parking kusan a tare suka fito daga mota koda suka shigo main parlor yana gyara tsaf sai ƙamshin turaren wuta ke tashi, bayan fitar AB Aydah da ta ji motsi komai ƙanƙatarsa sai ta zubura, duk ta bi ta tukura kanta da ta kasa samun natsuwa shine ta tashi ta koma can bayan cushion ta zauna tare da taƙure jikinta guri ɗaya turo ƙofar dasu Mami suka yi ya sa ta zubura da sauri ta miƙe tsaye idanunta suka faɗa cikin na Mami da gudu ta zo ta rungume Mami, uwa da ɗa sai Allah duk da Mami tana ji haushi Aydah saboda yadda ta ƙi yiwa Daddy bore akan wannan aure da ya yi mata don har ga Allah so tayi Aydah ta bijirewa Daddy, yanzu da ta ji Aydah a jikinta sai ta ji zuciyata ya karye har ta yi hugging nata back kukan shagwaɓa Aydah tasa "I miss you Mami I absolutely miss you ina Daddy, yaya Siyam, da yaya Sadiya meyasa Mami ba ku zo tare ba? Mami ɗazu na kiraki da wayan yayanmu you refuse to pick the call why Mami miyasa?" Yadda ta karasa magana tana zuba shagwaɓa har wanin cuno baki gaba take yi, da sauri Mami ta cireta daga jikinta har tana haɗawa da ture ta "Saboda ban ga amfani magana dake ba Aydah, lokaci da labari ya riske kika ji Daddynku ya aura miki da wancan ɗan iska yaro marar asali meyasa ba ki yi bore ba kaman yadda Sadiya ta yiwa Daddynku da ya aura mata shi. Sai gashi kin kwana gidansa cikin kwanciya hankali da walwala ko Aydah?" "Ni gaskiya Mami sai dai ki yi haƙuri ba zan iya kallon Daddy na ce masa bana so aure nan ba. Daddy yana da yakini akaina ni ce zan kawowa yaya Abba farin ciki wa rayuwar...... kafin Aydah ta ƙarashe magana Mami ta buge mata baki wani kalan raɗaɗi Aydah ta ji a bakinta sakamakon buge shi da Mami ta yi haƙora ta suka datse mata lebben ta na sama har sai da ya yi jini shafa bakin nata ta yi tana gani jini a tafin hannunta ba ma wani sosai ba ta tsandara ihu mai ƙarar gaske, daidai AB yana parking motarsa wannan ihun nata yai masifar gigitashi ya balle murfin mota ya fito ko takeaway ɗin da ya yo musu bai tsaya dauka ba ya, nufi cikin gida cikin saurinsa yana tura ƙofa daidai sanda Mami ta dakawa Aydah tsawa "ke rufe mana bakinki sakarya yarinya kawai marar kishi kai ga baki ɗaya Aydah ba kisan ciwo kanki ba. Aunty Safeena ta karɓe zancen tana faɗin "Ke yanzu banda daƙiƙanci idan aka barki da wannan gabjejen kato sai ki yi zaman aure dashi? To bari ki ji duk ranar da kika bari wannan murɗaɗɗen kato ya buɗa ki kwanakin sun ƙare ba abinda zai hanaki kamuwa da yoyon fitsari idan ma an taki sa'a kin rayu kenan ba ki mutu ba. Masifar da suke ta zubawa Aydah ya hana su ji ƙarar buɗe ƙofa da AB ya yi sai kawai ya ya yi tsaye yana saurarensu, suka cigaba da fadar maganganu marasa kyau da daɗi akansa. "Wai Mami me yayanmu ya yi miki ne da kika tsane shi har haka?" Aydah ta tambaya tana sharar hawaye da suka gama wanke mata kumatunta. "Ubanki ya yi min na ce ubanki ya yi min Aydah ana nuna miki Annabi kina runtse ido sakarya yarinya shashasha kawai to bari ki ji idan har ina ƙaunar mutuwata to ina ƙaunar wannan auren naku, maza wuce ki kira min Abba saboda duk abunda zan faɗa sakarcin ki ba zai barki ki fahimta ba. Aydah ta yi banza da Mami tana cigaba da sharɓe hawaye, damtse hannunta Mami ta kama ta girgiza ta da ƙarfi kafin ta ingiza ƙeyarta "Wuce ki je ki kira min shi tun kafin nayi mugun ɓata miki rai. Yadda Mami ta ingiza ta yasa ta yi tangal-tangal ta fadi daman ga yadda ɗan jikin yake sai a hankali ba wani karfi ne da ita ba. AB yana gani Mami tana shiri yiwa Aydah rauni ya karasa shiga parlorn yana faɗin. "Mami!!" Daga Mami har aunty Safeena waigawa suka yi, da sauri ya nufi wurin da Aydah take yashe tana gunji kuka ya ɗago ta "Sannu baby in ji ba ki ji ciwo ba??" Yana magana tare da sa ta a jikinsa daman haka ya saba rarrashinta duk lokacin datake kuka, kafin Aydah ta bashi amsa aunty Safeena ta ce "iyeee! Ba shakka Abba a gabanmu kake kwakume 'yar jinjira yarinya nan saboda ba kada kunya ba ka gaje ta ba ko?" Ran AB ya sosu da jin wannan furuncin na aunty Safeena sai dai bai isa ya mayar mata da magana ba saboda har gobe yana mata kallon ƙanwar mahaifiyarsa. "Ai idan bai yi mata hakan a gabanmu bai cika cikkaken tsintaccen, ɗa shege ba. Abba ka zama annoba gashi nan ta silarka rayuwar Sadiya tana neman gurbacewa mijina da muka yi aure shekara da shekaru ko kallon banza bai taɓa haɗani dashi ba amman saboda kai Abba ya wanke min fuska da mari. Mami ta faɗa tana huci dan ba ƙaramin haushi da tsanar Abba take ji deep down na zuciyarta sai lokaci Abba ya ɗan runsuna ya gaishesu a tsawace Mami ta ce "Kai dakata! Ban zo nan don ka gaishe ni ba na zo na kashe maka gargadi da kakkausar murya karka sake ka nemi ka haɗa shimfiɗa da 'yata domin Aydah yarinya ce ba za ta iya ɗaukar ƙato kamar ka ba. Ba zan zuba ido ka cutar min da yarinya ba ko ɗan yatsanta ka taɓa da niyar jin daɗi Allah ya isa dawainiya da na yi da kai. Kuma ka sani Abba ko tsine maka nayi wallahi tsinuwata za ta bi ka domin ba kalar wahalar da ban yi da kai ba. Har Mami ta kai ƙarshen zancenta kansa yana kasa wata zufa ce taketa keto mishi a can kasan zuciyarsa yana ta auna maganganu Mami, dukka ya danganta su da tsanar da take masa daman tana so taci zarafin sa shine ta fake da wannan zance da hankali ba zai dauka ba ko giyar wake ya sha ba zai tunkari Aydah da wata bukatarsa ba. Mami da aunty Safeena sai da suka kare masa zagi da gori kamin su fi ce jikinsa a mace ya bi su ya raka su har waje mota yana musu fatan sauka lafiya, muguwar harara aunty Safeena ta galla masa Mami kuma ta ja tsaki. Wannan irin abu ya ji ya danne masa kirji ya ja sanyayyu ƙafafuwansa ya koma cikin gida Aydah tana zaune a two seater ta kifa kanta a hannun kujarar tana abunda da ta saba, tausayin kansa da nata yake ji domin yasan duk wannan abun da Mami da aunty Safeena suka yi mata duk ta dalilinsa ne. Tausayin kansa da yake ji kuma yana tuna irin kalubalen da yake ta facing daga wannan sai wancan gaba ɗaya duniya ta yi masa zafi komai ya fice masa arai. Damuwa tana neman ta kassara masa rayuwa. Kusa da ita ya zauna cikin taushin muryarsa wacce ko da yaushe take a sanyayye da matukar wahala ka ji AB ya yi magana da kaushin murya mutane ne shi mai sanyi hali da rashin so hayaniya. "Ki yi hakuri baby ki daina kuka kada kanki ya yi ciwo. "Yaya Abba meyasa Mami za ta tsaneka me ka yi mata dan Allah?" "Baby saboda Daddy ya ƙi amincewa da bukatarsu ita da Sadiya?" "Wannan wacce irin bukata ce wacce za ta juyarda kauna da Mami take maka cikin ƙanƙani lokaci ta koma zazzafar kiyayya irin wannan? Dan Allah yaya Abba idan bai sabawa addini Islama ba ka yi musu abunda su keso ko hakan zai dawo da irin ƙaunar da Mami take maka. "Abunda suke so ikonsa baya hannuna Aydah yana hannun Daddy kuma ni mai biyayya ne ga dukka abunda ya umarci ni. Kwata-kwata Aydah bata fahimci idan kurman allon nasa ya dosa ba, sai kawai ta ce "Duk ranar da na je gida zan yiwa Daddy magana yasaka ka yi musu abunda suke so don ni gaskiya ba zan iya cigaba da jure gani Mami tana fushi da kai ba. Murmushin gefen baki ya yi tare da jan karan hancinta tasa ihun shagwaɓa ya tashi ya je ya dauko musu takeaway ɗin da ya yo musu daga Gusto restaurant suna cikin ci abinci Rumaisa ta kira wayarsa nan take Aydah taga fuskarsa ta cika da murmushi ya dauki kiran ya tsallake abinci ya haura sama yabarta da plate ɗin abinci tana jujjuya spoon, wani kololon abu ta ji ya tokare mata maƙoshi ta kasa cigaba da ci abincinta rai ɓace ta ture plate ɗin, ita daman can ta tsani Rumaisa madawaki tun kafin tasan AB ba yayanta na jini bane. Bata ƙaunar Rumaisa ko kaɗan. *MASARAUTAR KUDU* (Bangaren Kilishi) Ciroma ne ya shigo sai faman saɓa babbar rigarsa yake, yana zuwa ya zube a gaban mahaifiyar tasa "Barka da hutawa umma. Kilishi ta yi mishi kuri da idanunta tana karanta yanayinsa cikin sarƙewar lafazi ya sake furta. "Allah ya taimake ki gani hidima Jumma ta faɗamin kina so ganawa dani Allah yasa dai lafiya?" Ya faɗi haka ne a dalilin yadda yaga fuskar Kilishi a haɗe sai faman karkaɗa ƙafa take lokaci zuwa lokaci tana furzar iska daga bakinta alama ce dake nuni da ranta a ɓace yake. "Ciroma tun jiya na aika hadimi kogiji ya kira min kai kuma ya isar maka da saƙona kuma har ka ce dashi ya faɗamin za ka zo amman ba ka zo ba shin ko zan iya sani dalilinka na ƙin amsa kirana? Yaushe na zama abokiyar wasanka Ciroma?" Zufa ce taketa ketowa Ciroma a sassan jikinsa zuciyarsa ta cika da fargaba ko Kilishi ta sami labari akan plan ɗinsa ne. "Ciroma!!! Ta kira sunansa a tsawace wadda har sai da Ciroma ya zabura sai kuma ya tuna matsoraci baya zama gwani idan har yana so hakarsa ta cimma ruwa to kuwa sai ya fatattake tsoro daga zuciyarsa sai ya zama jajirtaccen namiji. "Na'am Ranki shi dade. "Ka faɗamin hakikanin gaskiya inda kake zuwa kwana?" "Allah ya ƙara miki lafiya ai ni sabgogina yawa ne dasu, saboda haka ko'ina ma zan iya zuwa. Ciroma ya yi magana kansa tsaye. "Ina so ka dakatar da duk wani shirinka Ciroma domin bakin rijiya ba wajen wasan makaho bane. Kada ka kunno wutar da ba kada ruwan kashe ta. Wani abu Ciroma ya ji ya tsarga masa rashin gaskiyar ya bayyana kiri-kiri akan fuskarsa, sai kawai ya dake tare da gyara zamansa yana tankwasa yatsun ƙafarsa ta dama sai sauti suke fitarwa ƙas!ƙas! Cikin sakakkiyar fuska ya ce "Ranka shi dade idan kika ji makaho ya ce ayi wasa 'yar jifa wallahi ya taka dutse ne Allah ya t miki nisan kwana sai nake gani kamar ruwa ne suka ƙarewa ɗan kada, kuma ni sai nake gani ranki shi dade kowa ya iya allonsa ya wanke ba laifi bane. Wani yawu mai bala'in ɗaci Kilishi ta haɗiye tana kallon Ciroma da fusatattun idanuwanta, kamin ta ce "Umarnin nake ba ka Ciroma a matsayina, na mahaifiyarka ka watsar da kudirinka akan karagar mulkin kudu ka mayar da hankalinka akan mulkar birnin kudu. "Ko zan iya sani dalili?". "Dalili bai wuce mulkin kudu bai dace da kai ba. Wata irin dariyar shakiyanci Ciroma ya sheƙe da ita sai da ya yi mai isarsa kafin ya turɓune fuska yana kallon Kilishi a ɗage tamkar ba mahaifiyarsa ba. #Love story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/29/2023, 2:19 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*: Jeddah 3256 #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 044. "Baby!hayati!" Duk ni ɗaya wannan sunayen masu tsada haka?."Ya faɗa wearing a big smile shimfiɗe akan kyakkyawar fuskarsa duk da tarin damuwar dake lullube akasan zuciyarsa. bai san miyasa duk lokacin da yaji muryar Rumaisa wani farin ciki da nishadi ke saukar masa."farin cikin ki ya yi yawa,har ana jin haka cikin muryarki ki cigaba da farin ciki."yar kankanuwar dariya ta saki cikin muryar nishadi ta ce."Ina farin ciki Habibi farin ciki da nake fatar ya dore har izuwa ƙarshen rayuwata. "Nima ina fatar haka habibty domin kuwa farin cikinki shine nawa. "Yanzu dai albishir ka?"sai da ya juya eyes ɗinsa tamkar tana ganinsa kafin yace goro fari sol. "Idan na faɗa me zaka bani a matsayin goro."komai ma zan baki, "No ban yarda ba ka faɗamin me za ka bani. Yasan jan ran Rumaisa suna iya kai dare bata faɗa masa ba. "Komai kike so zan baki. "ka tabbata ?" Wannan karon ta faɗa da muryar mai shauki da nishadi. "Rumaisa mana.!" Yadda ya kira sunanta yasa tace "owk!Daddy yana nemanka, ya amince da aurenmu a karo na biyu hayatee.!"sai da y aji bugun zuciyarsa ya tsaya na kusan sakan biyu kafin zuciyar tasa ta cigaba da bugawa da wani irin karfi,jin ya yi shiru nasa yasa Rumaisa faɗin "Da gaske nake habeebi !"dan Allah ka zo anjima mu yi amfani da damar mu,babu Abunda Daddy, zai yi maka asalima haƙuri zai baka."zan zo Rumaisa. Ya faɗa murya can ƙasan maƙoshi sallama ya yi mata yana sauke wayar akan kunnensa zaunawa ya yi a gefen bed bai san me yake ji ba a labarin da Rumaisa ta zo masa dashi ba in har da gaske take Alh Ballo Madawaki ya amince zai karbesa a matsayin suruki a karo na biyu zai auri Rumaisa to kuwa ya fi kowa sa'a a duniya farin ciki yake ji da dukkan zuciyarsa haka zai basa kariya sosai na zamansa da Aydah a gida daya,to amman kuma Daddynsa yake ji wannan lokacin bai san taya zai dauki wannan al'amarin ba. Sai da ya yi sallar magarib ya yi wanka cikin dakakkiyyar shadda ruwan kasa wacce tayi mugun karbarsa sai kamshin turare yake tamkar wanda yayi wankansu ajikinsa. Dakin Aydah ya leka kwance ya sameta tayi ruf da ciki jin karar buɗe kofar da kuma kamshin turarensa da ya rika ziyartar hancinta yasa ta maida kallonta kan kofar,cike da izzarsa ya ƙaraso cikin ɗakin nata suna haɗa ido ta wani haɗe rai ta turo baki tana juyar da kanta gefe ɗaya gefen bed ya zauna dai- dai wurin kanta."Baby har yanzu wai fushin ba'a gama ba ?"ni kawai ka ficemin daga daki yayanmu. Ta faɗa sounding so very childishness, "To tashi sai na rarrasheki. Ba musu ta mike zaune ta wani harɗe hannunta akan kirjinta wayarsa ya daga ya saita camera yana daukarta snap."kukan tabara ta fashe masa dashi da sauri ya jawota jikinsa yana dan buga bayanta alamar rarrashi, lamo tayi tana shaƙar kamshin dake tashi acikin jikinsa dagota ya yi yasa yatsansa yana goge hawayen dake zubo mata."wai ke kuka baya miki wuya baby kin zama fa budurwa yanzun. Lokaci ɗaya yanayinta ya canja ta tsani wannan kalmar ta budurwa."da sauri ya rufe bakinsa da ido yake bata haƙuri,ya mike tsaye ganin kiran Rumaisa na shigowa a wayarsa,kallonsa Aydah ke yi ya shafa kanta yana faɗin. zai je ya dawo yanzu tamkar zata yi kuka take faɗin."dan Allah ka je dani yayanmu tsoro nake ji ni kaɗai za ka bari dan Allah."ta faɗa tana wani fashe masa da wani kukan shagwaɓa. "oya tashi ki shirya minti biyar na ba ki ina jiranki a parlor. Da sauri ta sauka daga kan bed shi kuma ya juya yabar cikin ɗakin zama ya yi a parlor mintunan biyar da ya bata basu idar da cika ba ta fito cikin lack Indonesiya Abaya,mai maballai ajikinta babu komai cikin fuskarta sai man bakin da ta shafawa lebunanta sai kyalli suke sai veil ɗin abayan da tayi rolling kanta dashi . Kallonta kawai Abba yake yana kissima abubuwa da dama akanta har ta karaso gabansa ganin yadda yake kallonta yasa ta shiga juyi agabansa tamkar yadda take masa a koda yaushe idan ta yi kwaliyya yana a wuri,yayanmu na yi kyau miƙewa ya yi tsaye ya fara tafiya da sauri ta cimmasa suka jera tana faɗin."Yayanmu B bakace nayi kyau ba."kinyi kyau baby.!" Tare suka jera har cikin parking lot ya danna car key tun kafin ya saka hannunsa ajikin handling ɗin motar Aydah ta rigasa ita ta buɗe masa motar kusan a tare suka saki murmushi sai da ya shiga tayi salute agabansa tamkar wata soja harararta yayi bata san lokacin da ta saki dariya ba da sauri ta zagaya frontseat ta buɗe ta shige haka ya ja motar maigadi ya wangale masu gate a hanya Rumaisa ta ƙara kiran wayarsa wannan karon dauka ya yi ya saka a speaker."ina hanya Madam! Addu'ar isowa lafiya ta yi masa kafin ta katse kiran. Sosai ya mayar da hankalinsa kan tuki Aydah ta kara gyara zamanta tun lokacin da taga sunan Rumaisa kan wayar mood ɗinta ya canja."Yayanmu ina zamu je ne?" "Idan mun isa zaki gani ba yawo kike so ba?"To tadi zan je duk lokacin da na kai dole ki jirani."ta wani haɗe rai tana kallon sa take faɗin."To ni ka kaini gida. Ko kallonta bai yi ba baran tana ta saka ran zai amsa. dai-dai gate ɗin gidansu Rumaisa ya tsaya, ya kirata a waya tace ya shigo horn ya yi maigadi ya buɗe gate ɗin,har ya yi parking motar bata kalli gefen da yake ba. Ba a jima ba Rumaisa ta fito tun daga nesa ta hango Rumaisa ta ƙara bata rai sosai ta tsani wannan Rumaisa ɗin,hannu tasa ta buɗe gefen da AB yake zaune sanye take da riga da skirt na atamfa wanda ɗinkin ya dace da jikinta sosai haka ya yi mata kyau ta yi light make up akan fuskarta daman Rumaida badai gayu da iya tsara make up ba. Kallonsa ta rika yi soyayyarsa tana bin dukkan jinin jikinta ,ta yi masa kyau fiye da yadda zai iya kwanatantawa. fitowa yayi daga motar murya kasa-kasa ta yadda ita kaɗai zata iya ji ya ce mata tayi kyau."wani wide smile ta saki tana juya idonta alamar jin dadi. Kai tsaye bangaren da Aydah take ya nufa yaga bata da alamar fitowa, hannu yasa ya buɗe motar "fito. Ya faɗa yana daure fuska kallonsa Rumaisa take ganin wadda ta fito daga motar yasa taji zuciyarta ta yi wani mummunan bugawa, da sauri ta mayar da idanunta wurin AB dashima hankalinsa ga baki ɗaya yana kan Rumaisar, karasowa Aydah tayi tamkar bata so haka ta gaisheda Rumaisa sai da ta haɗe wani abu da taji ya tsaya mata a wuya kafin ta amsawa Aydah da kyar. Dukansu uku babu wanda ya kara magana, haka suka nufi entrance ɗin shiga gidan, duk yadda yaso ya haɗa ido da Rumaisa ta kasa basa damar hakan Parlor farko ta tsaya ta ɗan kalli AB tace ya jirata nan bari ta karasa da Aydah cikin gida, lokaci ɗaya Aydah ta haɗe rai taja ta tsaya gafda AB tana kallon Rumaisa take faɗin."ita nan yayi mata , "ki bita" Abba ya faɗa cikin sanyin murya yana kallon yanayin Aydah yadda ya tsareta da ido yasa tabi bayan Rumaisa da saboda yadda take jin zuciyarta tana iya kwadawa Aydahn mari."ki zauna anan Bara na saka mai aiki ta kawo maki Ruwa. Rumaisa ta faɗa babu wani annuri akan fuskarta ta juya tabar cikin parlor bata jima ba sai ga mai aiki a bayanta anan kan rug ta aje mata madaidaicin tray da ta shigo dashi har kuma lokacin Aydah tana tsaye taki zama. Batareda Rumaisa ta kara koda kallonta ba ta juya tabar cikin parlor, zaune ta samesa yana famar danna wayar hannunsa ɗan nesa dashi taje ta zauna, batareda ta yi magana ba har mai aiki ta shigo da tray a hannu ta aje agabansa."na tashi na tafi kenan ?"irin wannan tarbar zan samu a wurinki." Ya fada yana kallonta daman kaman jira take cikin wata irin murya mai tattare da kishi take faɗin."Basai ka nuna min ka aureta ba ba sai ka nuna min matar ka bace nasan da wannan tun jiya da igiyoyin aurenta suka hau kanka.!"wannan ai cin fuska ne. Ta ƙarasa maganar da karaya a muryarta runtse ido ya yi yana juya kalamanta aransa duk yadda zai yi mata bayani yasan bazata fahimta ba saboda kishin dake dawainiya da ita. "Ba dan na tozartaki na taho tare da Aydah ba, kin santa da tsoro hankalina bazai kwanta ba idan na barota ita kadai a gida. "Saboda ita jariri ce. Ta faɗa sounding so very jealousy "wai meyasa kike kishi da Aydah Rumaisa kin manta matsayinta a zuciyata ne kanwatace fa." "Muje parlorn Daddy yana jiranka." Ta faɗa tana kauda wancan zancen duk da yadda take jin zuciyarta na wani irin tafarfasa, har Parlor Alh Bello ta yi masa iso, kan rug AB ya zube yana gaisheda mahaifin Rumaisa da respect da fara'a ya amsa sa yana tambayarsa gida da kuma aikinsa. AB ya amsa da Alhmdullahi! shiru ne ya biyo baya na kusan minti biyar kafin Alh Bello ya nisa cikin kararriyar murya ya soma baiwa AB haƙuri ya faɗa masa shi kansa bai san meyasa yayi irin wannan tunanin ba, a karo na biyu zai kara basa auren Rumaisa dan Allah kar yace a'ah haka kuma zai je har gida ya baiwa mahaifinsa haƙuri. "Babu komai Daddy wallahi ban rike ka araina ba "Ka fara magana da mahaifinka kafin naje da kaina dan sosai mahaifinka ya kullaceni kuma kaga ba'ayi rabuwar arziki ba."Insha Allahu Daddy." AB ya dade sosai a Parlon Alh Bello Madawaki kamin ya koma wurin Rumaisa har yanzu babu wani sakin fuska atattare da ita kusan karfe tara ya yi mata sallama, har parlor ta samu Aydah hankalinta yana kan Tv amman gabaki ɗaya bata cikin yanayi mai daɗi ko kallon Rumaisa ba tayi ba ta fice daga parlorn, sai bayan da suka tafi ne Rumaisa ta dawo cikin gida, Ammi ta bita da kallo ta cire mayafin kanta ta aje a gefe. "Har ya tafi ne?"Ammi ta faɗa cike da kulawa tana kallon Rumaisa,"Eh! ya tafi." Rumaisa ta bata amsa murya a sarke "Ya naga yanayinki ya canja me kuma ya faru?" Cikin rawar murya Rumaisa ke faɗin. "Ammi kin san Bashir da shegiyar yarinyar nan yazo min."cike da mamaki Ammi ke faɗin wacce yarinya kenan?"cikin kunnar zucci Rumaisa ke faɗin."wacce aka yi masu aure. "To ke me abun damuwa tunda yarinya ce kuma ya maki alkawarin bazai kulata ba. Cikin Rawar murya Rumaisa ta ce."Ammi tsoro nake ji baki ga yadda yake son yarinyar nan ba tun tana ƙarama wata irin shakuwace a tsakaninsu fa "wuyarta dai ki shiga gidan da kin shiga ko kissa da kisisina za ki iya yi ki rabata da gidan rabuwa na har abada,shiru Rumaisa ta yi tana ya juya maganar mahaifiyarta aranta. kafin ta saki wani irin murmushi na gefen baki. Ganin yanayinta na son rigima bai kulata ba,har suka karasa gida kowa ya nufi nasa ɗakin wanka ya yi ,ya fito da alwallah sallar ishaai ya yi kusan karfe goma har da rabi ya fito nasa dakyin ya leka ɗakin Aydah ya samu tayi bacci ƙara gyara mata kwanciyarta yayi tare da yi mata addu'a ya tofa mata ya ja mata duvet,samun kansa ya yi da jan gefen cheek ɗinta Fitilar ɗakin ya kashe mata yabar mata (dim light)kasa ya sauka kitchen ya shiga ya haɗa coffee fitowa ya yi ya zauna a parlor yana sha a hankali acan kasyan ransa kuma ta yadda zai tunkari Daddy da maganar mahaifin Rumaisa kawai yake ta tunani bai san ta yadda Daddy zai dauki al'amarin ba har kusan 11 na dare yana a parlor kafin ya tashi ya kashe komai ya haura sama zuwa dakinsa,ya samu miss calls na Rumaisa har guda biyu, ya cire jallabiyyar jikinsa ya haye kan bed sai da yaja duvet ya rufe jikinsa kafin yayi dialling numberta dauka tayi da sallama a bakinta, ya faɗa mata ta kira yana down stairs yana shan coffee yanzu ya dawo ɗaki hirarsu ta masoya suka cigaba da yi cikin farin ciki kusan 12 yana ta hamma yace mata bacci yake ji "Bara na kira ka video call naga idonka. "Ko kin kira ba dauka zan yi ba. "Saboda me?". "Babu riga ajikina. 'Yar siririyar dariya Rumaisa ta yi, tana faɗin "habeebi kunyarka ya yi yawa idan muka yi aure yaya za kayi."ki bari sai ranar da aka kawoki gidana za ki ga yadda zan yi. Wannan karon ma dariya Rumaisa ta yi kafin ta sauke wayar. *MASARAUTAR KUDU* "Haba! Umma wannan wane irin son kaine? A matsayina na babban ɗa a gareki nine na dace ace ki yiwa yaƙi mulkar kudu ba ƙanina mai bi min ba idan kika yi haka tamkar kin fiffita Ahmadu akaina ne, alhali dukkan mu 'ya'yanki ne. Ina faɗa miki wannan maganar ne acikin tattausan kalami. "Kai Ciroma! Ka fi kowa sani wacece ni bana magana biyu kuma duk abunda na hana dole akwai babban dalili da yasa ni yi hakan. Saboda haka ina daɗa gargaɗin ka da ka watsar da duk wani kudirinka ka dauke idonka daga masarautar kudu. "Bantaɓa gani uwar da take yiwa ɗanta ƙafar ungulu ba sai akanki Kilishi. Wani irin zabura Kilishi ta yi a firgice ta zubawa Ciroma idanunta, ba ƙaramin kaduwa ta yi ba na ji yadda ya kira sunanta cikin gatsali, wani irin mugun tsoro ne ya lulluɓeta hanta cikinta ya kaɗa zufa tana ta faman keto mata, kafin ta samu ta lallaɓo kalmar da za ta furta Ciroma har ya tashi sai da ya kare mata kallo a sheƙeƙe kamin ya kade babbar rigarsa ya juya yana faɗin "Allah ya ba mu wuni lafiya Kilishi uwar Ahmadu. Sake jefa ta cikin zurfin tunani ya yi cikin mugun yanayi ta bishi da kallo baki sake ta ja dogon numfashi tana mai dafe saitin da zuciyarta yake. Wannan shi ake kira da ana zaton wuta a makera aka iske ta masaka an yanka ta tashi lallai tsugunne bata kare ba, wani shuɗadden al'amari wanda take kallo a matsayin kurman allo shi ne yake shiri fallasawa wannan ne kuma ba za ta taɓa bari ya faru ba dole ta yi gaggawar yiwa tufka hanci tun kamin kwabarta ta yi ruwa tsululu. *BANGAREN MAI BABBAN ƊAKI* A yau Aliyu na uku ya yanke shawarar komawa Lagos saboda tarin muhimman ayyukansa da ya baro gashi tare da Anaal yake daman ita ce idonsa idan baya Lagos, yanzu kuma gasu anan tare kuma mai babban ɗaki ta ce ba za a fitar da mai martaba waje ba don haka bai ga amfani da zaman da yake ba. Yanzu ma da ya nufo ɓangaren na mai babban ɗaki ya zo ne da zimmar yi mata sallama yau zai koma Lagos bakin aikinsa. As usual tana kishingiɗe hidimai biyu suna mata gyaran farce. Suna ganinsa suka kwashe gaisuwa ya ɗaga musu hannu kana suka fice. "Barka da hutawa Ummi! "Yawwa mai sabon birnin. "Na zo ne nayi miki sallama yau in-sha-Allah zan koma Lagos saboda irin tarin ayyukan da na baro gashi dukka da yara nan na zo daman su ne ke taimaka min idan bana nan su jagoranci ayyukan da nake yi. Shiru mai babban ɗaki ta yi na ɗan wani takaitaccen lokaci kamin ta yi gyaran murya. #love story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Team kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/29/2023, 2:22 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*:Jeddah3256 Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 045. Yadda ta yi gyaran murya yasa Aliyu na Uku ya tattara hankalinsa kacokan! Akanta duk lokaci da ta yi irin wannan gyaran murya za ta yi magana mai muhimmanci ko kuma ba da umarni. "Mai sabon birnin ina so ka natsu kasan me kake ciki lokaci yana ta tafiya shekarunka sun ja amman har yanzu bansan takamaiman inda ka sa gaba ba. Ni ce mahaifiyarka a tunanina nice mutum ta farko da na dace na san damuwarka idan kuma ni ban isa nasani ita fa iyalin naka? Mai sabon birnin kai ba yaro bane da ace Allah yasa ka yi aure da wuri da yanzu kana da ɗa ko 'ya da za ka sha mamaki yawan shekarunsa. Furuncin mai babban ɗaki na ƙarshe ya haifar masa da shiga mugun yanayi goshinsa ya tsatsafo da zufa jikinsa ya yi sanyi ya ciro handkerchief ya ciro daga aljihunsa, ya goge fuskarsa kamin ya furta "Umma na sha faɗa miki bani ciki kowacce irin damuwa ya kamata ki yarda dani da akwai da tuntuni na faɗa miki duk duniya nan banida kamarki saboda haka banga dalili da zai sa na ɓoye miki idan ina cikin wata damuwa. Kyakkyawar ajiyar zuciya mai babban ɗaki ta sauke. "Sai magana ta biyu Aliyu dangane da Fatimah (Anaal) yarinya nan girma ya kamata takai muzali aure, ka yiwa kanka faɗa ka aurar da ita tun da sauran ƙuruciyarta. "Allah ya ƙara miki lafiya har yanzu Anaal bata da ko saurayi ni kaina ina yawan tuntuɓarta amman sai ta ce min bata sami wanda ya kwanta mata arai ba. Kuma kinga bai kamata mu yi mata dole ba. "Mai sabon birnin ban ce ka yiwa 'yarka auren dole ba amman idan kana nuna mata darajar ta shine aure sai ka ga ta fito da wanda take so ba zai yiwu ace kaman Anaal bata da tsayayyen saurayi ba. "Shi kenan Ranki shi dade zan yi yadda kika ce. Ni zan wuce ki yi min addu'a. Sosai ta dinga kwararo masa addu'o'in su ka yi sallama ya fice yana fita koma ya koma ɓangarensa ya yi sallama da Hajiya Safiya, a parking lot ya tarar da Anaal da twins suna jiransa batareda da ɓata lokaci ba ya shiga mota direba ya ja ya yi dropping ɗinsu airport. Rai ɓace Ciroma yake korawa mai ɗakinsa Hajiya Umaima labari yadda suka yi da Kilishi ita ma Umaima fusata ta yi cikin masifa ta ce "Wallahi ranka shi daɗe idan har ba ka tashi tsaye tsayin daka ba kana kallo za a ci kasuwa abarka da kuturun jaki. Kaini tun da Allah ya halicci ni ban taɓa gani uwar da take yiwa ɗanta ƙafar ungulu irin taka mahaifiya, duk wani cigaban ka ba sonshi take yi ba. Ta fiffita ƙannanka akanka. To bari ka ji karka sake ka yi sanyi a wannan tafiya jikina yana bani za ka yi nasara musamman sabon aiki nan da boka mai Gundulelliya ya yi maka, mun aiwatar da duk abunda ya umarce mu cikin nasara batareda da kuskure ko ƙanƙani ba. Saboda haka ka kwantar da hankalinka washin wuƙa baya faɗar da gaban doki, ba gudu ba ja da baya in Allah ya yardar kaine sabon sarkin kudu. "Koda kuwa za a rasa rayukka masu dimbin yawa. Ciroma ya yi magana yana sakin murmushin mugunta. Fulani karama tana gani Fulani babba ta fito daga ɗakin da mai martaba yake ta fara addu'ar Allah yasa Fulani babba gida za ta tafi tun jiya take dakon ta fita, ta samu ta aiwatar da aikin da boka ya bayar ko ɗazu Galadima ya kira ta yana ƙara jaddada mata muhimmanci da mutuwar mai martaba a daidai wannan gabba, idan har suka yi sake da wannan damar to kuwa da matuƙar wahala kafin su sake samun irinta. Sai gashi Fulani babba tana so kawo musu cikass ta kasa ta tsare bata da wani aiki sai karantawa mai martaba Alqur'ani wannan ya sanya Fulani karama shiga firgici sai da Galadima ya kwantar mata da hankali, ya ce ta dai yi kokari ko ta hali yaya ta yi aikin da suka saka ta. Yanzu tana gani Fulani babba ta fito sai da ta sauke ɓoyayyiyar ajiyar zuciya. "Yaya fita za ki yi ne?" "Eh! Amman sai Yarima babba ya ƙaraso zai kula da mai martaba kamin na dawo. Da wani irin mamaki Fulani karama take kallon Fulani babba gashi sai wani irin bugawa zuciyarta ke yi amman duk da haka da ta yi kokari ɓoye firgicinta ta hanyar furta. "To ni miye amfanina yaya idan har ba zan iya kula da mijina ba? Ki tuna alhakin kula da mai martaba ba akan wuyanki kaɗai ya rataya ba nima ina da hakki, kwana biyu nan naga kin kasa kin tsare, ke kaɗai ke zama kusa dashi sai kace ke kaɗai ce matarsa. Cikin isa da zallan iko Fulani babba ta buɗe bakiinta ta ce "Ba dole na nayi kane-kane akan mai martaba ba saboda na fahimci magauta nasa na kusa dashi ne ke kokarin cutar dashi ni sai in da ƙarfina ya ƙare. Kafin Fulani karama ta kai da mayar mata da martani yarima babba ya ƙaraso ya gaishe su cikin girmamawa, Fulani babba ta yi masa umarni da ya zauna a ɗakin da mai martaba yake kada ya kuskura ya fita daga ɗakin har sai ta je ta dawo. Har Fulani babba ta ɓacewa Fulani karama da gani bata dauke idanunta daga bi ta da kallo da ta yi ba, ba ƙaramin mamaki furuncin Fulani babba ya haifar mata dashi ba yayin da tasha alwashi ko ana ha maza ha mata sai ta aiwatar da manufofin su akan mai martaba. *ABBA BASHIR MANSION* Tun bayan sallar asuba da AB ya tashe Aydah ta yi sallah ta koma bacci abinta, daman can ita masoyiyar bacci ce Mami ce ke tsawata mata akan lalaci da yawan bacci yau kuma an waye gari basu guri ɗaya saboda haka wata dama ce ta samu taci karenta babu babbaka daman shi AB ba so abunda zai takura ta yake yi ba. Har ten o'clock ya yi tana kwance cikin duvet tana sharar bacci, AB ya tashi tun eight da yake shi ba shi da ɗabi'ar baccin safe ya fita jogging ya dawo ya yi wanka ya shirya cikin ƙanana kayan ya kira Gusto restaurant ya yi musu order break fast kamin break fast ɗin ya iso ya wuce ɗakin Aydah ya tura kofa ya iso dab da fuskarta ya zauna ya kasa tashin ta ya yi sai kawai ya tsare ta da idanunsa yana kallon baby innocent face ɗinta, sai kurum ya tsince kansa da sakin tattausan murmushi kafin ya janye duvet ɗin zuwa cikin ta ya kama hannunta ya haɗe tafin hannunsa da nata ɗayan hannunsa ya ɗora shi akan kitson kanta a zuciyarsa yake yaba lazineess irin na Aydah daidai da kitson kanta idan ba shi ya matsa mata ta tsife ba sai tabar sa har sai tsaga ya ɓata wannan ma na kanta idan bai manta da lissafi ba almost three weeks ago da yinsa amma batada niyar tsife shi. A hankali yake shasshafa kitso ɗin cikin kwatacciyar murya yake kiran sunanta. "Baby! Baby! Please wake up almost past ten kina bacci ki tashi ki yi wanka ki ci break fast sai idan bacci bai isheki ba ki koma kin ji?" Yadda yake tashe ta za ka rantse da Allah yarinya mai shekaru biyu yake tayarwa, yatsine fuska tayi ta ƙara gyara kwanciyar ta, cikin wani turo baki ta yi kamin cikin shagwaɓaɓbiyar muryarta ta ce "Ni ka kyaleni ban gaji da bacci ba. "Kin ga Baby Allah dole ki tashi koda ba za ki yi wanka ba at least have a breakfast sai ki cigaba da baccinki daman can kin saba da lalaci ki ba hana ki zan yi ba. Ya karashe magana yana sakin hannunta ya kama shoulder ta sai kawai ta mirgina ta shige jikinsa, ta zagaye hannayenta akan ƙugunsa ta sunne kanta akan mararsa, tana wani kalan kukan tabara tare da shaƙar ƙamshin jikinsa nan take AB ya ji yanayinsa yana canzawa tsigar jikinsa tana mimmiƙe wa, yayin da mazantakarsa ta halba, bai san sanda ya ja deep breath ba cikin sarƙewar lafazi ya ce "Ke miye haka? Aydah ta ɗago kanta a maimakon ta bar jikin nasa sai ta ja jikinta ta manne ƙirjinta akan nasa tana kallon cikin idanunsa ta cuno baki, rigar bacci da take sanye da ita irin mai tsantse nan ce shiyasa ta jaye har yana iya gani pink lace color pant ɗinta, ga baki ɗaya Baby Aydah tana neman ta rikita dan bawa Allah, musamman yadda take kallon cikin idanunsa tana zuba shagwaɓa abinta da sauri AB ya ture ta ya miƙe tsaye jikinsa yana rawa, ya haɗe fuska cike da bada umarni haɗe da kakkausar murya ya ce "Tashi ki je ki yi wanka ki same ni a parlor. Yadda taga yayi maganar babu alamar wasa ga fuskarsa a murtuƙe yasa tayi saurin sauka daga gado, ta wuce bathroom kafin ta fito ya gyara mata bed ɗinta, murmushi Aydah tayi tana ji son yayan nata a cikin zuciyarta. Ranta farise sol ta shirya cikin party gown mai siririn hannu rigare bata wuce guiwayoyinta ba. Daga mai sai turare su kaɗai ta shafa ta fi ce, AB yana zaune akan cushion ɗin downstairs parlor yana waya da Rumaisa da gudu Aydah take tattaka mattakalar bene wanda hakan ya jawo hankali AB kanta, yadda take gudu da kuma rigar dake jikinta yasa ta dawo kamar wata 'yar tsana, kusa da ƙugunsa ta yiwa kanta masauki kallonta yake yi yana cigaba da magana da Rumaisa "Habibty na fi ki shiga damuwa babban burina mu kasance a inuwar aure, Rumaisa ke kaɗai ce mace da nake ji zan iya rayuwa irin ta aure dake ki ƙara hakuri ki bani koda two months ne kamin na yiwa Daddy maganar aurenmu a hali da ake ciki yanzu na yi gaggawa da sake bijiro da zance aure duba da dukka yaushe na yi aure. "Habibi na ba ka one month domin nima inaso na ji ɗumin mijina a kusa dani kuma Allah ne kadai yasan hali da nake shiga a duk sanda na tuna kana kwana gida ɗaya da wannan brat girl ɗin. AB ya ji zafin kalmar brat da ta kira Aydah dashi amman saboda gujewa fitinarta ya yi shiru, Rumaisa ta cigaba da jaddada masa da gaske wata ɗaya ta bashi. Tana gama magana ta kashe wayarta. Aydah da ta fahimci da Rumaisa yake waya duk tasha jini jikinta "I hate that Rumaisa, I don't love her even a little. AB ya jiyo ta tana faɗa ƙasa-ƙasa ya yi murmushi tare da mitsine mata cinya "maimata abunda kika ce ko na cire miki fatar cinya. "Ouuchhh! Ka bari yayanmu Allah da zafi zan, faɗa zan faɗa yayanmu dan Allah ka daina Allah da zafi har cikin zuciyata nake jinsa. Door bell da aka danna yasa shi miƙewa yana zuwa ya buɗe ƙofa a zaton shi delivery ne sai kawai ya yi arba da Abdulkarim riƙe da leda mai tambarin Gusto restaurant ga wani munafiki murmushi shimfiɗe akan fuskarsa "Amma gaskiya abokina kai ɗin tsohon ɗan iska ne me kake yiwa ɗiyar taka na ji tana ihun neman taimako?" Kar dai ka ce min haikewa 'yar jinjira yarinya nan ka yi. Sosai AB ya ji ransa ya ɓaci da jin abunda Abdulkarim ya faɗa sai kawai ya haɗe fuska "Me ka zo yi min a gida da sassafe nan?" "Zuwa nayi naga lafiyarka sai kuma gashi na ci karo kana lallube Babynka ashe cika bakinka na banza ne. "Bana so kuturun iskanci Ak idan za ka shigo Bismillah ga hanya in kuma za ka tsaya munafuci da shiga abunda bai shafe ka ba sai ka yi ta tsayuwa. Abdulkarim ya sheƙe da dariyar shakiyanci, AB ya ja guntun tsaki ya juya biyo shi Abdulkarim ya yi yana cigaba da dariya har da faɗin "abokina tsaya na goge maka jan baki a gefen wuyanka. AB bai saurarensa ya nufi three seater ya zauna, Aydah tana gani Abdulkarim ta washe haƙora ta gaishe dashi ya miƙa mata ledar hannunsa yana faɗin "Babyn yaya Abba ga breakfast na kawo miki. Aydah ta karbi ledar da hannu bibbiyu tana masa godiya. AB ya kalleta da daurarriyar fuska ya ce ta tashi ta je ɗakinta ta yi break fast ɗin. Yadda taga ya haɗe rai yasa bata yi gardama ta tashi ta haura sama. Hakan yasa Abdulkarim ya buɗe shafin tsokanar AB tun AB yana jin haushi har ya sake yana mayar masa da martani. Aydah har ta shiga ɗakinta sai ta tuna da bata dauko plate da spoon ba duk abinci yana cikin takeaway container amma ita tafi jin daɗi ta juye a plate sai ta ajiye ledar ta juyo sai ta tsikayi muryar AB yana faɗin "za ka gaji da iskanci ka ne ka kyale ni Ak ni da nake da ƙosasshiyar budurwa irin Rumaisa madawaki me zan tsita a jikin Baby Aydah , kana gani yarinya ba nono ba duwawu. Sai kawai suka fashe da dariya har suna tafawa cak Aydah ta tsaya duk da tana da karancin shekaru ita ɗin ba shashasha bace tabarar ta bata hana mata sani me ake nufi da aure ba, wani irin bugawa zuciyarta ta yi nan take ji ranta ya yi mugun ɓaci da sauri ta juya ta koma ɗaki ta faɗa kan gado tasa kuka ba ƙaramin zafin maganganu AB suka yi mata ba. Wato shi ya raina halittar da Allah ya yi mata kamar yarda Mami take gani ba za ta iya zaman aure dashi ba ashe shima kallo da yake mata kenan. An gayamasa girman nono da duwawu shine kadai cikakkiyar halittar mace. Abdulkarim bai tafi ba sai kusan 11:30am daman wasu takardun ne ya zo karɓa wurin AB. Bayan ya wuce AB ya nufo ɗakin Aydah, yana tura ƙofa ya ji shasshekar kukanta. "Subhanalillah! Ya faɗa cikin zaro idanu ya ƙarasa kusa da ita ya zauna ya kai hannunsa da nufi ya tashe ta zaune ta buge mishi hannu tana gunji kuka take faɗin "Karka taɓa ni bana sonka yaya Abba ka tashi ka fice min daga ɗaki. Na ji ni ba ƙosasshiyar budurwa bace bani da manya-manyan nonuwa da duwawu amman ina so ka sani ba ni na halicci kaina a haka ba, Allah da ya halicci Rumaisa da manyan abubuwa da kake so da marari a jikinta shine ya halicce ni da kananuwa kuma na gode masa da irin halittar da ya yi min, ban kuma raina ba. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/31/2023, 10:21 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*:jeddah3256 #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 046. Kanta ta saka cikin pillow ta cigaba da raira kukanta ,with shock AB ke kallonta maganganunta yake juyawa acikin kansa. Bai taɓa tunanin ƙanwar tasa zata rike wannan maganganun acikin kanta ba, har bakinta ya furta hakan. Bai taɓa tunanin wayonta har ya kai haka ba duk da kananun shekarunta. Kenan duk maganganun da yayi da Abdulkarim acikin kunnenta tsoro da fargaba da kuma wata irin kunyar Aydah suka lullube masa shi. "Ya rabbi kasa bata ji dukkan maganganun da muka tattauna da Abdulkarim bai dace Aydah taji maganganun da muka tattauna ba. Ya faɗa yana murza goshinsa da tafin hannunsa kukan Aydah yake ji yana hargitsa sa. Cikin sanyin murya ya kira sunanta banza tayi masa maganganun da su kayi da Abdulkarim akanta ba karamin tsaya mata arai sukayi ba. Kenan shima yana cikin jerin mutane da ke mata kushen halitta?'meyasa kowa ke kallonta yar kankanuwar yarinya don kawai bata da manyan boobs da duwawu. Yasan Aydah ba jin rarrashi take ba. "Tashi muyi magana baby.!"Ya faɗa cikin sanyin murya mai dauke da rarrashi acikinta. "ka tafi dan Allah Yayanmu ni bana son magana dakai." Ta faɗa sounding so very pissed up kara kiran sunanta yayi haka yasa ta miƙe daga kan gado ta nufi hanyar toilet cikin wata irin rigima yana jin yadda ta wani bugo kofar har cikin kwanyar kansa ya ji hakan. Yafi minti biyar zaune yana kallon ƙofar fitowa daga toilet ɗin, ganin Aydah batada alamar fitowa yasa shi barin dakin. Har kusan karfe 3 na rana yana a ɗaki tamkar wanda aka yiwa duka har waya yayi da Daddy kuma ya tambayi Aydah ya faɗa masa tana bacci har fargabar haduwa da Aydar yake yi. Car key ya dauka yaje ya siyo masu abinci yana dawowa direct ɗakinta ya nufa da abinci yana tura kofar ɗakin nata suka yi ido biyu daita tana zaune kan abun sallah da alamar sai lokacin tayi sallar azahar ,tura masa baki tayi tana wani kauda kanta gefe bai san lokacin da ya saki murmushi ba tsaye yayi a bakin kofar cikin kwantar da murya ya ce."Salamu Alaikum yar budurwa kinyi min izini na shigo ashe kin girma ban sani ba."wani irin kuka ta fashe dashi ta tsani wannan kalmar ta budurwa da yaya Abba ke kiranta dashi, taga abun nasa yayi yawa, ware ido yayi yana kallon yadda ta saka kanta cikin kafafunta tana yimasa kukan tabara ƙarasawa yayi wajenta ya aje ledar takeway ɗin kan bed side drawer. Zama yayi agabanta ya tankwashe kafafunsa.Aydaah!!"ya kira sunanta da wani irin tone da yasa ta daga ido ta kallesa hawayen idanunta suka kasa tsayawa. "Ɗazun me kika gama faɗa an raina maki halitta kuma bakyason kalmar budurwa yaya kikeso nayi baby.?"ta turo baki tana faɗin."Ni banda manyan kaya right sai itace keda manyan abubuwa nima shekaruna zasu kai yayanmu ba sai kunyi min gori ba. Ta karasa maganar a fusace da kuma muryar kuka kokarin miƙewa take tsaye hannu ɗaya yasa ya fisgota Ta zube akan jikinsa kifa kanta tayi acikin jikinsa ta cigaba da rera kukanta a hankali shiru yayi yana sauraren kukan nata yadda yake hargitsa masa zuciya ko kaɗan baya kaunar kukan Aydah kuma yasan ba wai jin rarrashi take ba sai an taki sa'a. Tunani yake me zai mata ta manta da maganganun da suka tattauna da Abdulkarim,yayi da yasanin tattaunawar nan da Abdulkarim bai taɓa kawowa ransa zata ji ba da basu fara taba."my better half.!"Ya faɗa daidai kunnenta make masa kafada tayi tana kara tura kanta cikin jikinsa "Me zanyi maki wanda zaisa ki huce dan Allah?" Mu fa bada wata manufa muka faɗa ba ana maganar aurena da Rumaisa ne kurum keda za kiyi karatu meye hadinki da wannan auren huun."Ya faɗa yana saka hannunsa yana tallabo fuskarta duka yana kallon cikin kyawawan idanunta da suka rine saboda kuka. Ta turo baki tana jan majina take faɗin."ai ko za ka faɗa bai kamata ka faɗa gaban abokinka ba yayanmu."kuma ai na san kai yayana ne babu aure a tsakaninmu idan kana faɗar ban cika macce ba batamin rai kake."to na daina daga yau kin haƙura?"make kafada tayi yayi rolling ɗin eyes ɗinsa yana faɗin."to faɗamin me zan maki ki hakura?"abu biyu.!"ya daga kai kafin yace "ohhhh really??"dage girarta tayi duka biyu ɗin. "Tau ina jinki."gabanta na faɗuwa take kallonsa bata san taya zai karbi zancenta ba ,duka tana bukatar abu biyu ɗin da zata faɗa yanzu, tasan kuma da wuya yaya Abban ya amince zai ma iya daukar ɗayan yayi mata to ɗayan fa?"tana bukatar waya da gaske friends ɗinta suna da waya wanda suke group ɗaya banda ita. Kuma tasan matsalar rashin wayarta duk daga wurin yaya Abba ne, daga Mami har dayddy basu da matsala. Jin tayi shiru yace "baki shirya magana ba yunwa nake ji dauko mana plate muci anan, "Yayanmu dan Allah ka kaini gida anjima da dare sai mu dawo dan Allah. Yadda tayi narai-narai da ido yasa yaja numfashi yana kallonta yake faɗin."naji ɗaya bayan la'asar zamu je faɗi daya,wannan karon hannunsa ta kamo ta rike cikin nata hannun tana kallon cikin idonsa, cikin rawar murya ta ce."Dan Allah Yayanmu za kayi min ɗayan?" Ka fara yimin Alkawari yayanmu."ki faɗa baby.!" "Yayanmu dan Allah ka siyamun waya duka Friends ɗina suna waya. Ta karasa maganar tamkar zata fashe masa da kuka girarsa ya tattare wuri ɗaya yana kallonta kamin ya ce "Tashi ki dauko plate da spoon muci abinci."ganin babu wata walwala acikin fuskarsa yasa ta miƙe tsaye ta fice daga ɗakin cikin sanyin jiki. Har suka gama cin abinci bata ga walwalar yaya Abba ba.Ya kalli ɗakin da alamar yau bai ga shara ba, "ki gyara ɗakin nan tas kiyi wanka idan munyi sallar la'asar zamu fita. Da haka ya fice daga ɗakin,cikin ƙunci ta share ɗakin tamkar zata yi kuka ganin yadda bayanta ya riƙe sai huɗu da rabi ya shigo ɗakin nata zaune take gefen bed da riga da skirt na Atamfa ajikinta kalar purple da baki kayan sun zauna daidai jikinta ga mayafinta nan aje agefe da ƙaramar handbag ɗinta ɗakin ya shiga karewa kallo sai da yayi masa yadda yakeso ya kalleta yace ta taso su tafi. Haka tabi bayansa tana yafa ɗan ƙaramin veil ɗinta da duka bayanta a waje bai damu da yanayin shigarta ba dan yasan yarinya ce...ko a mota zaman shiru suka yi sai dai ganin inda ya nufa da motar yasa ta kallesa da sauri ko kallonta baiyyi ba ya cigaba da tukinsa a natse. Manyan wayoyi ne aka zube agabanta ya harɗe hannunsa a ƙirjinsa yana kallon fuskarta yadda farin cikinta ya bayyana nan take. "Ki dauki wacce kikeso baby mubar wajen nan.!"hannu tasa tana daukar manyan wayoyin tana jujjuyasu a hannunta idonta ya kai kan latest iPhone ta dauka ganin yadda ta riketa yace ita kikeso?'"daga masa kai tayi da sauri tana tsaye ya bada card ɗinsa aka cire kudin,wani irin farin ciki ta tsinci kanta acikin tun cikin parking lot ta kasa daurewa ta rungumesa tare da peck ɗin kumatunsa "Allah ya biyaka da aljanna yayanmu. Ganin yadda ta rikesa ta zagaye hannunta a bayansa ya ɗan sunkuya tana faɗin."baby.!"da sauri ta sakesa ta karasa bangaren driver ta buɗe masa tana kallonsa still wearing a loverly smile shimfide akan fuskarta, shiga motar yayi ta mayar da kofar ta rufe zagayawa tayi frontseat ta buɗe ta shiga ta mayar da kofar ta rufe,kai tsaye office ɗin MTN suka nufa aka siya mata layi akayi mata register,tana ganin sun dauki hanyar zuwa gidansu bata san lokacin da ta riƙe masa hannu ba tana sakin yar dariya take faɗin."thank you yayanmu. Ai yana gama parking cikin parking lot ta balle marfin motar ta ruga da gudu zuwa cikin gidan tun kafin ta shiga cikin parlor take kwalawa su Siyama kira hardasu Mami, Sadiya da Mami ne zaune a parlor Sadiya tana zaune gefen Mami, yayin da plate a hannun Mami tana feeding ɗin Sadiya basu dade da dawowa hospital ba jiya cikin dare suka kwasheta sai yanxu aka sallamota, da sauri Aydah ta zagaya ta bayan kujera ta sakala hannunta cikin wuyan Mami."I miss you Mami i really miss you.!"wata uwar tsawa Mami tayi mata tana faɗin.''kasheni za kiyi da ne kin wani riƙe min wuya dallah cikani. Sauri Aydah ta saketa tana ɗan turo baki zata yi magana AB ya shigo da sallama cikin takunsa na izza da kasaita tuni parlorn ya game da kamshin turarensa, tunda ya bayyana cikin parlor Sadiya ta kafesa da idanunta wani irin bugawa zuciyarta take da sauri da sauri tamkar zata fito daga ƙirjinta samun kanta tayi da miƙewa tsaye cikin bin Umarnin zuciya da gangar jikinta ta nufesa daga Mami har Aydah kallonta suke shima tsayawa yayi cak!"yana kallonta yadda tayi wani irin rama na ban mamaki tana karasowa gafda shi ta haɗe filin da yayi saura a tsakaninsu rungumesa tayi sosai tana zagaye hannayenta a bayansa,wani irin kuka mai rauni gamida wani irin ciwo Sadiya ta fashe dashi. Jin yayi zuciyarsa ta karye lokaci ɗaya sai kokarin rabata yake da jikinsa cikin wani irin raunin murya ya kira sunanta "Sadiya!" Yana kokarin cireta daga jikinsa"Yayanmu Please karka rabani da gangar jikinka dan Allah wallahi zan iya mutuwa. Ta faɗa tana rikesa sosai tamkar wacce za'a yiwa kwacensa, cikin wani irin murya taji Mami ta kira sunanta."ta rasa sadiya wace irin manya ce !"wannan masifa har ina tamkar babu zuciya a kirjinta. Dakyar AB ya raba Sadiya da jikinsa yana jin kukanta na tabasa tamkar zata shede riƙe hannunta ya yi ya karasa daita cikin parlor ya zaunar daita ɗaya daga cikin kujerun dake zagaye da parlor."meyasa bazaki yarda da ƙaddara ba Sadiya?. Babu abunda ya canja matsayinku a zuciyata ina jinku tamkar wa'yanda muka fito ciki ɗaya daku. Ita Aydah bata tsaya sauraren dramar tasu ba ta nufi up stairs wurin Siyama dan gwada mata wayarta. AB ya kalli saitin da Mami take tana riƙe da plate ɗin shinkafar da take baiwa Sadiya cikin wani irin sanyin murya ya gaisheta ta dauke kanta akansa ta kalli Sadiya kamar zata shege jikinsa."za ki taso ki karasa cin abincin ko sai kin gama nacewa mutumin da bai san darajar ki ba mutumin da bai san halacci ba, runtse ido yayi yana jin kalaman Mami na ratsasa suna samun wurin zama a zuciyarsa tare da illata ruhinsa, miƙewa tsaye yayi ya fice daga Parlor da wani irin kallon tsana Mami ta bisa da tana da iko da ta kashe Abba Bashir da hannayenta ta tsani duk wani abu da ya shafesa tana ganin yadda Sadiya ke famar goge hawayen da suka kasa tsaya mata har lokacin ba zata iya haƙura da soyayyar yayan nata ba ba zata iya rasasa ba ya kamata tayi wani abu akai dan zuciyarta na gafda bugawa. Siyama na rike da wayar Aydah a hannunta take faɗin."lallai yayanmu yana ji dake baby sis?"kin san nawa wannan wayar take kuwa? Tafi tawa fa tsada fa. Aydah jin tayi kanta ya ƙara girma bata san lokacin da ta juyawa siyama ido ba. Siyama ta haɗa wayar ta saka mata caji anan ɗakinta zamanta ta gyara akan gadon Siyama ta kalli Siyama dake rike da wani text book tana dubawa ta daga kai ta kalli Aydah ganin ta bata rai lokaci ɗaya, "Ban san me nayiwa Mami ba kwanan nan tabi ta tsaneni nida yayanmu. Ta faɗa da wani irin sauti mai karya zuciya anan ta baiwa Siyama labarin yadda Mami tayi mata, murmushin gefen baki kurum Siyama tayi mata ita kanta mamin fushi take daita tun ranar da aka daura auren Abban da Aydah bata kara samun farin ciki ba Komai tayi Mami tayi ta hantararta tana mata tsawa tana ce mata munafuka sai kace ita ta daura auren Abba da Aydah."Yanzu kije ki bata haƙuri maybe kinyi mata laifi. "To kuma idan naje tayi min tsawa fa ko ta korani?" "Ai bazata yi ba tunda haƙuri za ki bata. Da haka Aydah tabi shawarar Siyama da ido Siyama ɗin tabita har ta fice daga dakin na Siyama. Acan ƙasan ran Siyama tausayin little sis ɗinta ne manne a zuciyarta babu kowa a parlor juyawa tayi ta koma sama ɗakin Sadiya ta buɗe a hankali ta ɗan tura kanta suka yi ido biyu da Sadiyar da take bin ta da wani mugun kallo a bakin kofa ta tsaya tana ƙarewa Sadiyar kallo sai yanzu ta lura da yar ramar da tayi wacce kana gani har cikin idanunta. "Yaya Sadiya bakida lafiya ne?" "Ubanwa ya faɗa maki bani da lafiya ki wuce ki barmin ƙofar ɗaki ko na taso nayi kuli-kulin kubra dake. Ɗan turo baki tayi ta juya tabar kofar ɗakin na Sadiya dake masifa tana jin da kusa ga Aydah take da ta kwada mata mari tana kin yadda Sadiyar ke kwala mata kira akan tazo ta rufe mata kofa da gudu Aydah ta ƙarasa ƙofar ɗakin Mami." #love story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [12/31/2023, 10:25 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU *AREWABOOK*: Jiddah 3256 Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 047. Ta tura ƙofar ɗakin Mami cikin sanɗa ta ƙarasa kaman munafuka cikin yanayi na tsoro ta yi sallama Mami wacce fitowar ta daga bathroom kenan ta gallawa Aydah uwar harara tana faɗin "Me kika zo yi min a ɗaki?" "Mami zuwa nayi na ganki Allah Mami na yi kewarki. "Mtss! Ai ni Aydah kin gwada min da wuya ake yanka, tun da har kika zaɓi bijere min ki duba hali da 'yar uwarki take ciki duk akan wannan gantalalle yaro amman kika iya amincewa da aurensa Sadiya ta mutu ko tayi rai ke kan ba abunda ya shafe ki, sai walwala da farin ciki kike yi. Ke ko kunya bakya ji kin aure mijin'yar uwarki. Hawaye ne suka fara bin kumatun Aydah Mami tana gani ta fara dulmiyar da tunani Aydah sai ta matsa kusa da ita ta kama haɓarta ta ɗago da fuskarta ta jefa idanunta cikin na Aydah, cike da wayau ta cigaba da faɗin. "Aydah ki tuna Abba shine wanda ya raine ki haifar ki ne kawai bai yi ba, amman duk wani abu na halittar jikinki ba wanda bai sani ba to taya ma kike tunani wanda ya gama sani cikin da waje na halittarki zai iya zama dake a matsayin matarsa. No matter how Abba ba zai taɓa iya kallonki a matsayin matarsa ba gara ki yiwa Daddynku bori ya raba aure nan Abba ya sami damar mayar da Sadiya. Girgiza kai Aydah ta shiga yi hawaye suna taruwa akan kuncinta "Mami ki yi haƙuri ba zan iya bijirewa Daddy ba saboda ya yarda dani kuma yana da tabbacin zan masa biyayya bayan duk wannan yadda da ya yi min sai na watsa masa ƙasa a ido wallahi Mami ba zan iya ba. Kawai dai zan miki alƙawa.... "Ya isa na ce ya isa Aydah tunda har ban isa dake ba ban isa na saki ko na hana ki ba, kama hanya ki tafi karki sake zuwa inda nake daga yau babu ni babu ke wuce ki barmin ɗakina shashasha kawai. "Mami Please!! "Fita ko na rufe ki da ɗan banza duka useless girl. Mami da ta fahimci Aydah za ta cigaba da yi mata magiya sai kawai ta kama damtse hannunta ta tura ta waje ta rufe ƙofarta, Aydah ta faɗi zaune a take ta fashe da matsanancin kuka cikin sauti mai ƙarfi, sautin kukanta ne yasa Siyama fitowa da sauri yayin da Sadiya tana jin kukan Aydah ta saki murmushi zuciyarta, ta cika da farin ciki tasan kukan nata yana da alaka da Mami ta cije lower lips ɗinta tana kisima irin abubuwa da za ta yiwa Aydah har sai ta bar gidan Abba bada shiri ba. "Subhanalillah! Aydah menene me kike yiwa kuka?" "Yaya Siyam! Sai kuma ta kasa cigaba da magana ta rushe da kuka. "Talk to me lil sis ko faɗuwa kika yi ne?" Aydah ta girgiza kanta cikin harɗewa harshe ta ce "Mami ce Yaya Siyam. "Ikon Allah! Aydah dan Mami ta kore ki daga ɗakinta ai bai kamata ki dinga wannan taratsin kukan ba. Sai a zaci wani mummunan abu tai miki. "Yaya Siyam ba korana kaɗai ta yi ba cewa ta yi babu ni babu ita kar na sake zuwa inda take. Yaya Siyam miye laifina anan ba ni nace Daddy ya aura min Yayanmu ba radinsa kansa ya aura mana junanmu kuma dukkan mu ba za mu iya bijirewa masa ba. Duk da dukkan mu ba son junanmu muke yi ba. Numfashi Siyama ta sauke ta ɗaga Aydah ta miƙe tsaye ta kama hannunta suka nufi ɗakinta ta zaunar da ita gefen gado kana ta zauna kusa da ita cikin taushin murya take faɗin "Duk yadda nake so na fahimtar dake Aydah ba za ki taɓa ganewa ba kawai dai zan ce dake duk abunda Mami za ta ce ko ta sakaki ki amsa mata kurum amman kada ki yi ko ɗaya kawai so nake ki daina musu ko gardama da ita. "Yaya Siyam.... "Please Aydah don't say anything ki yi abunda nace kin ji lil sis bana ji daɗi yadda Mami ke treating ɗinki. Aydah ta share hawayenta da suka kasa tsayawa ta tashi ta fice da sauri Siyama ta ciro mata wayarta daga charging ta maida charger ɗin acikin box ɗin wayar, ta bi bayanta AB yana zaune a mota yana waya da Rumaisa Aydah ta buɗe front seat ta zauna tana sharar hawaye da bayan hannunta, batareda da ya kashe wayar ba ya maida hankalinsa kanta yana firfito da idanunsa "Ke da wa me aka yi miki kike kuka?" Aydah bata yi magana ba sai kawai ta kifa kanta a dashboard tana shasshekar kukanta wanda har da shagwaɓa acikinsa, ga baki ɗaya AB ya ruɗe ya manta da waya yake yi ya ajiye wayar batare da ya sami damar disconnected ɗin kiran, ya ɗago fuskar Aydah tuni fuskarta, ta ta caɓe da hawaye da majina "Ya subhanalillah! Please Baby, stop crying, I don't want to see tears coming out of your eyes kukanki yana saurin ɗaga min hankali wallahi. Zuwan Siyama ne yasa ya maida tambayarsa zuwa kanta cikin sanyi murya ta faɗa masa ita da Mami ne bai ce komai ba ya karɓi wayarta da Siyama take miƙa mata. "Ki shiga gida Siyama mu za mu wuce daman ta matsa ne na kawo ta sai dare na dawo na dauke ta amman tun abun ya zama haka gara mu koma gida. "Shi kenan Yayanmu Allah tsare ya kaiku lafiya lil sis sai mun yi waya ko? Tun da yanzu kina da naki waya ba sai mun dame yaya Abba da kira ba. Aydah ta gyada mata kai AB ya yi reverse ya fi ce daga parking lot kamin ya nufi gate Balmo maigadi ya buɗe masa, sai da suka dau hanya kamin ya tuna da wayar da yake yi da Rumaisa a firgice ya dauko wayar still Rumaisa ba ta kashe ba dukka abunda ya wakana tsakaninsu akan kunnenta, sai kawai ya kashe kiran ya yi concentrate tukinsa. A maimakon ya nufi gida sai ya wuce da ita Aj beauty palace and spa yana buƙatar ayi mata kitso ya gaji da gani kanta a ya mutse yau kan har gyara jikin aka yi mata, Aydah har da su kuka sa'ili da ake tirza fatar jikinta ana cire datti. After four hours har kitso an kammala mata a lokaci har an kammala sallar isha kamin ta kira AB sai gashi ya zo tun acikin ya shagon ya kama cheeks ɗinta ya goga tsini hancinsa akan nata yana yaba yadda ta yi kyau ita kuma sai daɗi take ji tana washe haƙora, yana riƙe da hannunta suka fito daga shagon shi ya buɗe mata murfin mota ta shiga sannan ya shiga ya tashi mota, sai da ya tsaya ya yi musu takeaway ya kuma siya musu tsire yasan Aydah da son tsire, sai da dukkan su biyu suka yo wanka shi ya shirya cikin fararen kayan baccinsa sai dai bai rufe bottoms ɗin rigar ba, ita kuma ta saka riga da wando light pink wando iya cinyarta rigar kuma ta kaɗan ta wuce cibiyarta, ta saki kitsonta da aka yi mata two step mai zigzag ya sauka gefen wuyanta jikinta ta ko'ina fidda ƙamshi turare yake. Ta sauko parlorn ƙasa ta nemi cushion ta zauna ta miƙar da ƙafafuwanta akan kujerar ta jingina bayanta a hannun kujerar, ta dukufa dannar wayata yau farin tass! Take ji ranta yaya Abba ya wanke mata duk wani takaicinta na duniya. Burinta ta mallaki wayata kanta sai gashi yau yayanta ya cika mata wannan burin nata. Abba yana ƙoƙarin saukowa ƙasa Rumaisa ta kira sa kaman ba zai yi picking ba saboda yasan karshenta za ta yi masa ƙorafi abunda ya faru ɗazu gudun korafi da mita yasa bai kira ta ba. Ya yi picking cikin taushin murya ya kira sunanta a dalili ya ji ta ya shiru sai ta ja wani kalan numfashi wanda ke bayyanar da ɓacin ranta a fili, kamin ta zarce zuwa ga gundarin maganarta "Nagode Habibi nagode sosai da wulaƙanci ba sai ka yi min hakan ba zan fahimci muhimmancin da Aydah take dashi a wurinka. Abba ni na kira ka fa amman tsabar wulaƙanci ka ajiye waya kana rarrashi 'yar gold, kamata ya yi ka bani uzurinka mu yi sallama in yaso ka dinga rarrashinta har a busa ƙaho sai ka ajiye min waya ina ji duk abunda kake yi, tsakani da Allah Abba na gaji da kalolin wulaƙanci da kake min. Sai da ya murza fatar goshinsa yana sauke numfashi kafin ya ƙara yi ƙasa da murya ya shiga rarrashinta shi mutum ne da baya so tashin hankali ko kaɗan shiyasa duk yadda Rumaisa ta kai da so su yi rigama baya biye mata sai ya kwatar da kansa yana rarrashinta, yana daɗewa kafin ya yi fushi sai dai fa duk ranar da ya yi fushi abin ba kyau, kamin ya sauko wani jan aiki ne. Ya cigaba da rarrashin Rumaisa dakyar ya samu ta sauko ya faɗa mata zai ci abinci idan ya kammala before ya kwanta bacci zai kira ta da haka suka yi sallama zuciyar Rumaisa wasai ita gani take yi tana juya AB son ranta. Har ya iso cikin parlor ya yi kusa da kanta batasani ba saboda ta yi nisa sosai akan wayarta, ya kai hannunsa ya wafce waya sai da Aydah ta diro ƙasa tana haɗawa da ihu don ta tsorata, tana gani yayanta ne ya yi mata wannan danye aiki sai kawai ta fara kukan nata na zallan shagwaɓa, kukan da babu hawaye ya ajiye wayata ta, a centre table ya kama hannunta ya miƙar da ita tsaye ya maida ta kan kujera ya zaunar da ita yana faɗin ta bari ta ci abinci zai bata wayar kansa ya je kitchen ya dauko plates ya juye musu abinci tare suka ci sai dai dukkan su ba su ci sosai ba shi ya haɗa coffee ita kuma ta ci tsirenta da ya siya mata bayan sun kammala still shine ya tattare wuri hatta da ledar tsire shi ya ɗauke, ba abunda ta yi cikin natsuwarsa wacce ta zama mishi jiki ya faɗa mata gobe monday za ta koma school ita kanta Aydah ta yi farin ciki ji za ta koma school saboda ta nunawa ƙawaye ita fa ta faso gari ta yi waya ta kece raini. Washegari gari tun da asuba da AB ya tashe ta yi sallah ya hanata komawa bacci suka yi tilawa Alqur'ani mai girma sai 6:30am suka gama ya umarce ta da ta je tayi wanka, ta shirya cikin clean uniform ɗinta. 7:30am daidai ya yi dropping ɗinta a school ya kawo three thousand ya bata duk da yana da tabbaci ba abinda za ta yi dasu. Ya dawo gida ya kwanta ƙarfe 10:22am ya kammala shirinsa na tafiya office ya haɗa coffee ya sha ya hau motarsa sai da ya fara biyawa gida ya gaida Daddy da Mami gani Daddy yana nan yasa dole Mami ta amsar gaisuwar tasa har da karin tambayarsa Aydah ya ce tana school. Yana fitowa ya tarar da Sadiya tsaye jikin motarsa ko kaɗan bai yi mamaki ganinta ba saboda, yasan za ta aikata fiye da hakan nan take ya murtuƙe fuska, ya yi tamkar bai gannta ba ya buɗe mota ya shiga kamin ya tashe motar sai kawai Sadiya ta ɓalle murfin front seat ta shiga ta zauna a natse ya kalleta sai lokaci ya lura da kayan bacci ne sanye da jikinta riga da wando irin masu tsatsin nan ya kauda fuska. "Sadiya dan Allah ki fita sauri nake yi idan magana kike so yi dani ki yi hakuri har na dawo daga office zan biyo ta nan. Tun sanda ya fara magana cikin zallan natsuwa da taushin murya Sadiya ta yi mishi kur da idanunta, tana kallon yadda tattausan laɓɓansa ke motsi ji take kamar ta kai mishi sumbata akansu, a halin yanzu komai AB ke yi bala'in burge ta yake yi sai da ta ja deep breath kamin ta furta "Shikenan zan jira ka Yayanmu nasan za ka zo saboda ba ka saba faɗar karya ko saɓa alƙawari ba. Amman kafin na fita inaso na faɗa maka Yayanmu ina sonka kwatakwacin yadda nake so rai da numfashina na yarda na kuma amince soyayyarka jabranta ce gare ni da zan iya yaƙi da zuciyata Yaya Abba da na yi yaƙi da ita ta dangana da kai kasantuwar a yanzu kana matsayin mijin ƙanwata ne, sai dai zuciyata ba za ta iya ba domin ta yi nitso acikin kogin sonka da ƙaunarka. shiyasa na yanke wa kaina shawara zan nemi soyayyarka ko ta ƙarfin tsiya wata kila za ka, kalle ni a matsayin mai sonka kai wata kila kuma za ka ce ina da matsala a ƙwaƙwalwata amman a zahirin gaskiya sonka ne kawai ya yi min yawa idan akanka ne yaya Abba bana ji bana gani na kuma shirya wa fuskantar kowanne irin kalubalen. Na yi zurfin a sonka har bana iya banbance me nafi so a tare da kai ba, zai iya zama muryarka ko kuma kyawunka, amma in mun hadu sai na ji gaba ɗayanka nake so tinda zuciya ta bataso nayi son kai. Dan haka na shirya tsaf domin cikar muradin zuciyata, ni ban damu da ka soni ko karka soni ni dai kawai naga na mallake ka a matsayin nawa ni kaɗai anan ne zan tantance tsakanin me nake so a tare da kai na kuma share kokwanto na. Batareda AB ya ce uffan ba sai jujjuya key ɗin mota yake yi tana dasa aya ya ce "To naji duk abunda kika faɗa Sadiya ba kuma zan hana ki abunda shaɗaniyar zuciyarki take kisimamiki akaina ba. Kawai alfarma guda za ki yi min ki fita min daga mota kada ki sa nayi latti akwai masu jira na a company. Yadda ya yi magana cikin tattausan kalami yasa ta buɗe motar ta fita amman duk da haka sai da ta sake tuna mishi da tana jiransa kar ya saɓa alƙawari bai ce da ita komai ba ya ja motarsa ya wuce office, ya tarar da ayyuka da dama yana cikin duba wasu cars design kira ya shigo wayarsa na wata baƙuwar number ta truecaller yaga sunan Anaal Aliyu na Uku sai lokacin ya tuna da kulla yarjejeniyar kasuwanci da kamfanin KIM'S Automobile ya yi requesting za su yi a can Lagos. Cikin sanyi muryarsa ya ya picking wani abin mamaki muryar Anaal na Uku tana sauka a dodon kunnensa ya ji wani irin bugawa zuciya ita ma Anaal ana ta bangaren haka ta ji ita har da wani sanyi-sanyi ke ratsa kasusuwan jikinta, tun sanda kamfanin whitepaper Automotive Germany ya nemi su kulla yarjejeniyar kasuwanci da kamfani su AB bata taɓa magana dashi a waya ba iyakanci su chat shima sau biyu ne suka taɓa magana, gaba ɗayansu jikinsu ya dau rawa sakamakon jin muryoyin junansu. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/2, 9:38 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye. 048. Da kyar Abba ya haɗa natsuwarsa guri ɗaya ya amsa sallama da gaishesa da Anaal ta yi, ba ƙaramin namijin kokari Anaal ta yi ba da ta iya tattara kalaman bakinta har ta tuna masa da makasudin kira shi da ta yi sun dauki mintuna biyar shiru kafin AB ya iya bata amsa da cewa zai zo on Wednesday daga nan suka yi sallama. Ya maida ganinsa akan secretary Skyler wacce ta shigo ofishin nasa lokacin da yake waya da Anaal. "What is happening Skyler? "Sir, there is a girl who wants to see you. I told her to wait. I will let you know if you want to see her because her name is not in the list of people who have an appointment with you. Shiru AB ya yi tare da nazarin wacce yarinya ce za ta zo neman sa ƙosai wannan mahaukaciya ce Sadiya yasan Skyler tasan Rumaisa da ita ce bama za ta tsaya jiran permission ɗinsa ba za ta bankaɗo ƙofa ta shigo. "She told you her name?" "Yes sir she said her name is Mufeeda Habib Bichi sir she's beautiful.tsayawar da fuskarsa yayi cikin ta Skyler yana son ya tuna inda ya taɓa jin sunan kafin kwakwalwarsa ta tariyo masa komai Wannan karon bai san meya kawota ba.Ya rabbi !"kasa wannan karon abubuwa suzo masa da sauki ya faɗa murya can ciki har lokacin Skyler na tsaye tana jiran umurnin maigidan nata,ya juya kan Skyler ya faɗa mata tace ta shigo.kamshin turarenta ne ya fara ziyartarsa kafin ya daga kai ya kalleta , gaskiyyar Skyler ne mufeeda ta cika macce a duk inda namiji yake neman macce cikakkiyya mufeeda ta kai ,zama tayi akan doguwar soofar dake girke a katafaren office din nasa ta dauki kafa daya akan ɗaya ta cigaba da bin AB din da wani asiritaccen kallo wanda ya kasa fassara sa."mufeeda ya kike!"Ya faɗa yana kallon gefen da take murmushi ta ɗan saki cike da kunya tana sauke murya take faɗin."ina kwana.!"dan har lokacin safiya ne,lafiya lau ya guda ya kwana biyu."muryarsa kawai da takeji tana sata cikin wani irin yanayin kaunarsa mai dulmiyar daita.cikin rawar murya take faɗin."gida lafiya lau Alhmdullahi,ta faɗa cikin rawar murya idonta na taruwa da hawaye lokaci ɗaya,duk girmanta duk kyawonta duk ajinta durkusawa tayi agaban Abba Bashir tana wani irin kuka na ban mamaki mai taɓa zuciya da ruhin mai saurare lumshe ido yayi a hankali ko kaɗan bayason kukan macce har cikin kansa yakejin kukanta yana wani hargitsa Ba shiri ya taso daga kan kujerar da yake zaune ya tsaya a gabanta.da sanyin muryarsa ya kira sunanta ta dago kanta fuskarta da hawaye har lokacin da suka kasa tsayawa."mufeeda tashi ki zauna muyi magana."Ya faɗa yana bata umurni kanta take girgiza masa cikin raunin murya take faɗin bazan tashi anan ba har sai ka amince da zaka aureni Abba,nayi kokarin na cireka araina nabi umurnin mahaifina hakan bai yuyuba.idan ka amince zaka aureni zan kaika wurin baffana a daura aurenmu baffana yana da jinkai ba kamar mahaifina ba da yake da zafi."ina sonka ina sonka Abba tun ranar da na fara ɗora idanuna akanka!"wani irin bugawa zuciyarsa keyi da sauri da sauri wannan wace irin rayuwace?"daga wannan sai wannan."shiru ya ratsa a tsakaninsu na kusan minti biyar Abba ya faɗa cikin duniyar tunani ta yadda zai bullowa Al'amarin mufeeda batareda ta kara jefa kanta cikin rikici ba ko taji haushinsa.mufeeda tashi zauna muyi magana,yadda yayi mata magana cikin sauke kai ta zata zaiji tausayinta yace zai aureta sai tayi yadda yace ta tashi ta koma kan soofa ta zauna ta shiga share hawayenta da mayafin kayanta.zaki yimin wata alfarma mufeeda."daga kai tayi tana kallonsa sai ya daga mata kai ya cigaba da faɗin."ki dauka kaddarar haɗuwarmu bazai sa muyi aure ba mufeeda ki dauki haka a matsayin ƙaddara Acikin salloli biyar ki rika addu'a Allah ya cire maki soyayyata aranki ya kawo maki Alkhairi acikin Rayuwarki."mufeeda aurenmu bazai yuyuba bazan boye maki ba mahaifina ya riga yayi min aure tun lokacin da Mahaifinka yaki yadda da zancen aurenmu ko sati ɗaya baayi ba.kallonsa take cikin tashin hankali da kidemewa cikin rawar murya take faɗin "na amince zan zo a matsayin matarka ta biyu na yadda zanbi matarka yadda kakeso zan tafi da duk yadda ka tsara gidanka.ba karamin karya masa zuciya Nabeela tayi ba.bai taɓa sonta ba,yaji mugun tausayinta sosai,sai ya zauna ya soma rarrashinta cikin kalamai masu tausasa zuciya kuma babu laifi ta fahimcesa har bakin mota ya taka mata sai da yaga motarta ta fice daga harabar companyn ya shiga sauke numfashin da yake rike dashi addu'a ya shigayi aransa Allah yasa karshen wannan matsalar kenan Allah yasa bazai kara haduwa da mufeeda ba a rayuwarsa inhar akan wannan matsalar ne.yana mata fatan Alkhairi a duk inda rayuwa zata kaita.karfe biyu ya dauko Aidah school ganin sun nufi hanyar restaurant ta kallesa yana tuki take faɗin."Yayanmu ni na gaji da cin abincin Restaurant snacks kawai za'a karbo ,shi kaɗai yayi oder abincin da zai ci ita kuma aka haɗota da snacks, gida suka wuce daman shi yayi sallarsa a office.sai da ta fara yin wanka tayi sallah sa'annan ta sauko kasa taci samosarta ,AB dake zaune cikin parlor da laptop yana aiki akanta dan shi har lokacin ya dade da kammala cin abincinsa.Aidah ta kalli gefensa tana faɗin."Yayanmu kai bazakaci snacks din ba.?"girgiza mata kai yaqi batareda ya kalli gegenta ba Kwanciyarta ta gyara cikin kujera da wayarta a hannunta da lokacin har ta buɗe kafafen sada zumunta ,tun daga kan facebook, twitter,IG, TikTok wahtsapp,wani Hausa book da Farhaa Kabir ta tura mata takeso ta fara karantawa ,taji anata zuzuta haduwar littafin mai suna (fathiyya)rike Wayarta tayi ta soma karatu cike da nishadi da walwala daman tafi son haka ba irin gidan Mami ba ayita takurawa mutum ana sakasa aiki a kitchen,jin shirun yayiwa yasa AB ya daga kai ya kalleta karfa kiyi bacci zuwa 4 zan kaiki islamiyya baby."wani kalar turnuke fuska tayi tana tura masa baki cikin Shagwaba take faɗin."Yayanmu yanzu fa inada aure ya kamata ace na aje islamiyyar nan na sauki Alkur'ani harda haddar wani bangare acikinsa ga kuma sauran littafan addini Nidai kawai nabar zuwa."ta faɗa sounding so very free a muryarta,wannan karon bude baki yayi yana kallonta yaji ransa ya ɓaci jin wai har Tasan tanada aure. "Dawa kike AUREN?"ya faɗa cikin kakkausar murya ,sai ta tura masa baki a tsawace ya kara yimata tambayar,cikin rawar murya tace kayi hakuri juyawa kawai yayi ya cigaba da abunda yake bai san meyasa maganarta ta bata masa rai ba.karfe huɗu kamar yadda yace ya sauketa a school ya shige cikin gari sai da suka tashi yaje ya dauketa direct gida suka wuce dan ana gafda kiran sallar magarib har lokacin kuma Fuskar AB a tamke take dan hakama Aidah ta shiga hankalinta ,ita yanzu tunda tana da Wayarta bata wani damu da fushin da yayan nata yayi ba daman suna shigowa kowane ya nufi bangarensa.har bayan sallar magarib sadiya na zaune a parlor Gabaki ɗaya ranta a ɓace yake ganin har lokacin babu alamar Abba zaizo kasa daurewa tayi daman kowa na daki ita kaɗaice a parlor ,sama ta koma ta dauki hijab har kasa ta dauki car key ta fice daga gidan batareda ta sanarwa Mami ba sai da ta duddurawa maigadin gidan AB ashar kafin ya bude mata get shi dai da kallon mamaki ya rika Binta ,AB na zaune a parlor ya rikajin karar door bell daman aidah tunda ta taso islamiyya bata sauko kasa ba ,da mamaki yaje ya buɗe kofar ,sai da gabansa ya fadi ganin wacce ke tsaye a bakin kofa da sauri sadiya ta nufesa babu kunya barantana tsoron Allah ta wani shige cikin jikinsa ta rikesa sosai ta kwantar da kanta cikin jikinsa da sauri AB ya hankadata a tsawace yake faɗin."sadiya daga ina kike cikin wannan daren,ta shagwabe fuska tana fadin."nata jiranka baka zoba na kasa daurewa ne yayanmu.!"da gaske sadiya bata da hankali !"ya faɗa can kasan ransa shigewa tayi acikin parlor da kallo ya bita ya rufe kofar ya biyo bayanta."Yayanmu dan Allah kayimin rai ka saki AYDAH kamarya Dani gidanka ko kaɗan baka dace da ita ba wallahi."ta faɗa cikin Muryar tausayi kallonta yake yana mamakin halinta da son zuciyarta.tau naji kibani wata daya sadiya zanyi tunani akai,cikin farin ciki Sadiya ke faɗin."dan Allah da gaske kake Yayanmu?"daga mata kai kurum yayi miƙewa tsaye tayi cike da wani irin farin ciki take faɗin."sai da safe yayanmu,kar mami ta nemeni dan Allah karika daukar wayata dan allah.nan ma dai daga mata kai kurum Abba,yayi ta juya tana faɗin."bari ta tafi batareda tayi tunanin neman Aydah ba daman ba ita ta kawota ba.bai samu natsuwar zuciya ba sai da sadiya tabar gidan.acan kasan ransa yana ta tunanin yadda zai shigo da maganar auren Rumaisa a wajen daddy ta yadda bazaiji haushinsa ba maybe idan yayi aure sadiya ta hakura.shiryen-shiryen tafia Legos AB ya shigayi bai sanar da Aidah ba sai ana gobe zai wuce. Da dare AB da Aydah suna zaune a downstairs parlor shi yana kallon wrestling ita kuma ta dukufa akan rabin ranta (phone) sai da aka gama haska wrestling ɗin ya tattara hankalinsa akan Aydah ya kira sunanta cikin natsuwa "Baby Aydah! "Na'am! Ta amsa batareda ta ɗago ta kalle shi ba. "in-sha-Allahu gobe zan yi tafiya zuwa Lagos zan bi morning flight ba zan wuce one-two days ba. Za ki koma gidan Mami da zama kamin na dawo. Gobe daga school direba zai kai ki can, kafin ki kwanta ki tabbata kin haɗa abubuwan buƙatarki. Ɓata fuska Aydah ta yi a yanzu sam bata so zuwa dalili kuwa furuncin da Mami ta yi akanta, rau-rau ta yi da idanunta har sun cicciko da ƙwalla ya lura da yanda yanayinta ya sauya nan take ya matsa ya kama hannunta ya haɗe cikin nasa cikin kwatar da murya ya ce "Baby menene ya naga idanunki sun ciko da ƙwalla?" "Yayanmu ka tafi dani banaso zuwa gidan Mami za ta dinga tsangwama ta. Iskar ya fesar daga bakinsa kamin ya kara langwasa murya cikin rarrashi da dabara da ake yiwa yara ƙanana marar wayau "Baby ba zai yu na tafi dake ba kinga kina zuwa school ga islamiyya, banaso na katse miki karatu da ba don haka ba ai kema kinsan ƙafana ƙafarki. Yanzu ki yi hakuri ki je tsananin daɗewa ta kwana biyu ina dira Kano zan je na taho dake. Ki list duk abunda kike so zan siya miki kin ji Babyn yaya Abba?" Duk da wannan daɗin baki da ya yi mata ta amince ne kawai amman ba don tana ji farin ciki tafiya can gidan ba. Tun da ya ambaci tafiyarsa gobe Aydah ta sha jini jikinta ita fil'azal bataso abunda zai nisanta ta da yayanta koda na wuni ɗaya ne. Duk lokacin da tafiya ta kama shi zuwa wani garin da kuka suke rabuwa shi kanshi yasan irin shaƙuwa dake tsakaninsu bata wasa bace. A fakaice yake satar kallonta ta ajiye wayata tana sharar hawaye. A hankali ya shigar da ita jikinsa tasa hannayenta ta zagaye waist ɗinsa ta sunne kanta akan cikinsa duk da yana zaune amman kanta ba zai kai a ƙirjinsa ba saboda tsawon da Allah ya yi masa AB is very long and huge ga Aydah 'yar firitt da ita. Sannu-sannu yake taping bayanta irin yadda ake rarrashin rigimammun yara masu kukan banza "Oh! My Baby stop crying kinsan banaso kukanki ko?" Ta yi nodding head. "To goge hawaye insha-Allah har na je na dawo ba abunda Mami za ta yi miki. Ya ƙarashe magana tare da ɗago haɓarta ya goge mata hawayen kan fuskarta daga ƙarshe ma shi ya haɗa mata ɗan ƙaramin akwatin ta kafin ya kwanta sai da ya tattara inners wears da sleeping dress ɗinta dake cikin laundry basket ya wanke mata saboda yasan halinta ko sanda tana gida da kuka Mami take tsareta kamin ta wanke su, har sai da ya kai da haɗa baki da Huwaila mai aiki duk sanda ta je gyara mata ɗaki ta dinga wanke mata saboda wannan wanki da take yiwa Aydah har salary yake mata a boye. Yanzu kuma da babu Huwaila dole ya wanke mata shi fa har gobe kallon 'yar kankanuwa yarinya yake wa Aydah shiyasa a koda yaushe cikin lallaɓata yake. Bai kwanta ba sai around 12 sai da ya yi waya da Rumaisa kamin bacci ya dauke shi. Duk da bai kwanta da wuri ba hakan bai sa ya yi missing jam'i ba, bayan ya sauke Aydah school ya wuce gidan Mami da akwatin sannan kuma ya yi mata sallama da yake Daddy ya yi tafiya zuwa abuja akwai friend ɗin Daddy dake neman kujerar senate shiyasa yanzu bai cika zama ba. Siyama kaɗai ya tarar a main parlor da sauri ta taso ta karbi luggage ɗin Aydah a hannunsa ta gaida shi ya amsa da sakakkiyar fuska ya tambayi Mami ta ce tana sama a gurguje ya yiwa Siyama bayani zai yi tafiya ta kula masa da ƙanwarsa "Siyam please take good care of her and don't let her cry or worry kada ki barta ta dinga zama gun da Sadiya take. Murmushi Siyama ta yi duk da wannan bada amana ba yau ya fara ba don ko Mami da haifi Aydah idan zai yi tafiya sai ya bata amana ta kula mishi da ita kada ta saka ta kuka, kalamansa shi na ƙarshe sune suka haifar mata da sakin murmushi. Ta wuce da akwatin Aydah ɗakinta shi kuma ya wuce ɗakin Mami sai da ya yi knocking Mami ta bashi izinin shiga, sannan ya tura kofa ya shiga tana tsaye a jikin closet ɗinta ya durƙusa ya gaisheta, ta amsa mishi ba yabo ba fallasa cikin sanyi murya ya ce "Mami tafiya ta kamani zuwa Lagos Aydah za ta zauna anan kamin na dawo Dan Allah Mami ki yi hakuri da ita kinsan yarinya ce sai ana hakuri da ita. Murmushin takaici Mami ta yi kamin ta ce "To ubana daman ka saba ɗora min dokokin akanta ba yau ne ka fara ba kafin ka dawo har baby bottle zan siya na dinga feeding ɗinta madara ko ba ka ce Baby bace? AB ya sadda kansa ƙasa Mami kuma ta ja guntun tsaki "Dallah tashi ka bace min da gani shashasha kawai ba dai taurin kai ne da kai ba to kuwa a haka za ka kare acikin raino. AB ya miƙe jiki a sabule ya fice direban gidan ya kira ya faɗa masa idan lokacin tashi Aydah ya yi ya je ya dauko ta har da kyautar 20k ya yi mishi duk dan ya dinga zuwa daukarta on time. Jirgin da ya dauko passengers daga Kano ya ya yi landing a Murtala Muhammad International airport, koda AB ya fito daga jirgi direban kamfanin Kim's Automobile industry yana jiransa ya dauke shi kaitsaye kamfanin suka nufa kafin AB ya fito daga mota sai da ya kara gyara zaman facemask ɗin da ke kan fuskarsa, shi mutum ne wanda duk sanda zai shiga taron jama'a yana kokarin kare lafiyarsa. A matsayin Anaal na marketing manager ta tattaro dukka bayanai cinikayya na kamfanin tuni conference hall ɗin ya cika kusan duk wanda ke cikin hall ɗin fuskarsa yana dauke da facemask bayan gudanar da tattaunawa tsakanin kamfanonin biyu daga nan yarjejeniyar ta fada kowanne bangare ya yi signing aka yi pictures daga nan taro ya watse sai dai wannan meeting ɗin da aka yi babu Aliyu na Uku saboda jiya ya wuce cotonou wasu daga cikin motocin su suka iso dole kuma ya kasance a wurin. Shiyasa bai samu damar hallatar wannan meeting ɗin ba. AB yana buɗe murfin mota zai shiga ya tsikayi muryar Anaal na uku tana kiran sunansa, sai ya maida murfin ya rufe ya waiga bayansa cikin tafiyarta mai kama da yanga take tunƙaro sa. #love story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/2, 9:41 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 049. Sosai yake mamakin dalilin da zai sa ta tsayar dashi bayan sun riga da sun kammala abunda ya haɗa su sai da ta iso gaf dashi ta ce "Mr Abba ya za ka tafi ne ba ko sallama?" Batare da ya cire facemask ɗin fuskarsa ba ya amsa mata da cewa "Ina sauri ne zan wuce masaukina. "A'ah gaskiya bai kamata ka tafi ba because we are responsible for your accommodation and everything you need before you go back to kano wanna alhakin yana kanmu ne. "No thanks mss Anaal I can take of myself because garin Lagos ba bako bane a wurina already ma na yi booking ɗakin a villa toscana hotel ni zan tafi sai wani lokaci idan Allah ya sake haɗa mu. Kamin Anaal ta sake magana har ya ɓalle murfin mota ya shiga daman direba yana cikin motar yana jiransa yana shiga sai kawai ya ja motar Anaal ta bi motar da kallo gabanta yana cigaba da faɗuwa tun haɗuwarta dashi a conference hall take ji kwatakwacin irin wannan faɗuwar gaba har kuma yanzu da suka rabu gaban nata bai fasa faduwa ba ta rasa dalili. Direban yana sauke Ab a villa toscana hotel ya wuce reception ya karɓi key ya wuce ɗakin da ya kama wanka ya fara yi sannan ya hau gado ya kwanta bacci ya sha sosai don sai around 4:30pm ya falka idan Allah ya taimake shi ya yi sallar azhar kamin ya kwata agurguje ya yi wanka ya shirya cikin milk colour ɗin jallabiya mai gajeren hannu ya yi sallah la'asar yana gamawa ya kira reception akawo mishi abinci ya tsakura sama-sama da yake Abba mutum ne da bai cika cin abinci irin sosai ɗinan ba kuma bayaso zama da yunwa. Rumaisa ya kira suka sha firar su ta soyayya har yana faɗa mata gobe zai dawo saboda tun a yau ya kammala abunda ya zo yi bayan sun yi sallama ya fice zuwa harabar hotel ɗin ya ɗan miƙa ƙafafunsa. A Kano kuma bayan an tashi daga school direba ya je ya dauko Aydah ɗari-ɗari ta shigo main parlor kaman wata baƙuwa Mami da Huwaila kaɗai ta isko a parlor duk sai tasha jinin jikinta cikin murya mai cike da tsoro ta gaishe da Mami a dage Mami ta kalleta ta watsar cikin tsawa ta ce "Riƙe gaisuwarki banaso gida kuma ba zan hana miki zama acikinsa ba saboda gidan ubanki ne amman ina da right da zan hana ki gaida ni. Daga yau daga rana mai kama da yau ba zan sake amsa gaisuwarki ba har sai kin yi abunda nake so. Ba dai kin zaɓi shege marar asali akaina ba to daɗi abun ba ke kadai na haifa ba. Ki je ga ki ga Abba wallahi ba baki nayi maki ba da yardar Allah daga ke har uban naki sai ya sakaku kukan da sai hawayen idanuwanku ya ƙafe. Aydah ta yi zugun tana kallon Mami can kuma ta kwantar da muryarta ta ce "Mami wai dan Allah me Yayanmu ya yi miki ne kika tsane shi har haka shin meye laifin mu meyasa ita yaya Sadiya ba za ki lurar da ita ta yarda da ƙaddara ta yarda da komai tsari ubangiji ne duk kafiya da nacinta ba zai sa Ubangiji ya sauya abunda ya tsara mata a rayuwarta ba?" A mugun fusace Mami ta miƙe tsaye ta ɗauke Aydah da mari, ta kuma daka mata tsawa "watau Abba ya fara tattaɓa miki jiki ko Aydah?" Kin fara sani daɗin namiji shine kike min rashin kunya. Cikin muryar kuka Aydah take faɗin "Mami kema kinsan Yayanmu ba ɗan iska bane balle ya taɓa min jiki kuma ko ya taɓa ai ni matarsa ce addini ya halatta masa ni halak-malak ya yi yadda yake so dani. "La'illaha illallahu muhammadu Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam! Hasbunallahu wal-imaal wakil! Zulaiha ke ce ko kuwa wata Zulaiha ce aka musanya min? Mami ta yi magana cikin ɗimaucewa gaba ɗaya yau Aydah ta shayar da ita zallan mamaki har ga Allah Mami ɓata taɓa tunani yarinta da wautar Aydah zai sa tasan menene aure da manufofin sa ashe kallon kitse da take yiwa rogo ashe tana yi mata kallon biri ne tana mata na ayaba. Cikin kaɗuwa Mami take cigaba da kallon Aydah da baki buɗe. Aydah a shirye take a yau ɗinan ta kare martabar aurenta da yayanta duk kallon da suke mata na ƙaramar yarinya kar take kallonsu tana bin su ne a haka ba wai dan batasan me aure yake nufi ba. Banda ma su da abin su ta ya za a ce batasan aure ba to da ina amfanin zuwan ta islamiyya da littatafai da ake karantar dasu da suka shafi aure da hakkokinsa. Cikin kuka ta cigaba da cewa "Wallahi Allah ba zan taɓa yi abunda kike so ba Mami saboda ina son mijina ina so zama dashi ada ina kallon aurenmu ta wata siga ta daban amman a yanzu da na fahimci ba abunda yaya Sadiya take so sama da mijina nima a yanzu ina son abina na kuma shirya fuskantar duk wani kalubale akansa. Da baya-baya Mami ta koma ta faɗa kan kujera tana dafe saitin da zuciyarta take wani irin bugawa take mata ga kuma tsanani shock da ya lulluɓeta. Aydah ta duƙa ta dauke backpack ɗinta da garin marinta da Mami ta yi ta faɗi daga kafaɗarta daman akan kafaɗarta take, ta haura upstairs da gudu ta shiga ɗakinta ta rufe da key ta faɗa kan gado tasa kuka da taga ji da kukanta ta jefa yantsata a baki ta yi baccin dole. AB ya nemi gefen swimming pool nesa inda babu mutane ya zauna ya zura ƙafafuwansa acikin ruwan sanyi su ya ratsa jikinsa ya lumsashe manyan idanunsa ya dauki lokaci a haka kamin ya buɗe idanunsa, sai kawai ya tsinci kansa da son kira Aydah yasan zuwa yanzu ta dawo daga school islamiyya ce bai da tabbacin ko ta je tun da daman can sai ya yi artabo da ita kafin ta tafi. Can cikin bacci Aydah ta ji ringing ɗin wayarta ta zubura ta tashi ta miƙa hannunta kan bedside drawer ta dauko backpack ɗinta ta yi unzipping gefen aljihun jakkar ta ciro wayarta tana ganin sunan yaya Abba ta ja ajiyar zuciya, cikin dushewar murya ta ce "Hello Yayanmu da fatan ka isa lafiya ya hanya?" Ras! Gabansa ya faɗi sakamakon yadda ya ji muryata ke fita. "Kuka kika yi ko Baby?" "A'ah! Kawai dai koda kiranka ya shigo ina bacci. "Oh! I'm so sorry for interrupted your sleep my baby Allah yasa kada na jawo miki headache. Ya faɗa with so much caring acikin muryarsa. "To ai ni taimakona ka yi Yayanmu saboda ban yi sallar la'asar ba ko uniform ban cire ba na yi bacci. "Aydah sarkin ƙazanta oya tashi ki je ki yi wanka da sallah idan kika gama ki kunna Data za mu yi vid call I really want to see my Baby face. Dariya ta yi mai ban sha'awa "me too ina so naga fuskar yayana yini guda kurum har nayi kewarsa. Murmushi ya yi mata mai ɗan sauti wanda sautin ya sauka a kunneta kana ya kashe wayarsa. Da gudu ta shiga bathroom anan ta cire uniform ɗin jikinta ta jifar ta kunna shower tana wanka take tunano fuskar Mami sai kawai ta kwashe da dariya da sauri ta rufe bakinta da tafin hannunta da tuna tana banɗaki ne. Watau yau Mami za ta yini ta kwana da mamaki ita wai kallon yarinya take min za ta ga yarinta kuwa. Aydah ta faɗa cikin zuciyarta tana gama wanka ta fito ta tsane jikinta da hand towel ta saka half cotton gown wacce ba ta wuce cinyoyinta daman ire-iren kayanta kenan matuƙar ba fita za ta yi ba, ba za ka taba ganinta da suturar kirki a cewar suna mata nauyi da ta kammala sallah ko addu'a bata yi ba ta cire hijab ta yi flinging dashi ta hau gado tare da kunna Data wayarta, tana gani yaya Abba online ta saki murmushi shi kuma yana can yana chat da rabin ransa Rumaisa kusan sau uku Aydah tana mishi magana bai yi respond ba sai kawai ta kira shi vid call ɗin yana gani kiranta ya katse sai da ya gama hirar sa da Rumaisa suka yi sallama yana tsoron ya yi laifi a wurinta sannan ya kira Aydah zuwa lokacin Aydah har ta yi fushi sai dai fushin nata ba wani tasiri yake yi ba ta yi picking kyakkyawar fuskarsa ta bayyana akan screen ɗin wayarta "Hey my little Baby yau kin ci abinci kuwa?" Sai da ta cuno baki kamin ta amsa mishi da eh. "Meyasa ba ki je islamiyya ba?" "Yayanmu ba na gayamaka bacci nayi ba. "Owk! Na ji ya naga idanuwanki sun yi luhu-luhu kaman kin yi kuka. "Ni ban yi kuka ba to me ma zai saka ni kuka? "Yoo ai ke ƙanƙani abu ma sai ya saka ki kuka duk duniya babu abu mai sauki a wurinki Aydah irin kuka. "Kai Ya.... innalillahi! Yayanmu menene nake gani a bayanka?" Yadda ta yi magana a tsorace tana ɗaga murya ya yasa shi kaɗuwa har ya juya babu shiri macce sanye cikin bikini yadda ya kalleta ita ma haka ta yi mishi kur da nata idanunta taga kyakkyawa har wani kara langwashe jiki take yi. "Yayanmu! Dan Allah ka daina kallonta ita da wacce take tsirara bambancin su kaɗan ne fa. Ya tsikayi muryar Aydah sai ya dawo da ganinsa akan wayarsa yana murmushi, yayin da Aydah ta bata fuska "amman dai yayanmu wannan matar 'yar iska ce ko?" Murmushi kawai ya ci-gaba da yi Aydah sai ƙara lekawa cikin waya take yi ta yadda za ta hango ta. tsanani mamaki ne ya rufeta tasake cewa "yayanmu daga ita fa sai pant da bra wallahi tana kama da 'yan iska ko yayanmu?" AB ya yi murmushi haɗe da cewa ba kama bace Baby dama can 'yar iska ce. "To Allah ya isa ban yafe mata ba tun da ta kalla min yayana. Aydah taƙarasa magana har da su murguɗa baki. AB bai sanda ya fashe da dariya ba da kyar ya tsagaita dariyar tasa, yana wani shafa gashin kansa still da murmushi akan fuskarsa "Aydah troublemaker wannan Allah, ya isa naki har da ni ciki saboda nima na kalleta kin ga kuwa Allah ya isa ɗin har da ni aciki. Kukan shagwaɓa tasa masa tana faɗin "ni bada kai nake ba saboda ni na ankarar da kai tsyuwarta a bayanka na kuma yafe maka kallon da ka yi mata amma ita kan ban yafe mata ba, muguwar kawai wacce batada kunya. Yadda ta takarkare tana ta faɗa ya yi masifar bashi dariya sai dariya yake abinsa can da yaga rigimar ta Aydah ba mai ƙarewa bace ya ce "Bara na koma ɗakina don ba zan iya da wannan rigimar taki ba. "Eh! Gwara ka koma ɗin daman ai Yayanmu ba yawon bude ido ka zo ba. Ba dole bane sai ka zauna bakin ruwa. AB bai fahimci Aydah kishi ne ke dawainiya da ita ba shi ya zaci shirmenta ne ya motsa tun da shi a wurinsa duk abunda za ta yi, a matsayin childness yake daukarsa dole ya koma ɗakinsa suka cigaba da firarsu sai saka shi nishaɗi take da ka ji sautin dariyarsa to tare da Aydah yake, tuni Aydah ta manta da wata Mami sai da aka fara kiran sallar magarib suka rabu sai dai bai faɗa mata gobe zai dawo ba. *MASARAUTAR KUDU* Duk yadda Fulani babba ke ba wa mai martaba kariya sai da Fulani karama ta fakaice idanunta ta aiwatar da aikin boka, kwana biyu a tsakani ciwon na mai martaba ya ƙara tsanani hakan ya kara tayawar masaurata da iyalinsa hankali. A daren ranar ba wanda ya zaci mai martaba zai kai safe ba. Ita kanta mai babban ɗaki duk juriyarta a wannan karo da ta je duba shi sai ta zubda masa da hawaye. Cike da ƙasaita Kilishi take sauraren bayani da hadimi kallamu ke mata dangane da yanda ciwon mai martaba ya tashi, sai wani murmushi take tana jinjina kai Kallamu shine amintaccen bawanta duk wani information na masaurata shi ke zuwa mata dashi sai dai wani abin mamaki akwai ranar da ya nadin maganganu Ciroma da Galadima a gidan gonar Ciroma har ya yi gina ya binne wayar wacce har yau ɗinan bai kawowa wayar ba Kilishi asalima ya ɓoye wannan sirri ɗin. Shi kadai yasan manufarsa na ɓoye wannan sirri. "Kallamu inason duk wani shige da ficen Ciroma ya kasance akan idonka inason sani duk wani motsinsa, ita kanta Fulani karama ban yarda da ita ba saboda haka ita ma ka samin ido akanta sosai. "An gama Ranki shi dade duk abunda kika ce shi haka za a yi Allah ya ƙara miki lafiya. "Tashi ka tafi gobe da safe ka sami jakadiya zan bata sako ta ba ka. "Godiya nake uwar sarkin gobe sikari ba ki yi farin banza ba Da hannun tai mishi alama ya miƙe da sauri ya fice. Sosai Ciroma da Galadima ke farin ciki da yadda jikin mai martaba ya yi tsanani, da wannan daman Ciroma ya fara bin uwayen fada da 'yan majalisar sarki yana kamun ƙafa ba kunya balle tsoron Allah sa'ili da ya je wurin waziri duk da cikin hikima da azanci ya yi masa magana hakan bai hana waziri fahimtar inda kurman allonsa ya dosa ba cike da gundarin mamaki waziri yake kallonsa kafin ya bashi amsa "Ikon Allah! Lallai Ciroma bakada imani ban kara tabbatar da 'yan ubanci mugun abu bane ba sai yau ɗan uwanka yana kwance akan gadon asibiti cikin matsanancin hali, ba ma fatar kake ya sami lafiya ba Allah ya tashe kafaɗarsa cikin iyalinsa da al'ummar da yake mullka kai sarautar sa a gabanka. To bari ka ji Ciroma koda ta Allah ta kasance da mai martaba ba za ka taɓa hawa karagar mulkin kudu ba gwara tun wuri ka kauda idanunka akanta. Kada ka bari shaɗaniyar zuciyarka ta yaudare ka, ta jefa ka mahalaka. Tashi ka bace muna da gani shashasha kawai, mai zuciyar kafirai farko. Jiki a sabule Ciroma ya baro gidan waziri amman da kudirin duk da ranar da ya cimma burinsa na zama sarki sai waziri yagane kuskurensa na faɗa masa magana. *AMINU KANO INTERNATIONAL AIRPORT* Misali ƙarfen 3:22pm jirgin da AB ya biyo daga Lagos zuwa Kano ya yi landing Abdulkarim ya kira ya zo ya yi picking dinsa, suna tafe suna fira "Ak gidan Daddy za mu fara zuwa dan na yiwa Baby Aydah alkawarin da zarar na dawo zan zo na dauke ta kasan ba wani dadin zaman can gidan take ji ba, Sadiya takura mata take yi. Tun sanda ya fara magana Abdulkarim yake satar kallonsa sai kuma ya ce "Ni na rasa wane irin jahilci ne ke dawainiya da Sadiya? Banda daƙiƙanci me Aydah ta yi mata meye laifinta da za ta ta uzira mata? Amman ba laifinta bane duk wannan sanyi hali ne naka AB ya jawowa Aydah. "Ak bansan me zan yi mata ba in fact Sadiya ƙanwa ta ce duk yanda ta zama matsayinta ba zai taɓa canzawa ba a wurina. "Mtss! Ai ka ji matsalarka duk sanda aka yi magana za ka ce ƙanwarka ce shiyasa take amfani da sanyi halinka tana yi yadda tagama dama. Har suka iso AB bai ƙara cewa komai ba. A babban parlor suka tarar da Mami da su Siyama yau lectures ɗin safe suka yi shiyasa dukkan su suna gida, Aydah kuma tana ɗakinta a ƙunshe da ta fito parlor ta zauna Mami ta kore ta dole ta koma ɗakin, ta cigaba da karanta novel ɗinta. Ita daman ta fi sabawa da zaman ɗaki fiye da parlor shiyasa ko kaɗan bata damu ba. Siyama ta dinga murnar ganinsa ita ma Sadiya fara'a take yi ta kasa ɓoye farin cikinta. #love story2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/3, 3:53 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 050. Gaisuwa da suka yiwa Mami da kyar ta amsa shi ma a dage Siyama ta tashi ta je kitchen ta hado masa abinci har ya kammala ci abinci bai ga Aydah ba sai kawai ya wuce ɓangarensa na da ya yi wanka, yana dawowa daga sallar la'asar ya kira Siyama ya ce ta kira masa Aydah ta zo su tafi. Mami dake kitchen ta fito a fusace Sadiya na biye da ita, Sadiya ta jingina jikinta ga bangon kitchen ta harɗe hannayenta a ƙirji sai da Mami ta fara jefa masa mugun kallo kamin ta ce "Abba ba inda Aydah za ta je ta dawo kenan ina jiran ka kawo min takardar sakin 'yata mai goyon bayanka baya gari saboda haka Aydah ta dawo kenan. Mamaki ne ya lulluɓe AB ya kasa furta uffan Siyama ta fadawa Aydah sakon AB ta zubura ta shiga tattara kayanta da ta yi amfani dasu ta mayar cikin akwatinta, ta fito Siyama sai faman kallonta take yi tana murmushi suna saukowa ƙasa suka yi turus sakamakon yadda Mami ke ta fadar bakaken maganganu akan Abba. "Da alama ka fara taɓa jikin Aydah zuwa gaba ma za ka iya wuce haka har ni Aydah za ta duba ta cemin duk abunda za ka yi mata ba haramu bane yaushe Aydah tasan da hakan idan har ba kaine ka fara ɗora ta a hanya ba. Tun da na fahimci ɗan iska ne kai ba zan bari ka lalatawa 'yata rayuwa ba kai ko kunya ba ka ji da girman kana lalluɓar yarinya ƙarama. Wata irin kunya ce ta lulluɓe shi a maimakon maganganu Mami su farantawa Sadiya rai sai ta ji wani mugun haushi cikin fusata ta ce "Mami ki daina gani laifin yayanmu laifi na wannan little brat ne ita ke shige masa. "Don me ba za ta shige masa ba yaya Sadiya ko kin manta su ɗin miji da mata ne ko akwai wani nafsi da ya yi hani mata ta shigewa mijinta. Siyama ta faɗa cikin fushi don ba ƙaramin haushi Sadiya da Mami suka bata ba. "Ya isa Siyama! AB ya faɗa kamin ya mayar da ganinsa wurin Aydah ya tambaye ta gaskiyar abunda Mami ta faɗa girgiza kai Aydah ta yi idanunta har sun cicciko da hawaye "Yayanmu tun zuwana gidanan ko downstairs parlor ban sauko ba ko gaida Mami nayi bata amsawa, yaya Sadiya kuma ta bini da zagi to yaushe naga Mami balle na faɗa mata wannan maganar ba ni ban ma fahimci me kuke nufi ba. Ta ƙarashe magana tana sharar hawaye da bayan hannunta. Sosai ran Mami ya ƙara ɓaci ban taɓa tsammani Aydah ta iya tsara magana irin wannan ba. "Aydah ni nake miki karya?" Aydah ta girgiza kai alamar a'ah! "To shi kenan bara na kira Huwaila ai a gabanta aka yi Huwaila zo nan! Mami ta faɗa cikin daga murya Huwaila ta fito daga kitchen da sauri ta rakuɓe jikin bango saboda duk abunda ke faruwa akan kunneta cikin tsawa Mami ta tambaye ta Huwaila ta girgiza kai muryata yana rawa ta ce "Ki gafarce ni Mami ni kan ban ji sanda Aydah ta faɗi haka ba Allah na tuba dukka Aydah guda nawa ce da za ta faɗin manyan zantuka irin waɗannan. Wani kalan ajiyar zuciya Aydah ta yi har cikin zuciyarta ta ji dadin yanda Huwaila ta kare ta. "La'illaha illallahu muhammadu Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam! Huwaila daman ke munafuka ce bansani ba ina zaune dake da zuciya guda za ki karyata ni koda karya nake yi Huwaila na zaci za ki rufan asiri to bari ki ji yau zamanki ya ƙare a gidanan yanzu nan za ki bar min gidana munafuka algunguma. Huwaila ta zube guiwayoyinta ƙasa tana kuka tana rokon Mami ta yi hakuri amman Mami sai rantsuwa take yi sai ta bar mata gida, Sadiya ta fizgo hannun Huwaila har sai da ta miƙe tsaye ta tusa ƙeyarta gaba zuwa ɗakin da ya kasance nata a gidan. AB ya kalli Mami "Mami dan Allah ki yi haƙuri kada ki kore Huwaila kada ki yi mata hukunci da laifin da ba nata ba. "Mtss! Mami ta ja tsaki tare da watsa masa mugun kallo ta haura haura bene a fusace tana ji kamar zuciyarta za ta kama da wuta, wata kila dole sai ta bi hanyar da Hajiya Zeena take so ɗora ta akai kamin ta raba wannan ɗan iska yaron da Aydah. Sadiya ba ta bar Huwaila ba sai ta haɗa kayanta kaf sannan suka dawo parlor, kallonta kurum AB yake yi yana jin tsanarta tana bin jini jikinsa ya yi ƙwafa ya juya domin idan ya ce zai cigaba da tsayuwa a wurin komai zai iya faruwa, Siyama ta kama hannun Aydah ta ce da Huwaila "zo mu tafi Huwaila wani hani ga bawa baiwa ce don an kore ki daga aiki a gidanan ba shi yake nufi kwanaki ki a duniya sun ƙare ba. Suka fice Sadiya ta bi su da tsaki tana durawa musu ashariya, a parking lot suka tarar da AB ya shigo motarsa Siyama ta buɗewa Aydah front seat ta shiga kana ta dawo ta buɗewa Huwaila backseat ta ce ta shiga sannan ta miƙa mata akwatin Aydah. Ta dawo saitin da AB yake ta ce "Yayanmu ka cigaba da haƙuri da kake yi Allah yana tare da masu hakuri wata rana sai labari, ga Huwaila nan nasan kuna bukatar ta a gidanku. Har suka isa gida ba wanda ya yi magana AB ya nunawa Huwaila ɗakin da za ta zauna ta shigar da kayanta fuskar nan tasa a haɗe ya ce Aydah ita ma ta ɗauki akwatinta ta wuce ɗakinta shi kuma ya wuce nasa bai sauko ƙasa ba sai da aka yi kiran sallar magarib bai baro masallaci ba sai da aka yi sallar isha daga nan ya wuce restaurant ya siyo musu abinci. Parlor ya ajiye takeaway ɗin ya haura sama kaitsaye ɗakin Aydah ya nufa har zuwa lokaci fuskarsa babu walwala ko kaɗan ya tura kofar ɗakin nata, tana kwance akan gado ƙarar buɗe ƙofar yasa ta juyowa cikin sauri idanunta suka faɗa cikin nasa yanda taga fuskarsa a murtuƙe sai da gabanta ya faɗi. "Abinci yana parlor ki taso ki ci amman ki tabbatar kin yi wanka kin canza waɗannan kayan na jikinki. Aydah ta ya mutsa fuska tamkar za ta fashe da kuka take kallonsa, yi ya yi kamar bai ga abun da take shirin yi ba ya fice abinsa. Jikin Aydah ya yi sanyi don ta gama fahimtar fushi ne yake yi ta tashi ta shiga bathroom ta yi wanka kaman yadda ya umarce ta, ta shirya cikin doguwar rigar bacci ta sauka mata har ƙasa, ta ɗan shafa turare ta fice tun kamin ta karasa saukowa ta hango shi zaune yana waya, ta nemi kujera ta zauna da hannunsa ya yi mata nuni da ledoji takeaway ɗin dake kan centre table, ta ɗauki pack guda da spoon ɗin dake ciki ta shiga sai da ya gama waya batareda ya kalleta ba ya ce daita idan ta kammala ta ɗauki guda ɗaya ta kaiwa Huwaila, tana gamawa ta dauka ta kai mata ganin yau bai bata fuska ba sai kawai ta komawarta ɗakinta. Bata tsaya a parlor sunyi kallo kaman yadda suka saba ba ita yau tsoronshi ma take ji gwada tayi nesa-nesa dashi. Washegari Huwaila tana kammala sallar asuba ta shiga gyaran gida ko'ina ya yi fess, da duba kitchen babu foodstuffs da nufinta ta yiwa masu gidan break fast dole ta koma ɗakinta ta kwanta ba don tana jin bacci ba. Aydah tana kammala shirinta na school ta fito bayanta goye da bagpack ɗinta, ta zauna a parlor tana jiran AB ya sauko ya kaita school bata fi five minutes da zama ba sai gashi ya sauko kaman dai jiya fuskarsa a haɗe. "Ina kwana Yayanmu! "Lafiya ƙalau tashi mu tafi. Ta tashi jikinta a sanyayye tana mamakin wannan canzawa da ya yi mata, sai da ya tsaya a restaurant tayi break fast shi kuma ya yi musu takeaway shi da Huwaila sannan ya sauke ta school ya kawo three thousand as usual ya bata, bayan ya dawo ya yi wanka ya shirya cikin blue suit da white colour long sleeve shirt, ya saka necktie white ya yi matuƙar kyau a parlor ya tarar da Huwaila tana ƙara goge centre table ɗin da ke girke a tsakiyar parlorn, ya nuna mata abincinta kana ya ce zai aiko da direban Kamfani ya kawo foodstuffs sai ta yi musu girki. Huwaila ta amsa cikin girmamawa tare da yi masa fatar adawo lafiya. Bayan tafiyarsa ne ta haura sama ta shiga ɗakinsa ta gyara masa tsaf ta wanke bathroom tare da saka turaren wuta ɗakin ya gauraye da ƙamshi ta rufo ƙofar ta nufi na Aydah shi ma ta gyara shi ta wanke banɗaki da panties ɗin Aydah guda biyu da tarar a cikin laundry basket. Tana gamawa da ɗakin Aydah ta dawo downstairs parlor ta zauna. *MASARAUTAR KUDU* A yau Masarautar Kudu ta tashi da mummunan labari na mutuwar sarki Mahmood, ba ƙaramin tashin hankali iyalansa da jama'ar gari suka shiga ba Fulani babba ta yi kuka har ta gode Allah ita kuma dramar queen Fulani ƙarama har da suman ƙarya lokacin dasa mutuwar mai martaba ta riske Ciroma a lokacin yana parlornsa tare da iyalinsa suna taking breakfast Galadima ya kirasa a waya ya faɗa masa daddaɗan albishir, tsabar farin ciki mantawa ya yi da yana gaban Uwargidansa Maryama da 'ya'yansa wanda basu san takamaiman abun da ya aikata ba sai gashi tsanani farin cikinsa da ya kasa boyuwa ya miƙe tsaye yana hamdallah har dasu sujjudi shukur hakan yasa yana gafda fallasa sirrinsa. Mamaki ne ya lulluɓe Maryama har ta gaza haƙuri ta furta "Ciroma wani abun farin ciki ne ya same mu?" Ya ɗago daga sujjadar da ya yi yana wani tattara babbar rigarsa sai yaƙar haƙora yake yi "wallahi kuwa Maryama mai martaba dai wa'adi ya cika burina na zama sarkin kudu zai cika. Kai Al-hamdullilah Allah abin godiya boka mai Gundulelliya aikinka ya yi kyau dole nai maka babban tukuici. Zazzaro idanuwa Maryama ta yi cikin kaɗuwa ta furta "Innalillahi wa'inna illahim raji'um! Ciroma daman kana da sa hannun a ciwon mai martaba? Anya kuwa Ciroma kana so ka gama da duniya lafiya? Meyasa kai Kwata-kwata babu tsoron Allah a zuciyarka? Wallahi Ciroma ka yi asara amman ba laifinka bane har da zugar wannan tsinanniyar matar taka Umaima kin zama annoba kin zama silar jefa rayuwar mijina halaka Allah ba zai barki ba Umaima. Ciroma ya yi sakwarkwatai ya rasa me zance da zai kare kansa, maganar zarar bunu idan ta fito bata komuwa balle ya maidata, sai rarraba idanuwa yake yi na rashin gaskiya muraran. Umaima ce ta zuburo daman ita ba gudun abun kunya take yi ba. "A'ah! Ya haka malama za ki kirani da tsinanniya? Don kawai na taimaki mijina domin ya cimma burinsa, in dai akan taimakon mijina ne ki kirani da abun da ya fi tsananniya ba abun da ya dame ni Allah na tuba me tsinuwarki za tayi me. Ko kuma ko kina so ko bakya so sai Ciroma ya zama sarkin kudu sai dai bakin ciki ya kar ki. "Ke dallah ya isa haka! Maryama sa'arki ce da za ki dinga faɗa mata magana banaso kama hanya ki tafi ɓangarenki banaso fitina. Ciroma ya yi magana a tsawace har wani zarewa Umaima idanunsa yake yi, dole ta fice ranta yana mata tuƙuƙi duk da Umaima bata yi mamaki yadda ya daka mata tsawa ba bakon abu bane a wurinta, daman can haka yake mata akan Maryama ta rasa wane irin tsoronta yake ji tasan Maryama bata bin malaman tsinbo balle bokaye hasali ma shahararriyar malamar addini ce da babu na biyun ta acikin da wajen masarautar kudu. Kuma riƙaƙƙiyar 'yar Ahalil sunnah ce. Sai dai Umaima ta danganta hakan da tsanani son Maryama da Ciroma ke yi yadda yake so ko Kilishi da ta haife shi baya mata ƙaunar da yake yiwa Maryama. To daman an ce wanda Allah ke yiwa faɗa baya faɗa dukkanin bukatun Maryama wurin Ubangiji talikai ta ke miƙa su shiyasa duk biye-biye bokaye Umaima har yau ta kasa cin nasara akanta, haka zalika ta kasa farraka zamanta da Ciroma. "Kai kuma ku fice ku ba mu wuri manyan suna magana kun yi tsaye cirko-cirko kuma baza kunnuwa ku fita mana! Ciroma ya yi magana cikin hargowa yana kallon yaransa ƙanana, da gudu suka fice kowanne ya nufi ɓangaren mahaifiyarsa. "Meyasa Ciroma? Na ce meyasa za ka biyewa shaɗaniyar matarka har ta kai ka da aikata mummunan aiki irin wannan?" Ciroma ya yi shiru ya rasa abun faɗa cike da tsanarsa Maryama take kallonsa kamin ta girgiza kai ta nufi ƙofar fita da sauri ya bi ta yana kiran sunanta ko waigowa bata yi ba balle ta tsaya ta riga tasan duk abun da zai mata ba zai ƙara ta da komai ba. Tun da aikin gama ya riga da ya gama burinsa mai martaba ya mutu ya kuma mutu to me ya rage?" Kamin ka ce kwabo masarautar ta cika da mutane babu masaka tsinke ƙarfe 2:00pm za a yi jana'izar koda ƙarfe 1:00pm ta yi Aliyu na uku da yaransa sun iso mai babban ɗaki ta yi tawakalli sosai domin ita ma ke rarrashin ƙannai mai martaba take ta faman kukan saboda tashin hankali yaya Gimbiya har da suma tayi sai aka zuba mata ruwa ta farfaɗo. Mai martaba ya yi jama'a ta ko'ina zuwa ake ƙarfe 2:00pm aka masa sallah kamar yadda addini musulunci ya tanada aka wuce dashi makwacinsa na gaskiya da yake akwai maƙabarta acikin masaurata duk wani sarki ko jinin sarauta anan ake binne shi. Wani abun da zai ba ka mamaki tun kamin adawo daga kai mai martaba maƙabarta Ciroma ya fara shige da fice na neman sarauta, idanunsa sun rufe da kwaɗayin mulki kamar shi ba zai mutu ba. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. [1/3, 3:55 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 051. Koda ta dawo makaranta da rana Huwaila tayi masu abincin rana gidan sai kyalli yake ko'ina fes daman Huwaila badai tsafta ba ,anan cikin parlor ta wullar da bag dinta ta makaranta ta cire takalmin kafarta da ƙaramin hijab ɗinta na uniform ta wullar cikin parlor fitowar Huwaila daga ɗakin bakin dake cikin down stairs ta hango Aydah cikin parlor,da fara'a sosai Huwaila ta ƙaraso gabanta tana faɗin "Auta har an taso makaranta Aydah na zama cikin kujera take ɗagawa Huwaila kai, "Abinci za kici ko wanka?"duka ina bukatar kowane Aunty huwaila ,Amman zan fara cin abincin tukuna daidai lokacin Abba Bashir ya ƙaraso cikin parlor kuma yabi kayan da Aydah ta yasar a kasa. Fuska a daure yake faɗin."wannan kayan fa wa zai kwashe?"da sauri Huwaila ta nufi kayan tana kokarin daukewa AB ya dakatar da ita ya kalli Aydah yace ta kwashi kayanta ta kai ɗaki,yadda yayi mata babu wata cikakkiyar fara'a akan fuskarsa yasa tabi umurnin yayan nata ranta ita ma a ɓace tun jiya da suka dawo daga gidan Mami yabi ya canja mata,abu kankani zata yi masa ya hauta da faɗa a karo na farko da taji tana jin haushin yayan nata har cikin ranta. Har tayi wanka bata fito daga dakin ba ,kwanciyarta tayi a ɗaki har Abba yayi wanka ya sauka kasa yaci abincin da Huwaila ta jera cikin dinning area baiji alamar motsin Aydah ba.yana gama ci ya koma sama murda handling din kofar ɗakinta yayi ya shiga kwance ya sameta kan bed tayi ruf da ciki idonta a rufe suke kuma yana jin yadda numafashinta ke fita da alamar bacci ne ya dauketa yafi minti ɗaya tsaye akanta dogayen yatsun kafanta ya shiga ja , buɗe idonta tayi da suka sauya kala saboda bacci.Ba za ki ci abinci ba kika dawo ɗaki kika kwanta?" "idan na tashi bacci zan ci yayanmu."ta faɗa tana son ta kara rufe idanunta ,tashi muje kici abinci ki gama ci na saukeki a islamiyya yau babu fashi."yayi maganar sounding so very serious tamkar zata yi kuka ta tashi zaune tana murza ido tana jin yadda kanta ke wani irin juyawa ,da gaske bacci takeji kamar yadda ta faɗa masa kallon yanayinta kawai yasan bacci takeji sai dai ba zai yadda tayi bacci ba taki zuwa islamiyya Shiya dauki plate ya zuba mata shinkafa da miyar da Huwaila tayi masu da naman kaza a sama,haka Aydah ta rika ci kamar ana sakata dole yana zaune a gefe yana danna wayar hannunsa,akai akai yake dagowa ya kalli gefen da take idan zata kai lomar abinci a bakinta tamkar zata fashe da kuma kamar yadda take yi da fuska.sai dai yayi murmushin gefen baki ya dauke kansa akanta.Baccin da Aydah bata samu ba kenan har lokacin islamiyya yayi yana dawo masallaci ya dauketa da mota ya aje ta islamiyya duk ranta a ɓace yake.haka yaja motarsa ya barta tana famar kumbure-kumbure. Har ya daukota daga islamiyya ran nan nata a ɓace yake shima sanin Huwaila na gidan kuma ba karamin dadi yaji ba da tazo gidan yasan Aydah bazata yi kewa ba yana sauketa ya juya kan motarsa kai tsaye wurin Abdulkarim ya wuce."Aure nakeso nayi Abdulkarim !"Ya fadi kalmar batareda ya kalli Abdulkarim ba da ya buɗe baki yana kallonsa da mamaki."aure kamar yaya ban fahimceka ba.?"mahaifin Rumaisa ya samu ganawa dani ya bani hakuri akan laifin da yayi min a baya."haka ya kara bani damar auren Rumaisa a karo na biyu sai dai ban san tayar da zan yiwa Daddy bayani ba."da kurciyarka za ka aje mata har biyu meke damunka Meya shiga kanka."duk ka manta irin mummunan wulakancin da mahaifin yarinyar nan yayi ma a ranar daurin aurenka.!"ai ina tunanin daga ranar bazaka kara kallon 'yarsa ba ashe ba haka bane AB Abdulkarim ya faɗa da wani yanayi a Muryarsa yana ganin hoton sadda abun ya faru acikin kwanyar kansa,Yaya zan yi Abdulkarim ina son Rumaisa da dukkan zuciya da ruhi a baya nayi yunkurin rabuwa da ita na har abada,sai dai tausayin ta da nake ji na kasa duk irin soyayyar da ta nuna min a baya kuma bata da laifi ko kaɗan duk mahaifinta ne."ban baka shawara ka tun kari Daddy da wannan zancen ba ,ana barin halal dan kunya ka tuna yadda Daddy ya tsaya maka akan komai na rayuwarka."ita kuma wacce kake aure a gida isarka ne ba tayi ko yaya?"lokaci ɗaya Yanayin AB ya canja,jin inda Abdulkarim ya bullo masa, "sau nawa zan faɗa maka babu wannan maganar a tsakanina da Aydah lokacin sakinta na zuwa lokacin da tazo min da wanda take so ta aura. murmushi Abdulkarim yayi bai kara cewa komai ba sai murmushin da yake yi har kullum AB ba zai daina basa mamaki ba ga gaskiya kiri-kiri yana gani Amman sai ya take,da dare Abba ya yanke shawarar ya kira Daddy ya faɗa masa tunda baya gari sai dai yana dialling lambar Daddy yayi saurin katsewa idan ya tuna maganganun Abdulkarim sai yaji akwai kamshin gaskiya a maganganunsa ,to kuma yana bukatar Rumaisa cikin rayuwarsa acikin gidansa na aure ko dan ya kauda zargin da Mami keyi masa akan Aydah ,ya kamata yayi aure sai dai bai san taya zai fara tunkarar Daddy da maganar ba." Cikin kwana biyu Mami tayi bala'in saka damuwar Aydah aranta musanman da ta ƙaryata a gaban Abba Bashir ta fahimci idan bata tashi tsaye ba Aydah neman take tafi karfinta duk akan Abba Bashir,da safe karfe goma tunda Daddy baya gari ta dauki motarta tayi gidan kawarta Hajiya zeenah ,Mami bata tsaya kofar gidan kowa da motarta ba sai kofar gidan Alhaji Sanusi ƙanin Daddy,nan tayi horn maigadi ya leko ta karamar kofa ya shaida motar ta Mami dan tana yawan zuwa gidan buɗe mata kofar gate yayi yana daga mata hannu alamar gaisuwa. A hankali ta shiga danna door bell,bata jima ba aka zo aka buɗe mai aiki ta gaisheta tayi mata iso cikin parlor, tace Bara ta karasa bangaren Hajiya zeenah ta kirata daga kai kurum mami tayi saboda damuwar dake kwance a kasan zucuyarta ,ba'a jimaba Hajiya zeena ta fito sanye cikin kayan bacci riga da wando masu kauri kana ganin fuskarta da take a yamutse kasan bata dade da tashi bacci ba,har cikin parlor ta karaso ta zauna da mamaki take kallon Mami,ko jia munyi waya baki cemin zaki zo ba Hajiya mariya."Hajiya zeenah ta faɗa tana kallonta,da raunin murya Mami ke faɗin."bana cikin hankalina zeenah bana cikin natsuwata ina gafda rasa tunani na zuciyata tana iya bugawa lokaci ɗaya,inhar Abba ya kusanci Aydah."Mami ta faɗa da wani irin yanayi a muryarta wani murmushin gefen baki Hajiya zeenah tayi tana faɗin."mu karasa kiyi break fast idan kin samu natsuwar da nake bukata sai muyi magana."da sauri Mami ta shiga girgiza kai tana faɗin."taya kike tunanin zan iya haɗe wani abinci cikin kwanakin nan ai abinci baya zama acikina zeenah mu karasa dakinki muyi magana cikin sirri."har bedroom din hajia Zeena suka shige suka zauna akan makeken gadonta Mami ta cire mayafin kanta , Zeena na yanke shawarar kawai zaki kaini wurin malaminki na yadda da maganarki sai ta wannan kaɗai zan samu Abba,ya rabu da ya'ta na har abada ke ko Sadiyar da nakeso ya aura na haramta mata aurensa ki tashi mu tafi wurin malamanki raba auren nan shine kwanciyar hankalina Zeenatu lamarin Aydah ya gigita Ni zautukkanta sun dauremin kai kwanakin nan ko baccin kirki bana samu wallahi saboda damuwa."yanzu kika dawo hanya Hajiya Mariya ai yanzu ai daina zama a ga ikon Allah in har kina da kuɗi babu wata matsala da zata sakaki a gaba,bari na watsa ruwa nayi karin kumallo kin san fa ba'a cikin garin Kano yake ba a gaya yake ,zaki iya janmu da mota mu tafi ko mu tafi da driver na."kin san bazan iya dogon driving ba saboda ciwon baya,muje dai da driver zaifi sauki. Hajiya Zeena ta gyada kai alamar gamsuwa ta shige toilet minti goma sha biyar ta gama karin kumallo ta shirya cikin atamfar super da mayafinta,suka fito cikin shirin zuwa garin (gaya)itada Mami,suna hanya kiran daddy ya shigo a Wayarta sai da gabanta yayi wata irin dokawa.dan bata faɗa masa zata fita ba,cike da karfin hali ta daga wayarsa bayan sun gaisa yake tambayarta bata gidane ?"yana jin karar abun hawa.?"da ido Hajiya Zeena ke kwatantawa Mami yadda zata fadawa daddy,naje gidan Safeena ne bata dan jin dadi Amman ba dadewa zanyi ba."kayi hakuri na manta ban faɗa maka ba, Daddy yayi mata addu'ar Allah ya bata lafiya haka yayiwa Mami alƙawarin idan ya samu lokaci zai kirata.da haka suka aje wayar Da sauri Mami ta kira Aunty Safeena a waya tace idan Daddy ya kirata ya tambayeta ya jiki."ta faɗa masa taji sauki,dan tafita bata faɗa masa ba tace tana gidanta bata jin dadi. Safeena tace Insha Yaya,Allah ya tsare hanya."Mami ta amsa da Ameen tana sauke wayar,Hajiya Zeenah ta cigaba da zuzuta maganin malamin da zasuje wurinsa tace cikin minti goma idan har maganin ya fara aiki Abba, zai iya sakin Aydah,shiru Mami kawai tayi tafi Hajiya Zeena son auren nan ya tarwatse kowa ma ya huta.tafia suke Amman bata ganin ma driver na taka motar yadda takeso dan har magana tayi masa akan ya kara gudun motar, da suka isa garin gaya har kofar gidan malam (dogo)motarsu ta tsaya ,suna fita daga motar Hajiya Zeenah ta karasa wurin driver ta ciro kudi a bag dinta ta kirga dubu goma ta soka masa a hannu,tace uzairu ka shiga gari ka ɗan shana da mungama zan kiraka."baki har kunne uzairu ya karbe kuɗin sa yayi reverse yabar cikin lungun dakyar mota ke shigowa kafin ka shigo da mota duka sai gabobin jikinka sunyi ciwo.mutum ɗaya suka samu yana dubawa Hajiya zeena tayi hamdala tana faɗin."Yau munzo a sa'a Kinga babu wani layi, kusan rabin awa da zuwa su suka samu ganin malamin ,nan Hajiya Zeenah ta gabatar da Mami a gaban malam dogo da kuma bukatar da ta kawosu wurinsa ,Aran Mami tace lallai kam kaci sunanka malam dogo irin wannan tsayi haka.Ya kalli Mami sa'annan ya soke kai yayi rubutu a kasa sai da ya kusa shafe wasu dakikai a haka kafin ya dago idonsa cikin na Mami yake faɗin."me kike so ayi masa?"kawai malam ina son ya sakar min ya'ta shi kawai nake bukata."malam dogo ya gyada kai ya kara soke kansa kasa yana cigaba da shafa kasa,ya dago ya kalli Mami yana faɗin."zamu fara saka masa tsanarta kafin mu saka ya saketa dan yaron nan da yarinyarki wani al'amari ne mai girma a tsakaninsu da ba'a bani ikon ganin ko menene ba, bazai iya rabuwa da ita cikin sauki ba yana yawan addu'a sosai sai dai zamu saka masa muguwar tsanarta aransa daga nan sai musan abunyi ,tau ayi haka Malam."Mami ta faɗa a gaggauce, Malam dogo ya haɗe hannuwansa wuri ɗaya ya runtse ido yana karanto kalmomin tsafi sai ga bakar laya ta bayyana a hannunsa ya mikawa Mami jiki na rawa Mami ta karba, Kusan yadda kukayi a sakata a inda yake kwanciyya ina nufin makwancinsa idan yau aka sakata aiki zai fara a yau.da sauri Mami ta turata cikin handbag cikin zumudi Mami,ke faɗin "malam nawa ne kudin aikin."Naira dubu dari biyar!"sai da Mami ta ɗan girgiza da kudin,ta kalli Zeenah da sauri tana faɗin."ba'a yi masa transfer na hannuna basu kai haka ba."nawa ne a wurinki dubu dari uku."tau zan ara maki sai kiyi min transfer anan wurin suka haɗawa malam dogo naira dubu ɗari biyar , suka yi masa sallama a mota Mami ta kalli hajia Zeenah cikin saukar da murya take faɗin."Tayaya xanyi wannan aikin zeena ?"kin san ko cikin mafarki bazan ba aidah ba nace ta saka ."na lura sadiya tanada wayau sosai da ita kawai zamu yi amfani wannan karon Mami tana kyaftawa Hajiya zeena ido alamar tana son taji karin bayani ,nan Hajiya Zeenah ta saka bakinta daidai kunne mami. Wani murmushi Mami ta saki da haka suka shiga garin Kano cikin farin ciki Hajiya Zeenah ta yiwa driver umurni kawai su wuce gidan Alhaji Bashir. #Love story2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. [1/4, 5:11 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 054. Banda zufa babu abun da take haɗawa tana dafe da cikinta tana bin ɗakin da kallo duk a tsorace take,mafarki ne !mafarki ne!"sai kuma ta fashe da kuka tana kiran sunan Abba da sauri ta lallubi wayarta ta kunna hasken fitilarta hannu ta kai ta kunna maballan fitilah da sauri ta sauka daga kan bed ta nufi kofa ta cire key, kai tsaye master bedroom ɗin Abba ta nufa ta rika buga masa ƙofa tana waiwayen bayanta,cikin bacci yaji ana buga masa ƙofa na fitar hankali da kyar ya buɗe idanunsa da mamaki jin muryar Aydah yayi tana faman ƙwalla masa kira bai san meyasa yake jin muryarta wani iri ba acikin kunnuwansa muryarta yake ji kamar ana doka masa wani abu acikin kwanyar kansa da gaske baya son jin wannan muryar da sauri ya dafe kansa jin ta cigaba da kiran sunansa kamar kansa zai fita da gangar jikinsa haka yake ji dakyar ya sauka kan bed ya nufi ƙofar ya cire key tana ganinsa ta faɗa jikinsa ta ƙanƙamesa babu inda baya rawa ajikinta jin yayi tamkar an zuba masa tafasasshen ruwan zafi ajikinsa jin Aydah ajikinsa ya fisgota yana kallon fuskarta a tsawace yake faɗin ."menene baki da hankali ne ya faɗa yana turata da karfi bai damu da inda zata fadi ba ya dafe kansa yana kallonta da fusassatun idanunsa bai san meyesa kallon fuskarta kurum yana saukar masa da wani irin ɓacin rai,cikin kuka Aydah tana ƙoƙarin kamo hannunsa tana faɗin."Yayanmu mafarki mafarki nayi."ta faɗa tana jan numfashi "saboda kinyi mafarki shine zaki rika bugamin ƙofa da daren nan are You crazy.?"ya faɗa sounding more angry ,tana ƙoƙarin shigowa ɗakin nasa ya daka mata wata irin razananniyar tsawa.keeeeee!"da mamaki take kallon yayan nata tamkar bashi ba dafe kansa yayi jin yana wani juya masa idan ya cigaba da ganin fuskarta komai zai iya faruwa dashi maida kofar yayi ya rufe batareda ya kara magana ba,yana jin yadda Aydah take kiran sunansa tana basa haƙuri wani irin tsanarta yake ji na zagaye ruhinsa duka.ta daɗe tana buga masa ƙofa ganin yayan nata yaƙi buɗewa yasa ta sauka ƙasa tana bugawa Huwaila kofa,cikin bacci Huwaila taji bugun ƙofa a firgice ta tashi cikin muryar tsoro take tambayar "waye? Muryar Aydah taji tana kuka A tsorace ta nufi ƙofar ta buɗe mata faɗawa cikin ɗakin Aydah tayi tamkar wacce aka jeho gaban Huwaila yayi mummunan bugawa da sauri Huwaila ta mayar da key,ta nufi Aydah ta rungume Huwaila tamkar zata shige cikin jikinta ga baki ɗaya. Sunfi minti goma a haka sai saukar ajiyar zuciya Aydah ke saki ajikin Huwaila sai lokacin wani tunani ya zowa Huwaila kodai Aydah daga wurin Abba ta gudu yau yana so ya karɓi hakkinsa ne taƙi basa haɗin kai?"dan irin yadda ta firgice lokaci ɗaya, "Aydah ki natsu ki faɗamin menene ina kuma yaya Abba?"yana ɗakinsa Aunty Huwaila tsoro nake ji mafarki nayi kibarni na kwanta dake, shiru Huwaila tayi can kuma kama hannun Aydah zuwa ga gadonta jikin Aydah yana rawa ta hau gadon ta kwanta tare da dunƙule jikinta wurin ɗaya, Huwaila ta zauna kusa da ita tana shafa kanta tana tofa mata duk addu'ar da tazo bakinta nan take bacci mai nauyi ya dauke Aydah,sai da Huwaila ta tabbatar da tayi bacci ta samu ta kwanta gefenta acan ƙasan ran Huwaila damuwa ce tayi mata yawa tana tausayin yaya Abba,da Aydah musamman Aydah Mami taki karbar ƙaddarar Aydah da hannu bibbiyu shiyasa har yanzu babu wani jin dadi da kwanciyyar hankali a wurin Aydah,ta rasa Mami wace irin uwa ce wacce son kanta yayi mata yawa."tana yiwa Aydah addu'a rayuwa mai sassauci da sauki a dukkan lamuranta,da haka ita ma bacci mai nauyi ya dauketa dukansu yau sun makara yau AB ko kallon room ɗin Aydah bai yi ba ya rasa meyasa ya kasa yin haka har ya dawo masallaci ya koma nasa ɗakin kwanciyya ya sake yi badan yana jin bacci ba yana ta kokayrin tuna abun da ya faru tsakaninsa da Aydah a daren jiya da ya damu kansa da sai ya tuna komai sai yaji kansa na wani irin juyawa tsaki kawai ya saki ya lumshe idanunsa, Aydah har ta gama shirin zuwa school taci indomie da Huwaila tayi mata tana ta kallon upstairs taga har lokacin AB bai fito ba idan kuma ta tuna ihun da yayi mata jiya sai taji jikinta yayi mugun sanyi, ganin 7:38 yasa ta nufi upstairs tsaye tayi bakin ƙofar ɗakinsa tayi knocking shiru taji har sau uku batareda tunanin komai ba ta murɗa ƙofar room din,hangosa tayi kwance kan soofa yana bacci ɗan ware ido tayi akansa kafin ta isa garesa sai da ta leƙa fuskarsa ƙarasawa tayi wurin kunnensa ta kira sunansa da karfi a firgice ya buɗe ido ya tashi zaune suna yin ido biyu da Aydah yaji ransa yayi mummunan ɓaci fuskarta yake kallo tamkar bakin maciji ya yi tsaki yarinyar nan.!"ubanwa ya kawoki ɗakina?"ya faɗa a tsawace ganin yadda idanunsa suka juye lokaci ɗaya yasa jikin Aydah ya soma wani irin rawa bata taɓa ganin yayanta haka ba ita idanunsa ma tsoro suke bata,bata taɓa ganinsa cikin wannan yanayin ba tamkar ba yayanta ba. Cikin rawar murya hawaye na taruwa a idonta take faɗin."nagama shirin makaranta."da mamaki yake kallonta kafin ya tattare girarsa wuri ɗaya da wata irin murya yace "Daga yau ba sai na kai ki makaranta ba zan yi kokari na samo maki driver ko ki dinga bin school bus,ita dai kallon yayan nata take da mamakinsa da ya hanata magana.ya dauko wallet ɗinsa dake kan mirror dressing ya ciro 5k ya karaso gabanta ya bata kuɗin ta karba tana kasa riƙe hawayen idanunta "ki shiga adaidaita kamin ki dawo zan yi kokari na samo maki driver ko na kira school ɗinku ki dinga bin school bus. Juyawa kawai Aydah tayi ta fice daga room ɗin nasa hawaye suka shiga zuba akan kyakkyawar fuskarta har ta bacewa ganinsa ya kasa motsawa daga inda yake sai bayan fitarta kansa da yaji yayi masa nauyi ya sauka. kwanciyyarsa ya koma ya yi bai kara tuna wata Aydah ba daman kuma idan ya matsawa kansa da tunaninta sai ya ji wani mugun ciwon kai na shigarsa.Aydah ko sallama bata tsaya yiwa Huwaila ba ta fice daga gidan da kafa ta riƙa takawa tana yi tana tare hawayen da suka kasa tsaya mata cikin fuskarsa ga baki ɗaya a rude take ta rasa wane irin tunani zata yi akan yayan nata ta dauka jiya cikin bacci yake shiyasa ya rika yimata ihu da tsawa yanzun ma haka,yayanta kowanne irin uzuri yake da ko bashi da lafiya sai ya kaita makaranta yau shine yake cewa ta tafi ta shiga adaidaita."ta kasa yarda yayanta ne da take matuƙar so da ƙauna, tana ta tunanin laifin da ta yiwa yayanta ta basa haƙuri ya sauko su dawo yadda suke ada, wannan bad attitude ɗin da ya tsiro mata ko kaɗan baiyi mata daɗi ba zuciyarta ba zata iya dauka ba,har taje school wannan ranar ga baki ɗaya friends ɗinta basu gane kanta ba. Haka ta dawowa Huwaila tamkar wacce bata da lafiya,har tambayarta Huwaila tayi ko bata da lafiya ne."ta faɗa mata lafiyarta ƙalau ɗaki ta shige ta kwanta ko uniform din jikinta bata cire ba. Ƙarfe 3 daidai yaje ya dauko Daddy a Airport tare suka ƙarasa gida sosai Mami tayi mamakin ganin Daddy ya dawo ranar dan bai faɗa mata zai dawo ba Amman tunda ta gansa tareda Abba tasan ya faɗawa Abban,a wani irin wulaƙance Mami ta amsa gaisuwar Abba ta shiga hidima da Daddy kusan tare suka ci abinci rana da Daddy yayi wanka ya kimtsa. Suna dawowa Masallaci Daddy ya yiwa Abba umurnin suje parlornsa su tattauna gaban AB banda faɗuwa babu abunda yake yabi bayan Daddy. Daddy sai da ya gama kallon yanayin Abba ga baki ɗaya,sa'annan ya daidaita murya "Ashe kun daidaita da surukinka baka faɗamin ba?" Sai da gaban AB ya buga jin irin tambayar da Daddy yayi masa,dakyar ya tattara natsuwarsa cikin daburcewa ya soma baiwa Daddy labari babu abun da ya boye masa,sai dai har lokacin bai fito kai tsaye ya nunawa Daddy yana da ra'ayin auren Rumaisa ba.sosai Daddy,yake mamakin zurfin cikin Abba."mun haɗu da Alhaji Bello Madawaki a Abuja ya bani haƙuri acikin taron jama'a kuma yace ko yanzu kake son Auren Rumaisa zai ɗaura maku aure."sai dai har yanzu banji ra'ayinka ba."da sauri AB ya shiga shafa kansa bai san me zai cewa Daddy ba da kunya yacewa Daddy ya amince zai auri Rumaisa."mun yanke shawarar nan da sati biyu za'a daura maku aure sai ka je ka cigaba da shirye shiryen biki mahaifinta yace baya bukatar ka wahalar da kanka tunda na farko kayi kuma baka karbi lefen da kayi mata ba.mamana kuma ka barni da ita gobe ka kawomin ita zan yi mata bayanin komai. godiya AB yayiwa Daddy,ya fice daga parlor yana jin wani irin tsantsar farin ciki aransa ga mamakinsa jin yayi kamar ya jawo ranar aurensa da Rumaisa bai san yana bukatar aure ba sai yanzu bai san shima cikakken namiji ne wanda keda burikka kala-kala acikin rayuwar aure sai yanzu, sunyi waya da Rumaisa yanata tsokanarta da amaryarsa ita ma farin cikinta ya kasa boyuwa har a muryarta "habeebi anjima za ka shigo ko? "sai bayan magarib. Da haka ya sauke wayar ya kira Ak ya tambayesa yana ina?"ya faɗa masa yana (hotoro)a majalisarsu sai da AB ya ɗan yi tsaki yana faɗin."banga amfanin wannan majalissar ba. "Kaine bata da amfani a wurinka kaima da sannu za ka zama ɗan gari tsaki AB yayi yana faɗin."ka jirani gani nan zuwa da haka AB ya sauke wayarsa ganin kiran Aydah na shigowa a wayarsa ya wani haɗe rai lokaci ɗaya yayi rejecting kiran karshe ya saka wayar a silent, a mota Ak ya cimma AB dan Abban cewa yayi shi ba zai karasa wurin ba, "mafarkina ya kusa zama gaskiya nan da sati biyu zan zama Angon Rumaisa.!"Abba ya faɗa da wani yanayi a muryarsa yana kallon Abdulkarim ɗin da shima shi yake kallo, ganin yadda Abdulkarim ya tsura masa ido yasan karin bayani yake nema. Anan ya faɗa masa yadda suka yi da Daddy,ko kaɗan Ak bai nuna wani jin daɗinsa ba shima Abban bai damu ba fatan alkhairi kawai Abdulkarim yayi masa ya masa sallama ya wuce sai da yayi sallah ya shiga gida Aydah najin shigowarsa ta fito daga ɗakinta komai ta tuna ta koma da sauri tun kafin su kai ga haɗa ido taji zuciyarta na wani irin bugawa.gargadinsa ta tuna shima ko kallon ɗakinta baiyi ba nasa ɗakin ya nufa yayi wanka a gurguje ya shirya cikin shadda milk colour sabuwa dal ,ya kafa hula akansa sai ƙamshi ke tashi tamkar wanda yayi wanka turare yana sauka falo Huwaila ta russuna ta gaishesa ya amsa fuska babu walwala.ita kanta Huwaila sai da gabanta ya fadi ganin yadda ya haɗe fuska.cikin sarkewar harshe take faɗin."daman Aydah tunda ta dawo bata ci abinci ba ta shige a daki babu irin rarrashin da ban mata ba taki taci. "ai ba yarinya bace ki kyaleta cikinta daga yau karki kara sakani a sabgoginku kina jina kiyi aikin da ya kawoki a gidan nan."da sauri Huwaila ta daga kai ficewa yayi daga parlor batareda ya ƙara bi takanta ba.wani irin mugun sanyi jikin Huwaila yayi meke damun yaya Abba,haka da gani akwai abunda Aydah,tayi masa da zafi kai tsaye ɗakin Aydah ta nufa tayi knocking jin shiru yasa ta tura kofar. Aydah ce zaune akan bed ta zuba uban tagumi idonta sun kumbura da alamar tayi kuka har ta gaji da sauri Huwaila ta nufeta tana faɗin."Subahanalilah Auta meya sameki haka?"dama tamkar jira Aydah,take ta fashewa da Huwaila kuka mai cin rai tana faɗin "yayanmu baya sona Aunty Huwaila yabi ya tsaneni ban san laifin da nayi masa ba."Huwaila ta sakata ajikinta tana rarrashinta cikin taushin murya Huwaila ke faɗin."ki faɗamin me kika yi masa da zafi har haka?"da sauri Aydah ta shiga girgiza kai hawaye na rolling cikin fuskarta take faɗin.'"babu abun da nayi masa nan ta faɗawa Huwaila abun da ya faru a daren jiya har mafarkin da tayi, ita kanta Huwaila da tafi Aydah,wayau sai da ta tsorata sai dai bata bayyanasa ga Aydah ba tace "yanzu dai yace kici abinci na faɗa masa bakici abinci ba."yace kuma na tabbatar kinci na kawo maki yanzu kici? "kaɗan zanci. Aydah ta faɗa tana komawa ta kwanta cike da matsananciyar damuwa.. #Love story2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/4, 5:14 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 055. Da rarrashi hadi da daɗin baki Huwaila ta samu Aydah ta ci abinci ta fita da plate ɗin Aydah kuma ta koma ta kwanta jin kanta take yi tamkar wacce bata da lafiya ko wacce aka zarewa lakkar jiki. Bata ji kuzari ko kadan, zuciyarta ya kasa accepting wannan bakon al'amari daga yayanta iya tunani tayi ta kasa gano laifin da tayi masa da cancanci wannan zazzafan hukunci daga garesa. Zuciyar AB fal farin ciki ya isa compound ɗin gidansu Rumaisa ya yi parking tare da kashe motar ya kira ta a waya jin kadan sai ga Rumaisa ta fito ta ci kwalliya jikinta sanye cikin light purple lace skirt and blouse sosai style ɗin ya karɓi jikinta tun kamin taƙaraso AB ya tsare ta da mayatattun idanuwansa yana kallon yadda jikinta ke jujjuyawa da yake ko mayafi bata saka ba. A zuciyarsa yake faɗin "Ka ga inda mata suke kalli yadda komai ya ji a jikinta Allah na tuba ni da zan mallaki wannan manyan kaya me zan tsinta a jikin kwaila. Rumaisa ta iso tare kwakwasa masa glass ya buɗe ƙofa ya fito yana mata wani kalar kallon kasan ido "kin yi kyau my habibty anya two weeks ɗinan ba su yi min yawa ba?" Ɗan zaro idanuwa Rumaisa tayi tana dariya "Bana so yaudara irin taku ta maza Habibi kai da kake da sabon jini a gida. "Mtss! Karki ɓatamin mood mana wannan yarinyar ita da babu bambanci su kaɗai ne a wurina don haka idan ba so kike ki ɓatamin rai ba kada ki sake sako min zancenta. Ba ƙaramin kaɗuwa Rumaisa ta yi ba da ta ji irin waɗannan maganganu sun fito daga bakin AB sani da tayi masa ada idan ta dauko masa zance Aydah, baya taɓa furta kalma marar daɗi akanta. Sai kawai ta taɓe baki ba tare da ta matsantawa kanta da wani dogon tunani ba ta wuce gaba ya bi ta a baya har zuwa parlor da suka saba zama, tsarin yadda bikinsu zai kasance suka tsara. Bayan ya baro wurin Rumaisa ya shiga gari don kwata-kwata bayaso ganin fuskar Aydah gudun kada ya haɗu da ita yasa ya yi zamansa sai around ten na dare ya shigo gida sai dai abun da yake gudu shi ya tarar Aydah tana zaune a parlor ta yi tagumi idanuwanta sun yi luhu-luhu alamar tasha kuka ta yiwa kofar shigowa kurr da koɗaɗɗun idanunta, yana arba da ya ita ya ji takaici da tsanarta sun lulluɓe masa zuciya. Ya gitta ta ya wuce batareda da ya ko kalleta ba har ya fara haura mattakalar bene Aydah ta taso da gudu ta rungume shi ta baya sosai ta ƙanƙame shi tasa kuka "i'm sorry Yayanmu please forgive me ba zan sake ba, dan Allah ka daina fushi dani ko kayi min duka idan har za ka huce daga wannan fushi da kake dani kayi min duka ka zane ni. Ta ƙarashe magana cikin gunji kuka gwanin ban tausayi Huwaila wacce ke laɓe a jikin ƙofar ɗakinta tana leƙo abun da ke faruwa babu yanda bata yi da Aydah ba akan ta je ta kwanta amman taƙi ta ce sai yayanta ya dawo ta bashi haƙuri, nan da nan idanun Huwaila suka cicciko da hawayen tausayin Aydah. Yarinyar da ke tsoron duka yau ita ce ke insisting a dake ta lallai hali da take ciki ya yi tsanani domin abu ne da bata saɓa dashi ba. A mugun fusace AB ya juyo ya fincike hannayenta daga riƙo da tai masa ya ware kyawawan zara-zaran yatsunsa ya sauke su akan tattausan kumatunta "How dare you to touch me kin ji min iskanci ni sa'anki ne? Wannan shine gargadina dake na ƙarshe karki sake wa'yannan kazaman hannuwa naki su sake gigi tabani duk abun da nayi miki ke kika siya da kudinki stupid girl! Ya ƙarasa magana tare da kyasta mata yatsun hannunsa alamar gargaɗi kana ya haura sama abinsa, yayin da Aydah ta bishi da kallo da sauri Huwaila ta zo ta kama ta kasa kuka tayi sai kurum ta lafe a jikin Huwaila tana wani jan numfashi, a kidime Huwaila ta ƙarasa da ita dakinta ta zaunar da ita gefen gado, babu abun da Aydah ke yi sai jan numfashi gani take yi duka abubuwa nan dake faruwa tsakaninta da Yayanta mafalki ne ko illusion ta kasa yarda a zahiri ne hakan ke faruwa. "Ki yi haƙuri Auta bawa baya zama babu jarabawa duk wanda yasan Yayanmu zai iya bata da tabbacin akan irin ƙaunar da yake min kwatsam! A waye gari yana nuna miki tsana wannan wani abu ne da hankali da tunani ba zai dauka ba. Dole akwai abun da ke faruwa. Aydah ta ɗago soyayyun idanunta ta kalli Huwaila dasu tana girgiza kanta irin na wanda ke jin zafi acan ƙasan zuciyarsa "Ban san nayi masa wani laifi ba aunty Huwaila kawai dai ya tsaneni batare da wata hujja ba ko kuma Mami ta yi nasara akansa ta cilasta masa tsanata idan ba haka ba aunty Huwaila me na yi masa da yake min haka?" "Allah ne masani gaibu auta ni ba zan yanke hukunci akan abun da banada masani akansa, amman ki bashi lokaci har zuwa sanda zai huce na tabbata ba zai iya dogon fushi dake ba. Deep breath Aydah ta ja tare da jan pillow ta kwanta"Ba komai aunty Huwaila Allah shine shaida ta ina son Yayanmu banaso daidai da kwarar zarar nagansa cikin damuwa amman haka zan yi haƙuri na nisanta kaina daga gare shi. Kalamanta suka ƙara narkarda zuciyar Huwaila ta dinga sharar hawaye a fakaice yayin da Aydah kumatunta kawai take shafa wanda har yatsunsa sun kwanta, mata radau-radau har zuwa lokaci ta kasa kuka ashe ko kuka rahama ne ashe akwai abun da zai iya faruwa da ita da zai hana mata kuka. AB ya shiga ɗakinsa rai ɓace har ya cire kayan jikinsa zuciyarsa bata daina tafarfasa ba,tsabar ɓacin rai a naked ya shiga banɗaki yana wanka kwanyarsa ta dinga yimasa backwards ɗin abun da ya faru a tsorace ya ɗago hannunsa yana kallon palm ɗinsa wai gaske da wannan tafin hannu ya mari Aydah, shin wai me ya hau kansa ne da yake ji mahaukaciyar tsanar Babynsa me tayi masa haka da zafi ne?"Ko kaɗan ya kasa tunano laifi guda kwakkwara da tai masa da ta cancanci ya dinga treating ɗinta like this. "Oh! God, fix my problems, I don't want to continue to mistreat this girl ni ba mugu bane and I don't want to be a merciless villain. AB ya yi magana a bayyane can kasan zuciyarsa yake ji zafin abun da ya aikatawa Aydah ya kashe shower ya dauki towel ya ɗaura ya fito, har ya shirya cikin kayan baccinsa zuciyarsa bata masa daɗi he's feeling guilty about what he did to her, sai dai baya ji zai iya tunkarar inda take. Washegari Aydah tana tashe ta shirya cikin school uniform ta goya backpack ɗinta ta sauko kasa a kitchen ta tarar da Huwaila cikin sanyi muryarta ta gaishe da Huwaila anan cikin kitchen ta yi breakfast, bata nemi AB ba ta wuce school during breakfast period, PC ta aiko nemanta ta je office ta same ta anan take faɗa mata yayanta ya kirata ya ce daga yanzu za ta dinga bin school bus Aydah was not happy a tunaninta yayanta ya faɗa ne kawai ba zai barta da gaske ta dinga bin bus ba, kamin ta kai class ɗinsu ta shara hawaye yafi a kirga ƙawarta shiru-shiru ƙawayeta suna jiranta ta dawo su yi breakfast amman bata dawo ba. Koda suka shigo class suka ganta ta kifa kanta a jikin desk ɗinta tana shasshekar kuka a kidime suka yo kanta "what happened, why are you crying, what did the PC say, you did something wrong?" Dukkan waɗannan tambayoyi ƙawayenta biyu ke mata, kuma ba wanda ta amsa kurum ta cigaba da kukanta. "Abeg Aydah tell us mana remember we're good a friends you can't sharing your problem with us ko ba haka bane Meera??" "Kwarai kuwa Zaliha mu ƙawaye ne tun daga nursery school muke tare ba mu taɓa rabuwa ba matsalarki Aydah na mu ne Please ki faɗamin me ke faruwa tun safe da kika zo fuskarki ya nuna kina cikin damuwa. Batareda Aydah ta yi magana ba ta fice da sauri suka bi bayanta suna kiranta sunanta can bayan ajujuwa ta nufa gun da babu hayaniya ta zauna, akan wasu chairs da aka yi su da siminti Zaliha da Ameera suka saka ta a tsakiya, sai rarrashinta suke yi Zaliha da yake tana da zuciya nan take ta fara hasala "me damuwarki ne Aydah Bashir huh? Mun tambaye ki matsalarki but you refuse to tell us, sai wani banzan kuka da kike mana kuka zai yi miki magani damuwarki ne?" "Ki yi mata a hankali Zaliha ba ki san actual abun da yake damu ta ba. "Duk abun da yake damunta mu ma yana damu mu she's our friend we have good time together, akan me ba za ta buɗe baki ta faɗa mana damuwarta ba ko dai bata dauke mu ƙawayeta ba?" Aydah ta ɗago kodadun idanunta ta kalli Zaliha, sai kuma ta goge fuskarta da tafukan hannayenta tana jan majina irin ta wanda yaci kuka har ya godewa Allah. Cikin sanyi murya ta faɗa musu abun da ya faru tsakaninta da yayanta, sai kawai Zaliha ta sa dariya tare da rungume Aydah "OMG! Aydah Bashir when will you grow up? Just because your brother is angry with you sai ki dinga wannan uban kuka. "Gaskiya Aydah Bashir ya kamata ki rage shagwaɓa gaba ɗaya kin tashe hankalin mu akan abun da bai taka kara ya karya ba. Idan kin koma gida ki bashi haƙuri in sha Allah zai haƙura kin ji crying baby? Ameera ta faɗa tana kwantowa jikin Aydah shiru kawai Aydah ta yi tana bin su da ido tasan ba za su fahimci abun da take ji ba. Bayan an tashi daga school ta bi school bus kamar yadda AB ya bukata. Bangaren AB da ya tashi ya shirya abinsa ya wuce office bayan ya je ne ya kira principal ɗin su Aydah ya gayamata aiki ya yi masa yawa daga yanzu Aydah za ta dinga bi school bus. *********** Sannu a hankali Ciroma ke samun nasara akan muradinsa a wannan zaman na ƙarshe da za a yi sai da ya kai wa bokansa ziyara ya sake basa wani turare ya ce idan za a yi zaman ya shafe jikinsa dashi, zai ga abin mamaki haka kowa aka yi kamin ya shiga ɗakin da za a gudanar da taron ya bade jikinsa da turare da bashi da daɗi ko kaɗan kamar turaren 'yan bore sai azabar hawan kai, a haka ya kutse ɗakin manyan fada suna shaƙar ƙamshin kowanne su ya sha jinin jikinsa Ciroma ya nemi wuri ya kame sai hura hanci yake yana kallonsu ɗaɗɗaya, yana jiran me za su ce wambai ne ya yi gyaran murya da kalle shi za ka gane a tsorace yake da har wani rawa muryarsa ke yi "Dangane da tsari na wannan masarautar ta mu mai albarka muka yi duba da cancanta ne mu naɗa sarki, da farin dukanmu kowa anan yasan Ciroma shine yafi dacewa haɗe da cancanta da ya zama sarkin mu saboda haka mu 'yan majalisar sarki mu yanke shawarar naɗa Ciroma a matsayin sarkin wannan masarauta kun amince ko kuma akwai wani mai ja?" "A'ah!mun amince mun amince. Kusan a tare manyan fada suka haɗa baki, wannan al'amari ba ƙaramin daɗi ya yiwa Ciroma ba don sai wani kaɗa kai yake yi kamar kadangare. "To Al-hamdullilah tun da kowa anan ya yi na'am sai mu fara shirye-shirye naɗin sa nan da sati mai zuwa. Aliyu na Uku ne ya fara miƙewa ya fice daga ɗakin taron bayaso sarautar nan ko kaɗan amman ya rasa dalili da yasa yake ji babu daɗi da ya kasance Ciroma ne ya same ta, yana ji a jikinsa kamar hawan Ciroma a karagar mulki kudu tamkar wani mummunan al'amari ne zai faru. #Love story2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Kurman Aliyu Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/5, 8:02 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 056. AB bai samu kai Aidah gida ba sai a washe garin kamar yadda Daddy yayi masa umarni kuma an shiga hutun weekend,a kitchen ya samu Huwaila tana 'yan aikace-aikace wake-wakenta take yi cikin nishadi amman acan kasan ranta damuwa ce a tattare da ita ganin uwar ɗakinta cikin mugun yanayin da ko a mafarki bata taɓa tunanin zuwansa ba ita kanta taga yadda yaya Abba ya canja lokaci ɗaya tamkar mai cutar jinnu har tsoron haɗa hanya take dashi.tamkar ance ta juya bayanta taga Abba,tsaye a bakin ƙofar shigowa kitchen ya harɗe hannunsa a kirjinsa yana kallonta fuskarsa babu annuri acikinta nan take jikin Huwaila ya fara rawa tsoronta Allah kar ya rabata da gidan nan tasan idan bata cikinsa waye zai kula da Aydah wa zai riƙa cewa taci abinci. Gyaran murya yayi yana faɗin."ina yarinyar nan take ?"a tsorace Huwaila ta bashi amsa."tana ɗaki! "Kice ta sameni a mota. Da haka ya juya ya bar kofar kitchen ɗin,da sauri Huwaila ta haura sama ɗakin Aydah ta tura ta sameta kwance akan bed tayi rubda ciki taji ta ɗan samu natsuwa ganin break fast ɗin da ta kawo mata ta ɗan ci haka zalika tayi wanka tana sanye da doguwar atamfa ajikinta kanta babu ɗan kwali Huwaila ta kira sunanta a hankali,shiru Aydah tayi mata kanta ciwo yake kamar zai rabe mata gida biyu "Auta ki tashi Yayanmu na jiranki a mota. Ai tana jin sunan yayanmu lokaci ɗaya ta buɗe ido kuma ta miƙe zaune tana kallon Huwaila "ki saka hijab ɗinki yana jiranki."wani murmushi ne Aydah ke yi nan da nan fuskarta ta cika da fara'a tace"Da gaske Aunty Huwaila yayanmu ne ke kirana?ta faɗa sounding so very emotional hawaye na taruwa a idanunta,da sauri Huwaila ta daga mata kai alamar tabbatarwa , "Na canja kaya Aunty ko na tafi a haka?"Aydah ta faɗa tana nufar wurin kayanta,wannan ma yayi Amman ki canja da sauri Aydah ta buɗe closet ɗinta tana bincike duka kayanta tana faɗin Huwaila ta ƙaraso ta tayata zaben wanda zata saka,Huwaila jiki a sanyaye ta karaso tana ganin irin murnar da Aydah keyi tamkar ba ita ba tana ta addu'a Allah yasa ta tarar da farin ciki a wurin Abba."Yayanmu yana son abaya Aunty Huwaila ki zabar min wacce zan saka. Ta faɗa tana kaita gaban dogayen rigunanta masu kyau da tsadar gaske wata maroon color Huwaila ta dauko mata mai adon duwatsu ajikinta nan take Aydah ta shiga shirya kanta ta saka powder a fuskarta har kwalli ta saka da man baki , takalminta ta saka ta dauki handbag ɗinsu juya kanta ta shigayi a gaban huwaila tana faɗin "nayi kyau Aunty Huwaila?"dariya Huwaila tayi tana faɗin "kinyi kyau sosai Auta har ƙofar parlor Huwaila ta rakata tayi mata fatan dawowa lafiya. Koda ta iso waya yake da sahibarsa Rumaisa har ta buɗe motar ta shiga ta zauna bai katse wayar da yake da rumaisa ba, tafi minti goma zaune a motar tana jin yanda ranta ya sosu sosai, ya katse wayar tana jin yana faɗawa Rumaisa zuwa anjima zai shigo wurinta yaci abincin rana, sai da bugun zuciyar Aydah ya tsaya na kusan sakan talatin bai damu da yanayin da Aydah ta shiga ba,yaja motar batareda ya kalleta ba ballantana ta saka ran zai mata magana. Har zata buɗe baki tayi masa magana tuna irin marin da yayi mata jiya sai ta fasa daidai kofar gidansu taga yayi parking motar batareda ta kallesa ba ta balle marfin motar daman duk lokacin da taga yayi haka ba shiga zai yi ba.tana rufe ƙofar motar ya wani fisge motar da wani irin gudu ya badeta da kura.wani irin mugun rauni taji zuciyarta tayi duk yadda taso rike hawayenta kasawa tayi sai da suka zubo da sauri tasa hannu ta goge cike da sagewar gwiwa ta doshi gate ɗin gidansu....ido biyu suka yi da Siyama dake zaune cikin parlor Siyama,ta ware ido tana kallon little sis ɗin tata da sauri ta karasa ta rungume Aydah ita ma Aydah,rungume Siyama tayi wani kuka ta fashewa da Siyama dashi mai fitowa tun daga karkashin zuciya. A rude Siyama ta ɗagota tana ta kallon parlor kar wani ya fito yaga Aydah tana kuka a gigice ta riƙa hannunta tayi hanyar kofar ɗakinta ,har cikin ɗakinta Siyama ta jata anan kasan rug ta zube ta rika rerawa Siyama kuka na fitar hankali duk Siyama ta rude ta jawo kanwar tata murya can ciki take faɗin."ki natsu Aydah ki rage wannan kukan kar Mami,taji kiyi min bayani wani abu ya samu yayanmu ne?"Siyama ta faɗa cikin rawar murya cikin kuks Aydah ke faɗin."ban san me na yiwa yayanmu ba duk yabi ya tsaneni yaya Siyam, Yayanmu ya daina sona. Sai da gaban Siyama yayi wani irin buguwa kallon Aydah take ganin yadda tayi rama lokaci ɗaya "ke me kika yi ma yayan namu nasan bakida gaskiya Aydah ba haka kawai zai yi fushi dake ba."Ni fa yaya Siyam babu abunda nayi masa."shiru kawai Siyam tayi ta zuba tagumi tana kallon kanwartata dake famar sharar hawaye.dialling lambar Yaya Abba,tayi yana ɗagawa yace Siyam ya akayi ne?"gaishesa tukun siyama ta fara yi sai kuma tayi shiru ta rasa abun da za ta ce masa jin shirun ya yi yawa yasa yace "Ya aka yi ne Siyama.?"cikin rawar murya Siyama tace "Daman Aydah ce ta zo tana kuka yaya."sai tace maki wani abu nayi mata dan ni mugune kou?"Abba ya faɗa da wata irin murya wacce Siyama bata taɓa jinsa da ita ba, rudewa da gigicewa yasa Siyama ta rasa me zata faɗa masa sai kawai ya kashe wayar,da ido kawai Aydah take bin ta batace komai ba ta koma kan bed din Siyama ta cire doguwar rigar jikinta daman akwai riga da skirt na english wears ajikinta taja duvet ɗin Siyama ta rufe har kanta batareda tace komai ba da ido Siyama ta bita ta kira sunanta a hankali sai dai Aydah tana jinta tayi mata shiru hawayen idonta sun kasa tsayawa wani irin rauni zuciyarta tayi har lokacin ta kasa yadda yayanta ne yake hukuntata da laifin da bata san ta aikata ba.da haka wani nauyayyen bacci ya dauketa bar mata dakin Siyama tayi ita ma jikinta yayi mugun sanyi,zamanta ta cigaba dayi a parlor suna chat da Saleem,sama-sama sai kusan la'asar ta koma ɗakin har lokacin kuma aAydah bacci take wanka tayi ta dauro alwallah tana zaune a gaban mirror dressing tana shafa cream ɗinta da take using,taga Aydah ta cire duvet din jikinta da sauri ta sauka daga kan bed ɗin tayi saurin rufe bakinta da hannunta biyu da gudu ta nufi toilet tun kafin ta karasa ta durkushe a wurin ta rika amai tsoro da gigicewa yasa Siyama ta karaso wurinta ta riketa duk ta gama galabaita ga jikinta yayi wani irin saki ga shi yayi zafi sosai ,Siyama ta taimaka mata ta wanke bakinta a kan rug ta kwanta tana mayar da numfashi ,kai tsaye Siyama ta nufi ɗakin Mami a tsorace ,zaune ta samu Mami da Sadiya da alamar magana suke suna ganin Siyama suka yi tsit daman Sadiya ko kallon Siyama bata yi ba ta cigaba da danna wayar hannunta. Lafiya kika shigo mana a gigice sai kace mutuwa akayi."tuni Siyama ta fara hawaye cikin rawar baki take cewa Mami,Aydah ce keta amai a dakina.!"Siyama ta faɗa hawaye idonta suka kasa tsayawa daga Mami har Sadiya sai da zuciyarsu tayi tsalle cikin rawar baki Sadiya tace yaushe ta zo gidan."tun wuraren 12,ai tuni mami tayi waje bata tsaya jiran bayanin da Siyama ke yiwa Sadiya ,ba da sauri Siyama ta bi bayan Mami aka bar Sadiya cikin gigicewa da kidemewa ,hannu ta ɗora akai tuni hawaye suka fara rolling cikin fuskarta zagaye dakin Mami ta soma yi shikenan yaya Abba ,ya haɗa gado da Aydah dah tunda har amai take duk wani buri da ta ɗora akan yayan nata a hankali taji yana rugujewa ,Aydah ta cuceta ta cuci rayuwarta bata taɓajin tsanar wani a rayuwarta ba kamar yadda ta tsani Aydah bata san me zata yi mata ba ta ɗandana mata bakin cikin da ta dasa mata acikin zuciyarta har abada bazai gogu ba ,tayi alkawari kamar yadda Aydah tayi gudu da rayuwarta sai ta tarwatsa mata rayuwarta ta dauki alwashin ko da shine abu na karshe da zata aikata cikin rayuwarta sai ta san yadda cikin nan ya fita ajikin Aydah da haka ta dauki wayarta ta fice daga ɗakin na Mami ko kallon dakin Siyama batayi ba ɗakinta ta shige ta rufo kofa.babu irin lallashin da Mami bata yiwa Aydah ba akan ta faɗa mata meke damunta banda kuka babu abunda Aydah take, haushi duk ya kama Mami tsoronta Allah kar ace ciki ne ajikin Aydah da Abba ya cuceta ya gama da rayuwarta.ta dubi Siyama tace ki fito da ita muje asibiti Da haka Mami ta fice daga dakin tashin hankali bayyane cikin fuskarta dialling ɗin lambar AB tayi a wayrta harta katse bai dauka ba tana kokarin kara kiransa sai ga kiran sa ya shigo da respect ya gaisheta ,bata ko saurari gaisuwarsa ba cikin bala'i da masifa tac "Bashir uban me ka yiwa yarinyata?"ciki kayi mata ko tsoron Allah bakaji me zaka tsinta a jikin Aydah don ubanka?"Mami ta faɗa a tsawace juya maganganun Mami,ya shiga yi aransa gabaki ɗaya kansa ya daure wallahi-tallahi idan wani abu ya sameta sai na tsine maka Abba ."Mami ta faɗa so pissed up tana sauke wayar. "Na kawo maki abinci kici?"Siyama ta faɗa tana kallon Aydah dake mayar da numfashi dakyar,daga kai kurum Aydah tayi da sauri Siyama ta fita dan kawowa Aydah abinci, cikin kayan Siyama ta nufa ta ciro pant sabo da pad ta nufi toilet dakyar ta shirya kanta daman duk zata yi period sai tayi rashin lafiya ,har da kwanciya a asibiti haka take duk wata a gidan har fargabar zuwan period ɗin Aydah suke yadda take cin wahala tamkar wata mai ciki. Koda Siyama ta kawo mata abincin tana toilet sai bayan ta fito ne ta samu Siyama ta kawo mata abinci kallon abincin kurum da tayi sai da taji zuciyarta na yamutsewa wani amai taji yana zo mata da gudu ta koma toilet nan ma aman ta ƙara yi kamar zata amayar da duka hanjin cikinta Siyama dai sai sannu take mata. Siyama ta fito rike da ita daidai lokacin da Mami,ta shigo dakin da hijab ajikinta da car key.wani aman ta sake yi. Siyama ta ɗagawa Mami kai Ki saka mata hijab muje asibiti yanzun nan,in banda jaraba uban me zai tsinta acikin Aydah idan ma cikine wallahi Ba zasu dawo gidan nan ba sai an zubar dashi. Daga Mami sai Siyama suka kai Aydah asibiti. Dr.firdausi ce suka samu ita ta duba Aydah ta kalli Mami,tana faɗin."Hajiya ko period ɗinta yazo ?"sai lokacin Mami ta tuna da idan tana period tana ciwo kamar zata mutu. "Bana tunanin haka doctor. Dr. Firdausi ta dubi Aydah tana faɗin."Autar Mami,period ɗinki yazo?"daga kai kurum tayi ko magana bata son yi, wani numfashi Mami ta rika saukewa gigicewa ma yasa bata yi wannan tunanin ba sai yanzu hankalinta ya kwanta sai da aka kwantar da Aydah ganin yadda take amai sosai duk ta galabaita ta fice daga hayyacinta dole aka saka mata drip.har bayan magrib Siyama na tare da Aydah ,lokacin Mami ta koma gida har lokacin Aydah bacci take. Siyama na sallar ishaai Daddy,da AB suka shigo (amenity room) ɗin da aka kai Aydah,tunda ya shigo idonsa ya sauke akanta tayi rama ba yar kaɗan ba.da sauri ya dauke kansa kuma ya kasa ƙarasawa cikin room ɗin,Siyama sai kallon yayan nasu take da mamaki, Daddy ne ke yiwa Siyama tambayoyi taci abinci?"tea kaɗai ta sha daddy kasan idan tana ciwon nan bata cin abinci."har kusan 9 Daddy,da AB na asibitin kuma har lokacin bai ƙarasa wurin Aydah ba ita ma lokacin ta falka hankalinta Ga baki ɗaya yana wurin yayan nata.daman shi ya dauko Daddy,sallama suka yiwa Siyama Daddy yana faɗin."idan da matsala ta kirasa,Mamana ko kina bukatar wani abu?"da sauri ta girgiza kai hawaye na taruwa a idonta tana kallon saitin da AB ɗin yake ,danna wayar hannunsa kurum yake ganin saitin da take kallo yasa Daddy ya saki murmushi yana faɗin."Ni ina maki magana yayanki kike kallo tau shikenan sai da safe Daddy,ya faɗa yana shafa kanta. bayan fitar daddy, still AB bai karasa gaban Aydah ba ya juya yana yiwa Siyama sallama,yace idan suna bukatar wani abu su kirasa daga masa kai Kurum tayi. #love story2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/5, 8:07 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 057 Washe gari wuraren karfe 9 na safe sai ga Mami,ita da Daddy sun shigo ɗakin,daidai lokacin da Aydah ta fito daga wanka.kallonta kawai Mami take ganin yadda Aydah ta zabge lokaci ɗaya,daga Mami har Daddy sannu suke yimata Siyama ta gaishe da iyayen nata,ganin su mami yasa Aydah ta dauki kayanta ta koma toilet ta shirya,tana fitowa Mami da Daddy suka sake yi mata sannu da jiki. Mami ta kalli Siyama tace ta haɗa mata tea nan take yanayin fuskar Aydah ya canja ta kalli Mami kamar zata yi kuka take "ni sai na jira yayanmu."baki sake Mami ke kallonta ,cikin banbamin faɗa Mami ta ce ."cikin uban waye idan baki sha ba munafuka da ya damu dake ai da ya zo ya kwana tare dake,da sauri Daddy ya katse Mami ,yana faɗin "Haba Mariya menene abun faɗa aciki ?"tace zata jira yayanta ba sai ki lallabata ba. Takaici yasa Mami tabar masu ɗakin tana jin ranta na bala'in ɓacin ,acan kasan ranta kuma tana ta tunanin ko maganin da aka yiwa Abba,yayi tasiri akansa ne?"akwai ayar tambaya, da yanzu yana asibiti ko shine zai kwana tare da ita duk soyayyar da yake yiwa Aydah ace ta kwanta asibiti bai kwana tare da ita ba wannan al'amari abun dubawa ne, dan sanyin Mami taji aranta tana ta addu'a Allah yasa ma maganin ya kamasa zamanta tayi anan waje batareda ta koma ciki ba. Babu yadda Daddy,bai lallaba Aydah ba akan ko tea ne tasha idan yayan nata yazo sai suyi break fast tare taki yadda,daga waya Daddy yayi ya kira Abba with respect Abba ya daga yana gaishe da Daddy, cikin sakin fuska Daddy ya amsa yana faɗin."muna asibiti ashe baka karasowa ba?"gaban Abba sai da yayi wata irin dokawa har ga Allah ya manta da Aydah tana kwance a asibiti mantawa yake ma da ita acikin rayuwarsa, dakyar ya haɗa kalmomin faɗawa Daddy nacewa gashi nan zuwa. "To kinji yana hanya."daddy ya faɗa yana kallon Aydah da ta koma ta kwanta bayan ya sauke wayar,lumshe ido tayi zuciyarta na wani irin bugawa samun kanta tayi da addu'ar Allah yasa yayan nata ya huce.bai taɓa fushi da ita irin wannan ba tana bala'in azabtuwa kamar da minti talatin sai ga AB ya bayyana cikin ɗakin da sallama a bakinsa har lokacin Daddy na tare da Aydah,tun kafin ta kallesa zuciyarta ke wani irin tsalle ƙamshin turarensa kurum da taji ya saukar mata da wata irin kasala.tsaye yayi a bakin kofar ya kasa shigowa Siyama tana gaishesa ta dauke kanta akansa, Daddy ya daga kai yana kallonsa da mamaki yake faɗin."ka karaso mana."tamkar wanda aka zarewa lakka ya nufi gadon da Aydah take kwance duk yadda yake jin zuciyarsa na rawa haka kafufunsa na son kasa daukarsa haka ya nufi gadon da Aydah ke kwance "mamana ki tashi ga yayan naki nan ya zo. Daddy,ya faɗa yana miƙewa tsaye yana barin wurin gadon yana baiwa AB wuri dakyar AB ya zauna kan bed ɗin yana jin kusancinsa da Aydah tamkar ana hura masa wuta a dukka sassan jikinsa nan take idanunsa suka fara juyewa suna zama wani kala tamkar ba nasa ba ,da sauri Aydah ta buɗe idonta ta riƙe masa hannu cikin rawar murya tace "Yayana!"tamkar wanda aka jonawa wayar lantarki haka yaji hannun nata kuma taki sakin hannun nasa,wayar Daddyy ce tayi kara da alamar kirana ne ya shigo masa ya fice daga room ɗin dan amsa kiran da sauri ya fisge hannunta ya kuma mike tsaye yana bin ta da mugun kallo, daman daga shi sai ita ya rage a dakin,da sauri ta mike zaune hawaye har sun taru a idonta "kayi hakuri dan Allah Yayanmu na tuba nabi Allah na bika. Ta faɗa cikin fashewa da kuka yana juyawa suka yi ido biyu da Mami da take tsaye a bakin ƙofa tana kallonsu, atsorace Mami ta karaso cikin ɗakin tana tambayarsa meya faru kuma.?"tsit Aydah tayi tana haɗe kukanta dan bata son Mami ta fahimci akwai matsala ita da yaya Abba,tasan wani sabon rikici ne za'a yi gara ta rufawa kanta asiri kar Mami ta hanata komawa gidan yayanta shima Abba kusan tunani ɗaya ne yayi da Aydah da sauri ya koma kan bed ya zauna ya Jawota gefensa yana tambayarta menene kuma abun Kuka?"duk da karfin hali kawai yake,tsaye Mami tayi tana kallon su zuciyarta na ɗan bugawa. A daburce AB ke faɗin."na haɗa maki tea zaki sha?"da sauri Aydah ta daga kai tana jin wani irin farin ciki na lullube mata zuciya, a gaban Mami ya haɗa mata tea ya shiga bata da kansa duk da jin yake kamar ana zare masa rayuwa jin kusancinsu ,a haka Daddy ya dawo ɗakin ya samesa yana bata tea ita dai Mami saboda takaici ficewa tayi daga ɗakin. Bayan fitar ta ta daga waya ta kira Hajiya Zeenah a rikice take faɗin ."wai yaushe maganin nan zai fara aiki akan Abba.?" "kefa Hajiya mariya kin fiye gaggawa tunda malam dogo ya tabbatar mana komai zai tafi daidai ba sai mu zuba ido mugani ba in har Sadiya ta saka layar ga yadda aka umarce ta. Ajiyar zuciya Mami ta sauke tana faɗin."Sadiya lafiya lau ta saka ita kanta bata son tayi wani kuskuren da za'a samu tangarda. "To shi kenan sai ki kwatar da hankalinki in sha Allah haƙar mu za ta cimma ruwa. Nan take Aydah ta shanye tea Daddy sai tsokanarta yake Daddy ya fice daga asibitin ya koma gida aka bar Mami a wurin Aydah daman Siyama gida ta koma Daddy na fita ko minti biyar bai yi ba AB ya faɗawa Mami zai wuce sai zuwa anjima zai daso,ko kallon arziki bai samu daga Mami ba da ido Aydah ta bisa har ya fice daga ɗakin nan take yanayin fuskar Aydah ya canja, komawa tayi ta kwanta Bayan magrib aka sallami Aydah zuwa gida AB mane ya daukosu da motarsa mami ta bi ta haɗe rai tana faɗin.'can gida zai kaisu sai Aydah ta kwana biyu jikinta ya yi kyau kamin ta koma gidansa. AB baiyi musu ba ya kai su can gida ko kaɗan Aydah bata ji daɗin wannan hukuncin da Mami,ta yanke ba har suka isa gida bata saki ranta ba kwanan ta biyu ta samu sauki sosai haka AB yana daurewa yazo kullum ya dubata sau biyu kar iyayen nasu suka fara fahimtar kamar da akwai matsala a tsakaninsu gashi sai shirye-shiryen bikin sa ake da Rumaisa, daga Mami har 'ya'yanta babu wanda ya san wainar da ake toyawa, dan har lokacin Daddy bai zauna dasu ya faɗa masu ba ,kwanan Aydah uku a gidan ana sauran kwana goma bikin Rumaisa da Abba, Daddy ya tarasu a falonsa bayan magrib har AB ya halarci taron daga nesa kawai Aydah ke hango yayan nata da yabi ya canja mata lokaci ɗaya, Sadiya sai wani shige masa take,Daddy ya saka Aydah ta buɗe taro da addu'a tayi yadda daddy ,ya umarce ta kafin Daddy ya buɗe baki ya fara yiwa kowa bayanin auren Abba da Rumaisa akan kowa yayi haƙuri ya ɗaukesa a matsayin ƙaddara daman Rumaisa tana cikin ƙaddarar Abba, Daddy yayi masu bayanin haduwarsu da mahaifin Rumaisa biki yanzun sauran kwana goma, babu wanda bai shiga shock ba,musamman Aydah da ta kafawa yayan nata ido nasiha mai ratsa jiki Daddy ya shiga yiwa Aydah wacce ta haɗe kai da gwiwa tana wani irin kuka mai sosa rai ,a mugun hasale Mami ta miƙe tsaye cikin daga murya da zafin rai take faɗin ''idan kuma Abba har ya amince zai auri wannan matsiyaciyar yarinyar da iyayenta suka wulakanta mu sai dai ya sakar masu 'ya domin shekarun Aydah ba su kai ayi mata kishiya ba. Baki buɗe daddy,ke kallon Mami rai a ɓace Daddy ya kalli Aydah da Abba yace su tashi su wuce gidansu ya sallamesu.Mami ta kalli Daddy cikin tsakiyar ido "babu fa inda yarinya ta zata je dashi kawai ya rubuta takardar saki ya bata.!"Aydah ta mike tsaye ta nufi kofa ko gabanta bata gani da nufi tabi bayan AB Mami ta wani fisgota tana faɗin "idan kika yadda kika bisa ki dauka bakida wata uwa a duniya Zulaiha na yadda ke shashasha ce kuma wawuya ina nemar maki hakkin ki shine zaki tozartani agabansa dan uwarki.!"hawaye na zuba a idon Aydah cikin rawar murya take faɗin "Mami zan bi mijina Allah ya ba shi damar ya auri macce ba daya ba ba biyu ba har huɗu kan me za'a hanasa?"zan bi mijina mami Allah ya huci zuciyarki ranar da kika huce zan dawo."ta faɗa wani kuka mai karya zuciya na kwace mata ta riga Abba ficewa daga Parlor, murmushi kurum Daddy yayi ya dauke kansa. A mugun fusace Mami ta fice daga parlor na Daddy sai lokacin ma ta tuna da Sadiya gabanta na wani irin bugawa,ta nufi ɗakinta da sauri tana turawa ta ji sa a rufe ta shiga bugun kofar tana kiran sunanta,a lokacin Sadiya tana zube akan bed tana wani irin kuka mai sosa zuciya da ruhi gashinta ta rike taja da dukkan karfinta tana sakin wani irin ihu mai wani irin razanarwa ga jikinta dake wani irin rawa.so take kawai ta sha abun da zai kawar mata da hankalinta ,tana son ta jita cikin wata duniya ba irin wannan ba duk kalar bugun kofar da Mami keyi da irin magiyar da take yiwa Sadiya ta buɗe kofar dakinta ta yi biris da Mami. Jikin motarsa ya sameta ta kifa kanta jikin motar tana wani irin kuka kamar zata shede wani irin zafi take jin zuciyarta na yi mata da wani irin nauyi da kanta yayi mata,saboda zai auri Rumaisa shiyasa yake kakkauce mata yana wulaƙanta ta saboda rumaisa tana da abubuwan da zata basa ita kuma bata dasu ita ma macce ce lokaci zai zo da zata yi girman da yake bukata meyasa ba zai jira ba meyesa yayanta zai bari wata macce ta shiga tsakanins ,har suka isa gida kuka take kamar ranta zai fita shi dai ko kallonta bai yi ba yana gama parking ta fice daga motar da gudu da ido ya bita yana ɗan tabe bakinsa jin yayi mata ba zai iya shiga gidan ba sake ficewa daga gidan yayi bashi ya dawo ba sai wuraren karfe goma ,har lokacin kuma Huwaila tana gidan koda Aydah na asibiti,tsoron Mami ya hanata zuwa ga kuma Abba da yabi ya canja lokaci ɗaya,tana shiga cikin parlor ta saki wani irin ihu ta zube akasa ta shiga mirgina tamkar me cutar jinnu da gudu Huwaila ta fito daga ɗakinta ta nufi Aydah tana tambayarta menene."da sauri ta faɗa jikin Huwaila ta riketa gagam jikinta na wani irin rawa take faɗin."ki tadani daga wannan mummunan mafarkin aunty Huwaila ki tadani kice Aydah mafarki ne ba gaskiya bane."dan Allah Huwaila kice yayanmu kar ya auri wannan Rumaisar na yadda ya auri duk wacce yake so amman banda rumaisa bana sonta na tsaneta ta karashe maganar cikin gunjin kuka, haka Huwaila taja Aydah har ɗakinta tana famar rarrashinta Amman kamar dada tunzurata take yi,Huwaila ta rasa yadda zata yi da ita ta samu dakyar tabar kukan sai dai har lokacin tana zube ajikin Huwaila tana kuka mai sosai rai tana faɗin. Huwaila ta roƙar mata yayanta kar ya auri Rumaisa sun fi awa biyu a haka ana abu ɗaya banda addu'a babu abun da Huwaila ke tofawa mata da haka ta samu ta natsu tayi bacci kallo ɗaya za kayi mata kasan baccin wahala take yi, Huwaila tayi tagumi tana ta kallon innocent face ɗin Aydah. #Love sory2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/7, 10:17 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 058. Washegari da Zazzafan zazzaɓi Aydah ta tashi dashi gaba ɗaya ciwonta ya dawo sabo ko sau ɗaya AB bai neme ta ba, sabgogin gabansa kawai ya saka a gaba Huwaila kaɗai ce ke dawainiya da ita da gashi Aydah taƙi ci komai ta kunduddune kanta cikin duvet tana kuka, ba kalar lallaɓa ta da Huwaila bata yi ba. Amman taƙi ta saurarareta abu ɗaya take ta faɗa tana nanata wa bataso yayanta ya aure Rumaisa, wanda tuni Huwaila ta fahimceta kishi ne ke damunta, gudun kada mummunan abu ya faru da 'yar mutane yasa Huwaila ta danne duk wani tsoronta ta haura sama falon AB dake sama ta nufa gabanta yana dukan tara-tara ta kai hannunta tayi knocking ƙofar tana jin muryarsa yana waya hakan yasa ta ɗan dakata da knocking ɗin har sai da ya kammala wayar ɗin kana ta sake buga ƙofar sai gashi ya zo ya buɗe yana gani ita ce ya ɓata fuska "ya aka yi ne Huwaila? Sai da Huwaila ta ɗan runsuna tare da marairaice murya ta dawo kalar tausayi, kamin ta ce "Dan girman Allah yayanmu Dan darajar soyayyarka da Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallam! Ka zo ka duba yarinya nan wallahi-azim tana cikin mummunan yanayi tun jiya take tana kuka yanzu ma ta wayi gari tana cigaba da kuka nan jikinta ya yi bala'in zafi taƙi taci komai sunanka kurum take ambata. Bai yi gigi katse Huwaila ba har sai da ta kai ƙarshen zancenta, kana ya rausayar da kai ba don haɗa shi da Allah da Manzonsa da tayi ba da ba abun da zai kai shi wurin Aydah, wata kalar tsanarta yake ji tana huda kasusuwan jikinsa tana bin jini da ɓargon sa, sai da ya furzar da iska daga bakinsa kamin ya ce da Huwaila ta tafi idan ya yi wanka zai shigo ya duba ta. Huwaila ta kara runsunawa tayi mishi godiya kana ta juya, kitchen ta wuce ta dafa wa Aydah noodles koda AB ya fito ya cilasta mata ko ita ne ta ci. After some minutes Huwaila ta ji footsteps ɗinsa yana saukowa ƙasa, ga kuma Ƙamshin fitinannen turarensa da ya gama cika sassan gidan. Da sauri ta fito daga kitchen tana gani ya nufi ƙofar fita tayi sauri tuna masa da Aydah ya juyo yana mata wani irin kallo, da sauri ta sadda kanta ƙasa, batareda da yace komai ba ya sake haurawa sama direct ɗakin Aydah ya nufo duk da yana ji yadda zuciyarsa ke masa wani irin dokawa da ƙarfi, ga ƙunci da takaicin Aydah ɗin dake ƙara lulluɓe shi. Cike da ƙarfin hali ya tura ƙofa ɗin kakkarin amanta ya ji a banɗaki tsintar kansa ya yi da nufar bathroom ɗin da saurinsa tana zube akan tiles ta dafe cikinta da dukkan hannayenta, wani irin kumfa ke fita daga cikinta a dalili babu komai acikin nata da sassarfa ya isa wurinta ba ƙaramin namijin ƙoƙari ya yi ba tare da danne abun da yake ji ya ɗago ta Aydah tana shaƙar ƙamshin turarensa ta saki kuka irin mai cin zuciya ɗinan ta rirriƙe shi tana nuna masa ƙirjinta so take tayi magana amman ta kasa, saboda wani irin nauyi da ƙirjin nata ya yi tausayinta ne ya yi masa dirar makiya duk da wani ɓangare na zuciyarsa yana jin haushi da tsanarta kasancewarsa mutum mai tsananin tausayi, sai ya ji duk ta karya masa zuciya rigar baccin jikinta ya fara cire mata ta dawo daga ita sai pant saboda duk ta jiƙa rigar bai damu da nakedness ɗinta ba ya fito daga banɗaki dauke da ita ya shimfiɗe ta akan gado, ta sauri Aydah ta riƙe masa hannu tana fizgar numfashi cikin harɗewa harshe ta furta "Yayanmu mutuwa zan yi ƙirjina ciwo yake min. Ƙaramin tsaki marar sauti ya ja har ya juya da zimmar yai tafiyarsa sai kuma ji ba zai iya tafiya yabarta a haka ba, ya dawo ya zauna kusa da ita ya kai hannayensa ya jawo ta zuwa jikinsa har zuwa lokaci babu kaya a jikinta zafin da ya ji jikin nata ya yi gashi sai rawar sanyi take yi yasa shi sakata a ƙirjinsa Aydah tana jin kanta a jikinsa tasaka hannayenta ta gazaye shi tare da ƙanƙame shi like whole her life depend on him sai kawai ta ƙara fashewa da kuka cikin dushewar murya take faɗin "yayanmu ƙirjina yana min ciwo sosai zuciyata tana zafi kamar za ta kama da wuta bana ji daɗin komai ji nake tamkar rayuwata za ta fita daga gangar jikina, a duk sanda na tuna kana fushi dani za ka yi aure yayanmu hakan yana min zafi da raɗaɗi a zuciyana. Ta ƙarashe magana tana wani kalan sheɗewa tamkar numfashinta zai fice daga jikinta, hakan ya ƙara tsorata AB ya har ya iya hugging nata back 'yan matasan boobs ɗinta manne a ƙirjinsa duk da yana sanye da kaya a jikinsa hakan bai hanani shi jin tsini nipples ɗinta, a jikinsa nan da nan tsigar jikinsa ta shiga mimmiƙewa a ƙoƙarinsa na so ya cireta daga jikinsa ita kuma sai kara manne masa take a dalili dumin jikinsa da take ji a nata jiki ba ƙaramin daɗi da natsuwa hakan ya haifar mata ba. Huwaila ce ta turo ƙofa ta shigo hannunta ɗauke da tray silver wanda ta ɗora breakfast ɗin da ta yiwa Aydah idanunta suna sauka akansu tai maza ta juya bata taɓa kawowa zuciyarta za ta riske su cikin wannan yanayin ba "Huwaila dawo ki kawo mata abinci mana. AB ya faɗa cikin rawar murya tare da yakice Aydah daga jikinsa ya jawo duvet ya rufa mata, cike da matsananciyar kunya Huwaila ta dawo ta ajiye tray ɗin ta fice da sauri zuciyata cike da farin ciki, na gani AB ya sauko har wani babban al'amari yana shirin wakana tsakanin sa da Aydah har ta isa cikin kitchen tana yiwa Allah godiya. AB ya miƙa hannunsa ya dauko tray ɗin ya haɗa mata tea ya miƙa mata ta karba ya saka ta a gaba sai da ta shanye shi tass ya kuma zuba mata noodles ɗin da Huwaila ta dafa mata, ta ci kaɗan tace ta ƙoshi ya karɓi plate ɗin ya ajiye ya ce tashi ta je tayi wanka noke kafaɗa tayi tana turo baki "tashi mana ki je ki yi wanka in kika fito ki sha magani yatsine fuska tayi cikin shagwaɓe murya ta furta "banaso magani Yayanmu. Mugun kallo da watsa mata yasa ta sauri shigewa bathroom shi kuma ya juya ya fice sai da ya fara leiƙawa kitchen ya faɗawa Huwaila taje ta gyara mata ɗaki ta kuma tabbata tasha maganinta yana fita gidansu Rumaisa ya nufo, su ƙarasa shirye-shiryen bikinsu duk abun da Rumaisa tace da AB baya musanta mata party kusan kala uku tace za a yi duk da bashi da ra'ayi ire-iren bidi'o'i nan amman haka ya biye mata yana gudu abun da zai ɓata mata shiyasa duk abun da ta tsara ya zauna koda kuwa zuciyarsa bata so. Sai misali ƙarfe 10:30pm ya dawo gida zuwa lokacin Aydah tayi bacci ya wuce ɗakinsa ya yi wanka bai bi ta kan abinci ba saboda Rumaisa ta cika masa cikinsa, kamin ya kwanta sai da ya ƙarasa wasu ayyuka da ya fara a company da bai ƙarasa su ba ya zo dasu gida. Washegari gari kamin ya fita office sai da ya fara lekawa dakin Aydah ya duba lafiyarta daidai ta fito daga wanka waist ɗinta ɗaure da towel tana fitowa tai arba dashi tsaye ya jingina bayansa ga dressing mirror ɗinta farin cikinta kasa boyuwa ya yi sai fara'a da take yi "Good morning Yayanmu! "How are you feeling today?" "A little better! Aydah ta faɗa tana wani narkewa murmushi ya yi tare da taɓe baki "shi kenan ki shirya mu je ki ga doctor wata kila sai an ƙara yi miki waɗansu allurai. Wani kalan zare idanuwa Aydah ta yi tana girgiza kanta "wallahi na ji sauki sosai Yayanmu ba sai an min wasu allurai ba. Girgiza kai kawai ya yi ya juya tare da nufar ƙofar fita daman wannan tsayuwar da ya yi a tare da ita jiki yake tamkar ana hura masa wuta ne a jikinsa, daurewa kawai yake yi Aydah ta bishi da kallo tana jin wata irin ƙaunar yayan nata ta musamman tana bin zuciyarta. Tun daga sanda Aydah tasan zance auren AB da Rumaisa ta bi ta tsangwami kanta da yawan tunani duk ta bi ta kare kamar kuɗin guzuri daman ga jikin nata sai a hankali. Ta bangaren Sadiya ita ma kamar za ta yi hauka takanas ta shirya ta je har office ɗin AB ta same shi tana mishi kuka tagumi kurum ya yi tare da zuba mata ido sai da tayi kukanta mai isarta ta share hawayenta "Yanzu yayanmu duk irin ƙaunar da nake maka kana nufi za ta, tashi a banza ne? "To miye amfaninta ne Sadiya? Sanin kanki ne koda ban aure Aydah ba Sadiya da matuƙar wahala mu sake kasancewar a karkashin inuwar aure. "Wai me kake nufi ne yayanmu soyayyar tawa ce bata gamsar da kai ba ko ban kai matsayin da zaka soni ba?" "Ba ko ɗaya kawai dai ita zuciya ba a mata dole tun farko zuciyata da wacce take so Rumaisa ita kadai ce mace da na tsara rayuwata da ita daga kanta bana tunani zuciyata za ta iya karbar wata mace. "Wallahi-azim Abba ba ka isa ba ko sama da ƙasa za su haɗe sai na mallake ka walau ta saukaƙkiyar hanya ko kuma akasin ta daga Rumaisa har wannan kwaila sai na fincike su ta karfin tsiya daga rayuwarka, don ni kaɗai Halimatus-Sadiya aka halicci ka idan har ba za ka zama nawa ni kaɗai ba na rantse da Ubangiji sammai bakwai ba wata 'ya mace da zan bari ta rabe ka, cikin sauki wannan alƙawarina ne. Sadiya ta faɗa a mugun fusace tana mai miƙewa tsaye tana dukan desk ɗinsa, shi ma Abban miƙewa ya yi saboda ta fara kai shi makura, ga baki ɗaya ta bi ta gallazawa rayuwarsa haka take kiran wayarsa dare da rana sam ba ruwanta da duba lokaci, ta zarar abin ya motsa mata numbernsa kawai za tayi dialling wani lokaci yana tsakiyar bacci kiranta ne zai tada shi wasu lokuta yana aiki, shi bai taɓa gani mace marar class da kamun kai irin Sadiya Bashir ba, har mamaki yake yi uwa ɗaya uba ɗaya ne ya basu tarbiyya a wasu lokuta kuma sai ya yi mata uzuri a dalili fahimtar da ya yi tana tu'anmali da miyagun kwayoyi wanda yake gani har da taimakon su wajen yaye mata kunyarta, ta 'ya mace. "Sadiya tashi maza ki fice min daga office na fahimci kwayoyi da kike sha sun fara taɓa miki ƙwaƙwalwa. "Yes! Abba ina sha kwayoyi, kasani sonka da ƙaunarka sune silar jefa ni cikin wannan mummunan hali, idai akanka ne yayanmu bana ji bana gani na shirya tsaf na ƙara jefa kaina acikin hali da yafi shan kwayoyi da nake yi muni wallahi ko rai zan iya dauka akanka. Tsaye kawai AB ya yi yana kallon Sadiya yadda take ta faɗa munana maganganu, bai yi mamaki ba saboda shi ya dauketa ne ya jefa a layin marasa cikakken hankali. "Idan kin fasa ɗaukar rai akaina Sadiya Allah ya tsine miki, so nake ki ɗauki rai ɗin shashasha banza mahaukaciyar wofi dakikakiya, 'yar ƙwaya kawai wacce batasan inda yake mata ciwo ba. "Ni, ni yaya Abba ni Sadiya kake jifa da wannan muggan maganganu?" "Ke ɗin har wata tsiya ce da ba za a jefa ki da muggan maganganu ba? Ke bari ki ji ki daina gani ina daga miki ƙafa ina lallaɓaki ki ɗauke ni just for granted, duk lokacin da kika sha ƙwayar ki ta birkita miki tunani ki zo ki baza min hauka, to daga yau ba zan sake lamunta da wannan iskanci ba wuce ga hanya nan ki fita min daga office. Wani zazzafan numfashi Sadiya ta sauke hawaye masu zafin gaske suna silalo mata akan kumatunta, sai da ta ƙare masa kallo from head to toe kamin ta wani girgiza kai hawaye suna watse akan fuskarta "Kada ka yi tunani waɗannan maganganu naka za su yi tasiri akaina na haƙura da kai wallahi ko dar ban ji ba asalima sun daɗa ƙara min kwarin gwiwa, sai na sake zama matarka Yayanmu a karo na biyu ko kana so ko baka so we'll surely get back together saboda zallan ƙiyayya da kake min sai ka tanadin wuƙa da za ka dabamin ko ka yanka ni a daren farkon mu kamar dai yadda nai maka a wancan karo. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/7, 10:18 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 059. (MASARAUTAR KUDU) Abu kamar wasa masu iya magana suka ce ƙaramar magana ta zama babba, domin kuwa ta tabbata Ciroma shi ne zaɓaɓɓen sabon sarkin kudu, lokaci da wannan magana ta kai kunnen Kilishi yanke jiki tayi ta faɗi ta riga ta ƙwallafa ranta, akan Ahmadu ne zai zama sabon sarki duk wani burinta akan Ahmadu yake, sai gashi Ciroma ya yi mata shigar sauri lokacin da wannan labarin ya riske mai babban ɗaki ko kaɗan hakan bai mata daɗi ba domin ita ma burinta ace Aliyu ne zai hau karagar mulkin kudu shi kansa Aliyu yaso ace Ahmadu ne ya zama sarki ba Ciroma ba. A dalilin mugun halin Ciroma da ya gama sani da wahala ya yiwa talakawa adalci. Sai dai ba yadda suka iya saboda manyan fada ne suka zaɓe shi. Aliyu na Uku bai baro masarauta ba har sai da aka saka date ɗin nadin su a wannan karo bai nuna ƙin amincewarsa ba, fahimtar da ya yi burin mahaifiyarsa kenan na gani ya karɓi sarauta. Koda ya koma Lagos kwana sa uku a ya wuce Germany akan wani business trip. KIM'S AUTOMOBILE INDUSTRY LAGOS Anaal zaune a office ɗinta hannunta riƙe da wayarta picture ɗin AB take kallo batasan yaushe zuciyarta ta kamu da matsananciyar soyayyarsa ba, tana ji a yanzu ya zama wani bangare na jikinta, soyayyarsa tayi mata wani kalan kamu da ba za ta iya haƙura dashi ba. Shi ne namiji na farko da zuciyarta ta fara so gashi bai masan tana yi ba iyakacinsa da ita abun da ya shafi business ɗinsu duk da tana da masaniyar bai daɗe da yin aure ba, sai take gani shi ɗin mijin mace huɗu ne za ta iya samun gurbi a zuciyarsa. Number ɗinsa ta yi dialling tana dab da tsinkewa ya yi picking muryarsa kaɗai da Anaal ta ji a dodon kunnenta sai da ta saki ƙarfaffiyar ajiyar zuciya ta ji wata irin natsuwa tana saukar mata cikin taushin muryarsa yai mata sallama, sai dai wani irin zullumi na rashin sani me za ta ce dashi ya lulluɓe ta "Hello mss Anaal kina ji na kuwa? Da sauri Anaal ta katse kiran tana danne sautin da zuciyarta yake, tana sauke wahalallen numfashi a tunaninta AB zai kirata sai daga sabanin tunanin nata, don kuwa bai kira ta ɗin ba ga zuciyarta sai azalzalarta da son sake jin muryarsa tayi nisa a tunaninsa har bata ji sanda Zaheed ya turo ƙofar office ɗin nata ya shigo yana gani yadda ta kurawa wayarta ido cikin sanɗa ya qaraso gabda ita ya fizge wayar hakan yasa ta zubura ta miƙe tsaye Zaheed ya tintsire da dariya yana mai kai idanunsa akan screen ɗin wayarta, picture ɗin wanda yaga tana kallo yasa shi ɗagowa da sauri ya yada ganinsa akanta cikin sauri ta kauda fuska "Sis kar dai ki cemin you're in love with this guy?" Kasa bashi amsa Anaal tayi sai kawai ta nufi ɗaya daga cikin cushion ɗin dake cikin office ɗin nata, ta zauna tare da tallaɓe kumatunta da hannayenta biyu. Zaheed ya tako ya zauna kusa da ita sai da ya kare mata kallo kamin ya sake maimaita mata tambayarsa da farko "I don't know. "Ban gane ba kisani ba me hakan yake nufi Anaal?" "Zaheed koda ina sonshi ba wani amfani acikin soyayyar da nake masa gara kawai nayi kokari yakice shi daga raina. "Hey! Don't say that idan har da gaske kina sonshi you have to fight for his love, ba abun da kika rasa na cikakkiyar mace firstly you're an educated both boko da ilimin addini Allah ya wadata ki dasu also you're a very beautiful girl kowanne namiji yana da burin mallakar mace irinki saboda haka kada ki tsaya wasa just fight to get his love. "Ba za ka gane ba Zaheed he's married yana da mata ko wata ɗaya bai yi ba da aure. "So what don yana da aure kin manta da Addini ya hore masa da ya aure mace har guda huɗu?" "Ban manta ba Zaheed sai dai bansan nayi abun da zai taɓa kima da darajata, ta 'ya mace. "Anaal ni kaina ba zan so ki yi abun da zai taɓa mutuncinki ba amman zan so ki sami namiji da kike so, dan ki faɗamasa kina sonshi ba zunubi bane dan Allah kada ki cuce kanki. "Okay! Na ji zan yi tunani akai idan naga dacewar na gayamasa zan faɗamasa ɗin. "Shi kenan ki yi tunani mai kyau kada ki kwari kanki ki dawo daga baya kina danasani. Murmushi kurum Anaal tayi tare da amsar wayarta daga hannunsa. *********** Wata kalar tsawa AB ya dakawa Sadiya har ga Allah haƙuri sa ya fara karewa ta fara kai shi makura, cikin kakkausar murya ya ce da ita "Sadiya wannan shi ne kashedi na dake na ƙarshe idan ba ki ficemin daga office ba wallahil-azim zan yi miki wulaƙanci da ba a taɓa yi miki kwatakwacinsa ba. "Zan fita Yayanmu ba wai dan kace za ka wulakanta ni ba kawai dai zan fita ne a bisa ra'ayin kaina, duk masifa da wulaƙanci da za ka yi ba zai dame ni ba ballantana ya hana min cimma burina akanka. Tana ƙarasa magana ta dauki handbag ɗinta a fusace ta fice ta buɗe kofa tare da rufu ta da ƙarfi, AB ya ɗauki telephone ya kira secretary ɗinsa Skyler ya bata umarnin daga yanzu ko Sadiya ta zo karta sake ta barta ta shigo masa office. Sadiya tana baro office ɗin AB tayo gidansu Rumaisa har cikin compound ɗin gidan tayi parking motarta ta kashe motar tare da fitowa ta nufi entrance ɗin gidan kanta tsaye ta tura ƙofar main parlor mai aikin gidan ta fara cin karo da ita cikin zuciyarta tana bugawa da kalli mai aikin tare da tambayarta mutane gidan "Ammi ta fita sai in aunty Rumaisa za a kira miki. Kyakkyawar ajiyar zuciya Sadiya tayi tare da faɗin a kira mata Rumaisa ɗin daman gunta ta zo, 'yar aiki har ta fara haura mattakalar bene Sadiya ta dakatar da ita ta hanyar faɗin ta nuna mata ɗakin nata kawai ta same ta acan, a tunani mai aiki Sadiya tana ɗaya daga cikin ƙawayen Rumaisa ne saboda kusan kullum sai ƙawayen nata sun zo suna tayata shirye-shiryen bikinta da ya karato don haka bata kawo komai aranta ba ta wuce gaba Sadiya ta bi ta a baya suna zuwa daidai ƙofar shiga ɗakin Sadiya ta dakatar da ita "Komawarki bakin aikinki zan ƙarasa da kaina. Batareda da mai aikin tace komai ba ta juya abinta, kai tsaye Sadiya ta tura ƙofar ta shiga ba ko neman izni balle sallama daidai Rumaisa ta fito daga wanka tana daure da ƙaramin towel wanda iyakancinsa cinyoyinta, hannunta riƙe da hand towel tana goge gefen wuyanta, jin an turo ƙofar ɗakinta batareda da an yi knocking ba yasata yada ganinta akan ƙofar wacce ta gani ta shigo ce ta haifar mata da faduwa gaba "Sadiya!! Ta kira sunanta da madaukakin mamaki shimfiɗe akan fuskarta. Cike da izza da zallan izgilanci Sadiya ta tako ta iso gaban Rumaisa ta tsaya ta shiga kare mata kallo from head to toe, sai kuma ta ja dogon tsaki "Sadiya lafiya za ka fadomin ɗaki babu neman izinina tsabar wulaƙanci da rainin wayau ki dube ni sama da ƙasa ki ka min tsaki kanki ɗaya kuwa kodai kin fara shaye-shaye ne?" Cikin tafarfasar zuciya Sadiya ta jefa idanunta cikin ƙwayar idon Rumaisa, ranta yana mata ƙuna wato kowa ma ya gama sani tana tu'ammali da miyagun kwayoyi wato yanzu kowa ya buɗe bakinsa zai mata magana sai ya gorata mata saboda haka ta ji ranta na ɓaci zuciyata ta harzuƙa "Zuwa nayi na kashe miki gargaɗi da kakkausar murya Rumaisa kada soyayyar yayanmu ta rufe miki ido ki kasa gane irin masifar da kike kokarin jefa kanki. Rumaisa kisani bakin rijiya fa ba wurin wasan makaho bane mijina yafi karfin kucakar mace irinki kada ki sake ki aure mijina idan har kika bari ƙaddarar aure ta shiga tsakaninku na rantse wanda rayuwata take hannunsa sai na gana miki azaba sai na mayar da rayuwarki abin kwatancce. Abba nawa ne ni kaɗai duk 'yar da ta kuskura ta rabe shi sai na datse mata farin cikinta sai na mayar da duniyarta baƙa wulik! Rumaisa ta ɗage girar ido tare da rungume hannuwanta a ƙirjinta, tana kallon bakin Sadiya yadda take da irin wannan ƙarfin hali na shigowa cikin gidansu, kuma har cikin ɗakinta sannan kuma tana mata gargadi ta rabuda AB wanda dukka kwanaki ƙalilan ya rage musu, su mallaki juna ta hanyar aure lallai kuwa Sadiya bata da hankali cikakkiyar mahaukaciya ce in ma banda hauka ita da AB yake auren ƙanwarta uwa ɗaya uba ɗaya meye gamin ta da zuwa yi mata kashedi akansa sai dai Aydah ita da take matarsa ba dai ita ba da ta gama zama tarihi acikin rayuwarsa. Sai kawai abin yabawa Rumaisa dariya ta saukar da hannayenta daga ƙirjinta tayi flagging da hand towel ɗin dake riƙe da hannun nata, ta yiwa Sadiya kaskantatcen kallo "Ke wama kike da suna?oh Sadiya ko ke har kin isa ki shigo mana gida ki karanta min bayan littafi sannan kuma ki yi tunani karatun naki zai girgiza ni?" Idan haka yaudararriyar zuciyarki ta gayamiki Sadiya tayi kuskure, Abba Bashir ya yi miki nisan da har ki kwanta dama ba za ki taba samun sa ai abin da ba ki sani ba Sadiya opportunity comes once kin ri ga da ki yi wasa da damarki Abba Bashir ya subuce miki, yadda kika bar nonon uwarki haka zalika kika bar Abba. Wani irin zazzafan numfashi Sadiya take saukewa Rumaisa tana dasa aya tayi kukan kure ta cafke wuyanta, nan take suka kaure da ƙazamin dambe ɗan towel ɗin jikin Rumaisa ya zame ya faɗi ƙasa hakan ne ya bawa Sadiya damar cafkar boobs ɗin Rumaisa ta ja su da bala'in ƙarfi tamkar dai yadda ake jan hanjin akuya wani kalan ihu Rumaisa ta ƙwalla ji take tamkar ana zare mata rai Sadiya bata sakar mata boobs ɗin nata ba sai ƙara murɗe su take yi, a haka ta ja ta zuwa ga dressing mirror ta buga kanta ga mirror ɗin nan take ya tarwatse jini ya yi inda yake so yayin da numfashin Rumaisa ya tsaya cak! Sadiya ta sake ta ta zube ƙasa hakan bai sa Sadiya ta kyaleta bin ta tayi ta haye ruwan cikinta tayi ta dukanta ga Rumaisa yashe tsirara haihuwar uwarta, buri da fatan Sadiya Rumaisa ta mutu, cikin sauri ta fito daga ɗakin har ta sauko downstairs parlor ta fice bata haɗu da mai aiki ba. Zuciyata ba ko dar balle alamar tsorata ta ja motarta maigadi ya buɗe mata gate ta fice abinta. Daga gidansu Rumaisa tayo gida kai tsaye ɗakin Mami ta wuce ta tarar da Mami tsaye a jikin wardrobe ɗinta tana shirya kayanta da aka kawo daga wurin wanki, zubewa tayi akan gadon Mami tana wani sauke numfashi ɗaɗɗaya da gaske ba za ta lamunci ta rasa AB ba domin kuwa ya zama mata tamkar rayuwata ne tana sonsa kwatankwacin Irin so da komai za ta iya aikatawa dan kawai ta same shi wannan abun da ta yiwa Rumaisa somin taɓi ne wanda tanadarwa da Aydah sai yafi na Rumaisa madawaki muni sai ta fincike su da ƙarfin tsiya daga rayuwar Abba Bashir, guntun tsaki Mami ta ja tare da rufe wardrobe ɗin ta ƙaraso gefen Sadiya ta zauna "ke lafiya kika shigo min kina wannan irin sauke numfashi tamkar wacce ta yi tseren gudun gasar Olympic ta zo ta ɗaya?" Sadiya bata iya furta uffan ba jin maganganu Mami take yi suna amsa kuwa acikin kwayar kanta, ta runtse idanuwanta da karfi har Mami na iya gani yanda ƙirjinta ke bugawa fat fat "Sadiya ki yi min magana mana ko bakida lafiya ne na kira doctor ya zo ya duba ki ko kuma ki tashi mu tafi asibiti. Still Sadiya bata ce komai ba hakan ya hasala Mami ta rufe ta da faɗa, cikin mugun yanayi Sadiya ta buɗe idanunta da suka yi jajur ta kalle Mami dasu kamin cikin rawar murya ta furta "Mami ina sonsa ina azabar sonsa idan har zan rasa shi to kuwa babu wata 'ya mace da za ta same shi na kashe Rumaisa madawaki saura Aydah dukka su biyu ba zan barsu da rai ba. "Innalillahi wa'inna illahim raji'um! Me kike faɗa ne Sadiya kisa fa na ji kin faɗa? Anya kuwa Sadiya ba ki shawo kwayar da tafi ƙarfin ƙwaƙwalwarki ba?" Aydah fa ƙanwarki ce ta jini kike faɗar za ki kasheta saboda wani ƙato ɗan shegiya wanda bai da cikakken asali. "Mami ko daga sama Yayanmu ya fado ina sonsa a haka shi ne duniya ta kisa ita ce hanyar da kaɗai zai gamsar da Yayanmu irin matsanancin so da nake masa. Wawan duka Mami ta kai mata a baki ta shiga zuba mata masifa a rikice Mami ta fizge hannunta ta miƙar da ita tsaye hijab Mami ta dauko kasa saka shi tayi, ta ja hannun Sadiya suka fice da sauri parking lot Mami ta nufa da ita ta buɗe front seat ta tura ta kana ta maida murfi ta rufe ta zagaya ta zauna a mazaunin direba ta ja mota Balmo maigadi ya buɗe musu gate "Mami ina za ki kaini ne naga sai sharara gudu kike? "Gidan ubanki zan kai ki Sadiya shegiyar yarinya wacce ke shirin dauko min bala'i da masifa da suka fi ƙarfina ina zaman zamana kin je ki dauko mana masifa kina tsammani za ki kashe Rumaisa a banza ne wawuyar banza mahaukaciya. Sadiya ta dafe goshinta sai lokaci ƙwaƙwalwata ta fara aiki daidai tabbas idan Rumaisa ta mutu kashinta ya bushe ita ma dole a kashe ta, domin ita ma Rumaisa tana da gata iyayenta ba za su bar kisanta ya je a banza ba. Nan da nan Sadiya ta fara nadaman abun da ta aikata ta fashe da kuka "Na shiga uku Mami. "Baki shiga ba tukuna dai tun da ke kin zama daƙiƙƙiya Kwata-kwata bakya tunani da ƙwaƙwalwarki gashinan akan wani shege za ki jefa mu a masifa ke kuma ki kare rayuwarki a gidan kaso. Jin abun da Mami take faɗa yasa Sadiya ta karawa kukanta sauti Mami tana tafe tana faɗa tare da zagin Sadiya. Unguwar su aunty Safeena suka nufa daidai gate ɗin gidan Mami ta tsaya tayi horn maigadi ya buɗe musu gate sai dab da entrance ɗin gidan tayi parking. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/7, 10:22 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 060. Mami hankali tashe ta faɗa parlor Aunty Safeena ko sallama ba tayi ba hankalinta ga baki ɗaya baya jikinta tana riƙe da hannun Sadiya,Jamal kaɗai ne zaune a parlorn da waya a hannunsa yana dannawa daga Mami har Sadiya binsu kurum yake da kallo "Ina Safeena?"Mami ta faɗa tana kallon Jamal da shima kallonsu yake "Tana sama meya faru Mami?"ya faɗa yana kallon Sadiya da hawayen idanunta suka kasa tsayawa ga jikinta yadda yake rawa bata manta irin azabar na farko da tasha a cell ba. Zama Mami tayi ɗaya daga cikin kujerun dake zagaye da parlor Mami na sauke numfashi banda bugawa babu abun da zuciyar Mami keyi. "Kira min Safeena Jamal,ban iya ƙarasawa sama nan."Mami ta faɗa da wani yanayi a muryarta, ba jimawa Jamal ya sauko tareda mahaifiyarsa,Aunty Safeena ta nufi Mami da sauri tana faɗin."Lafiya yaya mariya?"Aunty Safeena ta faɗa tana mayar da hankalinta kan Sadiya da tayi wani irin zuru-zuru ina cikin tashin hankali Safeena, wallahi Sadiya so take taja min masifa ina zaman -zamana na. Gaban Aunty Safeena na faduwa ta kalli Sadiya a rude take faɗin."me kuma kika yi a wannan karon?"Shiru Sadiya tayi babu magana nan Mami ta shiga zayyanawa aunty Safeena irin aika-aikar da Sadiyar tayi Jagwaf aunty Safeena ta zauna kan kujera tana salati, jin take kamar ta tashi ta rufe Sadiya da shegen duka."a sanyaye aunty Safeena ta kalli Mami,tana faɗin."menene abun yi yaya?"na tabbatar idan iyayen yarinyar nan suka gano Bazasu kyale Sadiya haka ba kar ma su kyaleta a daketa kuma a hanata kuka."Jamal ya faɗa a tsawace Ya tsani Abba Bashir fiye da yadda ya tsani mutuwarsa tun lokacin da ya dawo hutu gida ya samu wai Aydah ta auresa yarinyar da ya dade da ƙwallafa wa zuciyarsa da gangar jikinsa ita yarinyar da yake mafarkin ta zama mallakinsa a lokacin da wannan labari ya riske shi sai da ya kwanta gadon asibiti ba ƙaramin damuwa ya shiga ba. Duk da haka har yanzu bai fidda ran zai samu Aydah ba tunda mum ɗinsa tayi masa alƙawarin ai Abba zai saki Aydah ba da jimawa ba.mami kallon Jamal kawai take batareda tace komai ba , daman daga shi har Sadiya babu mai cikakken hankali kusan tsarar juna suke da Sadiyar babu mai shekara talatin acikinsu "Yanzu mu jira zuwa anjima sai ki koma gida yaya kar ki taɓa nuna kin san inda Sadiya take komai haukar da mahaifinta zai yi miki ki barta anan,daman ko giyar wake yasha ba zai yadda yazo gidan nan ba. *BELLO MADAWAKI MANSION* Raliya Madawaki ce ta fito daga ɗakin mahaifiyarsu kai tsaye ta nufi ɗakin Rumaisa tun kafin ta karasa kofar ɗakin take faɗa tana "ita fa haushinta da Rumaisa idan za'a fita tare sai an bata lokaci sosai idan za'a fita sai ta kwashe fiye da awa ɗaya tana tsaye a gaban mirror dressing tana tsara kwalliyya wannan kwaliyyar yafi komai batawa Raliya Madawaki rai.kai tsaye ta rika handling kofar ta tura kofar dakin Yanayin da ta samu yar uwar Tata aciki yasa ta saki ihu mai razanarwa da duka gidan sai da ya amsa sai ga Ammi a rude ta karaso tana tambayar Raliya menene?"tun kafin idanunta su sauka akan yar Tata cikin wani yanayi mai wuyar fassarawa.a rude Ammi ta nufi rumaisa ta wani irin dagowa zuciyarta banda dokawa babu abunda take.a haukace Raliya ta sauka kasa tana kwalawa mai aikinsu kira itama a rikice ta fito kitchen,waya shigo gidan nan waya shiga dakin Rumaisa Abida?"Raliya ta faɗa a hargitse gaban Abida na dokawa take faɗin."dazun nan wata kawarta Tazo."nan Abida ta baiwa Raliya labari kin taba ganinta ne?"dama kuma tana zuwa wurinta?"da sauri Abida ta girgiza kai ,zata kara yin magana taji mahaifiyarsu na kwala mata kira a rude ta koma sama. Cike da karfin hali Ammi ke faɗin."taimaka ki kiramin driver yanzu ya taimaka mu kaita asibiti Da sauri Raliya ta koma,fiye da awa daya likitan da ta karbi case din Rumaisa tana aikin dubata sun tsayarda jinin dake fita ta goshinta da ya tsaga ta hanyar yimata ɗinki ,sai allurar da sukayi mata har dai bata farfaɗo ba,har Alhaji Bello Madawaki ya karaso hospital din ya rufe Ammi da faɗa yana faɗin."suna ina wannan mummunar al'amari ya samu yarsa a shigo gidansa a aikatawa yarsa ta'addanci babu wanda ya sani.har daddy yabar asibitin bata farfaɗo ba haka yayi umurnin daman da ta farfaɗo a kirasa haka ya dauki alwashin koma wanene ya aikatawa Yarinyyarsa wannan ta'addancin sai ya karbi mummunan hukunci.sai wuraren karfe biyar na yamma Rumaisa ta farfaɗo a firgice ta farka tana sakin wani irin ihu marar sauti tana kiran sunan sadiya da dukkan karfinta."da sauri Raliya ta karaso gaban gadon ta rike kanwar Tata tana tambayarta wacece sadiya?"hakama Ammi da ta karaso gaban gadon da sauri cike da karfin hali rumaisa ta shiga yimasu bayanin mai ya faru Wani uban Ashar Raliya ta saki ta dauki key din mota kai tsaye ta fice daga dakin dan ko sauraran kiran da Ammi keyi mata batayi ba.itama Ammi duk ta shiga mamaki,kai tsaye dama Raliya police station ta wuce ta saka karar sadiya haka aka bata motar yan sanda ɗaya suka bi bayanta zuwa gidan Alhaji Bashir. *ALHAJI BASHIR MANTION* Daman Mami awarta ɗaya gidan kanwarta Safeena ganin babu wanda ya kirata har lokacin yasa ta koma gida tabar sadiya a gidan haka tayi mata gargadi da babbar murya akan Karta kuskura ta baro gidan Safeena sai idan ita ta nemeta kayanta na sakawa da yamma,zata saka driver ya kawo mata sa'annan Mami tabar gidan duk da hankalinta a matukar tashe yake har lokacin,tana ta addu'ar Allah yasa Rumaisa ta rayu kodan rayuwar yarta ya tsira ,har ta dawo gida bata cikin natsuwarta daman koda suka bar gidan Siyama bata gidan sun shiga hidimar bikin kawarta,har wuraren karfe huɗu Mami bata da cikakkiyyar natsuwa duk lokacin da aka kirata a waya sai ziciyarta ta tsinke.har maigidanta Alhaji Bashir ya dawo daga office abinci kawai ta kai masa a bangarensa ta koma ɗakinta ta kwanta har wani sanyi taji yana lullubeta mai alamar zazzaɓi, keso kamata banda bugawa babu abun da zuciyarta keyi. Tana nan kwance sai sake-sake take yi duk bai fi minti goma da kwanciyarta,taji jiniyar motar yan sanda tare da bugun gate ɗin da ake masu tamkar za'a karya kofar,da sauri ta tashi tsaye ta sakawa kofarta key da mamaki Alhaji Bashir ya nufi cikin compound ɗinsa ya yiwa Balmo Umarnin ya buɗe gate,duk a tsorace Balmo yake jin jiniyar motar yan sanda ya rasa ma ta hanyar da ake bude kofar a fusace Daddy ya karasa ya buɗe gate ɗin Raliya yaci karo da ita da police guda biyu,wata yar sanda macce ce tacewa Alhaji Bashir wajen 'yarsa Sadiya suka zo wacce tayi kokarin kisan kai, innalillah wainnah ilaihir Raji'um! Daddy ya rika maimaita wa cikin girgiza kai da cike da tashin hankali yake faɗin."bayin Allah kodai kunyi batan kai ne?"kuna nufin Sadiya ta?" Daddy ya faɗa cikin wani irin raunin murya,Raliya ta karaso gabansa tana faɗin."Bari dai nayi maka gwari-gwari ta yanda za ka gane nan take Raliya ta zayyana masa abun da Sadiya tayi har cikin gidansu yanzu haka Rumaisa na kwance a gadon asibiti dan 'yan sanda basu zo nan ba sai da suka samu kwakkwarar shaida, Daddy ya daga kai yana kallon Police ɗin dake tsaye har lokacin yace su biyosa, binsa suka yi tun cikin parlor Daddy ya rika kwallawa Mami kira kamar zai tada gidan duka,har ya haura sama yan sanda suka tsaya cikin parlor,Mami tana jin Daddy na kwalla mata kira yana dukan kofar tayi shiru sai da ya daga murya yayi rantsuwa akan idan bata fito ta buɗe masa kofa ba a bakin aurenta,haka Mami tazo ta buɗe masa kofa kallo ɗaya yayi mata yaga alamun rashin gaskiya a bayyane akan fuskarta tunda ya dawo yake kula da yanayinta."ina Sadiya take? "Tana makaranta. Mami ta faɗa cike da dakiya,ki fito da Sadiya ko nayi masu Umarnin ke su tafi dake daman kuma idan kika sake suka tafi dake ke da dawowa gidan nan har abada.!"Daddy ya karasa maganar cikin ɓacin rai da kakkausar murya,a rude Mami ke faɗin "Amman kasan haka kawai Sadiya ba zata farma yarinya nan ba. "Dauko mayafinki. Daddy ya faɗa mata yana kallon cikin tsakiyar idonta abun da ya take hanga acikin idanun Daddy,a wannan lokacin tasan tsaf yake da tsinka igiyar aurensu babu shiri ta dauki hijab ɗinta na sallah tabi bayansa ,Mami tana fitowa ko kallon Police ɗin dake tsaye cikin parlornta bata yi ba har lokacin suka nufi kofa Daddy,ya kallesu yana faɗin."mu je da mota ta nuna maku inda take da haka suka bi bayan Daddy,babu mai magana acikin su har suka karasa kofar gidan Aunty Safeena har suka tsayar da motocin su fuskar Mami a murtuƙe take "Ki shiga ki fito da ita. Daddy ya faɗa sounding so very command!"ficewa Mami tayi daga motar a kitchen ta samu Aunty Safeena suna haɗa abincin dare ita da yan aiki maleeka tazo ta rike Mami tana mata sannu da zuwa,jeki ki kira min momynki maleeka da gudu ta nufi kitchen tana kwallawa mum ɗinta kira babu jimawa ta fito ganin Mami yasa Zuciyar Aunty Safeena wani irin dokawa."kafin ki zauna ki kiramin Sadiya yanzu ta fito mu tafi."cike da tsoro Aunty Safeena ke faɗin."ta je ina yaya?"cikin dakewa Mami ke faɗin "Police na jiranmu a waje. Sallati Aunty Safeena ta rikayi da wani irin yanayi ta nufi ɗakinta ta samu Sadiya kwance sai dai ba bacci take ba Ta mata umarnin ta dauko mayafi Ita ma Sadiya cike da tsoro ta fito parlor ganin mami kai tsaye Mami ta riƙa hannun Sadiya suka nufi kofa a haka Aunty Safeena tabi bayansu tana kokarin dakar da Mami dabata ma tsaya sauraren ta ba,tsayawa tayi cak!'Aunty Safeena tana kallon Daddy da ya nufi Sadiya a hargitse mari ya shiga zuba mata hagu da dama yasa kafa yayi ball da ita yana huci sai da yan sandan suka ceci Sadiya da wata irin zuciya Daddy yake yake nuna Sadiya yana faɗin."Ashe ke babbar yar iska kika zama ban sani ba ?"Yaushe kika zama yar ta'addah?"tun da na gano har yanzu baki yi hankali ba ku je gata nan ko gidan yari za'a kaiki bazan tsorata ba,kuma har abada ba zan so ooilnuhymonhbyohnje karbo belin ki ba.idan kin zama gidan kaso ki dawo gida ki karbi hukuncin da zanyi maki bancin wani abu sadiya yau da na tsine maki Albarka."a fusace daddy ya nufi motarsa cikin zafin zuciya ya tada motar ya bade su da kura ya fisgi motar da wani irin gudu,da yasa Mami tabi motar da kallo hawayen idanunta suka kasa tsayawa,nan kuma polisawa suka saka sadiya cikin motarsa suka wuce daita ,dakyar Aunty Safeena ta saka Mami cikin gida da take wani irin kuka mai sosa rai tunda har daddy yace bazaije belin sadiya ba bazai jeba daman kuma daddy ,baya magana biyu."ina cikin tashin hankali Safeena yanzu menene abun yi? Ga Abba su Jamal baya gari,ki natsu yaya musan ta inda zamu bullowa wannan al'amari har akayi sallar magarib Mami da Safeena sun kasa samun mafita.Aunty Safeena ta numfasa tana faɗin."mafita ɗaya ta rage mana yaya kawai Abba zaki kira ki basa umarni ya je ya saka baki a saki Sadiya nasan ai ba zai ki bin umarninki ba "Idan kin san yadda na tsani koda jin sunan wannan yaron Baran tana har naji muryarsa Safeena da baki kawo wannan shawarar ba Allah ya tsare na nemi alfarma a wajensa "kin fiso ta kwana a cell kenan?"kibarta ta kwana din gobe ba zata kara ba, "yaya wannan fa ba shawara bace ni bari na kira Abban Batareda wani tunani ba ,Aunty Safeena ta kira AB ta faɗa masa tana nemansa yanzu idan babu damuwa. Yace zai zo nan da minti talatin,da haka ya sauke wayar dan acikin dangin Rumaisa babu wanda ya kira AB har lokacin hakama Daddy,bai kirasa ba kamar yadda ya faɗa cikin minti talatin ya nufi gidan Aunty Safeena a bakin gate ya aje motar da ƙafarsa ya taka zuwa kofar gidan yayi knocking ta karamar kofar maigadi ya leƙo yana ganin Abba ne ya washe baki ya buɗe masa gate yana masa sannu da zuwa Abba ya amsa yana gaishesa daman sun saba da mai gadin,kai tsaye entrance din shiga gidan ya nufa kusan cin karo sukayi da Jamal da yafito shi kuma zai shiga jada baya suka yi suka daga kai suna kallon junansu tamkar wasu zakaru. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/8, 9:24 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 061. Tsayawa suka yi suna kallon juna kamar wasu zakaru kowanne su fuskarsa tamkar an aiko masa da sakon mutuwa,haka zalika kowanne da sakon da yake tattaunawa da zuciyarsa,a bangaren AB yana tuno kalaman Jamal acikin kunnayensa yaron da ya bai wa tazarar shekaru goma, shi zai kirasa a waya yana datsa masa magana,har yake iya buɗar baki yayi masa gargaɗi gami da barazana akan Aydah har yana faɗin Aydah ta shi ce mallakinsa ce shi kaɗai ko yana so ko baya so dole ya saketa.Kallonsa AB ya cigaba da yi yana ganin shekarun da yaron da ya yi girma akan idanunsa shi ne har yayi zarrar gayamasa magana a mugun fusace Jamal,yabi ta gefensa ya wuce tamkar zai tashi sama. Murmushin gefen baki AB ya saki ya karasa cikin parlor da sallama a bakinsa, Aunty Safeena,kawai ce ta amsa masa Mami ta shiga danna wayar hannunta fuskar nan ta ta a murtuke tamkar ba'a taɓa halittar dariya ba acikin fuskarta, AB ya nemi wuri ya zauna ya gaisheda Mami da Aunty Safeena lokaci ɗaya, Wannan karon ma Aunty Safeena ce,ta amsa masa shiru ya ratsa a tsakaninsu na kusan sakan goma. Ganin da gaske mami, bazata yi magana ba yasa Aunty Safeena,ta sauke numfashi tayi gyaran murya tana sauke idonta akan AB ta kira sunansa dago kansa yayi ya mayar da hankalinsa wurin Aunty Safeena. Kasan meke faruwa kuwa da yar uwarka Abba?"a gaggauce AB yace '"wacce 'yar uwar tawa Aunty??"Aunty Safeena bata boyewa masa komai ba ta yi masa bayani "mun san Sadiya tayi kuskure ka dubi girman Allah Abba ka rufawa kanwarka asiri kar ta kwana a cell yau, duk da girman kuskure da tayi Abba bai kamata yan uwan matarka su dauki irin wannan tsatsaura hukuncin ba, kaga an kusa daura muku aure bakwa gudun bakin mutane da kuma yan jarida da kiris suke jira su dinga yaɗa labarai karya da na gaskiya cike da jimami AB ke faɗin."babu wanda ya kira ni Aunty bara na je yanzu in shaa Allah zan dawo tare da Sadiya, ba zan bari wani abu ya same ta ba. Ya ƙarasa maganar tare da mikewa tsaye Aunty tayi masa fatan sauka lafiya,a boye Mami ta rika sauke wata irin ajiyar zuciya har AB ya fice daga parlor da sassarfa. Mami ta rika bin sa da wani ɗan iskan kallo ta kalli Aunty Safeena,rai a ɓace "ke kin yarda da wannan karyar da yazo ya gilla miki yaron nan munafuki ne na karshen lissafi waya sani koda haɗin bakinsa aka kai Sadiya cell ɗin. "Ni wallahi ina mamakin irin wannan tsanar da kike nunawa Abba,yaya mariya wanda ko a mafarki ba zan yarda zaki yi masa wannan kalar tsanar ba jikina wallahi har yayi sanyi ganinsa ya karya min zuciya, daman za mu haƙura mu zubar da makaman yakin mu akan auren Abba da Aydah haka Allah ya tsara masu mu bi su da addu'a kawai. Saboda takaici Mami ko kallon Aunty Safeena,bata sake yi ba tun a hanya ya rika kiran wayar Rumaisa bata daga ba, lokacin an basu sallama tana gida ganin har lokacin bata daga ba ya kira wayar Aunty Raliya, daman kuma yana da digit ɗinta bayan ta dauka ya gaisheta da respect ta amsa yace daman yana ta kiran wayar Rumaisa bata dauka ba,Aunty Raliya tace ya kashe bara ta mika mata tana shiga ɗakin Rumaisa daidai lokacin Rumaisa ta fito daga wanka aunty Raliya ta karaso tana faɗin."ina kika jefa wayar Abba yana ta kira baki daga ba da sauri Rumaisa ta nufi wurin pillow ta dauki wayar,Aunty Raliya ta juya ta fita yana ganin kiran Rumaisa ya shigo a wayarsa ya katse ya kirata. Tana ɗagawa ya fara tambayarta tana gida yana kan hanya zai zo, ta amsa masa tana nan da haka ya sauke wayar kara gudun motar yayi cikin mintuna goma sha biyar yayi parking motarsa bakin gidansu Rumaisa ya kirata a waya ya faɗa mata yana waje yana jiranta. Cikin kwantar da murya take faɗin "Hayati ka karaso cikin gida mana sai kace wani bako bana jin dadi fa. Zaman mituna biyar yayi a parlor mai aiki ta cika gabansa da kayan motsa baki kamar koda yaushe, ƙamshin turaren da ya cika parlor yasa ya daga kai ya zubawa kofar ido tana cikin shigar alfarma doguwar rigar atamfa bubu sai mayafin da ya dace da kalar atamfar da ta ɗora daidai kan kafadarta yana hango ɗinkin dake manne a gefen goshinta,har ta karaso wurinsa bai daina kallonta ba. Ta zauna gafda shi ta zuba idananunta cikin nasa tana wani narke masa,cikin sarkewar murya yace "meya haɗaki da Sadiya Rumaisa?"jin ya kira mata sunan sadiya ya saka yanayinta ya canja lokaci ɗaya,cikin ɓacin rai ta soma basa labarin yadda Sadiya tazo har cikin gidansu har ɗakinta na bacci taso ta kasheta."!ashe da gaske wannan Sadiyar bata da hankali habeebi?"Runtse idanu AB yayi batareda ya furta kalma ko ɗaya ba bai san me zai cewa Rumaisa ba yasan sadiya ita ke da laifi bai san taya zai yi mata bayanin ta janye case ɗin ba kamar yadda su Aunty Safeena suka bukata. Idan yayi haka tamkar bai yiwa Rumaisa adalci ba,buɗe idanunsa yayi akan Rumaisa dake kallon yanayinsa nan take fuskarsa ta canja alamar bacin rai baro-baro ya bayyana akan fuskarsa.Bai san lokacin da ya riko hannayen Rumaisa duka biyu ba ya damke cikin nasa hannun,cikin sarkewar murya ya shiga rarrashinta da daddaɗan maganganu tare da bata hakuri,kamin ya kalli cikin kwayar idanunta yana faɗin "zan nemi alfarma a wurinki Rumaisa dan Allah zan samu?"Yadda yai mata magana cikin sanyin kalamai da kwantar da murya taji zuciyarta na kara narkewa da sabon sonsa,dake zagaye lungu da sako na zuciyarta samun kanta tayi da daga masa kai alamar ehhhh,ya kalli cikin tsakiyar idonta yana faɗin "Please Rumaisa ki yafewa kanwarki Sadiya,ki janye case ɗin nan a hannun yan sanda,wani irin kallo Rumaisa ta rika yi masa tana kokarin fisge hannayenta cikin nasa ya kare damke hannayen yana mannesu yana girgiza mata kai "Na sani ita ce bata da gaskiya kiyi haƙuri dan soyayyar dake tsakanin mu ki janye ba haka kawai zan barta ba zan dauki mummunan mataki akanta ki bar komai a hannuna Please. Ya faɗa yana narke mata fuska,cikin rawar murya ta shiga faɗin."kana ganin raunin da tayi min a fuska taya zanyi hidimar biki a haka.?"ta faɗa hawaye na taruwa a idonta "Ni daman tun farko bana son wannan bidi'o'i ki bar sa kawai muyi dinner ranar da za'a kai ki da kuma walima shi kenan sauran a haƙura albarka aure ake so Habibty kada mu biyewa son zuciyar mu. "Na riga na gama tsara komai Habeebi meyasa za'a fasa?"ta faɗa hawaye na ballewa cikin idanunta da sauri ya dora hannayensa akan fuskarta yana tare hawayen idanunta "nifa ke nakeso ba wani party ba baby. Da azama ta buge masa hannu jin irin sunan da taji ya kirata dashi watau sunan da yake kiran Aydah dashi ranta a jagule ta furta"karka kara kirana da wannan sunan bana so. murmushi ne ya subuce masa yasan kishi ne ya motsa kenan,ya mike tsaye still yana riƙe da hannunta yana faɗin."kije ki fadawa Ammi zamu fita sai mu je ki janye case ɗin,harara ta bisa da ita tana fincike hannunta cikin nasa tayi gaba abunta da murmushi ya bita yana shafa kansa yana jin sonta na karuwa a zuciyarsa sauƙin kanta yana ɗaya daga cikin abun da ke burgesa da ita. A fusace Aunty Raliya take duban Rumaisa take Faɗin."dan kina wawuya sai kika biyewa maganganun da ya tsara maki Ammi meke damun Rumaisa akan wannan Abba,duk tabi ta mutu akansa bataji bata ganin komai sai shi.!" Raliya Madawaki ta faɗa sounding so pissed up ,ita ma Rumaisa cikin ɓacin rai tace "alfarma fa ya zo ya nema a wurina Aunty Raliya kan meyasa ba zan yimasa ba. "ke dai wallahi kin shiga uku Rumaisa ga baki ɗaya kin haukace akan wannan yaron. Ammi ta dakawa Raliya tsawa tana faɗin."kiyi shiru dan Allah ,ba ita taji ta gani ba ki saka mata ido tun farko Daddynku bai so aka kai case ɗin police station ba keda ita kuka kafe akan ra'ayinku tunda wacce aka yiwa ta haƙura sai aje a haka,a fusace Raliya ta fice daga ɗakin da wani kallo Rumaisa ta bita tana haɗe rai ta mayar da kallonta kan mahaifiyarta da ita ma ta haɗe rai lokaci ɗaya tana mata gargadi da babbar murya akan tayi tsaye ayi mata iyaka da yarinyar nan har abada babu ita ba ke bataci darajar kowa ba sai mahaifin Abba,da kuma Abban da sai sun yi shari'a da ita su ga uban da ya tsaya mata da haka Rumaisa ta juya ta fice daga parlor cikin awa ɗaya suka gama komai a police station aka bai wa Sadiya tayi dogon rubutu a takarda ta dauki alƙawarin ba zata kara shiga gonar Rumaisa ba kallo daya za kayi wa Sadiya kasan ta wahala a cikin cell ɗin ga baki ɗaya ta wani ya mutse kamar wacce ta kwanta jinya. Daman tun kafin AB da Rumaisa su karasa wurin motar Sadiya ta rigasu isa gaban motar tayi tsaye tana jiran a buɗe ta shiga wani irin mugun kallo Rumaisa take aikawa ta saitin ta ta dai yi shiru taga hukuncin da AB zai dauka dan ta dauki alwashin ba zata zauna bayan mota ba. Lokaci ɗaya Sadiya taji AB ya fisgota ya zuba mata mari hagu da dama, kafin ya shakota yana zare mata manyan idonsa cikin zafin zuciya "gargadina na karshe dake idan kika kara kusantar inda mata ta take wallahi-tallahi sai na miki mummunan wulakanci da har abada ba za ki taba mantawa dani ba ,wawuya kawai jaka!"wani irin murmushi Rumaisa ta saki tana folding hannunta akan kirjinta ba karamin burgeta AB yayi ba ko babu komai ya nunawa Sadiya matsayin da take dashi a wurinsa, "jaye min a hanya. Ya faɗa yana dakawa Sadiya wata irin tsawa da sauri ta kauce tana dafe da duka kunnuwanta jikinta babu inda baya bari ga hawaye dake mugun gudu akan kumatunta tamkar an buɗe famfo agabanta AB ya buɗewa Rumaisa kofar mota tana hango mahaukaciyar soyayyar da yake yiwa Rumaisa acikin kwayar idanunsa. gigitaccen horn ɗin da taji yana danna mata yasa ta buɗe back seat ta shiga ta mayar da kofar ta rufe da gudu ya fisgi motar,gudun da yake yi dasu ya tsorata Rumaisa sosai bata taɓa ganinsa cikin fushi irin wannan ba,da sauri ta rike hannunsa cikin kwantar da muryar da shi kaɗai ,zai ji tace "please habeebi control your temper karka watsar da mu akan titi, bai ce komai ba ya dai rage gudun tare da ya mayar da hankalinsa kan tukin da yake. Sadiya tana ganin yadda Rumaisa ke rike da dayan hannun AB har yanzu wani irin abu ta rika ji yana sokar mata zuciya, daidai kofar gidan Aunty Safeena yayi parking mota ,tun kafin ma yayi magana Sadiya ta balle marfin motar ta fice sai ko kokuwa take da numafashinta da ke barazanar daukewa duka. AB bai kara kallon gefen da take ba ya kara tada motar suka bar layin.Kallo ɗaya maigadi yayiwa Sadiya zuciyarsa ta tsinke musamman yadda yaga tana layi tamkar wacce tasha wani abu zai riketa ganin zata fadi a tsawace tace dashi "don't you dare touch me.!"Tayi maganar a tsawace tana zare ido a tsorace maigadi ya matsa baya jin irin tsawar da tai masa ta fitar hankali duk cikin 'ya'yan Mami ita ce marar kirki acikinsu tsaki maigadi yayi ya koma kan benci ya ƙara yar karamar redio a kunnensa bai kara kallon gefen da Sadiya take ba. adaddafe ta karasa cikin parlor Aunty Safeena har lokacin Mami na zaune a parlor tana kan salayya ta idar da sallar ishaai ɗinta kenan ga baki ɗaya zuciyarta da tunaninta na kan Sadiya da batasan a wane hali take ciki ba ga Siyama sai kiranta take a waya har yanzu bata dawo ba yaya Sadiya ma haka, sai da mami,ta faɗa mata tana wani uzuri za ta dawo ba da daɗewa ba. Tsakiyar parlorn Sadiya ta zube tana jin yadda parlor ke jujjuya mata sama-sama ta rika jin murya Mami akanta daga nan bata sake sanin inda take ba. Cikin shawagaba Rumaisa ke faɗin "meyasa ba zaka shigo dare baiyi ba habeebi?" "Zan je na huta Rumaisa duk yau ban zauna ba. Girgiza kai tayi ta cigaba da kallonsa ba zato Ab yaji Rumaisa ta Rungumesa ta zagaye hannayenta ta gadon bayansa cikin muryar rada ta furta "I love you! numfashinsa yaji yana wani irin sarkewa jin Rumaisa ajikinsa ya fara jin kansa wani irin da sauri ya cireta ajikinsa yana kallonta yana lumshe idanuwansa "so kike ki har gitsani ina zaman zamana ko habibty?" 'Yar dariya Rumaisa tayi fari da ido tayi tana faɗin."Ban cin kana da Baby Aydah a gida. Jin ta ambata masa Aydah yanayinsa nan take ya canja,kallon da taga yana yimata yasa ta fice daga motar tana yimasa daria. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/8, 9:28 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 062. Direct gida AB ya taho wata irin gajiya yake ji a jiki da zuciyarsa lamarin Sadiya yafi komai gajiyar da zuciya da gangar jikinsa ya rasa yanda zai yi da ita amma azahiri gaskiya ta kai shi bango haƙurinsa yana gafda da karewa akanta. Yana turo ƙofar main parlor idanunsa suka sauka akan Aydah wacce ke saukowa daga bene, da wani kalan kallo yake bin jikinta dashi tana sanye da boomshort wanda iyakancinsa matse-matsinta saura kaɗan ya zama pant sai rigar half vest gashin kanta a tsife tayi masa two baby sai fito tamkar wata 'yar tsana. Yanda take saukowa da sauri yasa illahirin jikinta motsawa, duk iya ƙokarin da AB ya yi naso ya ɗauke idanunsa daga kanta, ya kasa saboda zuciyarsa tana mararin kallonta. Aydah tana hango shi ta fara sakin tattausan murmushi da zumudi ta nufo shi "Sannu da hanya Yayanmu tun safe da ka fita sai yanzu ka dawo na gwada kiran wayarka na ji lafiyarka amman bata shiga. Fuskar nan tasa a turɓune ya amsa mata da "Yawwa ya jikin naki hope kin sha maganinki?" Turo baki tayi "Ni fa Yayanmu na warke sumul ba abun da ke damuna. "Oh! Da gaske kin warke?" Ya yi magana da girar ido ɗage wani juyi tayi wai don ya tabbatar da gasken ta warke batasan cewa hakan da tayi ba ƙaramin dagule masa lissafi tayi ba makutt! Haɗiye wasu busassu miyau wata irin muguwar sha'awa yake ji tana taso masa gudun kada ya tafka abin kunya yasa shi sauri nufar upstairs har ya fara tattaka mattakalar bene ya ji sawun tafiyarta a baya sa yana so ya juya ya yi mata magana amman yana jin kunyar ta ga yadda yanayinsa ya sauya "Yayanmu yaushe za ka kaini ayi min kitso da gyaran jiki har da ƙunshi nake so ayi min. Batareda da juya ba ya shiga bata amsa "Bani da lokaci ki je da kanki ko Huwaila ta rakaki ai za ki iya gane Aj beauty palace and spa?" "Ni gaskiya naka nake so idan ba za ka kaini ba sai na haƙura daman tun-tuni na gama fahimtar yanzu ka daina sona, duk sanda na kalli cikin idanunka ina hango tsananin ƙiyayyar da kake min. Cak ya tsaya wanda Aydah bata lura da tsayuwar tasa ba hakan yasa ta buge shi sai kawai tayi baya za ta faɗi cikin zafin nama ya riƙo hannunta na dama, kallon cikin tsakiyar idanunta ya yi duk da yana ji yanda zuciyarsa ke masa zafi da zogi a haka ya daure, ya riƙe ta damau cikin raunin murya ya furta "Baby yaushe na taɓa furta miki kalmar da ta danganci tsana?" Duk da ta tsorata da yanda tayi baya don kuwa ba abun da gabanta ke yi sai dukan uku-uku, sai ta lumshe idanunta eyelashes ɗinta suka yi wani irin kwantawa za ka yi zaci an yi mata fixing da na kanti alhali a haka Allah ya halicce ta "Ai Yayanmu ita kiyayya da soyayya ba sai fatar baki ta furta su ba ko acikin ƙwayar idanu za a iya karantar sakon zuciya, saboda haka sakon dake shimfiɗe a zuciyarka ƙwayar idanunka ta isar min dashi sai dai ba zan gaji da faɗa maka ba laifina bane Yayanmu zanen ƙaddarar mu ne ya zo da haka. Sai da lumshe idanuwansa kana ya buɗe su akan kyakkyawar fuskarta, kamin ya ce "idan har da gaske ni ɗin na tsaneki kamar yanda kika gama faɗa yanzu nan meyasa da kika je faɗuwa ban bar ki ba kika faɗi na tabbata daga kan step ɗinan kamin ki ƙarasa kai wa ƙasa, koda ba ki mutu ba za ki ji mummunan rauni ki tambaye kanki ki kuma ba wa kanki amsa wanda ya daina sonki ne zai cece ki a lokaci da wani mummunan abu ke shirin faruwa dake. Daga haka ya sakar mata hannu tayi sauri dafa karafe da aka ƙawata bene dashi domin dafawa yayin tafiya, za tayi magana ya katse ta ya ce "A gajiye nake ina bukatar hutawa za ki iya tafiya. Yayi magana cikin dusashewar muryarsa da ke fita a hankali domin maganganunta ba ƙaramin taɓa mishi zuciya suka yi ba, shi kansa a wasu lokuta yana mamakin yadda yake ji kiyayyar Aydah, wacce ba zai iya misalta ta ba kuma ya rasa laifin da tai masa da kesa yake mata Irin wannan kiyayya. Ya juya da sassarfa yana jin yanayi marar daɗi a zuciyarsa sai da ya shige ɗakinsa kamin Aydah ta juya ta sauka ƙasa, Huwaila dake cikin kitchen tai sauri fitowa ta kama hannun Aydah suka shiga kitchen sai da Huwaila ta datse ƙofar kitchen ɗin kamin ta dubi Aydah sama da ƙasa cikin ƙaramin sauti ta ce "Auta kanki na ja ashe duk lakca da na ba ki ɗazu kin haddace ai na gayamiki yanzu dole ki tashi tsaye ki tsaya da ƙafafuwanki, ki yi faɗa akan mijinki kada ki sake wannan kodaddiyar yarinya ta shigo gidanan ba ki daidaita almurarra tsakanin ki dashi ba. Allah na tuba Auta ban da Allah ya yi ki da shegiyar wautar tsiya wa zai sami miji kamar Yayanmu ya tsaya wasa. "To ni Aunty Huwaila ya kike so nayi? Ke fa kika ce nace masa ya kaini wurin gyaran jiki amman yana buɗe baki sai cewa ya yi na tafi ni kaɗai ai nasan wuri ko mu tafi ni dake, alhali tun ina 'yar mitsiyaya shi ke kaini gurin kitso yanzu tsabar ya tsaneni kin ji abin da ya faɗa. "Ke tafi can marar wayau don kawai ya fadi haka sai me? Ai gara ki tafi ɗin da kanki hakan zai sa ya fara gano ke yanzu ba kamar wacce mitsiyaya yarinya da raina bace. Shiru Aydah tayi tana nazarin kalaman Huwaila bi-da-bi can kuma ta kyasta yatsanta "you're right Aunty Huwaila kin ga su yaya Sadiya suke zuwa da kansu ba wanda ke kaisu wata kila ma idan yaga ina iya fita da kaina na kuma dawo da kaina ya bani mota koda zan zana SSCE ɗina na iya driving. Cike da takaici Huwaila ta dafe goshinta "Ke dai ba a taɓa raba ki da sakalci amman mu tafi a haka tun da ta wannan sigar kika fahimta. Aydah ta buɗe baki za ta yi magana Huwaila tai sauri katse ta "Kin ga dauki tray ɗinan kika masa abincinsa ne duk ihu da tsawan da zai yi miki kada ki fito har sai yaci abinci nan, ki koyi naci da kafiya akansa duk korar da zai miki ki basar ki yi kamar ba ki masan yanayi ba. In shaa Allah kamin waccan kodaddiyar ta shigo mun ciyo kansa yanda Yayanmu ke matuƙar ƙaunarki Auta kawai a waye gari yana nuna miki halin ko in kula ni nasan da walaki goro a miya ba banza ba dole da akwai wani tsinannen da ya shiga ya fita ya shiga tsakaninku kuma da yarda da Ubangiji haƙarsa ba zai cimma ruwa ba. Aydah ta langwaɓar da kai "Aunty Huwaila ni tsoron ihunsa nake yi kada na je ya harzuƙa yai min duka. Cikin sigar rarrashe Huwaila ta dafa kafaɗarta "in shaa Allah ba ma zai dake ki ba dauki maza ki kai masa 'yar albarka. Aydah tana murmushi ta kinkime tray ɗin tana tafe tana nishi ita a dole sai ta nuna dauki abu mai nauyi sai da ta fara sauke tray ɗin kasa ta tura ƙofar parlornsa dake sama ta aje tray ɗin akan centre table kana ta nufi master bedroom ɗinsa kanta tsaye ta tura kofa yana tsaye gaban dressing mirror yana goge, baƙa wulik ɗin sumar kansa turo ƙofar da tayi yasa shi waigawa ya dube ta kafin ya dauke fuska ya cigaba da goge jikinsa da hand towel ɗin dake hannunsa Aydah tana zuwa ta nufi kan gadonsa inda tufafinsa da ya cire, ta dauka tana linke masa "Yayanmu ga abinci can parlorn ka na kawo maka, nasan yanda ka ɗebo gajiyar nan ba lallai bane ka iya saukowa ƙasa ba. Da mamaki ya juya yake kallonta ita ko a jikinta aikin gabanta kawai take yi "Aydah bana gayamiki ki daina shigo min ɗaki gaba gadi ba? Ki fara neman izinina kamin ki shigo min ke duk abun da aka faɗa miki baya shiga kunnenki ko?" Murmushi kurum tayi tare da nufar closet ɗinsa ta buɗe ta saka masa kayansa da ta linke tayi tsaye tana kallon jerin tufafinsa dake jere aciki can ta dauko masa wata riga armless coffee color, ta ajiye gefen gado ta sake buɗe bangaren da trousers dinsa suke ta ciro masa blue three quarter bai yi mamaki ciro masa kayan da zai saka da tayi tun da ba yau ne karo na farko da ta fara yi masa hakan ba. "Wai Aydah ba magana nake miki ba ki fita kamin ki fusata ni. "Allah ya ba ka haƙuri yayanmu in shaa Allah ba zan sake shigowa ba sai da izinin ka. Tana karasa magana ta fice tana mai jawo masa ƙofa, ya dawo da idanunsa daga kallon da ya bi ta dashi yana kammala shafar mai ya dauki kayan da ta fito masa dasu ya saka ya fesa turare, yana fitowa parlor yaga Aydah zaune akan cushion tana jiran fitowarsa ta kasa ta tsare duk faɗa da yake mata bai sa ta fice masa a parlor ba ta nace masa sai da yaci abincin sosai yana gamawa ta tattara kayan ta fita dasu Huwaila tana ganinta ta biyo ta kitchen tana tambayar da yanda ta kaya a tsakaninsu "Allah Aunty Huwaila karo na farko da na ji tsoron Yayanmu ya fara raguwa a zuciyata. Aydah ta faɗa very excited for all over her face. "Maa shaa Allah! To daga yanzu haka za mu dinga yi masa sannu-sannu wata rana shaiɗanin da ke jikinsa zai fece duka, zan dinga tayaki da addu'a Allah ya daidaita tsakaninku kema ki ɗage da addu'a da sallar dare in shaa Allah komai zai dawo yanda yake. Cike da farin ciki Aydah ta rungume Huwaila tana dariya ita kadai tasan irin mayuwaci hali da take ciki a dalili wannan sauyawar ta yayan nata. *ALHAJI BASHIR MANSION* Koda Mami da Sadiya suka dawo gida Daddy baya gida lokacin da Siyama tayi arba dasu wujiga-wujiga dasu daga Sadiyar har Mami sun fita daga hayyacinsu,sai da hantar cikin Siyama ta kada cikin kaɗuwa take tambayarsu meke faruwa ta dawo ta tarar da dukkansu basa gida kuma Balmo maigadi ya faɗa mata 'yan sanda ne suka zo suka tafi da Sadiya laifin me tayi musu?" Rai ɓace Mami ta bata labari abunda ya faru, sosai Siyama ta tsorata ita kan yanzu Sadiya ta fara bata tsoro yanzu sau biyu kenan tana attempting kisan kai ta dinga mata alamar tambaya. Tsabar kaɗuwar da Siyama tayi kasa magana tayi sai kurum ta bi su da kallo har Sadiya da Mami kowacce su ta wuce ɗakinta Siyama bata dawo ainihin natsuwarta ba. Da dare da Daddy ya dawo yasa Siyama ta kira masa Sadiya ta dukkansu Siyama da Sadiya suna zaune a kasan rug carpet, Mami tana zaune akan kujerar dake kusa da ta Daddy, ta wani kici-kici da fuska yayin da gabanta ke dokawa tana cike da zullumi haɗe da fargaba irin hukuncin da Daddy zai yanke wa shalelen 'yarta Sadiya kam ko a jikinta asalima ko dar bata ji ba. Wani mugun kallo Daddy yake aika mata dashi kamin cikin kakkausar murya ya kira sunanta "Sadiya. Ta ɗago shegun idanuwanta ta kalle shi sai kuma ta maida kanta ƙasa batareda da ta amsa ba. "Sadiyaaaa! Wannan karo a matuƙar fusace Daddy ya sake ambatar sunanta, ta ɗago tare da amsawa ciki-ciki "na'am Daddy! "Sadiya ki shiga taitayinki dani idan ma wasu shaiɗanu ƙawaye ne kika haɗu dasu suke hora miki kunne suna dora ki a mugun tafarki, daga ke har su har gami da wannan sakarya uwar taki da ke goyon bayanki zan yi maganinku. Baki isa ki haifar min damuwa kin yi kaɗan yaushe ma aka haife ki da zan kasa bi dake?" Ina mai gargaɗin ki daga yau daga rana mai kama da yau babu ke ba Abba duk wani abu da ya shafe shi da ki cire hannunki aciki, idan kika bari na sake kama ki da aikata laifin kwatankwacin wannan da kika aikata wallahi-azim Sadiya zan yi mummunan saɓa miki. Da ace ba nina haife ki ba Sadiya da bani bane mahaifin ki ba da yau ɗinan sai ki barmin gidana,sai dai kashh jinin kai ne da baya ketare wuya kin ci albarkaci ni na haife ki. Magana ta ta karshe dake ki fito da miji idan nan da watanni biyu suka cika ba ki kawo min wanda za ki aura ba ni zan nemo miki da kaina. Ke kuma Mariya ba zan ce dake komai ba kawai dai zance ki cigaba da abin da kike yi kada ki fasa ke ɗin ma ki sani kina cin albarkacin 'ya'ya dake tsakaninmu ne mugun hali nan da kika tsirawa kanki yasa kin fice min daga rai, nan da wani lokaci zan kawo ƙarshen rashin mutuncinki. Ku tashi ku ɓace min dagani har ke Mariya bana buƙatarki ki fita. Yanda Daddy ya yi magana a tsawace yasa a lokaci ɗaya suka miƙe tsaye sai ya tsayar da Siyama ya yi mata nasiha. Washegari gari Aydah tana dawowa daga school kasancewar Thursday ne babu islamiyya ta shirya ita da Huwaila za su fita gyaran jiki kuma aka yi dace da AB yana gida ta je har parlornsa na sama ta same shi ta karɓo kudi adaidaita suka shiga ita da Huwaila sai Aj beauty palace and spa. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/10, 11:24 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 063. Kusan awarsu biyu cikin ta uku,aka gama yiwa Aydah duk abubuwan da ta lissafa an mata tun daga kan gyaran jiki ,saloon,kitso zanen ƙunshi da yayi matukar yimata kyau. Har suka fito bakin titi korafi take yiwa Huwaila da ita ma aka yi mata gyaran kai dan Aydah ta matsa ayi mata shine aka wankewa mata kai kurum tace bada kitso ba kuma bada zanen lalle ba haka Aydah ta haƙura badan taso ba. Korafi take yimata kanta har ya fara ciwo sun matse mata kai jin take tamkar zata yi zazzaɓi, ta faɗa tamkar zata sakawa Huwaila kuka Huwaila ta rike hannunta tana murmushi raki irin na Aydah ba zai daina bata mamaki ba tun da tun fil'azal bata san wahala komai kankantar ta ba. Basu jima ba suka samu adaidaita sahu har ƙofar gida ya sauke su har lokacin kuma AB yana gida tana ganin motarsa tun a parlor kasa ta cire mayafin kanta ta wurgar da handbag ɗinta kan doguwar soofa ɗin dake girke a parlor sai kuma ta tuna da halinsa ya tsani wannan zubar da kayan da take yi sai da tattare su ta kai ɗakinta sannan ta nufi parlorn sa dake sama tayi knocking haɗe da yin sallama jin shiru yasa ta tura ƙofar parlor baya ciki har ta nufi ƙofar ɗakinsa daidai lokacin AB ya fito daga master bedroom ɗinsa farin yadi ne ajikinsa fari kal marar zane ko kaɗan har ana hango farar shimin dake jikinsa banda ƙamshinsa da ya cika parlor babu abunda ke tashi sosai yayi mata kyau a idanu samun kanta tayi da zuwa da gudu ta shige jikinsa ta zagaye duka hannayenta ta bayansa wani irin bugawa ƙirjin AB ya shiga yi ko kafadarsa Aydah bata kai ba sai akan cikinsa ta kwantar da fuskarsa yayin da take shaƙar ƙamshin jikinsa, har natsuwa ke shigarta wanda bata san lokacin da ta fara sauke numfashi ba. Shiru suka yi Dukansu zuciyoyinsu na irin wani dokawa cikin wani yanayi mai wuyar fassarawa da sauri ta ɗago kanta tana kallon cikin kyawawan idanunsa "Yayanmu har mun dawo kaga kitsona" tana matsowa tana haɗe filin da yayi saura a tsakaninsu tana nuna masa kitson kanta wannan karan bugun zuciyarsa yake ji har cikin tafin ƙafarsa ba wannan ne karo na farko da Aydah ta saba zama kusa dashi ba ba wannan karon ne na farko da ta fara rungumarsa ba meyasa komai yanzu yake jin sa ya canja."wani irin deep breath ya shiga ja yana saukewa kafin ya kafawa kitson ta ido yayi masa kyau ainun,hannayenta duka biyu ya riƙe yana kallon yadda lallen yayi kyau. Ganin lallenta yake kalla har ya kasa dauke idonsa cike da ɗoki Aydah ke faɗin."Yayanmu yayi kyau ko?"sakin hannun ya yi yana faɗin "Ba laifi yayi kyau" juyawa ya yi ya soma tafiya da sauri ta cimmasa tana faɗin."Yayanmu ina kuma za kaje?" Ware ido yayi akanta cike da gajiya a muryarsa ya furta "zan je gidansu Rumaisa.!"wannan karon ya mutse fuska tayi tamkar bata ji sunan da ya kira mata ba taji zuciyarta na wani irin tafarfasa bai kara kulata ba har ya fice daga parlor tana tsaye a wurin tamkar an kafata da gaske auren Rumaisa zai yi?"wani irin abu taji yana tsaya mata a wuya,wasu irin hawaye masu radadin gaske suka rika fita daga idanunta suna sauka akan fuskarta,anan parlor ta zube ta rika rera kuks tamkar wacce aka daka ta tsani wannan Rumaisa da duk wani abu da ya shafeta bata tunanin zata taɓa sonta har abada. Sai bayan magarib ya karasa gidansu Rumaisa ita ma bata jima ba ta fito dan mai mata gyaran jiki bata jima da tafiya ba sai da tayi wanka kamin ƙarasowar AB kallonta kawai yake Ƙamshinta yana hargitsa sa ga baki ɗaya yanayinsa ya canja kula da yanayinsa yasa tace "Habeebi lafiya?"kai yake girgiza mata yana faɗin."kamshin nan yayi yawa Rumaisa har tsakiyar kaina nake jinsa,hop cikin gida kawai kike sakawa banda waje ko?"juya ƙwayar idonta tayi tana daga masa kai "gobe Aunty Raliya suke son suje suga gida ban san wane gidan zamu zauna ba. "Gidan da muke ciki da Aydah zai ishemu ai bana son raba hankalina na fison iyalina suna haɗe a guri ɗaya."ya faɗa mata kai tsaye, Aydah da ya kira mata taji ranta ya ɗan sosu har wani kiranta da iyalinsa yake yi wai me AB yake nufi ne?sai kawai tayi kokarin danne ɓacin ranta ta ce "To ya za'a yi kenan ya kuma tsarin gidan yake?"kasan ba wancan gidan bane wanda na zaba lokacin cikin gidajenka ni ban ma san da wannan ba. "Wannan yafi wancan da kika taɓa zaɓa kyau da girma wannan har da swimming pool akwai ciki, gashi kuma sama da kasa ne ƙasa akwai ɗakunan bacci uku sai babban parlor sai dakin da mai aiki take ciki,sai kitchen da store sama kuma ɗakunan bacci biyu ne sai babban parlor sai master bedroom ɗina Aydah tana cikin ɗaya ɗayan babu kowa so duk inda kike so babu matsala."wani abu taji ya tsaya mata a wuya ba zata iya zama kasa ba ɗakin Aydah yana a sama,kuma ba zata iya zama da Aydah a sama ba sai dai Aydah ta bar mata sama ta dawo kasa kawai kanta tsaye ta furta "kace ta koma ƙasa sai ta bar mana sama ni da kai za mu fi sakewa. Da sauri ya shiga girgiza kai bai san taya zai fara wannan rashin hankalin da Rumaisa take so yayi ba yanzu,Daddy ya mallaka masa gidan ya zuba musu duka furnitures ɗin dake cikin gidan taya zai ce Aydah tabaro sama ta dawo kasa,ai ko dan rigimar Aydah yasan ba zai fara ba. "Idan babu damuwa duka mu zauna a sama Rumaisa akwai wani extra daki sai ki zaun acikinsa ƙasa kuma ki ɗauki ɗakuna biyu ki bar mata ɗaya ni ina gani hakan zai fi batareda da kowacce acikinku an shiga hakkenta ba. "Ban gane me kake nufi ba Abba ya za'ayi da kayan ɗakina?" wannan karon da ɓacin rai sosai a muryarsa,saboda zaman lafiya yace zai sa akwashe kayan ɗayan bedroom ɗin na sama da kuma kujerun parlor sa dake sama sai ayi mata jere kayan kitchen ɗinta tun da kitchen ɗin yana da girma tamkar ɗaki daya yake zata iya aza nata a gefe kuma ya wadace su. Rumaisa bata kara cewa komai ba ga baki ɗaya ranta a mugun ɓace yake har AB ya wuce ba suyi wata kyakkyawar sallama ba, kuma ita ta azalzale sai ya zo ta ganshi gashi ya zo ɗin daga ƙarshe ya tafi da takaici da bacin ranta. Da Rumaisa ta koma cikin gida take yiwa mahaifiyarta bayanin yadda suka yi da AB murmushin takaici kawai Raliya tayi ta cigaba da danna wayarta tana tausayawa kanwartata taga ga baki ɗaya son wannan yaron ya riga ya rufe mata ido tana tsoron ranar da zai nuna mata halinsu na maza. A yanda ta fahimta soyayyar da Rumaisa take masa tafi wacce yake mata. AB yana baro gidansu Rumaisa ya wuce majalisa wurin Abdulkarim saboda ya kira sa ya zo ga katunan daurin aure ya karbo anan Abdulkarim ya cire na 'yan zaman majalisa ya basu, duk wanda yaga sunan AB da Rumaisa a jikin katin sai ya furta albarkacin bakinsa,sun yi mamakin rashin zuciya irin na AB da har zai iya sake neman auren Rumaisa, a bisa irin mugun wulaƙanci da cin zarafin da mahaifinta ya yi masa a ranar daurin aurensu , shi ne don rashin zuciya zai sake komawa gareta. Duk abun da suke faɗa AB ya ya biris dasu saboda shi yaji ya gani shan koko ɗaukar rai. AB bai dawo gida ba sai misalin ƙarfe goma na dare koda ya shigo main parlor babu kowa ya haura sama. Huwaila dake zaune a ɗakinta tana dakon dawowarsa da ta ji ya haura sama ta tashi da sauri ta fito ta nufi ɗakin Aydah, ta tura kofa ta shiga da sallama Aydah tana kwance da waya a hannunta tana karanta wani littafi mai suna izgilanci wanda Hajja ta rubuta sosai littafin ya yi mata daɗi daman ita tafi sha'awa littattafan soyayya. "Auta ajiye wayar nan ki zo ki kai masa abincinsa yanzu nan ya dawo. Ya mutsa fuska Aydah tayi tashi zaune tayi tana faɗin "Ni gaskiya aunty Huwaila na gaji ki kai masa kawai, kuma yanda littafi nan ya dauko daɗi bana jin zan iya katse karatunsa. Maka mata harara Huwaila ta fara yi tukun kafin ta isa gareta ta fincike wayar hannunta "Ka ji min shashanci wofi yanzu banda ke da abinki Auta karatun littafi yafi miki kula da mijinki?"naga dai ko cikin littafin abun da marubutan suke koya muku kenan tattali da kulawa da maigida amman shi kenan babu amfani gayamiki cigaba da karatunki kwana nakki nawa Rumaisa ya rage ta shigo gidanan na tabbata za ta bashi kulawa ta musamman anan za ki raina kanki. Huwaila tana ƙarasa magana ta kama hannun Aydah ta dankwara mata wayarta a tafin hannunta, sunan Rumaisa da ta ambata har tana faɗin za ta kula da yayanta yasa ta ji wani irin mugun kishi da har yasa ta miƙewa tana faɗin "Wallahi babu wata Rumaisa da ta isa ta zo gidanan ta shiga tsakanina da Yayanmu. Murmushin gefen baki Huwaila tayi "To mu je ki kai masa abincinsa amman kuma sai kin canza wannan rigar bacci kwata-kwata bata dace da zuwa turaka ba. Ko kaɗan Aydah bata fahimci inda Huwaila ta dosa ba sai kawai ta nufi wardrobe ɗinta da sauri tana faɗin "Aunty Huwaila idan kayan bacci ne ina dasu kala-kala zo ki zaɓar min wacce ta dace na saka ai ni yanzu duk abun da zai farantawa Yayanmu rai shi nake so na kuma dauke hankalinsa daga kan wacce kodaddiya mai idanuwa irin na 'yan China. Sosai Huwaila ke kwasar dariya jin sharrin da Aydah ta yiwa Rumaisa wai idanunta masu kama da na 'yan China, Huwaila ta ciro mata wata 'yar karamar riga mai siririn hannu wacce bata wuce cinyoyinta, rigar light purple ce a gaban rigar an yi mata ado da lace mai raga wanda ta wannan jikin lace ɗin ana iya hango 'yan matasan boobs ɗin Aydah, sau ɗaya ta taɓa saka ta yaya Abba ya ganta sanye da ita a main parlor ya yi mata faɗa tare da korata daki ta je ta canza ta tun daga lokacin bata sake marmarin sakawa ba. A takaice ma ta manta da ita sai yanzu da Huwaila ta ciro ta cikin jerin kayan baccinta wanda Siyama ce tai mata arranging ɗinsu acikin wardrob. "Aunty Huwaila idan na saka wannan rigar Yayanmu zai yi min faɗa saboda na taɓa saka ta a lokacin muna gidan Mami ya dinga yi min faɗa har ya yi min gargadi kar na sake sakawa. "Auta a wancan lokaci da ya hane ki ai babu aure ne a tsakaninku kema kinsan da wannan, a yanzu kuma duk abun da yake jikinki mallakinsa ne ko Rumaisa idan ta shigo gidanan fiye da wannan rigar za ta dinga sakawa don ta dauke hankalinsa. Da sauri Aydah ta fizge rigar daga hannun Huwaila ta cire ta jikinta ta maye gurbin ta da wannan, turare kusan kala uku Huwaila ta bi jikin Aydah dasu nan da nan ta ɗauki fitinannen ƙamshi na fitar hankali. Sai faman yaba kyawun da tayi Huwaila ke yi ita kanta Aydah da ta kalli mirror sai ta sake kallawa kitson kanta ya sauka a kafaɗarta tare suka shiga kitchen Huwaila ta haɗa abincin AB kamar yanda ɗazu da rana tai masa ta miƙawa Aydah ta nufi bangaren sa dake sama yana zaune a parlor yana kallon news jikinsa sanye da kayan bacci farare kal sai dai bai rufe bottoms ɗin rigar ba kamar ma hakan ya zama masa dabi'a. Sai dai tayi knocking ya bata izinin shiga sannan ta sunkunya ta ɗauki tray ɗin ta shiga tun kamin ta iso gafda shi ƙamshinta ya gama lulluɓe masa ƙofufin hanci, ya sauke ajiyar zuciya "Yayanmu ga abincika na kawo ma na fahimci kwanan nan baka so cin abinci da alama so kake ulcer ta kama ka aunty Rumaisa ta tuhume ni da rashin kula mata da kai. Wani sakatoto da baki AB ya yi yai mata kur da idanuwansa, wani irin mayataccen kallo yake mata tsigar jikinsa na tashi Aydah ta iso gabansa ta ɗora tray akan centre table, sunkuyawar da tayi matasan boobs ɗinta suka kara fitowa AB ya ƙara rikicewa ya haɗiye yawu har sai da adams apple ɗinsa ya yi wani bala'in motsawa jikinsa ya dauki charging yasan ya yi matuƙar kokari tsawon lokaci da ya dauka yana jurewa yana kare hakkokin ubangiji bai taɓa kusanta zina ba, haka zalika shi lafiyayye ne dole yana bukatar mace a halin yanzu an kai stage ɗin da haƙurinsa da juriyarsa sun ƙare, musamman yanzu da yaci karo da nonuwan Aydah da suka birkita masa lissafin ƙwaƙwalwa. Aydah batasan me ke faruwa da yayan nata ba sai kawai ta nufi fridge ɗin da ke cikin parlorn nasa tana faɗin "Bari na dauko maka drinks da ruwa Yayanmu. Yanda ta juya tana tafiya duk da bata da butt amman yanayin tafiyarta da yanda rigar jikinta tabi ta lafe a jikinta ya ƙara gigita AB, bai san sanda ya miƙe tsaye ya bi ta Aydah tana maida murfin fridge ta rufe juyawar da za tayi sai taga AB tsaye a bayanta idanunsa sun kada sun yi jajur wata irin jaraba yake ji tamkar zai ci babu. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/10, 11:28 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 064. Ba ƙaramin tsorata Aydah tayi ba da ganinsa don har jikinta ya fara rawa a zatonta dukanta zai yi idanunta har sun cicciko da ƙwalla cikin sarƙewar murya ta furta "Yayanmu Dan Allah kayi haƙuri karka dake ni. "Shhhhh! AB ya faɗa tare da ɗora yatsansa akan lips ɗinsa daga shi har ita bugawar zuciyoyin su ya kara gudu matsawa ya yi ya haɗe tazarar dake tsakaninsu a rikice Aydah ta ja da baya, bayanta ya buge jikin fridge sai kawai ta ƙara rikicewa Ab ji yake buƙatarsa na kara hauhawa, ba kuma zai iya control ɗin kansa ba infact ya manta da wacece Aydah a gurinsa burinsa a yanzu ya sami natsuwa ya rage loading dake dankare da mararsa haɓarta AB ya kama ya ɗago fuskarta a hankali ya shigar da ƙwayar idonsa acikin nata kasa jure cigaba da kallon cikin idanunsa Aydah tayi sai kawai ta runtse idanuwanta, a hankali yake bin fuskarta ta, da idanunsa jajayen labbanta yake kallo zazzafan numfashi ya ja iskarsa ta fita daga bakinsa ya sauka akan fuskarta, wanda hakan yasa ta buɗe idanunta "me kuma nayi ma Yayanmu wallahi kana tsorata ni. "I want to kiss you Baby! AB whispered bending his head to her height, he claimed her soft lips and started kissing her very slowly. Wani kalar dasƙarewa Aydah tayi ta nemi hankali da tunaninta ta rasa bata masan duniyar da take ciki ba. Ba tace batasan mene ne kiss ba because tasha karantawa a novel tana kuma kallo anayinsa a indian series da take kallo, amman azahirance yau ne daga ita har shi kansa AB suka fara dandanarsa AB bai taba sani haka French kiss yake da dadi ba sai da ya tsoma bakinsa cikin na Babynsa. Ga wani wahalalle numfashi da gurnani da yake ta faman saukewa irin na mutumin da ya kai last stage da bukatuwa hannayen Aydah ya kama ya yi pinned ɗin su a jikin fridge ya yi increased kiss ɗin sosai yake tsotse lungu da sako na bakinta, ya saki hannayenta holding her tiny waist Aydah mutuwar tsaye tayi ta kasa katabus jingine kurum dake a jikin fridge AB yana bi da ita yanda yake so batareda da tayi yunkuri hana shi ba wanda hakan ne ya bashi gwarin gwiwa ya zame ɗayan hannun rigarta ya yi ƙasa dashi hakan yasa ɗayan boobs ɗinta ya bayyana AB ya ƙure shi da jajayen idanunsa wasu tsikakku yawu suka cika masa baki, illahirin jikinsa ya dauki rawa sai kakkarwa yake yi tamkar mai jin sanyi da yantsunsa biyu ya kai ya kama nipples ɗinta, kamar mai jin tsoro haka yake murza su yoo dole yaji tsoro saboda shi ne karonsa na farko da ya fara taɓa wadannan abubuwan. Aydah kuma ji tayi wani abu mai kama da tafiyar tsutsa ya tsirga mata tun daga tsakiyar kanta har zuwa ga tafin ƙafafunta, sai wani jujjuya kanta take yi daga ɓangaren dama zuwa na hagu ga baki ɗaya ta rasa gane mene ne yayanta ke mata. Tun AB yana murza su da yatsunsa har ya ɗora tafin hannunsa duka kasancewar abubuwan kananun ne shiyasa ko rabin cika masa tafin hannu basu yi ba abin mamaki shi dake da burin mallakar manya-manya sai gashi kananun da ya gama rainawa sun yi masa bala'in daɗi tabawa har suna gafda da saka shi ya fice hayyacinsa duka, launshin su baya misaltuwa amman zai iya cewa tsawon rayuwarsa bai taɓa cin karo da abu mai launshin su ba. Tsintar kansa ya yi da kai bakinsa akansu zuƙa ɗaya ya yi ya kurma ihu yana sakin sambatu "lahaula walakuwati illah billah, Hasbunallahu wal-imaal wakil, fatabarakallahu ahasanal halikkkkkk! Ya ƙarasa jan kalmar halik ɗin da karfi sai kuma ya shiga jan iska ta bakinsa tamkar wanda yaci yaji, Aydah kam tsanani shock ɗin da ta shiga yasa ta dinga zamewa daga jikin fridge kaɗan-kaɗan har ta kai ƙasa da sauri AB ya zube guiwayoyinsa biyu a gabanta a kokarinta naso ta ja hannun rigarta ta mayar cike da fitar hayyaci ya kwaɓar da hannunta tankar mayuwanci zaki da ya yi kwana da kwanaki bai ci abinci ba ya sake rarumar kafaɗar Aydah ya ja rigar jikinta da mugun ƙarfi sai ga hannun rigar ya tsinke, a gigice ya sake mayar da bakinsa ɗayan hannunsa na kan ɗaya lailayarsa ya dawowa Aydah tamkar wani mahaukaci sabon kamu dan kuwa idan ya sha wannan sai saki ya kama wannan, 'yar karamar ƙwaƙwalwar Aydah ta gaza ɗaukar wannan babban al'amari da yayanta yake mata, ga wani fitsari-fitsari da take ji yana fita daga jikinta sai kawai ta dagargaje da dukan ƙarfinta ta kurma ihu haɗe da faɗin "wayyo Allah na shiga uku Yayanmu kada ka tsinka min su don Allah ka daina banaso, yayanmu ka bari naceee! Gigitaccen ihun da ta karasa magana dashi ya dawo da AB da dukkan natsuwarsa bakinsa yana kafe akan boobs ɗinta ya dago slowly yana sauke ganinsa akan fuskarsa akan ta, ta ya kuma kai idanunsa akan boobs ɗinta da bakinsa ke kansu dumu-dumu, zaro idanuwa ya yi cikin kaɗuwa ya cire bakin nasa sai kuma ya miƙe da sauri daga durƙuso da ya yi ya shiga ja da baya yana kallon Aydah da ƙirjinta da yake buɗe, ita ma kallon nasa take yi yanda yake kallonta yana ja da baya tamkar yaga wani abin tsoro ya hartsuna mata ƙwaƙwalwa ta kasa tabuka komai sai bin sa take da kallon kurum. Sai kawai AB ya ya juya ya wuce da sassarfa ko waiwayen aidah bai sake yiba kamin yakai ɗakinsa sau biyu yana faduwa yana tashi, yana kai wa ƙofar da za ta sada shi da master bedroom ɗinsa ya tura ƙofar da ƙarfi ya shige ɗakin. Aydah ta zaro idanuwanta yanayin da taga yayan nata ya yi matuƙar kara linka mata tashin hankali da take ciki,zuciyarta ta shiga bugawa da ƙarfi kamar za ta tsaga ƙirjinta ta fito ba ko shakka ƙwaƙwalwar yayanta ta sami matsala da yana cikin cikakken hankalinsa ko kusa ba zai aikata mata wannan abun ba, ga kuma wannan gudu da ya kwasa ya shige ɗaki kai ina da walaki goro a miya, sai kawai tasa kuka ta miƙe tsaye ta manta da rigarta da a zame take tana miƙewa cikin azama rigar ta karasa zamewa ta faɗi kan tiles, daman rigar mai tsantse ce a rikice tabi rigar ta dauko ta mayar a jikinta sai dai hannun rigar guda a ya tsinke illahirin gangar jikinta yana rawa ta nufi ɗakin nasa, tana tura ƙofa ta hango shi ya kifa kansa a gefen gado, ta ƙarasa da sauri ta tsaya gefen da fuskarsa take idanunta suka sauka akansa jijjiyoyin kansa sun firfito sun yi radau-radau sai zufa ke keto masa. Aydah ta kai hannunta ta dafa shoulder ɗinsa "Yayanmu lafiya kake meke faruwa da kai?" Bai iya magana ba sai kawai ya damƙe duvet ɗin da ke jikin gado ya matse shi da ƙarfi "Na shiga uku dan Allah Yayanmu ka yi magana ko na kira Daddy ko yaya Abdulkarim gayamasu baka da lafiya gudan su ya zo ya kai ka asibiti?" "Fita ki barmin ɗakina banaso ganinki Baby na tsaneki. AB ya furta cikin dusashewar muryarsa dake fita a hankali. "Ka yi haƙuri Yayanmu ba zan iya tafiya na bar ka alhali kana bukatar taimako bari na kira Dad.... "I say get out before I kill you just leave!!!! Last sentence ɗinsa ya yi matuƙar tsorata Aydah ta juya da sauri ta fice, da gudu ta koma ɗakinta ta faɗa kan gado tana gunji kuka lallai yayanta ya haɗu da lularar tabin ƙwaƙwalwa, wani irin tausayinsa ne take yi yana tsarga mata a zuciya "Allah sarki Yayanmu kai dai kana haɗuwa da jarabawa kala daban-daban daga wannan sai wancan yanzu kuma wannan iftala'i ka faɗa. Aydah ta faɗa cikin zuciyarta ai ko yanda ya dinga tsotse ta kaɗai ya isa ya gamsar da ita tabbatuwar gushewar hankalinsa, har ta dauko wayarta ta kira Daddy sai kuma ta fasa ta nemo numbern yaya Abdulkarim shi ma sai taga rashin dacewar hakan, to ita kan ta shiga tara bama uku ba wa za ta kira a daren nan ta faɗa masa halin da bawan Allah yayanta ya shiga tunawa da tayi da Huwaila ta gayamata ta dinga tashe cikin dare tana yin ƙiyamullaili tana kai kukanta wurin ubangiji zai yaye mata duk wata matsala ko damuwar da ta shiga, ai kuwa wani irin kuzari ta ji yana shigarta ta tashi da saurinta ta sauka daga kan gado ta shiga banɗaki ta kama ruwa tare da alwallah ta fito ta zura bubu da long hijab ɗinta, ta shiga jera nafilfili. AB yana jin ƙarar rufe ƙofa da Aydah tayi ya maida idanunsa ya lumshe ƙwaƙwalwarsa tana sake tunano masa, da abin kunyar da ya aikata kan 'yar mitsiyaya yarinya ko mitsiyaya ma Babynsa kaiconsa baisan me ya hau kansa da ya kai shi aikata wannan ɗanye aiki da Aydah, zuciyarsa sai daɗa ɗora masa laifi take yi, bai ankara ba yaji saukar hawaye a kamatunsa sannu-sannu ya fara rera kukan takaicin kansa. Ya share dogon lokaci a haka kamin ya mike jeri yana ɗibarsa ya shiga bathroom sa'ilin da ya cire boxer ɗin jikinsa yaga yanda ya lalace sai ya ji ya ƙara tsanar kansa da Aydah duka, wani wawan duka ya kai wa bakinsa da ya tsotse bakin Aydah da 'yan mitsitsi abubuwanta, da gaske sai dukan bakinsa yake yi har sai da ya fasa gefen lips ɗinsa na ƙasa zogi da raɗaɗin da yaji a bakinsa ya dauka ga kuma jini da ya gani a tafin hannunsa yasa ya haƙura ya zube guiwayoyinsa kan tiles yana ya mutsa sumar kansa yana fizgarta AB dai 'yar karamar hauka ya yi a banɗaki kamin ya yi wanka ya fito ya saka jallabiya tare da shimfida praymat ya shiga yin sallah, da kammala har dasu Istigifari akan abun da ya wakana tsakaninsa da Babynsa shi a ganinsa wannan abin da ya aikata tamkar ya haura katangar da bata dace da ya haura ba. Daga shi har Aydah adaddafe suka ga wayewar gari, kasala ta lulluɓe Aydah ga boobs ɗinta da suke mata mugun zafi ko wanka da taje yi tana ɗora sponge bath akansu tayi maza ta janye tana runtsar ido duk da sponge bath ɗin yana taushi amman ji tayi tamkar sosun ƙarfe ne. Gani yanayin da take ciki ya hanata zuwa makaranta tasan ba za ta sami sakewa ba daga ƙarshe ƙawayeta za su cika ta ne da tarin tambayoyi da bata da gamsasshiyar amsar basu. Tun da asuba da AB ya je masallaci tsabar yana jin kunyar haduwa da Aydah ya kasa dawowa gida sai kawai ya wuce kamfani daga shi sai farar jallabiya mai gajeren hannu ya shige office ɗinsa ya kwanta ƙwaƙwalwarsa ta kasa bari tunano masa abun da ya faru idan ya lumshe idanuwansa sai yaga hoton abin, sai kuma tsigar jikinsa ta shiga mimmiƙewa yana ji sha'awarsa na kara ƙaruwa. Huwaila da taji Aydah shiru-shiru bata fito ta tafi school ba tana shirin zuwa ɗakinta ta duba ta ko lafiya sai ga maigadi ya yi knocking ta nufi kofar ta buɗe yake sanar da ita Aydah ta fito ga school bus ta zo ɗaukar ta. Da sauri Huwaila ta haura ɗakinta ta tarar da ita ta tattake cikin duvet tun kafin ta tambaye ta ta fahimci babu lafiya domin ga dark circle nan a idanuwanta dake nuna alamar rashin bacci. "Auta lafiya kike kwance har yanzu ba ki yi shirin zuwa makaranta ba? Har gashi motar makarantarku ta zo har sun kai da aikowa ki fito. "Aunty Huwaila ki faɗa musu banida lafiya ba zan sami zuwa ba. "To shi kenan Allah ya saukawa bari na je na faɗa musu kada abarsu suna jira amman ki yi kokari ki yi wanka ki sauko ƙasa koda ɗan tea ne ki sha kin ji?" Aydah ta gyaɗa kai Huwaila kuma ta fita da kanta ta leƙa ƙofar gida ta faɗawa direba ɗin sakon Aydah. *ALHAJI BASHIR MANSION* Sadiya ta fito rike da car key ɗinta haɗe da handbag ɗinta za ta shiga school kasancewar yau tana da morning lectures gashi kuma tana expecting za su yi test, sai dai matsanancin halin damuwar da take ciki ya hanata fahimtar lectures ɗin har lecturer ɗin ya kammala ya fita ba abun da ta tsinta a test ɗin ma rubbish ta rubuta tayi submitted, bayan sun fito ne Sarah take tambayarta meke damunta duk da ta daɗe da sanin asalin damuwar ta, ta anan take bata labari yau saura kwanaki ƙalilan daurin auren AB da Rumaisa kuma bata da buri na gani koda an yi nasarar ɗaure auren ta hana musu zaman lafiya, kai a takaice ita da bataso AB ya kusance wata 'ya mace idan ba ita ba. "Kwantar da hankalinki ƙawata kamar kin yi bako ya mutu akwai wani shahararren malami wanda Ruby ta taɓa haɗani dashi ya yi min aiki akan Alhaji mussadik shi ne ya yi min aiki da na mallake sa, nake juya sa tamkar masa a tanda na dusashewa tauraron matansa na gida, baya gani kowacce mace a gabansa sai ni kaɗai. Ki shirya na kai ki gunsa matsala da damuwarki sun gama zuwa ƙarshe. Cike da farin ciki Sadiya ta amince domin ko mamin ta taje gun nata malami da nata bukata ita ma me zai hanata zuwa, Sadiya ta azalzale Sarah sai da tashi suka tafi batareda sun jira an ƙarasa lectures ɗin ba. Cikin tsananin rashin imani da tausayi Sadiya take korawa malamin bayani buƙatarta "Malam so nake idan da hali hana faruwar wannan aure da zai yi sannan kuma a saka shi ya saki ƙanwata da yake aure. Malamin bai ce komai ba ya share ƙasar dake cikin tray ɗin dake girke a gabansa ya yi 'yan zane-zanensa ya sake ɗaukar dogon casbinsa ya shiga ja yana furta kalaman tsafi. da baki can ya aje casbin ya gyara zamansa tare da fuskar Sadiya da Sarah da kyau "Wannan aure sai ya faru amman za mu iya kashe sa daga baya sannan kuma ita ƙanwarki da kike zance ta ƙasa ta nuna min babu ko burbushinta a zuciyarsa,wannan Rumaisa ɗin ita ce ta cika ciki da wajen zuciyarsa yana bala'in sonta saboda haka akanta za mu mayar da hankali domin yanzu haka mahaifiyarta asiri ta yiwa mahaifin ita Rumaisa ɗin ya amince da aurenta da Abba amman kwata-kwata bayason Abba da 'yarsa. Sadiya taja ƙarfaffiyar ajiyar zuciya"Malam idan da hali a sakawa Rumaisa zubar jini ta yanda Yayanmu ba zai taɓa kusantarta ba, sannan ka haddasa musu fitina a tsakaninsu su kasa zaman lafiya. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/11, 2:31 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 065. Sadiya basu bar wurin malam ba har sai da ya tabbatar da zai yi aikinta. Anan ta zube masa dubu ɗari yace idan aikin ya kankama zata dawo ta cika sauran, Sadiya tace masa kar ya damu batada matsalar kudi a mota Sarah ta dubeta tana faɗin "kina son yayan nan naku dayawa. Juya ido Sadiya tayi ta saki murmushin gefen baki tana kare rike sitiyarin motar cikin kwarewa kafin ta numfasa tana faɗin "ban taɓa son wani mahaluki a rayuwata ba Sarah kamar yadda nake jin son yayanmu,komai da kika sani zan iya yi dan ya zama nawa ni kaɗai, dariya Sarah tayi tana faɗin "Allah ya mallaka maki shi kawata. "Ameen ke dai.!Allah ya karbi addu'arki. "Yanzu ina muka nufa?"sarah ta faɗa tana kallon Sadiyar dake tuki "Ni kaina ban sani ba Ina dai bukatar jin kaina a sama ina bukatar na jini shiru kuma hostel hayaniya yayi yawa,ko mu biya ta cikin gari na amshi cocaine wurin TK sai mu kama hotel ina bukatar kaina ya dauki caji. "Amman fa Ba zan dade ba akwai babban bakon da zan yi yana hanya daga Kaduna. Da haka suka karasa cikin gari wurin TK ta karbi sako sai suka dauke hanyar hotel ɗin da take buƙata. Ta tusa soyayyen dankali da ta saka huwaila tayi mata na Hausa sai kuma miyar source ta tarugu wacce taji kayan haɗi,ga cup ɗin tea a gefe,a duk lokacin da ta tuna yanayin da suka kasance tareda yayanta sai taji wani abu na bin duka jinin jikinta. Wani irin yanayi ta tsinci kanta ciki wanda ba zai fassaru ba gashi tsoron yayan nata ya hanata zuwa taga halin da yake ciki,door bell da suka ji ana dannawa Huwaila ta fito daga kitchen da sauri baki ta buɗe tana kallon Aydah da komai bataci ba "wai har yanzu zazzabin ne?"daga kai kurum Aydah tayi kici ko kaɗan ne sai kisha magani Aydah bata dai ce komai ba Huwaila ta nufi kofa ta buɗe baƙin fuska tagani Aunty Raliya dake waya tana gamawa ta karaso tana yiwa Huwaila wani kallo sai da ta shaki numfashi ta fesar cike da izza tace."mun zo da masu haɗa kayan amarya za a shigo dasu. Sai da zuciyar Huwaila ta kusa fitowa daga kirjinta Aunty Raliya bata tsaya sauraren Huwaila ba,tayiwa mazan dake bayanta umurni akan suje su fara shigowa da kayan a sama zasu sameta dan ranar sun zo ganin gidan,tun da Aydah taga Raliya Madawaki ,ta shigo cikin parlor take kallonta da mamaki tana ta son ta tuna inda ta san fuskar ta sai kuma ta manta ganin ta nufi up stairs tamkar wacce tasan gidan,da wani irin kallo tabi Raliya har ta bacewa ganinta wani irin miƙewa tsaye tayi tana bin upstairs ɗin da kallo kafin ta mayar da dubanta akan Huwaila ta kankance ido tana faɗin ."wacece wannan Aunty huwaila ?"shiru Huwaila tayi kafin tace ''wanda zasu jerawa Rumaisa kaya ne. Wani irin dokawa kirjin Aydah ya shiga yi da ido take bin Huwaila tana son tantance mai kalmar jere ke nufi, kafin ta dawo cikin hankalinta a birkice Aydah ke faɗin."duk fadin ƙasa bai masu ba sai sun je sama?"bangaren yayanmu fa Aunty Huwaila."ita ma Huwailar shiru tayi tana Rasa mema zata cewa Aydah jin Huwaila tayi shiru yasa Aydah ta nufi stairs ko gani ba tayi saboda ɓacin rai har wani dishi -dishi take gani kai tsaye ɗakinta ta nufa wayarta ta dauka har hawaye sun fara Rolling cikin fuskarta lambar Yaya Abba tayi dialling,har tagama ring bai daga ba kara kira tayi nan ma shiru tana kara kira akace a kashe Wani irin kuka ta fashe dashi tamkar wata karamar yarinya ta tsani wannan Rumaisa da duk abun da ya shafeta bata tunanin zata taɓa son Rumaisa har abada. Wani irin haushin yaya Abba yazo ya danne mata zuciya lokaci ɗaya,meyasa meyasa duk fadin ƙasa bai isheta ba sai anan? Ana nufin kayansu za'a kwashe a saka mata nata.wannan karon babu abun da ke cikin kanta sai Siyama da ta faɗo mata lokaci ɗaya,lokacin da Siyama ta daga wayar tamkar ma bacci take sai dai kukan da Aydah take yi ta cikin wayar yasa tayi saurin miƙewa zaune,tana murza idanunta Cikin tashin hankali take faɗin "menene ko baki da lafiya ne?"nan ma Aydah still shiru tayi sai kukan da take yiwa Siyama din tamkar zata fasa mata dodon kunne."Aydah zan kashe wayata tunda bazakiyi magana ba. Siyama ta faɗa a mugun hasale cikin kuka Aydah ke baiwa Siyama labari ta karashe da faɗin "Da gaske yayanmu bai hakura da wannan Rumaisar ba Aunty siyam.!"jin nake kamar na kashe kaina zuciyata ciwo take min!"da sauri Siyama tace kina jina Aydah "idan kina ɗaki ke kaɗai ki tafi wurin Aunty Huwaila yanzun nan zan karaso kina jina?" Daga kai kurum Aydah tayi yanayin da take jin kanta aciki ba zai barta ma tayi magana ba Da sauri Siyama ta diro daga kan bed kai tsaye wanka ta shiga agurguje take yin komai ko tunanin karin kumallo batayi ba ta dauki karamar handbag dinta ta zuba duka abubuwan da zata bukata ,kai tsaye ɗakin Mami ta shiga ta tura kofar ɗakin da sallama,Mami ta amsa tana kallonta tsaye Siyama tayi ta rasa me zata faɗawa Mami dan har ga Allah bata taɓajin haushin yayansu ba irin wannan lokacin ace duk faɗin."gidan Rumaisa bazata zauna a kasa ba sai a sama.wannan ai zalunci ne dan anga Aydah ƙaramar Yarinya baya na nufin bata san Abun da take yi ba. Zama Siyama tayi tana tauna maganganun da zata faɗawa Mami, can dai tayi karfin halin faɗin."Mami dama zanje gidan Ahdah ne,idan kin isa ki gaisheta."Mami ta faɗa kai tsaye Sosai Siyama ta sha mamaki dan batayi tunanin Mami zata barta taje cikin sauqi ba,dan a kwanan baya Mami har rantsuwa tayi akan idan siyama taje gidan Aidah bada yawunta ba Allah ya isa.!!"kuma har ga Allah tayi furucin ne saboda idan aidah bata ganin kowa kusa da ita bata ganin su Siyama ,na zuwa wahala zai saka ta gudu da kanta ,sai dai yanzu a kwana biyun nan Aydah na manne aranta karfin hali kawai take Yadda ta tsani Rumaisa kamar yadda ta tsani mutuwarta. Wani bangare tana taya yar tata jimani wai kamar aidah ce za'ayiwa kishi abar maza kawai munafukai !!"yan tofin Allah tsine...!"sallama Siyama ta yiwa Mami da har takai bakin kofa ta dakatar da ita ta ce ta debi dambu ta kaiwa Aydah ,murmushi Siyama tayi tana faɗin "to ta gode Mami,sanin murmushi munafurci ne Siyama ta ke yi yasa Mami ta bita da kallo,koda Siyama ta iso Aydah na a ɗakin Huwaila tayi kuka har ta godewa Allah da ta gaji sai tayi shiru sai yawan ajiyar zuciyar da take saukewa,da sauri Siyama ta karasa wurin Aydah ta kira sunanta tana riƙota jin muryar Siyama yasa Aydah ta shiga buɗe idonta da suka yi mugun nauyi, Siyama ta rike Aydah a jikinta kamar jira Aydah ke yi ta rike Siyama tayi tana kwantar da kanta cikin kafadarta wani kuka mai cin rai ta fashe dashi dakyar Siyama ta gaisa da Huwaila ?"tana tambayar Aydah tayi karin kumallo?"girgiza kai kurum Huwaila tayi "idan babu damuwa dan Allah Aunty Huwaila a kawo min wani ni da Aydah a ɗakinta muci ki haɗamin bakin shayi da haka taja hannun Aydah suka nufi sama tana jin hayaniyar masu haɗa kayan Rumaisa a parlor da sauri Aydah ta shige ɗakinta wani irin kuka mai cin rai na kwace mata anan ta zube kan rug ta haɗe kai da gwiwa ta shiga rera kuka shiru Siyama tayi tana kallon little sis dinta wani abu taji yana karyewa acikin zuciyarta ƙarasawa tayi tana dago Aydah ta haɗata da jikinta tana dan bugun bayanta alamar rarrashi. "Be a gud girl mana baby Aydah."har zaki daga hankalinki ban cin kin san yayanmu yafi kowa sonki me akayi-akayi Rumaisa ai bata isa ta raba ki da yayanki ba. Cikin kuka da majina Aydah take faɗin."Ban cin gashi nan a bangarensa ake mata jeren ɗaki, Kenan ma a ɗakin nasa zata rika kwana koni dake kanwarsa ai baya kwana tare dani sai ita, wallahi ba zan yadda ba ranar da ta gwada kwana a bangaren yayanmu zata ga hauka. Aydah ta faɗa sounding so very jealousy a muryarta,sau ran kaɗan Siyama ta saki dariya sai dai babu halin yinta tasan rigimar Aydah ba mai sauki bane yayansu kawai ne yake iya handling dinta ko Mami da Daddy,basa iyawa Siyama ta langwabe kai tana faɗin "baby Aydah an girma daman kina kishin yayanmu har haka. Shiru kawai Aydah ta yiwa Siyama ,tana tare hawayen da suka kasa tsayawa cikin fuskarta komai na duniyar bata jin dadinsa. Huwaila ce ta kawo masu kayan karin kumallo dakyar tasa Aydah ta sauko suka yi karin kumallon su a tare kafin ta bata sakon mami, cike da farin ciki Aydah ke faɗin "Mami ce ta baki ki kawo min da gaske yaya Siyam.?"ta faɗa da wani yanayi dauke a muryarta Juya ido Siyama tayi tana sakin murmushi take faɗin."da gaske nake baby sis. "Ni naji ma ina so naganta kawai mu tafi gida yaya Siyam bana son ganin mutanen nan,da sauri Siyama ke faɗin "Ba gashi nazo ba muyi zaman mu anan mana,anjima kaɗan mu fita yawo daman zan je gidan Saudah kinga sai mu tafi ku gaisa duk sanda muka haɗu a school sai tayi zancenki. Murmushi Aydah tayi ta mayar da hankalinta wurin cin dambunta tana ta so ta yiwa yaya Siyam zancen yadda yaya Abba ya sha mata nono bata san ta inda zata fara ba ko Huwaila kasa fadawa tayi dan wata irin kunyar Huwaila take ji,dan gyaran murya Ahdah tayi tana kallon Siyama kafin tace daman yaya Siyam akwai tambayar da nakeso nayi maki dan Allah. "ina jinki little sis. Aydah ta shiga ja fingers dinta sai kuma ta sakasu a baki tana ɗan cizawa. "Wannan kallon fa Aydah?" "Ban san ta inda zan fara bane Yaya Siyam. Siyama ta warewa Aydah ido da sauri Aydah ta rufe ido tana sakin yar dariya , dariyar Siyama tayi ki faɗamin bana son gulma. Siyama ta faɗa tana kallon Aydah ɗin,kin min alƙawari dagani sai ke ?daman tambaya kawai ce zanyi da kema ba zan faɗa maki ba sirri na ne. gyaɗa kai Siyama kurum ta shiga yi ta zubawa Aydah ido tana sauraren me zatace "dama jiya ne uhm ummm to ki daina kallona ido cikin ido yaya Siyam. Da sauri Siyama ta dauke kanta. "Ba jiya bane sai yayanmu yayi min kiss ya sha min no.....da sauri Siyama ta rufe bakin Aydah tana wani irin zaro ido,baki da hankali wannan yarinyar da gaske bakida hankali "Ubanwa ya faɗa maki ana faɗin,wannan maganar "Tamkar Aydah zata yi kuka ganin yadda Siyama ta rude lokaci ɗaya. "Nifa daman tambayarki zanyi ai naga shi yayana ne Right?"yace babu aure a tsakaninmu kuma a islamiyya ana faɗa idan babu aure tsakaninka da mutum bai kamata.....!"da sauri Siyama ta katseta ta gano dai har yau kanwar tata doluwa ce da alamar babu Abun da ya shiga tsakaninta da yaya Abba ,har lokacin kallon juna kawai suke wani irin tausayin kanwarta ya lullubeta musamman idan ta tuna wacce za'a kawo mata a matsayin kishiya. "Duk karatun littafan Hausan da kike har ma dana turanci sun tashi abanza, waya faɗa maki yaya Abba ba mijinki bane?" Siyama aje kunya tayi ta soma yiwa kanwar tata bayani sai taga Aydah ta tura baki tana faɗin "nifa duka nasan waya'annan abubuwan yaya Siyam ni wallahi tsoron yayanmu ma nakeji tun jiha baki ga yadda ya birkice ba kamar mai dauke da jinnu akansa. Baki sake Siyama ke kallonta "Auh Allah ?"tsoronsa kike ji kou?"shikenan tunda bakya so ya taba ki idan Rumaisa tazo sai ya taba ta ai ta ba za ta ce bata so ba. Nan take Aydah ta dauke wuta tamkar an aiko mata da sakon mutuwa yadda take tsare Rumaisa da ido yasa tace "Ehhhh! kina kallona gaskiya na faɗa sai ita ya rika tabata tunda tsoro kike ji. kwanciyya Aydah tayi tana wani juyawa Siyama ɗin baya da alamar dai maganar Siyama ta bata mata rai har ta hango yadda Rumaisa zata hau jikin yayanta haushi duk ya gama cikata ita ko hannun Rumaisa bata son ya rika barantana yayi wani abu da jikinta. Dakin Siyama ta rika kallo ta sauke numfashi tana faɗin."duk yau baki share dakin nan ba Aydah kalli kan gadonki? kamar kinyi dambe akansa halinki na nan ba zaki taɓa canjawa ba kinga idan Rumaisa tazo sai ta yiwa yayanmu gyaran ɗaki. A wani irin zabura tayi ta mike tana kallon Siyama,sauran kaɗan Siyama ta saki dariya da gaske little sis din nata she's madly in love with Yaya Abba.! addu'a Siyama ke Allah yasa shima yayan nasu yana jin kwatankwacin abun da Aydah ke ji akansa. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/11, 2:41 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 066. Sai da Siyama ta taimaka mata suka gyara ɗakin aka share akayi mopping har toilet ta kunna turaren wuta ,bayan sun gama Siyama ta koma ta kwanta ganin Aydah still tana tsaye tamkar wacce aka saka tayi tsaye ɗin. "Ba wankan zaki shiga ba rana nayi,na fiso na koma gida da wuri?" Siyama ta faɗa tana kallon Aydah ɗakin yayanmu zanje na gyara. Ɗan buɗe ido Siyama tayi kafin ta mike daga kwance da take tamkar wacce ta tuna wani abu tace "To muje ki gyara masa mana. Koda suka shiga su Aunty Raliya na a parlor ana saka kujeru dama daga Siyama har Aydah babu wanda ya kulasu sukayi hanyar master bedroom ɗin yayansu da ido Aunty Raliya tabisu ta rasa ma wacece matar Abban acikinsu. tunaninta yafi karkata akan ko Siyama ce. Siyama sai tsaki take ita ɗaya, idan banda wulakanci duk parlor gidan nan ba'a ga inda za'a aza mata kujeru ba sai a bangaren yaya Abba dan salon iyayi meyaci parlor kasa yaushe ma aka zuba kayan, ita dai Aydah batace komai ba kan soofa ta koma ta zauna duk ranta a dagule ta rasa meke mata dadi."auh zaunawa ma kikayi ko kin fasa?"ki shiga ki wanke masa toilet ki bari na gyara gadon,ai gara ɗakin yaya Abba da dakin ki dan nasa yafi tsari duk abun da yayi amfani yana mayar dashi wurinsa. Sai kusan 2 na rana suka yi shirin fita har ɗaki Aydah ta samu Huwaila lokacin ta kammala abincin rana tana kwance kawai tana hutawa. "Aunty Huwaila zamu fita da yaya Siyam Amman ba dadewa zamu yi ba, Huwaila tabi Aydah da kallo tana cikin riga da skirt na Atamfar kalar blue da fari ajikinta tayi kyau sosai kamar ka saceta ka gudu sallama suka yiwa Huwaila, acikin motar Siyama ta kunna wakar hamisu breaker mai suna(BURI)shiru Ahdah tayi gami da kwantar da kanta cikin seat ɗin motar tunanin yayanta duk ya cika ta yau koda ta tashi bata gansa ba. Huwaila ma tace mata bata ji fitarsa ba wata irin kewarsa ce ke zagaye mata zuciyarta babu wanda yasan yana office dan rufe kansa yayi sai wuraren la'asar da yayi bacci ya tashi ga kansa da yayi masa wani irin nauyi ga mugun jirin da yake ji sai lokacin ya tuna da ko break fast bai yi ba dafe kansa yayi yana karanto addu'a dan neman samun nutsuwa ,sai da ya kai minti goma a haka ya lalubi car key ɗinsa da ya aje ya mayar cikin aljihun wandonsa, ta baya ya fice daga office ɗinsa addu'a daya ya ta maimaita wa Allah yasa kar ya hadu da wani a parking lot Allah ya karbi addu'arsa har ya fice babu wanda ya lura sai maigadi da ya buɗe masa gate sai lokacin ya kunna wayarsa ya ajeta messages sun gama shigowa wanda duk na Rumaisa ne sai kuma na MTN. Saƙon Rumaisa na farko shi ne "Habeebi inata kiran wayarka a kashe hop Lafiya?"sai kuma na biyu su Aunty Raliya zasu zo da mai jera kaya, Na uku."ka sakani a damu dan Allah ka kunna wayarka muyi magana. haka ya ta karanta sakonanta duk na tambayar lafiarsa ne,dilaliing lambarta yayi tamkar jira take tana shiga ta dauka yana jin yadda take jan numfashi tana saukewa cikin shagwaba take faɗin."ba ka saba kashe waya ba meya samu wayarka tun safe.?"nan ma shiru yayi babu amsa shi ya daga hankalin Rumaisa?"baka da lafiya ne hayati. "Ya kike?"ya faɗa da muryar da ta kusan karya zuciyar Rumaisa,kamar baka da lafiya Are you really owk?"Lafiya lau muryarka wani iri kana ina haka?"kamar kana driving,ina hanya Rumaisa idan na isa zan kiraki. Bai jira me zata faɗa ba ya sauke wayar,dama bukatarsa taji lafiyarsa kuma taji baya son magana da kowa da komai duk lokacin da ya tuna abunda ya haɗasa da Aidah kwakwarsa hargitsewa take baya ma son ya tuna wani tsakar kansa da na Aydah yake jin yana sauka cikin zuciyarsa,aodaddafe ya karasa gida jikinsa gabaki ɗaya ciwo yake yana kuma bukatar yin wanka Huwaila taje ta buɗe masa kofa lokacin da ya shigo gidan gaishesa tayi batareda ya haɗa ido daita ba ya amsa kafin yace yana bukatar bakin tea ta soya masa egg ta baiwa Aydah ta kawo masa sai da zuciyar Huwaila ta tsinke.cikin rawar murya take faɗin. "Yayanmu Aydah sun fita da Siyama.!"wani irin kallo ya juya yana yimata tamkar itace Aydah Wanda Huwaila tasa hanjin cikinta sun fara ya mutsewa bai kara cewa komai ba ya wuce sama direct zuwa lokacin su Aunty Raliya sun gama jerawa Rumaisa kayanta,bin parlor ya riƙa yi da kallo yadda aka canja sa lokaci ɗaya har aransa yaji tsarin wancan kayan yafi yimasa kyau akan wannan ko kaɗan baiga abunda ya burgesa ba acikin parlor sai window side na hotonsu da aka kafa a parlor wanda yasan aikin Rumaisa ne ire-iren hotunan da take dauka dashi ne a gidansu ta cira ta bada aka wanka mata ,hoton yayi kyau sosai duk da Rumaisa kawai ke murmushi a hoton kai tsaye master bedroom ɗinsa ya wuce,yana bin bedroom ɗin da kallo sai Ƙamshin turaren wuta ke tashi kai tsaye ransa ya faɗa masa aikin Siyama ne dan yasan Aydah son jiki ba zai barta ta gyara masa daki ba ita ma neman me gyara mata take dan haka yake gyara abunsa bai taɓa bai wa Huwaila damar shigowa bangarensa ba. Sai lokacin ma ya tuna fitar da Siyama ɗin tayi da Aydah ransa yaji yana wani irin ɓaci daukar wayarsa yayi ya shiga kiran Siyama har ta gama bata dauka ba yana kara kira ta dauka da cikakkiyar sallama bai tsaya karbar sallamarta ba yake tambayarta ina suka tafi?"da izinin wa zata zo har gidansa ta dauki Aydah su fita yawo. yadda Siyama taji yana faɗa tamkar zai canyeta a wayar da alamar ransa a ɓace yake taji idanunta sun ciko da hawaye,minti goma sha biyar Siyam ki dawo min da matata idan ba haka ba sai nayi mummunan saɓa maki. Da haka ya sauke wayar sai huci yake tamkar wani mayunwacin zaki mai jin yunwa, hannu yasa cikin sumar kansa yana ta hargitsawa, toilet ya shige yana sakarwa kansa ruwa akai,baya son tuna wannan yanayin shida Aydah ya hana zuciyarsa hutawa daga bugawa tun a mota Aydah taga yanayin Siyama ya canja dan bata nan lokacin da tayi wayar ta shiga toilet. Yaya Siyam baki biya Dani siyan ice cream din ba kuma fa kinyi alkawari. "Ki kira mijinki sai ya siyo maki ni gida zan wuce yammah tayi ,rai a ɓace Aydah ke faɗin "babu kyau saba alkawari yaya Siyam."ita dai Siyama banza tayi wa aidah a motar suna ƙarasawa gidan AB tayi parking motarta a bakin gate batareda tayi horn ba mai gadi ya bude,da mamaki Aydah ke faɗin."kin fasa kwana anan ɗin "sai wani lokaci Siyam ta faɗa rai a haɗe,haushi ya kama aidah ta fice daga motar ta nufi get.tunda ta doshi cikin compound ta hangi motar AB taji hanjin cikinta na yamutsewa,tamkar tayi kuka take faɗin "shine yaya siyam tasan yayanmu ya dawo ne shiyasa taki shiga,kasa bi ta cikin gidan tayi zagayawa tayi ta cikin balcony kofar kitchen tana ta addu'a Allah yasa babu key ajikin kofar tana rika handling kofar ta Murda tana turawa taji ya bude wata irin ajiyar zuciya ta sauke dai dai me wanda tayi ido biyu dashi yasa gabanta yayi mummunan bugawa ya harɗe hannunsa akan kirjinsa yana bin ta da wani irin kallon da tunda tayi wayau bai taɓa yimata kalarsa ba jin take tamkar ta juya,hawaye taji suna cika idonta lokaci ɗaya jikinta ya shiga kadawa duk takun da yake yana zuwa gabanta da yadda kalar bugun zuciyarta ke canjawa sai da ya karaso har inda take yana haɗe filin da yayi saura a tsakaninsu ga bango Aydah ta nanne tana tattare jikinta wuri ɗaya,kallon yadda jikinta ke kadawa yake ta rufe idonta hawaye na forming akan fuskarta, fuskarta kawai yake bi da kallo tamkar mai son gano wani abu acikin fuskartata har ya tsayar da idanunsa akan bakinta wani irin bugawa zuciyarsa keyi pink din janbakin da ta shafa yaji yana wani irin jansa tamkar an jona masa wutar lantarki yadda jikin nasa ke kadawa yadda zuciyarsa ke umartarsa akan yayi abunda gangar jikinsa ke so lokaci ɗaya taji an wani rike kafadarta kara ta saki tana buɗe idonta a tsorace cikin rawar murya da banbaki take faɗin ."dan Allah Yayanmu kayi hakuri tarefa da yaya Siyam muka fita kuma na kira wayarka baka dauka ba ta karasa cikin kalar shawagabar da ta kusa rikita sauran lissafin dake cikin kansa Jada baya ya shigayi murya a shake yake faɗin "ta kawo masa bakin tea yanzu.juyawa yayi ya fice daga kitchen din.kunkuni ta shigayi aranta tana faɗin "na zata Rumaisa zaka kira ta kaima."ta faɗa rai a ɓace tamkar yana ganinta dakin Huwaila ta shige tana tambayarta bakin tea yayanta huwaila sai tambayarta take ina siyama din."a gajarce take faɗin."ta wuce juyawa tayi ta tafi cikin dinning area ta haɗa masa bakin tea ta dauki wainar kwai acikin plate ta nufi sama.tana shiga cikin parlor nasa tayi wani kicin-kicin da fuska sai bin parlor take da kallo har lokaci Abba na zaune cikin parlor ya dafe kansa da duka hannu biyu daga shi sai tree quarter da shirt marar nauyi,ƙarasawa tayi ta ɗora masa akan side table hankalinta duk yana kan window side din hoton yayanta da Rumaisa ashe bata aza cup tea din daidai ba jin kawai tayi ya dawo mata a kafa wani irin kalar ihu ta saki tana zama a kasa tana rike kafarta tamkar wacce aka yanka."a gigice AB ya karaso wurin yana rika kafar wani irin kuka ta fashe dashi ga kukan ruwan zafin data kona kafa dashi gana kuma kan me Rumaisa zata wani kafa hotonsu a parlor yayanta."kukan da take yaketa har gitsa sa har yana kasa controlling din fushinsa ya wani daka mata tsawa yana fiddo mata da manyyan fararen idanunsa yana faɗin."tayi masa shiru. Tsit tayi tana haɗe kukan sakin kafar yayi ya miqe tsaye ya nufi master bedroom dinsa bai jima ba ya fito da cream a hannunsa dukawa yayi ya shiga shafa mata saboda takaici jin take kamar ta fisge kafar har ya gama hawaye basu daina zubar mata ba daman yana sakin kafar tayi kokarin mikewa tsaye ganin bata son tafia yasan ta fiye raki ba Tareda wani tunani ba taji ya dauketa dukanta ya fice daga parlor kai tsaye ɗakinta ya nufa daita har kan gadonta ya kaita ya aje,ya juya batareda yace mata komai ba ya fice daga dakin daman yana fita ta kifa kanta a pillow ta fashe da wani irin kuka mai sosa rai.tayi kukanta ta gaji a haka tayi bacci sai bayan sallar magarib jin shirun yayi yawa yasa huwaila ta taho sama.kai tsaye dakin aidah ta buɗe,ganin tayi har lokacin tana bacci dakyar huwaila ta tasheta ganin yadda idonta ya rine lokaci ɗaya Tasan kuka tayi sai dai bata tambayi dalilin kukanta ba tace mata har angama sallah. An kusa fara series ɗinki."(unfortunately love)daman aidah tana kalla a zeeword kullum.ita yau yadda take jin zuciyarta a cunkushe bata ma da karfin yin wani kallo.huwaila na barin dakin itama ta nufi toilet... #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/12, 3:42 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 067. Bayan Aydah ta fito daga wanka ta shimfida praymat tayi sallar magarib tana sallamewa ta sunne kanta tsakanin cinyoyinta ita ba kuka take yi ba amma gara ma ace kukan ne take yi a irin raɗaɗi da ƙunci da take ji a zuciyarta. A duk sanda ta tuna da cewa saura kwanaki uku Rumaisa ta shigo gidanan a matsayin matar yaya Abba sai ta ji wani abu ya dunƙule mata a ƙahon zuciya. Tana nan zaune tana tufka da warwara har aka yi kiran sallar isha ta tashi ta gabatar da sallah, jikinta a mugun mace ta nufi closet ɗinta ta ciro riga da wando na bacci ta saka kana ta sauka ƙasa motsin Huwaila ta ji a kitchen shiyasa kanta tsaye ta wuce kitchen ɗin "sannu da aiki aunty Huwaila fruits salad ake haɗa mana?" "Uhm! Yayanmu ne ya umarce ni da na haɗa masa. "To nima a haɗa ni zan sha. Ƙarasawa tayi kusa da Huwaila ta tayata yanka fruits ɗin tare suka yi komai bayan sun kammala Huwaila ta zubawa AB nasa acikin matsakaici bowl 🥣 tare da spoon ta miƙawa Aydah ta ce ta je ta kai mishi a ɗan tsorace Aydah ta ja baya tana faɗin "Ki rufa min asiri aunty Huwaila ɗazu ma da naje kai masa black tea na je aje masa bisa tsautsayi na ɓarar masa ya zuba min a ƙafana yanzu haka wurin yana min zafi. Banaso naje kuma na sake maimata kuskure da nayi ɗazu. Murmushi Huwaila ta yi tare da maida bowl ɗin kan kitchen island ya riƙo hannayen Aydah, tayi ƙasa da murya "Haba Auta ya kike yi abu kamar marar wayau yanzu idan ba ki dinga shisshige masa so kike sai wacce kodaddiyar ta zo ta mamaye shi?" Cikin sauri Aydah ta shiga girgiza kanta kamin cikin shagwaɓaɓbiyar muryarta ta furta "Wallahi aunty Huwaila da ina da dama ko ɗan yatsan yayana ba zan bari ta taɓa ba ballantana har ta kai ga mamayarsa. "To idan haka ne kuwa yi maza ɗauki bowl ɗinan ki kai masa yadda kike zuba wannan ƙamshin na tabbata sai Yayanmu ya kusa zaucewa. "Kai aunty Huwaila!! Aydah ta faɗa cikin shagwaɓa. "Yoo ai gaskiya na faɗa ban da ma namiji da shege gane-gane wanda keda yarinya ɗanya latsaf me zai yi da kodaddiyar mace irin Rumaisa sai ɗan banza fari kamar zabiya. "Ba ma nata ne kaɗai ba tana haɗawa da na kanti. Aydah ta faɗa tana cuno baki, Huwaila dai ta gama fahimtar mutuniyar ta, ta kishi ne ke cinta. Aydah ta ɗauki bowl ta nufi Parlorn AB, tana tura ƙofa yana zaune akan three seater da remote a hannunsa da sallama ta shigo ya amsa tare da yada ganinsa akanta, ya kasa ɗauke idanunsa akanta yayin da Ƙamshin turaren ta ya cika ƙofufin hancinsa, Aydah ta nufi side table ta ajiye tana faɗin "barka da hutawa Yayanmu sai ƙyali angwaci kake yi. Zaro idanuwa AB yana kallon ɗan mitsitsi bakinta da ya furta masa wannan magana daga bisani kuma ya galla mata harara "Baby yaushe raini ya shiga tsakanina dake da za ki faɗamin magana irin wannan ko ni sa'anki ne?" Aydah tasa dariya ta tako tare da zaunawa kan centre table dake gabansa "Kai Yayanmu daga faɗar gaskiya to Allah ya ba ka haƙuri amman duk wanda yaganka dole zai faɗi kwatankwacin abun da na faɗa. "Kowa zai iya faɗa amma ban dake saboda ni ba abokin wasar ki bane. "Babu wani nan Yayanmu kawai dai ni ka tsaneni shiyasa ka faɗi haka da adane wani ko wata yace dani akwai ranar da za ta zo yayana ya tsaneni ya nuna min zazzafar kiyayya duka ƙaunar da yake min za ta rikiɗe zuwa kiyayya, ba zan yarda ba asalima da akwai takobi a hannuna ko a kusa dani sai na fille kan ko waye ya faɗi hakan idan kuma wuka ce a hannuna ba abun da zai hanani gimtse masa harshe. Yayanmu ban gino akan soyayyar uwa da uba ba kamar yadda na gino akan soyayyarka, duk da na taso a gaban iyayena amman bansan daɗi ƙaunarsu ba, kamar yanda nasan daɗin taka. Shin Yayanmu ka raine ni a bisa so da ƙaunarka don kawai wata rana ka juya baya?" Yadda Aydah take magana cikin rauni da kariyar zuciya ga hawaye kwance akan kamatunta dole duk rashin imanin mutum ta bashi tausayi koda ɗan ƙanƙani ne,balle irin AB da Allah ya zuba masa tausayin mata da ƙanana yara sosai kalaman Aydah suka yi tasiri a jikinsa shi kansa yana yawan tambayar kansa da kansa meyasa yake jin tsanar Aydah wanda can farkon aurensu baya jin hakan akanta rana ɗaya ya waye gari cikin wannan sabon al'amari akanta, wanda da za a rutsa shi ba zai iya faɗin dalili da yasa ya tsane ta ba. Hannunsa ya kai jikin centre table ɗin da take zaune ya matso dashi gafda shi sosai gaban Aydah ya faɗi yanda taga ya matso da table ɗin izuwa gabansa ya haɗe tazarar dake tsakaninsu, ya saki table ɗin ya kama dukkan hannuwanta ya matse cikin tafin hannunsa duk da yana jin wannan al'amari da yake ji a duk sanda kusanci irin wannan ya shiga tsakaninsu amman ya danne zuciyarsa har ya shiga kwararo addu'a a ƙasan zuciyar tasa, abin mamaki sai ya ji wannan abun yana fita a hankali tamkar dai wuri da ya yi kura ana kade shi da tsintsiya "Ki yi haƙuri dani Baby Aydah nima a can kasan zuciyata bana jin daɗi yadda nake treating ɗinki ban kuma san me ya hau kaina ba da nake miki hakan, amman ki tayani da addu'a Allah ya sassauta min koma mene ne ya kuma dawo mana da kyakkyawar alaƙarmu ta tun asali. In shaa Allah ba zan sake bari shaidan ya yi wasa da zuciyata akanki my Baby. Wani irin daɗi ne ya lulluɓe Aydah wanda batasan lokaci da ta miƙe da sauri ta faɗa jikinsa ta zagaye hannayenta a gadon bayansa, tana karawa kukanta sauti "Nagode Yayanmu, kalaman bakina ba za su ishe ni ba wurin bayyana maka irin farin ciki da ka haifar min, kawai dai zan yi maka addu'a Allah ya rufa maka asiri fil dunniya wal akhar Allah ya tsare min gabanka da bayanka Ubangiji ya haskaka zuciyarka da farin ciki marar adadi. Tsanani daɗin addu'arta yasa shi matse ta gam akan ƙirjinsa yana bubbuga bayanta,tare da wata sabuwar ƙaunarta da tasha banban da wacce ya gina zuciyarsa akai. "Amin thumma Amin! Kuma duk abun nan da kika roka min my little Baby Allahu ya ba mu su a tare. "Amin! Yayanmu mai kirki. Aydah ta faɗa da raguwar hawaye a idanunta, AB ya ciro ta daga jikinsa ta sake ƙanƙame shi "Bari nasha fruits salad ɗina Baby kin ga ɗazu kin ɓarar min da tea ban sha ba kuma yunwa nake ji. "Uhm! Yayanmu dan Allah ka barni na ji ɗumin jikinka kaɗan na manta when last da na samun irin hakan. Murmushi mai sauti ne ya subuce wa AB ya cire ta, ta ƙarfi sannan ya ja karan hancinta "baby yaushe kika koyi karya naga ko ɗazu da kaina na dauke ki, na kaiki ɗakinki za ki ce kin daina jin ɗumin jikina. "Yayanmu wannan daukar ta dole ce saboda na kona ƙafana. Sai lokaci ya tuna da zance konuwar ta, ta da azama ya kama ƙafarta yana dubawa ba abun da ya same kafar hamdallah ya yi tare da ɗaukar bowl ɗin fruits salad ɗinsa, sai ga AB idan ya yi one spoon ya ɗiba ya saka wa Aydah a baki tare suka shanye fruits salad ɗin tass! Sai da Aydah ta fara gyangyadi sa'annan AB ya rako ta ɗakinta, ta kwanta bai baro ɗakin nata ba sai da yaga baccinta ya yi nauyi ya tofe ta da addu'a ya sumbace forehead da lips ɗinta kana ya kashe mata wuta ya fice. A hotel ɗin da Sadiya ta kama sai da tasha sha kayan mayenta yi tatul sai da ta sha baccinta sannan ta nufo gida koda ta dawo babu kowa a main parlor da sauri ta wuce ɗakinta tana zuwa ta zube kan gado ta shiga baccinta na asara sai dab da magarib tashi shima Mami ce ta tashe ta, bayan tayi wanka da salolin da ake bin ta sai lokaci ta tuna da abun da malam ya bata ya ce ta nemi murhun gargajiya ta jefa laya acikin idan ta kama da wuta sai ta ciro ta,ta ajiye a ƙasa ta dinga ambatar sunan Rumaisa har sai laya ɗin ya cinye ya zama toka, babbar damuwarta inda za ta sami murhun gargajiya saboda Mami dai gas take aiki Kwata-kwata gidan Babu murhu idan kaga an yi amfani dashi sai ga sallar layya, sai lokacin Sadiya ta shiga damuwa ta rasa yanda za ta yi gaba ɗaya kanta ya kwance ta rasa mafita, ta ɗauki wayarta ta kira Sarah ta faɗa mata halin da ake ciki kai tsaye Sarah ta ce ta je kawai ta kona kan gas ai wuta duk wuta ce "Sarah kina gani idan na kona kan gas kina gani babu matsala aikina ba zai lalace ba?" "Ba abun da zai faru ƙawata ki jaraba kawai shima malam dan babu gas a gidansa ne ya shiyasa ya yi amfani da abun da yake da amma miye banbanci murhu da gas naga dai dukkun su wuta ne. "Haka ne ƙawata. "To jeki ki aiwatar da aikinki Please karki sake kirana bacci nake yi ko yanzu da ba don ke bace wallahi ba zan ɗaga ba. Kafin Sadiya ta bata amsa har ta kashe wayarta sai da dare ya raba tsakiya Sadiya ta fito ta shiga kitchen ta kunna gas ta ɗora laya akai da ya kama da wuta ta kashe gas ta ciro shi ta jefar kan tiles ɗin kitchen, ta shiga kiran sunan Rumaisa har sai da layar ta zama toka Sadiya ta fice abinta da sassafe da mai aikinsu ta shigo taga toka a tsakiyar kitchen tasaka tsintsiya da parker ta kwashe shi tass ta zuba a bin. Aydah tana tashi tayi wanka da sallah kana ta shirya cikin school uniform ɗinta, agurguje ta wuce school saboda tayi latti gashi yau za su kammala exams. *MASARAUTAR KUDU* Galadima ya dubi Ciroma da daurarriyar fuska yanayi kallo da kaɗai yake aikawa Ciroma ya isa ya bayyanar da irin matsanancin fushi da yake ciki "Ciroma kasani bari fa bari fa ba shegiya bace da ubanta idan ka nemi raina min hankali to kuwa za ka haɗu da fushina. Wani makirin murmushi Ciroma ya yi yana shafar geminsa"kai dai Galadima ka cika gaggawa kuma gaggawa aikin shaidan ce komai na duniya a hankali ake bin sa matukar ana so ayi nasara akansa Aliyu da kake gani ba kamar gama gari saura mutane bane. Cire shi daga sarautar sabon birnin kudu ba abu mai sauki bane da kunnenka, ka ji abin da boka mai Gundulelliya ya faɗa akansa idan har baso kake yi allura ta tono galma ba ka bari mu bi wannan al'amari daki-daki. "Mtss! Ciroma karka mayar dani wani sabon yankar rake mana. Meyasa shi bokan naka ba zai bi hanyar da yabi ka cimma burinka nima na cimma nawa?" "Wallahi Galadima kana da matsala bayani nake maka amma sai yi kake yi tamkar ba ka fahimci me nake nufi ba. Idan har muna so mu yi nasara akan Aliyu dole mu nemo wani da za mu bata shi a idanuwan al'umma abun da zai yi tarnishing image ɗinsa wanda hakan zai sa manyan fada su tsige shi da kansu ita fa siyasa 'yar zabo ce. "To naji amma kai a ganinka me za mu yi amfani dashi da za mu goga masa bakin fanti wanda zai sa har ya rasa kujerar mulkin sabon birnin kudu?" Shiru Ciroma ya yi tare da zurfafa tunaninsa can ya sauke ƙarfaffiyar ajiyar zuciya kamin ya ce "Dole ka yi haƙuri Galadima sai bayan an naɗa ni sarkin kudu sannan ne abubuwa za su kankama daga nan burinka zai cika. Wani mugun kallo Galadima ya watsawa Ciroma "Amman gaskiya Ciroma ka raina min da hankali shi ko ka manta tare za a yi naɗin ku kai da Aliyu?" "Ban manta ba Galadima dalilin hakan yasa nace ka ɗan dakata idan har ban cika maka burinka ba na zama sarkin sabon birnin kudu na yarda ka fallasa sirrina. Murmushi kurum Galadima ya yi mugu shi yasan makwancin mugu. *ALHAJI BELLO MADAWAKI MANSION* Yau ce ranar da ta kasance za a fara shagalin bikin Rumaisa da AB kamu za a fara yi a yau ɗinan a wani hadadden hall suka kama amarya Rumaisa tasha makeup tayi masifar kyau kamar ka sace ta ka gudu makeup artists ta musamman tayo haya ɗinta tun daga garin Lagos, komai na bikinta so take ya zama na musamman adade ana zancensa a kafafen sada zumunta(social media) saboda haka manyan kudade Ammi ta karɓa wuri Alhaji Bello madawaki. Gyara kuma tasha shi in and out har na fitar hankali kayan mata ba kalar wanda bata yi amfani dashi ba. Burinta ta gigita AB a daren farkon su. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/12, 3:46 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 068. Shagalin bikin na kece raini ake gudanarwa duk da AB ya nunawa Rumaisa rashin amincewarsa amman sai tayi biris dashi, ta cigaba da aiwatar da shagulgula ta. Sai da abun da ya dara dagulawa amarya lissafi bai wuce yadda aka yi kamu babu dangin ango ko ɗaya da farko abin bai dame ta sai da taji danginta da 'yan uwata sun fara korafi suna faɗar wannan wane irin aure ne ace babu dangin ango koda mutum ɗaya ne. Shi yasa bayan an kammala kamu ta nemi AB bayan ya zo ta fito daga cikin gida zuwa lokaci ta goge makeup ɗin da aka yi mata hatta da bridal outfit ɗin ta cire tasaka doguwar rigar cotton material, sai uban ƙamshi dake zubawa sai kace wacce aka tsamo daga cikin tanker turare. Ƙasancewar gidan nasu cike yake da jama'a 'yan biki shi ya hana AB ƙarasawa ciki sai ya tsaya wajen gate. Rumaisa ta buɗe front seat ta zauna tuni fitinannen ƙamshinta ya cika ƙofufin hanci AB don sai da ya ja ƙarfaffiyar ajiyar zuciya, ya ɗago idanunsa daga screen ɗin wayarsa ya sauke su akan fuskarta, tsanani gyaran jiki da tasha har ya saka skin ɗinta ya yi wani yellow-yellow "Barka da fitowa habibty kin ga yadda kika yi kyau abinki anya kuwa ba sace ki zan ba ina ji kamar ba zan iya haƙuri har zuwa jibi a ɗaura mana aure ga baki ɗaya kin damalmala min tunani. Dariya Rumaisa tasa yayin da kanta yaƙara girma tana ji cewa tafi sauran mata "Uhm! Ka ji dashi Habibi wai ciwon ajali a ɗan yatsa ɗazu da na tura maka pic ɗin kwalliya ta ai cemin ka yi an canzawa matarka kamanni ba za ka lamunta ba. "Ai da gaskiya ta Habibty an bi an fante min fuskar mata ta koma wata halitta ta daban ba dole nayi magana ba. Yanzu dai kika fito matar Abba sak! Dariya suka sa, su duka daga bisani Rumaisa ta dauko ainihin zance da yasa ta nemi ganinsa a wannan daren "Habibi ɗazu a wurin kamu mutane sai korafi suke yi babu dangin ka ko ɗaya musamman dangin Abbana. "Rass! Gaban AB ya bada wannan sauti nan da nan annuri da yake kan fuskarsa ya gushe, domin wannan wani miki ne da Rumaisa ta tado masa dashi shi wanda yake kokarin ya danne ya kuma manta dashi sai gashi ta tuna masa adaidai lokaci da yake cikin farin ciki domin aurenta shi ne cikar farin cikinsa. "Ka yi hakuri Habibi naga kamar maganar ta ɓata maka rai ni kaina ban ji dadi yadda aka dinga ce-ce-kuce akan rashin danginka ba, kasan idan ana shagalin biki irin wannan dole za a nemi 'yan uwan ango. AB ya ja dogon numfashi tare da saukewa cikin raunin murya ya ce "Yanzu Habibty da kika kirani kina min wannan zance me kike so nayi alhali kinsan ba dangin ne dani ba a tunanina za ki faɗa masu ainihin gaskiyar waye ni danginki ne ba wani ɓoye-boye da za ki yi musu. "Haba! Habibi so kake a dinga yamadidi da ni ace na aure marar asali gaskiya wannan ba shawara mai kyau bace ni kiran da nai maka gobe za a yi dinner ka yi kokari ko wadancan mutane da suke matsayin danginka kasa su, su zo mana amman gaskiya ba zan so ayi dinner ɗinan babu wani da za a gabatar a matsayin danginka. Sosai AB ya shiga kaduwa wani irin azababben tsoro ya lulluɓe shi har ya kasa furta komai sai faman kallon Rumaisa yake yi, ya kasa yarda Rumaisa ce ta buɗe baki ta kirasa da marar asali a tunaninsa idan kowa zai iya bugun ƙirji ya kirasa da wannan suna ban da ita ashe kallon kitse ne yake yiwa rogo. Tsawon zamansa da ita bata taɓa furta masa kalmar da ta tsaya masa arai ta tokare masa maƙoshi irin wannan. "Habibi magana nake yi ka yi shiru kar dai ka cemin maganar tawa ta ɓata maka rai naga cikin lokaci guda fuskarka ta sauya ba kamar yanda na zo na tarar da kai ba. "Ba komai Habibty kuma koda raina ya ɓaci ba abun da zan yi da ya wuce sauyawar fuska, sai dai ina so ki sani ba zan iya cilasta wa kowa ya zo bikinmu idan baya da ra'ayi tun sanda 'yan uwan Daddy suka san gaskiya waye ni da yawansu suka daina hulda dani shi yasa kika ji tun farko na nuna miki bai sai mu yi ire-iren waɗannan bidi'o'i ba. Ke kuma kika kafe. "Haba Habibi akan me ba zan yi farin ciki Allah ya gwada min aurena da wanda na daɗe ina mafalki musanman yadda aure namu ya zo da complications iri-irin sai yanzu da ya tabbata zan kasa nunawa gaskiya ba zan iya ba. Ka nemi kawai ko su Siyama ne su zo su gayyato ƙawaye su amman gaskiya banaso abun da ya faru a wurin kamu ya sake faruwa a dinner shi yasa na nemi ka tun a dare nan mu yiwa tufka hanci. "Ki fahimci ni Rumaisa da gaske nake ba zan iya cilasta wa kowa sai ya zo bikina ba. Wannan dinner ba dole bace tun farko ke kika ji za ki iya saboda haka sai kisan yadda za ki yi handling ɗin family and friends ɗinki. "Habibi abun da za ka ce kenan?" "To me kike so nace da ya wuce wannan?" "Shi kenan Allah ya ba mu alkhairi. Ta faɗa tare da buɗe murfin mota da karfi ta fita, rai ɓace da sauri AB ya fito yana kiran sunanta amma tayi masa banza ta buɗe ƙofar gidansu ta shige ya daɗe tsaye a wurin yana kiran wayarta taki picking daga ƙarshe ma sai ta kashe wayar duka. Cikin wani yanayi na karayar zuciya ya shiga motarsa ya yo gida tun yanzu kenan zai fara fuskantar kalubale rashin asali wato ba ƙaramin gata Daddy ya yi masa ba na aura masa Aydah da ya yi ashe aurenta shi ne rufin asirinsa, sai yanzu da hakan ta faru tsakaninsa da Rumaisa ƙwaƙwalwarsa ta fahimci manufar Daddy. Sosai ya shiga damuwa shiyasa yana shigowa gida ya wuce parlornsa dake sama ya zauna akan sofa tare da ture hular kansa zuwa ƙeya sai zazzafar iska da yake ta faman fesarwa daga bakinsa. Anan ya kusa raba dare kafin ya wuce master bedroom ɗinsa yadda yaga rana haka yaga dare, washegari da sassafe Rumaisa ta turo masa da text tana ƙara jaddada masa manufarta. Ban yi mamaki ba saboda tun jiya mamakin da ta shahara dashi bai gama sakinsa ba. Wanka ya yi ya shirya cikin shadda blue in color ya sauko ƙasa da Aydah ya fara ci karo tana kwance akan three seater da waya manne a kunneta sai magana take tana dariya ya yi tsaye yana kallonta sai kuma ya yi gyaran murya hakan ne ya sakata juyawa ta kalle shi da sauri ta katse kiran tana faɗin "Ina kwana yayanmu?" "Lafiya ƙalau! Ya aka yi yau ba ki je school ba? "Yayanmu mun kammala exams jiya yau ba a komai shiyasa na bari sai gobe na je na karbo report card ɗina. "Okay! Ya faɗa tare da nufar kofar fita "Yayanmu fita za ka yi ne?" "Eh! "Break fast fa?" "Sauri nake yi idan na isa office zan yi. "Shi kenan Allah ya tsare ya kai ka lafiya. "Amin! Ya faɗa a takaice ya juya tare da buɗe ƙofa ya fice ransa duk a jagule damuwa tana so tai masa yawa, yau da matsanancin ciwon kai ya tashi yana fita ya kira Abdulkarim ya tambaye shi inda yake ya ce masa yana office ya zo ya same shi a can, ya juya akalar motarsa ya nufi ma'aikatar su Abdulkarim ɗin. Koda ya shiga office ɗin Abdulkarim har wani hazo-hazo yake gani adaddafe ya nemi kujera ya zauna yana mai dafe ƙoƙon kansa fuskarsa fal damuwa. Abdulkarim ya ture file ɗin dake gabansa ya taso cikin sauri ya nufi wurin AB ya zauna tare da dafa kafaɗarsa "Yadai abokina tun a waya da na ji muryarka jikina ya bani you're not okay faɗamin mene ne?" "Ak wai ni har sai yaushe zan ji daɗin rayuwata? Ak me na yiwa iyayena da suka zabi su jefar dani batareda su yi tunani hakan zai dinga bibbiyata ne? Me nayi musu da na cancanci haka. "Calm down abokina ka natsuwa ka sakawa zuciyarka sallama. Kasani kowanne dan Adam yana tafiya ne a bisa bagiren ƙaddararsa kai ka ma godewa Allah da ya musanya maka da mahaifi irin Alhaji Bashir domin samun mahaifi irinsa a wannan zamani sai an tona. "Haka ne Ak amman jiya maganganu da Rumaisa ta faɗamin sune silar damuwata. Ɓata fuska Abdulkarim ya yi har yana haɗawa da guntun tsaki shi dama tun fil'azal bason Rumaisa yake yi ba don dai kawai AB ya nace akanta ne cikin rauni murya AB ya kwashe labari abunda ya wakana tsakaninsa da Rumaisa duka ya faɗawa Abdulkarim ai kuwa Abdulkarim ya shiga zazzaga masifa har cewa ya yi "ko yanzu bata ɓaci ba idan ba za ta iya aurenka a haka ba babu dole kowa ya kama gabansa amman ina amfani ace ƙanana maganganu daga wurinta suke fitowa, har idan soyayyar da take maka ta gaskiya ce ina ruwanta da danginka. Shi dai AB bai ce uffan ba sai bin Abdulkarim kurum yake da idanunsa da suka yi ja, AB bai baro office ɗin Abdulkarim ba sai bayan azhar yau kasa zuwa kamfani ya yi duk da yana da tabbacin tarin ayyukan da ke jiransa da yake so ya kammala su yau ɗinan daga gobe zai ɗauki hutun mako ɗaya domin ci amarci gida ya dawo jikinsa duk ya yi masa wani irin ga wata irin kasala da yake ji a main parlor ya tarar da Aydah da Huwaila suna kallo, Huwaila ce ta fara gaishesa kamin Aydah ya amsa musu da kasalalliyar murya ya haura sama "Auta tashi ki bishi yadda ya dawo ɗinan akwai abun da yake damunsa ga baki ɗaya ya yi wani irin kamar ba Yayanmu ba. Huwaila tayi magana tana kallon Aydah, da sauri ta yunƙura ta tashi tsaye tana faɗin "Tun safe na gansa ciki wannan yanayi ai na gayamiki ko breakfast bai yi ba ya fita, kuma yanzu ya dawo ba lokaci da ya saba dawowa ba. "Haka ne yi maza ki je ki ji damuwarsa. Aydah ta nufi upstairs da saurinta tana tura ƙofar parlor ta hango shi zaune akan sofa yana amsa waya tun kafin ta iso kusa dashi ta tsikayi muryarsa yana faɗin "Haba Rumaisa ya kike so nayi da rayuwata huh? Wannan abun da kike bukata bai mai yiyuwa bane, shiyasa tun farko na nuna ƙi amincewa ta da party nan da kika shirya. Ya yi shiru can kuma ya sake cewa "Ni fa ba zan iya ba idan har party ya zama dole sai da dangina ki haƙura dashi mana tun da dai kinsan ba dangin ne dani ba. Aydah ta sauke numfashi tare da zaunawa gefensa "shi kenan ki yi yadda kike so ni dai na faɗa miki farar gaskiya kuna kuma daga kanta bansan me kike so na sake faɗa ba. Yana ƙarashe magana ya kashe wayar duka yana sauke numfashi ji yake kamar ya dora hannun aka ya yi ta rusa kuka "Yayanmu lafiya kake kuwa?" Ya tsikayi sanyayya muryar Aydah a dodon kunnensa sai da ya ja deep breath kamin ya furta "Da dama zance Baby abubuwa suna neman su yi min yawa. "Subhanalillah! To Allah ya ye maka. "Amin! Ya furta tare da kakkalo murmushin dole. "Na kawo maka abinci?" "Uhm! Ta tashi da sauri ta fice koda ta sauko ƙasa har Huwaila ta shirya masa abincinsa ta jera akan tray Aydah ta dauko ta kawo masa kaɗan ya tsukura sama-sama, Aydah ta tattare raguwa ta maida kitchen ta sake dawowa ta zauna akan kujera dake facing ɗinsa ta saka shi a gaba tana kallo, ita bata yi magana ba shi bai yi ba da ya gaji da kallo da take masa ya tashi ya wuce master bedroom ɗinsa ya ce da ita zai kwanta idan la'asar tayi ta tashe shi. Ta bangaren Rumaisa ba ƙaramin haushi ta ji ba na yadda AB ya kashe mata waya hatta dashi bai je dinner ɗin ba balle wasu danginsa da take ƙorafi akai, gashi ta kira wayarsa yafi a kirga a kashe daga ƙarshe sai Abdulkarim ta kira shi daman yana jiraye da ita ya yi mata tass sai abin da bakinsa ya manta. Haka aka yi wannan dinner ɗin babu dangin AB daga shi sai friends ɗinsa, har aka tashi daga dinner ɗin Rumaisa bata sakar masa fuska ba yadda take share sa ba ƙaramin ciwo ya yi masa ba sai dai ba shida yarda zai yi. Da aka watse daga dinner su Rumaisa suka dawo gida tun a cikin daren aunty Raliya ta dinga faɗa da zage-zage sai da Ammy ta taka mata birki sa'annan ta dawo cikin hankalinta. Washegari gari da misali ƙarfe 2 daidai aka ɗaura auren AB da Rumaisa a bisa sadaki Naira duba ɗari ɗaurin aure ne da ya tara dubbanin mutane. Bayan an kammala ɗaurin aure maza suka wuce wurin liyafar ci abinci wanda Abdulkarim ya shiryawa abokansu da colleague ɗin AB, kuma har zuwa sanda aka ɗaura aure AB bai sake magana da Rumaisa ba sai bayan kammala ɗaurin aure ya tura mata gejeren text Alhamdullah an ɗaura aurenmu daga yanzu kin zama mallakina Habibty. Ko kaɗan bai yi tunani za ta bashi amsa ba sai gashi ta tura masa dukkanin godiya da yabo sun tabbata ga Ubangiji da ya nuna mana wannan babbar rana ina tayaka murna Habibina. Wani kalar sanyayye murmushi ne ya subuce masa duk wata damuwarsa ya nemi ta ya rasa. Lokaci da labari daurin aure AB da Rumaisa ya riske Mami da Sadiya kowanne su tamkar zai haɗe zuciya Mami ta dinga faɗa da yiwa AB gori tamkar yana gabanta, yayin da Sadiya ta shige ɗakinta ta rufe ta dinga rusar kuka ji take kamar daga wannan aure na Ab ta rasa shi kenan. Ta bangaren Aydah tun safe da tashi sukuku batada sukuni ko kaɗan ga wani abu da take ji ya tokare mata a maƙogwaro, sai rarrashinta Huwaila da Siyama suke yi tun safe Siyama ta zo gidan nata har dare tana gidan kamin a kawo amarya suka shirya Aydah cikin wani tsadadden lace suka dawo parlor ƙasa suka zauna wanda suka turaren wuta mai azabar Ƙamshin misali ƙarfe 9:30pm suka ji dirar motocin 'yan rakiyar amarya Rumaisa. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/15, 12:21 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 069. Wanda suka shigo da amarya cikin parlor daman sallama kawai suka yi basu kara kallan su Siyama dake cikin parlor ba suka rika Rumaisa zuwa sama. Da wani irin kallo Aydah ta bisu tana jin kamar zuciyarta zata faso ƙirjinta ta fito ƙanƙame Siyama tayi wani irin kuka mai cin rai na kwace mata ga jikinta ya dauki wani irin rawa,a tsorace Siyama ta rufe mata baki da wani yanayi a muryarta tace "kiyi shiru Aydah wai so kike suji kukanki sun rainaki. "Ba zan iya ba yaya Siyam zuciyata, ƙirjina ciwo suke min. Ta faɗa tana shesshekar kuka tun daga nan ƙasan parlor suke jin hayaniyar ƙawayen amarya a parlon AB basu jima ba sai ga AB ya shigo shi da friends ɗinsa har lokacin Aydah na kwance jikin Siyama tana sauke ajiyar zuciya. Huwaila ce kawai ta amsa masu sallamar cikin raunin zuciya, daman Siyama ko kallo ba su isheta ba. Tana yi tana dauke hawayen dake son su zubo mata jin take tamkar taje ta rufe yayan nasu da duka ta tambayesa me suka yi masa da zai masu Irin wannan sakayyar, sai dai girman da yake dashi a wurinta da kuma matsayinsa ba zata iya yimasa rashin kunya ba. Daman Aydah na jin sallamarsu tayi ƙoƙarin fita daga jikin Siyama,karo na farko a rayuwarta da taji bata son ganin fuskar yayanta da gudu ta shige ɗakin Huwaila gamida rufo kofar, shiru AB yayi yana kallon kofar da ta rufe, Siyama ce tabi bayanta batareda ta gaisheda AB da friends ɗinsa ba. Anan cikin parlor su Abdulkarim suka zauna Huwaila ta nufi kitchen dan kawo masu ruwa. Da sassarfa AB ya nufi ɗakin na Huwaila zuciyarsa na wani irin bugawa ko kaɗan bai ji daɗi gani Aydah a cikin wannan yanayi ba, cikin shesshekar kuka Aydah ke faɗin."yaya Siyam zan bi ki wurin Mami, ba zan iya zama ba zuciyata fashewa zatayi.! Dai dai lokacin AB ya turo kofar room ɗin daman Siyama na ganin ya shigo ta raba Aydah da jikinta ta miƙe tsaye, ita ma Aydah tamkar jira take ta tashi ta mike tsaye tana kokarin riƙe hannun Siyama ɗin tana cigaba da kukanta wanda sautinsa ya gama cika ɗakin. Hannunsa ya harɗe akan ƙirjinsa yana kallon yadda baby face ɗinta ta zama saboda kukan da tasha har wani kumburi saman idanunta yayi. Dakyar Siyama ta haɗe abun da take ji ta gaisheda yayanta amsawa yayi yana kallonta yana faɗin."wa zai maida ki gida? "Daman da mota nazo. Ta faɗa fuska babu walwala,ya lura da haka murmushi ya ɗan saki yasan tana taya yar uwarta kishine kawai ba wani abu ba. Ya duba agogon rolex ɗin dake cikin tsintsiyar hannunsa,yaga har kusan karfe goma da rabi na dare, dare yayi sosai ya dubeta a natse ya ce "Ki kwana anan ki bari sai gobe. Da sauri ta girgiza kai tana faɗin."mami za tayi faɗa. Dan shiru yayi da gaskiyarta Mami za tayi faɗa,wani numfashi ya sauke yana faɗin."kibar motarki zan saka Abdulkarim ya mayar dake,daga kai tayi kurum tana ficewa daga room ɗin dan ta lura hankalinsa ga baki ɗaya yana kan Aydah daman tana fita Aydah tabi bayanta caraf! Taji ya riƙe mata hannu duk yadda taso ta kwace hannunta ta kasa gashi ko kaɗan bata son haɗa ido dashi jawota yayi ga baki ɗaya cikin jikinsa, tamkar jira take ta sakar masa kuka zagaye hannunta yayi da bayansa cikin taushin murya ya kira sunanta ga baki ɗaya kukanta neman yake ya hargitsa masa ƙwaƙwalwa, kukanta ta cigaba dayi yana rike da ita."Baby so kike nima na tayaki kukan ne? Ya faɗa da ƙaramar murya har sai da Aydah ta dago kumburrun idanunta ta saukesa cikin nasa,wannan karon abun da yake gani cikin ƙwayar idanunta yasa shi saurin dauke idanunsa cikin nata. Zuciyarsa wani irin bugawa take da kalar bugun da bai taɓa jin irinsa ba, addu'a yake Allah yasa abun da yake gani cikin ƙwayar idanun kanwar tasa ba gaskiya bane. Allah yasa matsayinsa na yayanta bai canja ba a zuciyarta dama duniyarta ga baki ɗaya "Bana son na kara jin wannan kukan kina jina?" Ya faɗa yana tallabe da haɓarta daga masa kai kurum tayi tana jin kusancinsu da ƙamshin turarensa yana haifar mata da wata irin kasala wacce bata taɓa tsintar kanta acikinta ba. "Ina son naje wurin Mami ina son na kwana tare da Mami. Ta karasa maganar cikin rawar murya, girgiza mata kai ya yi cikin ido yake kallonta kamin ya haɗe goshinsa da nata ,cikin wata murya yake faɗin."Ni kuma kiyi yaya dani?" Tamkar a mafarki ya ji ta ce "Baga aunty Rumaisa nan ba burin ranka matar so ai atare za ku kwana. Ta faɗa da murya mai rauni mai haɗe da zallar kishi tana jin hawaye na zuba cikin fuskarta. With shock yake kallonta bai taɓa tunanin tana da wayon fahimtar abubuwa kamar waya'anan ba,tsoro gami da mamaki ne shimfiɗe akan fuskarsa taya ma Aydah tasan a ɗakin Rumaisa zai kwana a yau?"shi da yake mata kallon batada wayau tamkar bata san wasu abubuwa ba ashe shine marar wayau, hannu yasa yana goge mata hawayen idonta da suka kasa tsayawa har lokaci suna zuba, ya ɗan haɗe rai yana faɗin."Bana son na sake ganin kina kuka kuma bana son na kara jin kince za ki bi Siyama,na maki alkawarin gobe da kaina zan dauko miki ita. Batace komai ba sai kallonsa kurum take yayi kyau sosai acikin farar shaddar dake jikinsa da aka yiwa hadi da babbar riga,sai lokacin ta lura da hodar da ta gama goge masa akan farar shaddarsa bata san lokacin da murmushi ya kubuce mata ba tana juya masa baya,inda tabi da kallo tana murmushi ya kalla da sauri,ganin yayi duk hodar dake kan fuskarta ta dawo a farar shaddarsa ware ido yayi yana kallonta hankali tashe ya kira sunanta "Baby! Juyowa tayi ta saki dariya ganin yadda firgici ya bayyana sosai akan fuskarsa "Kinga yadda kika batamin farar shadda haka kikeso naje wurin amaryarta.?" Jin kalmomin da yayi amfani dasu yasa ta haɗe rai lokaci ɗaya tamkar ba ita bace ke dariya yanzu nan ba,da sauri ya riƙo hannunta "Da wasa nake mu je mu raka su Siyama,dare yanayi. Ya faɗa yana ƙara tamƙe hannunta cikin nasa suka koma parlor kowa bin su yake da kallo da alamar AB ya manta amarya aka kawo masa wata ƙawar Rumaisa ce ta sauko ƙasa da mamaki take kallon AB da Aydah da ya rike hannunta ficewa tayi daga parlor dama fitowa tayi amsa waya,ta matsu ta gama wayar taje ta fesawa Rumaisa labari tun ɗazu ango ya shigo shine dan kuturun wulaƙanci zai wani shanyasu ya tsaya yana biyewa wannan kwailar yarinya dako nonon kirki bata dashi a kirjinta lallai akwai aiki agaban Rumaisa. Har bakin motar Abdulkarim Aydah da AB suka raka Siyama sauran friends ɗinsa guda biyu daman a mota ɗaya suka zo suka ce su sun wuce sai ya sallami friends ɗin amarya. Kallon Siyama kawai Aydah take ga baki ɗaya jikinta yayi sanyi wani irin tsoro taji yana cika mata zuciya suna tsaye maigadi ya buɗe masu gate suna ficewa Aydah ta fisge hannunta dake cikin na AB ta fashe da kuka da sauri AB ya fisgota cikin jikinsa yayi sauri saka ɗayan hannunsa ya rufe mata baki,murya can ciki ya furta"Meye haka?"sai kin sa mutane sun taru su dauka wani mummunan abu nayi maki, bana son wannan sakarci mu je ki canja kaya ki kwanta. Ya faɗa cike da bada umarni yana ɗan haɗe rai da haka yaja hannunta suka koma ciki komai da ya faru akan idanun Kamila ƙawar Rumaisa AB yana rike da hannun Aydah har cikin ɗakin baccinta. Kamila na tsaye tana bai wa kawayensu labarin yadda AB yake ta nan-nan da Aydah tamkar zai mayar da ita ciki,Rumaisa bata dai ce komai ba Amman kana ganin yanayin fuskarta kasan acike take kowane ya miƙe tsaye yana faɗin."Bari mu wuce sai gobe,muhibba tace "Sai kin tashi tsaye ƙawata dan wallahi irin waya'anann cwt 16 ɗin bala'i ne idan suka samu zama lashe zuciyar namiji suke saboda iskanci cikakkiyyar halitta ce kawai basa da Amman wallahi sun iya sace zuciyar namiji. "Ku tafi dan Allah karku ƙara min wani ciwo. Rumaisa ta faɗa cikin rawar murya basu jima da fita ba AB ya shigo ɗakin nata kanta na a kasa da mayafin data mayar akanta da sallama ya shigo cikin ɗakin,ya aje bakar ledar da ya shigo da ita akan side table ɗin dake gefen ɗakin,ya cire takalmin ƙafarsa ya karaso cikin ɗakin da ƙamshi ke tashi acikinsa da kuma ƙamshin turaren wuta zama yayi a gefen Rumaisa ya jawota ajikinsa zuciyarsa na tsananin bugawa yana addu'a yana kabbara kamin ya sassauta rikon da yayi mata a hankali ya dage mayafin dake saman kanta yana ganin yadda idanunta suka yi canja saboda kukan da tasha da za'a kawota gidansa. "Habibaty! Ya faɗa yana kamo hannunta a hankali ya sumbaci hannun nata sai da tsikar jikinta ya tashi yarrrr! Irin sumbar da yayi mata,haka yasa ta runtse ido da sauri kafin kuma ta janye hannunta tana barin fili a tsakaninsu,da wani irin yanayi da kuma kishi mai tsanani cikin muryarta ta ce ."Na dauka acan za ka kwana a wurin babyn naka. Ta karasa tana zube idanunta cikin farar shaddar jikinsa daidai inda Aydah ta kwanta ta saka masa hoda runtse idonta tayi tana jin ƙirjinta na wani irin zafi yana sama da kasa. Bai ce komai ba ya miƙe tsaye yana faɗin."Kiyi wanka bara naje nayi wanka na dawo,da ido kawai ta bisa cike da takaici bayan fitarsa tayi kwafa aranta tana faɗin."duk wannnan girman kan nasa sauke mata shi zai yi a daren yau ta tuna maganin da Aunty Raliya ta bata tace ta saka masa cikin abun shan sa kaɗan,na.maza ne kamar ruwa yake ko an saka ba'a ganewa da sauri ta buɗe handbag ɗinta ta dauko karamar kwalbar ledar da ya shigo da ita ta buɗe kwallin fresh milk ne,batareda wani tunani ba ta buɗe ta zuba kusan rabi ta mayar ta rufe ta jujjuya kwalin ya haɗe wuri ɗaya ta mayar da kwalin da sauri cikin ledar, kayan jikinta ta shiga ragewa daman tamkar kan ƙaya haka take jin kanta saboda nauyin da suka yi mata,kai tsaye wanka ta shiga duk turarrukanta na wanka da mai mata gyaran jiki ta haɗa mata tazo da abunta Aunty Raliya ta jera mata su cikin toilet ,wanka tayi ta fito daure da towel a ƙirjinta sai yanzu take jin gajiyar da ta tara tana saukar mata. Ga baki ɗaya gabobbin jikinta wani irin ciwo suke mata. A bangaren AB kuwa shima wanka yayi ya saka Black jallabiyya ajikinsa marar nauyi mai gajeren hannu,ya saka (casual slippers a ƙafarsa ya nufi ɗakin Aydah yana tura kofar ɗakin nata ya sameta bakin gado zaune tayi tagumi daga ita sai baby pink,towel a jikinta suna haɗa ido tayi saurin sauke idonta a ƙasa,karasowa yayi ya zauna gafda ita murya ƙasa-ƙasa yace "Baby ya baki saka kayan bacci ba?" Shiru Aydah tayi babu amsa sai famar jan dogayen fingers ɗinta take yi AB bai kara kulata ba ya tashi ya karasa gaban closet nata ya ciro mata riga da wando na bacci ya miƙa mata yace ta shiga toilet ta saka ta amsa tana kallonsa aranta take faɗin."idan Rumaisa ce ai ba za ka ce ta shiga toilet ta saka ba ni anan zan saka abuna ta faɗa aranta batareda wani tunani ba ta kwance towel ɗin jikinta a wani irin kidime AB ya kauda kansa ya shiga tari babu kakkautawa. Hakan ba ƙaramin bata dariya yayi ba ganin yadda yayanta ya rude dan kawai ta saki towel agabansa wandon kawai ta saka ta karasa gaban bedside drawer ta dauko masa water bottle ta tsaya agabansa ta miƙa masa daga kai yayi ya wani fisge bottle ɗin idonsa suka sauka akan matasan ƙirjinta "Aydah bakida hankali ne?" Ya yi magana yana buɗe marfin ruwan ya kafa kai ya shiga sha sai da ya sha fiye da rabi ya sauke yana kallonta zuwa lokacin ta saka rigar. "Je ki dauko plate a kitchen ki zo kici kazarki kartayi sanyi. Daman har huwaila sai da ya riƙowa ledarta da zai shigo kai tsaye kitchen ta nufa plate ta wanko da glass cup har biyu dan ta dauka tare zasu ci kazar tana ta jin dadi yayan nata ba zai wulaƙanta ta ba dan yaga Rumaisa dama tana haurowa sama ta wani kafe ɗakin Rumaisa da ido ta murguda baki tana wani irin juya ido,sai ta koyawa Rumaisa hankali a gidanan za ta ga yadda za ta kwana da yayanta ayau ɗinan. Da haka ta shige ɗakinta har lokacin AB na zaune yana jiranta ya karbi plate ɗin ya ciro kazar ya aza mata da kansa ya shiga bata kazar ganin baya ci yasa tace "Yayanmu kai bazaka ci bane?" g Girgiza kai yayi yana faɗin."Tawa da ta Rumaisa tana a ɗakinta wannan naki ne. Lokaci ɗaya yanayin Aydah ya canja zai kara kai wata a bakinta tace ta koshi ya tsiyaya mata fresh milk a glass cup ya nufi bakinta dashi dai-dai kuma lokacin aka turo kofar dakin da suke suran kaɗan AB ya saki glass cup ɗin hannunsa. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/16, 11:11 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 070. Shiru AB yayi yana bin Rumaisa da ido da mamaki shi bai kuma jaye cup ɗin ba a bakin Aydah. Dan murmushi AB ya kirkira yana faɗin "ki ƙaraso Habeebty,ki tayani rarrashin wannan rigimammiyar kanwar taki. Cikin murmushi mai kama dana yan duniya Rumaisa ta ƙaraso cikin ɗakin ƙamshinta ga baki ɗaya ya gama cika ko'ina a ɗakin rigar bacci ce ajikinta mai kauri doguwa har ƙasa kalar sky blue sai hular net data aza akanta, wanda har ake iya hango gashinta. Zama Rumaisa tayi cikin soofar dake girke acikin dakin ta wani harɗe hannayenta tana bin Aydah da kallo tana kula da yanayinta ,Aydah ta karbi cup ɗin dake hannun AB ta kafa kai sai da tasha rabi ta sauke,cike da karfin hali AB ke faɗin "baby baki gaisheda aunty Rumaisa ba,cikin rawar murya Aydah ta gaishe da Rumaisa ta miƙe tsaye ta nufi toilet batareda tasan me zata yi acikin toilet ɗin ba daga AB har Rumaisa bin ta suka yi da kallo,har kusan minti biyar da Rumaisa taga AB bayada alamar tashi su tafi su kwanta tasan da gangan Aydah ta shige toilet ta miƙe tsaye tana murza ido "Ni kam Habibi mu tafi mu kwanta bacci ne sosai a idona da kuma gajiya. Ba haka AB yaso ba yabi bayan Rumaisa dan baya son bata ranta ko kaɗan,daman Aydah najin fitarsu ta haɗa kai ga bangon toilet din ta shiga rera kuka. Sallah ya jasu raka'a biyu,kamar yadda addini ya tsara ya dade dafe da kanta yana karanto mata addu'oin tsari ya tambayeta kaɗan daga cikin addininta babu laifi tana da sani akan addini,ganin yadda take jera hamma yasa shi jawo kazar da ya shigo masu da ita ya juye cikin plate,shiya rika ciyar da ita kazar ita ma tana basa a haka har suka cinye kaza ɗaya. Daman kowanne su da yunwa a tare dashi AB ya zuba musu fresh milk cikin glass cup ya nufi bakin Rumaisa da sauri ta dauke kai tana faɗin."cikina ya cika dayawa Habeebi kasha kawai bara na sha ruwa,shi kaɗai ya riƙa shan fresh milk ɗinsa kusan cup biyu yasha duk Rumaisa na kallonsa kasa-kasa kai tsaye toilet ta wuce ta kara yin brush tana fitowa tabi jikinta da khumurah Ta hau gado tayi kwanciyarta. Still AB yana zaune a wurin na kusan minti goma yana jin wani irin yanayi a tare dashi wanda bai taɓa jin kalarsa ba. dakyar ya shiga toilet yayi brush ya fito yana kallon yanayinsa da ya canja cikin mintuna ƙalilan,cire jallabiyyar jikinsa yayi ya ninke ya ajeta a wurin da ya dace,ya rage daga shi sai boxer ajikinsa kai tsaye kan gadon ya nufa yana kashe fitillun dake da haske a ɗakin yana barin mai duhu,Rumaisa tana jin lokacin da ya kwanta sai ta kara runtse ido sosai zuciyarta na wani irin harbawa da karfi. Shiru AB yayi yana ɗora tafin hannunsa akan shafaffen cikinta ya runtse ido sosai yanayin yana kara shiga jikinta sosai har na kusan mintuna goma Rumaisa bata ji AB ya fara tabata tanata mamaki tana karawa kodai ba maganin bane Aunty Raliya ta karbo mata yadda ta rika bata labarinsa ita ba haka ta gani ba. (Nasiha da tuni ga duk wata budurwa kafin aure dan Allah dan Annabi karki kuskura a matsayin ki na budurwa daren da za'a kaiki a gidan miji kiyi amfani da maganin maza ki zubawa namiji acikin abun sha,wannan babbar illah ne sosai ke baki san illar da hakan zai yi masa ba kema baki san illar da haka zai yi maki ba a matsayin ki na budurwa)Gaban Rumaisa yayi bala'in faɗuwa ganin AB zaune ya haɗe kansa da gwiwowinsa jikinsa banda shaking babu abun da yake tamkar wanda aka sakawa wayoyin wutar lantarki acikin jikinsa. Yanayinsa yayi bala'in ba ta tsoro da sauri ta dawo kusa garesa ta dagosa wannan karon abun da ta gani acikin idanunsa yayi bala'in shallake tunaninta rike fuskarsa tayi cikin fitilar da bata da haske take karewa fuskarsa kallo,samun kanta tayi da shigewa cikin jikinsa zuciyarta na tsananin bugawa. Kamar jira yake yayi wani irin sakata cikin jikinsa yana lalubarta a gigice tamkar wani mayunwacin zaki ,halin da Rumaisa ta shiga a hannun Abba Bashir halin a tausaya matane dan tamkar an cirewa Abba Bashir tausayi a wannan daren kansa kawai ya sani ciwon da yake tare dashi yake so kawai yabar jikinsa tun yana bin Rumaisa cikin sauki har yazo ya haukace mata tun tana dauriya har ta kasa duka da yakushe da kuka da majina duk yasha sa a wannan daren bai ma san tana yi ba dan jinsa yayi a wata duniya ta daban wacce bai taɓa jin kansa aciki ba duk wani girmansa sai da ya tabbatar ya juyewa Rumaisa shi duka. A wannan daren daga shi har Rumaisa sun wahala ko sallar asuba basu samu ba sai kusan 6 suka yi wanka suka yi sallar asuba,duk da haka AB yaga jarumtar Rumaisa da ta iya yin wanka tayi sallah batareda taimakonsa ba sai lokacin ta samu wani wahalallen bacci ya dauketa ko ina gabobbin jikinta ciwo yake. Kwamciya yayi agefenta yana jawota ga baki ɗaya cikin jikinsa sai da ta tsorata irin rikon da yayi mata murmushi yayi cikin muryar rada yake faɗin."Babu abun da zan yi miki bacci zamu yi. Thank you habibty kin bani farin cikin da babu wanda ya taɓa bani kalarsa Allah yayi miki albarka matata. Shigewa tayi cikin jikinsa tana sauke wata irin ajiyar zuciya tana godiya ga Allah da ya mallaka mata abun da takeso a rayuwarta daren jiya kawai ya tabbatar mata da Abba Bashir nata ne ita ɗaya yadda ya riƙa yimata ne jiya tasan babu abun da ya taɓa shiga tsakaninsa da Aydah wani irin daɗi da farin ciki ya lulluɓeta. Baccinsu suka koma cikin natsuwa sai wuraren ƙarfe goma na safe suka farka ko shi sai da hasken rana ya haske fuskokinsu,ya rigata shiga wanka koda ya fito ta gyara gadonta tsaf yana bin ta da ido sai sannu yake mata da kanta ta ƙaraso inda yake tasa hannu ta amshi karamin towel ɗin dake hannunsa ta shiga goge masa sumar kansa tsaf! Jallabiyarsa ya mayar ya faɗa mata zai ƙarasa bangarensa ya shirya wani iri taji kyau ace komai nasu na haɗe a wuri ɗaya tayi mai fari da ido tana faɗin "Ya kamata dai ace komai namu yana a haɗe wuri ɗaya,ina ganin haka zai fi. Dan jim AB yayi tamkar mai tunanin wani abu sai kuma ya girgiza kai yana faɗin."kin manta ku biyu ne kar a shiga hakkin baby Aydah kuma. Juyawa kawai Rumaisa tayi ta nufi toilet batareda ta kara kula AB ba. Shima ficewa yayi daga ɗakin kai tsaye bangarensa ya nufa ya shafa mayukansa ya saka riga da wando na English wears ajikinsa wanda suka yi bala'in karbarsa kai tsaye ɗakin Aydah ya wuce kwance ya sameta tamkar haɗin baki ita ma da English wears ajikinta riga da wando, wando same color da nashi rigar ce kowane su da color ɗinsa. Kallonta kawai yake tana riƙe da wayar hannunta ko mai take kalla aciki oho. Ta amsa sallamarsa ciki-ciki ta tashi zaune kana ganin idanunta kasan taci kuka haka kuma babu wadataccen bacci acikinsu "Baby yau ba gaisuwa?" Nan turo baki sa'annan ta gaishesa ya harareta yana faɗin."Sai da na roƙa, kin yi break fast?" Ita fa yayan nata yanzu haushi yake bata Allah kaɗai yasan abun da suka yi jiya shi da Rumaisa zai zo yabi ya dameta. Wata kwallah taji tana taruwa cikin idanunta,lokaci zai zo da zata rama duk irin abubuwan da yayanta yayi mata yaje can ya haɗe Rumaisa idan yana iyawa. "Aydaah!" AB ya faɗa da sauri dan kusan sau biyu na kiran sunanta tayi nisa a tunanin da take a firgice ta dago tana kallonsa. "Tunanin me kike haka?"kin ma yi break fast kuwa?" Ranta haɗe tace. "Ban yi ba. Ya gyada kai yana faɗin "Tau tashi kije kasa ki kwaso mana kayan break fast ɗin sai muyi a parlorna har Rumaisa. Jin ya ambaci sunan Rumaisa taji wani abu ya tsaya mata daidai wuyanta miƙewa tayi tsaye ta nufi kofa a kitchen ta samu Huwaila tana markada kayan miya na abincin rana,ta gaisheta tana mata sannu da aiki ganin yanayin Aydah ita ma Huwaila bata wani dame Aydah da surutu ba ,ta faɗa mata kayan karin kumallo su suna can dinning area. Ficewa kawai daga kitchen din Aydah tayi ta dauki breakfast ɗin ta wuce dashi falon AB babu kowa a cikinsa sai karar AC aje kayan karin kumallon tayi akan rug ta nufi ɗakin baccinsa,sai da tayi knocking ta tura kofar ɗakin nasa AB ne tsaye agaban mirror dressing shi da Rumaisa ya rungumeta ta baya ya sakalo kansa cikin kafaɗarta karar buɗe kofa yasa suka kalli kofar da sauri fuskarsu kan Aydah da ta haɗe rai tamkar ba'a taba halittar dariya akan fuskarta ba ta juya tabar kofar ɗakin haka ta kasa jamasu kofar. Da sauri AB ya saki Rumaisa ta ƙarasa ta gyara masa gadonsa,rai abace take faɗin."ita wannan ƙanwar taka bata da hankali ne da za ta dinga shigowa mutane ɗaki anyhow idan da a wani yanayi ta same mu fa?" Rumaisa ta faɗa duk ranta a ɓace,tun farko bata so AB ya ajesu gida ɗaya da Aydah ba tana bukatar Kebantacciyyar rayuwa ita da mijin aurenta. Shi kansa AB ransa ya ɗan ɓaci ganin Aydah ta shigo ba tayi sallama ba,ya juya yana faɗin."Rumaisa idan kin gama ki sami ni a falo muyi break fast. Da haka ya fice daga ɗakin,dan ƙaramin tsaki Rumaisa ta saki. AB yabi kayan karin kumallon da Aydah ta aje sai dai babu ita a parlor kai tsaye ɗakinta ya nufa samunta yayi tana kuka tsaye yayi a bakin kofa. Da mamaki yake tambayarta wani abu akayi mata?"lokaci ɗaya ya haɗe fuska da sauri ta girgiza kanta ganin yadda ya koma lokaci ɗaya tamkar ba'a taɓa halittar dariya cikin fuskarsa ba. "Tashi mu je kiyi break fast. Ya faɗa babu alamar wasa a muryarsa cikin rawar murya take faɗin "Na koshi yayanmu. Kallon da ya shiga yimata yasa ta miƙe ta nufi kofa parlor sa Rumaisa na zaune tana jiransu ganin sun shigo tare ta wani dauke kai Dakyar Aydah ta gaisheta tuno faɗan da AB yayi mata na rashin gaisar da Rumaisa da tayi jiya ita ma Rumaisa bata kalli gefen da Aydah take ba ta amsa. Ta dauki cup ta shiga haɗawa AB tea ta dibi dankali da farfesun naman kai ta tura a gabansa sai da ya saki murmushi sa'annan yace "Na gode. Ita ma murmushin ta saki tea kawai ta haɗa acikin plate ɗin AB tayi joining ɗinsa dakyar Aydah ta haɗa tea ta dibi dankalin ta koma gefe ta soma ci badan tasan daɗin sa a bakinta ba ita dai turawa kawai take sai AB yaji duk babu daɗi a haka dai aka gama breakfast ɗin, Aydah ta kwashi kayan ta kai kitchen,AB yace idan taje ta wanke komai karta bai wa Huwaila idan ta gama ta zo yana jiranta zaiyi magana da dukansu, tamkar guguwa haka Aydah ta fice daga falon ta sauka kasa wani marayan kuka na taho mata tana jin kamar ta cakawa Rumaisa wuƙa ta mutu kowa ma ya huta ji wani shigewa yayanta da take tana fari da idanu tamkar wata karuwa. Ganin tana shirin sakin tray Huwaila ta karba da sauri anan kasan kitchen din Aydah ta durkushe tana kuka hankalin Huwaila idan yayi dubu ya tashi,a rude ta shiga tambayarta menene?"kasa cewa komai Aydah tayi sai kukan da ta cigaba dayi. Hakan ba ƙaramin haushi ya bai wa Huwaila ba. Yanzu idan da agaban Rumaisa ne fa?"ai sai ta rainata da abun da ya isa da wanda bai isa ba duk na kuka ne a wurin Aydah wannan sakarcin dame yayi kama."To bari naje na tambayi yayanmu dalilin kukan ki tun da naga daga wurinsa kika fito. Da sauri Aydah ta miyke tsaye cikin shesshekar kuka take faɗin "Ni wallahi na gaji wurin Mamina zan koma amma ba zan zauna a gidanan ba. Huwaila ta ware ido tana kallon Aydah cike da mamaki cikin jin haushi Huwaila tace."shi kwana ɗaya da Rumaisa tayi cikin gidan nan har ta saka gidan ya fice miki arai Auta?" Cikin kuka Aydah ta bata amsa."Ba ki ga yadda take shisshige masa bane gara nabar masu gidan kar zuciyata ta buga Aunty Huwaila. Tana gama faɗin haka ta karasa wurin sink ta shiga wanke kayan da suka bata kamar yadda yayanta yayi mata umarnin sai da ta wanke komai ta mayar a inda yake Ta juya ta koma sama sai da tayi sallama tayi knocking sa'annan ta shiga. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/17, 4:40 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels. 071. Kallo ɗaya tai musu ta kauda fuska tana taɓe baki zaune suke akan kujera guda ƙugunta manne da nasa, sai wani banza murmushi da take ta faman dokawa ita a dole sai ta nunawa Aydah ita ke da miji. Zuciyar Aydah tamkar za ta tsaga ƙirjinta ta fito ta nemi kujera dake nesa dasu ta zauna tare da sadda kanta ƙasa tana lankwasa yatsunta sai sautinsu kake ji ƙass!ƙass! AB ya kalle side ɗin da Aydah take ya fito ta da hannunsa "Baby zo nan ki zauna. Ya ƙarashe magana tare da nuna bangaren hagunsa da yake Rumaisa tana zaune ne a bangaren damansa, Aydah ta ɗago a natse ta kalle shi sau daya ta maida kanta ƙasa tana girgiza kanta "Ka bar shi kawai Yayanmu nan ya isa. Yadda tai magana cikin dushewar murya tai bala'in basa tausayi ya sake cewa "Magana mai muhimmanci zan yi daku baby idan kina nesa dani taya za ki ji abun da nake faɗa?" Batareda ta ce komai ba ta taso kanta yana ƙasa ta zauna kusa dashi sai da ta bada tazara a tsakaninsu ta sake sadda kanta ƙasa AB ya kalle rata da ta bayar a tsakaninsu ya yi murmushi ya juya ya kalle Rumaisa wacce tayi kici-kici da fuska, nan ma ya sake murmusawa kana ya ɗora da yi basmallah nasiha sosai ya yi musu ta su haɗa kansu su zauna lafiya "Rumaisa duk da a shekaru kin girme Baby Aydah nesa ba kusa ba amma a gidanan ita ce babba domin ita ce na fara aure saboda haka ki kama girmanki ki ja ƙanwarki a jiki ku idan tayi kuskure a matsayin ki na babba mai hankali ki lurar da ita. Iya sani da na yiwa baby Aydah batada matsala za ki ji daɗin zama da ita. Sai dangane da kwana ya kuke gani za a tsara duk a yanzu sai na sake maida kwanaki shidda a ɗakin Rumaisa kamar yadda addini ya tsara amman yana da kyau a wannan zaman da muka yi ku raba girki ko me ku ka ce?" Rumaisa wacce ta cika tayi bam! Jira take a taɓa ta fashe ba ta kalle AB a ɗage ta watsar sai wani yatsine fuska take yi ba ƙaramin haifar mata da mamaki AB ya yi ba wato ya mayar da ita shashasha ai kamin ta shigo gidansa ya sha faɗa mata ba abunda zai tsinta a jikin Aydah ashe duk zuƙi ta malle ce yake mata kai maza munafukai ne gane gaskiyarsu sai Allah. Tabo ƙafarta da ya yi da ƙafarsa yasa ta dawo da ganinta kansa "Habibty ba ki ce komai ba?" "Duk abun da kace Habibi ya yi. "Amman ya kamata na ji ra'ayinku dangane da kwanaki da ku ka tsara na girki?" "Ka tambaye uwargida duk yadda ta tsara ni banida matsala. Yadda Rumaisa tayi magana kai da ji kasa da walaki goro a miya sai lokacin Aydah ta ɗago ta kalle su ta sake maida kanta ƙasa "Yayanmu ni ba sai an raba girki dani ba na bar mata duka daman can kasan ban iya girki ba. Unexpected ya ji wannan maganar tana fita daga bakin Aydah ya zuba mata manyan idanunsa yana kallonta yayin da Rumaisa ta saki murmushi mai sautin gaske don ita kan ba ƙaramin daɗi furuncin Aydah ya yi mata ba. "Baby bani na tsara raba girki a tsakaninku ba addini ne ya tsara kuma ni ba zan so na danne haqqin ko ɗaya daga cikinku ba, banaso gobe kiyama Allah ya tuhume ni da cutar guda daga cikinku saboda haka na raba muku girki kwana bibbiyu idan da akwai wacce hakan bai mata ba tayi magana ko ta faɗi ra'ayinta. Dukkansu shiru suka yi ita daman Aydaah batada abun faɗa ita kuma Rumaisa duk haushinsa ya gama cikata saboda haka ta miƙe zubur tana faɗin "Habibi zan je na ƙarasa kimtsa ɗakina kada nayi baƙi su zo ɗaki a ya mutse. Kamin ya bata amsa har ta nufi ƙofar fita, daga shi har Aydah da ido suka bi ta Aydah ta taɓe baki ita ma ta tashi tana faɗin "nima zan je na kwanta Yayanmu bacci nake ji. Kamar dai yarda Rumaisa tai masa ita ma haka tayi bata jira jin ta bakinsa ba ta fice abinta, kaitsaye ɗakinta ta wuce ta haye gado ta kwanta hawayen da tun ɗazu take rikewa suka dinga bi gefen idanunta suna sauka a wuyanta. *HAMBURG GERMANY* Tun saukar Aliyu na Uku hamburg bai samun kansa ba sai yau shi ma shi ne last day na seminar ɗin da suke yi na gamayyar kamfanoni wannan seminar ɗin suna yinsa ne a duk ƙarshen shekara a wannan karo a mercure hotel suka gudanar dashi a katafaren conference hall dake cikin hotel ɗin. Yanzu ma sun tashi ne domin kowa ya je ya yi lunch su dawo a karasa tun daga wannan zaman shi kenan sun kammala seminar ɗin, yayin da kowa ya nufi gun ci abinci shi kuma Aliyu na uku ya nufi harabar hotel ɗin domin ya sha fresh air jikinsa sanya da Italian suit blue-black in color daidai yana kawowa entrance ɗin fita daga receptionist hankalinsa yana ga wayar da yake yi da Anaal shiyasa hankalinsa ya tafi sosai sai kawai ya ji yaci karo da mutum kusan a tare wayarsa ta zame daga hannunsa ta fadi kusan a tare suka sunkunya domin dauko wayar kafin ya kai hannunsa har ta riga shi ɗaukar wayar ta miƙa masa tana faɗin "I'm sorry sir, I didn't hit you on purpose, I was in a hurry. Ya ɗago tare da miƙewa tsaye ita ma ta miƙe tana ƙara miƙa masa wayarsa sai lokacin idanunsa suka sauka akan fuskarta cikin shock yake kallon kyakkyawar fusrkarta jikinta sanye da baƙar Abaya tayi rolling da kanta da mayafin rigar cikin kaɗuwa ya furta "Maysun!Maysun are you the one I am seeing in reality or it is a dream that I used to have?" Kamar ba za ta amsa mishi ba sai faman kallonsa take yi tana tunano irin rayuwar da suka yi a shekarun baya, yau shi ne a tsaye a gabanta duk da shekarunsa sun tafi amman kyawunsa da kwarjininsa yana nan sai ma taga kamar ya daɗa ƙaruwa ko kaɗan bataso ta kula shi ba saboda ganinsa da tayi yanzu nan ya tayar mata da tsohon miki da ya tafi ya barta dashi a tsawon shekaru da tayi basa tare sai dai zuciyarta tana cike da kwadayin so sani lafiyar yaronta wanda kullum da tunaninsa a dankare a zuciyarta, cikin nauyin harshe ta ce "It's not a dream, I'm the Maysun you knew years ago, the one you ran away and left her. "Kada ki ce haka Maysun ni ban gudu ba kawai dai tafiya ce ta gaggawa ta kamani kuma na dawo na tarar da bakya nan kum... "Ali where's is my son yanzu ya girma ko?" Tayi sauri katse shi da tambayar da ta gigita masa ƙwaƙwalwarsa har jikinsa ya dau rawa cikin kaɗuwa ya ce "Me kike nufi da wannan tambaya Maysun? "Ali banaso wata doguwar magana a tsakanin mu kawai ka faɗamin lafiyar yarona idan da hali ka taimaka ka haɗani dashi. "Maysun idan wasa kike yi dan Allah ki daina nima na damu da na ji labarin Azhar daga wurinki. Wani irin ja da baya Maysun ta shiga yi idanunta sun firfito da sauri Aliyu ya riƙo hannunta, zuciyarta tana wani kalan bugawa kaitsaye ɗakinsa dake hotel ɗin ya nufa da ita kafanɗunta biyu ya riƙe ya girgiza ta da dukkan ƙarfinsa "Maysun where's our son idan baya tare dake Maysun yana ina kisan dai tare na tafi na barku a lokacin yana bacci akan gado ke kuma kina bathroom do you remember? Maysun ji tayi wani abu ya tsaya mata a wuya sai girgiza kai take yi numfashinta ya shiga sarkewa ta durƙushe ƙasa tana dafe ƙirjinta da sauri Aliyu ya zube a gabanta yadda yaga tana fizgar numfashi ya tashi hankalinsa idan bai manta ba tana da Asthma cikin fitar hayyaci ya fizge jakkar hannunta ya zuge zip ya zazzage kayan dake ciki kamin idonsa ya kai kan inheler ɗinta ya ɗauka ya danna mata a baki, dakyar take shaƙar iheler ɗin ta ɗauki lokaci tana shaƙar iskar inheler kamin numfashinta ya daidaita sai kuma ta fashe da kuka tana faɗin أين ابني علي؟(where's my son Ali) "لا أعرف ميسون(I don't know Maysun) shi ma ya faɗa hawaye na bin fuskarsa "Ki faɗamin hakikanin gaskiyar abun da ya faru bayan tafiyata?" "Bayan na fito daga bathroom sai na tarar da short note ɗinka kana gayamin tafiyar gaggawa ta kama ka ba za ka wuce three ɗays za ka dawo har tsawon wata ɗaya ba ka dawo ba ni kuma aka kira ni daga gida na zo Abbie ɗina bashi da lafiya, sai na kai Azhar gidan cousin ɗinka na ce su ajiye ma shi koda Allah zai sa ka dawo saboda nima ina jin tsoron na tafi dashi Qatar iyayena su tuhume inda na samu shi ina jin tsoron asirina ya tono sun gano nayi aure batareda da sani su ba. "Innalillahi wa'inna illahim raji'um! Maysun kin kashe ni waya gayamiki ina da alaƙa da waɗannan mutane?" Makwabtaka kawai ta haɗa ni dasu sai kuma kasantuwar mun fito ƙasa ɗaya amma daga wannan babu wata alaƙa a tsakanin mu. Ai kuwa Maysun ta karawa kukanta kaimi kusan larabawa da mugun so 'ya'ya tun Aliyu na Uku yana rarrashinta har ya zuba mata ido shi ma ya ji da kansa. *NIGERIA* Bugun kofar ɗakin Sadiya Mami ke yi tare da kiran sunanta amman Sadiya tana ji tai banza da ita, hali yanzu kowa haushinsa take ji Mami bata fasa buga mata ƙofa ba sai da ta kai da yi mata rantsuwa sannan ta taso da kumburarrin idanunta tana zuburo baki fuskar nan ta, ta a haɗe "Mami ba fa mutuwa nayi ba da za a dame ni da bugun ƙofa. Ta faɗa sa'ili da ta buɗe kofar wawan duka Mami ta kai mata tai sauri kaucewa cikin ɓacin rai Mami ta shiga zazzaga mata masifa "Ka ji min 'yar banza yarinya har ni za ki faɗa wa maganar banza da ki mutu ɗin ja'irar yarinya mai taurin kan tsiya to da kika ƙunshe kanki ɗaki tun jiya nufinki kika kashe kanko ko me?" "Ba za ki taɓa gane halin da nake ciki ba Mami. "Dallah rufe min baki shashasha banza Abba ne kaɗai namiji da ya rage a duniya da har za ki nemi ki illatar da rayuwarki domin sa?" "Mami ni fa duk abunda za ki faɗa jin ki kawai nake yi amman zuciyata ta riga tayi nisa akan Yayanmu shi ne namiji tilo dake sarrafa zuciyata. Duk mugun kallo da Mami ke yiwa Sadiya bai sa tayi shiru da sai da kai aya, hakan kuwa ba ƙaramin linkawa Mami ɓacin ranta ya yi ba,dan haka ta cigaba da zazzaga mata faɗa "To bari ki ji idan ma kwayoyi da kike sha ne ke ƙara tunzira ki kina wannan shashanci a banza don kuwa Abban da kike hauka akansa yana can gidansa da matansa har gudu biyu hankalinsa kwace zuciyarsa zaune,ke kuma kina nan kina haukar banza. Sosai kalaman Mami suka taɓawa Sadiya zuciya don kuwa jin su take yi tamkar tafasasshen ruwa zafi ne Mami ta watsa mata a sassan jikinta, ta juya a fusace ta nufi bathroom Mami ta bi ta da kallon takaici, tana kissima dole ta ɗauki tsatsauran mataki akanta. *ABBA BASHIR MANSION* Rumaisa tana komawa ɗaki kiran Aunty Raliya yana shigowa wayarta da hanzari tayi picking daman tana buƙatar abokin da za ta fesarwa da abun da ke cinta a zuciya, ko gaisawa bata bari suka yi da kyau ba ta shiga fadar "Aunty kin ga maganarki ta kusa tabbatar ko?ba kisan Habibi raba mana girki ya yi ni da wannan kwailar yarinya ba. Dariyar takaici Aunty Raliya ta yi kamin ta ce "Yoo bana gayamiki ba ai su maza da kike gani munafukai ne ke ce kike mata kallon kwaila shi ai ganinta yake yi daidai da ke. "Uhm! Aunty daina fadar wannan magana domin idan ana sallah ba a magana ni kadai nasan irin dimaunta Abba da nayi a daren jiya ba ki ga yadda ya hauka cemin da dukka alama bai taɓa sani 'ya mace ba sai jiya ni fa ko yau sai na sake zuba masa wannan abu da kika bani dan ni naga amfaninsa aunty, ba ki ga yadda Abba ya dawo tamkar wani ingarman doki. Dariya aunty Raliya ta kece da ita "yarinya ki ce kin zama 'yar gari?" "Wallahi kuwa aunty ai al'amarin babba ne sannu a hankali sai na ɗauke hankali Abba kacokan ya dawo gareni ni kaɗai, sai na mantar dashi wacce kwaila. Aunty Raliya ta ce "Da kyau ƙanwata gara ki nuna mata ruwa ba sa'an kwado bane. Daga haka suka cigaba da hira yayin da Aunty Raliya sai ƙara koyawa Rumaisa yadda za ta mallake AB ta hanyar sex ta kuma yi mata alƙawari za ta sake kawo mata wasu magunguna mata masu zafi tare da rikita ƙwaƙwalwar namiji. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/17, 4:43 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 072. AB yana shirya wa ya fice daga gidan kafin ya fita sai da ya leƙa ɗakin Rumaisa ya gayamata ya fita, ta rako shi tana gani ya nufi ɗakin Aydah ta bata fuska duk ta bi ta haɗe rai. Koda Ya shiga ɗakin sai ya tarar da Aydah tana bacci bai tashe ta ba sai ya fito, Rumaisa tana nan tsaye akan staircase tana jiransa, tana gani ya yi saurin fitowa ta saki ɓoyayyiyar ajiyar zuciya suka jera side by side, Huwaila dake kitchen ta bi su da harara daidai ƙofar fita daga main parlor ya dakatar da ita ta sumbaci kumatunsa da lips ɗinsa wai good bye kiss ne aka basa shi kuma sai washe haƙora yake yi. Sosai Aydah tasha bacci sai wuraren la'asar ta falka da sauri ta nufi bathroom ta watsawa jikinta ruwa ko zai sake daga kasala da take ji ta lulluɓe ta, tayi sallar azahar bata shi ba sai da aka yi la'asar tayi tunawa da hudubar da Siyama da Huwaila suka yi mata dinga kwalliya da saka tufafi masu kyau, shiyasa tana linke praymat ta nufi gaban dressing mirror ta ja stool ta zauna kasancewarta wacce bataso kwalliya iya powder ta shafa wacce ta dace da skin ɗinta, ta zizzirawa idanunta kwalli shi ma don ta tuna da yayanta yana so kwalli da ba don haka ba da ba za ta shafa ba, ta bi lips ɗinta da man lebe ba wata kwalliya a zo a gani tayi ba amman sai tayi wani irin kyau na ɗaukar hankali. Ta tashi ta nufi closet ɗinta gefen da sababbin tufafinta ta buɗe, ta dinga bin su da kallo daga ƙarshe ta ciro wani tsadadden lace red color wanda aka yiwa adon flower light green ɗinkin straight gown ta bi jikinta da khumurah tare da designer perfume Aydah bata iya dauri ba iyakancinta tayi ture ko yanzu shi tayi yayin ta saki kitson kanta ya sauka a shoulder ɗinta. Ta zura plate shoe ta dauki wayarta ta sauko ƙasa direct ɗakin Huwaila ta nufo da yake bata ganta a downstairs parlor ba. "Maa shaa Allah barakallah! Kin ga yadda kika yi kyau Auta sai kace kece amarya. Huwaila ta faɗa sa'ili da Aydah ta zauna kusa da ita murmushi kurum Aydah tayi "Ai sau uku ina zuwa duba ki sai naga baki tashi ba baccin naki ya yi nisa tausayinki ya hana ni tashe ki don nasan jiya ba wani bacci kirki kika yi ba. "Uhm! Aunty Huwaila da kin sani ko tashe ni kinga ko da na tashi har lokacin sallar azahar ya wuce. "Dama da yanzu nake da niyar na je na tashe ki to kuma sai wannan kodaddiyar amaryar ta kira ni na kai wa baƙinta abinci. Ke ci abinci kuwa?" "Ban ci ba, bana ji yunwa idan dai da akwai raguwar smoothie a fridge zan sha. "Akwai shi ma tashi mu je parlor na dauko miki har da cupcake akwai ban daɗe da gama shi ba nayi saboda baƙi da za a dinga yi masu zuwa gulmar gani amarya. Dariya Aydah tayi tana faɗin kai "Aunty Huwaila da sharri kike duk ranar da bakinki ya subuce kika faɗin wannan sunan a gabanYayanmu za ku kwashe 'yan kallo ni dai ina gefe. Hannunta Huwaila ta kama Aydaah ta miƙe yayin da Huwaila ta cigaba da faɗar "Ke rabani da wahala in shaa Allah ba zan taɓa wannan subul da baka ba don naga Yayanmu sai wani rawar ƙafa yake yi akanta. "Atoh! Kema dai kya faɗa gara ki yiwa bakinki linzami. Yayin da Aydah ta ƙarasa magana tana zipping bakinta,da wannan zance suka iso parlor Aydah ta nufi kujera ta zauna Huwaila kuma ta wuce kitchen ta dauko mata smoothie ɗin da cupcakes da ta zuba mata cikin plate. Aydah tana ci suna taɓa hira sai ga Rumaisa da ƙawayenta su uku suna saukowa daga bene, kallo guda Aydah tai musu ta kauda fusrkarta ta cigaba da cin cake ɗinta. Da suka iso tsakiyar parlorn sai ƙawayen nata suka tsaya sai da suka kare ma su Aydah kallon wulaƙanci sai kuma suka taɓe baki, sai guda daga cikinsu ta dubi Rumaisa tana wani irin yatsina fuska "Rumaisa wacece kishiyar taki acikinsu ita dai wannan tayi zubin 'yan ƙauye wannan kuma tayi kankanta da shiga other room?" Wani guntun tsaki Rumaisa ta ja wanda yafi kama da na takaici kamin ta juya tayi pointing Aydah da bakinta "kin ganta nan kwaila nan ita ce uwargidan Abba Bashir. Tana dasa aya suka kece da dariyar izgilanci har suna tafawa a tsakaninsu "Wai dan Allah Rumaisa da gaske kike yi wannan kwailar yarinya ita ce uwargidan Abba Bashir?" "Allah kuwa ita ce ba ki ga lokacin da muka shigo parlor nan yadda ta kalleta ta watsar ba?" "Na ko gani har acikin zuciyata na ce ina Rumaisa ta haɗu da yarinya karamar marar tarbiyya ashe-ashe! Sai suka sake kwashe da dariya wacce tafi ta farko, Huwaila har ta buɗe baki da zimmar yi magana Aydah ta riƙe mata hannu tare da girgiza mata kai dole ta haɗiye martani da taso ta mayar masu. "Mtss! Gaskiya Abba Bashir ya ci baya wanda yake da ƙosasshiyar mace ga gaba ga baya ga ko'ina ya cika dam! Me zai yi da wannan jinjira?" Ɗaya daga cikin ƙawayen Rumaisa mai suna khady ta faɗa. "Gane min hanya ƙawata ai sunan tana matarsa ne kawai bai taɓa ko kama ɗan yatsanta da suna wani abu ba kinsan aure huce haushi ne aka yi masa. Cewar Rumaisa tana wani bubbuɗa hanci. "Aure huce haushi ko kuma dai na ƙarin haushi? Kamila ta faɗa tana taɓe baki. Anan ma dariya suka sake yi Aydah dai bata ce uffan ba sai cake ɗinta take ci tana haɗawa da smoothie, sai da suka gama yi mata izgilanci kala daban daban kamin su fice har parking lot Rumaisa ta raka su suna ƙara yi mata hudubar ta zage damtse ta kori Aydah daga gidan. Don wannan kwaila ba a kira ta da sunan kishiya ba. "Auta meyasa kika hanani mayar wa waɗannan sakarkarun amsa?" Sai da Aydah ta haɗiye cake ɗin bakinta kafin ta ce "Babu amfani aunty Huwaila gara ki bar su kawai su yi ta haukar su, su kaɗai ai ɗan hakki da ka raina shi ke tsokane maka ido ba dai kallon kwaila suke min ba. Sai ta girgiza kai tayi ƙwafa sai kuma tasaki murmushi tare da faɗin "Mu tafi a haka ni kwaila ce amma wallahi sai wannan da ta raina ta hana mata rawar gabar hantse. "Da kyau uwar ɗakina haka nake so ji da yarda Allah sai kin juya Yayanmu a tafin hannunki, sai kin sarrafa shi da masarrafi da babu wata 'ya mace a duniya nan da ta isa ta sarrafa shi. Kamin Aydah tayi magana Rumaisa ta turo ƙofa don haka sai Aydah ta haɗiye maganarta,har Rumaisa ta fara tattaka mattakalar bene sai kuma ta tsaya ta waigo ta ce "ke 'yar aiki zo mu je ki gyara min parlorna. Tana karasa magana ta juya tana wani jujjuya mazaunai. Daga Aydah har Huwaila suka bi ta da kallo baki buɗe Huwaila ta ce ba inda za ta sai da Aydah ta lallaɓa ta kamin ta je ta gyara mata parlor ɗin. *HAMBURG GERMANY* (Mercure hotel) Sai da Maysun taci kukanta mai isarta shi dai Aliyu na Uku yana zaune dafe da goshinsa,yana jin kukanta har tsakiyar kansa amman ya gaza rarrashinta, abin ka da farar fata nan da nan fuskar Maysun ta kumbura tayi jajur ta ɗago da kumburarrin idanunta ta kalli side ɗin da Aliyu yake aranta ji take kamar ta taso ta rufe shi da duka domin duk abin da ya faru laifinsa ne. Cikin kakkausar murya wacce da jin ta kasan mai ita yasha kuka ta kira sunan Aliyu na Uku "Ali!! Ali ka faɗamin gaskiyar lamarin nan idan har kasan inda ɗana yake kada ka yi wasa da raunina na 'ya mace ka yi gaggawar haɗani da ɗana shi kaɗai ne gudan jinina a duniya domin kai ina da yaƙini a yanzu ka yi aure ka haifi wasu 'ya'ya saboda haka kada ka yi wasa da hankalina ka faɗamin ina Azhar yake?" A hankali ya ɗago idanunsa ya jefa su cikin ƙwayar idonta wacce ke saurin kassara masa jinin jiki kallonta ya cigaba da yi da mamaki ga wani irin jaa da idanunsa suka yi wanda sai da gaban Maysun ya buga "Maysun sau nawa kike so nace dake bansan idan ɗanmu yake ba, da nasan inda yake Maysun me zai sa na ɓoye miki bayan nasan kina da cikakken hakki akansa. Wani sabon kuka ta sake fashewa dashi ta kifa kanta gefen gado jiki a sanyayye Aliyu na Uku ya taso ya zauna kusa da ita ya dafa kafaɗarta cikin sigar rarrashe da son kwantar mata da hankali yake faɗin "Kuka nan ya isa haka Maysun na yi miki alƙawari matuƙar yaronmu yana raye sai na nemo shi zan dawo miki da Azhar wannan alƙawarina ne. Da sauri Maysun ta faɗa jikinsa ta ƙamƙame sa cikin murya kuka take faɗin "Ali meyasa duk tsawon shekaru nan ba ka nemi ni ba bayan kasan akwai igiyoyin aurenka akaina shin Ali ko kadaina sona ne?" Girgiza kansa ya yi yana ji tsohon miki da ke can ƙasan zuciyarsa. "Ali ka dube ni da kyau na canza na daina saka tufafin da ba ka so yanzu na zama cikakkiyar musulma dukka abubuwan da ba ka so Ali na daina dan Allah karka sake barina ina sonka ina so na rayu da kai har izuwa ƙarshen numfashina. Dukka maganganu da Maysun ke yi Aliyu na Uku ba abun da yake yi sai jujjaya kansa domin shi kadai yasan irin halin kunci da ya share tsawon shekaru acikinsa da baya tare da ita Maysun ita ce mace ta farko da ya fara so kuma har kawo yanzu ita ce ke sarrafa zuciya da gangar jikinsa farin cikinsa yana tare da ita. "Idan har da gaske har yanzu kina sona Maysun za ki rayu dani ki shirya mu tafi Nigeria tare mu nemo yaron mu a tare. Cikin muryar kuka ta ce ta amince daman can Abbie ne matsalarta yanzu kuma ya mutu mahaifiyarta dake nan ƙasar Germany kuma batada matsala, don ta tsufa ita ma ta kanta take yi. Bayan kwana uku Aliyu na Uku da Maysun suka dira a garin Lagos kasancewa gidan da yake su Anaal na ciki sai kawai ya kamawa Maysun hotel kamin ya nema mata gida. *ABBA BASHIR MANSION* Sai around 9:10pm AB ya dawo gida sa'ilin da ya shigo main parlor Huwaila kaɗai ya tarar a zaune tai masa sannu da hanya ya amsa tare da tambayarta Aydah ta ce tana ɗakinta, kaitsaye ɗakin Aydaah ɗin ya nufa hankalinsa kwace ya tura ƙofa Aydah dake zaune a gaban dressing mirror tana shafa mai tasaki towel ɗin jikinta sai faman massage ɗin 'yan mitsitsi abubuwanta da coconut oil ɗazu ne tayi browsing a Google tana neman abun da ke sa nonuwa su ƙara girma sai taci da massage ɗin boobs da coconut oil yana kara musu girma, Allah yasa tana da oil ɗin shi ne fa tana fitowa daga wanka ta dukufa ganawa bayin Allah azaba. Ashe ta manta bata rufe ƙofa ba, bata tashi tunawa ba sai da taga AB ya shigo yana yi arba da abun da take yi ya saki baki tare da zaro idanuwa"what the hell are you doing, baby? Cikin sauri Aydah ta rarumi towel ɗinta ta mayar a ƙirjinta sai tayi rau-rau da idanuwa, cikin sanyi murya kamar za ta yi kuka take magana "Why would you come into my room without knocking on Yayanmu kai fa kace babu kyau shiga wuri out permission. Murmushi gefen baki ya yi ya tako a hankali ya iso wurinta "Ni kam me kike yi ne haka baby sai na kamar kina murza no.... "Yayanmu Dan Allah karka ƙarasa faɗar sunan kai ba ka ji kunya ne?" Dariya mai ƙaramin sauti AB ya yi yana girgiza kai "me zai sa na ji kunya ko kin manta nasan lokacin da bakida su. Aydah ta ɗago tare da galla masa harara tana murguɗa baki sai ta miƙe tsaye tana ƙara dafe towel ɗinta ta kalle shi tana tuna sanda ya nemi zaucewa akansu,sai kawai ta sakar masa murmushi ta nufi closet ta buɗe ta ciro kayan baccinta. A natse AB yake ƙara mata kallo yana wassafa nan da shekaru uku ko hudu Aydah za ta iya zama cikakkiyar budurwa kalar da yake so wata kila ma ta zarce yadda yake tunani ko zai ɗauki shawarar Abdulkarim ne ya dinga ɗora ta a hanya sannu-sannu yana biya mata karatu tana dauka Abdulkarim ya sha faɗa masa 'yan cwt 16 ɗinan sun fi daɗin sha'ani ko yanzu ma kafin ya shigo gida sai da Abdulkarim ya kara jaddada masa haka. To kodai zai dauki shawarar abokinsa ne don ko yace zai rabuda Aydah anan gaba idan ya tuna da halaccin Daddy a garesa ya ji, jikinsa ya yi bala'in sanyi. Har Aydah ta wuce ta gabansa ta shiga bathroom ta sako kayan baccinta yana tsaye ya yi nisa a duniyar tunani. "Yayanmu!! Aydah ta kira sa cikin ɗaga murya ya yi firgigit kamar wanda ya tashi daga bacci sai kurum ya shiga sosa ƙeya. "Wai me ke damunka ne? Na ga ka zurfafa tunani. Ya ja numfashi tare da saukewa ya ce "Ba komai bara na je nayi wanka ki dauko mana abinci ki kawo parlorna mu ci. Ya ƙarashe magana tare da juyawa ya buɗe ƙofa ya fita, Aydah ta bishi da murmushi ta ciro ƙaramin veil daga closet ta yane kanta ta sauka ƙasa already Huwaila ta haɗa abinci ta dauka ta haura zuwa parlorn sa. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only. ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/18, 1:40 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 073. Koda ta shiga parlor ɗin babu kowa aciki ta kunna kayan kallo tasaka zee world ta nemi kujera ta kame jin kaɗan da zamanta sai ga Rumaisa ta shigo cikin wata sexy transparent night gown har ɗan siririn pant ɗin jikinta ana gani, sai wani fitinannen ƙamshinta da ya cika parlorn ta kalli Aydah a ɗage ta taɓe baki, ita ma ta nemi kujera ta zauna bayan kamar mintuna goma sai ga AB ya shigo jikinsa sanye da fararen kayan bacci, idanunsa na sauka kan Rumaisa ya nemi natsuwarsa ya rasa nan da nan jarabarsa ta fara motsawa da kyar ya yi control ɗin kansa ya zauna ya umarce Aydah da ta zo tayi musu serving, Aydah kamar ta ce ba za ta iya ba don ta lura da mayataccen kallo da yake yiwa Rumaisa ita kuma sai rausayar da kai take yi cikin sigar jan hankali adaddafe Aydah ta tsakura abincin ta bar musu parlon, kamar jira Rumaisa take yi Aydah ta fice ta, tashi ta je ɗakinta ta dauko mango juice ɗin da ta zubawa AB men power aciki ta kawo masa daman tasan yana ɗaya daga cikin favorite juice ɗinsa. Cike da farin ciki ya karɓa ya shiga sha, sai da tabbatar da ya shanye ta tashi ta koma ɗakinta ta dauko wani matsi daga cikin kayan 'yar Sudan ta haɗo mata tun daga Sudan kimanin duba hamsin ake saida shi ɗan firitt acikin mini container, ɗan kaɗan ake matsawa kuma ba a wanke shi yana bala'in matse virgina mace za ta dawo budurwa koda an taɓa saninta 'ya mace wannan yasa Rumaisa ta siye shi so take kullum idan Ab ya yi tarayya da ita ya ji ta kamar shi ne farko da ya fara saninta 'ya mace. Jikinta har wani kalar rawa yake yi ta shige bathroom ta matsa mitsinta, da gangan taƙi komawa parlorn sa tayi kwanciyarta. Ab ya ji shiru-shiru Rumaisa bata dawo ba dama gogan naku ya fara ɗaukar charging da sassarfa ya shigo ɗakinta, tun daga bakin ƙofa ya cire rigar jikinsa. Wani kalan romance ɗin junansu suke yi hatta da bulbs sun kashe kashewa cikin fitar hayyaci AB ya zare pant ɗin jikin Rumaisa sai kawai idonsa ya sauka akan pant ɗin da ya jiƙe da jini cikin kaɗuwa ya zaro ido "ji...ji..jini habibty! Ya faɗa cikin shaƙaƙƙiyar muryarsa da bata fita sosai saboda tsananin sha'awa, a tsorace ita ma Rumaisa ta taso daga kwance da take ta kalli pant ɗinta da AB ke nuna mata "Na shiga uku Habibi period ɗinan ne ya dawo. Cewar Rumaisa kamar za ta rushe da kuka sakin pant ɗin Ab ya yi ya koma ya kwanta rigingine yana dafe mararsa ji yake ana kartarsa a mara, har wasu ƙwalla jaraba ke fitar masa a idanuwa, Rumaisa ta yi shiru tare da zurfafa tunani dukka yaushe ne ta gama period da za a ce ya dawo mata idan bata manta ba ana jibi fara bikinsu tayi wanka sai kuma ya dawo mata yanzu abun da bai taɓa faruwa da ita ba. Da ta matsanta wa ƙwaƙwalwarta da tunani sai ta alakanta hakan da wata kila sex ɗin da ya faru tsakanin ta da AB ne saboda shi ne first time ɗinta da wani namiji ya taɓa sani ta 'ya mace daman Kamila ta gayamata ana ganin jini a daren farko to amma wannan jini ba a daren farkonsu ya zo ba. Gudu kada ta hartsunawa kanta tunani sai kawai tayi watsi da al'amari ta, tashi ta shiga bathroom ta kimtsa jikinta. Koda ta dawo ta tarar da AB sai faman munguli yake yi dafe da mara,idanunsa sun kada sun yi jajur ita kanta da tayi arba dashi sai da gabanta ya faɗi musamman da ta tuna ita ce sanadin shigarsa wannan hali da saurinta ta ƙarasa kusa dashi ta zauna tana ɗora hannunta kan sumarsa tana shafa "i'm sorry Habibi period ɗina ne ya dawo amma zan taimaka maka ka sami relief okay?" Su AB babu bakin magana sai gyaɗa kai yake yi Rumaisa ta miƙe ta cire rigar jikinta ta kashe musu bulbs, sosai ta baje basirar ta a ƙokarinta na gani AB ya sami natsuwa a maimakon haka sai ma ya ji abun da yake ji yana ƙaruwa yayin da ita ma Rumaisa ta gaji likis gabobbin jikinta ko'ina ciwo yake mata boobs ɗinta sai zogi suke mata kamar kan zai cire,duk iya ƙokarin Rumaisa kasa jurewa tayi batasan lokaci da ta hankada AB daga jikinta ta buga tsalle ta sauka daga gado tana yarfe hannayen, cikin fitar hayyaci AB ya taso ya wawuro ta, ya mayar da ita kan gado ya shiga tattaɓa ta "Dan Allah Habibi ya isa haka jikina ko'ina ciwo yake min. "Ki yi haƙuri Habibty ki taimaka min nayi realizing ni kaɗai nasan irin azabar da nake ji a mara ta. "Ba zan iya ba Habibi wallahi na gaji haba tun ɗazu kake abu guda da za ka yi realizing ɗin da zuwa yanzu ka yi ni dai ka kyaleni. Ab bai kyaleta ba ya cigaba da nemawa kansa natsuwa, cikin fusata ta sake ture shi ta sauka ƙasa tana galla masa harara "Wannan wacce Irin jaraba ce Abba ni fa na gaji ba abin da za ka sake samu a wurina ehee! "Rumaisa ni fa mijinki ne idan ba ki taimaka min ba wa nake dashi da zai taimaka min?" Kallo uku saura kwabo tai yi masa ciki ta ja masa tsaki cikin gatsali ta ce "Ka ji ka da wani zance halan ni kaɗai ce matarka a gidanan, ita wancan da ka yi ikirarin ita ce uwargidan ka miye amfaninta?"Ka je wurinta na yafe mata kwana na ka je ka sami natsuwa a wurinta na yarje maka. Duk da AB yana cikin hali tsananin bukatuwa hakan bai hana masa fahimtar wacce take nufi ba, ya zaro idanuwa "Habibty Aydah fa yarinya ce ƙarama ba za ta iya daukana ba idan har ba so kike na kisan kai ba ki daina alaƙanta wannan babban al'amari a tsakanin mu. Wani kalan kishi da takaicinsa ya kama Rumaisa dan gani take yi ya ma raina mata da hankali, idan har Aydah bata isa ba miye amfaninta a wurinsa?" Saboda haka ta saki murmushin mugunta "To tun da ba zata iya daukarka ba batada amfani ka sake ta kawai,ni kuma nayi maka alƙawari zan yi ta ba ka farin ciki har izuwa ƙarshen rayuwata. "Mtss! Gaskiya kina da matsala Rumaisa ke yanzu ko cewa nayi zan saki Aydah idan kina da hankali da tunani ai ke mai hanani ce. "Auu! Haka ma za ka ce? To ka tafi wurinta mana da bata isa aure ba da ubanta bai aura maka ita ba, ka je ka sauke buƙatarka akanta. Tana ƙarashe magana ta shige bathroom ta rufe ƙofa da key Ab ya bita ya dinga dukan ƙofar yana mata magiya, ita kam daɗi ne ya lulluɓeta sai ƙara maimata masa take yi ita fa ta yafe ya je wurin uwargidansa, tsabar takaici yasa shi baro mata ɗakinta ya nufi nasa, wanka ya yi da ruwa masu sanyi ko zai ji sassauci a maimakon haka sai ya ji sha'awar tasa ta ƙara karuwa bai san cewa magani bai ma fara aiki ba yanzu ne zai fara, jikinsa har wani kakkarwa yake yi haƙora sa na sama na haɗewa da na ƙasa da fari yaso ya yi ta maza ya danne abun da yake ji sai dai gangar jikinsa ta kasa bashi haɗin kai, ƙwaƙwalwarsa ta dinga tunano masa abun da ya taɓa wakana tsakaninsa da Aydah ya tabbata wannan romance ɗin kaɗai idan ya samu a yanzu natsuwarsa za ta dawo jikinsa,abubuwan Aydah sun fi masa na Rumaisa daɗi taɓawa duk da ya raina girmansu. Nan da nan tsigar jikinsa ta dinga mimmiƙewa da sauri ya tashi ya sauka daga gado ya saka jallabiya akan boxer ɗin jikinsa ya fice adaddafe ya isa ƙofar ɗakin Aydah cikin rashin sa'a ya tarar da ƙofar ɗakinta a rufe, ji ya ya kamar zai rusa ihu ya daɗe a wurin tsaye daga ƙarshe ya juya da nufi komawa ɗakinsa, sai kuma ya fasa saboda yanayinsa sai ƙara sauyawa yake idan har ya ce zai biyewa zuciyarsa zai cutu a banza dan haka ya dawo batareda da ɓata lokaci ba ya yi knocking ƙofarta. Aydah daman ba bacci take yi ba tun sanda ta baro parlornsa ta dawo ɗakinta take kwance cikin ƙunci da ɓacin rai, duk duniya idan da akwai abun da ta tsana yake sauri jefa ta cikin ɓacin rai bai wuce idan taga Rumaisa tana mannewa yayanta ji take kamar zuciyata za ta fashe. Kamar daga sama ta ji ana bubbuga mata ƙofa da sauri ta yada ganinta akan ƙofar "waye anan ko Aunty Huwaila ce?" Aydaah ta furta cikin yanayin tsoro. "Baby yayanki ne zo ki buɗe masa ƙofa. Ab ya faɗa cikin rikitacciyar murya. "Yayanmu kaine da gaske? "Ni ne baby zo ki buɗe min. "Yayanmu lafiya kake kuwa na ji muryarka ya shaƙe?" "Baby banida lafiya idan ba ki buɗe min ƙofa ba mutuwa zan yi dan Allah ki zo ki buɗe kin ji?" Aydah tana ji ya ambaci kalmar mutuwa tayi wani wawan tsalle tsalle ta sauko daga gado,tana faɗin "Na shiga uku Dan Allah Yayanmu karka ka mutu ka barni. Ta karashe magana tare da buɗe ƙofar yana tsaye idanun sa ya yi masa jajur yana dafe da cikinsa. "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Sannu Yayanmu shigo daga ciki na je na nemo maka magani. Aydah tayi magana tana jawo hannunsa ya shigo ta maida ƙofa ta rufe dakyar yake iya cira ƙafafuwansa ya taka su koda ya isa kan gado ji yake yi kamar zai kife ƙasa, Aydah ta tausayinsa ya gama cikata dan har idanunta sun fara ciccikowa da ƙwalla ta zauna kusa dashi tana leƙa fuskarsa "Sannu Yayanmu halan cikinka ne ke ciwo?" "Uhm! Ya faɗa tare da gyaɗa kansa yana wani marairaice wa hakan kuwa ya ƙara tasirantuwa a zuciyar Aydah, duk ta bi ta ƙara rudewa sai sannu take masa, AB ya rasa ta ina zai fara wannan shi ake kira ga ƙoshi ga kwanan yunwa ga dai Aydah zaune a gabansa amma farga da kunya sun hana masa tabuka komai, cike da karaya zuciya ya kwanta akan gadon nata da yake jin sa wani irin ya rufe idonsa yana ji sanda ta hayo gado tana leƙa fuskarsa "Yayanmu ina ka ajiye first aid box na duba maka ko da akwai magani ciwon ciki. Batareda da ya buɗe idanunsa ba ya ce "Baby ciwona bana magani bane ina ji mutuwa zan yi ki yi min addu'a kin ji?" Yana rufe bakinsa Aydah tana faɗawa jikinsa ta ƙamƙame shi tare da fashe da kuka tana masa magiyar kada ya mutu ya barta idan ya mutu ita ma mutuwa za ta yi, yadda tai bala'in ƙamƙame shi yasa ya ji noti kansa na kwancewa daman mai nema a duhu ballantana an kunna masa haske, nan da nan ya saka hannayensa biyu ya zagaye tiny waist ɗinta, ya tura kansa cikin wuyanta yana sauke mata numfashinsa mai ɗankaran zafi sannu-sannu yake shaƙar ƙamshinta kamin ya saki ƙugunta ya shiga shasshafa ta, Aydah dai tayi lankwas a jikinsa tana ji yadda ake bi sassan jikinta da hannayensa kamar daga sama ta ji ya ɗago ta daga jikinsa ya cire rigar jikinsa tare da cire mata, ta ta tofa anan Aydah jikinta ya fara rawa ta kare ƙirjinta da hannayenta cikin fitar hayyaci AB ya ce "Baby idan kika hana ni mutuwa zan yi ko kina so na mutu ne?" Aydah ta girgiza kai hawaye na bi kumatunta "To zo ki ji wani labari zan ba ki ba wani abu zan miki. A tsorace ta ɗan matsa jikinsa da sauri ya rarumo ta ya manna ta a ƙirjinsa yana sauke numfashi, ɗan ƙaramin bakinta da ba zai taɓa mantawa da gardinsa ya lallaɓo ya haɗe da nasa, wani kalar sha yake yiwa bakin nata cikin wayau da dabara ya kwantar da ita ya bi ta ya yi mata rumfa da faffadan ƙirjinsa saboda faɗin ƙirjinsa ko gani Aydaah ba a yi da sauri ta tura hannayenta ta karkashin damtse hannunsa ta rufe boobs ɗinta "meye haka baby?" Ya yi magana yana ɓata rai duk sai Aydah ta ji ta daburce ganinsa take yi tamkar wata sabuwar halitta ba yayanta da ta sani ba. Ta daga idanuwanta kaɗan ta kalle shi suna haɗa ido tai sauri runtse idanuwanta "Baby kada mu yi haka dake a yanzu wurinki kaɗai na ke da tabbacin magance matsalata idan kika hana ni samun natsuwa daga gareki wallahi komai zai iya faruwa dani. Kaɗan daga cikin maganganunsa Aydah ta fahimci su yayin da waɗansu bata gama fahimtar su ba ta ji ya ware hannayenta daga rufe ƙirjinta da tayi. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/19, 2:49 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 074. Saukar tattausan lips ɗinsa ta ji akan ƙirjinta da sauri ta runtse idanuwanta gan-gan hakan da tayi yasa AB ya ɗago Ya kalli rufaffun idanuwanta murmushin gefen baki ya subuce masa hakan da tayi sai ya ba shi kwarin gwiwa cigaba da aiwatar da manufarsa, kowacce gaɓɓa dake jikin Aydah sai da AB ya bi ya lashe ya tande, tuni ruwan kan Aydaah suka tsiyaya jinin jikinta ya dasƙare ta rasa wacce duniya take. Bata dawo ainihin hankalinta ba sai da ta ji AB ya ware mata kafafuwa yana neman hanyarsa anan kam sai da ta saki kakkarfan ihu ta damƙe muscles ɗinsa ta riƙe su gan-gan, duk da AB bai ƙarasa shigewa wurin dukka ba ya ji notin kansa ya kwance ya shiga kurma ihu da sambatu marasa kan gado,da farin tausayin Aydah yake ji shi ya hana shi kutsawa dukka sannu-sannu da daɗi ya fara kai masa makura bai san sanda ya ƙarasa shigewa ba. Daga nan ya fara ihun kiran sunaye jama'a da fari Daddy da Mami ya fara kira da tafiya tai tafiya sai ya dawo kiran Sadiya da Siyama hatta Rumaisa da Abdulkarim sai da ya kira sunayen su, tsoro da mamaki suka lulluɓe ƙwaƙwalwar Aydah har ta shiga kokwanto kodai yayanta ya zare ne Allah na tuba idan ba zarewa yayi ba me zai sa ya dinga ihu yana kiran sunayen waɗannan mutane. Ga baki ɗaya Ab zaucewa ya yi ya manta da wacce nahiya yake ya cigaba da buga aiki babu kakkautawa ya manta da little Baby ɗinsa yake yi, tun Aydah tana kuka da hawaye da iface-iface har ta sadakat ta zubawa sarautar Allah ido. Sai ya zamana shi yana kuka ita ma tana yi sai dai kukansa yafi nata fita saboda ita muryarta ta shaƙe Ab bai tsaya ba har da ya amayar da dukka masifar da Rumaisa ta shayar dashi kamin ya yi collapsed a ƙirjin Aydah ga baki ɗaya ya sakar mata nauyinsa azaba ta zama mata bibbiyu ga zafi da mugun zogi da take ji a ƙasanta ga kuma nauyinsa da sakar mata saboda azaba dakyar take iya jan numfashinta. So take ta ce dashi ya ɗaga ta kada ya ƙarasa ta amma ta kasa magana ji bakinta take yi ya yi bala'in yi mata nauyi sannu a hankali AB ya fara sauke wani wahalalle numfashi sai kuma ya gangara gefen Aydah ya kwanta ya cigaba da sauke numfashi kamar wanda feverish ya kama, jikinsa na rawa. Ita kuma ta ƙanƙame jikinta tana rera kukan da babu hawaye ƙasa-ƙasa yadda muryarta ta dusashe yasa kukan nata baya fita sosai, sai da AB ya share kusan ten good minutes kamin natsuwarsa ta gama dawowa jikinsa ya tuna aika-aikar da ya yiwa Babynsa ya yi zubur ya tashi zaune ya kalleta yaga idanunta a rufe tana kuka amman babu hawaye lips ɗinta sun yi jajir nan da nan tausayinta ya dirar masa a ƙahon zuciya, ya matsa jikinta yana tattaɓata tare da kiran sunanta shi fa ya zaci ko ta sheƙa barzahu Kwata-kwata bai ji sautin kukan da take yi ba, cikin fitar hayyaci ya rarumo ta zuwa jikinsa "Baby Aydah! Baby Aydah ki buɗe idanunki dan Allah karki ki mutu na shiga uku na kashetaaaa! Ab ya ƙarashe magana da sauti mai ƙarfi hakan yasa Aydah ta buɗe kumburarrin idanunta ta kalle shi dasu cikin nauyin harshe ta furta "Yayanmu! Wata ƙarfaffiyar ajiyar zuciya Ab ya sauke tare da rungume Aydah gan-gan kamar zai maida ta cikinsa, sai kuma ya dinga sauke mata kisses akan kumatunta da tsakiyar kanta "I'm sorry Baby Yaya Abba mugu ne bai kyauta miki ba ki yi hakuri ki yafe masa. Duk da tana ji kanta wani irin hakan bai hana mata ɗagowa ta kalle shi tana cuno baki "yayana ba mugu bane kuma ni bai yi min komai ba asalima abun da yake hakkinsa mallakinsa ya karɓa ko kaɗan ban ji haushinsa ba. Tsananin mamaki da furucinta ya haifar masa bai sanda ya yi kabbara ba "Allahu Akbar! Ya ƙara rungumeta yana jin ƙaunarta tana huda jinin jikinsa, daga shi har ita a lokaci guda kasala da zazzaɓin suka rufe su yana so ya ɗaga ta su yi wanka sai dai zazzaɓi da yake ji sai daɗa ƙaruwa yake yi dole ya ja musu duvet ya kunduddune su, kana ya mannata a jikinsa zafin jikinsu yana ratsa fatar jikinsu da yake su dukka babu mai kaya a jikinsa babu ɓata lokaci wani irin naunnayan bacci ya ɗauke su. Misali ƙarfe 8 na safe Aydah tai nasarar farkawa ta shiga ware idanunta da suka yi mata bala'in nauyi a hankali har ta gama sauke su akan kyakkyawar fuskar yayanta, tai masa kur tana kallonsa ji take kamar ta cinye shi kamar ta dauwama a haka tana kallonsa. AB bai masan tana yi ba,baccinsa yake yana sauke numfashi cikin natsuwa da kwanciyar hankali, daga bisani ƙwaƙwalwarta ta dinga yi mata backwards ɗin abun da ya faru tsakaninta da yayanta a daren jiya nan take ta ji wata irin matsananciyar kunyarsa ta lulluɓeta, tana ji ba za ta sake iya haɗa ido dashi cikin ƙarfin hali da dauriya ta soma kokarin tashi zaune dakyar ta samu ta tashi ɗin ta ɗauki night gown ɗinta ta mayar. A hankali take bin ɗakin da kallo har yanzu dakin yana da raguwar duhu kasancewar window ɗin suna rufe da curtain, so take ta sauka a hankali daga kan gado ta shiga bathroom bataso ya ji tashin ta batasan cewa tun sanda ta farka shi ma ya yi nasarar tashi kallon da take masa ya hana shi buɗe idanunsa Aydah ta sake yunƙurawa a ƙaro na biyu tsananin zafin da ta ji ya ratsa ƙasanta yasa ta sakin ɗan ƙaramin ihu, da sauri AB ya tashi shi ma rigarsa ya dauka da ke yarshe akan marbles a gaggauce ya mayar a jikinsa. Aydah tana ƙyalla ido taga ya tashi tai sauri komawa ta kwanta ta ɗauki pillow ta danna akanta ita a dole kunyar yayanta take ji, kyakkyawan murmushi ne ya sake subuce masa duk yadda yaso ya taimaka mata fafur Aydah taƙi sai ma tasa mishi kuka dole ya fita kamin ya wuce ɗakinsa sai da Ya leƙa ɗakin Huwaila ya faɗa mata ta je wurin Aydah bata da lafiya domin yasan a shekarun Aydah ba za ta iya kula da kanta ba dole tana buƙatar mataimaki AB yana wanka yana tuna moment ɗinsu da Babynsa wani irin nishaɗi da farin ciki ke ta kwararo masa, gamsuwar da ya samu a jikin kwaila da ya gama rainawa ba same shi a jikin mai manya abubuwa ba asalima yanzu ne yake ji kansa cikakken namiji wanda ya amsa sunansa ango. Ashe dai kallo kitse yake wa rugo Aydah ta zama raina kama kaga gayya yarinyar ta shayar dashi ruwan mamaki ya tuna da zance Mami da ta ce idan ya haɗa shimfiɗa da Aydah sai kakkarya ta, sai ta kwana a gadon asibiti blah,blah,blah,blah shi kansa abun da zata kenan sai gashi Aydah ta tashi sumul duk da bai da yaƙini akan bai ji mata rauni ba amma duk da haka tayi kokari don bai zaci haka daga gareta ba. Ransa farin tass! Ya kammala wankansa har zuwa lokaci yana ji zazzaɓi a jikinsa ga ciwon kai da jiri adaddafe ya yi sallah koda ya gama sallah kamar kansa zai rabe gida biyu, dakyar ya tashi ya hau gado ya shige cikin duvet yana rawar sanyi. Sa'ili da AB ya kwakwasa wa Huwaila ƙofa tana zaune akan praymat tana lazimi, a tunaninta ko Aydah ce ta taso da sauri ta zare sakata sai kurum idanunta suka faɗa kansa,da farin jallabiya jikinsa da yasaka a bai-bai ta fara bi da kallo ga wani ɗan uban squeezing da tayi shi kansa AB ɗin a birkice yake sai kace wanda ya yi dambe da kura, ga baki ɗaya ya dawo wani kala na daban. Maganar da ya yi yasa Huwaila ta dawo natsuwarta ta gaishesa bai amsa ba sai ya ce ta je Aydah bata da lafiya, da yake Huwaila ba yarinya bace tuni ta fahimci abun da ya faru Ab yana juyawa ta washe baki ko hijab ɗin jikinta bata cire ba ta ruga ɗakin Aydah, tana tura ƙofa Aydah da ke bin bango za ta shiga bathroom ta juya a rikice sai tana gani Huwaila ce sai kawai tasaki kukan shagwaɓa, cikin sauri Huwaila ta cire hijab ɗin jikinta ta kama Aydah suka ƙarasa bathroom ruwa masu zafi ta sirka a bathtub ta zuba dentol kaɗan ta umarce Aydah da ta shiga tai ka ji ihun da Aydaah ta kurma sai da Huwaila ta gwada mata ƙarfi ta danne ta cikin ruwa. Sosai Huwaila ta gasa Aydah ita kanta Aydah ɗin ta ji daɗin ƙasanta sai dai zazzaɓi da take ji ya hana ta ji daɗin jikinta, a zaune tayi sallah Huwaila ta kawo mata tea mai zafi dakyar tasha rabin cup sakamakon appetite da bata dashi anan wurin da tayi sallah ta dunƙule jikin hijabin jikinta, Huwaila tana taɓa jikin Aydah ta ji wani irin mugun zafi daman ta zaci faruwar haka saboda shi ne farko yi ta gashi abun ya haɗu da ƙarancin shekaru. Panadol ta nemo ta bata tasha ta dauko duvet ta rufa mata, sannan ta cire bedsheet da ya yi kaca-kaca da jini ta jifa shi cikin washing machine ta wanke ta nufi backyard inda igiyar shanya take ta shanya shi ta dawo gun Aydah sai da tayi bacci sa'annan Huwaila ta fice kitchen ta shiga ta soma haɗa breakfast. Gimbiya Rumaisa yau baccinta tasha mai rai da lafiya ba ita ta tashi ba sai misalin ƙarfe 11:07am ta yi miƙa tare da doguwar hamma kana ta ture duvet ɗin jikinta ta zuro ƙafafuwanta akan tiles ta sauka daga kan gado ta wuce bathroom lokacin da ta cire rigar jikinta mamaki ne ya rufe ta gani yadda rigar tayi staining da jini bata taɓa period tayi rushing irin wannan ba duk tsoro da fargaba ya gama cikata cike da rashin natsuwa tayi wanka ta fito, tana kammala shiryawa ta daga waya ta kira aunty Raliya ta zayyana mata halin da take ciki, Raliya ta ce ta kwantar da hankalinta jinin al'ada yanayin haka nan ta jira idan har ta cika wa'adin kwanaki da take yi bai dauke ba to dole ta tafi asibiti taga likita. Wannan bayanin na Aunty Raliya ya kwantar wa da Rumaisa da hankali har ta sami kwarin gwiwa zuwa ɗakin Ab, a kwance ta iske shi kunduddune cikin duvet mamaki ne ya kamata sai kuma ta tuna da halin da jiya ta jefa shi nan da nan tausayinsa ya rufe ta, ta hayo gadon tana kiransa "Habibi!Habibi lafiyar ka kuwa kake bacci har yanzu ba ka tashi ba?" A wahale Ab ya buɗe idanunsa kaɗan ya kalleta yadda Rumaisa taga ƙwayar idonsa ta koma jaa ta kara tsorata ta shiga tattaɓa jikinsa "Na shiga uku Habibi bakada lafiya jikinka ya yi bala'in zafi. AB ya ja numfashi tare da saukewa zazzafar iska ta fita daga ƙofufin hancinsa ya maida idanunsa ya rufe ya ɗora hannunsa a goshinsa saboda sarawar da kansa ke masa, Rumaisa ta sake cewa "Habibi za ka iya tashi na kai ka asibiti?" Batareda da AB ya buɗe idanunsa ba ya kaɗa mata ɗan yatsansa alamar ba zai iya ba. Gani yadda ya yi yasa Rumaisa ta bi ta ruɗe a rikice ta sauko ƙasa jin motsin Huwaila a kitchen yasa ta nufar can cikin rawar murya ta ce da Huwaila "Ke Huwaila ajiye aiki nan ki je bakin gate ki kira min maigadi ya zo ya taimaka min mu saka Habibi a mota na kai shi asibiti bashida lafiya. Da sauri Huwaila ta aje wuƙa hannunta ta fi ce bata daɗe da fita ba sai gata ta dawo tare da maigadi, tunawa da tayi da halin da ta baro Aydah a ciki sai ta nufi ɗakinta domin ta ƙara dubata duk da dazu kamin ta baro ɗakin tayi bacci tana tura ƙofa tayi turus sakamakon gani Aydah ta yi yarshe a kasan tiles tana amai har ta galabaita kamar ma bata numfashi a ruɗe Huwaila tayi kanta tana kiran sunanta da taga tabbas bata motsi ta fice da gudu daidai sanda maigadi ya fito tallaɓe da gefen kafadar AB a jikinsa yana dagawa dakyar don har yanzu jiri yake ji Rumaisa na biye dasu cikin tashin hankali Huwaila ta ce "Aunty Rumaisa zo ki gani kamar Aydah bata numfashi. Duk Ab yana cikin hali jin jiki hakan bai hana shi zare jikinsa daga jikin maigadi, da nufi ya je yaga halin da Aydah take ciki, yana ɗaga ƙafarsa sau ɗaya jiri ya watsar dashi "Subhanalillah! Yallaɓai ba za ka iya ba ka bari madam su daukata mu tafi asibiti duka. Maigadi ya faɗa tare da ɗaga Ab da sauri Rumaisa ta bi bayan Huwaila suka shiga ɗakin Aydah tana nan kwance magashiyam yadda Huwaila ta ganta, Rumaisa ta kara hannunta a ƙofufin hancin Aydah ta ji da gaske bata numfashi, a rikice ta ce Huwaila ta kamata su kai ta mota yadda AB yaga sun fito da Aydah kamar gawa hankalinsa yai bala'in tashi kaitsaye asibitin da suke zuwa Rumaisa ta wuce dasu sai lokacin Huwaila ta yi tunanin ta kira Siyama ta faɗa mata hali da Abba da Aydah suke ciki, ta ciro wayarta da ta sakade a zaninta ta kira Siyama. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/19, 2:50 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 075. Koda kiran Huwaila ya shigo wayar Siyama gaba ɗaya ahalin gidan suna kan dinning table suna taking breakfast, yau har da Daddy yana gida saboda haka suke yi breakfast ɗin a tare. Siyama tana gani sunan Huwaila sai da gabanta ya faɗi cikin sauri tayi picking muryar Huwaila ta karaɗe mata kunne cikin tashin hankali take magana "Siyama gamu a asibiti Abba da Aydah duka basuda lafiya, ita Aydah ma koda muka kawo ta asibiti bata motsi. "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Meyasa me su ne alokaci ɗaya za su kamu da rashin lafiya kodai food poisoning ne?" Shiru Huwaila tayi dan ita kam tana jin tsoro a ji mutuwar sarki a bakinta yoo ta isa ma ta faɗi abun da ya faru wannan sirrin Abba da Aydah ne, sai dai kuma in likita ne ya fadi musanbabbin ciwon nasu. "Hello! Huwaila ina magana kin yi shiru ki faɗamin gaskiyar abun da ya same su?" "Da dai hakuri kika yi Siyama ki zo asibitin da kanki dan tun sanda aka shiga dasu wani ɗaki har yanzu ba wanda ya ce damu komai. "Shi kenan ga mu nan zuwa. Siyama ta faɗa tare da katse kiran ta kalli su Daddy da suka yi tsuru-tsuru sunan kallonta cikin rawar murya ta kwashe abun da Huwaila ta faɗa mata ta gayamusu, Daddy ya riga su fita saboda su sun tafi neman veil shi kuma daga nan kan dinning waje ya nufa direbansa yana ganinsa hankalinsa tashe ya jawo mota, koda su Mami suka fito tuni Daddy ya daɗe da barin gida Siyama ke driving Sadiya tana zaune a front seat yayin da Mami ke zaune a gidan baya. Koda suka iso asibiti kowanne su hankalinsa ya yi bala'in tashi Daddy sai kai da kawo yake yi daga Mami har su Sadiya sun yi zugu-zugun Sadiya sai addu'a take yi a zuciyarta Allah ya tashi kafaɗar Abba ita kuma Aydah Allah yasa ta mutu. Sun fi one hour a tsaye kafin likitocin da suka duba su mace ɗaya da namiji biyu suka fito sai kuma nurses biyu da suka turo Aydah akan kujera daukar marasa lafiya suka kai ta wani ɗaki daban shi ma Ab aka kai shi nasa daga nan Daddy ya bi bayan likitocin domin jin Musababbin ciwon yaransa, Mami tana gani Daddy ya bisu ita ma ta bi bayansa a ofishin babban likitar suka shiga dukka, bayan Daddy ya zauna likita ya zare eyeglasses ɗin idonsa ya dubi Daddy da Mami dake tsaye a bayan Daddy ya furzar da numfashi kafin ya ce "A bincike da muka yi akan Abba ya nuna ya yi amfani da wani men power da yake mugun hatsari ga lafiyar namiji, kuma wani abun takaici yana amfani dashi ba a bisa ka'ida ba yana over dosage ɗinsa wanda hakan ne ya haifar masa da matsanancin zazzaɓi. "To kuma ita Aydah me ya same ta?" Mami tayi tambaya gabanta na mugun bugawa. Likitan ya kalli mace likita ɗin wacce ita ce ta duba Aydah cikin kamilalliyar muryarta ta soma magana "ita Aydah ɗin case ɗinta ba wani babba bane hakan yana faru akan wasu mata har ma da maza idan ya kasance shi ne first sexy ɗinsu za su kamu da zazzaɓi mai zafi waɗansu har ma sai sun kwanta jinya kamar dai yarda ya faru da ita Aydah ɗin. In shaa Allah da zarar ta farka za ta wartsake sai dai ta dinga zama a cikin ruwan dumi saboda ya ɗan farka ta kaɗan an mata ɗimki idan tana shiga ruwan ɗumi hakan zai sa wurin ya yi saurin healing Likita tana dasa aya Mami ta ɗauki dogon sallati taɓa tafa hannuwa "Yanzu dan Abba yana tsinannen wannan 'yar ƙaramar alhakki ce zai sha wa men power nufin sa ya kashe ta ko me? To wallahi ba zan lamunta ba Alhaji dole ka ɗauki mataki ai wannan child abuse ne. A fusace Daddy ya ɗago ya gallawa Mami harara rai ɓace yake faɗin "Child abuse a ina?" Na ga dai Aydah matarsa ce addini ya halatta masa ita kuma ban aurar da ita ba sai da ta kai muzalin balaga dan kina mahaukaciya za ki buɗe baki kina faɗar maganar banza. "To idan ma ba child abuse bane sexual violence ne kuma wallahi sai na shigar da ƙara an kwatowa 'yata hakkinta kana ji fa likita ya ce men power ya sha kuma over dosage, har fa farka ta ya yi Alhaji ka kuwa san irin azabar da ɗinki yake dashi kasan irin azabar raɗaɗin da ake ji yayin yinsa?" Mami ta ƙarashe magana tare da ɗora hannu aka ta rushewa da kuka, duk sai kuma jikin Daddy ya yi bala'in sanyi ya kasa mayar wa da Mami magana hakan da Mami ta gani ya bata karfin gwiwa cigaba da fadar maganganu ta dubi likita da hawaye akan fuskarta ta ce "likita ka faɗi tsakanin ka da Allah ka cire son zuciya Abba yana da rashin kuzari da zai sa sai ya sha maganin ƙarin ƙarfi a yayin mu'amala da iyalinsa?" Likita ya girgiza kansa cikin sanyi murya ya ce "zance na gaskiya Abba yana da cikakkiyar lafiya wanda ko mace mace huɗu zai iya sarrafawa, sannan dadin daɗawa zai iya taɓa lafiyar jikinsa. Shi kansa likitan Abba ya yi bala'in basa mamaki ace duk iliminsa da wayewarsa ya rasa abun da zai sha saboda kuzari sai wannan guba. Ai kuwa Mami ta ƙara samun kwarin gwiwa zazzaga masifa sai muggan maganganu take faɗa akan Abba, daga ƙarshe ma sai ta baro office ɗin a fusace har ta iso ɗakin da Aydah take tana sharar hawaye ta nufi gadon da Aydah take kwance da cannula manne a hannunta ana ƙara mata ruwa sai bacci take abin ta, Sadiya da Siyama suka yo kan Mami har suna haɗa baki wurin tambayarta dalilin kukanta Sadiya ta ƙagu ta ji wane mummunan abu ne ya sami Aydah da Mami take kallonta tana kuka, sai da Mami ta share hawaye kafin ta basu labari abun da ya faru wani irin mugun shock Sadiya ta ji ya kamata, zuciyata tayi baƙi ƙirim! Ji take kamar ta shaƙewa Aydah wuya har taƙarasa ta, Aydah ta gama da ita da kwanta da muradin zuciyarta shi kenan Abba Bashir yasan Aydah 'ya mace ta dandani zumar Abba Bashir , lallai ta cika cikakkiyar marar nasara a rayuwa. Shin ina asiri da suka yiwa Abba da zai tsani Aydah ana nufi bai kama sa bane ko kuma tsanarta ce kawai amman zai iya haɗa shimfiɗa da ita?" Tunda taga AB ya yi tarayya da Aydah alhali ga amaryarsa Rumaisa wacce duka kwananta biyu a gidansa hakan na nuni da cewa asiri da ta yiwa Rumaisa ya kamata, da tasani dukkansu za ta saka a sako musu zubar jini. (Kashh! Sadiya dokin inda baya sukuwa kin ri ga da kin makaro) Sadiya bata ankara ba ta ji hawayen baƙin ciki na bin kumatunta. Siyama ta yi ajiyar zuciya ta ce "Mami dan Allah ki daina fadar za ki shigar da Yayanmu ƙara da Aydah da Yayanmu duka yayanki ne. "Ke dallah rufe min bakinki ta ina ya zama ɗana ke ko kishi 'yar uwarki bakya yi meyasa ita Rumaisa bai yi using men power akanta ba sai akan Aydah?" "Uhm! Koma mene ne haƙuri za ki yi Mami. "To ba zan haƙura ba na ce ba zan haƙura ba Siyama. Mami ta faɗa tana zarewa Siyama idanu dole Siyama taja bakinta tayi gun! Daddy yana baro office ɗin likita ya wuce ɗakin da AB yake Rumaisa ce kaɗai a ɗakin shi ma Ab da drip ɗinsa a hannu yana bacci Daddy ya tambaye Rumaisa jikinsa ta ce ya ji sauki don har zazzabin jikinsa ya sauka, Daddy ya daɗe cikin ɗakin kafin ya nufo na Aydah Mami tana ganinsa ta tada masifa sai faɗar take kotu ce za ta rabata da Abba. A fusace Daddy ya kalleta ya ce idan ya sake jin kalmar sexual violence da kotu a bakinta sai ya yi mummunan saɓa mata yadda taga idanun Daddy sun yi jajir ta tabbatar da cewa da gaske yake yi dole ta ja bakinta ta tsuke amma acikin zuciyarta ta kudurta ko ana ha maza ha mata sai ta raba auren Abba da Aydah don taga cuta acikinsa ƙarara. *VICTORIA ISLAND LAGOS* (The George hotel) Aliyu na Uku yana kwance akan katafaren gadon hotel ɗin the george hotel ɗin da ya kamawa Maysun, yau kwana su uku da sauka a Lagos bai je gidansa ba dukka wayoyinsa rufe su ya yi sai amarci suke ci shi da Maysun ɗinsa wacce yake jin ta tamkar yau ne ya fara tarayya da ita, ya rasa gane irin matsanancin so sa yake mata cikin kwanaki uku nan da suka yi a tare ji wata irin natsuwa da kwanciyar hankali wanda ya manta rabon da ya ji irinsu. Duk iya kyautatawa da Safiya ke masa baya samun gamsuwar da ya samu a kwanaki uku ɗinan a tare da Maysun tabbas sai yanzu ya ƙara tabbatar da cewa alaƙa aure bata yiyuwa sai da soyayya, bai taɓa jin son Safiya a zuciyarsa ba amman yana gani girmanta da ƙimarta yana daraja ta, sai dai zuciyarsa tana ga Maysun. Yayi nisa a tunanin rayuwarsa da Maysun a garin London karar buɗe ƙofar bathroom da Maysun ta yi ya dawo masa da natsuwarsa ya kalleta cike da shaukin so tana sanye da white bathrobe ta yane kanta da farin ƙaramin towel, wani bala'in kyau yaga tayi masa ga zazzafar soyayyarta da ke ratsa sassan jikinsa, duk da yana cikin farin ciki kasancewa tare da ita amman hakan bai hana masa hasaso irin kalubalen da zai fuskanta akanta, har kawo yau ɗinan kaf zuri'arsa ba wanda yasan ya taɓa aure har da ɗa sai Anaal ita kaɗai ce tasan da wannan ɓoyayyen sirri. Yana cike da alhini ta wacce fuska zai fuskanci masauratar kudu ya gabatar da Maysun a matsayin matarsa da farko wannan Kurman allo ba kowa ne zai fahimce sa cikin sauki ba. Yasani idan ya bayyana Maysun a yanzu a matsayin matarsa zai iya rasa sarautarsa wacce a yanzu yake da burin akanta saboda ya farantawa mai babban ɗaki a dalilin fahimtar da ya yi batada da wani buri da ya wuce taga ya hau karagar mulkin sabon birnin kudu. Maysun tana zuwa ta zauna daidai fuskarsa cikin zazzaƙar muryarta da ya fi so ta ce "Abu Azhar me ke damunka ne kasan duk duniya ba abin da yake saurin ɗaga min hankali irin naganka cikin damuwa saboda haka kada ka ɓoye min komai ka tuna mu yi alkawari wa junan mu za mu dinga sharing damuwarmu?" A kasalance ya tashi zaune sai da ya jawo ta cikin jikinsa ta kwantar da kanta a faffadan ƙirjinsa jiƙaƙƙiyar sumarta ta baje masa a ƙirji, a hankali yake shafar sumarta ta, kamin cikin raunin murya ya ce "Oum Azhar ina cikin damuwa zuciyata tana cike da son bayyana ki ga dangina sai dai ina fargaba irin karɓar da za su yi miki. Na kuma tabbata bayyana ki ɗin zai iya jawo min matsaloli da dama daga cikinsu har da rasa sarauta ta, wacce mahaifiyarta ta ƙwallafa ranta akai. Ga kuma ɗan mu da ya ɓata wanda nake so na fara neman sa, sai dai na rasa ta ina zan fara neman nasa domin bana da cikakken bayani akan garin da Bashir da matarsa Maryam suke da zama anan Nigeria . Ina so na nemo su at any cost su faɗa mana ina yaronmu shin har yanzu yana raye idan yana raye yana hannunsu?" Wannan ita ce asalin damuwata Oum Azhar ki tayani da addu'a amman nasan akwai cakwakiyya a gabana ba kaɗan ba. Wata ƙarfaffiyar ajiyar zuciya Maysun ta sauke taji aikinta komai rintsi komai wahala ba za ta sake rabuwa da Aliyu ba domin shi ne cikon farin cikinta, saboda haka ta ce "Kana ji ko Abu Azhar ka cigaba da ɓoye ni har zuwa sanda za mu gano yaronmu. Na tabbata zuwa lokacin mun nemo mafita. Ba yadda Aliyu na Uku ya iya dole ya yi na'am da shawararta. *KANO* (Soft care private hospital) Abba ya riga Aydah farfadowa yana dawowa natsuwarsa ya kalli Rumaisa duk sannu da take masa gami da tambayarsa me yake ji a jikinsa bai amsa mata ba sai kawai ya ce da ita "Ina Aydah ya jikinta na ji mata rauni ko Habibty?" Cikin shock Rumaisa take kallonsa sai da ta haɗiye wasu busassu miyau kafin ta ce "Ban fahimce wannan tambayar taka ba Habibi wane irin rauni ka yi mata?" Shiru AB ya yi ya kasa bata amsa "Habibi ka yi magana ka yi shiru ko dukanta ka yi?" "Ni dai kurum ki faɗamin tana ina?" Tana ɗaki da ke kusa da naka sai dai tun zuwan mu ban je na dubata ba saboda banaso na fita na bar ka kai kaɗai. Da sauri AB ya sakko daga gado daman an cire masa drip, jikinsa sai rawa yake yi don har yanzu yana ji jiri sai dai ba sosai ba, Rumaisa ta bi shi da kallo ta ja tsaki ƙasa-ƙasa da har taso tayi zamanta sai kuma wani zuciya ya kwaɓe ta, ta tashi ta bishi a baya. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/22, 2:34 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 076. Riƙo hannunsa Rumaisa tayi da sauri da mamaki yake kallonta ya zuba mata idanunsa da suka ɗan faɗa. Yana jira dalilin da zai sa ta tsayar dashi "Habeebi kaima fa ba cikakkiyar lafiyar ne da kai ba, kuma family ɗin Aydah suna tare da ita,kaima nasan da kana da muhimmanci a wurinsu da basu tafi sun barka kai kaɗai ba sai kace wani marar gata. Rumaisa ta ƙarasa maganar rai a haɗe ta tsani mutanen da AB ke faɗar danginsa ne alhali su ba ƙaunarsa suke yi ba, hannu yasa ya zare hannunta dake cikin nasa hannun,ya nufi ƙofa kai tsaye batareda ya tsaya kula zantuka ta ba. Baki buɗe tabisa da kallo har ya fice daga room ɗin kai tsaye ɗakin da Aydah take ciki ya nufa a hankali ya tura kofar ɗakin,sai sukayi ido biyu da Mami samun kansa yayi da muguwar faduwar gaba ga wata matsananciyar kunya da ta lulluɓe shi, Sadiya na ganinsa da sauri ta nufo shi ta wani riƙo hannunsa daidai lokacin da Rumaisa ta ƙaraso cikin room ɗin ta biyo bayansa dan kasa daurewa tayi. Da wani irin sauri Sadiya ta Rungumesa wani irin natsuwa ta rika ji tana shigarta lokaci ɗaya duk da girman laifin da yayi mata na kusanta Aydah da ya yi bata ji soyayyarsa ta ragu ko kaɗan a zuciyarta ba."Yayanmu ya jikin?"Siyama ta faɗa tana kallonsa sai lokacin ya samu ya raba jikinsa da Sadiya ,still ta kasa barin gefensa murya a raunane ya gaisheda Mami, ko kallonsa daman Mami batayi ba wani irin ma tafarfasa zuciyarta ta riƙa yi Allah-Allah take Aydah ta farka a sallamesu su bar asibitin nan dan ta dauki alwashin daga nan sai gidanta Aydah ba zata koma gidan AB ba. Daman Rumaisa ko kallon gefen su Mami bata yi ba ta cigaba da tsayi a bakin ƙofar shigowa duk babu wata walwala a tare da ita. Shi ma dai AB bai ƙarasa ba ganin Mami gafda Aydah ɗin tsayuwa ya cigaba dayi a haka duk da jirin dake dibarsa. Siyama data kula da yanayinsa tace yayanmu kaje ka huta kaga tana bacci na haɗa maka tea zaka sha?"murmushi kawai ya yiwa Siyama."zaka sha din na haɗa maka? Sadiya ta faɗa tana kallonsa ɗaga mata kai kurum yayi duk daɗi ya gama cika Sadiya da sauri ta nufi wurin kayan da suka zo dasu dake cikin (basket)tsawar da Mami tayi mata ne yasa ta dakata ta haɗe rai da mamaki take kallon Mamin da ita ma ranta a ɓace yake. "Akace maki da sunan sa na hado abinci mayya mai nacin tsiya wai sai yaushe za kiyi hankali ki daina kula wannan mutumin da ya rusa miki dukkan farin cikin ki.!" Rumaisa ta riko hannun AB tana faɗin."Ka ga ga Habibi zo mu je na hada maka tea ɗin kasha daɗin abun bama da yunwar abincin baran tana ayi mana gori. "Rumaisaaa!!!! AB ya faɗa cike da kashedi a muryarsa "Mami kike yiwa rashin kunya, buɗe ido tayi cike da mamaki take faɗin."rashin kunya ita ta kama girmanta ne?" tun da muka shigo take faɗa maka baƙaƙen maganganu. "Kiyi shiru please. Ya faɗa yana daka mata tsawa ita ma cikin daga murya take faɗin."meyasa zanyi shiru, hayaniyarsu yasa Aydah ta shiga buɗe idanunta da sukayyi mata nauyi wani wawan tsaki Rumaisa tayi ta fice daga ɗakin ga baki ɗaya cike da jin haushin Abban aranta. shi ma juyawa yayi yabi bayanta. Ganin Aydah ta shiga motsi Mami ta kira sunanta tana rika hannunta a hankali Aydah ta buɗe idanunta ta sauke su cikin fuskar mami cikin rawar murya Aydah ta kira sunan mami cike da kulawa Mami ke mata sannu tana tambayarta babu inda keyi mata ciwo,girgiza kai kurum take tana bin ɗakin da kallo tana so taga ta inda zata ga yayanta Siyama ta karaso tana mata sannu daman Sadiya tunda Mami ta kunyata ta agaban AB da Rumaisa tabar dakin,da taimako Siyama Aydah ta tashi zaune Siyama ta taimaka mata ta kaita toilet tamkar zata yi ihu wurin yin fitsari,ta wanke bakinta Siyama ta haɗa mata tea mami dai tana zaune sai bin ta take da kallo kaɗan tasha tea tace ta koshi maganin da doctor ya rubuta mata wanda Daddy,ya siyo Siyama ta taimaka ta bata tasha komawa tayi ta kwanta tare da lumshe idanunta zuciyarta cike da tunanin yayanta,miƙewa tsaye Mami tayi batareda tayi magana ba ta fice daga room ɗin kai tsaye office ɗin likita ta nufa sai da akayi mata izinin shiga ta shiga,yana ganinta ya tambayeta Aydah ta farka ne ta faɗa mata ta farka,ta numfasa tana faɗin "likita zamu iya samun sallama a yanzu?" Za'a iya samu tunda dama jikinta da sauki kuma an mata ɗinki ta dai cigaba da zama a ruwan zafi a dinga saka gishiri aciki kaɗan. Ya rubuta masu takardar sallama Mami tayi masa godiya ban cin ta karɓi takardar tayi masa sallama, ɗakin da Aydah take ta koma ta kalli Siyama tace ta haɗa kaya su wuce gida an basu sallama. Shiru Aydah tayi tana kallon Mami cikin sanyin murya Aydah ta ce "Mami yayanmu fa?" A mugun hasale Mami ke kallonta kafin ta zuba mata wani uban ashar tsit Aydah tayi tamkar ruwa ya cinyeta Siyama na rike da hannunta har zuwa cikin compound inda Mami tayi parking motar ta,tunda suka shiga motar ta haɗe kanta da gwiwa bata kara magana ba har suka isa gida duk ranta a ɓace,Mami ta umarci Siyama ta haɗa mata ruwa tayi wanka ta haɗa mata wasu daban ta shiga ciki ta zauna. Tunda ya koma ɗaki ya kwanta ya rufe ido bai kara kallon Rumaisa dake ƙoƙarin haɗa masa tea babu irin maganar da bata yiwa AB ba akan ya tashi ya sha tea ba yayi mata banza. gajiya Rumaisa tayi ta aje cup tea ɗin tayi zaune duk abun duniya ya taru yayi mata yawa suna cikin wannan yanayin likita ya shigo room ɗin tare da nurse a bayansa ya kalli Rumaisa yana tambayarta mai jiki kuma ya farka.?"ta faɗa masa da sauƙi ya kuma farka Amman bai ci komai ba,jin likita yasa AB ya tashi zaune yana fuskantar likita, likita yayi masa ya jiki ya faɗa masa da sauƙi kafin ya ɗora da faɗin yana son a sallamesa,murmushi likitan yayi yana faɗin ,zasu basa sallama dan basu ma dade da sallamar matarsa ba kafin nan yana so ya gansa a office ɗinsa cike da mamaki AB ke kallon likita jin ance an sallami Aydah kuma har sun wuce,har office ɗin likita AB ya shiga Rumaisa na a bayansa likita ya dubi Rumaisa da ta samu wuri ta zauna "mene ne alaƙarki dashi?"Rumaisa ta daga kai tana kallon likita sosai taji haushin tambayar da yayi mata Da sauri AB ya kalli likita yana faɗin."matata ce likita. Likita ya mayar da hankalinsa kan AB. "kana da rai da lafiya meya kaika amfani da men power da ya kusa yi maka illah?" Wani irin faɗuwa gaban Rumaisa yayi ko kaɗan bata taɓa kawo irin tambayar da likita zai yiwa AB kenan ba da bata yadda ta biyosu ba,da mamaki AB ke kallon likita yana girgiza kai yake faɗin "ban taɓa amfani da irin waya'annan drugs din ba na kara karfi likita kadai kara dubawa. murmushi likita yayi ya kalli bangaren da Rumaisa take sai famar danna wayar hannunta take amman kar kuso ku shiga zuciyarta tashin hankali ne sosai acikinta ga wani irin gumi da take haɗawa duk sanyin dake cikin office ɗin zufa take haɗawa, yadda ta mayar da hankali kan wayar sai mutum ya rantse bata cikin office ɗin ake magana, karshe sai ta mike tsaye ta nufi hanyar barin office ɗin batareda ta yiwa kowa magana ba murya AB taji akanta ya kira sunanta cikin wani irin sauti tsayawa tayi batareda ta juya ba "kenan abun da likita ya faɗa gaskiya ne?"wani bangare na zuciyarsa na tambayarsa ban zuba sa da hannuna na sha ba likita sai idan matata ta zuba min cikin abun sha. A wani irin rikice Rumaisa ta juyo ta dawo gaban AB daɗin abun bani kaɗai bace matarka ina tunanin matar taka guda ita ce wacce ta zuba maka ba dai ni ba. Kallonta kurum yake yana mamakin karfin halinta likita ya juya yana yiwa AB bayanin ilollin dake cikin shan irin wannan maganin."kafin ma nayi maka bayani sai da na yiwa mahaifinka da mahaifiyarka bayanin haka a rude AB ke kallon likita cikin rawar murya yake faɗin "bayanin me kayi masu likita? "wanda nayi maka yanzu dan ɗayar matarka ta auna arziki duk da har da ɗimki akayi mata gaskiya tana da dauriya sosai tamkar ba mai ƙarancin shekaru ba. AB ya murza goshinsa yana jin yadda iskar wurin keyi masa kaɗan jijiyoyin kansa suka fito sarari alamar ransa yayi bala'in ɓacin taya zai kara kallon Daddy da wannan abun kunyar?"Rumaisa ta kashesa ta cucesa,duk sauran bayanin da likita yayi masa kafin ya rubuta masa takardar sallama baya ma fahimtarsa Wannan karon Rumaisa taja motar tunda ya shiga motar ya zauna bai ce komai ba har suka isa gida Huwaila tayi masu sannu da zuwa kai tsaye ɗakinsa ya wuce bai kara kallon bangaren da Rumaisa take ba ita ma tabe baki tayi ta nufi nata dakin,aranta take faɗin sai kace wani mugun abu tayi zai bi ya daga hankalinsa ko kaɗan bata yi nadamar abunda tayi ba.wanka yayi tare da sallar azzahar kusan karfe 3 yana zaune a parlor Rumaisa ta shigo cikin gayu ta cokare dauri gaban goshi sai uban ƙamshi ke fita ajikinta ta shigo da madaidaicin tray a hannunta har ta aje ta koma ta dauko sauran kayan AB bai kalli gefen da take ba,har ta gama sarving dinsu ya ja abinci ya fara ci ita daman tana cin abinci tana danna wayar hannunta batareda ta kara kula kan yanayinsa ba saboda Rumaisa irin matan nan ne da ko miji yana fushi dasu basa damun kansu barantana su kwantar da kai su gano kuskurensu su bada hakuri sai da ya kammala cin abincinsa a natse AB ya mayar da hankalinsa kanta ya kira sunanta ta daga kai tana kallonsa "ki aje wayar hannunki zamu yi magana,bana son ina magana ana danna min waya. Ya faɗa da rashin walwala a fuskarsa Aje wayar tayi tana kallonsa."waya faɗa maki ba zan iya dauke bukatar ki a gadon auren mu ba har sai kin ha'incin ni kin zubamin magani acikin abun sha?"meyasa baki jira kika ga iyawata ba ko zan iya ko ba zan iya ba? Dan Allah dan Annabi Habeebi ka daina damun kanka akan wannan abun nifa ban ga illar dake cikinsa ba kawai dai yana karawa maza karfi ne ba wani abu na daban ba meya ma laifina dan na taimake ka? "taimako?taimako da kike magana ya kaini gadon asibiti Rumaisa. Ya faɗa sounding so very harsh a muryarsa,kin farasa na kasa yadda dake akan mu'amalar mu kin riga kin saka rashin yadda a tsakanin mu daga yau duk abun sha da ya fito daga hannunki inhar ba'a gama kika haɗasa a zan sha ba,ya rage naki ki gyara ko karki gyara. Yana gama faɗar haka ya bar mata falon ya shige ɗakinsa wannan karon harda saka key ko kaɗan baya son damuwa ba karamin bata masa rai Rumaisa tayi ba,ga tunanin Aydah dake manne a zuciyarsa idan har yana da kunya ai ba zai iya haɗa ido da Mami ba, addu'a ya shigayi aransa Allah yasa zuwa dare Aydah ta dawo Yanayin da suka kasance tare da kanwar tasa ya kasa bacewa daga zuciyarsa har zuwa dare Aydah bata wata walwala a gidan gabaki ɗaya hankalinta na kan yayanta kuma bata ga fuskar tambayar Mami,yaushe zata wuce gidanta ba.duk a takure take jinta koda Daddy ya dawo da dare yaga Aydah ya mata ya jiki har washe gari AB yayi shirin fita office yayi dilaliing lambar Siyama lokacin ma Siyama tana bacci cikin bacci ta daga wayar tana jin shine tayi saurin tashi zaune tana murza ido take gaishesa ya amsa yana tambayarta ya jikin Aydah ta tashi jiya ta samu barci kuwa?"yana jin sautin murmushi Siyama ta ciki wayar "ta samu sauki yayanmu ni ina dakina ban sani ba ko ta tashi dan tana dakin Mami,batare muka kwana ba. numfashi AB ya sauke yana faɗin idan ta tashi ta kirasa da haka ya sauke wayar har aran Siyama taji daɗin wannan al'amarin da ya faru tsakanin Aydah da Yayan nasu sai Mami ta haƙura ta sakawa ranta dangana ta karbi kaddarar su har AB ya gama break fast ɗin da Huwaila ta shirya masu cikin dinning area gimbiya Rumaisa tana can ɗakinta tana bacci kafin ya sauko kasa sai da ya fara leƙa dakin Rumaisa ya tarar tana bacci yana gama break fast yayi sallama ,da Huwaila har take tambayarsa yaushe Aydah zata dawo. Ya faɗa mata sai ta samu sauƙi da haka ya fice office gimbiya Rumaisa ana can an hangame baki ana bacci batare da tasan fitar mijin nata ba. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #AYDAH #AB #RUMAISA #KURMAN ALLO Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/22, 2:38 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 077. Da wani irin bakin ciki ta riƙa bin zanin gadonta da kallo yadda jini ya batasa ita ga baki ɗaya jinin nan tsoro yake bata bai taɓa yimata rushing yadda yake yimata yanzu ba. Ita kanta kyamar kanta take ji cire zanin gadon tayi duka ta wuce dashi toilet ta sakasa cikin washing machine ta cire kayan jikinta na bacci da suma sun gama lalacewa duka ta saka aciki washing machine. Ruwan zafi ta haɗa tayi wanka zuciyarta duk a cakude zata kira Aunty Raliya taji idan akwai mafita,ga wata irin muguwar sha'awar mijinta dake damunta a dalili kayan mata da ta dinga dirkawa cikinta. wankan tayi ta fito ta shiga shirya kanta bacin ta gama ta saka riga da wando na English wears ajikinta ta dauko sabon zanin gado ta shimfida toilet ta koma ta wanke zanin gadon da kayan baccinta. A bayan gidan taje ta shanya,ta dawo ta shiga wankin toilet da taji yayi mata wani iri ko kaɗan bata son wanke toilet zata rika sa Huwaila tana wankewa tunda yar aiki ce,sai ta riƙa wanke na AB da kanta dan ita a tsarinta yadda take da kishi bata son yar aiki ko parlor maigidanta ta taka,share ɗakinta tayi tas ta kunna turaren wuta,ficewa tayi ta nufi part ɗin AB yunwa take ji sosai babu kowa a parlor kai tsaye master bedroom ɗinsa ta nufa nan din ma babu kowa. kai tsaye ta karasa kofar toilet tayi knocking tana kiran sunan AB jin shiru yasa ta tura kofar toilet ɗin da mamaki babu AB babu alamarsa tambayar kanta take ina yaje?"Tasan dai ba office ya tafi ba dan suna cikin hutun cin amarci. gyara gadonsa tayi ta fice kai tsaye kasa ta sauka tana kwallawa Huwaila kira da tayi nisa tana karanta littafin da suka saka a YouTube channel mai suna (zamanin mu A yau)tana saurara wanda Aydah keyi mata downloading ɗinsu a wayarta,sai ta tura mata duka jin shiru yasa Rumaisa ta nufi daktin da take tunanin na Huwaila ne ga mamakinta wayace kare a kunnenta ta bada dukkan hankalinta kacokam tana sauraren (mai sanyi) tana bala'in son karanta duk wani littafin da mai sanyi ya wallafa a channel ɗinsa dake YouTube mai suna(limamin tsakar gida)duk wani littafi da zai karanta acan bata danasanin karanta sa saboda yadda yake karanta sa daki-daki yana fitar da kowace kalma yadda ta dace. A fusace Rumaisa ta daki kofar,a wani irin rude Huwaila ta daga kai tana kallon kofar ganin Rumaice ta mike tsaye da sauri ta kashe wayar cikin rawar jiki ta gaisheda Rumaisa. "Saboda wulakanci tun a falo nake kiran ki shine zaki shareni ?" A tsorace Huwaila ke faɗin."dan Allah Aunty kiyi hakuri wallahi ban ji bane. wata uwar harara Rumaisar ta sakar mata tana yatsine fuska take faɗin."habeebi ya fita ne? "eh! ya fita office tun ɗazun. Ɗan jim Rumaisa tayi kamin kuma ta sake cewa "yayi break fast" "ehhhh yayi. Da haka Rumaisa ta juya tabar ɗakin da ido kurum Huwaila ta bita "Mtss! Mazaunanta har wani rawa suke tsabar yadda sukayi mata yawa wai kuma a haka Abba Bashir ke sonta ita har ga Allah bataga abun so a wurin Rumaisa ba waya sani ma ko tana haɗawa da maganin kara girman halitta kamar yadda wasu mata keyi. Kamar dai irin Maryama ta cikin labarin (zamanin mu a yau)tabe baki Huwaila tayi ta koma tayi kwanciyarta ta cigaba da sauraren littafinta. Anan cikin dinning area Rumaisa ta zauna tayi break fast, addu'a take aranta Allah yasa Aydah karta dawo. Tana gamawa ta koma ɗakinta waya ta dauka ta fara kiran Aunty Raliya tana dauka ta gaisheta ,ta amsa tana tambayarta ya gidan anan kuma suka shiga tattaunawa akan matsalarta har take bata labarin AB ya gano ta saka masa men power a abun sha sanadin haka sai da ya kwanta gadon asibiti."Ni bama wannan ne ya dameni ba Aunty Raliya jini nan yaki tsayawa,wane drugs ya kamata na sha dan ya tsaya ina bukatar mijina ina matukar bukatarsa kin san saboda wannan jinin yasa yaje wurin Aydah."zan tura maki magani sai kije pharmacy ki siya maybe zuwa dare ya tsaya. wani dadi ne ya lullube Rumaisa da haka suka yi sallama tana aje kiran Rumaisa ta shiga kiran AB sai da ta katse ya kirata "ina kwana Habeebi ya jikin? "kin tashi Lafia?" AB ya faɗa "lafiya lau koda na tashi bacci Huwaila ta cemin ka tafi office,nayi mamaki gaskiya na zata ko ka dauki hutu a wurin aiki. ta karasa maganar da rashin jin dadi a muryarta "kin tuna bashine aurena na farko ba a aurena na farko sun bani banda yanzu. Idan tace maganarsa bata bata mata rai ba tayi karya, "shikenan Allah ya taimaka me za kaci da rana? "Amin duk abunda ya samu. "owk tam I love you. sai da ya furzar da iska mai zafi kafin yace " i love You to." Da haka suka yi sallama Parlor sa da dakinsa taje ta share ta wanke toilet ta saka turaren wuta cikin shirin fita ta fito ta samu Huwaila tsaye a kitchen tana kokarin ɗora girkin rana ta tambayeta me zata yi ta faɗa mata rice and stew, tayi farfesu kayan ciki zan je yanzu na dawo. Huwaila ta mata fatan sauka lafiya ,daman tun washe gari aka kawo mata motarta kai tsaye pharmacy ta nufa ta karbo magani bata jima ba ta dawo tun kafin ta zauna tasha maganin tana ta addu'ar Allah yasa ya tsaya kafin dare. Yana zaune a office kiran Daddy,ya shigo a wayarsa tun jiya ya kasa daga kiran Daddy,wata irin mahaukaciyar kunyar Daddy yake ji Rumaisah ta cucesa, dakyar ya daga yayi sallama, Daddy ya amsa ya gaisheda Daddy cikin girmamawa Daddy ya ce dashi "ya jikinka? "Na ji samu sauqi Daddy. "Allah ya kara sauqi ya tsare gaba. dakyar ya amsa da Ameen, ɗan shiru ne ya biyo baya kafin Daddy yace yaushe za ka zo ka dauki matarka?"ɗan jim AB yayi yana jin shakkar haɗuwa da Mami har ga Allah. "Daman Daddy nufi na tayi kwana biyu a gida kamin ta samu sauqiInsha Allahu zuwa dare zan shigo na dubata. "Allah ya kaimu. Daddy ya faɗa "Ameen! AB yace yana sauke wayar,dafe kansa yayi duka da hannu biyu ba zai fasa faɗin Rumaisa ta cucesa ba wuraren karfe 3 ya koma gida Rumaisah an ci wanka cikin wani less riga da skirt da ya zauna sosai a jikinta tayi kyau sosai sai fitinannen ƙamshi ke tashi ajikinta da sauri ta rungume AB tana manna masa kiss a gefen checks ɗinsa "Sannu da zuwa Habeebi wanka zaka yi ko abinci zaka fara ci?"ta faɗa tana kallon fuskarsa. "mu fara cin abinci. ya faɗa yana sakinta har daki ta bisa ta tayasa rage kayan jikinsa. Jallabiya ya saka ajikinsa tana manne dashi suka sauka kasa zuwa cikin dinning area wannan karon akan cinyarsa ta zauna a haka suka ci abincin suka gama,suka kara komawa sama ruwan zafi ta haɗa masa ya shiga wanka koda ya fito wankan ita ta tayasa ya shirya cikin riga da wando tree quarter na shan iska. Parlor suka koma kwanciya yayi akan doguwar soofa a haka tabisa Ta kwanta ajikinsa,daga nan kuma ta rika yi masa wasanni da wata irin shakakkiyar murya yake tambayarta tayi wanka ne?"juya ido tayi tana wasa da kasumbarsa take faɗin."zuwa dare dai ɗan jim yayi bayason wasar ma tayi nisa ya hargitse tunda babu tsarki a tare da ita bai san meyasa duk yadda zai yi romance da Rumaisa baya samun gamsuwa kamar yadda yake samu a wurin Aydah ya tuna haɗuwarsu na farko yadda ya rikice akan jikinta samun kansa yayi da sakin murmushi "Habeebi wannan murmushi fa. "Na tuna baby Aydah ne. Da sauri tabar jikinsa wani baƙin ciki yana saukar mata a zuciya. "Muna tare shi ne kake tunanin wata Habeebi ?"ta faɗa da mugun kishi a muryarta,da mamaki yake faɗin."ita din ba matata bace? Rai a ɓace Rumaisa tabar jikinsa komawa tayi gefe,ya dauki remote yana canja channel shi ma bai kara magana ba sai bayan sallar la'asar ya shirya cikin shadda kalar light blue yayi kyau sosai sai ƙamshi yake fita ajikinsa. Ya leƙa dakin Rumaisah kwance ya tarar da ita da waya a hannunta alamar chat take yo."Ni zan fita. Da mamaki ta tashi zaune tana faɗin."zuwa ina?" "Gari zan shiga. Da sauri Rumaisah ta sauko kan bed tana kokarin neman mayafi tana faɗin."sai mu shiga garin tare daman duk kewa ta dameni. "kwanan ki nawa da zuwa gidan nan?"kawai kiyi zaman ki ba daɗewa zan yi ba zuwa bayan ishaai zan dawo. Lokaci ɗaya yanayin Rumaisah ya canja ta haɗe rai sosai "na tafi. Da haka ya juya ya rufo mata kofar baƙin ciki kamar zai kasheta yanzu haka wurin wannan mayyar zai je daga shi har ita za tayi maganinsu bada jimawa ba. kan sallaya Mami ta samu Aydah da alamar gama sallar ta kenan ta dubi abincin da aka kawo mata ganin bata taɓa komai ba,da mamaki Mami ke faɗin. "abinci baki ci ba kenan?" idanunta sunyi wani irin zuru-zuru ta turo baki tana faɗin ita ta koshi,Mami tayi kwafa tana faɗin "cikin ki kika yiwa maganar komawa gidan wancan dan iskan yaron ma ki ciresa cikin tunaninki dan ba komawa za kiyi ba. Da haka Mami ta dauki abunda zata dauka ta fice daga ɗakin ranta duk a ɓace,wannan shegen yaron duk yabi ya cinye mata kurwar ya'yanta mami bata jima da fita ba Siyama ta shigo da waya a hannunta ta tarar da Aydah na kuka ta ware ido tana faɗin."me kuma ya faru wani abu ke maki ciwo ne? Ita dai Aydah batace komai ba sai famar sharar hawaye take "karbi waya yayanmu nason magana dake. Da sauri Aydah ta amshi wayar."Baby ya karfin jiki? cikin rawar murya Aydah ke faɗin "yaushe za ka zo mu tafi gida yayanmu?" "kin ji sauki kenan? "uhmmm! "Did you miss me baby?" ɓoye fuskarta tayi da tafin hannunta tamkar yana ganinta "zuwa anjima zan shigo na dubaki me zaki bani. "komai ma yayanmu!" ta faɗa cikin shagwabarta da yakeso tana jin sautin murmushinsa ta cikin wayar kafin ya ɗora da faɗin. "kinyi alkawari?" "nayi tau. " Allah ya kaimu, Ta amsa masa da Ameen sun dade suna magana kafin yayi mata sallama,haka yace taci abinci dan ta faɗa masa bata ci abinci ba wayar da suka yi da yayan nata ya ɗan samar mata da natsuwa haka ta sauka kasa Ta zuba abinci ta dawo cikin parlor tana ci a hankali Mami dai ko kallonta batayi ba,tana cikin cin abinci Jamal ya shigo cikin parlor ta daga kai tana kallonsa tun da tayi aure bata gansa ba tun da ba wai anan yake karatu ba Ko yanzun ma hutu yazo da ido yabi Aydah yana jin wani abu na taɓa masa zuciya,ta kara cikowa tayi wani irin fresh na ban mamaki duk kishi ya gama cika Jamal waya sani ma ko AB yana taɓa jikin Aydah irin wannan cikar da yaga tayi a kwanan nan,da sauri wata zuciya ta kwabesa da faɗin."ai shima yasan ba zai fara wannan gangancin ba Aydah tashi ce shi kadai babu wani namijin da ya isa ya mallaketa bayan shi. Ya zauna cikin parlor da murmushi a fuskarsa ya gaisheda Mami,ita ma Mamin da fara'a sosai ta amsa masa ya mayar da kansa gefen Aydah ya zuba mata ido ganin halin ko ina kula da take nuna masa. "Kinfi karfin ki gaisheda mutane ko Aydah?"dan tura baki tayi tana faɗin "kai matsalata da kai yaya Jamal shegen son girma wallahi."ina wuni."ta faɗa tana tura masa ɗan mitsitsin bakinta,bakin kawai yake bi da kallo yana jin wani irin yanayi a tare dashi,ya juya kan Mami yana faɗin "Mami har yanzu bai saketa ba." "Zai ma saketa ne Jamal yanzu baga shi tana gida ba takardar ta kawai nake jira. ɗan sanyi Jamal yaji aransa lokaci ɗaya Aydah ta haɗe rai jin maganar da Mami keyi ta mike tsaye tana faɗin "Ni ina son mijina wallahi.!"tayi hanyar kitchen fuuuiuu daga Mami har Jamal din bin ta suke da kallon mamaki wani irin zafi-zafi kirjin Jamal ya riƙa yi,kiran waya ne ya shigo a wayar Mami dole Mami tabar parlor yana ganin haka ya nufi kitchen din a mugun fusace tana tsaye jikin sink tana wanke plate ɗin da taci abinci taji an wani irin fisgota an mannata da bango buɗe baki tayi da mamaki tana kallon yadda Jamal ya riƙeta a jikinsa duk yadda taso kwantar kanta kasawa tayi babu inda jikinta baya rawa "Yaya Jamal!!" Yaji an kira sunansa da karfi. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #JAMAL #AYDAH #RUMAISA #AB #KURMAN ALLO Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/23, 1:36 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 078. Juyawa yayi yana kallon saitin da sunansa ke fitowa Siyama ce ta karaso kitchen ɗin Aydah naganin haka ta fisge hannunta dake cikin na Jamal din ta nufi Siyama da sauri ta shige jikinta,siyama tana jin yadda kirjin Aydah ke wani irin dokawa.duk a firgice take, Siyama ta mayar da kallonta wurin Jamal da wani irin expression kwance cikin fuskarsa wanda baka bambance ɓacin rai ne ko kuma mamaki da jin haushi lokaci ɗaya suka taru suka yi masa yawa."Yaya Jamal kana cikin right mind ɗinka kuwa?"matar aure kake ƙoƙarin runguma ko ka manta Aydah tana da aure akanta?" "Siyama! Ya kira sunanta cikin ihu,ya tsani kalmar da za'a danganta Aydah da aure, Siyama ta kara ware idonta akansa tana ganin yadda jikinsa ke wani irin rawa. "ƙarya nayi ko bA matar wani ce ba?" Ganin ya nufosu gadan-gadan daga ita har Aydah suka daga kafa suka fice daga kitchen ɗin kamar kiftawar ido. Shi ma Jamal cikin zafin zuciya yabar gidan batarda yayiwa Mami sallama. Sai da Mami,ta fito ganin babu Jamal ɗin ta tambayi Siyama ya tafi ne?" "Daman ya shigo ne?" cewar Siyama dan ko a fuska Siyama bata nunawa Mami tasan da zuwan Jamal ɗin ba,har bayan magrib Aydah na kwance a ɗakin Siyama,tunanin yayanta kawai take ta kasa kunne taji karar motarsa sai dai shiru kusan ishaai taji karar horn Da gudu ta nufi wurin window ta yaye labule a maimakon taga motar wanda take dakon jira sai taga motar Daddy ce ta shigo cikin compound ɗin gidan a hankali ta saki labulen tana jin zuciyarta wani iri, wasa-wasa har aka yi ishaai babu alamar yayan nata zai6zo duk ta zama wani iri,sai da Siyama ta shigo bayan idar da sallah ta faɗa mata Daddy yace ta fito taci abinci tamkar bata so haka tabi bayan siyama, ta gaisheda Daddy,tayi masa sannu da dawowa cikin kulawa ya amsa yana tambayarta ƙarfin jikinta tace masa ta samu sauƙi Siyama ta ɗauki plate ta shiga zubawa Aydah tuwon semovita da miyar eguisi da aka yi da naman kai,kwabe fuska tayi tamkar zata yi kuka tana faɗin "Ni yayi min yawa yaya Siyam salon ki saka mami tace ba zan bar mata ragi ba. Siyama ta daukesa ta zuba mata wani wanda bai kai yawansa ba Sadiya,dai da Mami sai bins u take da kallo sallama suka ji ta zazzaƙar muryarsa a bayansu Ƙamshin turarensa ya fara ziyarta hancinsu tun kafin ya iso cikin dinning area ɗin. Da kasaitatccen takunsa na jan hankali mai cike da izza da taƙama ya iso wurin,ya sunkuyar da kansa yana gaisheda Daddy,batareda ya iya haɗa ido da Daddyn ɗin ba. Daddy ya amsa yana tambayarsa karfin jiki ya amsa masa da sauƙi, mami dai sai cin abinci ta take Sadiya,da Siyama suka gaishesa ya amsa ya gaisheda Mami ko inda yake bata kalla ba Aydah sai bin sa take da kallo tana murmusawa ganin yadda yaki yadda ya kalli inda take "Yayanmu zauna nayi sarving ɗinka. Sadiya ta faɗa da kulawa a muryarta duk yadda Mami ke aika mata harara ta bangaren ta bata ma san tana yi ba, Sadiya tayi sarving ɗinsa,kusan tare suka ci abinci banda bugawa babu abunda zuciyar Aydah keyi ganin shisshigewa da Sadiya ke yiwa yayan nasu har yaso ya wuce ka'ida. Daddy yana gamawa ya miƙe tsaye shima Abba yai sauri miƙewa batareda ya haɗa ido da Daddy ba yace zai wuce gida. Dan jim Daddy yayi ya kalli gefen da Aydah take sai ya mayar da hankalinsa wurin Abba. "Ko zaka tafi da Aydah ne? Ga mamakin Aydah sai taji yayan nata na fadin."A'ah! Daddy abarta ta dai kara jin sauki da nan da can duk ɗaya ne. A boye Mami ta sauke ajiyar zuciya ta kara tamke fuska, ahankali Daddy ya kira sunan Aydah ta tashi tazo gabansa "je ki raka yayanki Mamana. Daga masa kai kurum tayi da sauri tabi bayan AB har tana cin tuntube kar Mami,ta hanata ganin yayanta a mota ta samesa da bottle wata a hannunsa yana wanke baki bata yi magana ba ta karbi ragowar ta wanke bakinta da fuskarta."Yayanmu Ni dai zan bika naji sauki wallahi.! Ta faɗa tamkar zatayi kuka murmushi kurum yayi ya bude bangaren driver ya shiga ya zauna ta wani riƙe kofar tana buga kafafunta cikin tabara take faɗin."naji fa sauki. Lokaci ɗaya taji ya fisgota dukanta sai gata acikin jikinsa,ware ido tayi tana kallonsa hannunsa yasa akaran hancinta kafin ya gangaro daidai kan ɗan mitsitsin bakinta Yana jin yadda numfashinsa ke fisga jinta ajikinsa,ta langwabe kai tana kallon cikin fararen idanunsa cikin narkakkiyar murya ta ce "Please yayanmu mu tafi. ƙara gyara mata zama yayi acikin jikinsa in a lower tune yake faɗin."idan muka tafi gidan me zaki bani baby?" "komai ma!" Ya juya ido irin da gaske ɗin nan girarta duka biyu ta dage masa,ba ƙaramin kyau tayi masa a haka ba, hannunsa yasa ya kara matseta cikin jikinsa har cikinsa na gogar nata cikin, ya haɗe fuskarsa yayi da ta,ta yana sakar mata zazzafan numfashinsa da sauri ta runtse idonta tana kara riƙe masa wuya. A hankali ya lalubi bakinta cikin bin umarnin zuciya da gangar jiki ya shiga yi mata wani irin deep kisses ga mamakinsa Aydah tayasa ta shiga yi wanda ya kusan zaucewa nan da nan notikkan kansa suka fara kwancewa a hankali da wani irin sauri ya kwantar da seat ta tafi baya ya mirgino da ita ta koma kasa ya koma samanta sai dai bai sakar mata nauyinsa duka ba still idanunta a lumshe suke sai numfashinta dake fita da sauri da sauri,hannu yasa kan zip ɗin rigarta yana kokarin ja da sauri ta buɗe ido ta riƙe masa hannu tamkar zata yi kuka ita bata son ana tabasu har yanzu basu dawo daidai ba zafi suke mata, murya a shake tamkar ba yayanta ba yake faɗin. "gaisawa zamu yi baby.! "zafi suke min yayanmu. "zasu daina idan muka gaisa. Ya faɗa da muryar da ba za'a iya fassara wane irin yanayi yake ciki ba a daidai wannan lokacin. maƙe kafada tayi alamar taki. "Naje wurin Rumaisah kenan?" Nan take yanayinta ya canja bata san lokacin da ta ɗora hannunsa a gaban rigar ba wani irin miskilin murmushin ya saki da sauri ta runtse ido jin hannunsa a wurin cikin zaucewa da fita hayyaci ya kafa bakinsa,duk kokarinsa da son rike kansa kasawa yayi yana kokarin daga kafafunta ta riƙesa a tsorace ta fashe masa da kuka bata manta azabar da tasha ba a wancan daren lokaci ɗaya kuma yaji ana knocking glass ɗin motar daman tinted ne,daga Aydah yayi da sauri ta tsallaka back seat tana gyara zaman rigarta duk ta rikice a hankali ya tada seat ɗin ya haɗe kansa da sitiyari yana ƙoƙarin daidaita numfashinsa still jin yayi an cigaba da knocking kofar motar,a hankali ya sauke glass ɗin da mamaki yake kallon Sadiya duk a daburce take cikin rawar murya take faɗin "Daman Mami tace nazo na kira Aydah. Tana maganar tana kokarin leƙa motar ko magana bayan sonyi saboda halin da yake ciki a gefe ɗaya kuma yana mamakin halin Sadiya,lokaci ɗaya Aydah ta buɗe backseat ta fito tun daga sama har kasa Sadiya ke bin ta da kallo ganinta duk a hargitse tasan akwai abunda ya faru cikin motar wani irin mummunan bugawa zuciyar Sadiya ta shiga yi yaushe Aydah ta zama haka?"tana mata kallon marar wayau wacce bata san komai ba akan harkar aure ashe ba haka bane. Aydah ta juya ta nufi entrance ɗin shiga gidan da sanyi jiki Sadiya tabi bayanta daidai tsakiyar parlor Sadiya ta finciko Aydah da mamaki Aydah ke kallonta Sadiya tana huci take faɗin. "mekike yi keda Yayanmu acikin mota ji gaban rigarki. "Kamar ya me nake yi yaya Sadiya?"me kika san macce nayi da mijinta ai ina ganin hakan ba haramun bane. hannu Sadiya tasa da nufin ta zabgawa Aydah shegen mari taji an riƙe hannunta a fusace ta juya tana kallon Siyama da mugun mamaki gamida jin haushinta "don me zaki riƙe min hannu dallah sakar min hannu na koyawa yarinyar nan hankali. "Akan me zan sake ki ai gaskiya ta gayamiki mijinta fa ne yaya Sadiya ba iskanci tayi ba don haka ki bar yarinya ta sakata ta wala ki daina takura ta dan Allah. kukan kura Sadiya tayi ta cakumi wuyan Siyama ta shaketa cikin daka tsawa Mami ta kira sunan Sadiya da sauri Sadiya ta saki Siyama wata shewa Siyama,tayi tana faɗin "wallahi-tallahi kinyi kaɗan yaya Sadiya da da yanzu ba ɗaya bane ke kin isa ki sakamin hannu. "kibarmin cikin parlor Siyama kafin nayi mummunan saɓa miki Mami ta faɗa cikin zafin rai A zuciya Siyama ta nufi stairs Aydah tabi bayanta anan cikin parlor Sadiya ta zube ta rushe da kukan baƙin ciki cikin shesshekar kuka take faɗin "Mami kin san minti na nawa nayi tsaye a wurin motarsa yaki budewa saboda ya nuna min shi ɗan iska ne na karshe Mami baki ga yanayin Aydah ba haike mata fa yaso yayi cikin motar saboda bai san kunya ba. Ban taɓa ganin jarababben namiji ba irin yaya Abba,yasa yar cikinsa agaba yana murkusa,duk yabi ya lalata Aydah wallahi Mami zuciyata tana gafda bugawa idan baki dauki mataki ba nagaji da jira ko wane irin hukuncin na yanke karki tuhumeni. Sadiya ta ƙarashe maganar cikin fita hayyaci tana barin parlor da kallon takaici kurum Mami tabi ta kanta ya dauki zafi sosai ta rasa ma wane irin mataki ya kamata ta dauka akan Abba Bashir ba zata yadda ba aci gaba da tafiya a haka Abba Bashir yana kokarin tarwatsa mata kan yara duk kuma saboda shi kaɗai. Tun bayan magarib da Rumaisa tayi wanka taga jinin ya tsaya saboda maganin da tayi amfani dashi murna ta kamata ana sallar Ishai tayi wanka tsarki duk ta rikice ta matsu AB yazo ta fesa masa wannan albishir wani haɗi na musamman da ake kira da sharp-sharp ta dauko ta shanye, ta haɗa da matsi so take AB yasan akwai bambancin tsakani ɗan duma da kabewa har kusan ƙarfe tara bai dawo ba tana ta zama a parlorn ƙasa tana jiran dawowarsa ta haɗe cikin wata riga bacci da ana hango komai na jikinta, tana jin lokacin da motarsa ta shigo bayan wasu mintuna ya buɗe kofar dakin, ko kaɗan bata lura da yanayin da ya shigo dashi ba taje ta faɗa jikinsa ta kankamesa gan-gan can cikin wuyansa take sauke masa Ƙananun kiss masu rikitarwa daman a yunwace ya shigo Aydah duk tagama hargitsa sa haka ya rika taya Rumaisa Jin tsayuwar na neman gagararsu yasa ya dauketa cak!ya nufi stairs Huwaila na fitowa daga ɗakinta tayi mugun gani da sauri ta koma zuciyarta na harbawa,aranta tana ta tsinewa Rumaisa wannan matar anyi jarababbiya daga dawowarsa babu ko cin abinci barantana wanka ta farmasa da fitina har master bedroom ɗinsa ya karasa da ita idonsa a birkice yana rage kayan jikinsa yake faɗin. "kin samu tsarki ne?" Da sauri ta daga masa kai cikin zakuwa ajiyar zuciya ya sauke,sai da al'amari yayi nisa sai kuma ya tsaya cak!" A rude Rumaisa ke tambayar "menene?" A hankali ya kunna fitilar dake gefen gadonsa haske ya bayyana ganin jini a tafin hannunsa yayi mugun daga hankalinta a rude takai hannunta kasanta gabanta yayi mummunan bugawa. Tasan ya dauke meyesa zai dawo,da sauri ya sauka daga kan bed ɗin yana tafiya yana haɗa hanya haka ya shige toilet yana bugo kofar cike da mugun jin haushin Rumaisa. Ruwan sanyi sosai ya rika sakarwa kansa ga wani irin kartawa da mararsa keyi yafi minti talatin a toilet kafin ya fito babu Rumaisa a ɗakin boxer kawai ya saka a jikinsa ya kwanta a hankali ya lumshe ido yana mayar da numfashi. Washe gari wuraren karfe takwas Aydah ta kalli gefen Siyama still bacci take ta nufi handbag ɗinta da sauri ta zuge zip ta ciro dari biyar aciki ta mayar ta dauki hijab ɗin da tayi sallah wanda na Siyama ne ta saka da sauri ta sauka downstairs tana jin mai aiki a kitchen da sauri ta nufi kofar barin parlor banda faduwa babu abunda gabanta keyi. Haka kawai tayi ta zama a gida Mami,ta kashe mata aure gara ta koma kawai da kanta bai sai yayanta ya zo daukar ta ba. Ta gaisheda Balmo maigadi ya amsa yana dai ta kallonta da mamaki ganin ina zata haka da sanyin safiya yadai buɗe mata ƙaramar kofa sai da tayi nisa ta samu abun hawa dakyar ta shiga tare da faɗa masa inda zai ka ita kai tsaye yace dari biyar tace su tafi sai da taga sun bar unguwar ta sauke ajiyar zuciya. Kusan karfe goma Siyama ta tashi bacci har tayi wanka bata ji motsin Aydah ba haka yasa ta fita daga daykin kai tsaye ɗakin Mami ta nufa tsayawa tayi cak!"cikin firgici da tashin hankali take jin muryar Sadiya tana faɗin "wallahi-tallahi nagaji Mami,sati nawa kenan da saka masa laya a kasan gadonsa dan kawai ya tsane Aydah ya saketa Amman har yanzu babu wani cigaba maimakon ma ya tsaneta sai kara sonta yake waya sani ma ko malamin kudinki kawai yaci ni idan ba zaki iya ba ina da malamina zan saka ya yi min aiki da Yayanmu zai saki Aydah. "Sadiya yaushe kika fara bin malammai?" Mami ta faɗa a rude, "Sau Daya ne kuma akan Rumaisa ne aka yi min aiki. "Karki kara zuwa wurin wani malami da sunan yayi maki magani meyasa bakya da hakuri ne?" sun shekara ne da ba ki ga ya saketa bane ki jira ki gani nan da ɗan wani lokaci zai sake ta ai komai a hankali yake tafiya. Mami ta faɗa ranta duk a ɓace da sauri Siyama lokacin,ta fara jada baya tana komawa ɗakinta hawayen idonta na gudu bisa fuskarta da gaske Mami ta yiwa yaya Abba magani dan ya saki Aydah ya rabu da ita.?"meyesa Mami meyasa za ki yi haka wannan wane irin mugun son zuciya ne?" Siyama ta faɗa cikin gunjin kuka gata ɗaya zata yiwa Aydah taje gidan har ɗakin yayansu ta ciro layar da aka saka mishi ta konata. Da sauri Siyama,ta saka hijab ta dauki car key da sauri ta fice daga ɗakin har ta fita daga gidan Mami bata sani ba. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/24, 2:09 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 079. Mai adaidaita yana sauke Aydah a ƙofar gida ta miƙa masa kuɗinsa da sassarfa ta nufi ƙofar gidan ta tura ta ji a rufe daman tasan da matuƙar wahala ta tarar da ita a buɗe duba da yanzu ne gari ya gama wayewa. Kuma ka'idar gidan ce koda yaushe ƙofa ta kasance a rufe dan ko masallaci Yayanmu ya fita maigadi zai maida ƙofa ya rufe idan ya dawo ya buɗe masa ya sake rufewa. A hankali ta shiga kwakwasa gate ɗin maigadi ya taso da sauri ya buɗe mata yana gani Aydah ce ya washe haƙora duk da acan kasan zuciyarsa yana mamakin daga ina ta fito da sassafe nan. "Barka da safiya ranki shi dade ya lafiyar jiki?" "Barka dai Mal Isa jiki Alhamdullah na sami sauki. "Maa shaa Allah! Allah ya ƙara afuwa ya ba ku lafiya mai amfani ke da maigida Abba dukka. "Amin mal Isah nagode. Daga haka ta wuce cikin gida koda ta iso cikin main parlor babu kowa da alama mutane gidan basu tashi ba, kanta tsaye ta wuce bedroom ɗinta ita kanta bacci take ji don jiya kwata-kwata bata sami baccin kirki ba. Don haka ta hau gado ta kwanta babu jimawa bacci ya yi awon gaba da ita. A rikice Siyama ta iso kofar gidan AB ta shiga danna wani irin horn da gudu mal Isah ya fito daga banɗaki dama ya ɗan zagaya ne yau tun da ya tashe yake fama da murdawa ciki gashi ba gudanawa yake yi ba, sai dai ya je ya hau masai ya dinga nishin bala'in yana tunani ko basir ne ya kama shi. Sai da ya fara leƙa ƙaramar ƙofa yaga waye wannan ke musu rikitaccen horn da sanyi safiya. Siyama tana gani sanda ya leƙo sai ta sauke gilashin mota tana faɗin "Barka da safiya mal Isah Siyama ce ƙanwar yaya Abba. Murmushi mal Isah ya yi tare da faɗin "Ai na sheda ki Siyama ga ma kamanu nan ke da baby kin taki sa'a don ita ma bata dade da shigowa ba. Mal Isah yana kira Aydah da baby dalili ya ji uban gidansa yana faɗa ya zaci cewa baby shi ne sunanta. Farkon zuwanta da Hajiya karama yake kiranta ranar yana faɗa ta rushe masa da kuka wai yana so ya mayar da ita tsohuwa alhali ita ko seventeen years bata kai ba ai sai ya tsofar da ita da wuri rana Ab ya ci dariya kamar ba gobe, anan mal Isah ya ji ya ce "baby kin cika rigima ina laifi ya karrama ki. "Ni dai wallahi banaso ya kira ni da ainihin sunana haka kawai zai dauki wani sunan tsofaffin yana kirana dashi. "To kai ka ji mal Isah sai ka dinga kiranta da sunanta. Ab ya faɗa yana murmushi tun daga ranar mal Isah bai sake kiran Aydah da Hajiya karama ba. Mamaki ne ya rufe Siyama tana tunani "daman ashe nan Aydah ta zo ai amma lallai Aydah ba karamar criminal bace. Siyama ta ƙarashe magana tana kecewa da dariya har tana haɗawa da dukan steering wheel zuciyarta tayi farin tass! Aydah bata taɓa burge ta irin ranar yau watau kallon ƙaramar yarinya suke mata ashe jikin ne kaɗai ƙarami ƙwaƙwalwarta ta manya ce masu hangen nesa. Cike da kwari jiki Siyama ta balle murfin mota ta fito, tuni rabin damuwar da ta fito da ita daga gida ta nemi ta, ta rasa. Tana tura ƙofar main parlor daidai AB yana saukowa daga bene jikinsa sanye da sport wears white in colour da bakaken takalmin sneaker a ƙafarsa hannunsa na cikin aljihun jacket ɗinsa da ɗan kuzarin sa yake saukowa kwana biyu ya daina motsa jikinsa, ga kuma hali da jiya ya kwana a ciki yana tashi ya ji jikinsa kamar an masa duka shiyasa ya fito da zimmar fita jogging, four eyes ya yi da Siyama sai da gabansa ya faɗi, fuskarsa ta cika da mamaki mai haɗe da tsoron ganinta a daidai wannan lokaci domin ya cire shakku sai da ya ƙara kallon agogon dake daure da tsintsiyar hannunsa yaga lokaci. Tun Kafin ya ƙarashe saukowa Siyama ta ce "Barka da safiya Yayanmu! "Barka Siyama lafiya na ganki da sassafe nan?" "Eh! To lafiya zan ce Yayanmu sai dai ba lau ba. "Subhanalillah! Ba dai jikin Baby bane ko?" "A'ah! Ba shi bane Aydah ai ta sami sauki sai dai ɗan abun da ba a rasa ba. Wata muhimmiyar magana ce ta kawo ni Yayanmu za mu je part ɗinka ne ko waje za mu fita saboda banaso iyalinka su ji maganar, saboda bansan ta wacce siga za su ɗauke ta ba. Ƙur AB ya yi da idanunsa yana kallon bakin Siyama da ke rattabo masa zance sai da ya ja numfashi ya sauke kamin ya ce "Zo mu je master bedroom ɗina babu kowa a ciki za mu fi sakewa acan fiye da compound. Ya juya Siyama ta biyo bayansa suna shiga ɗakin AB ya nunawa Siyama resting chair da yatsansa. "Ki zauna mana. "Ba sai na zauna ba Yayanmu gara mu yi abin da ya kawo ni, da fari kafin nai maka wani bayani fara kama min mu sauke wannan mattress ɗin ta kan gadonka. Cike da gundarin mamaki AB yake kallon Siyama, yayin da wani irin tsoro da shakku ke cika masa zuciya. "Siyam miyasa za mu sauke katifana me hakan yake nufi?" "Zan gayamaka Yayanmu ka dai daure mu dai fara sauke katifar shaida abun da zan gayamaka yana cikin gado ne. AB bai ce komai ba ya kama katifar Siyama ta yi sauri zuwa ta shiga neman abin da bata aje ba, ta ɗauki lokaci kafin idonta ya gane mata wata ƙatuwar baƙar laya sakade acikin gadon na AB sai da Siyama ta ambaci Bismillah! Kafin ta dauko laya ɗin ta umarci Ab ya maida katifar sai da ta gyara masa bedsheet, zuciyata tana bugawa ta nuna masa layar hannunta batasan ta yarda zai ɗauki al'amari ba, amma dai gara ta sanar dashi ko don ya ƙara riƙe mata ƙanwarta da kyau don ta fahimci irin zallan son da Aydah take masa bana yaya da kanwa bane. "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Siyama laya nake gani ya aka yi kika san da akwai laya a gadon baccina?" Dogon numfashi Siyama ta ja tare da saukewa "mu je motana nayi maka bayani banaso muna cikin magana ɗaya daga cikin matanka ta faɗo. Wani gwaron numfashi AB ya sauke batareda ya sake magana ba ya wuce gaba Siyama ta bi shi, sai da Siyama ta shiga kitchen ta dauko ashana tana fitowa ta ci karo da Huwaila da mamaki Huwaila ta gaisheta ta amsa tare da juyawa cikin sauri ta fice dan tuni Ab ya kai wurin motarta ya buɗe ya shiga Huwaila ta bi Siyama da kallo tana mamaki me Siyama ta zo yi a gidan da sassafe tun da Aydah bata gida barantana ace ko wurinta ta, zo. Zuciyar Siyama tana bugawa ta shiga ba wa AB labarin tattaunawar da ta ji Mami da Sadiya ke yi. "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Hasbunallahu wal-imaal wakil! Me na yiwa Mami da Sadiya da suke so cutar da mutane da suka ɗauke wani jigo na rayuwarsu?" Idan ita Rumaisa basu haɗa komai da ita ba to ita fa baby meye laifinta me tai musu fissibillahi da suke so, su ruguza mata farin cikinta. Siyam na kasa gane Mami wacce irin uwa ce da Aydah bata dauko kamannuku ba da na rantse miki da Allah nace ba ita bace ta haife ta ba. Wannan wacce irin kiyayya ce idan ni nayi mata laifi me ita Aydah ɗin tai mata ko kuma ita Rumaisa wacce bata san hawa ba barantana sauka. "Ka yi haƙuri Yayanmu kowanne dan Adam da bagiren ƙaddarar da yake tafiya akai sannan kuma ɗan adam ba ya zama babu jarabta, daɗin daɗawa Ubangiji yana sonka da rahamar sa shi yasa ya jarabe ka da jarabawa irin-irin ka cigaba da hakuri haɗe da takwalli in shaa Allahu komai zai zo ya wuce kamar ba a yi ba. Ni yanzu damuwata ɗaya ce da ba musan wane irin asiri ne Sadiya ta yiwa aunty Rumaisa ba barantana mu nemo shi kamar yadda muka nemo wannan. "Kin san Allah Siyam ga baki ɗaya na ji na fara tsanar kaina domin duk ta sanadiyya ta ne mutane da ke ƙaunata ke fuskanta kalubalen. "No, no, ka daina faɗar haka Yayanmu kamar yadda na faɗa ne ɗan adam baya zama babu jarabta duk wanda kaga Allah baya jaranbtarsa to kuwa ka bincike almurarransa. Sun ɗauki dogon lokaci Siyama tana bashi baki yayin da shi ma ya gargadeta ta kada ta gayawa Daddy wannan maganar su ɓoye ta daga su sai Ubangijin talikai, domin basu san irin matakin da Daddy zai dauka ba idan ya ji wannan mummunan al'amari da Mami da Sadiya suka aikata. Anan parking lot Siyama ta kwance layar sai ga farar takarda mai ɗauke da rubutun ajami da tawada ga sunansa da na Aydah ɓaro-ɓaro acikin takardar, sai lokacin ƙwaƙwalwarsa ta soma tunano masa irin abubuwan da ya dinga yiwa Aydah, nan da nan ya ji wata irin ƙaunar yarinyar tana ƙara samun masauki na musamman a zuciyarsa. Kafin Siyama ta kona layar sai da ta fakaice idon Ab tayi snapping ɗinta as a evidence don batasan abun da gaba za ta zo ta haifar ba. Ta yi masa sallama har ta ja mota sai ta tuna da bata gayamasa mutuniyar tasa ta dawo ba, sai tayi reverse ta baya ta dawo tana murmushi ta ce "Yayanmu Babynka fa ta zama 'yar gudun hijira ka bincike ta cikin gidanan tana nan ta tsiro daga gidan Mami. Ta ƙarashe magana tana dariya zaro ido Ab ya yi cikin rawar murya ya furta "wai kina nufi baby Aydah tana gidanan?" "Ai ya ma wuce wai Yayanmu domin mal Isah ya tabbatar min tana nan ciki shi ya buɗe mata ƙofa ta shigo ka dubata ɗakinta, wata kila tana bacci ne don jiya kwata-kwata bata sami bacci ba. "Allah sarki my little Baby ki gaida gida Siyama bara na je naga hali da take ciki. Ya karashe magana yana mai juyawa da sauri Siyama ta bi shi da kallo tana dariya a cikin zuciyata tana jin tausayinsa da na Aydah dukka. Direct ɗakin Aydah ya yi yana tura ƙofa ya hango ta tayi dadai akan gado tana sharar bacci har da ɗan ƙaramin snoring, wani kalar tattausan murmushi ya saki "Baby troublemaker! Ya faɗa a bayyane yana wani shafar ƙeyarsa yana ɗan iskan murmushi, a hankali ya maida kofar ya rufe har da su murza key tun kafin ya kai kan gado ya ji yadda gaban wandonsa ya ɗago da sauri ya kai hannunsa on his lap to hide his erection. Cike da jaraba ya kwanta kusa da ita ya yi gincire tare da tallaɓe gefen kansa da hannusa guda yana kallon innocent face ɗinta, ya ɗauki lokaci a haka yana kallonta daga bisani ya jawo ta zuwa jikinsa ya yi mata kyakkyawar runguma ya tura kansa cikin wuyanta yana sauke mata numfashi tare da wasu hot kisses, motsawa Aydah tayi sakamakon matse ta da ta ji anyi ta buɗe idanunta masu cike da bacci ta kallesa dasu bai masan tana yi ba sai kokari zura hannunsa yake yi cikin rigarta wai shi ya taɓa nono tun kafin ya kai ga taɓawa Aydah ta kabar masa da hannu ta tashi zaune tana yatsine fuska. "Good morning my beautiful baby! Ashe kin dawo shi ne ba ki nemi ni ba na zo na tayaki bacci. Murmushi gefen baki Aydah tayi. "Ina kwana Yayanmu. Aydah ta faɗa cikin tattausar murya. "Lafiya ƙalau Babyna ban san haka kika yi kewata ba ai da tun jiya na gudu dake. "Ni fa ba don kai na dawo ba. "Iyee to saboda wa kika dawo. "Saboda aurena don banaso Mami ta kashe min aure. Aydah ta faɗa cikin tabara, tana wani cuno baki. Zaro idanuwa AB ya yi yana mamakin yaushe 'yar kwailarsa tayi baki har haka. "Baby yaushe kika yi baki kodai dan karatun da na fara ɗora miki ne ya buɗe wannan ɗan tsurut ɗin baki nan naki mai kama da gidan tsuntsu?" Da sauri Aydah ta rufe fuskarta da tafukan hannayenta, tana faɗin. "Dan Allah Yayanmu ka daina faɗar irin zantuka irin wannan ni wallahi kunya kake sani ji. Dariya ya yi tare da fizgota ta faɗo kansa ya kwantar tare da ɗora ta akan cikinsa, ya kai bakinsa ya yi mata rada a kunnen "Baby Aydah ta gudu gidan Mami ta dawo wurin yayanta mai bata abin daɗi. "Wayyo Allahna Yayanmu ka daina Allah kunya nakeji. "Ni kuma kunyar ce nake so na cire miki dukka ki dawo kamar ni. Ya ƙarashe magana tare da mirgina ta, ta koma ƙasa ya yi mata rumfa yana ƙoƙari kai bakinsa akan lips ɗinta ta kauda fuska "Yayanmu ban yi brush ba. "Wayau dai kike so yi min baby ki hana ni abin daɗi. Ya mutsa fuska Aydah tayi kamar za tayi kuka "Ni kam na shiga uku da kai Yayanmu za ka ɓata ni. Karan hancinta ya ja "Ai yanzu kin kusa ki zama 'yar hannu sannu-sannu da kanki za ki dinga neman abin da.... Da sauri Aydah ta rufe masa baki tana girgiza kai dakyar ya kyaleta ta, ta shiga bathroom ta yi wanka tare da wanke baki a tunani Aydah koda za ta fito ya fice tana buɗe kofa ta ganshi kwance yana dannar wayarsa. Sai lokacin ta lura da takalma a ƙafarsa gashi ya hau mata gado da sauri ta zo ta sauke mai ƙafafunsa ƙasa tana mita "Kai Yayanmu wannan wacce irin ƙazanta ce za ka hau min gado da takalmin a ƙafarka. Ajiye wayarsa ya yi yana kallonta yake faɗin "uhm! Su Baby Aydah manya yaushe kika fara tsafta yoo ni idan an ce na lissafa kazamai sunanki ne na farko da zan fara ambata. Kukan shagwaɓa tasa tana yi tana bubbuga ƙafafu "wallahi ni ba kazama bace Yayanmu ka daina kirana da kazama banaso. Sai da AB ya fakaice idonta ya fincike towel ɗin jikinta wani ihu tasa ta faɗa jikinsa dama abun da yake so kenan don yana gani nakedness ɗinta ya gigice. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/24, 2:11 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 080. Wasanni masu zafi da rikita ƙwaƙwalwa ya shiga yi da ita duk wata gaɓɓa ta jikinta sai da AB ya tsotse ga baki ɗaya ya fitar da 'yar mutane daga hayyacinta sai faɗar yake "baby taɓa min nan tsatso min nan. Babu musu balle gardama Aydah take masa abun da ya umarce ta ai kuwa ɗan taliki nan notikkan kansa suka ƙara kwancewa ba ka ji komai sai ihu da gurnaninsa cikin ƙanƙani lokaci ya sami natsuwar da jiya ya kasa samu a wurin Rumaisa ya wani rungume Aydah yana sauke mata numfashinsa a fuska cikin sarƙewar lafazi ya kira sunanta. "Baby Aydah! "Uhm! "Ke ɗin ta daban ce kuma ta musamman sai yanzu nasan me ake nufi da kalmar “jindadi” ba komai yasa na fahimci hakan ba sai kasancewarki acikin rayuwata. Baby kin zamo wani jigo mai girma da daraja a idanuna bantaɓa tunani alaƙa ta dake za ta juye izuwa wannan babban matakin ba. Tunanin na yana da damar zuwa ko'ina ne, amma ina mamakin yadda yake zuwa ga naki tunanin a koda yaushe. Duk sanda na kadaice tare dake na kan ji ni acikin natsuwa marar misaltuwa Aydah kin zama zinariya acikin dubban mata kin cancanci na mallaka miki wannan duniyar, tawa ke kaɗai na miƙa miki ragamar shugabancin mafi girma acikin zuciyata. "Uhm! Yayanmu kalamanka daɗi sai dai daɗinsu ya hanani fahimtar me kake nufi ne da kuma ma'anar su. Sanyayyar dariya ya yi yana sumbatar forehead ɗinta "Ba lallai bane ki iya fahimtar kurman allona ba baby amman ina fatar anan gaba ki fahimci cewa kece mace ɗaya da ta iya mallakar duk wasu abubuwan da mace ke buƙata na ƙawatuwa halitta da saukar da natsuwa agareni ashe kece mafarkina da na daɗe ina yi na wata Kyakkyawar surar wacce a koda yaushe ke zuwa min a mafarkina, tattausar fatar jikinki da waɗannan abubuwan naki masu cike da daɗin taɓawa sune mafi kyawun bangarorin jikinki da suka tafi da ruhi da gangar jikina. "Yayanmu! "Baby. "Yayanmu bansan meyasa nake ji daɗin kalaman nan da ke fitowa daga bakinka ba, bansan meyasa nake jin su tamkar wasu na musamman ne duk da bana iya fahimtar manufarsa Amman zan iya cewa da kai ina ji natsuwa tare da wani irin nishaɗi yana shiga ta ni dai nasan ba zan iya rayuwa idan babu kai ba Yayanmu, ina ji kamar kaine jini da ke sarrafa gangar jikina. Sosai ya ƙara shigar da ita jikinsa yana ji shi ma ba zai iya rayuwa idan babu ita a duniyarsa ba duk da har yanzu bai gama tantance kalar mizanin da matsayinta yake dashi a zuciyarsa. Kalaman Aydah ba ƙaramin daɗi suka haifar masa ba duk da yana kallon kansa a matsayin wanda bai iya tsara daddaɗan kalamai ba amman domin ya faran zuciyar Aydah sai ƙiƙƙirar su yake yi domin ta cancanci fiye da hakan a garesa, fahimtar da ya yi kamar kalaman nasa suna neman ƙarewa sai kawai ya sauya akalar zancensa zuwa harshen mafi sauƙi da yafi kwarewa dashi. "I'll never stop trying. I'll never stop watching as you leave, I'll never stop loosing my breath everytime I see you looking back at me. I'll never stop holding your hand. I'll never stop opening your door I'll never stop choosing you Baby in my bed and I'll never stop get used to you. Ya ƙarashe magana tare da sake manna mata kiss a lips ɗinta "bari na je nayi wanka ke ma ki shirya ki sauko ƙasa ki ci abinci banaso zama da yunwa kin ji my hot Babe?" AB yana zare Aydah daga jikinsa tayi sauri sunne fuskarta a pillow ita fa har yanzu ta kasa sakewa da yayan nata wasu abubuwa idan yana yi mata su bala'in kunyarsa take ji har ya mayar da wandonsa ya fita Aydah bata daina mamakinsa ba wai da gaske wannan yayanta ne yake mata zafafan abubuwa masu rikitar da lissafi. Cike da karsashi Ab ya isa master bedroom ɗinsa kaitsaye ya wuce bathroom yana wanka yana tuna moment ɗinsa da Aydah ko a mafarki aka ce masa hakan za ta faru tsakanin su ba zai yarda ba. Wai yau shi ne ke bin 'yar ƙaramar yarinya ko ƙaramar ma Aydah Babynsa yana shagalinsa da ita duk daɗin da ya kwasa bai hana masa ji wani irin kamar abun da yake mata ba daidai bane yana gani kamar akwai cutarwa duba da har yanzu she's still teenager bai dace ace tasan ɗan namiji a wannan shekarun nata ba. A hankali ya saukar da idonsa akan mazantakarsa yaga girmanta shi kansa sai da ya ji tausayin Aydah ya tsirga masa. Gimbiya Rumaisa ana can kan gado hangame da baki tana kwasan bacci abinta sai da rana ta fito ta hantse sannan ta farka shi ma fa a dalili kiran wayarta da ake ta faman yi babu kakkautawa, ranta abace ta farka sai da tayi doguwar hamma tare da miƙa ta saki wata 'yar ƙaramar tusa, sannan fa ta sakko daga kan gado ta nufi wayarta da ke aje akan dressing mirror, sunan Aunty Raliya ta gani akan iD shiyasa tai sauri kiranta daman ko bata kira ta ba dole za ta nemi ta don magani da ta faɗa mata ta siya tasha bai mata aiki ba duk da tasan yayarta ta, kwararriyar likita ce ta fannin mata. Aunty Raliya tana picking Rumaisa ta shiga zayyana mata damuwarta "Aunty na ce kodai za ki haɗa ni da wani likita da kike da good connection dashi anan Kano. Rumaisa ta faɗa tana jin wani irin abu yana tokare mata maƙoshi. "Shi kenan bari nayi magana da doctor Sameer matawalle kwararre ne ki je asibitin sa in shaa Allah za a dace. Sannan kuma ki dakatar da shan wadancan magunguna na mata har ki sami lafiya. "To Aunty nagode. Sai da Aydah ta sake yi wanka sannan ta shirya cikin short mini skirt da flora half vest ta saki kitson kanta, bata yi kwalliya ba ta dai ɗan shafa lip balm a labbata jikinta na fitar da sanyayyen ƙamshi Huwaila tana ganinta ta sakar mata murmushi "oyoyo da uwar ɗakina ashe tare ku ka zo da Siyama shi ne bata faɗamin ba na tanadar miki karin kumallo mai rai da lafiya. "Yaya Siyam kuma?" Aydah ta furta da mamaki. "Eh! Ko batare da ita ku ka taho ba?" "Ni kaɗai na taho aunty Huwaila don koda na fito yaya Siyam tana bacci bata tashi ba. "Ikon Allah! Ai kuwa Siyama ta zo gidanan da sassafe nan da wancan rigimammiya ce sai na ce ko fitinarta ce ta motsa shi ne ta zo wurin Yayanmu neman magana. "To kodai yaya Siyam taga lokacin da na fito shi ne ta biyo bayana?" Aydah ta faɗa tana kallon fuskar Huwaila wacce har yanzu ita ma da raguwar mamaki akan fuskar ta, ta. "Wata kila haka ɗin ne je ki dining na kawo miki karin kumallo yanzu nan na kammala. "Aunty Huwaila ki haɗa da Yayanmu shi ma bai yi breakfast ɗin ba. Huwaila ta amsa mata da to Aydah ta juyo ta baro kitchen ɗin ta wuce dining room ta zauna. *KIM'S AUTOMOBILE INDUSTRY LAGOS * Anaal tana zaune a office ɗinta damuwa tana neman tai mata yawa tun jiya da Abbu ya kira ta ta je ta sami shi a the george hotel ta haɗu da wannan balarabiya matarsa, hankalinta ya yi mummunan tashi tun sanda ta baro hotel ɗin take cikin wannan yanayi na damuwa ba don komai ba sai irin tattali da zallan ƙauna da taga yana nunawa wannan balarabiya ɗin da ya kira da sunan matarsa. Bata taɓa ganinsa cikin farin ciki da walwala ba sai jiya a gabanta yake nunawa Maysun soyayya irin wacce bata taɓa gani ya nunawa mahaifiyarta ba wanda hakan ba ƙaramin kona mata rai ya yi ba, musamman da ta tuna da irin zaman da yake yi da mahaifiyarta, ta duk da Hajiya Safiya ta kasance mace mai haƙuri da kawaici ga sani ya kamata amma har illa yau Aliyu na uku ya kasa bata matsuguni mai girma a zuciyarsa kamar dai kwatakwacin wanda ya ba wa Maysun a ganinta mahaifiyata, ta cancanci ya ƙaunace kamar yadda yake ƙaunar Maysun. Tausayin ummie ta ne ya lulluɓeta ko wane irin hali, za ta shiga idan tasan da labarin mijinta wanda ta bashi yarda akwai wani Kurman allo da ya ɓoye ya kasa bayyana mata. Ita ko kaɗan damuwarta mahaifiyarta bata damu da hali da mai babban ɗaki da raguwar 'yan uwa Abbu za su shiga ba idan su kasan da wannan labarin damuwarta umminta wacce sanadin hali ko in kula da Abbu yake nuna mata ta kamu da cutar hawan jini sosai Anaal take gani rashin adalcin Abbu ga umminta,wanda hakan ne yasa ƙiyayyar Maysun tai mata shigar kutsu a zuciyarta. Ƙwaƙwalwarta ta shiga tunano mata yadda tasan da wanzuwa Maysun a duniyar Abbunta. *FlASH BACK* Wata rana Aliyu na Uku yana kwance a ɗakinsa dake gidansa dake unguwar Victoria island, wannan ita ce ranar da ba za ta taɓa gushewa a tarihin rayuwar Anaal Aliyu na uku. Yau ta kasance ranar weekend ne dukkansu suna gida twins suna bangaren su ita ma tana nata tun jiya Aliyu na Uku yake fama da zazzabin mura sani da Anaal tayi sosai mura take wahalar da mahaifin nata yasa tana tashi ta shiga kitchen ta dafa masa shayi mai ɗauke da tafarnuwa da kanufari sai 'yar citta ɗanya wanda ko a birnin kudu shi taga umminta tana dafa masa a duk sanda mura ta kama shi kuma shayi ne kaɗai ke warka masa da mura da wuri dalili da yasa ta koyi dafawa kenan, tun da tasan anan Lagos bashi da mai dafa masa. Tana kammala dafa shayi ta juye a ɗan madaidaicin flask ta ɗora akan tray haɗe da mug da container ɗin zuma, tana zuwa part ɗinsa ta tarar da baya cikin parlornsa sai kawai ta wuce master bedroom dinsa saboda batada shamaki da ɗakinsa, muradi dai ta nemi iznin shiga. Tana zuwa tayi knocking sai dai ba a amsa ta ba Anaal ta daɗe a tsaye tana knocking bata ji Abbu ya bata izinin shiga ba sai tayi tunani ko ciwon nasa ne ya yi tsanani saboda tasan mura bata masa da wasa, da sauri ta tura ƙofar ɗakin nasa ai kuwa ta hango shi kwance cikin duvet da sauri ta aje tray ɗin hannunta akan bedside drawer, ta zauna dai dai saitin da fuskarsa take ta kai hannunta a forehead ɗinsa ta ji zafi miƙewa tayi da zimmar ta dauko hand towel a bathroom ta jiƙa shi da ruwa ta ɗora masa a goshin nasa sai kawai idanunta suka sauka akan gefen pillow da yake kwance wasu daɗun hotuna ta gani da sauri ta dauko su ta dinga kallonsu ɗaya bayan ɗaya yayin da gabanta ke wani irin dokawa a dalilin a Abbunta da ta gani da wata mace wanda ba umminta ba ga kuma wani yaro wanda aƙalla ba zai haura shekara ɗaya zuwa biyu ba mai matuƙar kama da Abbu kamar an tsaga kara. Wani irin tsoro ne ya darsu a zuciyarta bata dawo daga duniyar da ta lula ba ta ji Abbu ya fincike hotunan da daga hannunta ya wani haɗe fuska don kada ta kawo masa wargi "waya ba ki izinin shigo min ɗaki kai tsaye Anaal?" "Abbu na zo na kawo maka tea dinka ne, na dinga knocking ba ka bani izinin ba shi ne na tsorata na shigo don na duba ka. "To da izinin wa kika ɗauki waɗannan hotuna?" "Abbu ka yi haƙuri bansan hakan zai ɓata maka rai ba. "Tashi ki fice min daga ɗaki. "Abbu Dan Allah ka faɗamin alaƙar ka da wannan matar da yaronta?" "Anaal ki fita nace!!! Ya ƙarashe magana cikin shouting da sauri Anaal tashi ta fice daga ɗakin bayan kwana biyu da faru al'amari Abbu ya zaunar da ita ya yi mata cikakken bayani akan Maysun ya kuma saka ta ta ɗaukar masa alƙawari ba za ta gayawa kowa ba wannan yasa Anaal ta binne wannan ɓoyayyen sirrin acikin zuciyarta batareda da ta fitar dashi ba. *FLASH BACK END* Anaal ta sauke ƙarfaffiyar ajiyar zuciya tana ji wani irin tuƙuƙi a cikin zuciyarta sai kuma tasaki wani tattausan murmushi tare da duka desk ɗin gabanta ko me ta tuna oho! A gaggauce ta fice daga office ɗin nata kai tsaye parking lot ta wuce anan ta haɗu da Zayeed yana ƙoƙarin parking motarsa duk horn ɗin da yake mata bai sa ta tsaya ba, ta ja motarta da wani irin speed ta fice daga company. *ALHAJI BASHIR MANSION* Har Siyama ta shige ɗakinta bata haɗu da kowa ba a downstairs parlor, tana fitowa daga wanka Mami tana shigowa ɗakin nata. "Ina Aydah?" Tsuru-tsuru da idanu Siyama tayi ta rasa wacce amsa za ta ba wa Mami. "Wai ba magana nake miki ba kin wani kakkafe ni da idanu kamar wata sa'arki. "Mami yanzu nan na tashi daga bacci kuma koda na tashi bata ɗakinan ki duba ta a downstairs parlor. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 10000[1/25, 1:42 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 081. Babu inda Mami bata nemi Aydah ba acikin gidan bata ganta ba,kai tsaye Mami ta nufi bangaren Daddy,sai famar huci take daga kai Daddy yayi ya kalleta ganin ko sallama batayi ba ta faɗo masa parlor zama Mami tayi fuska babu walwala take faɗawa Daddy,ta duba ko'ina bataga Aydah ba tasan kuma babu inda zata koma sai gidan Abba. Kuma tasan shine yazo ya dauke mata yarinya saboda bayada kunya. Wani murmushin gefen baki Daddy,yayi har aransa yasan Abba ba zai zo ya ɗauki Aydah batareda ya nemi izninsu ba. Sai dai ita Aydah ta gaji ta koma gidan mijinta, Daddy bai ce komai ba ya dauki wayarsa ya shiga kiran wayar Abba Bashir tun kafin ta katse AB ya daga da respect a muryarsa yake gaisheda Daddy, Daddy ya amsa yana tambayarsa jikinsa, cike da kunya AB ya amsa ko kaɗan bayason Daddy ya rika tambayarsa yanayin jikinsa. "Aydah ta dawo gidanka ne?"mun duba ko'ina a gidanan bamu ganta ba. Wata irin kunya ce ta rufe AB duk yabi ya daburce yadda ya yi ne ya tabbatarwa da Daddy,Aydah tana gidan. Sai kawai Daddy ya kashe wayarsa batareda ya jira amsar da Abban,zai basa ba ya mayar da kallonsa wurin mami yace "Ta koma gidanta zan baki shawara ki daina sakawa yaran nan ido mariya dan watarana kar su baki kunya musamman Aydah dake da zallar kurciya tana ganin komai tayi daidai ne a wurinta kinga yanzu bata nemi izinin ki ba ta koma gidan mijinta da ƙafafunta. Mami na huci ta miƙe tsaye tana faɗin."ko dai shi munafukin ya hure mata kunne yazo ya ɗauketa to wallahi zai gamu dani. A fusace Mami ta ƙarashe tare da ficewa daga parlorn na Daddy,tana jin wata kwallar takaici na taruwa a idanunta da gaske ta gaji idan Abba bai saki Aydah ba komai ma zai iya faruwa da ita kallo ɗaya ta yiwa Siyama dake zaune a parlor tana karin kumallo cikin nishadi da walwala ta nufi stairs,da ido Siyama tabi Mami tana yimata fatan shiriya aranta. Sai da Mami ta tabbatar Daddy,ya fita ta dauki mota ta fice daga gidan zuciyar Siyama duk babu dadi wannan karon kuma bata san me Mami zatyayi ba akan auren AB da Aydah, addu'a kurum Siyama ke yi Allah yasa komai yazo da sauki bata fatan Auren yaya Abba da Aydah ya rabu kamar yadda mami ta so. "Gaskiya da abun Mamaki Hajiya mariya ace har yanzu asirin nan bai yi tasiri akan Abba ba. "Kodai ita Aydah tana boye maki ne basa zaman dadi da yayanta?" "Me zata boye min zeenatu?"Karki manta ni na haifi Aydah na kawota a duniya duk wani takunta a tafin hannuna yake ina jin wancan aikin dai da ya yi ya lalace yanzu tashi za kiyi muje a ɗora sabo,wannan karon har Alhaji Bashir nakeso a saka aciki dan duk yadda nakeso na raba aure Aydah da wannan yaron mahaifinsu shine mutum na farko dake takamin burki. Wannan karon ko nawa zan iya zubewa Abba yabar rayuwar Aydah har abada ya saketa saki uku,shi kuma Alhaji Bashir ya kori Abba daga gidansa gab aki ɗaya,ya karbi duk wani abu da yasan na shine a wurin Abban wani miskilin murmushi Hajiya Zeenah tayi anzo wurin da take so a taho,daman bata da buri ita da mijinta da ya wuce Abba Bashir yabar rayuwar gidan Alh Bashir na har abada babu wani bata lokaci Hajiya Zeenah ta dauko mayafinta ta raka mami,wurin malam sun ɗan bata lokaci kafin su samu ganin malam. Anan Mami ta faɗa masa bukatarta Dan kafin su isa sai da Hajiya Zeenah ta gargadeta akan karta kuskura ta raina aikin da yayi mata a baya kawai ta faɗa masa tana son ai mata aiki wanda yafi wanda yayi mata a baya "buƙatar ki zata biya muna bukatar shanu guda biyu bakar akuya guda biyar za'a yanka jinin ne ga aljanin da zai yi maki aiki. Cikin rawar jiki Mami tace to zan iya bada kuɗin sai a siya?" za ki iya bayarwa wannan karon baƙaƙen aljannu ne za suyi maki aiki,daga yaron da za'a yi aiki akansa har mijin naki suna da ibada sosai, kuɗin aikin ki dubu ɗari biyar ne har dabbobin da za'a siya. Dan jim Mami tayi tana tunanin yawan kuɗin dake cikin account ɗinta ba zasu wuce naira dubu ɗari uku ba yanzun ma dubu ɗari biyu ta taho dasu cash,zan iya tura ma ta account idan na haɗa kuɗin.?" "Babu damuwa za mu sa aljannu su tura maki account number. Da haka Mami suka yi godiya suka fita daga ɗakin da baya da baya. A mota Mami ta kalli Hajiya Zeenah da damuwa a fuskarta tace "Hajiya Zeenah ina zan samu dubu ɗari biyar dukka kuɗin account din na bai kai haka ba. Da mamaki Hajiya Zeenah ke faɗin "auh dama baki da kuɗin kika saka muka je wurinsa?"ni watarana idan kina faɗin baki da kuɗi sai nayi ta mamaki wallahi,kamar ke matar Alhaji Bashir za'a ce dubu ɗari biyar tafi karfinki. "Uhm! Hajiya Zeenah kenan kamar dai baki san Alhaji bane,waya faɗa maki haka kawai yake sakin kuɗi batareda wani kwakkwaran dalili ba. "Yanzu dai tunda kina da kaddarori haka ma 'ya'yanki sai ki siyar da wani abu ki biya buƙatarki daman ance ranar biyan buƙatar rai ba a bakin komai yake ba. "Haka ne zan duba na gani me ya dace na kaɗarr. Mami ta faɗa a hankali sai tsinewa Abba Bashir take aranta duk yabi ya mayar da ita mushrikar karfi da yaji tana zaman-zamanta yajaza mata masifa. Da yamma wuraren karfe 5 AB ya fito cikin shirin fita da shi da Rumaisah sun yi kyau har sun gaji kana kallonsu kasan sababbin ma'aurata ne kai tsaye AB ya nufi ɗakin Aydah da wani irin kallo Rumaisa tabisa dashi tana jin wani katon abu yana tsaya mata a wuya, duk yadda take so ta hana kanta kishin Aydah ta gagara dan bataga wani abun da zata yi kishi dashi ba ajikin Aydah da tafita komai da komai nesa ba ma kusa ba. Banda namiji bai san kunya ba kuma maye ne yana da kamar ita me zai tsinta ajikin Aydah kwailah da ita downstairs ta nufa ta zauna can tana jirasa kar ta tsaya nan ranta ya ɓaci a banza a wofi. A hankali ya tura kofar ɗakin nata,kwance ya sameta da waya a hannunta tayi nisa cikin karatun da take na littafin (Muhabbatil Qalb)na Asmy b Aliyu har bata so ta tsayar da karatun sai take ganin jaruman cikin littafin kamar ita da yayanta lokaci ɗaya taji an fisge wayar,a mugun tsorace ta dago tayi arba da fuskar yayanta wanda ya haɗe cikin farin voyel mai manyyan zane yayi kyau matuka, zuciyarta ta shiga wani irin dokawa da wani irin ƙarfi kurawa wayar ido yayi na son ganin abunda ya dauke mata hankali har haka Da sauri ya kalleta da zallar mamaki cikin fuskar sa kunya kamar zata kashe Aydah kuma daidai wurin da ake zuba zallar soyayyah tsakanin maina saraki da Asma'a saraki ya duba. "Baby!!! yay faɗa da bayannanen mamaki a muryarsa,ko a mafarki ko a gaske bai taɓa tunanin kanwar tasa tana irin wa'yannan karance-karance ba. marairaicewa tayi duk jikinta yayi sanyi, da ido yake tambayarta yaushe ta fara wannan?"jin taki magana ya mika mata wayar da wani yanayi a muryarsa yake faɗin."zamu fita da Rumaisah me zan taho maki dashi?" Sai da ta kalli fuskarsa ganin ita yake kallo sai tayi saurin dauke fuskarta cikin nasa,wani irin kishi taji yazo ya rufe mata zuciya wanda bata taɓa jin kalarsa ba,batareda ta kallesa ba tayi masa fatan a sauka lafiya. Juyawa yayi ya nufi kofa batareda yace komai ba kasa jurewa tayi da gudu taje ta rungumesa ta baya gamida zagaye hannayenta acikinsa wani irin dumi jikinsa ya dauka tsikar jikinsa ta tashi ya saki kayataccen murmushi tare da shafa hannayenta dake zagaye da cikinsa. "Shagwabar ta motsa kenan. Ya faɗa yana dawowa da ita gabansa tura masa baki kawai tayi tana so tasan hanyar da zata hanasa wannan fitar tana so ta koyawa Rumaisah hankali da take daukarta ƙaramar yarinya. Samun kanta tayi da ɗora hannunta akan kafadarsa ta ɗora kafafunta akan nasa saboda tsayin yayan nata ya yi yawa. Wani irin numfashi AB ke fitarwa mai zafi sai kokarin kaucewa yanayin da baby Aydah ke son sakasa yake buɗe baki yayi da nufin yayi mata magana tayi saurin hura masa iska wani irin lumshe ido AB yayi yana kiran sunan Allah aransa. "Baby Aydaaah!" Ya faɗa yana jan sunan har ya fara fita a hayyacinsa ganin yadda take bin dogon wuyansa tana shafawa aranta ta shiga faɗin."1,2,3 gooooooo saukar bakinta yaji acikin nasa tana yi masa wani irin sha wanda ya kusan zautar da AB yasa jikinsa ya shiga jijjiga yana wani irin rawa zufa na karyo masa ta ko'ina duk da sanyin AC dake cikin dakin, ta ciga ba da kissing dinsa tana tallabe da kansa. "Allahu Akbar! AB ya cigaba da zuba kabbara aransa bai taɓa sanin daɗin kiss ba irin wannan lokacin tuni baby Aydah ta cillasa wata duniya,ran Rumaisa idan yayi dubu ya ɓace ta shiga duba agogon hannunta kusan minti goma zaune tana jiran Abba,wannan wane irin iskanci ne da rainin hankali A fusace ta nufi sama a zuciya tana faɗin."sai ta koyawa Aydah hankali tura kofar ɗakin tayi batareda neman izini ba dan kallon kofar Aydah tayi Dan AB har ya fara barin jahar Kano Wani irin mummunan bugawa ƙirjin Rumaisah yayi tsayawa tayi kamar statue tana kallon yadda AB yake sakin numfashi agaban yar cikinsa,miskilin murmushi Aydah ta saki ganin yadda shock ya kama Rumaisah lokaci ɗaya Aydah takai hannunta kan wandon AB tana jansa da mugun rawa Rumaisah ta buga kofar,da gudu ta nufi ɗakinta tana jin kamar zata shede saboda kishi wani irin mugun kuka ne ya kwacewa Rumaisa da sauri ta rufe bakinta kar Huwaila taji sai kusan ƙarfe shidda da rabi AB ya fito ɗakin Aydah acan ya samu yayi wanka daƙinsa ya nufa ya sauya kaya yana jin kunyar abun da ya aikata,sai lokacin ya tuna da Rumaisah zuciyarsa ta wani irin harbawa da sauri ya nufi ɗakin ta yana duba agogon hannunsa kwance ya sameta akan bed ta cire kayan jikinta daga ita sai yar shimi wacce ta sauka kan gwiwowinta yadda yaga idanunta sun kumbura abun ya basa tsoro da sauri ya nufeta yana kiran sunanta tun kafin yakai ga jikinta taja da baya a wani irin birkice tana daga masa hannu tsayawa yayi da mamaki yana kallonta ita ma ɗin kallonsa take ido cikin ido tana jin wani irin zugi har cikin tsakiyar zuciyarta,ta kasa mantawa da yanayin da ta samu Abba da Aydah ko ita da ya aura dan so bata taɓa ganin ya shiga wannan yanayin ba akanta. "Habibty ya kuma kika cire kayan kin fasa zuwa asibitin ne?" A haukace take faɗin."asibiti ashe kana sane? awa ta nawa ina jiranka zaune a parlor kana can kana nanniƙar 'yar cikinka dan Allah Abba bakaji kunya ba?"bakaji wani iri ba ka saka yar cikin ka agaba kana laluba?"wane kalar daɗin baki ne bakayi min ba kafin auren mu. Ka sha faɗamin baka sonta baza ka iya taɓa haɗa shimfiɗa da ita ba sai gashi yau da idanuwa na ganka ka saki tazuge wando ka miƙawa yarinya nan da ka gama rainawa ragamar rayuwarka tana sarrafa ka iya sarrafawa kai kuma sai ihu da sambatu kake zubawa kamar wani wawa kaiconka Abba wallahi-tallahi ka yi asara ka kuma bani kunya ka zama ganga mai baki biyu ka daki nan ka daki can nayi tir da halinka Abba tare da nadamar aure ƙasungumin munafuki kamar ka. "Rumaisah!!! Ya faɗa a tsawace ya zuba mata fararen idanunsa da suka fara canja kala yana wani kalan huci. "Ya isheni haka?"waya bani damar zuwa wurin Aydah ina jin ke kika buɗe min kofar zuwa wurinta ko kin manta ne ba tuna miki, ko kuma so kike naje nayi zina gani da mata acikin gidana wacce Ubangiji ya yarjemin na je gunta a duk sanda buƙata ta taso min?" Ya faɗa yana tsareta da idanunsa. "karki fara trying ɗina da yamman nan ki sameni a mota mu je a nema miki lafiya. Ya ƙarasa magana yana juyawa yana bar mata ɗakin gami da banging door ɗin. Har cikin kwanyar kanta taji bugun kofar,saboda lafiyarta ne zai sa ta bisa ba wai saboda tana tsoronsa ba daga shi har Aydah sai ta gyara masu zama saboda rashin ta ido irin na fa namiji wai kamar kato irin Abba Bashir shi zai riƙa haikewa kamar Aydah ita ma da tafita girma da cika watarana jarabar Abban isarta take sai dai ta daure kawai duk da kuwa tana shan maganin mata to ina da bata haɗawa dasu ta tabbata ba za ta iya jure jarabarsa ba,har ta shiga mota suka hau titi babu wanda ya kara magana a tsakaninsu kowane yana ji da miskilanci da ɓacin rai shi a ganin AB akan wane dalili Rumaisa zata tuhumesa akan alaƙarsa da Aydah alhalin tana matarsa,har cikin harabar asibitin Dr Sameer matawalle ya yi parking motarsa Rumaisa ta fitar da waya tana kiran Dr. Sameer matawalle ɗin wanda Auntyn ta Raliya ta haɗata dashi,bugu ɗaya ya dauka cikin sanyin murya take masa bayanin ita ce kanwar Raliya madawaki acikin wayar ya yi mata misalin office ɗinsa ,tana sauke wayar ta nufi reception batareda ta kara kula AB ba bin bayanta kawai yayi dr Sameer matawalle ya miƙawa AB hannu suka yi musabaha ya nuna masu wuri suka zauna kana ya dubi Rumaisa yana faɗin."kin batamin lokaci madam ina da gun da zan je amman haka na share wuri ina ta dakon zuwanki. Wani irin abu Rumaisah ta haɗe tana jin daci a maƙoshinta idan kuma ta tuna dalilin tsayawar tasu sai taji wani irin abu yana taɓa mata zuciya da ruhi har yanzu tunanin matakin da zata daukarwa Aydah take sai ta nuna mata ita karamar yar iska ce. Maganar Dr Sameer matawalle ya dawo da Rumaisah daga duniyar tunanin da ta faɗa. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/25, 1:45 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 082. "Madam ya kike ji yanayin jikin naki sannan jini yana zuba sosai ne?" Sai da Rumaisa ta gyara zamanta kamin ta shiga kwararowa Dr Sameer bayani har ta kammala bai katse ta ba. Ya ɗauki wayar landline ya kira nurse station ya nemi gani nurse Salma bayan ta zo da taimakonta ya yi yiwa Rumaisa duk wani bincike da ya dace ya yi mata, sai dai babban abun da ya ɗaure masa kai har ya kammala bincike nasa babu wani matsala da ya gani wanda zai haifar mata da bleeding. Ya dawo ya zauna akan kujerarsa ya kalli AB a natse ya ce "Gaskiya Yallaɓai iya bincike da na yiwa madam batada wata matsala da za ta haifar mata da zubar jini, amman duk da haka zan ɗora ta akan wa'yansu magunguna in shaa Allah za a dace. Ya rubuta musu prescription ɗin ya miƙawa AB godiya Ab ya yi masa tare da sake basa hannu suka yi musabaha akan hanyar su na zuwa gida ya tsaya a wani pharmacy ya siyo mata magani ɗin. Ɗan satar kallonta Ab ya yi yadda yaga ta rafka tagumi sai ya ji tayi bala'in basa tausayi abin ka da zuciyar masoyi, hannunsa ya kai ya sauke mata tagumin kana ya matse hannun nata cikin nasa, ya wani kwatar da murya ya ce "I'm so sorry Habibty nasàn kina jin haushina kisani duk yadda muka kai da ƙi abu ba mu isa mu gujewa ƙaddarar mu ba. Dukka waɗannan abubuwa suna faruwa ne a bisa tsarin Allah, saboda haka ina so ki kwantar da hankalinki ko kaɗan banaso na ganki cikin damuwa kin ji rabin raina?" Duk da Rumaisa ta ji dadin kalaman sa amma da tuna ko a baya da ire-iren waɗannan kalaman nasa ya yi amfani dasu ya yi mata igiza mai kattun ya ɗora ta akan hanyar da bata bullewa daga ƙarshe sai ta tsinci kanta a tashar kare yabarta da haushin karnuka. A wannan karo idan ta amince da maganganunsa shi kenan fa ta zama sa kayanka mota. Saboda haka ta kalle shi a lalace sai kuma ta kauda fuskarta ta maida ganinta akan ababen hawa dake kan titin. Yadda AB yaga Rumaisa ta ba banza ajiyarsa sai duk ya ji babu daɗi har yana ɗorawa kansa laifi na biyewa Aydah da ya yi alhali yasan za su fita da Rumaisa kuma fitar tasu ta shafi neman lafiyar ta ne. "Habibty na ce ki yi haƙuri in shaa Allah hakan ba za ta sake faruwa ba. "Abba please ka kyaleni na ji da abun da yake damuna daman an ce kana gane masoyinka na gaske ne da zarar ka haɗu da wata lalura don haka yanzu na gama gane matsayin da nake dashi a wurinka tun da ina zubar jini banida sauran amfani a wurinka ka je duk abun da ka yi don kanka. Rumaisa ta ƙarashe magana tare da rushewa da kuka irin mai cin rai ɗin nan hakan yasa AB ya nemi gefen titi ya yi parking, da sauri ya jawota jikinsa yana bubbuga bayanta. "Ke ma dai Rumaisa da rigima kike kin fi kowa sani irin matsananciyar soyayyar da nake miki da matuƙar wahala a sami wata mace da za ta haura matsayinki a zuciyata. "Uhm! A da ba nace a da ne nake da wannan matsayin ban da yanzu da ka dandani jikin ƙaramar yarinya. "Subhanalillah! Haba Habibty ba girman ki bane faɗar wannan magana ki dinga tauna kalami kafin ki faɗe sa. A fusace Rumaisa ta fincike jikinta daga nasa idanunta na ambaliyar hawaye ta ce "Na ƙi na tauna ɗin ai gaskiya ce na faɗa akan jikin Aydah duk ka bi ka canza min ka dawo wani susu ko uban me kake ji anata wanda ba ka ji anawa?" "Oh! Ni Bashir ɗan Bashir yau naga takaina ni dai ba za a ji mutuwar sarki a bakina duk masifar ki Rumaisa ni dai ba zan ce komai ba bakina da alawar madara. Ya ƙarashe magana yana sake jawota jikinsa ya cigaba da kanainaye ta da daɗin bakinsa har dai ya shawo kanta daga nan ya wuce da ita shopping mall kuɗi ya kashe mata bana wasa ba, babban abun da ya ƙara saka Rumaisa farin ciki yadda taga AB ko sweet bai siyawa Aydah ba. Suna fitowa daga mall ɗin wurin shakatawa suka nufa sai soyayya suke zuba abin su sai gafda da magarib suka baro wurin, akan hanyar su na zuwa gida ya tsaya wani masallaci ya yi sallah yabar Rumaisa a mota da yake ita ba sallar take yi ba. Yana dawowa mota Rumaisa ta kalle shi cikin shagwaɓe murya mai ɗauke da kissa da kisisina ta ce "Habibina ina ta kallon hankalinka ko za ka bani special gift na budurcina da na kawo maka da yawan ƙawayena suna turomin da pictures ɗin kyatuttuka da mazajen su, suka yi musu a daren farkonsu. Sai da AB ya tashi mota ya hau kan titi kamin ya juya ya kalle ta a ɗage ya ce "Idan haka ne meye amfani sadakinki da na biya kafin a ɗaura mana aure?" "Ka ji ka da wani zance Habibi sadaki daban wannan tukuici ne za ka bayar ba ka ji wani karin maganar da ake cewa yaba kyauta tukuici ba?" "Uhm! Haka ne. Amma wannan wata sabuwar bidi'a ce da ku mata ku ka kikkire ta daman can ku bakwso a zauna lafiya. Dariya Rumaisa tayi tana ƙara kwatawa jikinsa tare da marairaice murya "Allah Habibi haka ake yi kasan kai kifin rijiya ne wasu abubuwan ba damuwa ka yi dasu ba. "Ko ba kifin rijiya ba. AB ya faɗa yana mata malalaci kallo. "Habibi da gaske idan ka bani special gift ni kuma nayi maka alƙawari da zarar wannan munafukin jini ya ɗauke sai na gwagwaje ka da zafafan styles har sai ka ce ka ƙoshi. "Uhm! Ina fatar dai ba men power za ki sake bani ba?" "Kai Habibi abun da ya wuce ka daina tado shi nima bansan yana haifar da illa ba da ko kusa ba zan ba ka ba ai kasan ina sonka ko kusa ba zan so abun da zai cutar da kai ba. "To gayamin me kike so na ba ki a matsayin tukuici ɗin tun da kika fara wannan zance na tabbata idan har ba tukuici na bayar ba za ki barni na huta ba amman dai ki tuna da alkawarin da kika ɗauka. "In shaa Allah ba zan manta ba wayoyina nake so ka canza min kasan latest one sun fito. "Ya za a yi nasani tun ba wayoyi nake sayarwa ba da dai motoci kika ce wannan ne nake da cikakkiyar masaniya akai. "Ai kuwa dai to ni dai iphone 15 pro max nake so da samsung galaxy s24 ultra as my gift. Ta ƙarashe magana tana wani narkewa. "To su kuma waɗannan na hannunki, ki yi yaya dasu?" "Sayarwa zan yi nasha shagalina da kuɗin. Girgiza kai kurum AB ya yi tun ba yau ba ya fahimci halin Rumaisa naso spending kuɗi a wofi don kawai a zauna lafiya yasa ya biye mata suka je shagon siyar da waya ta zabi dukka wayoyin biyu da tace tana so ya biya kuɗin suka nufo gida, tsabar farin ciki da Rumaisa take ciki har baya misaltuwa, koda suka iso gida ana kiran sallar isha Ab ya wuce masallaci ita kuma ta kwaso tarkace shopping bags ɗinta ta shigo gida a main parlor ta tarar da Aydah da Huwaila, Aydah tana zaune ta ɗora ƙafafunta akan centre table Huwaila tana cire mata farce, batareda da sallama ba Rumaisa ta ƙaraso tana zuwa gaban Aydah ta zube shopping bags ɗinta ta faɗa kan kujera dake kusa da Aydah tana faɗin "Washhh! Allahna na gaji sosai jikina duk ciwo yake Habibi ya gajiyar dani ba kaɗan ba Aydah kin ga yawon da muka dinga yi sai da na fara masa kuka sannan fa ya amince muka dawo gida da har yace a hotel za mu kwana naƙi amincewa, na ce ba za a yi haka dani ba mubar 'yar yarinya mu ita kaɗai a gida. Ta ƙarashe magana tana shafa kamatun Aydah tare da sakar mata shu'umin murmushi, nan da nan fuskar Aydah ta canza tayi kici-kici wani irin malolo abu ya zo ya tokare mata ƙahon zuciya. Huwaila ta dakatar da abun da take yi ta zubawa Rumaisa ido sai lokaci Rumaisa ta kalleta a sheƙeƙe ta ce "Ke mai aiki tashi ki bar cikin parlor nan idan kika ga matan gida suna conversation a tsakanin su ki daina baza kunnuwa kina saurare wannan ai salon munafuci ne da so haɗa husuma, duk iya munafucin ki da kutunguilarki ba ki isa ki raba mana kawunan mu ba don ni da Aydah kanmu a haɗe yake tamkar ya da ƙanwa muke ko babyn yaya Abba?" Ta ƙarashe magana tana kashe wa Aydah ido. Tuni idanuwa Aydah sun fara ciccikowa da hawaye. "Tashi mana munafukar banza da wofi kina gafda da bari gidanan ba zan yi sake ki raba mana zaman lafiyarmu. Rumaisa ta faɗa a tsawace da sauri Huwaila ta tashi ta nufi ɗakinta. "Baby Aydah zo ki tayani duba kyaututtukan nan da yayanki ya yi min idan ma da akwai abun da kike so a ciki ki ɗauka ni da ke ai mun zama abu ɗaya. Gani yadda Aydah take mutso-mutso da baki tana ƙoƙarin danne hawaye Rumaisa ta saki murmushin mugunta ta soma firfito da kayayyakin dake cikin bags ɗin tana zubewa a gaban Aydah daga ƙarshe ta fito da wayoyinta "Aydah kin ga wayoyina da habibi ya siya min a matsayin tukuici budurcina da na kawo masa kin san fa haka maza suke yi da zarar su ji daɗin mace sun dinga kashe mata kuɗi kenan tamkar ba su san zafin neman su ba. Yanzu ki duba wayoyina duka yaushe ya siya min su amman har ya sake siya min wasu kai Abba Bashir duniya ne. Hawaye da Aydah take ɓoyewa ne suka kubce mata Rumaisa tana gani ta zaro idanuwa "la hula wala kuwwati illah billah! Aydah kuka fa kike yi? Ke kuwa me ya same ki haka kike zubda hawaye zo, nan ƙanwata faɗamin waya taɓa ki?" Buge mata hannu Aydah tayi ta miƙe da gudu ta haura sama tana gunji kuka, Rumaisa ta bi ta kallo sai kuma ta kece da muguwar dariya, har da su buga ƙafa a tiles "shegiyar yarinya mai baƙin kishin tsiya da sannu zan fitar dake gidanan sai na nuna miki bambancin dake tsakani babba da yaro. Tana magana haɗe da mayar da kayanta cikin shopping bags ta haura ɗakinta, zuciyarta wasai! AB yana dawowa daga masallaci sai ga Abdulkarim ya kawo masa ziyara suka tsaya a parking lot cikin motar Abdulkarim ɗin. "Ak saukar yaushe?" AB ya faɗa yana kallon Abdulkarim. "Ɗazu da yamma hankalina yana gunka tun sanda ka bani labari abun da Rumaisa tayi maka. "Uhm! Bari kawai abokina Rumaisa ta kashe ni tasa na aikata abin kunya na je na haikewa 'yar mutane sai da ta kwanta gadon asibiti. AB yana dasa aya Abdulkarim ya kece da dariya "Kai dai ba wani nan daman can ranka ya biye shi ne fa ka maida mugun yawu. "Mtss! Matsalata da kai Abdulkarim mugun ɗan iska ne kai ina faɗa maka gaskiyar abun da ya faru kai kuma kana shigowa da salon iskanci. "To na ji na daina amma wane irin mataki ka dauka akan Rumaisa?" "En! To na daina nuna mata fushina na kuma gargade ta kar ta kuskura ta sake zuba min komai a abun sha. "Mtss! Ni na zaci ka tura ta gidan ubanta a koya mata tarbiyya da ba a mata ba tun farko. "Akan me zan tura ta gidansu bayan ina sonta kuskure ne kuma ba wanda baya kuskure. "To ita kuma Aydah fa a wane matsayi ka ajiye ta kasan dai yanzu ta zama bazawara dole ka zauna da ita tunda dai kaine wanda ya kawar mata da budurcinta?" Ko kuma dai har yanzu kana nan akan bakarka na sakinta da ka ce za ka yi?" AB ya shafa kwatancce sajensa yana kallon Abdulkarim a dage kafin ya ce "Banaso bin diddigi Abdulkarim Aydah dai mata ta ce ba ruwanka da yadda zan yi da ita ban da ma kana munafuki yaushe na ce da kai zan sake ta?" Zaro idanuwa Abdulkarim ya yi "Ni ne munafuki Ab?" "Kai ɗin ko tsoronka nake ji da ba zan kira ka da munafuki ba?" Sheƙewa da dariya Abdulkarim ya yi har yana dukan dashboard ɗin mota "wallahi-azim AB ka ji kunya ka yi amanka ka lashe ɗan iska kawai mai cika bakin banza dallah kalle ka shirgegen ƙato da kai kana shigewa ɗaka da kwaila ko ba haka ka kira ta dashi ba?" "Mtss! Banza munafuki wanda bashida mantuwa koma dai mene ne ba haramun na aikata ba ehee barantana mutum ya dinga ya madidi dani. "Yoo amman dai ka yi abun kunya. "Idan mutum ya cika shi ma ya je ya yi abin kunya irin wanda nayi. "Allah ya tsare gatari da sarar shuka ni bana cika baki irin naka. Dariya kurum AB ya yi tare da faɗin "Ai sai ka yi Baby dai ta zama ni na zama ita tun da almurranmu sun daidaita na kuma riga na zura ƙwallo a raga duk abun da za ka faɗa ba zai dame ni ba domin ni kaɗai nasan irin duniyar da kwailata ta kaini, kai bari kawai Abdulkarim idan ana sallah ba'a magana Baby Aydah tayi hundred percent Baby Aydah wata duniya ce ta daban. Zaro idanuwa Abdulkarim ya yi cikin kaɗuwa yake kallon Ab ya kasa yarda waɗannan maganganu daga bakinsa suke fitowa anya kuwa Ab kansa ƙalau ko kuma dai ya zare ne. Fitilar dake cikin mota Abdulkarim ya kunna ya shiga ƙarewa kyakkyawar fuskar AB kallo yayin da AB ya dage girar ido ya yi masa kur da nasa idanuwa. "Ni ne dai Abba Bashir abokinka. "Wallahi kuwa kaine Abba Bashir amma kuwa Abba kai ɗin tantiri ɗan iska ne lamba ɗaya. Abdulkarim ya faɗa yana tu'ajjabin. "Yanzu kam ka yarda dani ni ne ko?" "Uhm! Na yarda amman Dan Allah ka dinga lallaɓa 'yar mutane kada ka mayar da ita sex addict. "Wannan kuma babu ruwanka tsakanina ne da matata. Har suka yi sallama Abdulkarim bai daina mamakin Ab ba duk da daman can ya sa ran faruwar hakan amman bai zaci hakan da wurwure ba. Direct Ab ya wuce ɗakinsa ya yi wanka ya sako dark green ɗin pajama yana zuba ƙamshin turarensa ya fito parlornsa ya zauna ya kunna tv yana kallon news sai ga Rumaisa ta shigo cikin ɗaya daga cikin sexy transparent night gown ɗin da ta siyo sosai rigar tayi bala'in yi mata kyau cikin tafiyar jan hankali ta nufi socket ta saka sababbin wayoyinta a charging. Ta dawo kusa da AB ta zauna ta dauke hannunsa dake kan hannun kujera ta haɗe da nata a hankali take massage ɗin tafin hannun nasa. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. Domin biyan ƙudin littafin nan 500 Naira only ACCOUNT NUMBER 0020428430 Ishaq Fatima A. Gtb Or 8098456130 Fatima Ishaq Opay digital services Shaidar biya 08098456130 KATIN MTN Ta👇 07043079282 Shaidar biya ta 07065283730 Ko a tuntubi 08086207764 0816 114 6563 +234 704 040 2435 ‪+234 903 056 9336 *ƳAN TAGWAYE BIYAR* KARO NA BIYU. *BAQEER* Ayusher Muhd Umm Asghar *KURMAN ALLO* Asmy b Aliyu Jidda Aliyu *AKWAI SIRRI* Zee Bawa Hajja ce *MUTALLAB ASAD* Nana Diso Billy S Fari *KULUWA* Zee yabour Sadiya Dan Duka Biyar ɗin akan 2k Hudu 1600 Uku 1200 Biyu 800 Ɗaya 500 VIP💕🔥 Duk guda ɗaya 1k NORMAL GROUP 500 VIP 1000 [1/26, 2:28 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 083. Har kusan ƙarfe goma na dare bai ga Aydah tazo wurinsa ba A hankali ya zare jikin Rumaisah daga nasa ya miƙe tsaye ya saka (casual slippers)a kafafunsa,da mamaki Rumaisah ke faɗin."ina kuma zaka je?" "Bara na duba baby Aydah nayi mata sai da safe. Ya faɗa batareda ya kalleta ba ya juya ya nufi ƙofar barin parlorn banda bugawa babu abunda zuciyar Rumaisah keyi,idan kuma daga nan ya kwana a dakin Aydah fa.?"nan take wata zuciya ta kwabeta akan faɗin. "Ai idan yana da kunya shi ma bazai farawa ba. Akan idanunta ya fice daga parlorn tana jin yadda zuciyarta tayi wani irin nauyi tana addu'a kafin ta gama shan maganin nan jinin ya tsaya,kafin kwanakin amarcinta su kare ta fara raba kwana da Aydah sai da yayi knocking yaji shiru ya kama handling ya ɗan tura ga mamakinsa a rufe yaji ta da alamar tasa key ta ciki ɗan kwankwasa wa ya shiga yi yana kiran sunan Aydah lokacin tana kwance akan bed ɗinta tayi ruf da ciki da rigar bacci ajikinta marar nauyi tana jin yadda yayanta ke kiran sunanta yana famar bugun kofa tayi masa banza haushinsa shi da Rumaisah take ji matuƙa kenan yayan nata ya fara zama munafuki mai son kansa da yawa meyasa itama da ya karbi budurcinta bai yi tunanin yimata kyauta komai kankantar ta ba.?"sai Rumaisah zaɓin ransa wacce zuciya da ruhinsa ke so sai ita wacce aka yi masa auren huce haushi da ita. Idan ta tuna siyayyar da Rumaisa ta zube mata a gabanta sai taji wani irin raɗaɗi a ƙirjinta duk bugun da AB ya riƙa yiwa kofa bai sa Aydah ta buɗe ba. Sai ma bin kofar tayi da wata irin harara tamkar yana ganinta a zuciye AB yabar kofar room ɗin yana tunanin wane irin iskanci ne ke damun Aydah yana buga mata kofa tayi masa banza. Yasan in har bacci take bata da nauyin bacci da gangan kawai taki buɗe masa kofa zuwa yayi ya wuce Rumaisah ya nufi master bedroom ɗinsa batareda yayi mata magana ba. Da kallo Rumaisa ta bisa tana sakin Murmushin mugunta Dan tana jin irin bugun kofar da yake yiwa Aydah Amman taki budewa. Koda ta samesa dakin har yayi light 0ff yabar (dim light.)a hankali Rumaisa ta hau kan bed ɗin tana kwantar da kanta a bayansa tana shafa ƙirjinsa cikin wani irin salo. Ƙoƙarin cire hannunta yake cikin jikinsa ko kaɗan baya cikin yanayin da zai biyewa Rumaisah ɗin,kuma baya so tafiya tayi nisa tunda ba lafiya gareta ba komai ya kwace masa juyowa yayi yana sakata cikin jikinsa duka cikin sanyin murya yake faɗin."muyi bacci Rumaisah,ɗan haɗe fuska tayi tana faɗin."saboda baka da lokacina baka bukata ta saboda kaga bani da lafiya.!" Ta ƙarasa magana cikin rawar muryar da AB yaji wani iri "Haba Rumaisah! Ya faɗa da wani yanayi a muryarsa. "Haka ne mana da ina da amfani a wurinka ba zan taɓa ka ba ka nuna baka so. Tana rufe baki ya shiga romancing ɗinta dan kurum ya faran ta mata rai sai da ta samu natsuwar da take buƙata ya juya mata baya yana sauke wani irin numfashi mai wahala,a daren ba wani baccin kirki ya samu yayi ba yayin da Rumaisah tayi baccinta cikin jin dadi da natsuwa. Yana dawowa sallar Asuba,ya koma ya kwanta daman saboda fushin da yake yi da Aydah ko kofar ɗakinta bai kalla ba baran tana ya tasheta tayi sallah. Haka ba ƙaramin faran tawa Rumaisah yayi ba. Ashe Aydah har yanzu wawuya ce doluwa ce ta gaske bata ma san menene kissa da makircin kishiya ba da sannu zata koya mata hankali. Karfe bakwai Rumaisah ta nufi kitchen daidai lokacin Huwaila ta fito Huwaila ta gaisheta babu yabo babu fallasa ta amsa tana faɗin."kawai tayi tafiyarta yau ita da kanta zata haɗawa mijinta break fast. Dan kallonta Huwaila tayi kafin ta juya tabar kofar kitchen ɗin. Duk gatan Rumaisa babu kalar abincin da bata iya sarrafawa ba,Ammi batayi wasa da wannan bangaren ba duk son da take yiwa ya'yanta. Cikin ƙanƙanin lokaci gidan ga baki ɗaya ya haɗe da ƙamshin girkin Rumaisah. Ko Huwaila da take zaune a ɗaki ta jinjina wa iya girkin Rumaisa a gefe tana ta tunanin yadda Aydah zata mayar da hankali ta koyi girki, dan da alama ko ta bangaren girki kawai Rumaisa zata iya sace zuciyar AB kusan ƙarfe takwas da mintuna goma,Rumaisah ta gama jera komai akan dinning table kai tsaye ɗakinta ta koma daman kafin ta sauko kasa ta gyara ɗakin haka ma parlor AB ta share wanka tayi ta haɗe cikin wata bingilar rigar kanti wacce rabin cibiyar ta a waje sai skirt da bai gama rufe cinyoyinta ba. Kwaliyya tayi sosai tayi wankan turare da khumra sauka kasa tayi zuwa ɗakin Huwaila,a bakin kofa ta tsaya tayi gyaran murya Da izza take kallon Huwaila tamkar bata son magana ta fara da cewa "waye ma kike da suna?" Da sauri Huwaila ta saukar da kanta ƙasa ta ce. "Huwaila! Dan tabe baki Rumaisa tayi tana faɗin."mu je ki yimin mopping ki wanke min toilet. Da haka ta juya huwaila na biye da ita a baya tana mamakin muguwar kissa irin na Rumaisah lallai sai tayi da gaske akan baby Aydah da mugun son jiki yayi mata yawa kai tsaye Rumaisah ta gwadawa Huwaila yadda zata wanke mata toilet tana gama nuna mata ta fito da burner a hannunta ta zuba turaren wuta ta nufi part ɗin AB har cikin bedroom ɗinsa ta shiga da burner ɗin bed kawai ne bata gyara ba dan yana bacci akai zama tayi a gefensa ta cigaba da kallon kyakkyawar fuskarsa ta dauki tsawon lokaci tana kallonsa tamkar zata cinyesa dan so. A hankali ta hau gadon ta kwanta gafda fuskarsa har tana jin saukar numfashinsa tsinin hancinta ta rika goga masa tana ganin yadda ya shiga ya motse fuskarsa still bai buɗe idon ba cigaba da goga tsinin hancinsa tayi wanda yasa dole ya shiga buɗe idonsa masu cike da bacci ya ɗora fuskarsa acikin fuskar Rumaisah yana jin yadda jikinta ke fitar da wani irin kamshi, ta langwabe kai tana kallon sa sai kuma ta sumbaci gefen fuskarsa "Mun gaisa,mu kara gaisawa. Ta faɗa tana sumbatar goshinsa kanne masa ido tayi cikin taushin murya take faɗin."wanka ko break fast? miƙewa yayi zaune gamida jawota dukka cikin jikinsa a hankali ya ɗora hannunsa akan abunda yafiso da kauna ajikinta ɗan shagwabe fuska tayi sai da ya gaisa dasu iya son ransa, sa'annan ta haɗa masa ruwan wanka a toilet yayi wanka ita ta taimaka ta fito masa kayan da zai saka tunda tasan dole zai je office sai kusan ƙarfe 9 suka fito kasa hannunsu sarƙe cikin na juna dan yau Rumaisah ta faɗa masa acikin dinning area take so suyi break fast. "Habeebi yau da kaina na shiga kitchen na yi maka break fast idan ka gama ci ina sauraran tukuici ba zan yi saurin yabon kaina ta wannan bangaren ba. Ta faɗa da murmushi a fuskarta tasa hannu tana buɗe warmers ɗin wasu irin yawu AB ya shiga hadewa da sauri dan yasan ƙamshin girkin huwaila, ya ji wannan its so different akan nata,tana kallon yadda yake wani lumshe ido yana buɗewa sarving ɗinsa tayi ,ta zuba masa hadadden kunun gyadar da tayi mai madara. "Yau fa ni zan ciyar da mijina. Ta faɗa a ɗan shagwaɓe,murmushi yayi yana ware mata manyan idanunsa,daga nan cikin dinning ɗin AB ya daga murya yana kiran Huwaila da sauri ta ƙaraso wurinsa ta zube gabansa tana gaishesa ya amsa yana faɗin taje ta kira Aydah suyi break fast nan take annurin fuskar Rumaisah ya canja har ga Allah bata ji daɗin yadda AB yace a kira Aydah ba. kwankwasa kofar ɗakin Aydah Huwaila tayi jin shiru yasa ta kira sunanta Aydah na jin muryar Huwaila tayi saurin saukowa daga kan bed ɗin still kayan bacci ne ajikinta tazo ta buɗewa Huwaila kofa. Sororo! Huwaila ta tsaya tana kallon Aydah ganin ko wanka ba tayi ba kayan bacci ne ajikinta,tana ganin irin wankan da Rumaisa tayi ita da Abba ya kamata ta zauna ko yaya ne ta yiwa Aydah karatun ta natsu,da kyar Aydah ta gaisheda Huwaila ita dai Huwaila bin ta kawai take da kallo ganin yadda idonta ya ɗan kumbura alamar dai tayi kuka. "ki sauko yanzu yayanmu na jiranki zaku yi break fast idan kin natsu mayi magana dan na lura kamar bakya cikin natsuwarki. Da sauri Aydah ta katse Huwaila tana faɗin."Ni na faɗa masa ina jin yunwa ne?"kawai suyi abin su Idan na tashi nayi nawa. Da mamaki Huwaila ke faɗin "ki rufamin asiri Auta kome ya miki karki ƙi zuwa kuyi break fast karki bata ransa bakya ganin kishiya gareki ai sai tayi maki dariya. Shiru kawai Aydah tayi tana jin ranta na ɗan tafasa dakyar dai Huwaila ta lallabata ta sauko kasa kallo ɗaya ta yiwa AB da Rumaisah ta wani dauke kai ganin yadda Rumaisah ɗin ke feeding ɗinsa shi kuma ya wani hangame baki sai kace ɗan yaye. Zama tayi batareda ta kula kowa acikinsu ba ta ɗauki plate ta shiga sarving ɗin kanta shi dai mamaki kusan kashesa yayi ganin Aydah bata gaishesa ba wannan shine karo na farko da ta nuna masa halin ko in kula,yaga lafiya lau jiya suka rabu suna cikin farin ciki to mai ya canja ta haka lokaci ɗaya? "Baby Aydah kin tashi lafiya babu gaisuwa yau?" Rumaisah ta faɗa tana kallonta wearing a big smile kwance akan fuskarta nan ma Aydah ta yiwa Rumaisah banza tamkar babu ita a wurin take magana abun da ya kara fusata AB kenan Aydah har nawa take zata gansa a wuri ta wulakantasa tayi kamar bata gansa ba wata irin zuciya ce ta kwashi Abba a mugun fusace ya fisgo Aydah yana kallonta da idanunsa da suka gama rikidewa saboda ɓacin rai. "me kika dauki kanki haaa?"kin wulakanta ni jiya yau ma haka ko don na fara haɗa gado dake kike ko fara raina ni ko me?" Banda kyarma babu abun da jikin Aydah yake hawaye sai rolling suke akan fuskarta bata taɓa ganin yayanta so upset ba irin na wannan lokaci cikin kuka da majina take faɗin."ban raina ka ba yayanmu Amman ko mai z akayi ka rika yin adalci jiya ka siyawa matarka gifts na budurcinta da ta ka kawo maka ni me nai maka da baka bani nawa ba. Ko don saboda ba ka sona dan biyan buƙatar ka da sauke sha'awarka kawai ka......! Saukar mari taji akan fuskarta yasata haɗiye raguwar kalamanta yana nunata da yatsa jikinsa banda rawa babu abunda yake ba'a taba tozarta sa ba irin wannan lokacin wai kamar Aydah ke faɗa masa irin wa'yannan maganganun dole raini ya shiga tsakaninsu tunda taga makwancinsa. Meyesa bai haɗe duk wani abu da yake ji ba ya danne sha'awarsa bai tun kari Aydah da bukatarsa ba, daman abun da yake ta gudu kenan raini tun kafin aje ko'ina raini ya fara giftawa a tsakaninsu da sauri Rumaisah ta shiga tsakaninsu tana rike hannayensa,cikin tattausan lafazin take faɗin "Haba Habibi idan rai ya bata hankali ake sawa ya nemo sa ai ko ba komai ka fita hankali meyesa zaka biye mata ita ɗin yarinya ce ƙarama ba hankali fahimtar abubuwa cikin sauki take da ba kamata ya yi ka lallaɓa ta. Wani irin mummunan tsaki Aydah ta saukewa Rumaisah cike da jaraba da tsiwa da rashin kunya ce "Duk abin da ya faru ba munafucin ki bane ya haɗasa shi ba baƙar munafuka kawai. Ganin AB ya juya kanta da gudu tabar cikin dinning ɗin tana jin wani mahaukacin kuka mai cike da kishi da bacin rai na kwace mata lokaci ɗaya, zama AB yayi yana dafe kansa da ya ɗauki zafi sosai jin yake tamkar ya amayar da zuciyarsa duka saboda takaici wani irin daɗi ne ya cika zuciyar Rumaisah idan zasu riƙa samun matsala haka a tsakaninsu ai ita ta kwanta kawai tayi ta bacci hadda kyakkyawan minshari. "Habeebi!" Ta wani kira sunansa da kwatacciyar murya, har da wani langwaɓar da kai take yi da wata irin zuciya AB ya ɗaga mata hannu miƙewa yayi cikin sassarfa yabar cikin dinning area din, tamkar zai tashi sama saboda zuciya dan tabe bakinta Rumaisah tayi zuciyarta fesss! Juyawa tayi ta shiga break fast ɗinta a natse dan ita bata ga tashin hankalin da zai saka taƙi cika cikinta ba. AB ko sallama bai yi mata ba ya wuce office duk ransa a ɓace yana mamakin Aydah yana ƙara regretting fara taɓa jikinta, Huwaila tayi tagumi tana kallon yadda Aydah ke shesshekar kuka. "Yanzu da kika faɗa masa magana haka cikin zafin rai kina gani shi zai sa ya fahimci ya yi maki laifi?"ita fa da kissar mu ta mata tayi amfani da ita ta haɗaki faɗa da mijinki mai sonki da kaunarki, ashe duk karatun litattafai da kike ya tashi a banza tun da baki san yadda za ki kama mijinki a hannunki ba nan gaba idan bakiyi hankali ba za ki zama yar kallo a gidanan ina faɗa maki gaskiya idan baki buɗe idonki ba kika bar wannan sakarcin ba kina ji kina gani Yayanmu zai fi ƙarfin ki tsakaninki dashi sai gani daga nesa. Cikin murya kuka Aydah tace "shi bakya ganin laifinsa sai ni ko Aunty Huwaila.?" Baki Huwaila ta buɗe tana kallon Aydah dashi da gaske wawancin Aydah ba zai daina bata mamaki ba dan takaici bar mata ɗakin tayi idan ta natsu zuwa anjima suyi magana. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO. [1/26, 2:29 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 084. Huwaila tana kammala share-share da 'yan goge-goge da take yi a kullum wanda kamar hakan ya zame mata jiki idan bata yi ba bata ji daɗi, ta nufo ɗakin Aydah babban abin takaici har yanzu Aydah tana nan kwance da rigar bacci a jikinta, haushinta kamar zai kashe Huwaila amma da tuno da irin tarbiyyar da Aydah ta samu ta ba kyara balle tsangwama sai ta haɗiye abin da take ji ta nemi gefen ta, ta zauna sai ta ƙare mata kallo da kyau kamin ta furta "Auta tashi ki zauna mu yi magana. Aydah ta ya mutsa fuska da gaske bata so duk wata magana idan dai ta shafi yayanta ne, gaba ɗaya haushinsa take ji ahalin yanzu tana masa kallon azzalumi mutum marar adalci don haka bata so duk wani da ya shafe sa. "Auta dake nake magana fa ki tashi wannan kwanciyar da kike yi kamar ruwa ba zai fishe ki ba. "Aunty Huwaila idan maganar Yayanmu ce banaso Dan Allah ki yi tafiyarki. "Mtss! Ni kam na tsani naga nama ya ja kare shin za ki tashi ne ko a'ah?" Aydah ta miƙe zaune tare da jingina bayanta ga allon gado tana ta faman ya mutsa fuska. "Auta ki natsu ki saurare abun da zan gayamiki muddin ba ki yi da gaske ba shakka babu zaman gidanan zai gaggare ki, wannan kodaddiyar mata da kike gani bala'in makira ce ba boka ba malam za ta raba ki da Yayanmu zallan kissa da makircinta za ta kashe miki aure dasu, ke kuma da yake kanki baya kawo wuta kin ƙi ki gane idan ta dosa sai uban shirme kike bugawa. "Aunty Huwaila ai akan idonki fa jiya ta shigo da tulin kayayyakin da ya siya mata, a matsayin kyautar ta musamman na budurcinta da ta kawo masa, amma ni ko me bai bani ba tun dani daman can ba ƙaunata yake yi ba kuma nayi magana cibi ya zama ƙari to ba zai yu ba matuƙar yana so zaman lafiya a gidanan dole nima ya bani nawa gift. "Aydah ki aro natsuwa ki yafawa kanki ina miki gudun kwabarki ta yi ruwa tsululu ki ɓata goma biyar bata samu ba. Ai shi yaƙi ɗan zamba ne kuma kowa ya iya allonsa ya wanke. Rumaisa a shirye take tsaf don gani ta kuntata miki ta kowace fuska, kuruciya da watau ne suka hana miki fahimtar manufarta akanki. Idan kika kwantar da hankalinki ni nan zan ɗora ki a hanyar da kema sai Yayanmu ya ba ki kyatuttuka wata kila ma naki su fi nata. Jin abin da Huwaila ta faɗa yasa Aydah gyara zama har tana haɗawa da sauke ajiyar zuciya, matuƙar Yayanmu zai siya mata nata gift to kuwa a shirye take da ta yi duk abun da Huwaila ta umarce ta. "Ina jin ki aunty Huwaila. Aydah ta faɗa cike da zumudi cikin sigar da ƙwaƙwalwar Aydah za ta fahimta nan take Huwaila take ɗora mata karatu "yanzu kalli kanki tun safe kike kwance da kayan bacci ba ki yi wanka ba amman ita ai kin ga kalar shigar da tayi to da wannan shigar za ta iya sace zuciyar Yayanmu dukka, yau da kanta ta shiga kitchen ta yi masa breakfast ke kuma bayan indomie sai ruwan tea su ne kaɗai abun da kika iya sarrafawa. Idan har kina so kema ki zama tamkar ita dole ki koyi abubuwa da ba ki iya ba. Sannan ki tashi ki yi wanka ki ci abinci idan Yayanmu ya dawo ki je ki basa hakuri idan ya haƙura zan gayamiki hanyar da za ki bi kema ya siya miki kyaututtuka. Ba ko musu balle gardama Aydah ta tashi ta shiga bathroom kamin ta fito Huwaila ta gyara mata ɗaki ta turare shi da hadaddun turaruka wuta masu bala'in ƙamshi. Tana kammalawa ta fice zuwa downstairs parlor Rumaisa dake kitchen ta fito fuskarta a gimtse ta kalli Huwaila. "Ke mai aiki zo nan. Sai da gaban Huwaila ya faɗi tsakani da Allah ta fara jin tsoron shu'umancin Rumaisa jikin a sabule ta ƙaraso gaban Rumaisa ta tsaya tare da sadda kanta ƙasa. "Gani Hajiya. "Ai na ganki munafuka kin san dai ni ba makauniya bace balle ki yi min tuni, daga ina kike sau biyu ina lekawa ɗakinki ba ki ciki?" "Ina bangaren Auta. "Kina dai can kina kimtsa mata munafuci da kinibibi to bari ki ji wallahi kina dab da bari gidanan munafuka wuce ki je ki gyara min kayan miya. Batareda da Huwaila ta tanka ba ta wuce cikin kitchen Rumaisa ta bi ta da mugun kallo tana kissima dole ta kore Huwaila daga gidanan. *LAGOS NIGERIA* (The George hotel) Aliyu na Uku ya kalli Maysun cikin natsuwarsa yana faɗin "Ki kula da kanki oum Azhar in shaa Allah ba zan daɗe ba da zarar an kammala naɗin sarautar zan dawo domin wanda na ba wa aikin bincike akan ɓata ɗan mu ina da tabbacin zan zo da min da kyakkyawan sakamako. Dauriya sosai Maysun ta ya fawa kanta tana jin ba dadi dangane da wannan tafiya da Aliyu zai yi zuwa masarautar kudu wanda dukka saura kwanaki ƙalilan an yi bikin naɗin sarautar sa shi da Ciroma, har parking lot ta rasa shi sai da taga tafiyarsa sannan ta koma ɗakin hotel ɗin da yanzu ya zama kamar nata. Daga hotel ɗin ya wuce gidansa inda ya tarar da Anaal da twins sun shirya har sun saka luggage ɗinsu a mota shi ƙarasowar sa kaɗai suke jira, dan haka yana zuwa batare da bata lokaci ba suka wuce airport, tun kamin su iso cikin masaurata har labarin zuwan Aliyu na Uku ya je kunne su Ciroma wanda har yau bai sami wata makama da zai rusa Aliyu na Uku da ita ba gashi Galadima ya sako shi a gaba shi fa lallai-lallai so yake ayi ta, ta ƙare ya cika masa alƙawari da ya ɗauka masa ga baki ɗaya Galadima ya hana masa sakatt, da dukkan alama Galadima yana so ya zame masa ƙarfen ƙafa. Tun zuwan su Anaal masarauta ta ƙunshe kanta a ɗaki Safiya ta lura da yadda 'yarta ta dawo mata cikin damuwa don ba haka ta saba dawowa mata ba sai dai bata sami cikakken lokaci ta zauna da ita ba saboda, tana fama da kula da Aliyu tun sanda ya dawo tana ɓangaren sa duk da babu wata hira da ke shiga tsakanin su, hatta da abinci da ta ɓata dogon lokaci ta girka masa kaɗan ya tsukura yace ya koshi, sai dai a wannan karon taga canji na saki fuska a wurinsa sabani yadda ya saba haɗe mata fuska. Sai wuraren bayan la'asar Aliyu na Uku ya fita zuwa bangaren mai babban ɗaki sai a lokacin Safiya ta sami damar shiga ɗakin Anaal a lokacin Anaal tana zaune a gefen gado da laptop akan lap ɗinta, tana wani binciken sirri da tasa kanta tsawon kwanaki kenan da ta fara wannan bincike, sai yau ta kawo karshen sa kuma abun da take zargi ne yake neman tabbata,shiru tayi tana kallon hoton da ke kan screen ɗin laptop ɗin bata yi mamaki ba ko kadan da sakamakon bincike nata domin ta daɗe tana zargin hakan amman domin tabbatar wa tare da cire kokwanto dole tayi wata tafiyar sirri. Turo kofar ɗakinta da ummie tayi yasa ta sauri rufe laptop ɗin, ta kakkalo murmushin dole ta yafawa fuskarta. Kusa da ita ummie ta nema ta zauna "Barka da warhaka ummie! "Barka Anaal halan bakya ji daɗi ne?" "Me kika gani ne ummie? "Naga tun da ku ka iso kike ƙunshe a ɗaki ga kuma damuwa akan fuskarki ko akwai wata matsala ne tsakaninki da Abbun ki?" "Gajiya ce kurum ummie sai migraine headache da nake ji sama-sama na kuma sha magani in shaa Allah zuwa anjima zan wartsake. "Anaal ki dinga sassautawa kanki wannan aikin wahala da kika daukawa kanki kina mace amma ace kullum ba ki da hutu, Allah ya sanar min Anaal na gaji da ganinki haka ya kamata ki yi wa kanki faɗa ki fara tunani gina rayuwarki ke fa ta mace ce rayuwarki gajeriya ce, gara ki yi aurenki tun kina da taguwar kuruciyarki. Ki daina biyewa mahaifinki domin na fahimci rashin aurenki ba damun sa ya yi ba. Wani gwaron numfashi Anaal ta sauke,tana jin tausayin kanta da na mahaifiyarta yana kamata domin tasan da zarar Abbu yaga ɗansa gwamnatinta zai rushe ne a wurinsa zai tattara duk wasu harkokinsa ya ɗora ɗansa akai daman can rashinsa ne yasa ya dora ta a harkokin kasuwancin sa, don haka za ta bi kowacce irin hanya ce domin ta hana sa ganinsa ko.... "Anaalll!!! Ummie ta kira sunanta da ɗan ƙarfi tana girgiza kafaɗarta firgigit Anaal tayi tare da dawowa dukkan natsuwarta yadda ummie ta tsare ta da idanuwanta yasa duk tabi ta ruɗe ta shiga kame-kame "Anaal kina da wata uwa ce da tafi ni da ba za ki gaya damuwarki ba?" "Ba haka bane ummie akwai wasu documents na yarjejeniyar kulla kasuwanci da Abbu ya bani na ajiye masa tun muna lagos nemi su na rasa kwata-kwata na manta da inda na ajiye su to shi ne jiya ya tambaya ni kuma na rasa amsar da zan basa banaso yaga sakacina ummie shi ne nake so ki bani dama batare da yasani ba gobe na tafi Kano na gana da CEO na kamfanin mu sake rubutu wasu. Ajiyar zuciya ummie ta sauke tare da dafa kafaɗar Anaal cikin sanyayyar muryata ta ce "Idan wannan ne babu matsala Anaal sai ki shirya ɗin gobe ki tafi amman in yaso sai ki sauka a gidan yaya Zeenah, banaso ki sauka a hotel tun da kina da gun da za ki zauna. Wani irin farin ciki ne mai cike da natsuwa ya saukarwa da Anaal rungume ummie tana hamdallah aranta yadda plan ɗinta yake tafiya yadda ta tsara. Hankali tashe Ciroma ya nufi gidan gonarsa inda Galadima yake zaman jiransa har ga Allah ya fara gajiya da halin nacin Galadima mutum sai kace ya haɗe tsatso da mayyu, tun daga sanda ya ji labarin isowar Aliyu na Uku masarauta ya bi ya tashi hankalinsa ya kuma tashe na Ciroma, sai buge-buge waya yake masa "ko uban me zan masa a yanzu da yai kirana izuwa nan, kwata-kwata Galadima bashi da haƙuri gashi da shegiyar zalama da gaggawar tsiya mtss! Me za a yi da mutum mai hali irin na Galadima. Ciroma ya faɗa cike da mita da zallan takaicin taso shi da Galadima ya yi adaidai lokaci da yake ganiyar hutawa. A fusace Ciroma ya isa wurin da suka sabawa haduwa da Galadima tun kamin ya ƙarasa ya hango Galadima sai safa da marwa yake yi da hannayensa naɗe a bayansa ya kasa zaune ya kasa tsaye wuri ɗaya shi fa da son samu ne kada jibi a naɗa Aliyu na Uku sarkin sabon birnin kudu, burinsa ace shi ne za a naɗa don haka ya bi ya tashe hankalinsa gani yake yi da zarar an naɗa Aliyu na Uku shi kenan ganyensa ya kaɗe da babu sauran wani abu da Ciroma zai masa. Har Ciroma ya zauna Galadima yana kai da komu wani mugun kallo Ciroma ya wurga masa yana faɗin "To ai sai ka nemi wuri ka zauna don kuwa wannan shawagi da kake yi ba zai rage ka da komai ba. A fusace Galadima ya fincike kujera ya zauna yana wani irin huci "Tura ta kai bango Ciroma haƙurina yana dab da ƙarewa ya kamata kasan yarda za ka yi dani domin idan haƙurin nawa ya je ƙarshe daga ni har kai za mu ji jiki. "Mtss! Kana bani mamaki Galadima kai a rayuwarka kwata-kwata bada haƙuri. "Ban san shi ba kalma ɗaya nake fahimta a halin yanzu ka bani tabbacin a bisa faruwar muradina. Wani malalacin kallo Ciroma yake wa Galadima kamin ya fito da goro daga gaban alhun babbar rigarsa ya kai bakinsa ya gutsara kana ya miƙe tsaye yana faɗin. "Na fahimci so kake yi mu ɓata goma biyar bata gyaru ba to kasani wannan kasassabar bada ni ba idan lokacin cikar muradina ya yi ni kaina zan zantar da haka, ina kuma gargadinka da babbar murya kada ka aiwatar da komai sai tare da izinina. Ciroma yana ƙarashe magana ya yi tafiyarsa yabar Galadima yana cizan yatsa shi da ya gaji da gafara sa bai ga ƙaho ba. *WASHEGARI* Gaba ɗaya masarauta ta kacame da shirye-shirye nadin sarakuna biyu, an painting ciki da wajen masarauta yayin da wasu abubuwa sababbin aka saka. Mutane da dama kansu ya daure matuka a dalilin yadda suka ga Aliyu na Uku yana farin ciki, sannan kuma tare dashi ake shirya yarda bikin nadin nasu zai ƙayatar. Da misalin ƙarfe goma daidai Anaal ta fito cikin shirinta na tafiya Kano, ummie ce kaɗai tasan da tafiyar ta, ta yayin da ummie ta dinga gargadinta da kada ta wuce gobe saboda jibi ne nadin sarautar Abbu. Da gwarin gwiwa cikar muradinta ta ja motarta ta baro masarauta ta daukin hanyar Kano zuciyarta cike da buruka kala daban-daban. Kilishi zaune a ɗakinta tare da amintacciyar jakadiyarta cikin lokaci kaɗan Kilishi ta zabge tayi wata mummunan rama, babban kuskure da za ta tafka a rayuwarta ta bar Ciroma ya hau karagar mulkin kudu idan har hakan ya tabbata, abubuwa da dama za su faru ba kuma masu daɗi ba dole tayi bi kowacce irin hanya ce domin gani ta hana faruwar naɗin sa da za a yi jibi amman ta yaya?" Tambayar da ta kasa nemo amsar ta shi ne ta nemi amintacciyar jakadiyarta ko za ta iya lallaɓo mata mafita. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. [1/29, 1:07 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 085. AB yana fitowa daga meeting da board members kiran Anaal Aliyu na Uku ya shigo wayarsa bai yi picking ba sai da ya isa ofishin sa ya zauna akan ɗaya daga cikin kujera da suka ƙawata ofishin nasa, yana mamakin kira me CEO Kim's Automobile ke masa yasan babu wani dalili da zai sa ta nemi shi a daidai wannan lokaci. Kamin ya kirata, ta sake kiransa ya yi picking tare da sallama a ɓangaren Anaal a natse ta amsa masa tamkar babu wata damuwa a tattare da ita. "Barka da warhaka mr Abba Bashir. "Barka mss Anaal. "Na kira ne domin mu warware wata 'yar matsala da ta kunno kai dangane da partnership ɗinmu. "Subhanalillah! Matsala kuma? Wacce irin matsala mss Anaal iya sanina mu riga da kowanne bangarori ya amince da tsarin da kowanne mu ya kawo, to wacce matsala ce za ta biyo baya?" "Ka kwantar da hankalinka mr Abba domin mu warware wannan matsala yanzu haka ina kan hanyar Kano ka yi min addu'a isowa lafiya. "Whats! Kina kan hanyar Kano fa?" Amman ya kamata mu fara tattaunawa wannan matsalar a waya kamin mu hadu da fari ma sai kin nemi amincewata kafin mu yi zama irin wannan. "Ka yi haƙuri mr Abba banida lokaci ne gani irin muhimmanci da tattaunawar ta mu take da yasa ban tsaya neman izinika ka ba na taho. "Shi kenan Allah ya kawo ki lafiya idan kin iso ki kira ni. Daga haka ya yi hanging up, secretary ɗinsa Skyler ce ta shigo hannunta ɗauke da wasu files ta ajiye akan desk ɗinsa "sir ga files ɗin da ka buƙaci na kawo maka daga cikinsu akwai file ɗin kamfanin three stars automobile suna buƙatar sa hannunka. "Shi kenan zan duba. Ya faɗa a takaice secretary Skyler ta juya ta fice bata daɗe da fita ba sai ga Abdulkarim ya shigo hannunsa riƙe da waɗansu files,sallamarsa ya saka Ab buɗe idanunsa saboda tun fitowarsa gida yake fama da ɓacin rai akan abun da Aydah tai masa a duk sanda ya tuna sai ya ji wani sabon samfurin haushinta ya kama shi. "Ango na Rumaisa da baby Aydah ya naganka sukuku da kai ko duk gajiya ce?"Gashi kuwa zuwa nan da nayi fita za mu yi akan wancan issue ɗin gara ayi komai a yau ɗinan mu karbi kuɗin mu a wuce wuri. Abdulkarim ya ƙarashe magana yana miƙawa AB hannu suka yi musabaha kamin ya nemi kusa dashi ya zauna kana ya jefa files ɗin hannunsa akan mini center table da ke kusa dashi. AB ya sauke numfashi tare da kallon Abdulkarim "Bari kawai Abdulkarim yau baby Aydah ta charger min battery ɗina, tun safe nake fama da ɓacin ranta. "Subhanalillah! Me ta yi maka?" Dan Allah ka dinga haƙuri kasan akwai ɗanyar kuruciyar a tare da ita. "Uhm! AB ya faɗa tare da furzar da iska daga bakinsa kamin ya rattabo wa Abdulkarim labarin abun da ya faru. "Gaskiya abokina ba ka kyauta ba yanzu ɗan wannan abun har ya kai matsayin ayi mari akansa?"Miyasa sanda Rumaisa ta dinga dura maka men power miyasa ita ba ka dake ta ba ka ce kuskure ne ko don ita baby Aydah ba ka sonta auren dole aka yi maka da ita?" "Ka ga Ak kada ka yi min mummunan fassara da Aydah da Rumaisa duk ɗaya suke a wurina.... "Ƙarya ka ke yi Abba Bashir da duk ɗaya suke a wurinka da ba za ka dauki Rumaisa ka kaita shopping ka kashe mata makudan kudade ita kaɗai dole ka haɗa da baby Aydah domin ita ma matarka ce ta sunnah yadda Rumaisa ta kawo maka virginity ɗinta haka zalika ita ma baby Aydah ta kawo ma wannan nuna bambanci ne da rashin adalci murara kuma sai Allah ya tambaye ka. "Ya salam! Abdulkarim please ka fahimci zancena da idon basira mana na gayamaka ba a bisa radin kaina na kai Rumaisah shopping ba ita ce ta buƙaci hakan, da ita ma baby ta buƙaci hakan ba abun da zai hanani kaita amman sai ta hau ni da rashin kunya sai kace wani sa'anta. "Ba rashin kunya bane Ab ta ji kishin yadda ka bambanta ta Rumaisa ne ko kaine a matsayinta za ka ji ba daɗi, dan Allah ka dinga bin Aydah a hankali ka fi kowa sani har yanzu ita ɗin yarinya ce ƙarama da ba za ta iya tantance waɗansu abubuwa ba. AB ya yi ajiyar zuciya shi kanshi daga baya ya ji babu daɗin marinta da ya yi yarinyar da zai saɓawa da kowa akanta, amman yau shi da kansa ya mare fuskarta. "Shi kenan na ji nayi kuskure in shaa Allah zan kiyaye gaba ita ma zan ɗauke ta na kaita shopping ɗin. "To ko kai fa. Abdulkarim ya faɗa yana dariya kana ya dauko zance da ya kawo sa da yake suna business ɗinsu a gefe shi da AB suna saye da sayarwa na filaye kana suna gina gidaje da plaza sai su sayar kuma su bada haya yanzu ma wani plaza ne da suka kammala gininsa a kwananan wani ke so siya shi ne ya zo su je a ƙarasa magana. AB ya ɗauki wayoyinsa da car key ɗinsa suka fice. Rumaisah ta shirya wa AB lunch mai rai da lafiya, tana kammala arranging table ta wuce ɗakinta lokacin da ta je wanka taga yadda jini ya sake dawowa bayan da ɗazu da taga ya ɗauke har tana murna yanzu za ta yi wanka tsarki sai gashi kuma yanzu ya dawo cikin tsanani tashin hankali ta zube guiwayoyinta akan tiles ɗin bathroom ta fashe da matsanancin kuka, wani irin baƙin ciki take ji yana ratsa mata zuciya don tasan da matuƙar wahala Ab bai je wa Aydah ba saboda tasan halinsa da rashin haƙuri wannan wacce irin masifa ce ta saukar mata a daidai lokacin da take ganiyar cin amarcinta. Adaddafe tayi wanka ta fito koda ta shiga bathroom taci burin idan ta fito za ta tsala kwalliya da za ta gigita AB amman dawowa bleeding ɗin duk sai ta ji komai ya fice mata arai, tana fitowa turare kaɗai ta shafa ta zura plain gown material ta ɗauki wayarta, ta kira Ammie cikin muryar kuka ta zayyana wa Ammie halin da take ciki. Shiru Ammie ta yi na ɗan wani takaitaccen lokaci kamin ta ce ta jira za ta kira ta. After thirty minutes sai ga Ammie ta kira ta, ta ce ta kira Ab ta faɗa masa za ta zo gida akwai likita da zai dubata. Rumaisa ta kira Ab ta faɗa masa da fari sai da ya rufe ta da faɗa yana faɗar ba sun je taga Dr Sameer matawalle ba ya kuma rubuta mata magani tun bata kammala shan maganin da ya rubuta mata ba, za ta je ganin wani likita shi fa bayaso haka. Da kyar ta rarrashe shi ya amince ta ce ya dawo gida ya yi lunch tayi masa girki na musamman, agaggauce ta canza kayan jikinta ta ɗauki car key da wayoyinta ta fice, Huwaila tana ganin fitar ta ta nufi ɗakin Aydah, kamar tasan AB zai dawo gida ta cilasta wa Aydah yi wanka ta shirya ta cikin wani tsadadden lace coffee color style ɗin skirt and blouse. Suka fito downstairs parlor Huwaila ta kunna musu kayan kallo, suna cikin kallo suka jiyo horn ɗin AB da sauri Huwaila ta kalli Aydah tana faɗin "Auta ki saurare ni da kyau tun da wannan kodaddiyar ta fita ga kuma Yayanmu ya dawo wannan shi ne lokaci mafi dacewa da za ki daidaita tsakaninki da mijinki, ki basa hakuri ki nuna masa kin yi kuskure ba za ki ƙara ba kin jin ni da kyau?" Aydah ta ɓata fuska tana cuno baki gaba "Aunty Huwaila mari na fa ya yi. "To don ya mare ki ba za ki iya yafe masa ba? Wai ni kam Aydah ko kin daina son Yayanmu ne?" "Ina sonsa sosai amman ba zan taɓa lamunta ya dinga danne min haqqena. "Kai Auta Ni kam yaushe kika koyi mita ne?" Kamin Aydah ta bata amsa Ab ya tura kofar main parlor ya shigo da sallama Huwaila ce ta amsa masa tare da yi masa barka da dawowa kallo guda Aydah tai masa ta kauda fuska, shi kuma ga baki ɗaya hankalinsa yana kanta don ba ƙaramin kyau tai masa ba, ji yadda yaga tana cin magani yasa shi saki murmushin gefen baki. Huwaila ta juya ta nufi ɗakinta, ta bar musu parlon. "Barka da dawowa! Aydah ta faɗa adakile kamar mai ciwon hakori. "Yawwa sarkin fushi da dai kin saki fuskar don wannan ɗaure fuska da kike yi ko kaɗan baya miki kyau asalima ya ɓata miki kwalliya da kin saki fuskar da wata kila mu je shopping. Murmushi Aydah ta yi tare da nufar wurinsa cikin sigar shagwaɓa ta ce "Na saki fuska Yayanmu har dariya ma zan maka. "Saboda kin ji zance shopping ko? To na fasa tun da dariya bata Allah da Annabi bace. Batasan sanda ta riƙe masa hannu ta marairaice murya tana faɗin "Ka yi haƙuri dan Allah ba zan sake ɓata maka rai ba. "Shi kenan mu je ki bani abinci idan nayi wanka na huta sai mu fita ɗin saboda nasan halin nacinki muddin ba shopping ɗinan na kai ki ba, ba zan sake gane kanki ba. Zuciyar Aydah tayi fari tass suka jera zuwa dinning room yana faɗin "kin yi matuƙar kyau cikin lace ɗinan baby ki dinga saka color ɗin ya karɓi jikinki sosai. Cikin shagwaɓaɓbiyar muryarta ta furta. "Thank you mi amor! Ta kama kujera ta ja masa ya zauna sai da ya zauna kana ya kalleta yana faɗin "me na ji kin ce?" "Cewa nayi nagode! "No bayan kalmar godiya ɗin na ji kin ambaci wani suna. Dariya Aydah ta yi tare da ajiye masa plate ɗin sa ta yi masa serving a gabansa. "Oh! Wai mi amor?" "Eh! Shi ɗin me hakan ke nufi?" Da sauri ya rufe fuskarta da tafukan hannayenta tana dariya ƙasa-ƙasa ta bar cikin dinning ɗin da kallo ya bita yana murmushi yayin da yake maimata sunan acikin zuciyarsa, yana so yasan me kalmar ke nufi, Aydah tana gani ya wuce ɗakinsa ta nufi parlornsa dake sama ta kasa ta tsare tun kamin ya ƙaraso cikin parlor ta fara shaƙar ƙamshin turarensa, ya fito sanye cikin filtex material milk colour ya saka hula zanna bukar da ta dace da kayan jikin nasa ƙafafunsa sanye cikin sandal shi ma milk in colour, ya kalli Aydah yana murmushi "Wannan tsarewa duk ta mene ne?" Ya yi magana yana daidaita zaman hular kansa. "Yayanmu ba ka ce za mu je shopping ba?" "Cewa nayi sai na huta. Ya yi magana yana zaunawa kusa da ita ya mutsa fuska ta yi tamkar za ta rushe masa da kuka "Dan Allah yayanmu. Ta karasa magana tana haɗe hannayenta. "Okay! Tashi mu tafi Ya yi maganar yana dugure mata goshi already ta dauko veil ɗinta, da takalminta a ƙafafunta sai wayarta dake riƙe da hannunta, tare suka sauko ƙasa "Yayanmu bara na leƙa ɗakin aunty Huwaila na faɗa mata mun fita ta kula da gida. "Shi kenan ki yi sauri ina jiranki a mota. Aydah tana zuwa ta rungume Huwaila tana tsalle murna dariya Huwaila ta yi tare da ciro ta daga jikinta tana faɗin "wannan farin cikin fa?" "Aunty Huwaila shopping za mu je ni da Yayanmu nima zan rama wulaƙanci da aunty Rumaisa tayi min. Aydah ta faɗa cike da zallan wauta da kuruciya tura ta waje Huwaila ta yi tana faɗin "je ki in kin dawo za mu yi celebration. Da dan gudun ta ta fice, har ta buɗe mota ta zauna Ab yana waya da ta baza kunne sai ta fahimci da mace ne yake magana musamman da ta ji ya kama suna. "Mss Anaal ashe har kin iso. Sai ya yi jim yana sauraren abun da Anaal ɗin take faɗa. "Okay! A bon hotel kika sauka? To meyasa kika kama masauki batareda da kin jira ni ba kika sani ko na tanadar miki da masaukinki ko kin manta lokacin da na je Lagos kin ce min accommodation ɗina yana kanku? Ya yi shiru kafin kuma ya yi dariya "Yanzu dai gani tare da madam za mu fita unguwa idan na dawo koda zuwa bayan ishaa ne zan zo mu tattauna ɗin. Yana ƙarasa magana tare da ajiye wayar akan dashboard kana ya maida ganinsa akan Aydah wacce ta yi kici-kici kishi ya bayyana ƙarara akan fuskarta. "Business partner ɗina ce ba budurwa ta ba. AB ya faɗa yana yiwa mota key. Turo baki Aydah ta yi tare da furta "To ai ban yi ƙorafi ba. "Nima ban ce kin yi korafi ba amman kin ɓata fuska. "To meye don na ɓata fuska naga dai fuskar ma marinta kake yi. "Baby kodai na tsaya a gefen titi ki rama marenki?" Zaro idanuwa ta yi tana kama bakinta. "Ai gara ki rama marenki baby kamar zai fi min sauki da ki dinga tuna min dashi. "Na rama fa ka ce?" "En mana! "Uhm! Wato Yayanmu so kake a saka ni wutar jahannama ko?" Dariya Ab ya yi sai da ya yi mai isarsa kamin ya ce "Ashe Babyn yaya Abba ta fara hankali. "Daman can da hankalina. Da haka suka iso ado bayero mall Aydah sai murna take yi ta dinga jidar kaya kamar za ta buɗe ɗan ƙaramin shop shi dai AB sai Kallonta yake yi yana murmushi, sai da ta gaji don kanta sannan ta ce iya abubuwan da take buƙata kenan. Suka je ya biya kuɗi aka zuba musu kayan a mota, kallonta ya ce "Yanzu sai mu wuce shagon waya ko? Girgiza kai Aydah ta yi tana turo baki "Ni banaso waya. "To me kike so?" "Mota nake so Yayanmu ka tuna ka yi min alƙawari since yanzu ne right time da za ka cika. "Baby cewa nayi sai kin kammala secondary school idan kika fara zuwa high school sannan zan ba ki mota. "Dan Allah Yayanmu ka bani yanzu ko ba zan fara driving ba zan so na dinga ganinta a parking lot a matsayin tawa. "Na ce ba yanzu ba. Ya faɗa yana tamƙe fuska cigaba da yi masa magiya ta yi har sai da ta haɗa da kuka kamin ya amince. "Shi kenan na ji zan ba ki ɗin sai ki shafa min lafiya. Amman ba yau ba sai dai gobe saboda yau. Ihun farin ciki Aydah tasa tare da rungume Ab ta da sauri ya saka signal ya gangara gefen titi ya yi parking. "Ke kin yi hauka ne da za ki yi min wannan wawan runguma salon na ɓarar da damu. Sumbatar kumatunsa ta yi "ina sonka ina sonka Yayanmu! Aydah ta faɗa very excited, tura mata bakinsa ya yi "anan za ki nuna farin cikinki ba a kumatuna ba. Ga mamakinsa sai gani ya yi ta zagaye hannayenta a wuyansa ta yi connecting lips ɗinsu wani kalar sucking lips ɗinsa take yi ga baki ɗaya AB ya gigice yana neman fita daga hayyacinsa ƙara shigar da ita jikinsa ya yi. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. [1/29, 1:07 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 086. Sun ɗauki lokaci suna ya mutsa junansu da kyar ya iya kyaleta ya koma jikin kujerar mota ya lafe sai wani wahalalle numfashi yake saukewa yayin da Aydah take kici-kici maida zip ɗin rigarta da zugesa ya janye hannayenta ya maida zip ɗin ya rufe mata sai da ya sakar mata kiss a wuya kamin ya tada mota "Baby na tambaye ki mana?" "Uhm! Aydah ta faɗa batareda da ta kallesa ba batasan meyasa a duk sanda irin haka ta faru a tsakaninta da yayanta take jin kunyar haɗa ido dashi. "Dinkin da aka yi miki ya warke ko?" Girgiza kai ta yi cikin sarƙewar lafazi ta furta "Da saura Yayanmu doctor ma ta ce idan na cika One week na koma za ta duba dinkin idan ya yi healing. Numfashi ya sauke tare da jin tausayinsa kansa ga shi da mata har guda biyu sai dai babu wacce daren yau zai more ta. Yana sauke Aydah ƙofar gida ya wuce masallaci ya yi sallah magarib da ishaa sannan ya nufi hotel ɗin da Anaal na uku ta sauka, restaurant ɗin da ke cikin hotel ɗin ya nufa a bangaren vip ya nemi wuri ya zauna sannan ya kira Anaal ya faɗa mata inda za ta same shi. Anaal ta tashi da sauri jikinta har rawa yake yi a can kasan zuciyata tana jin tsoro haɗe da shakku akan abun da take shirin aikatawa, har ta ji kamar ta fasa sai kuma tuna da girman al'amari da yake shirin tunkaro ta. Da sauri ta ɗauki wayoyinta tare da wani brown envelope cike da kuzari da kwarin gwiwa ta fice,har ta isa vip ɗin tana jin wasi-wasi a zuciyata. A hankali AB ya sauke idanunsa akanta tana sanye da Abaya dark green ta yi rolling da mayafin rigar abin ka da farar fata cikin green colour sai tayi bala'in kyau, gabansa ne ya yi wani irin bugawa wani abu yake ji mai wahalar fassara wa yana bin jini da ɓargon jikinsa, kasa ɗauke idonsa akanta ya yi har ta zo ta zauna ta sakar masa murmushi shi ma ya mayar mata da martanin murmushin nata. Murmushinsa yai masifar faɗar mata da gaba ta zauna a kujerar dake facing ɗinsa yayin da gabanta ke cigaba da dokawa, a kasan zuciyata tana ji rashin dacewar abun da take niyar aikatawa to amman wani sashe na zuciyata yana daɗa karfafa mata gwiwa da ta yi ɗin matsoraci baya taɓa zama gwani da wannan kwarin gwiwa da ta samu daga daga dayan bangare zuciyarta ta saita natsuwarta wuri ɗaya ta fuskance shi da kyau cike da jarumta ta gaishesa tare da tambayarsa iyalinsa duk yana amsa mata da alhamdullah! "Mr Abba na zo ne domin dangane da partnership ɗin dake tsakanin kamfanonin mu, a kwanaki huɗu da suka gabata mahaifina ya kira ni ya nuna min ayi cancel ɗin wannan yarjejeniya. Na nemi nasan dalilinsa na so yi hakan amman sai ya nuna min nayi abun da ya umarci ni shiyasa na zo da kaina na kawo maka waɗannan takardun ka sanya hannu. "Amman dai wasa kike yi ko?" AB ya faɗa da dimbin mamaki akan fuskarsa don shi bai taɓa ji irin wannan tatsuniya ba, idan har kamfaninsu yana so ya yi cancelling ɗin partnership kamata ya yi su zo tare da wasu daga cikin board members ɗinsu a haɗu da nasu kana sai su kawo hujjojin su da suka sa suke so cancel ɗin partnership ɗin, saboda tun asali gamayyar kamfani ne ya haɗa su dake Germany. Anaal ta kara gyaran zamanta tare da tattaro natsuwata wurin ɗaya "mr Abba babu zance wasa aciki da wasa nake yi me zai sa na wanko ƙafa na zo garin kano? "Idan ba wasa kike yi ba to ki sani kin zo min da raini hankali,kamin kula kowanne yarjejeniya akwai sharuddan da ake gindayawa domin gujewa zamba cikin aminci da dai sauransu, wanda hakan yasa dole acikin daya daga cikin gamayyar kamfanoni za a zaɓi ɗaya daga cikinsu a zantar da wannan harkala me yasa ba ki nemi mu hadu a Kamfanin mu kamar yadda na je na sami ku a Kamfanin ku, sai kika nuna mu haɗu a hotel?" "Wannan ba wata gamsasshiyar hujja bace mr Abba idan ka yi duba daga ni har kai muna da ƙarfin ikon zantar da hukunci ba dole sai a gaban board members ba. Tun da har kaga mahaifina yace a soke yarjejeniyar to tabbas akwai dalili mai ƙarfi don haka dan Allah kada kaga laifina ka sa hannu so nake gobe da sassafe na koma birnin kudu. "Birnin Kudu! AB ya tsinci kansa da maimata sunan yana ji wani irin matsanancin faduwar gaba, ga tsigar jikinsa da ta mimmiƙe a hankali yake ambaton Allah a zuciyarsa ji ya yi kamar zazzaɓi zai rufe sa, saboda haka batare da da ya sake magana ba ya dauki document ɗin ya dinga bin yana signing, yana kammala wa ya yi dropping pen ɗin da ƙarfi akan envelope ɗin ya miƙa jiki ba lakka. Ya juya Anaal ta bisa da kallo tana murmushi yana isa wurin motarsa kiran Rumaisa yana shigowa wayarsa sai da ya daidaita natsuwarsa kafin ya yi picking, kukan Rumaisa ya fara tsikayi har wani sheɗewa take yi "subhanalillah! Habibty mene ne me faru ya na ji kina mai kuka?" Kusan a tare ya aika mata da waɗannan jerin tambayoyi. Kafin Rumaisa ta yi magana Ammie ta karɓe wayar "Abba ka zo gida ka sami ni za mu yi magana. Daga haka Ammie ta kashe wayar, jikin Ab ya ƙara mutuwa yana tunani me kuma ya faru da mahaifiyar Rumaisa ke so ganinsa shi a tunaninsa Rumaisa ma ta koma gida. Iya hasashen sa ya kasa hasaso masa me ke faruwa?" Yana isa gidan kansa tsaye ya wuce babban parlor ɗin gida kasancewar yanzu bashida shamaki da gidan. Ya taki babbar sa'a Ammie da Rumaisa suna cikin parlor zaune kowacce da kalar damuwar dake kan fuskarta Rumaisa kam idanunta sun yi luhu-luhu ga wani uban ta gumi da ta doka. Cikin yanayi na girmamawa Ab ya gaida Ammie ta amsa masa da daurarriyar fuska. "Abba na kira ka ne domin na faɗa maka takamaiman ciwo da yake damun matarka wata kila idan ita ce ta gayamaka ba lallai bane ka yarda. Gaban Abba ya doka da karfi, kamin Ammie ta kai da gayamasa ciwo har zuciyarsa ta fara ayyana mai abubuwa barkatai. "Subhanalillah! Ammie wane irin ciwo ne Allah yasa yana da magani?" "Yana da don in shaa Allahu daga kan wannan babu ɗan la'ananna da zan ƙara bari ya jefa min 'ya an dai na farko da yarda ubangiji shi ne na ƙarshe. "Ban fahimci ki ba Ammie. AB ya faɗa cikin rawar murya. "Abba asiri ne aka yiwa Rumaisa aka sako mata zubar jini domin a rabata da kai kuma malamin da ya warware asiri ya tabbatar mana da matarka ce tai mata asiri don haka na kira ne domin na gargade ka da babbar murya idan ka koma gida ka jawa matarka kunnen ta kiyaye faɗa da batada makami, idan kuma tana ci ƙasa ta kiyaye ta shuri wallahi-azim karta sake ta kara taɓa min 'ya wannan ma na ɗaga mata ƙafa ne taci albarkacin ka, da duba da nayi da ƙarancin shekarunta wata kila ba ita ce ta yi mahaifiyarta ce. Ni uwa ce wacce bata haɗa ya'yanta da kowa ba akan yarana ba abun da ba zan iya aikatawa ba domin na kare martaba da ƙimarsu. AB was totally shock and speechless ya yi gun don bai masan me zai ce ba koda yana da abun cewa bai san daga ina zai fara ba. Tun sanda Ammie ta fara kora masa zance zuciyarsa ta yi nisan kiwo don har ta warware masa Kurman allo, don haka ya kwantar da murya ya shiga ba Ammie haƙuri tare da nuna mata komai fa muƙadarri ne daga Allah sannan kuma kada ta yarda da zancen asiri domin zato zunubi ne koda ya zama gaskiya ta guje ɗaukar maganganu malaman tsinbo domin da yawansu makaryata ne kuma haddasana masu haddasa fitina a tsakanin al'umma. Yana dasa aya Ammie ta rufe shi da faɗa har sai da Rumaisa ta taka mata birki sannan fa ta iya yi shiru AB ya sake bata haƙuri cikin kwatacciyar murya ya yi mata alkawarin daga nan zai wuce da Rumaisa Islamic chemist ya karbu mata magungunan musulunci idan ma asiri ne zai sake ta. "Babu buƙata duk wani magani da za ka karɓo mata na riga da na karbo mata ke tashi ku tafi matuƙar ina raye babu wani ɗan banza da ya isa ya wargaza miki gidan aurenki. Rumaisa ta tashi jikinta a sabule Ammie ta je ta dauko mata ledar maganinta tare da wani ruwan magani acikin madaidacin golan, ta miƙa mata tana ƙara jaddada mata ta dinga shan magani kamar yarda malamin ya ce. "Habibi da mota na, na zo. Rumaisa ta faɗa da suka iso parking lot. "Ki barta anan gobe direban Ammie ya kai miki kinsan dai ba zan bar ki ki yi driving da dare nan ba. Rumaisa ta buɗe motarsa ta shiga da suka zo bakin gate ta miƙawa maigadi key ɗin motarta ta faɗa masa ya kai wa Ammie za ta kirata a waya. Akan hanya Ab sai faman rarrashin Rumaisa yake yi tare da kwantar mata da hankali ta hanyar daddaɗan maganganu koda suka iso gida kaso damuwarta ya ragu da kaso saba'in cikin ɗari, main parlor babu kowa sai tulin shopping bags ɗin Aydah wanda da gangan ta zube su anan so take idan Rumaisa ta dawo ta gani, ai kuwa ta gani ɗin nan da nan ta haɗe fuska ta kalli AB wanda shi kwata-kwata bai lura da bags ɗin ba ya haura sama rai ɓace ta bi shi da fari ta so tai masa magana sai kuma ta yi wani gajeren tunani sai kawai ta wuce ɗakinta Aydah da Huwaila dake laɓe a jikin kofar ɗakin Huwaila suka kalle juna suka kece da dariya har suna kashewa daman suna jin shigowar motar AB Huwaila ta tashi da sauri ta leƙa window taga sun dawo tare, ta kwaso da gudu ta faɗawa Aydah shi ne suka baza bags ɗin. Kuma haƙarsu ta cimma ruwa don sun ga reaction ɗin Rumaisa da sauri suka fito daga maɓoyarsu suka tattare kayayyakin suka kai ɗakin Aydah. Bayan Ab ya yi wanka ya sauko ƙasa yaci abinci ya koma ɗakinsa babu wacce cikinsu ya nema kasancewar yana cikin damuwa ga cancelling partnership ɗinan da Anaal ta zo masa dashi ga kuma damuwar halin da Sadiya ta jefa Rumaisa yana jin tsoro ta sake aikata mummunan abu akan ɗaya daga cikin matansa, da farko yaso ya bar magana a matsayin sirri yanzu kuma yana gani dacewar ya gargadi Sadiya ya kuma nuna mata yasan abun da suka aikata masa idan hakan ta sake faruwa matakin da zai dauka ba zai mata kyau ba. Da wannan tunanin ya yi bacci washegari da wuri ya fice zuwa office saboda akwai sababbin motocin su da suka iso jiya da dare hatta da breakfast a office ya yi, daga Rumaisa har Aydah ba wacce tasan sanda ya fita sai a waya Rumaisa ta kira sa ya faɗa mata uzurinsa ta ce za ta yi masa lunch ya aiko direban kamfani ya karɓa masa. Aydah tana zaune a main parlor Rumaisah ta sauko cikin shigar English wears wani mugun kallo ta wurga wa Aydah ta yi ƙwafa ta shige kitchen, koda karfi ɗaya ta buga Rumaisa ta kammala girkin ta, ta zuzzuba a luxury warmers koda ta fito daga kitchen Aydah ta bar cikin parlor ɗakinta ta wuce ta sake yin wanka. Aydah tana kammala sallar azhar ta ɗauki wayarta ta kira Ab bai ɗaga ba bayan 'yan mintuna ya kirata back. "Good afternoon mi amor yau fitar safe aka yi ba ko sallama. "Afuwan ƙanwata fitar uzila ce ta kamani sababbin motocin mu ne suka iso dole na kasance a kamfani yau ba zan dawo da wuri ba, amman zan ba wa Rabi'u sakonki ya kawo miki Allah yasa zaɓina ya burge ki. "Saƙona kuma wane irin saƙo Yayanmu?" "Za ki gani idan Rabi'u ya kawo miki amman ki tanadi tukuici da za ki bani. Dariya tayi tana ƙara dafe wayar "idan wannan ne bakada matsala Yayanmu. "Haka nake so ji Babyn yaya Abba ni nasan ƙanwata jaruma ce. Fira suka yi sosai daga bisani ya kashe wayar. Yana gama waya da Aydah kiran Rumaisa yana shigowa "Habibi da wa kake waya tun ɗazu ina kiranka sai layinka busy?" "Kin kammala abinci ne na aiko Rabi'u?" Ya shashantar da tambayarta. "Eh! Na kammala shi ne ma dalilin kira da nake maka. "Nagode my love hope kin sha maganinki?" "Na sha Habibi kaima kasan ba zan yi wasa ba. "Haka ne ga Rabi'u nan zuwa da sako zai kawo sai ki basa abinci. "Okay! Take care I love you. "I love you too my sugary. Yayin magana tare da kashe wayar sosai sunan sugary ɗin da ya kira ta dashi ya yi mata daɗi ta tashi ta je kitchen ta dauko katon food basket ɗinta ta aje a parlor after like twenty minutes sai ga Rabi'u ya shigo gidan cikin wata tsalelliyar mota 'yar ƙarama irin ta mata maroon colour sabuwar dal cikin ledarta sai painting ta yana sheƙe da ɗaukar ido acikin rana, gashi an yi mata decorative da ballons different colours hatta da key ɗinta sai da aka yi decorative ɗinsa. Sai dab da entrance Rabi'u ya yi parking ɗinta ya fito ya nufi ƙofa ya danna door bell babu jimawa Rumaisa ta buɗe ƙofa hannunta ɗauke da food basket karaf idanunta suka sauka akan mota ɗin, wani kalar zaro idanuwa ta yi ga baki ɗaya kyawon motar ya tafi da imaninta, cikin kidimewa da gigicewa ta miƙawa Rabi'u basket ɗin ta nufi wurin mota ɗin ta buɗe ta shiga ta maida ƙofa ta rufe yayin da Rabi'u ya bi ta da kallo saboda shi yasan ba ita aka ce ya kawowa mota ba. AB ya kira Aydah ya ce ta je compound Rabi'u zai bata sako idan ta gani ta kira sa cike da zumudi ta sako hijab ɗinta ta fice tana buɗe ƙofa ta yi tozali da mota favorite colour ɗinta. Wani irin shock ta ji ya kamata sai da numfashinta ya ɗauke na wani dan lokaci sai kuma ta buga ihu very excited Rabi'u yana dariya ya miƙa mata key da gudu ta nufi motar yayin da Rumaisa ta yi nisa a begen motar da bana taba batasan kalar waina da ake toyawa ba da gudu Aydah ta nufi sabuwar motarta cikin zumudi ta buɗe ƙofa sai ta yi turuss! Sakamakon gani Rumaisa zaune a driving seat ta ƙanƙame steering wheel. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. [1/30, 1:26 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 087. Rabi'u tsaye yayi yana kallon matan na mai gidansa,wani irin mummunan bugawa ƙirjin Rumaisah yayi ganin car key a hannun Aydah tana jujjuyasa tana Murmushi, wasu irin yawu Rumaisah ta haɗe masu ɗacin gaske kenan da sunan Aydah aka siya motar?"lallai namiji munafuki ne. Shi ne zai ba wa Aydah mota ita ɗaya banda ita me yake nufi da haka?" Fitowa tayi daga motar tana yiwa Aydah wani mugun kallo kafin ta juya da sauri Aydah ta karaso gabanta tana sakin wani irin murmushi tana juya ido tana faɗin. "Aunty Rumaisah kinga motar da yayanmu ya bani a matsayin gift na budurcina dan Allah ki tayani godiya tayi kyau ko Aunty?" Da wani irin nauyi zuciya Rumaisah ta koma cikin parlor ranta yana mata ƙona shi dai Rabi'u lallabawa yayi yabar gidan batareda yayi masu sallama ba. Yana ta mamaki a kasan ransa meyasa mai gidansa yayi haka?"zai ba Aydah mota bai ba wa Rumaisa ba wannan ai babu adalci ko kaɗan gaskiya idan akayi duba ma da Rumaisa tafi zama cikakkiyyar macce bisa ga Aydah to ko don yana gani Aydah 'yar uwarsa ce ko kaɗan Rabi'u bai ji daɗin abun da maigidansa Abba Bashir yayi ba. Da ihu Aydah ta shigo cikin parlor tana kwalawa Huwaila kira, ita ma Huwaila a rikice ta fito da wani irin murna Aydah ta shiga jan hannun Huwaila bata saki hannun ba sai agaban motar da aka kawo mata. Huwaila ta zaro ido cikin rawar baki take faɗin."ki kara yimin bayani Auta. "Yayanmu ya aiko min dashi. Wani kalar zaro ido Huwaila tayi ta riƙe hanci ta saki wata irin guda "shiga Aunty Huwaila mu duba. Aydah ta faɗa tana buɗe mata frontseat da sauri Huwaila ta shige tana sakin dariyar farin ciki Ita ma Aydah gaban motar ta shige, ya kamata na dauko wayata kiyi min hotuna harda ma motar na turawa yaya Siyam da yaya Sadiya har ma da Mami. "Bari na dauko maki auta ai wannan abun farin cikin gara kowa yaji sa. Dafe kai Rumaisa tayi tamkar wata mahaukaciyya idonta sun kada sunyi ja jikinta har wani kaɗawa yake saboda bacin rai, tana ta tunanin me ta yiwa Abba Bashir da zai yi mata wannan tozarcin yana nufin yafi jin daɗin mu'amular aure da Aydah akanta?" idan ba haka ba meyasa zai siyawa Aydah motar da ta kudinta ya kai miliyan goma daukar wayarta tayi ta shiga kiran layin Aunty Raliya,tana ɗagawa ta fashe mata da matsanancin kuka mai girgiza zuciya da ruhi. "wallahi-tallahi ba zan iya kishi da wannan kwailar ba Aunty Raliya mutuwa zanyi. "Yau kuma me ya haɗa ku?" Raliya ta faɗa tana sauraren kukan kanwartata. Nan take Rumaisah ta faɗa mata abun da ya faru ita ma Raliya taji babu daɗi haka ta taya ƙanwarta kishi. "To ke yanzu wane mataki za ki dauka? Don wannan ma rainin hankali ne. Cikin kuka Rumaisa ke faɗin. "wallahi-tallahi jin nake kamar naje na sakawa motar fetur da mamallakiyyar motar dukka na ƙonasu uban kowa ma ya huta. Wata dariya Raliya tayi tana faɗin "idan kika ƙonasu kina jin haka za'a barki?" Ɗan shiru Rumaisah tayi tana jin bayanin da Aunty Raliya take mata ta cikin wayar "kema ki nuna masa bacin ranki kawai yau kema a kawo miki sabuwar mota idan har ana son zaman lafiya da kwanciyar hankali da haka suka yi sallama da Aunty Raliya. Hakan kuma yasa ta ji ɗan sanyi aranta jin kalar shawarar da auntyn ta ta bata ta kuma gamsu da ita ɗari bisa dari. "kina ji Auta! "Ina jin ki Aunty Huwaila yau ina cikin farin ciki na rasa ma me zan yiwa yayanmu wanda zan biyasa dashi saboda farin cikin da ya bani ayau. Ban taɓa tsintar kaina cikin farin ciki da annashuwa kamar yadda nake jin kaina yanzu ba Aunty Huwaila ki bani shawara me ya kamata na yiwa yayanmu a matsayin tukuici wannan babbar kyauta da ya yi min? nasan ba zan iya biyasa farin cikin da ya sakani ba dukka annan ina so shi ma na sanya shi cikin farin ciki. shiru Huwaila tayi alamar nazari tayi saurin kallon Aydah tana faɗin "shin kwanan Rumaisah nawa gidan nan?"ɗan shiru Aydah tayi tana faɗin,gobe zata cika sati ɗaya ɗan jim Huwaila tayi tana faɗin."ya kamata mu barsa zuwa gobe Auta tunda ya raba muku girki gobe za ki karbi girki ya zama dole gobe ki fara shiga kitchen duk wannan sakarcin ki ajesa a gefe ki riƙa yiwa mijinki girki da hannunki a da kaɗan-kaɗan za ki iya. Nan da nan Aydah ta bata fuska ita fa ta tsani girki gaskiya,ko kaɗan bata son shiga kitchen. "ke kina yi kuma Aunty Rumaisa tana yi ba shikenan ba?" Ni fa Aunty Huwaila kin san bana son zafin kitchen, duk abun da sai an wahala akansa ba sonsa nake yi ba. "Auh Allah?"ashe kuwa Rumaisah z ata kwace miki miji wai ke yaushe za ki yi hankali?"haka za ki zauna ba zaki riƙa yiwa mijinki girki ba. Ke bakya jin wani iri ne?"idan ma mafarki kike ki farka zamanki haka ba zai yiyu ba. son jikin ki yayi mugun yawa Auta. Ita dai Aydah jin Huwaila kawai take yi ranta duk babu daɗi musamman da Huwaila tayi zance shiga kitchen abun da ta tsana kenan. A gigice Siyama ta faɗa ɗakin Mami tana kwala mata kira jikinta sai bari yake "Mami kinga motar da yayanmu ya siyawa Aydah. Mami kalla kiga ta turamin Mami new model ce. Ɗan Jim Mami tayi batareda ta karɓi wayar da Siyama ke bata ba "Allah ya sanya Alkhairi. Ta faɗa adakile dan shiru Siyama tayi tana kallon yanayin Mami,sai kawai ta juya tabar ɗakin har cikin aranta yayan nata ya gama biyata musamman da Aydah ta faɗa mata matsayin gift ne na first night ɗinsu ne. Haka siyama ta rika posting kafafen sada zumunta tana taya little sis ɗin ta murna. AB bai shigo gida ba sai bayan ishaai a gajiye ya yake, parlor kasa ya tarar da Aydah da Huwaila da gudu Aydah taje ta shige jikinsa tana masa sannu da zuwa tayi wanka tana cikin riga da skirt na kanti wanda suka yi mata matukar kyau,kunya duk ta cika AB ganin yadda Aydah ta wani makalesa a gaban Huwaila. Huwaila nayi masa sannu da zuwa ta sulale tabar cikin parlor. "baby na gaji wanka nake bukata. ya faɗa yana manna mata kiss akan lips ɗinta. Ɗan lumshe ido tayi kafin ta budesa akansa da gaske yana tare da gajiya dan kana karanto hakan ta cikin fararen idanunsa da suka ɗan faɗa ta karbi suit jacket ɗinsa da kuma briefcase ɗinsa. "mu je na rakaka yayanmu. Tare suka jera har zuwa ɓangarensa ɗan turus Aydah tayi ganin Rumaisa zaune cikin parlornsa sai Ƙamshin turaren wuta ke tashi taci uban gayu cikin wasu tsinannun kaya,duk yadda Rumaisa taso share AB kasawa tayi musamman da ta gansa da Aydah ta saki fuska sosai ta nufesa da sauri ta shige jikinsa ganin haka da sauri Aydah ta juya ta nufi master bedroom ɗinsa zuciyarta na tsananin bugawa nan take hawaye suka cika mata ido, bata jima ba ta fito daidai lokacin da taji Rumaisah na faɗin. "Habeebi mu je na tayaka wanka. ɗan satar kallon Aydah ya yi sai yaga tayi mugun haɗe rai ta gefensu tabi ta wuce daga parlor,Rumaisah ta haɗa masa ruwan wanka ganin ya yi ta juya ta nufi kofa da mamaki yake faɗin."Daman ba tayani wankan za kiyi ba? wani irin kallo Rumaisa ta rika jefa masa cikin ƙunar rai da kishi take faɗin."ai na dauka bana da wannan matsayin wacce ka siyawa mota ta fini matsayi mai girma a wajenka sai ta zo ta tayaka wanka. Da haka Rumaisah ta wuce tana rufo masa kofar baki sake AB ya bita da kallo dafe kansa ya yi idan dai kana da mata biyu ka shiga uku duk yadda kaso faran ta masu baka taɓa yin daidai. Wanka yayi koda ya fito ya tarar Rumaisah ta fitar masa da kayan bacci kalar sararin samaniya riga da wando duk da tasan ba wai kwana yake da kayan baccin ba,tasan iyakancinsa ya zauna dasu a parlor yaci abincin dare kafin ya kwanta zai cire ya fito parlor ta aje masa abincinsa har coffee ta haɗa masa. "Habibty ki kira Aydah muci abinci tare. Dan jim Rumaisah tayi tana tauna maganarsa aranta jin take kamar tace masa ,shi mai zai hana ya tashi ya kirata da kansa,tasan ba zata fara ba saboda kwarjinin dake tare da AB har zata tashi yayi saurin dakatar da ita. "Yi zamanki bara na kirata a waya. Da haka AB ya shiga kiran Aydah sun ɗan dade suna magana kafin ya sauke wayar, ba'a jima ba Aydah ta shigo AB ya umarceta tayi sarving ɗinsu a plate ɗaya su ci haka tabi umarninsa tayi yadda yace har suka gama cin abinci fuskar Rumaisah babu wani walwala duk hirar motar da Aydah ke yi masa shi kuma sai biye mata yake Aydah ta karbi coffee hannun AB ta kai bakinta da sauri Rumaisa ta kalleta da zallar mamaki da takaici "coffee da na haɗa masa shine zaki wani karɓe ke ba zaki iya haɗa naki da kanki ba?" Aydah ta ware ido tana ɗan juyasu "Ni na yayanmu nake so na sha Aunty yafi dadi. Saboda takaici Rumaisa miƙewa tayi ta shigar tattara kayan da suka ci abinci bayan fitarta AB ya juya yana kallon Aydah yana faɗin."ki tayata kwashe kayan mana. Lokaci ɗaya Aydah ta tura baki tana faɗin."kowa ranar girkinsa dai ya kwashe yayanmu. Cike da mamaki AB ke kallon Aydah har zai buɗe baki yayi magana sai ga Rumaisah ta shigo shiru ya yi har Rumaisa ta gama kwashe komai ta mayar kitchen. Kan doguwar Soofa AB ya koma ya zauna yana daukar remote yana canja channel,kusa dashi Rumaisah taje ta zauna a hankali kuma ta zame ta kwanta ta ɗora kanta akan cinyoyinsa,ta gefen Ido Aydah ta kalleta shiru parlor yayi har na kusan minti goma ganin har lokacin Aydah bata da niyar tafiya yasa Rumaisah ta kara gyara kwanciyarta akan cinyoyin AB ta dauki remote ta canja channel ta mayar dashi kan tasha (African magic epic)da ake haska wani movie mata da miji ne aka nuna kan bed suna kissing ɗin junansu kamar za su cinye kansu, da sauri AB ya kalli ɓangaren da Aydah take sai yaga Aydah ta tsurawa Tv ido,yana ƙoƙarin ɗaukar remote dan canja channel ɗin Rumaisa tayi saurin riƙe masa hannu "Habeebi ka;bari mu kalla ina so. Da haka Rumaisah ta janye remote ɗin sai ta shiga wasa da hannunta akan tsakiyar cinyoyinsa duk yadda AB yaso dakatar da ita kasawa yayi da sauri Aydah ta miƙe tsaye ta kalli gefen da suke ta kalli yayanta ido cikin ido da har yanayinsa ya fara canjawa tayi masa sai da safe ta juya ta fice daga parlor da sassarfa tana fita yana ture Rumaisa daga jikinsa da mamaki take kallonsa. "kin san baki da lafiya meyasa kike ƙoƙarin hargitsa ni Rumaisah.?"idan kuma nace naje wurin Aydah kice na maki rashin adalci. "Anzo wurin da nake so daman azo! Rumaisa ta faɗa a masifance tana miƙewa zaune "Daman ko jarabarnan za ta cinyeka wallahi-tallahi baka isa kaje wurinta ba,tunda kwana na ne! Kai na lura ba zaka taɓa yin adalci a gidanka ba. "Ɗazu fa mota ka siyawa Aydah mota fa Habeebi meka daukeni marar daraja a wurinka ko me?" Da sauri AB ya dakatar da Rumaisa yana dafe kansa dan har kansa ya fara daukar zafi. "Me kike nufi da rashin adalci?"me nayi maki na rashin adalci ?"yadda na kai ki shopping haka na kaita yadda ta zabi abunda take so haka kema kika zaba. Ita tace mota takeso tun ban aureta ba daman nayi mata alkawarin ni zan bata mota kuma na cika alkawari na bata ɗin shine kike faɗar bana da adalci ke wayoyi kika sa na canja maki ita bata bukatar wayar mota ta bukata ke kin bukaci motar ne ban ba ki ba?"Rumaisah bana son tashin hankali na lura duk rashin zaman lafiya a gidan nan ke kike fara kawo sa ina sane da ke kika zube shopping ɗin da nayi maki a parlor kika gayawa Aydah har ta rika yi min rashin kunya,kawai dai na saka maki ido ne saboda bana son fitina. A Masifance Rumaisah tace "To ni ma motar nake so kuma irin nata yanzu ya za'ayi? Wani kallo AB yayi mata kafin yace "Sannu uwata tun da ke kika haife ni gara ki bani umarni, ko zan ba ki mota Rumaisa ba irin ta Baby ba kuma ki sani sai dai na siyar da ta ki na cika kuɗi na siya miki wata don ni ban gadi almubbazaranci ba. Yana gama faɗar haka ya mike yabar mata parlor ransa duk a ɓace yake gashi ta gama har gitsasa a parlor ta tayar masa da tsumi babu damar zuwa wajen Aydah ko shi maye ne ai ba zai je wurin Aydah ba tunda tana da ɗinkin ajikinta gashi Rumaisah ko romance ya fara yi da ita sai tace ta gaji har mamaki take basa duk yadda Rumaisa taso hana kanta hawaye sai da suka zubo tana addu'a taga mafarki ne take ta farka yanzu kam ta gama yarda da rashin aldalcin AB. Sai kusan 11 ta shiga master bedroom ɗinsa duk a zatonta yayi bacci kwantawa tayi gefensa tamkar jira yake ta kwanta ya jawota ya fara lalubarta da sauri ta kwace kanta ai wallahi sai ta rama yanzu nan ya gama gaya mata baƙeƙen maganganu shi ne don ya maida ta sakarya zai taɓa mata jiki. Sai ya ɗandana baƙin ciki da ya da ɗandana mata ko da kaɗan ne sai yasan jikinta yana da rana a wurinsa da mamaki AB ke kallon Rumaisah da tayi saurin tashi zaune ta dube shi a dage tana faɗin "ka manta bani da lafiya. Ta faɗa fuska a haɗe. "Ba sai kin tuna min ba na sani romance kurum zamuyi. 'yar dariya Rumaisah tayi tana mamakin karfin halinsa duk yadda yake cikin ɓacin rai ba zai iya zuciya da wannan abun ba, ƙara riƙota yayi tayi saurin dakatar dashi "Habeebi bana cikin yanayi mai dadi dan Allah ka kyaleni tana gama faɗa ta dauki pillow ta komawa kan doguwar Soofa tayi kwanciyarta,cike da tashin hankali yake kallonta bai taɓa sanin Rumaisah muguwa bace sai irin wannan lokacin. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO [1/30, 1:28 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 088. Yafi minti goma a haka duk wani motsi da yake rumaisa na kula dashi,sai dai ta danne duk wani feelings da takeji akansa tayi alkawarin daren yau sai ta koyawa Abba,mugun hankali sai ta nuna masa ita ma tana da rana ba shegiya bace. Ganin wayarsa ta yi haske yasa ya kalli gaban wayar da sauri ganin daga Aydah ne ya cire numbobin sirrin dake jikin wayar,miƙewa zaune yayi lokaci ɗaya yana kara bin saƙon da kanwar tasa ta tura masa *Yayana har kayi bacci ne? ni kam na kasa bacci irin kiss ɗin da naga anayi a tv nakeso da gaske na kasa bacci* daga ƙarshen text ɗin ta saka emoji na kuka da shagwaba. Wani irin murmushi ya riƙa saki shi ɗaya yana ta rike da wayar, idan babu Aydah cikin rayuwarsa bai san ya rayuwa zata zo masa ba,ya yi ammana da cewa wanzuwar Aydah cikin rayuwarsa yana cikin ƙaddarar sa. Da ido Rumaisa ta riƙa binsa lokaci ɗaya ya sauko daga kan bed ,kai tsaye ya dauki pyjamas ɗinsa ya saka ajikinsa da mugun mamaki Rumaisa ta tare kofa ganin da gaske fita zai yi zuciyarta na tsananin bugawa cike da karfin hali take faɗin."ina kuma zaka je?"ya kalleta sama da kasa fuska babu walwala yake faɗin."inda zan samu natsuwa matata na bukata ta nima ina bukatarta. Da shock Rumaisa ke kallonsa wani irin abu taji ya tsaya mata a wuya kafin kuma ta saki dariyar takaici "Kai bakaji kunya ba ?" Ya buɗe ido yana faɗin. "kunyar me zan ji matar aure na ce fa. Cikin huci Rumaisa ta mayar masa da cewa."Amman kasan wannan zalunci ne kou? ranar kwanan na ka tsallake ni kaje ɗakin wata? "Rumaisa karki ɓatamin rai a daren nan bani hanya na wuce. ƙara tare kofar tayi cike da bala'i take faɗin."babu fa inda zaka je a daren nan Abba idan har kana son kwanciyar hankali ka koma ka kwanta. Hannu ɗaya ya saka ya jawota ya matsar da ita gefe ya buɗe kofar ya fice ko waiwaye ta bai ya ba da wani irin shock Rumaisa take kallonsa zuciyarta banda tafasa babu abunda take daga Abba har Aydah ta lura dukkunsu jarababbu ne sai ta koya masu hankali, sai kuma ta zauna kan Soofa ta wani rushe da kukan baƙin ciki mai haɗe da kishi wanda ke fitowa tun daga ƙarƙashin zuciyarta. Aydah tana kwance tayi ruf da ciki ta ji kamar ana knocking kofarta duk ta yi wani sanyi tamkar marar lafiya tun sanda ta dawo daga wurin ƴayanta yanayinta ya canja wani irin mugun feelings take ji wanda bata taɓa jin kalarsa ba,musamman da Rumaisa ta canja channel sai ta riƙa gani kamar ita da yayanta ne bata san lokacin da hannunta ya kai ta shiga rubuta wa yayanta saƙo dangane da abun da take jin ana knocking yasa da sauri ta sauka daga kan bed,ta nufi kofa cikin rawar murya take faɗin. "waye?" "baby ni ne zo ki buɗe ƙofa. Jin muryar yayanta yasa cikin sauri ta ta murza key ƙofar ta buɗe. Kallonta yake tun daga sama har kasa rigar bacci ce a jikinta marar nauyi mai hannun supergheeti ,kalar Omo blue sai ƙamshin turarrukanta ke tashi a ɗakin,da kansa ya mayar da kofar ya rufe. Juyawa Aydah ta yi da sauri tun kafin ta isa kan bed ya kashe fitilar dake cikin ɗakin da sassarfa ya isa gareta rungumota yayi ta baya yana shaƙar ƙamshin gashin kanta da na kuma jikinta wanda ya haɗe ya bayarda wani kalar ƙamshi mai saukar da natsuwa,kananun kiss ya shiga manna mata a wuyanta still yana rike da ita da sauri ta rike hannayensa jikinta na shaking da wata irin murya yake faɗin "saƙon me kika turomin baby faɗamin naji da bakin ki?" Haka kawai ina tareda matata kin tasoni dan jaraba, yarinya ƙarama dake kin san kan tsiya. jin abun da yayan nata ke faɗa take ƙoƙarin kwace kanta cikin nasa cike da kishi lokaci ɗaya ya juyo da ita tana fuskantar sa yadda yaga fuskarta ta zama wani irin lokaci ɗaya har kwallar rigima yake hanga cikin kwayar idanunta saboda kishin ya kira Rumaisa da suna matarsa yana matukar son yadda baby nasa ke kishinsa sosai a hankali ya ɗora duka hannayenta akan kafadunsa yana rike da tiny waist ɗinta in a romantic way. A hankali ya ɗora hancinsa akan nata yana gogawa ,da sauri ta runtse idonta zuciyarta na bugawa tana kara rikesa sosai, muryarsa taji kasa-kasa yana faɗin. "To gani ki cinye ni duka baby idan ba ki cinye ni ba kin san sauran. Wani irin kunyar yayan nata taji ta rufeta lokaci ɗaya,tamkar ƙasa ta tsage ta shige bakinsa taji cikin nata shiru tayi tana karbar sakwannin da yake aika mata dasu tun tana dauriya har ta kasa ta shiga tayasa da sauri yasa hannu yana ƙoƙarin jan rigar jikinta ganin yana bata masa lokaci yasa hannu biyu ya raba rigar da sauri Aydah ta zube kasa tana kare jikinta tamkar zata yi kuka ta ce "Yayanmu ka yaga mun kaya. ɗagota ya yi ya nufi kan bed da ita hannu ya ɗora akan na shanunta da sauri ta rike hannunsa a tsorace take faɗin. "Yayanmu zafi. Ta faɗa tana ƙoƙarin fashe masa da kuka,lokaci ɗaya ya haɗe bakinsa da nata ya shiga gigitata da romantic kisses ɗinsa masu zafi da rikita ƙwaƙwalwa,kamin kuma ya ɗora hannunsa akansu tsit Aydah ta yi sai da tafiya ta yi tafiya yana ƙoƙarin neman hanyarsa a tsorace ta rikesa ta fashe da kuka jikinta na mugun rawa "yayanmu ɗinkina kada ka ji min ciwo. Da wata irin murya yake faɗin. "A hankali zan yi baby!" make masa kafaɗarta ta yi tana girgiza kai hankalinta duk a tashe,bata manta wahalar da ta sha a fisrt night ɗinsu ba haka bata manta wahalar da tasha a wurin yimata ɗinkin ba,dan sai da likitar ta gargadeta akan kar ta yarda da maigidanta ya kasanceta sai ta warke duka. Idan ta yadda ya kusanceta zai warware su kuma babu ruwansu ita ce zata samu matsala,babu irin rarrashin da AB bai yiwa Aydah ba Amman taki yadda ƙarshe ma fashe masa da mugun kuka tayi jikinta na rawa, babu musu ya sakata ajikinsa a fusace yake faɗin "kin san ba ki bani kanki ba uban wa yasa ki tura min da text wai miyasa ko mata bakwa da tausayi?" Cikin shasshekar kuka ta ce "Ka yi haƙuri Yayanmu kai ma kasan da ina da cikakkiyar lafiya ba zan hanaka ba ina tsoron ɗinkin ya warware ni ce zan sha wahala. Yadda ta ƙarashe magana cikin muryar kuka sai ta bashi tausayi, ya sake rungumo ta yana ɗan buga bayanta har na kusan minti goma suna a haka daidai kunnenta ya rada mata "Ba zan miki komai ba baby amman duk yadda nace kiyi min ki yi har na samu natsuwa kin ji?" Ya faɗa da muryarsa da bata fita sosai da sauri ta daga masa kai Wani irin wasa ya riƙa yi da ita har sai da ya tabbatar ya samu natsuwar da yake bukata ya wani kankameta cikin jikinsa yana saka mata albarka,da haka Aydah ta samu tayi bacci tana manne dashi wani irin ciwo jikinta yake duka ba ƙaramin wahala tasha ba a hannun yayan nata ba kafin ya samu natsuwar da yake bukata musamman ma ƙirjinta da take ji suna mata azabar zogi shi kansa yasan ba ƙaramin ƙoƙari Aydah ta yi masa ba,yasan da Rumaisa ce da yanzu tace ta gaji babu ruwanta da ko ya samu natsuwa ko bai samu ba haka za ta juya masa baya. Ya lura Aydah tana ɗaya daga cikin matan dake da mugun dauriya a gadon aurensu duk da ƙananun shekarunta da yanayin jikinta tafi mai Rumaisah wacce take cikakkiyar macce dakyar ya daga Aydah ya nufi toilet da ita duk irin magagin baccin da take haka ya haɗa mata ruwan zafi ta yi wanka,sai shagwaba take masa ita bacci takeji,kusan wanka tare suka yi shiya taimaka mata ta goge jikinta ya fiddo mata da wasu kayan baccin ya saka mata a haka ta kwanta ya kara yi mata addu'a ya ja mata duvet,kayansa ya mayar ya wuce ɓangarensa zuciyarsa wasai wannan karon akan bed ya samu Rumaisa taci kukanta ta gaji bacci ya dauketa kayan jikinsa ya cire ya canja boxer a hankali ya hau kan bed ɗin ya jawo pillow ya rungume a kirjinsa sai murmushi yake saki shi ɗaya,da haka shi ma bacci ya dauke sa. Washe gari da fushi Rumaisa ta tashi duk da ta tashi ta gansa a gefenta haka bai sa zuciyarta tayi sanyi ba. Dan ko gaishesa ranar ba tayi ba har kusan ƙarfe 8 tana a ɗakinta lokacin ta yi wanka kasa ta sauka ta leƙa ɗakin Huwaila ta mata umarnin ta aza ruwan tea ta soya kwai tun da taga jiya AB ya shigo da bread dan ta yi alkawarin yadda AB ya bata mata rai ba zata yimasa break fast ba baran tana har Aydah ta samu alfarmar sa taci kowa yasha ruwan tea kawai. Suna cikin breakfast wuraren karfe tara sai ga Aydah ta sauko ƙasa ita ma da alamar ta yi wanka dan ba kayan bacci a jikinta da alamar dai ta fara bin shawara Huwaila daman bata yadda ta fito ba sai da ta gyara ɗakinta ta share har toilet ta wanke. Mopping kawai ne bata yi ba tace sai ta huta da rana tayi,tun daga kan stairs AB ke kallon ta ita kuma sai wani noke kanta take yau ga baki ɗaya,kunyar yayan nata take ji ganin inda AB yake kallo yasa Rumaisa ta kalli wurin da sauri,tana hango Aydah ta wani haɗe rai ta dauke kai bayan kujera ta tsaya tana gaisheda yayan nata cike da kunya,ya amsa yana shafa kansa yana kallonta ta ƙasan ido tamkar bata so haka ta juya ta gaisheda Rumaisa ciki-ciki Rumaisa ta amsa mata. Daman Aydah na ƙoƙarin zama da sauri Rumaisa ta miƙe tsaye kai tsaye tabar cikin dinning area ɗin. AB na ganin Rumaisa tabar cikin dinning area ya kalli Aydah da sauri ya nuna mata kan cinyarsa ta wani zaro ido tana make kafaɗarta, ta shiga haɗa tea kasa daurewa yayi ya dawo gafda ita duk sai ta rikice sai ƙoƙarin sakin cup tea ɗin hannunta take, dariya ta bashi sosai da gaske wai babyn sa kunyarsa take ji. Kusan 12 Rumaisa da AB ne zaune a parlor shi yana aiki da laptop ɗinsa Rumaisa kuma tana chat ganin 12 tayi yasa Rumaisa ta mike tsaye tana faɗin."Bara na je na ɗora lunch yau me zaka ci? "Duk abun da ya samu. Ya faɗa still fuskarsa na kan laptop ɗinsa,sai kuma ya kalli Rumaisa yana faɗin. "zan nemi alfarma a wurinki Habeebty Allah yasa zan samu. Da sauri Rumaisa ta zauna tana kallonsa alamar dai tana jin sa,ki riƙa jan Aydah kitchen tana tayaki girki har ta iya tun da ba iyawa tayi ba haka kuma zai sa ku shaku da juna. Baki buɗe Rumaisa ke kallonsa "Ki yi hakuri dan Allah! Da gaske Abba ya raina mata hankali ita ce zata rika shiga kitchen da kishiya har ta koya mata abinci. Tun da daman yau Aydah za ta karɓi girki da dare ma sai ku yi tare bana jin daɗin yadda bakwa sakewa da juna. Da sauri Rumaisa ta kallesa "Bangane za ta karɓi girki ba kamar ya?" Da mamaki AB ke faɗin. "Kin manta kwana bakwai nayi a bangaren ki yau ya kamata na koma ɗakin Aydah? Da mamaki Rumaisa ke faɗin."Amman kana bangarena kuma kana zuwa wurin Aydah da kwanakina akanka kuma ka ga ai bani da lafiya ba wani amarci muka yi ba. kawai ka yi haƙuri ka ƙara min sati ɗaya. Da mamaki AB ke kallon Rumaisa jin yayi shiru tace "Ya naji ka yi shiru kuma. "Yoo ba dole nayi shiru ba naga kin zo min da hauka. "Hauka fa ka ce habeebi?" "Hauka mana Rumaisa akan me za ta ƙara miki sati ɗaya? "Saboda ban gama more amarcina ba ta cuce ni ta sako min zubar jini don haka dole ta ne ta kara min sati ɗaya koda kuwa bata so. "Ba zan iya ba Rumaisa kwana biyu kamar gobe ne nq dawo wurinki,duk wata kofa ta zuwa wurin Aydah ke kika buɗe min ita duk da bakya da lafiya da kina taimaka min ina samun natsuwa da ban je gareta ba. Da wani irin fusata Rumaisa ta wuce daga parlor nasa da ido ya bi ta kusan minti goma da fitar ta ya aje laptop ɗin ya nufi ɗakin Aydah samun ta ya yi tana karanta novel a wayarta ya shigo da sauri ta tura wayar cikin pillow tayi saurin tashi zaune a bakin kofa ya tsaya yace "me kike yi yanzu?" "Babu komai. "owk! fita ki rikawa Rumaisa aikin abinci rana. Babu musu Aydah ta miƙe ta nufi kofa shi ma bangarensa ya koma Huwaila da Rumaisa ta samu a kitchen daman Rumaisa na ganin ta shigo ta kalli gefen da Huwaila take tana gyara kayan miya tace "Huwaila ki barwa Aydah kayan miyan ta gyara zo ki gyara cabbage ɗin da za'a haɗa coslow. Huwaila tasan Aydah ba iya gyaran kayan miya tayi ba amman ita kanta Huwaila tana son Aydah ta zama full house wife kamar ko wace macce."Auta ƙaraso ki gyara tamkar Aydah za tayi kuka take faɗin."Aunty Huwaila ki dai gyara ya ji zai shigarmin a idona. A wani irin fusace Rumaisa ta yiwa Huwaila tsawa tace tabarwa Aydah gyaran kayan miyan. Wani irin kallo Aydah ta riƙa bin Rumaisa dashi "Ban san kin cika marar kunya ba sai kinzo ki dakeni zan san ke ɗin bakida tarbiyya baki iya komai ba Amman kin iya kwanciya da namiji a gado ki ware masa ƙafafu. Ita dai Huwaila bata ce komai ba da sauri ta saukar da kanta a kasa tarugu kawai Aydah ta gyara koshi tana gudun masifar yayanta daman tattasai gefe ta ajesa tace ba zata gyara ba hannunta zai yi yaji ta dauki albasa ta fara gyarawa sai hawaye take ga baki ɗaya ta galabaita kai da ganinta kasan bata saba ba,tana can ido a rufe ta datsawa yatsanta wuƙa ga wuƙar sabuwa, wani kalar ihu ta saki ta jefar da wuƙar tana riƙe da hannunta da jini ya fara fita da sauri Huwaila tayi wurinta tana ƙoƙarin riƙo hannunta AB ya shigo kitchen ɗin shi ma fitowar sa parlor kenan yaji ihunta kuma yau weekend babu inda ya fita da sauri AB ya nufeta Huwaila tayi saurin jada baya. Yadda take wani irin kukan tabara yasa AB duk ya gigice ya juya yana yiwa Rumaisa faɗan meyasa za'a bata aikin da zata rika wuƙa tun da tasan bata iya ba koya ne take yi kamata ya yi ta fara yi mata demonstration kafin ta bata wuƙa. Saboda takaici kasa cemasa komai tayi a haka ya riƙa hannun Aydah dake famar rusa kuka har lokacin suka fice daga kitchen ɗin wani mugun kallo Rumaisa tabi AB dashi a haka zata zauna tana shiga kitchen da wannan yarinyar duk iya ƙokarinta baya gani ashe kuwa akwai bala'i da masifa a gaba. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO. [1/31, 2:10 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 089. AB ya zaunar da Aydah akan kujera ya nufi upstairs da sauri ya je ya dauko first aid box ya yi mata dressing ciwon nata sai wani ƙara narkewa take yi shi kuma sai biye mata yake yi daga ƙarshe ya sake komawa kitchen ya tarar da Rumaisa har ta yi nisa da aikin ya kira sunansa cikin taushi murya. "Habibty! "Na'am! Ta amsa tare da juyawa tana kallonsa karasa shigowa kitchen ɗin ya yi hakan yasa Huwaila ta fice da sauri daman tana so ta sami dalili da za ta je ta duba Aydah, kamar Ab zai faɗin abu kirki musanman yadda ya kira Rumaisa da tattausan kalami. "Habibty ki yi haƙuri ki cigaba da yi mana girki har zuwa gaba idan baby ta ƙara girma sai ta karɓe ki. "Jar ubanan! Abba Bashir na gaji da raini hankalinka fa kar fa ka ɗauke ni shashasha wacce batasan abun da take yi ba. Cike da zallan mamaki AB ya zaro manyan idanunsa yana kallon Rumaisa yadda ta yi amfani da kalmar rashin ɗa'a akansa kanta tsaye sai ka ce wani sa'anta. "Rumaisa ni ke faɗa wa kalaman rashin ɗa'a to da kika ce jar ubanan da uban waye kike Allah yasa dai ba nawa kike nufi ba?" "Yoo kai kana da uba ne balle a zagi sa ai zagin ubanka tamkar harara ne a duhu. Abun da Rumaisa ta faɗa a can kasan zuciyarta kenan amman a bayyane sai ta ce "Ka ga Habibi banaso rigima yarinyar da duk ta iya kwanciya da namiji girki ne ba za ta iya ba. Ka cire son zuciya ka fuskanci gaskiya, ni dai ba 'yar aikinka bace balle ka cilasta min cigaba da girki a gidanan. Shiru AB ya yi yasan iya gaskiya Rumaisa ta faɗa to amma kuma bayaso duk wani abun da zai wahalar da Aydah. "Shi kenan duk ranar girkinta Huwaila ta dinga yi ke kuma ranar naki ki yi mana, har Allah yasa ta kara wayau ta dinga yi da kanta ai komai ɗan hakuri ne wata rana ma sai ki ga tafi ki iyawa. "Allah ko?" Rumaisa ta faɗa tare da yi masa kallon uku saura kwabo ta juya ta cigaba da aikinta tana ji wani irin tuƙuƙi baƙin ciki, lallai ya zama mata dole ta nemi hanyar da za ta dakile wannan iskancin da Ab ya tsira mata dashi, idan har bata yiwa tufkar hanci ba da wurwuri to kuwa kwabarta za ta yi ruwa tsululu abun da bata fatar faruwar sa. AB ya gallawa gadon bayanta harara ya juya ya fice yana mai jin haushinta don shi bai ga abun tada jijjiyoyin wuya anan ba, fitina ce kawai irin ta Rumaisa. ******* Anaal ta haɗa kayanta cikin farin ciki ta baro hotel ɗin gudun kada Ummie tai mata faɗa rashin sauka gidan Aunty Zeenah da ta yi yasa ta biya gidan cikin rashin sa'a ta tarar da Aunty Zeenah ɗin bata nan ta tafi Mubi bikin aure maigidanta kawai ta tarar Alhaji Sanusi, shi ma ya kira mata Aunty Zeenah ɗin a waya suka gaisa da yake ita bata da number ɗinta. Hajiya Zeenah matar ƙani Daddy mahaifin AB da Aydah ashe yayarta mahaifiyar Anaal ce uban su ɗaya.(tofa ana wata ga wata😳) Zuciyar Anaal wasai ta baro garin Kano ta ɗauki hanyar birnin kudu koda ƙarfe biyu ta buga tana cikin masaurata. Kilishi ga baki ɗaya ta gama ficewa daga hayyacinta domin duk wata dabara ta ƙare mata, tabi bokaye da malaman tsinbo daban-daban domin a hana wa Ciroma zama sarkin kudu sai dai kuɗin ta kawai suke ci, ta tsinewa Ciroma yafi shurin masaki ko son ganinsa bata yi shiyasa duk wannan shirye-shirye da ake yi na naɗin sarautar babu ita aciki ko raguwar yaranta taso ta hana masu su bar Ciroma shi kadai ya yi kidansa ya yi rawarsa sai da jakadiya ta ankarar da ita illar da take kokarin haifar wa da kanta, sannan fa ta barsu sai dai hakan ba ƙaramin ƙuna mata rai ya yi ba. Washegari masarauta ta cika da mutane daban-daban domin wasu sun zo ne daga wa'yansu garuruwa dake makwabtaka da birnin na kudu, ga manyan sarakuna dukka sun hallara mai martaba sarkin Kano ya je,ga mai martaba sarkin musulmi shi ma ya zo sai sarkin Zazzau duk wani basarake dake arewacin Nigeriya yana garin Kudu, Ciroma aka fara nadawa kafin a naɗa Aliyu na Uku sai kuma aka cigaba da naɗin ƙanana sarautu da suka biyo baya. Bayan an kammala naɗin aka wuce reception dukka anan cikin masarauta yayin da mata suka gundanar da kwarya-kwarya walima aka ci aka sha aka kuma raba sovaniers manyan bags masu ɗauke da hotunan sarakuna biyu. Bayan kammala reception kowa ya kama gabansa sai lokacin Aliyu na Uku ya nufi ɓangaren mai babban ɗaki tana arba dashi sanye da rawani ta fashe da kukan farin ciki ta dinga kwararo masa addu'o'in har tana cewa ko yau Allah ya dauki rayuwarta burinta ya cika. Sai wuraren karfe goma biyun dare Aliyu na Uku ya sami damar fitowa daga ɗakinsa yana so ya yi waya da Maysun throughout bai ji muryarta ba bata ji tasa ba. Sai da ya tabbatar da baccin Safiya ya yi nisa shi ne fa ya sato jiki ya fito balcony ya kira ta kamar jira take yi ta yi picking daman ta kasa bacci a dalilin rashin ji daga garesa, muryarta kaɗai dake ratsa masa kunne natsuwa take saukar masa ya rasa wane irin azababben so yake yiwa Maysun. Anaal da ta kasa bacci tana tunani ta ya ya za ta aiwatar da plan b ɗinta daman duk cikin plan ɗinta plan A ya fi sauki, a hankali ta nufi window ɗakinta dake cikin balcony ta buɗe sai ta hango Abbunta dafe da waya a kunnensa sai zuba uban murmushi yake yana shafa sumar kansa kamar dai wani ɗan saurayi mai shekaru talatin da bakwai a duniya jikin Abbu baya nuna shekarunsu ga kuma Abbu ɗan kwalisa ne koda yaushe cikin gyming yake yi ga kuma tsadaddun mayukan gyaran fata da yake amfani dasu. Ko a yanzu Abbu zai iya aure yarinya mai 'yar sha bakwai don kuwa he's very good looking ga kyau ga naira. Ko Anaal bata tambaya ba tasan da wannan ruwa biyu ce(halfcast) yake waya nan da nan ta ji ranta ya yi mugun ɓacin musamman da ta tuna da irin hidimomin da Ummie tayi masa yayin naɗinsa, ta aikatu ba kaɗan ba shi ne yanzu tana yi bacci ya sato jiki ya baro ta can kwance ita kadai tsabar rashin adalci irin nasa dole ta jajirce ta kawo karshen wannan baƙin zalunci da mahaifinta yake gwada wa mahaifiyarta. A fusace ta maida window ta rufe ta zura bedroom slippers ɗinta ta fice har ta iso bayansa bai sani ba ya yi nisan da fadawa Maysun tsadaddun kalaman soyayya, yadda yake fitar da kalaman ko waye kai sai ka girgiza ashe Abbu ɗan soyayya ne yasan yarda ake tattalin mace asata farin ciki ummie ce kawai da ya tsana ita ce baya iya ba wa lokacinsa. Lallai Abbu mugun mutum ne mai bala'in son zuciya. Duk Wadannan zantukan Anaal ce ke yi su acan kasan zuciyarta da ta fahimci al'amari na Abbunta ya fara fin ƙarfin ƙwaƙwalwarta sai tai hanzari taka masa birki ta hanyar gyaran murya a ɗan tsorace ya juyo a zatonsa ko Safiya ce har yanzu bai shirya gabatar mata da Maysun ba yana jiran lokacin da ya dace ya yi hakan. Yana juyawa idanunsa suka sarke da na Anaal wacce tayi bala'in murtuƙe fuskarta babu rahama ko kaɗan akanta, ga kuma wani kallon tuhuma da take bin Abbu dashi. "Anaal lafiya ba ki yi bacci ba?" Aliyu na Uku ya faɗa bayan ya yiwa Maysun goodnight. "Nima abun da zan tambaye ka kenan Abbu hankalina ya tashi da na hango ka tsaye anan kana waya duba da dare ne yanzu, shi ne na fito na duba ka na ji abun da ke faruwa da kai da ya hanaka bacci musamman yau da kake cikin dimbin gajiya. Deep breath Aliyu na Uku ya sauke tare da faɗin "na kira Maysun ne don na ji lafiyarta. "Uhm! Abbu Dan Allah ka bi a hankali kada Ummie ta rutsa ka kana waya da wannan matar duba da yadda ka ce ba ka shirya bayyana ta wa family ɗinka ba. Abbu karka manta Ummie tana fama da ciwon damuwa (depression) idan har ta tsinci wannan labari daga sama komai fa zai iya faruwa da ita. Abbu ka tuna ummie ta kamu da wannan ciwon ne ta dalilinka ko sau ɗaya ne ka yi mata adalci, Ummie ta yi maka sadaukarwa da dama ta kaunace ka da dukkan zuciyarta ta ba ka yarda dari bisa dari kada ka rushe wannan yarda a lokaci guda idan maganganu na sun yi maka ba daɗi ka yafe min Abbu dukkan ku biyu ina so naga kun yi rayuwar farin ciki zamantakewar ku ta daidaita kamar na sauran ma'aurata. Na barka lafiya Abbu zan je na kwanta sai da safe. Daga haka Anaal ta juya zuwa ɗakinta Aliyu na Uku ya bi ta da kallo yana auna maganganun ta a mizani na hankali kafin ya juya shi ma ya koma ɗakinsa adaidai kofar shiga ɗaki ya kusan cin karo da Safiya ta farka bata ganshi ba shi ne ta fito ta duba shi da damuwa akan fuskarta take kallonsa tare da faɗin "Abbu na farka ban ganka ba shi ne na fito na duba ka ko kana buƙatar wani abu ne?" Kafe ta ya yi da idanunsa wani irin tausayinta ne ya yi masa dirar makiya, batare da ya bata amsar tambayarta ba ya rungumo kafaɗarta "mu je mu kwanta mar'atul saliha. Ya yi magana ƙasa-ƙasa murmushi kurum Ummie ta yi mai nuni da ta ji daɗin sunan da ya kira ta dashi. Rumaisa ita kadai ta yi girkinta hatta da Huwaila da ke taimaka mata cewa ta yi bataso ta yi tafiyarta, tana kammala wa ta zuzzuba a warmers ta kai dining room ta yi arranging table sannan ta wuce ɗakinta ta yi wanka, lokaci da ta cire pant ɗin jikinta ta ga babu ko digon jini wani irin farin ciki ne marar misaltuwa ya lulluɓe ta, ranta farin tass tayi wanka tsarki da tuna yau Aydah za ta karbi girki duk sai ta ji farin cikinta yana komawa ciki tana idarda sallah ta zauna ta tsantsara kwalliya ta Musamman, ta nufi parlorn Ab dawowarsa daga masallaci kenan ta shigo ya shaƙi daddaɗan ƙamshinta har sai da ya lumshe idanuwansa tana murmushi ta zo ta zauna kusa dashi, sai ɗaya ya kalleta ya kauda fuska ya yi kamar bai ganta ba dan har yanzu da raguwar haushinta daƙare a zuciyarsa. Yadda ya yi mata ba ƙaramin ɓata mata rai ya yi ba kwalliyar da aka yi domin ko kallonta bai yi ba ballantana ya yaba ta kuma san dalili bai wuce ƙi amincewa da ta yi da bukatarsa na cigaba da yiwa Aydah girki dare ya yi su shige ɗaki shi da ita gaskiya Abba Bashir bala'in ɗan raini wayau ne shi ko cewa ta yi za ta dinga yiwa Aydah girki ai shi mai yi mata faɗa ne domin kuwa komawa baya ya yi yawa. "Wai Habibina fushi kake yi dani? Don na ce ba zan yiwa wancan yarinya girki ba?" "Kwarai kuwa domin kin nuna min ban isa dake ba. "Ayya! Ai kuwa indai sai na yiwa Aydah girki ne za ka isa dani ashe kuwa kana da jan aiki a gabanka don ba zan taɓa yi ba daga nan har bayyanar Isah. "Ya ishe ki kada ki sake ki yi min rashin kunya kin dai ce ba za ki yi ba fine banaso kananun maganganu. Rumaisa ta taɓe baki tare da maida hankalinta akan wayarta sai da ta ji haushinsa da take ji ya sauka kana ta ɗago ta kalle shi tana faɗin "Habibi tashi mu je mu ci abinci ya kalleta ba. "A'ah! Me zai hana na kira ta ai cin tuwon kishiya ranko nima za ta biyani nan da ɗan wani lokaci. Ta ƙarashe magana tare da miƙewa ta nufi ɗakin Aydah batare da neman izini ba kanta tsaye ta tura ƙofa Aydah dake tsaye gaban dressing mirror tana shafa turare ta juya idanunta suka sauka kan fuskar Rumaisah, ranta ta ji yana ɓaci akan me za ta shigo mata ɗaki batare da neman izinin ta ba. "Idan kin ga dama ki fito mu ci abinci. "Idan kuma banga ni ba fa?" "Sai ki yi ta zama har a busa ƙaho. "Ai shi mijinki da ya aiko ki, ki kirani ba zai taɓa yarda hakan ta faru ba. Idan kuma kina so na cire miki tantama ki je ki ce masa ba zan zo ba. Kallon ta taɓe da baki Rumaisa ke yi tana mamaki yaushe wannan kwailar yarinyar ta yi bakin mayar mata da magana, dole fa ta zage damtse ta koya mata hankali idan bata nuna mata banbanci dake tsakani babba da yaro ba, ba za ta taɓa dawowa cikin hankalinta ba. "Ke ni kike gayawa magana ashe bakida kunya fitsararriya?" "Auu! Wai ke sai yau kika sani?Ai kuwa tuntuni banida kunya kece kaɗai ba ki fahimci hakan ba amma ai shi mijinki yasan wacece ni a fagge rashin kunya da fitsara har kyautar tsadaddiyar mota ya yi min akan iya rashin kunyata. Tuni Rumaisah ta gama fahimtar shagwabe ne Aydah take mata wanka mai kamar jirwaye ranta ya yi mugun ɓaci musamman da ta ambata mata motar nan da AB ya bata wacce tai mata tsaye a ƙahon zuciya, sosai idanuwan Rumaisa suka rufe ta yi kan Aydah tana zuwa ta ɗauke ta da mugun mari. Da Aydah ta kurma ihu sai da ga baki ɗaya amon muryarta ya karaɗe gidan da gudun bala'in Ab yake haura mattakalar bene ya shigo ɗakin a gigice. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. [1/31, 2:11 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye. 090. Aydah tana gani AB ya shigo ta daka tsalle ta yi faɗuwar 'yan bori idan wannan makircin ne ta daɗe da iya shi don haka take yiwa su Sadiya idan sun dake ta muddin tasan AB yana ga wuri har suman karya take yi, shi kuma ya bi ya gigice ya hau su Sadiya da duka sai Mami ta kwace su. Saboda haka Rumaisah batasan wacece Aydah ba shiyasa ta gwada marinta. "Wayyo! Wayyo Allahna na shiga uku idona aunty Rumaisa kin makanta ni Yayanmu kana ina Dan Allah ka zo ka cece ni aunty Rumaisah ta cire min idona. Abun da Aydah ke ta faɗa tana maimata wa tare da gunji kuka a rikice Ab ya zube guiwayoyinsa gabanta tare da kama fuskarta ya ɗago ta, ta wani runtse idanuwanta gan-gan wani irin mugun tsoro ne ya rufe shi, cikin masifa ya kalli gefen da Rumaisa take tsaye da sakakken baki tana kallon dramar queen don bata taɓa tsammani Aydah ta iya kalar wannan makircin ba. "Me kike mata ne Rumaisa? "Babu abin da na yi mata sharri ne kawai take so tai min. "Yayanmu bottle ɗin turare ta buga min a idona Dan Allah ka kira Daddy ya yi maka izini ka maidani gidan Mami, ba zan iya cigaba da zama anan gidan aunty Rumaisa ta ce sai ta kwakule min idanuwana. "La'illaha illallahu muhammadu Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam! Yaushe na fadi haka ashe yarinya nan munafuka ce ke ni za ki haɗa wa makirci?" Rumaisah ta yi magana tana zaro idanuwa tare da tafa hannuwa tsoron Allah ne ya lulluɓeta ashe kallo biri da take yiwa Aydah ita kuma tana mata na ayaba sai yau ta kara yarda da karin maganar nan da ake cewa bari raina kankantar allura ita ma ƙarfe ce ɗan hakki da kai raina wata rana shi ke tsone maka ido. "Ƙarya kike yi Rumaisa da gaske kin buga mata bottle ɗin iya sanina da baby Aydah bata ƙarya don haka idan wani abu ya sami idonta idan duk Afrika danginki ne sai na yi shari'a dake. Ya ƙarashe magana yana huci sosai hanta cikin Rumaisa ta kada tai mutuwar tsaye, AB ya ɗauki Aydah in a bridal style ya bi ta gefen Rumaisa ya fice daga ɗakin koda ya fito Huwaila tana jikin dauko car key, da sauri Huwaila ta zo dafa Aydah "Sannu Auta Allah ya saka miki. A hankali Aydah ta ware idanunta da ta rufe su gam ta kalli Huwaila tare da sakar mata murmushi tuni Huwaila ta harbon jirgin ta, zaro idanuwa Huwaila ta yi tana kallon Aydah footsteps ɗin AB a asibiti zai kaita ta kula da gida kamin su dawo ta amsa masa da to. Kaitsaye asibiti eyes care center ya wuce da ita aka duba idon nata tare da rubuta mata magani abun da ya ƙara harzuƙa Ab bai wuce yadda yaga idonta Aydah guda jini ya kwanta a cikinsa, saboda a ido mari same ta ransa ɓace suka dawo gida ga Aydah sai kuka take masa ita a dole gidan Mami za ta koma. Suna shigowa ya wuce ɗakin Rumaisa ya tarar da ita kwance akan sofa tana waya da aunty Raliya dan tun fitarsu ta daga waya ta kira aunty Raliya domin neman mafita akan tarkon da Aydah ta danna mata. Yadda ya turo ƙofa a fusace yasa Rumaisa ta katse wayar babu shiri ta miƙe zaune tana zarar idon. "Ashe Rumaisa ke muguwa ce bansani ba? Ashe ke ɗinan za ki iya kisan kai?" Rumaisa ta haɗiye wasu yawu kafin tattaro jarunta ta yafawa kanta cikin dakewar zuciya ta ce "Ka ga Habibi daina jifana da muguye kalamai yarinya nan muguwar makira ce daga na je na ce ta zo mu ci abinci ta hau ni da zagi ni kuma na ji ba zan iya jurewa ba na mare ta, amma da yake ita ɗin munafuka ce sai ta ce na buga mata kwalbar turare to wallahi-azim sharri tai min marinta kawai na yi. "To akan me za ki mare ta haifar ta kika yi ne ko me? Da za ki ware wannan ƙaton hannun naki ki mare ta dashi to wallahi karki kuskure hannunki ya sake sauka a jikinta. "Ko gobe tai min rashin kunya sai na hukunta ta don ba zan zuba ido yarinya ƙarama tana min rashin kunya ba in kuma ka gaji dani ne Habibi babu dole ka fito fili ka gayamin don haƙurina yana dab da ƙarewa, dan ina sonka ba shi ne zai ba ka damar ka dinga wulakanta ni ba. "Ai kin ji matsalarki ba damar a nuna miki kuskurenki za ki hau faɗar maganganu marasa kai balle kan gado, ni fa zalunci ne banaso. Yarinya nan tamkar amana ce agare mu dukka ita ce mai karancin shekaru acikin mu dole sai mun lallaɓa ta. "Kashh! Rumaisa ta faɗa cike da takaici tana dafe goshinta "wai kai Habibi da zarar an yi magana akan Aydah sai ka dinga faɗar yarinya ce yoo yarinya ce tasan ta kwana da namiji ko namiji shirgegen ƙato kamar ka. To na dawo daga rakiyar wannan kalma. "Yarinya ce mana akanki ke da an maki auren wuri ai da tuni kin haifi kamar ta. "Iyeee! Rumaisah ta faɗa tana zazzare idanuwa tare da dafe ƙirjinta "Habibi ka ji tsoron Allah ka dinga fadar abun da hankali zai ɗauka dukka guda nawa nake da zai haifi kamar Aydah. "Ai tsoron Allah ne yasa na fadi haka don ki kama girmanki kada 'yar cikinki ta raina ki. "To na ji idan ni 'yar cikina ce kai kuma jikarka don wallahi abin kunya Habibi akanka ya ƙare kai da ke shige wa ɗaki da ita. "To ai ni namiji ne daman can ba kunya ce dani ba. "Ai kuwa naga alama. "Na dai faɗa miki ki kama girmanki idan kika sake dukanta wallahi riƙe ki zan yi ta rama. Cikin kaɗuwa Rumaisah ta dafe ƙirji al'amari Ab ya fara bata tsoro zuciyarta ta shiga kissima mata shi ma ba banza aka barsa ba domin son da AB yake mata bana wasa bane a yau a waye gari yana gasa mata zafafan maganganu irin wannan da akwai alamar tambaya. Ya juya yana cigaba karkashin pillow ta runtse idanuwanta Ab ya ƙaraso ɗauke da sallama ya nemi kusa da ita ya zauna tare da riƙo hannunta "sannu Baby ya kike ji idon naki har yanzu yana miki zafi?" Ya yi magana cikin sanyi murya Aydah ta buɗe idanuwan nata tana faɗin "Da sauki Yayanmu yaushe za ka kaini gida?" "Baby ina tunani ai mun gama wannan maganar ko?" "Amman Yayanmu ka... "Baby please karki ɗaga min hankali mana na ɗaukar miki alƙawari ko ɗan yatsa Rumaisah ba za ta sake nuna ki dashi ba. Aydah ta turo baki ya saki hannunta ya kwanta kusa da ita ya wani rungumo ta cikin jikinsa kiran sallar magarib yasa shi fitowa daga ɗakin. ****** Sadiya tana kwance a ɗakinta damuwa yana neman ya yi mata yawa duk ta bi ta lalace kullum soyayyar Ab daɗa karuwa take yi a zuciyata, ba yadda bata yi da zuciyarta akan ta ji ta tsane shi amman hakan ya ƙi samuwa, tana so ta yakice shi daga cikin rayuwarta ko za ta huta da azabar da soyayyarsa ke jefa ta ciki. Mami da ta ji shiru yau duk Sadiya bata fito ƙasa ba ta bi ta a ɗakinta, yayin da Mami ta tarar da ita ranta ya yi mugun ɓaci tasan duk saboda wancan Abba ɗin ne take azabtar da kanta, ita kanta Mami a yanzu bata da buri da ya wuce Sadiya ta cire Abba daga rayuwarta tun da ya riga ya yi mata nisa. "Sadiya wai har yaushe za ki cire sakaran yaro nan daga zuciyarki?" Ni fa ko Aydah dake gidansa da kika ga na yi shiru na zuba musu ido ina jiran zuwa lokaci da zan raba shi da ita banaso Abba ba kuma zan so shi ba ko anan gaba saboda haka ki zuba ido kika yarda zan raba shi da ahalina rabuwa ta har abada. Sai da Sadiya ta ya mutsa fuska kafin ta ce "Mami na rasa wane irin so ne nake wa yaya Abba da har yanzu zuciyata ta kasa haƙura dashi. "Koma wane irin so ne ki fitar dashi daga zuciyarki shi ne kwanciyar hankalinki da nawa dukka domin ko kaɗan banaso naganki cikin damuwa. Wasu zafafan hawaye ne suka shiga bin kumatun Sadiya cike da tausayinta Mami ta rungume ta, tana rarrashinta yayin da can kasan zuciyar Mami take kara jin tsanar Abba tana ƙara kudurta ko ta hali yaya sai ta raba Abba da ƴaƴanta da mijinta. Huwaila ce ta yi musu dinner saboda Rumaisa ta ce ba za ta taɓa yiwa Aydah girki wannan yasa AB ya umarci Huwaila da ta yi musu kafin Aydah ta sami sauki idanunta ta zai saka ta a catering school ta koyi girke-girke. Lokaci da AB ya kira Rumaisa ta zo su yi dinner ta ce ta koshi saboda haka bai ya takura ta ba. Yana kammala kallon news ya kira Aydah a wayarsa ta zo ta sami shi a master bedroom ɗinsa ko kaɗan bata kawo komai aranta ba. Ta zura bedroom slippers ta yo ɗakin nasa koda ta shigo yana kwance daga shi sai boxer, duk yasan batada lafiyar idanu amma hakan bai sa ya kyaleta ba har sai da ya sami abun da yake so duk da Aydah ta ji zafi sai da ba kamar ranar farko ba, ta kuma dinga yi masa kukan dinkin ta shiyasa washegari ya ɗauke ta suka je asibiti aka duba wurin har ya haɗe Dr ta ce zai iya cigaba da shagalinsa amma ya dinga yi a hankali ko don duba da ƙarancin shekarun ta. Ai kuwa Aydah ta ji jiki don kuwa Ab bai yi mata da wasa ba yayin da Rumaisa ke nanniƙar baƙin ciki ta kagara ta karbi girki saboda tun ranar da ta yi tsarki ta koma shan magangunanta. Ranar da ta karɓi girki Aydah da Huwaila sun ga kwarkwasa da iyayi shiyasa Aydah tun da magarib ta shige ɗakinta ta rufe duk kiran da AB yake mata taƙi buɗe ƙofa. Rumaisah yadda taga AB bai nuna dokinsa a fili ba da sanarda shi ta sami lafiya, sai tasha jinin jikinta bata raina kanta ba sai da suka haɗu a shimfiɗa round ɗaya ya yi ya mirgina gefenta yana sauke numfashi kafin kuma ya shiga yi mata korafi "Gaskiya Rumaisa ki rage cushe-cushe da kike yi idan na zo shiga wurin ina ji wa kaina rauni kada garin gyara gira arasa ido don haka ina shawartaki da ki daina don ni ake yi na ce banaso. Yana karashe magana ya tashi ya shigewarsa bedroom ya bar Rumaisa da sakakken baki, kuka za ta yi ko kuma masifa za tai masa ta ma rasa abun yi me wannan kankanuwa yarinya tai masa ne da ya canza lokaci ɗaya. *BAYAN SATI ƊAYA* Gidan AB ga baki ɗaya ya dawo tamkar sansanin yaƙi tsakani Rumaisa da Aydah babu zaman lafiya musamman yanzu da Rumaisa taga AB ya saka Aydah catering school tana zuwa ta fara koyi girke sai ta bi ta tashi hankalinta da zarar taga Aydah kitchen za ta ƙiƙƙire fitina a tsakaninsu, yayin da ita ma Aydah yanzu ta iya tana ce mata kul za ta ce mata ass! AB kullum cikin sulhu yake. Yau gidan shiru kowacce tana ɗakinta Huwaila kuma ta tafi kasuwa Sadiya ta yi horn maigadi ya buɗe mata gate ta nemi wuri ta yi parking, haka kawai tana school ta ji kewar Ab tana neman tai mata illa ta je office ɗinsa secretary ɗinsa ta ce mata yana gida don ita a tunaninta yana gidan ɗin batasan cewa sun ya fita shi da Abdulkarim wurin sabgogin su. Hankali kwace Sadiya ta tura ƙofar main parlor ta shigo ta tsaya tana ƙarewa parlor kallon kafin ta ja guntun tsaki, kanta ta haura upstairs parlorn Ab dake sama ta nufa batare da neman izinin ba ta tura ƙofa ta shiga gani baya cikin parlor ta wuce master bedroom ɗinsa anan ma bata gansa ba ita ce har da dubawa bathroom rashin ganinsa yasa hankalinta ya yi mummunan tashi zuciyarta kamar za ta faso ƙirjinta ta fito. Tana fitowa daga ɗakin suka kusan ci karo da Aydah wacce tana ɗakinta ta tuna da kafin Yayanmu ya fita ya ce ta canza mishi bedsheet shi ne ta zo ɗauke da bedsheet ɗin a hannunta kallo-kallo suka shiga yiwa junansu kafin a fusace Sadiya ta ce "Ke ina Yayanmu? Kallon kin ma raina min da hankali Aydah ta yi mata ta ja guntun tsaki gami da faɗin "Gashi nan goye a bayana. "Jar ubanan! Aydah ni kike yi wa baƙar magana?" "Wacece ke Sadiya da ba za a gayamiki baƙar magana ba?" Da fari ma me ya shigo dake ɗakin mijina me kike nema?" "Sadiya! Aydah sunana kika kira gatsal ba ko yaya. Sadiya ta yi magana fuskarta cike da mamaki tana kallon fuskar Aydah wacce sai kallon banza take aika mata dashi. "Kin ga baiwar Allah ka ma hanya ki fice mana daga gida tun kamin na tata miki rashin mutunci ke yanzu ko kunya bakya ji ki ɗebo jiki ki zo har turakar mijin ƙanwarki. "Aydaaah! Sadiya ta kira sunanta cikin shouting daman kafin ta zo gidan tasha tortulin ɗinta kan nan nata sama-sama take jin sa. "Na'am! Aydah ta amsa tana kallonta a ɗage "Wallahi ba ki isa ba ki wulakanta ni karki manta kamin Yayanmu ya aure ki ni ce ya fara aure kamin ki shigo gidanan ki zauna cikinsa, har ki amsa sunan matar gidan ni ce na fara amsa wannan sunan, saboda haka ki dawo cikin hankalinki ki san da wacce kike magana kada rudin kuruciya ya ɗibe ki faɗa min maganar da za ta harzuƙa ni na yi miki shegen duka a gidanan babu uban da ya isa ya kwace ki hannuna. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. [2/1, 12:50 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 091. Kallon amma bakida hankali Aydah take yi wa Sadiya kasa ɓoye mamakinta ta yi har sai da ta furta "Duka fa kika ce Yaya Sadiya? Ki zo har cikin gidan mijina cikin ɗakinsa kuma ki dake ni en gaskiya bakida hankali yaya Sadiya kina bukatar gani psychiatrist. Aydah tana dasa aya Sadiya ta ɗauke ta da mari ita ma Aydah bata yi kasa da gwiwa ba ta rama marinta, hakan ne ya fusata Sadiya ta rufe Aydah da duka abun ka da karfi ba ɗaya ba sosai take dukan Aydah kamar ba ƙanwa ta da suka fito ciki ɗaya ba. Ihun Aydah da Rumaisah ta ji yasa ta fitowa da gudu sai ta ji ihun yana fitowa daga ɓangaren Ab sai ta taka birki tana zaro idanu a tunaninta Ab ne yake dukan Aydah nan da nan daɗi ya lulluɓeta ta baza kunnuwa tana ji yadda Aydah ke ihu ga kuma ƙarar fashewar abubuwa da take ji, sai kuma ta ji zuciyarta ta karaya lallai duk laifin da Aydah ta yi wa AB yake mata Irin wannan dukan fitar rai ba ƙaramin laifi bane, idan har bata je ta kwance ta hannunsa zai iya kashe 'yar mutane iyayenta ba za su kyale shi ba tunawa da ta yi hakan zai iya zama silar rushewar rayuwarsa, yasa ta ruga da gudu ta shiga ɗakin turus Rumaisah ta yi tana kallon ikon Allah wanda ya fi gaban mamaki Sadiya ta sheƙewa Aydah wuya da dukkan hannayenta ga Aydah kwance ƙasa wanwar numfashinta yana ƙoƙarin fita daga jikinta, Rumaisah kamar wacce aka mintsina ta ruga ta yi kan Sadiya ta cafke wuyanta ita ma ta shaƙe ta da ƙarfi "Cika ta ko nima na kashe shi shegiya baƙar azzaluma ƙanwarki uwa ɗaya uba ɗaya ce kike neman rayuwarta ke kan wacce irin zuciya ce dashe a cikin ƙirjin ki?" Rumaisah ta faɗa cikin tashin hankali, zafin shaƙar da Rumaisah ta yi wa Sadiya yasa ta saki wuyan Aydah wacce tuni ta galabaita sai faɗa ya dawo tsakanin Sadiya da Rumaisah, dukan junansu suke yi kamar za su kashe juna Aydah dai tana kwance tana kallonsu tare da sauke wahalallen numfashi. Tun daga upstairs suke suna dambe har suka sauko ƙasa duk sun ji wa junansu rauni, da Sadiya ta fusata sai ta shiga kitchen da gudu ta dauko wuƙa Rumaisah tana gani ta nufo ta da wuƙa gadan-gadan ta kwasa da gudu ta shiga ɗaya daga cikin dakuna dake downstairs idan Allah ya taimake ta akwai key a jikin ƙofar ta rufe. Sadiya ta dinga ihu haɗe da dukan kofar tana faɗin sai ta kashe su dukka biyu dole Ab ya aureta Ab nata ne ita kadai, bata bambanci da mahaukaciya sabon kamu, Aydah da ta ji ɗan kuzari ya zo mata ta miƙe da kyar da nufi ta sauko ƙasa taga abun da ke faruwa saboda yanzu ihun Sadiya kaɗai take ji, tun kafin ta karasa sakkowa ta hango Sadiya da wuƙa tana faɗin Rumaisah ta buɗe ƙofa yau sai ta kashe ta. Wani wawan birki Aydah ta taka, ta juya ta koma ɗakin Ab ita ma ta datse ƙofa wani irin tsoron Sadiya ne ya baibaye tunawa da ta yi Sadiya ta taɓa attempting kashe yayansu ta kuma taɓa yi wa Rumaisah mummunan rauni don haka kisa ba bako abu bane a wurinta. Sadiya da ta gaji da dukan kofar ta jefar da wuƙa fice a compound ta ci karo da Huwaila hannunta ɗauke da ledoji da ta yo cefane, Sadiya ta gallawa muguwar hararar yayin da Huwaila ta bi ta kallon tsoro a rikice Huwaila ta nufi entrance tana sauri kamar za ta kife ƙasa. Ɗakin Aydah ta fara zuwa ta duba taga bata ganta ba, ta sake fitowa tana kwallawa Aydah kira Rumaisah ta buɗe ƙofa ta leƙo cikin parlor taga Sadiya bata nan Huwaila ce kaɗai a tsaye tana kiran sunan Aydah, da sauri Rumaisah ta fito tana faɗin "Ina Sadiya?" "Yanzu nan ta fita na haɗu da ita a compound. Huwaila ta faɗa cikin sanyi murya gaba ɗaya hankalinta yana ga Aydah tana tunani ina ta shiga ne. Rumaisah ta haura upstairs ta nufi ɗakin da Aydah take ta ji a rufe ta kwakwasa haɗe da kiran sunan Aydah "Aydah idan kina ji na ki taso ki buɗe ƙofa Sadiya ta tafi. Adaddafe Aydah ta taso ta buɗe ƙofar wuyanta jin sa take yi tamkar an ɗaɗɗaure mata shi ga maƙoshinta sai raɗaɗi yake mata. Karo na farko a rayuwar Rumaisah da ta ji tausayin Aydah ya kamata da sauri ta kama kafaɗarta suka sakko ƙasa Huwaila tana gani halin da Aydah take ciki ta kara rudewa gaba ɗaya fuskar Aydah ta kumbure Rumaisah ta zaunar da ita akan kujera ta ce Huwaila ta je ɗakinta ta dauko mata wayarta, da sauri Huwaila ta je ta dauko ta kawo mata ta kira Ab ta faɗa masa abun da ya faru "Da bacci nake yi Habibi sai da ka dawo ka tarar da gawar Aydah dan kuwa sheƙe mata wuya ta yi bayan ta yi mata ɗankaran duka, nima ba ka ga yadda ta yi min raunuka a jikina ba. Ya dai kamata ka ɗauki mataki akan Sadiya wannan abu da take yi mana ya yi yawa duk sanda ta sha kayan mayenta ta zo ta sauke haukarta akan iyalinka. Tun sanda Rumaisah ta fara magana zuciyar AB ke bugawa bai ce mata komai ba ya kashe wayar ransa ɓace ya kalli Abdulkarim dake zaune kusa dashi a mota daman suna kan hanyar zuwa gidan su Abdul ɗin zai sauke shi, shi kuma ya nufo gida kiran Rumaisah ya shigo wayarsa ya kwashe labari abun da ya faru ya fadawa Abdulkarim. "Gaskiya a wannan karo nima ina goyon bayanka da ka ɗauki mataki akan Sadiya hauka take yi da za ta dinga zuwa har cikin gidanka tana dukan matanka, kanta aka fara shaye-shaye ne ko me?" Sai da AB ya yi ƙwafa kafin ya ce "Ka barni da ita wallahi sai na nunawa Sadiya ita ɗin ƙaramar 'yar iska ce sai na yi mata abun da ko sunana ta ji sai gabanta ya faɗi ƙarya iskanci take yi. Ya ƙarashe magana ransa na ƙuna. "Da dai yafi gara ka nuna mata kuskurenta. Ak ya faɗa daidai suna isowa ƙofar gidansu suka yi sallama da ab kaitsaye Ab gida ya nufo yadda yaga fuskar matansa duk zane faratan Sadiya ne ya yi bala'in harzuƙa shi musamman fuskar Aydah da ta kumbure sutum! Dukkansu sai ya kwashe su zuwa asibiti aka duba su tare da rubuto masu magani. Sai bayan ishaa Ab ya sami zuwa gidan Mami, koda ya shiga babban parlon Sadiya da Siyama suna zaune suna kallon India series. Ya yi sallama fuskarsa a haɗe sallamarsa kaɗai da Sadiya ta ji sai da hanji cikinta ya hartsune, ta ji gudawa tana so kamata. "Barka da dare Yayanmu. Siyama ta faɗa da murmushi akan fuskarta. Yadda ran AB yake a ɓace baya tunani zai iya amsawa Siyama, kan Sadiya ya yi yana zuwa ya ɓalla mata mari, har sai da ta fado daga kan kujera, daidai Mami tana sakkowa daga bene "Kai Abba kanka ɗaya kuwa me ta yi ma da za ka mare ta?" Mami ta faɗa a fusace Ab ya ɗaga kai ya kalleta kamin ya dawo da ganinsa kan Sadiya ya kama hannunta ya ja ta da ƙarfi dole ta miƙe tsaye ya nufi ƙofar fita janye da ita cikin sauri Mami take tattaka mattakalar bene tana faɗin "Kai don ubanka ina za ka kai min yarinya Abba dawo min da 'yata na rantse idan wani abu ya same ta sai na yi shari'a da kai shegen yaro watsatse. A daidai ƙofar fita Ab ya tsaya a juya yana kallon Mami da fusatattun idanuwansa "Ga watsatsiya nan kin haifa Mami wannan da kike gani wata rana sai ta dauko miki bala'in da masifan da sai kin yi Allah wadarai haifar ta da kika yi. Daga ke har ita a sannu za ku girbi abubuwan da kuka shuka. AB yana gama faɗar haka ya juya ya buga ƙofar da ƙarfi yana cigaba da jan Sadiya kamar tinkiya, maganganu da AB ya gayawa Mami yasa ta yi mutuwar tsaye ta kasa bin sa, Siyama ta tashi ta bar cikin parlor ta wuce ɗakinta. Ta bar Mami tsaye cikin jimami. Da ƙarfi AB ya jifa Sadiya cikin mota ya shiga ya ja Balmo maigadi ya buɗe masa gate, yadda yake sharara gudu akan titi kaɗai ya isa ya jefa wa Sadiya tsoro, amman ita ko a jikinta sai ma kwantawa da ta yi jikin seat hakan da ta yi ya kara linkawa Ab ɓacin ransa ji yake yi zai iya kakkarya kasusuwan jikinta. Kaitsaye office ɗinsa ya nufa ya yi parking ya fito tare da fizgota ta fito kanta daga ita sai riga da wando na bacci kanta dauke da hula bata da takalmi a haka ya ja ta zuwa office ɗinsa securities ne kaɗai a cikin company. Yana buɗe kofar office ɗin ya tura ta da ƙarfi har sai da ta faɗi ƙasa ya maida kofar ya rufe, Sadiya ta miƙe tsaye tana kallonsa yana warware belt ɗin jikinsa ta sakar masa murmushi nan da nan ya ƙara harzuƙa ya zare belt ɗin a mugun fusace ya yi kanta ya dinga zuba mata duk duka da yake mata tsaye kawai take ta runtse idanuwanta gam! Da Ab ya gaji da dukanta da belt ya kama wuyanta kaita jikin bango ya shaƙe ta sosai tsabar taurin kai irin na Sadiya ko gizau bata yi ba sai ma ta kalle cikin idanunsa da shaƙaƙƙiyar muryarta ta ce "Zan yi farin ciki da zan mutu a hannun masoyina. AB ya ƙara hasalewa da jin furuncinta ya shiga wanke mata fuska da maruka duka sosai ya yi mata bana wasa ba duk ya farfasa mata jiki fuskarta ta kumbura saboda mari bakinta da hancinta yana zubda jini, amman ita ko a jikinta, sai ma maganganu banza da take faɗa masa. "Ka sani Yayanmu wannan duka da ka yi min babu abun da ya rage na daga dimbin son da nake maka asalima ƙara min sonka ya yi yanzu na daura damarar yaƙi da shegun matanka sai na yi ajalinsu dukkan su ba wacce zan bari a raye. Wani irin zuba mata ido Ab ya yi anya kuwa Sadiya bata samu matsala a ƙwaƙwalwarta ba. Ya dubi irin mugun dukan da ya yi mata amman bakinta bai mutu ba a duniya nan me zai yi mata da zai sa ta tsane shi ta fita daga rayuwarsa dukka. Ya tuna da wuƙa da ya dauko daga gida wacce ya yi kudirin ya tsorata ta da ita, a fusace ya zaro ta daga aljihun wandonsa ya fizgo ta, ta miƙe tsaye ya ɗora wuƙar a wuyanta cikin zare idanuwa cikin kakkausar murya ya ce "wannan shi ne kashedi na, na ƙarshe dake idan har kika kuskura hannunki ya sake sauka a jikin matana sai na shayar dake zallar mamaki. Kin ga wannan wuƙar da ita zan daddatsa naman jikinki na yi gunduwa-gunduwa da sassan jikinki ina tabbatar miki ko sallah ba za ki samu ba. Ba dai taƙamar ki taurin kai ba to nine Babanki a taurin kai. Jin abun da ya faɗa yasa Sadiya ta sheƙe da dariya tana kallonsa tana dariya abinta kai da gani wannan dariya da take yi kasan babu lafiya Ab ya rasa yadda zai yi da ita wani tunani ne ya fado masa shi ne kadai hanyar da zai bi ya kawo ƙarshen iskancin Sadiya. A fusace ya sake kama hannunta ya ja ta suka fito daga office ɗin suna tafe Sadiya take faɗin "Wai kana nufi Yayanmu har ka gama hora ni kenan? Dan Allah mu koma ciki ka cigaba da dukana har sai garin Allah ya waye hucin kaɗai yana haifar min da natsuwa a duk sanda hannunka ya sauka a jikina da sunan duka sai na ji wani irin daɗi yana lulluɓe ni. Ina sonka Yayanmu wallahi ina bala'in sonka Dan girman Allah ka saki shegun matanka ka aure ni ni kaɗai na isheka rayuwa. Tsabar takaicinta da ya gama cika Ab bai sake kula ta ba har suka iso ƙofar gidan Mami ya buɗe kofar mota ya fito ya zagaya wurinta ya ɓalle ƙofa ya daka mata tsawa "fito! Sadiya ta fito tana cigaba da tsoki burutsunta wanda Ab ya ma daina fahimtar me take cewa ya ja motarsa ya yi gaba Sadiya tana shiga main parlor ta tarar da Mami ta kai gwaro ta kai mari. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. [2/1, 12:51 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 092. Shiru Hajiya Zeenah tayi tana kallon Mami,dake mata bayani with shock har lokacin kuma taki tace komai. "Zeenatu kina jin ina maki bayani bakice komai ba. Mami ta faɗa cikin rawar murya,Hajiya Zeenah ta sauke ajiyar zuciya tana faɗin."to me kikeso nace Hajiya mariya bakya jin magana bakya bin shawara duk yadda mutum ya kawo maki shawara bakya dauka sai kinga dama. Ya kikeso nayi mun fi wata ɗaya da zuwa wurin mutumin nan da sunan zaki haɗa kudi ayi maki aiki shiru akeji, na tabbata bazaki rasa miliyan guda ba sai idan baki da dama bayarwa ba. "Wallahi-tallahi Zeenah tun lokacin na faɗa maki kudin dake cikin account ɗina bai kai miliyan ɗaya ba. "To wai ba kina da kaddarori ba? Mariya ki daga sarkarki ta zinari ki saida ayi aikin nan kema wallahi wata rana kin fiye son abun duniya. Shiru Mami tayi kafin ta sauke ajiyar zuciya tana faɗin. "In sha Allahu yanzun nan zan je na daga ɗaya daga cikin sarqoqina na sayar idan ma bamu samu tafiya yau ba sai gobe ki yi sammako mu tafi wallahi jiya banyi barci ba akan dukan mutuwar da Abba ya yiwa Sadiya ya tsaya min arai kuma babu damar na yiwa mahaifinsu bayani zai fara tambayar ina Sadiya ta haɗu da Abba laifi me tai masa kinsan dai halinsa da tambayar kwakwafi. Dole sai ya ji dalilin da yasa yayi mata wannan ta'asar ke yanzu ta kai ta kawo fa ko amsa gaisuwar Sadiya baya yi kiri-kiri ya cire hannunsa akan lamarinta duk akan shegen yaro nan. Alhaji Sanusi dake labe tun ɗazu yana jinsu ya saki wani murmushi kafin ya turo kofar ɗakin batareda an basa izinin shigowa ba,daga matarsa har Mami kallonsa suke ya zauna kan Soofa yana murmushi mami ta gaishesa da respect ya amsa yana tambayarta gida da yara ta amsa masa da duk suna lafiya. Sai kuma yayi fuskar tausayi yana kallon mami "ai wallahi Hajiya mariya ina gayama maki in har yaron nan bai bar cikin rayuwar yaya na har abada ba ba za ki taɓa farin ciki ke da alhalin ki ba. Baki ga nima yanzu komai na yayan ba sani nayi ba ai idan kin lura ko gidanku na rage zuwa. Mami ta sauke ajiyar zuciya tana faɗin."hakane Alhaji Sanusi ka kam rage zuwa,wannan karon ko na dauki alwashin idan komai da na tara zai kare sai Abba Bashir yabar rayuwar mu na har abada. "Hakan shi ne daidai kuma babbar mafita agareki, ba za ki raina kanki ba sai yaya ya faɗi ya mutu duk dukiyarsa tana hannun Abba ga kuma Aydah ya aure shi kadai zai mallake komai ke da yaranki za ku koma 'yan kallo. "In shaa Allahu hakan ba za ta taɓa faruwa ba inda karfina ya ƙare. Har mota Alhaji Sanusi da matarsa Hajiya Zeenah,suka raka Mami suna kara cusa mata kiyayyar Abba Bashir muraran. Koda Mami ta koma gida ta samu kanwarta Safeena ta je daman sunyi waya da safe ta faɗawa Safeena idan tana da lokaci tazo zasu yi magana mai muhimmanci,lokaci ɗaya Mami ta saki fuska ta karasa cikin parlor tana gaisawa da kanwarta, "hope baki dade da zuwa ba.? "A'ah! banji ma ba kam dan na kira wayarki a kashe. "A gida ma nabar wayar tunda nasan ba dadewa zan yi ba na saka caji.l sai kawai na kashe kar ayita kira bana nan. Da haka Mami taja kanwarta suka wuce cikin master bedroom ɗinta,bayan sun zauna Safeena ta kalli yayarta dauke da damuwa a fuskarta take faɗin."Na shiga ɗakin Sadiya ita kadai ce a gida mai aiki ta faɗa min Siyama ta tafi school. Yaya anya Sadiya akwai zuciya a kirjinta kuwa kan wani ɗa namiji take kokarin ta lalata rayuwarta a banza a wofi menene ribarta ?"ita ko Aydah akace ta mutu ace Abba ,ya aureta zai yarda ya aureta, ni na dauka tabar halin nata ashe sai abun da ya cigaba harda ke dake daure mata ki bani ita na sati ɗaya na gyara mata zama dan ni kam ba zan dauki wannan Kananun Iskanci na sadiya ba. Ita ko karatun taki tsayawa tayi samarin ma ta daina kulasu gaba baki ɗaya ta lalata rayuwarta. Lokaci ɗaya Mami ta ɗan haɗe fuska dan ita bata kaunar taji ana aibanta Sadiya agabanta nan take za taji ranta ya ɓaci "kin manta shi wanda kike zance akansa duk shi ya sakata cikin wannan ƙaddara. "Amman yaya har da son ran Sadiya akan ɗa namiji marar tabbas za ta dinga shan kayan maye akan me sai kace.... "Kin ga dan Allah muyi abun da ya kawoki malama karki batamin rai. Shiru Safeena tayi tana kallon yayar tata kawai. Fuskar Mami a tanke ta ce "Daman iyayen yaron dake neman auren Siyama suke so a saka masu rana Jibi zasu zo da kayan lefe da kuɗin saka rana. Ni bama wannan ba babban damuwa na shirun da Daddynsu yayi ya sakawa Sadiya ido ina tsoron ya je ya samo mata wanda bata so tunda ita taurin kaine da ita taki tsayawa ta kwantar da hankalinta tama kula samarin dake nemanta. Ke kin san da an sakawa siyama,rana babu makawa har da na Sadiya. Aunty Safeena da ta gama sauran Mami ta sauke numfashi tana kallon Mami kafin tace "to ke yanzu menene mafita?"da gaske yaya ya kamata ace Sadiya na gidan aurenta tuntuni Amman da yake taurin kaine da ita sai gashi wanda taso kashewa ta dawo kuma Allah ya jarbceta da mugun sonsa. "Ni ina da wata shawara. Da sauri Aunty Safeena tace "wace irin shawara kenan? "Me zai hana mu haɗa Sadiya da Jamal aure?" tunda Aydah Allah bai yi zai sameta ba. Kin ga asirin mu a rufe daga Jamal har Sadiyar babu wanda ba zai ƙi bin umarninmu ba. baki buɗe Aunty Safeena,ke kallonta tamkar bata fahimci me Mami ke faɗa ba. "Ban fahimci zancenki ba yaya mariya kina nufin a haɗa Jamal da Sadiya aure? "ehhhh haka nake nufi Safeena,ko bai yi maki bane.?"naga duk kin birkice ne lokaci ɗaya,wani ja'irin murmushi kurum Aunty Safeena tayi tana faɗin."kina ganin wannan auren zai yiwu tsakanin Jamal da Sadiya shi zuciya ita zuciya suna ganin ai sha'anin juna ne ya za'ayi suyi aure tsakaninsu kuma ma Jamal bai gama makaranta ba akwai shekara ɗaya a gaba kin manta ne?"kuma kin san mahaifinsa ba zai yarda yayi masa aure yanzu ba. Tun sanda Aunty Safeena ta buɗe baki tana magana Mami,ke kallonta har ta kai karshe. "Aure yana hana karatu ne Safeena?"ina jin ko anyi auren zai ci gaba da karatunsa ni banga wani abun daga hankali ba. "To yaya Allah yasa mahaifin Jamal da shi kansa Jamal ɗin su amince. "Jamal nasan bai da matsala mahaifinsa ma na tabbata idan yaji Sadiya ce ba zai ƙi amincewa ba sai dai kawai idan akwai wani nufi a zuciyarki Safeena.! Da sauri Aunty Safeena ta girgiza kai tana kallon Mami take faɗin "Ni babu komai a zuciya ta duk yadda muka yi zan kiraki. Da haka Aunty Safeena ,ta dauki jakkarta ta yiwa Mami,sallama Mami ta bin kanwartata da kallo kurum Har ta fice daga dakin. Sai da Aunty Safeena tabar gidan ta saki wani dariyar rainin hankali lallai yayarta ta ta samu tabin hankali da alama, idan ba tabin hankali ba taya zata haɗa Jamal da Sadiya?"ae Sadiya ba sa'ar aurensa bace yarinyar dake shaye-shaye take da tabin ƙwaƙwalwa haka kawai zata wani zo da zancen da hankali ba zai dauka ba. Tana komawa gida ta dauki waya ta kira Jamal,cikin basa umarni take faɗin duk inda yake yazo yanzu ya sameta jin yanayin muryar mahaifiyarsa kamar ba daidai ba yace "lafiya mum?"a fusace Aunty Safeena ke faɗin."Dan Allah ka zauna karka zo tun da har sai na faɗa maka dalilin kiran ka. Ta faɗa so pissed up a muryarta tana sauke wayar Jamal bai fi minti talatin ba ya ƙaraso gidan nasu duk hankalinsa a tashe ya zata wani mummunan abu ya samu mum,har ɗaki ya sameta ya zauna yana kallonta ita ma zaunawa tayi fuska babu walwala take faɗin "kana jina Jamal.? "Eh! Ina jinki mum. "sauran kwana nawa hutun naku ya ƙare?" "Akwai kusan sati biyu fa lafiya wani abu ya faru?" "Daman so nake yanzu ka dauki waya ka fara booking ɗin flight ka tattara ka koma makaranta ka karasa hutunka acan. Da mamaki yake kallon mum, ɗin tasa kamin ya furta "mum wani abune ya faru ?" Ai na faɗa maki fa akwai sauran sati biyu a gaba. A mugun fusace Aunty Safeena ta katsesa tana wani zare masa ido tana faɗin "kawai kayi abun da nace. shi dai kallon mum ɗin tasa kawai yake yi yana mamakin ta. "To mum,me zan faɗawa Abba kuma.?"kai kasan yadda za kayi dashi. Magana ta biyu ko bayan ka tafi yaya mariya ta kira wayarka tayi ma magana kana da sha'awar auren Sadiya kace kana da wacce kakeso acan familyn babanka. Da sauri Jamal ya kalli mum da mamaki yake faɗin."mum naji kamar kin ce Sadiya, faɗamaku aka yi dama akwai wani abu tsakani na da ita ne ko me?" Nan mahaifiyarsa tayi masa bayanin kudurin Mami wani dariya Jamal ya fashe dashi yana faɗin."lallai ni za'a haɗa da yar shaye-shaye da kurciyarta.?"ko na rasa matar aure Sadiya ba sa'ar aurena bace bata cikin zubin kalar matan da nakeso ,ko ita Aydah na haƙura da ita ina da kishi ba zan iya auren ƙaramar bazawara ba ragin wani ba. murmushi mum tayi daman tasan halin Jamal ba yadda za a yi ya yi na'am da wannan zancen na Mami. "Banda dai son kai irin na yayarta ina Jamal ina Sadiya. Sai da yamma Mami,ta dauki ɗaya daga cikin sarqoqinta na zinari ta tafi shago aka auna aka bata kusan dubu dari biyar,ta account ma aka tura mata kuɗin gobe idan zasu je wurin Malam sai ta ciro su je dasu. Bayan sallah ishaai sun kammala cin abincin dare Daddy ya koma parlor sa ya dauki wayarsa ya kira AB cike da girmamawa Ab ya gaishe da Daddy, Daddy ya amsa yana tambayarsa gida da kuma iyalinsa. Cike da jin kunya Abban yace duk suna lafiya nan Daddy ke sanar dashi zancen auren Siyama, sosai Abba Bashir yayi farin ciki kana ya yiwa kanwar tasa addu'ar fatan alkhairi da haka Daddy ya katse wayar yace sai sun haɗu gobe a office su ƙara tattaunawa. Siyama, Daddy ya kira a waya yace ta kira masa Sadiya. Siyama dake zaune a parlor tare da Mami,ta kalli Mami da sauri ganin irin kallon da mami keyi mata yasa ta saurin sadda kai ƙasa Mami tace "waye ya kira ki a waya.?" "Daddy ne wai nayi masa kiran yaya Sadiya. Jin abun da Siyama ke faɗa yasa gaban Mami yayi mummunan bugawa, Siyama batareda ta kula da yanayin da Mami ta shiga ba ta nufi up stairs dan kiran Sadiyar zaune ta samu Sadiya da waya a kunnenta da alamar waya take ,tana jin anyi knocking kofar ɗakin daman ta katse kiran, tayi gyaran murya, Siyama ta shigo ɗakin a bakin kofa ta tsaya tana kallon Sadiyar da ta zama wata iri. "ki je Daddy na nemanki a parlorn sa. Da haka Siyama ta juya ta rufewa Sadiya kofar ,wani irin tsoro na ban mamaki Sadiya ta shiga lokaci ɗaya hankalinta ya tashi ta shiga haɗa zufa duk Ac dake cikin ɗakin zufa take yi tashin hankali ya bayyana ƙarara akan fuskarta "na shiga Uku!"me kuma zai sa Daddy ya nemeta ko dai yaya Abba ya kawo masa ƙararta ne ya faɗawa Daddy ta je gidansa ta hau matansa da duka. Babu kalar tunanin da Sadiya bata yi ba duk hankalinta a tashe yake. Hijab ɗinta na sallah ta dauka har kasa ta saka akan kayan baccin dake jikinta ta nufi kofa Mami dai sai bin ta take da kallo har ta shige parlorn Daddy da sanyi murya tayi sallama." Ciki-ciki Daddy,ya amsa sallamar Sadiya ko shi dan tazamar masa dole ne adaddare Sadiya ta zauna kan rug cikin rawar murya ta gaisheda mahaifinta tana saukar da kanta kasa bai saurari gaisuwar da take yi masa ba yace "kina da labarin nan da kwana biyu za'a kawo kudin saka ranar siyama da kayan lefenta na jiki shiru har yanzu?"maganata tana nan babu fashi keda Siyama zan aurar a rana ɗaya,wani irin tashin hankali Sadiya ta shiga lokaci ɗaya cikin rawar murya Sadiya ke faɗin "Ni fa Daddy har yanzu bani da tsayayye why not a fara yin na Siyama, ɗin in yaso daga baya ayi zancen nawa. A mugun fusace Daddy ya dakatar da ita yana wani daka mata tsawa. "me na faɗa maki a kwanan baya huhh?" Idon Sadiya har sun tara kwallah ta fara yi wa Daddy rantsuwa ita fa yanzu babu wanda ke zuwa wurinta. "Da kyau tau naji ni zan nemo maki miji da kaina. A wani irin firgice ta daga kai tana kallon mahaifin nata babu alamar wasa a kalamansa tuni hawaye suka fara gudu cikin fuskar Sadiya wani irin kalar tashin hankali ta ji yana zagaye zuciyarta tasan tabbas tunda mahaifinta ya yanke hukunci babu wanda ya isa ya canjasa muryar Daddy,ta ji yana faɗin "tashi ki bani wuri. A wani irin gigice Sadiya ta fito parlorn mahaifin nata hankalinta tashe tayi wurin Mami tana kwala mata kira tana gunji kuka. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO [2/2, 10:15 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 093. Mami !!Mami!!"Sadiya take kiran sunan Mami agigice, yanayin yadda take nufo Mami,cikin fita hayyaci yai bala'in tsinka zuciyar Mami da sauri ta tash ta nufi Sadiya tana ƙoƙarin riƙota zubewa kawai Sadiya tayi akan rug tana ƙara sakin wani sabon kuka mai fitowa tun daga ƙarƙashin zuciyarta, tana jin yadda zuciyarta ke wani irin zafi tana tuna yanayin yadda Daddy ke mata magana tasan waye mahaifinta dakyar idan ba sadaka zai bai wa wani ita ba. "kiyi min bayani duk kin bi kin gigitani me Daddyn naku yace maki?ita dai Siyama tana zaune a parlor har lokacin tana danna wayar hannunta tamkar bata cikin parlor."Mami da gaske Daddy sadaka zai yi dani kiyi masa magana wallahi da gaske nake ya Mami ba zan iya zaman aure da kowane namiji ba idan ba yaya Abba ba,kiyi masa magana yadda zai fahimceki. "shi Daddyn naku ne yace aure zai yi miki?" Mami ta faɗa da wani tashin hankali kwance cikin fuskarta. "Haka ya faɗa yace babu fashi tare za'a saka mana rana da Siyama. Wani zufa Mami taji tana haɗawa ta kalli sadiya a gaggauce tace ta taso su je ɗaki daman akwai maganar da za suyi dakyar Sadiya ta miƙe tabi bayan Mami,tana jin yadda kwakwalwar kanta ke wani irin hargitsewa tana bukatar jin kanta sama na ɗan wani lokaci,da wani irin kallo siyama,ta riqa bin Mami daita da Sadiya. Mami jin tayi kamar idanun Siyama na yawo akansu sai taji jikinta yayi sanyi ɗan juyawa tayi tana kallon saitin da Siyama take,suka haɗa ido lokaci ɗaya Mami ta haɗe rai Siyama ita kuma tayi saurin dauke kanta ta mayar akan wayarta. Mami bata ce komai ba ta juya ta nufi ɗakinta Sadiya na biye da ita tana shasshakar kukanta zama Mami tayi a gefen bed yayin da Sadiya ta zauna gefenta. Mami ta riko hannun Sadiya duka biyum ta riqe cikin nata."natsuwarki nake bukata Sadiya sai kin daidaita natsuwarki wurin ɗaya kamin na iya sani mafita da zan nemo. Da sauri Sadiya ta girgiza kai hawaye na rolling cikin fuskarta da wani irin raunin murya Sadiya tace."Mami ta yaya?"auren dole fa Daddy yake kokarin yayi min taya kike tunanin na kwantar da hankali na kullum alkawari kike min baki taɓa cikamin ba koda sau ɗaya ne sai yaushe zan samu farin ciki ahali wanda nake so muradin zuciyata yana auren ƙanwata. Har asiri aka yi wa yaya Abba dan ya saki Aydah ya aure ni shiru Mami kusan wata nawa da yin asirin amma har yanzu babu abun da ya canja. Sadiya ta karashe maganar cikin shesshekar kuka. Sai jikin Mami,yayi sanyi lokaci ɗaya, ta rasa wane kalar so Sadiya ke yi wa Abba Bashir bata taɓa ganin irin wannan soyayyar ba. Yayi yawa har yana neman zauta tunanin yartata. "maganar Abba da kin sakawa kanki salama kin ciresa acikin lissafinki dan ba zaki taɓa samun sa ba har abada. kalaman Mami ba ƙaramin tarwatsata suka yi ba da wani irin shock take kallon Mami,sai kuma ta kwace hannayenta dake cikin na Mami tana sakin wata irin dariya da bata da alaka da farin ciki. "Dama kin cemin wasa ne Mami!" Karki yi wasa da hankali na,ke kika yimin alkawarin aurensa meyasa zaki ce na daina?"akan me zan daina?idan kika ga na daina sonsa bana cikin duniyar nan Mami. Sadiya ta faɗa cikin ihu tana jin kanta a sama hannu tasa tana dafe kanta duka. Shiru ya ratsa a tsakaninsu na kusan minti biyar kafin Mami ta buɗe baki "Mun yanke shawarar haɗaki aure da Jamal,zai fi maki sauki akan ki auri mutumin da baki san waye Mahaifinki zai haɗaki dashi ba. A wani irin birkice Sadiya ta daga kai tana kallon Mami da mugun mamaki,wani irin murmushi ta saki wanda ita kaɗai ta san ma'anarsa kafin ta miƙe tamkar wata zararra tana kallon Mami."kara ma kice min wasa ne Mami Jamal fa ƙanin baya na shi kuke tunanin na aura me zan tsinta ajikinsa?"Mami duka-duka shekarun jamal nawa?"ai wannan raini ne. A mugun fusace Mami ta katse ta "Ko shekara ɗaya kika basa meyasa ke bakya jin magana bakya daukar shawara?"to haka naga dama na yanke akanki karki kuskura kiyi min musu Sadiya ranki zai ɓaci na gama magana zan samu mahaifinki da zancen. Ita dai Sadiya kallon Mami kurum take tana mamakin karfin halinta juyawa kawai tayi tabarwa Mami ɗakin dan maganganun mamin,ma ciwon kai suke saka masa ko a mafarki ya za'ayi ta auri Jamal yaro dashi ai gara Daddyn ya zaba mata duk wanda yaga dama da dai ta auri Jamal yaro dashi ai wannan ma raini ne. Da ido Mami ta bita har ta fice daga ɗakin,ajiyar zuciya kawai Mami ta sauke wata kwallar takaici ce ta taru a idonta ta tsinewa Abba Bashir yafi sau dari acikin ranta duk shi ya ruguza masu dukkan wani farin cikinsu. Washe gari karfe goma na safe bayan Daddy ya wuce office daman Mami ta kira Hajiya Zeenah a waya akan ta jirata gata nan zata taho suje wurin Malam. Sai da Mami,ta tsaya ta ciri kuɗi tayi arranging ɗinsu cikin wata yar ƙaramar bag ta nufi gidan Hajiya Zeenah,tare suka wuce wurin Malam A hanya Hajiya Zeenah ta kalli Mami, Ta sauke numfashi kafin tace "Allah yasa dai kar ya canja ra'ayinsa ko ya kara mana kuɗi. kusan sati nawa da yin maganar,kin san halinsu basa son jira. "in Allah ya yadda ma haka ba zata faru ba. Mami ta faɗa da wani yanayi a muryarta,da dare Mami ta shiga kitchen da kanta ta yi wa Daddy abinci da tasan yafi so ko Siyama ,da ta shigo ta karbi girkin cewa ta yi kawai ta yi tafiyarta zata yi Siyama na daki bayan magarib kiran Aydah ya shigo a wayarta dauka tayi cike da farin ciki Aydah ke faɗin."congratulations yaya Siyam , Allah ya sanya Alkhairi kin kusa zama Mrs Saleem Sada."juya ido kawai Siyama tayi da murmushi dauke a fuskarta,tana jin yadda Aydah ke farin ciki ta cikin wayar da har ta kasa boye hakan. Ni wallahi yaya Siyam ba ƙaramin farin ciki nayi da ba da jiya yayanmu ya faɗamin ko ba komai yaya Siyam rayuwar gidan aure akwai daɗi wallahi kamar yadda dai kika san anayi a novel. Ta faɗa tana wani fashewa da dariya "Allah ya shiryaki auta da alamar yayanmu ya sakiki a hanya dayawa. Dariya kawai Aydah tayi ita ma dariya Siyama tayi sun daɗe suna waya sai can cike da damuwa a muryar Aydah take faɗin "to ita yaya Sadiya ta tsayar ne?" Dan shiru Siyama ta yi kamar bazata ce komai ba sai kuma tace ":6nima ban sani ba dan ajiyar zuciya Aydah ta sauke tana bai wa Siyama labarin yadda Sadiya ta zo har gidansu tayi mata duka ita da Rumaisa baki Siyama ya buɗe tana sauraren Aydah cike da mamaki,dan babu wanda yayi zancen daga Mami har Sadiya "meyasa baki kira Daddy a waya kin faɗa masa ba.?" Siyama ta faɗa sounding so piss up a muryarta Aydah ta saukar da murya tana faɗin."yayanmu fa ya hana na kira sa cewa yayi nabar komai a hannunsa. ɗan tsaki Siyama taja haƙurin yayanmu yayi yawa gaskiya. "uhmmm!" kawai Aydah tace "Ya Mami?" Aydah ta canja alakar zance. "Tana nan lafiya lau. Cikin rvawar murya Aydah ke faɗin "Mami ta daina sona yaya Siyam,wayar ma sai taga dama take ɗagawa idan na kirata ina mata magana ta wahtsapp ko dubawa ba tayi. Aydah ta karashe maganar cikin rawar murya ba ƙaramin ƙaryawa Siyama zuciya Aydah ta yi ba ita kanta idonta har sun ciko da kwallah karfin hali kurum take yi "ki yi wa Mami addu'a komai zai zama daidai kin san ba halin ta bane canjata aka yi lokaci ɗaya. "Yaya Siyam a kullum ina saka Mami a addu'a ita da Daddy. "Da kyau ki cigaba da yi komai zai wuce kamar ba'a yi ba. Siyama sun dade suna waya da kanwartata kafin suyi sallama mami ce zaune a parlorn Daddy bayan ya gama cin abincin da yau ta sakasa cinsa shi ɗaya cikin parlornsa sai hira take masa a hankali tana yanka masa kankana cikin wani ƙaramin bowl Daddy saurarenta kurum yake,har suka zo kwanciya Mami ita dai bata ga alamar yanayin maigidan nata ya canja ba sai kawai tabar komai aranta maybe sai zuwa gobe ko washe gari lafiya lau suka rabu da Daddy har ya wuce office. Daddy na zaune a office duk da yanayin da yake jin kansa cikinsa haka ya dauki waya ya kira Mami,akan Sadiya tana da bako bayan la'asar wannan karon umarni yake basu daga ita har Sadiya duk wanda ya kuskura yaƙi bin umarninsa wallahi sai dai yabar masa gida. Bayan ya sauke wayar Mami duk hankalinta a tashe yake bata taɓa jin Daddy yana faɗa da wannan yanayin ba,kiran lambar Hajiya Zeenah ta yi bayan ta dauka ,cikin rawar murya Mami ke faɗin."Hajiya Zeenah tun jiya nake zuba ido shiru har yanxu ban ji wani abu ya faru ba. "kuma kin tabbata yaci abincin?" "wallahi ina zaune yaci abinci Kuma na zuba maganin aciki. "kin san magani ba lokaci ɗaya yake aiki ba mu zuba ido har zuwa kwana biyu mu gani. Da sauri cikin rawar murya Mami tace "kwana biyu ai yayi yawa Zeenah. "dadina dake kuma gajen hakuri mariya kin san yadda aikin malamin nan yake yanayi meyasa za ki damu kanki in har kin tabbata kin zuba maganin nan komai zai faru. Dan ajiyar zuciya Mami ta sauke tana faɗin."to Allah yasa! Mami ta kira aunty Safeena awaya ta tambayeta sun yi magana da Jamal da kuma mahaifinsa "yaya Jamal baya ma kasar yanzu haka ya koma makaranta daman nasan haka zai faru jiyaa ina komawa nayi masa magana yau yabar kasar daman nasan ba wai yarda zai yi ba ke ce dai kika dage. Cike da mamaki Mami,ke faɗin."sai kuma kika biye masa ke kika haifesa Safeena ko shi ya haifeki?" Da sauri aunty Safeena ta katseta tana faɗin "Ya zan masa yaya kin san Jamal ya wuce ayi masa auren dole,kuma kin san mahaifinsa da masifar son ya'ya kamar me. "Allah ya kyauta! Mami ta faɗa tana katse wayar batareda ma ta ƙarashe sauraren kanwarta ta ba. Kai tsaye Mami ɗakin Sadiya ta nufa ta sameta tana bacci tashinta ta shiga yi cikin ɓacin rai Sadiya ta juyo duk a tunaninta ko Siyama,ce ta sauke mata kwandon masifa sai taga Mami agabanta ɗan yamutse fuska tayi tana kallon Mami, "Kina nan kina baccin asara na tabbata ko sallar azzahar baki yi ba idan kina da lokaci sai ki tashi ki shirya kina da bako bayan la'asar wannan Umarnin mahaifinki ne ba nawa bane. D haka Mami ta juya tabarwa Sadiya ɗakin dan wani irin takaicin Sadiya take ji sai kuma ta yi wani irin murmushi da gaske ko wanene Daddy yake so ya haɗata dashi tana tausayin rayuwarsa ta yarda ta amince zata karbi duk wanda Daddy ya kawo mata a matsayin miji sai dai ta dauki alwashin ba zata taɓa basa farin ciki ba a gidan aurensu. Kusan karfe biyar maigadi yayi knocking ƙofar parlor, Mami da kanta taje ta buɗe kofar tana kallon maigadi ya russuna ya gaisheta kafin yace "Hajiya Sadiya nada bako a compound Alhaji sammani. Mami ta shiga maimaita sunan aranta tana tuna inda ta san sunan nan take kwakwalwar Mami, ta tariyo mata Alh sammani abokin maigidanta ne tun suna yara kusan ma yafi Daddy kuɗi kuma yana da matar aure wacce sama-sama suke shiri da ita saboda matar tasa mugun girman kaine da ita na masifa. Mami sosai tayi mamaki dan tasan alhaji sammani duk lokaci da ya nemi ya yi aure auren baya tabbata ko an fara maganar sai ta warware saboda yadda uwargidansa ke biyar bokaye na masifa,hankalin Mami,ya tashi sosai tasan Hajiya Saratu tasan shu'umar mace ce Daddy,yana nufin Alhaji sammani zai aurawa Sadiya Mutuwa yake so tayi kenan,dakyar Mami tace ya kai bakon parlor baki Sadiyar tana zuwa,da haka Mami ta juya ta nufi ɗakin Sadiya duk a rikice take ta samu Sadiya zaune tana danna waya kallo ɗaya ta yi wa Mami,ta dauke kai. "kin san dawa mahaifinki ke kokarin haɗaki aure?" Ita dai Sadiya bata kalli Mami ba ta cigaba da danna wayar hannunta dan ita ba wai wani damuwa tayi da auren ba yanzu a fusace Mami,tace "Ina miki magana kima mayar dani wata yar iska Sadiya. Da mamaki Sadiya ke faɗin."me zance Mami ina jin mun riga mun gama maganar nan. A rude Mami ke faɗin "Alhaji sammani ne fa abokin Daddynku mijin Saratu! Wani murmushi Sadiya tayi ganin yadda Mami,ta rude "Mami yana da kuɗi daman sune matsalar kowa a duniya, zan iya aurensa a haka idan bai shiga rayuwata ba nima kar na shiga tasa. Baki buɗe Mami ke kallon Sadiya. "Ke har kin tsarawa kanki rayuwa dashi kenan mijin Saratu ne fa? matar dake bin bokaye har na fitar hankali shi ne kike cewa za ki aure mijinta. Wani murmushi Sadiya ta yi tana faɗin "Ai ni nafi son haka,kinga kowa ya iya allonsa ya wanke da kansa ya ƙaraso kenan?"Mami dai saboda shock kasa cewa Sadiya komai ta yi dan jin take kamar ta kwadawa Sadiyar mari. Sadiya daman tayi wanka ta dauki dan ƙaramin veil ɗinta mai shige da kayan ta ɗora akan kafaɗarta, ta ƙarasa gaban madubi ta ɗauki turare ta shiga shafawa da haka ta fice daga dakin tabar Mami sake da baki. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO. [2/2, 10:18 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 094. Da Siririyar sallama,ta shigo cikin parlorn kallonta kawai yake da wani yanayi shimfiɗe akan fuskarsa ga zuciyarsa dake wani irin dokawa. Da gaske bai san yana son Sadiya sosai,ba sai da ya bayyana a gabanta ta zauna akan ɗaya daga cikin kujerun da suka kawata parlor ta kalli Alhaji sammani,cikin kyakkyawar shigarsa ta alfarma ƙamshinsa ya gama cika ko'ina dake cikin parlor,yana da kyau babu laifi duk girma ya fara kama shi. Koda yake har yanzu bata ga wani namijin da zai burgeta a duniya ba baya ga yayanta. Wani yanayi ne kwance acikin fuskarta wanda ba zai fassaru ba. "Ina wuni ta faɗa murya can kasa. "kina Lafiya ya gida ya karatu?" Alhaji sammani ya faɗa cike da fara'a Sadiya ta amsa da Lafiya Alhmdullahi ya kuma yara da Madam. tayi magana tana wani sauke idonta cikin nasa ,ba ƙaramin kokari Alhaji sammani yayi ba wurin rike kansa ganin irin kallon da Sadiya ke jifarsa dashi hira suka taba yar kaɗan yana tambayarta abubuwan da take so da wanda kuma bata so tana basa amsa sauran hirar kuma ta matarsa ne da "ya'yansu biyu maza macce ɗaya. sun yi kusan awa ɗaya tare kamin Alhaji sammani ya yi mata sallama, maigadi ya saka ya kwaso masa kayan shopping ɗin da ya biya yayi mata ya bita dasu cikin gida. Har lokacin Mami,na zaune a parlor duk abun duniya ya dameta ganin Sadiya ta shigo Parlor yasa Mami ,ta daga kai ta kalleta ita ma Sadiyar Mami,take kallo "Ya tafi Mami yace agaisheki. Sadiya ta faɗa tana cigaba da tafiya hankalinta akan wayarta. Da wani yanayi Mami ke kallon ta kafin ta kira sunan Sadiyar cikin wata irin murya da bata taɓa jin Mami,ta kirata dashi ba. Dan juyowa tayi tana fuskantar Mami. "Da gaske za ki iya auren wannan mutumin? Cike da mamaki Sadiya take kallan mami,kafin ta nisa tana faɗin "Daman Mami yana da wani mugun hali ne wanda ban sani ba kuma dai naga Daddy ne ya kawosa?" Kuma ni banga illah acikin aurensa ba gwargwado Daddy yasan halinsa yana da hali mai kyau yana da asali mai kyau yana da kuɗito menene matsalar?"baki buɗe Mami ke kallon sadiya,baki san wacece matar sa ba shiyasa kike da zarar faɗar haka ko so kike ta kashemin ke ko ta yimaki wani abun da ba za ki kara muruwa ba a rayuwarki?" Cike da gajiya Sadiya ke faɗin "wannan bai dameni ba Mami,bani da matsala da matarsa hasalima ba gida ɗaya zai ajemu ba ni ban damu da ko bokaye nawa take bi ba. Tun kafin na shiga gidan ,nima zan je wurin nawa malami dan ba'ayi diya maccen da zata hanani rawar gaban hantsi ba. Da haka Sadiya ta juya tabar Mami sake da baki duk abun duniya ya taru yayi mata yawa ko baccin kirki bata samu ko kaɗan bata da wani kwanciyar hankali acikin kwanakin nan.bayan fitar Alhaji sammani da har lambar Sadiya ya karba ganin kamar ya samu karɓuwa a wurinta. Kiran Daddy yayi cikin farin ciki ya sanar dashi Sadiya tayi ammana dashi. sosai Daddy,yayi murna Sadiya bata taɓa saka sa farin ciki irin wannan ranar ba ,duk wata kullata da yayi mata ya ji a hankali tana warwarewa lokaci ɗaya,Allah ya karbi adduarsa.Bayan sati ɗaya aka kawo lefen Siyama,dana Sadiya aka saka rana lokaci ɗaya ,har lokacin kuma Mami bata ga alamar asirinta ya yi tasiri akansa ba sai dai Daddy,ya canja sosai kullum baya cikin walwala tana yawan farkawa da dare tagan shi zaune cikin tunani da damuwa har yar rama mamin taga ya yi. AB yana tsaye a gaban mirror dressing yana cubbing sumar kansa,tun sanda Daddy ya kirasa da safe yace yana son ya gansa a office ya fita da wuri yake ji wata irin damuwa tana lullubesa musamman da ya ji muryar Daddy,kamar batasa ba kamar yana cikin damuwa kusan kwana biyu ya lura da haka babu irin tambayar da AB bai masa ba akan ko akwai abunda ke damunsa yace masa a'ah!.wani irin yanayi yake ji cikin jikinsa tun da suka gama waya da Daddy,bai kara samun natsuwa ba. Yana cikin wannan yanayin Aydah ta zo ta maƙalesa ta baya ta kwantar da kanta cikin bayansa ta ɗora duka hannayenta adaidai saitin zuciyarsa yadda zuciyarsa ke bugawa kamar ya wuce ka'ida yasa ta rika shafa wurin,cikin sanyin murya take faɗin."yayanmu wannan bugun zuciyar ya yi yawa meke faru ne? "Babu komai baby muje muyi breakfast ya faɗa yana dawowa da ita gabansa ganin yadda ta kwaɓe fuska yasa yaja dogon hancinta ya russuna ya sumbaci dan ƙaramin bakinta murya can ciki yake faɗin. "I love you baby!" Rungumesa tayi tana fadin "I love you more yayana.!sunfi minti uku a haka kafin ya samu ya cireta daga jikinsa,da sauri ta dafe saitin zuciyarta taji yayi wani irin dokawa wanda bata taɓa jin kalarsa ba. Dan kallonta yayi yace "Lafiya?"tamkar zata yi kuka ta ce "gabana naji ya faɗin kamar wani abu marar daɗi zai faru. Aydah ta faɗa cikin rawar murya ɗan buɗe idonsa yayi akanta ya rike mata hannu ya fara tafiya da ita yana faɗin "Babu abunda zai faru ki yi addu'a. Ta gyada masa kai kurum tayi da yake ranar girkinta ne tare suka sauka kasa Huwaila ta gama jera komai cikin dinning area,daman yanzu ba koda yaushe Rumaisa ke fitowa ayi breakfast a tare da ita ba musamman idan tasan ba ranar girkinta bane,tare suka yi breakfast ya miƙe ya koma sama,ya leka ɗakin Rumaisa yaga tana bacci dakinsa ya nufa Daidai nan wayarsa ta soma ring ɗagawa yayi ganin Daddy ke kiransa ya dauka da sallama a bakinsa Daddy ya amsa yana faɗin."ya taso? "yanzu zan taho Daddy! ɗan shiru Daddy,ya yi kafin yace "kana jina Abba?" "Ina jinka Daddy. Cike da karfin hali Daddy yace "kafin ka taho ka zo min da duk wasu documents ɗina dake wurinka wanda kasan mallakina ne! Dan shiru AB ya yi yana sauraren Daddy da yanayin da ya kasa fahimta a muryar Daddy ɗin sai dai bai kawo komai aransa ba yace "Insha Allahu Daddy! Da haka suka yi sallama. Aydah ganin yayanta bai dawo ba yasa tabi bayansa baya falonsa kai tsaye master bedroom ɗinsa ta nufa ta samesa yana arranging din duk wasu kaddarori da Daddy ya mallaka masa da nasu Aydah wanda suke dauke da sunan kowa ,bai bar takarda ko ɗaya a gidansa ba ya yi wa Aydah sallama ya nufi office wurin Daddy,wani irin yanayi yakyeji ajikinsa marar Misiltawa jin yake tamkar zazzaɓi zai saukar masa dakyar yayi knocking kofar office ɗin Daddy aka yi masa izinin shiga ,suka yi ido biyu da Daddy shi ya yi saurin dauke nasa idon cikin na Daddy ya samu wuri ya zauna ,ya tura bag ɗin dake dauke da duk wasu dukiyoyin Daddy dake hannunsa da wanda ya mallaka masa da shi dasu Aydah ya tura agabansa jaye bag ɗin gefe Daddy ya yi. Ya daga kai ya kalli Daddy a karo na biyu sai da zuciyarsa ta doka da ya hango kwallah acikin idanuwan Daddy,shi baya son ganin wannan yanayi a tare da Daddy,rasa kwarin gwiwa yake yi. Murya a harhade tamkar ba muryar Daddy ba yake kallon AB ido cikin ido "zan nemi alfarma a wurinka Abba Allah yasa zan samu.?" A gaggauce AB ke faɗin."Daddy ka faɗi duk abunda kakeso a wurina na maka alkawarin idan bai fi karfina ba zan maka.!" dan shiru Alhaji Bashir yayi jin yake tamkar zuciyarsa zata fito daga kirjinsa yanayin da yake ji kansa tamkar ana hura masa wuta a sassan jikinsa. "Abba ina son ka bar rayuwarmu na har abada nida iyalina ina nufin idan zai son samu ne kayi nisa damu dan Allah. Alh Bashir ya faɗa yana haɗe hannayensa. A razane AB ke kallon mahaifinsa sai dai ganin hawaye a idanun mahaifin nasa yasa yaji komai nasa ya tsaya tsak! "Karka tambayeni meyasa idan zai yiwuwa yanzun Abba ka tashi ka tafi Allah yasa damu alkhari.! har AB ya bude baki zai yi magana Daddy,ya shiga girgiza masa kai "ka tafi dan Allah karka ce komai. Har lokacin Daddy bai sauke hannayensa ba A hankali AB ya mike tsaye yana jin wani nauyi a kasan zuciyarsa da sauri ya juya ya nufi ƙofar ya ji waɗansu zafafan hawaye suna fitowa daga cikin idanunsa. A hankali AB yaja kofar ya maida ya rufe da ido Daddy ya bisa kamin ya dora kansa akan desk ya fashe da wani irin kuka mai wuyar fassarawa kuka yake sosai jikinsa na wani irin kaɗawa tsanar kansa yaji tana cika masa zuciya miyasa ya aikatawa Abba haka idan Abba ya bar gidansa ina zai tafi wa yake dashi a duniyar nan sama dashi? Yana so ya tsayarda shi sai dai wani sashe na zuciyarsa yaƙi ya basa haɗin kai. Tafiya yake bai san inda yake jefa ƙafarsa ba,saboda tsananin tashin hankalin da ya shiga bai san rashin iyaye babban haɗari bane a rayuwa sai yanzu da maganganun Daddy,ke dawo masa cikin kansa shiga motarsa yayi tare da yin reverse da wani irin gudu ya fisgi motar maigadi yana bin sa da kallon mamaki,kuka yake yi yana jin tsanar iyayensa aransa bai ga laifin Daddy ba komai ya samesa iyayensa ne suka ja masa.Yawo ya rikayi da motar dan bai san inda zai je ba daga bisani sai kawai ya dauki hanyar barin garin Kano. Babu wani tunani akansa a wannan lokacin sai na son yin nisa da Kano baki daya addu'a ya riƙa yi Allah ya dauki ransa ga baki ɗaya kowa ma ya huta.Tun daga nesa babbar motar tankin mai keyi wa AB mahaukacin horn da aguje take shigowarta kenan cikin garin kano shi kuma yana kokarin fita ga baki ɗaya hankalinsa da natsuwarsa basa tare da shi tuki kawai yake yi bai ankara ba sai jin ya yi motarsa tayi sama dashi daga nan kuma bai kara sanin meke faruwa dashi ba. Har bayan ishai Aydah na zaune a parlornta suna kallo da Huwaila kallon kawai take hankalinta baya tare da ita ta rasa inda yayanta ya shiga har yanzu bai dawo ba ga wayarsa bata shiga ita ma Rumaisa kusan 9 ta fito parlor ta kalli Aydah data zama wani iri lokaci ɗaya tana tambayarta har yanzu yayan nata bai dawo ba,Aydah ta dagawa Rumaisa kai kurum zuciyarta duk babu dadi. Cikin rawar murya Aydah ke faɗin "haƙurina ya fara karewa Aunty Rumaisa gabana sai faduwa yake yi wani irin kunci nake ji ,ki bari mu kira Daddy mu je ko yana da masaniyar inda Yayanmu yake ba ma yi ta zama haka kurum mu zuba ido muna jiran tsammani ba. zama Rumaisa tayi gefen Aydah ita kanta bata da natsuwa gashi kwanan nan bata jin daɗi tana fama da laulayi sun je asibiti ita da AB aka yi gwaji, gwajin farko da akayi mata aka tabbatar da akwai ciki na kusan sati 3 ajikinta irin murnar da AB ya rika yi a ranar bata misaltuwa yadda ya dinga tattalinta da nuna mata kulawa ya saka ta farin ciki domin nuna farin cikinsa ya tashi sai da ya siya mata mota don kawai ya faranta mata,duk da bata shiryawa haihuwa ba a yanzu sai kawai ta haƙura ganin yadda AB ke son cikin jikinta ita ma Aydah ta yi murna amman da suka shiga daki har kuka sai da ta yiwa AB wai ita meyesa bata da ciki sai Rumaisa?" Baki ya buɗe kawai yana kallon drama Queen ɗin tasa,shi kuma har ga Allah bai mason ta yi ciki yanzu saboda karatun ta kuma ganin yake tayi kankanta rungumeta ya yi cikin jikinsa yana faɗin."sai kin gama jami'a baby. rigima ta rika yi masa akan tana so murmushi kawai yayi a lokacin yana faɗin."zai zo ta yi addu'a. Da haka ya samu ya rufe bakin rigimarta. Aydah ta kira lambar Mami, Mami na dauka Aydah ta sakarwa Mami kuka,cikin kuka ta ke yiwa Mami bayani da sauri Mami ke tambayar Aydah tun yaushe?"ta faɗa mata tun sanda ya fita office tana jin damuwa a muryar Mami,kafin tace mata bara ta yiwa Daddy magana. Da haka Mami,ta aje wayar murna fal aranta tana tunanin Allah yasa Abba yabar garin duka da haka ta nufi bangaren Daddy,hankalin ta a tashe take faɗa masa har yanzu Abba bai koma gida ba kuma Aydah har Abdulkarim ta kira basa tare, Daddy bai kalleta ba kawai yace mata ai Abba ba yaro bane. Kallon yanayin Daddy kawai Mami ta yi sai ta juya tabar parlorn murna fal aranta. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. [2/5, 2:00 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 095. *LAGOS NIGERIA* Tun bayan dawowar Aliyu na Uku lagos ya ƙara zurfafa bincike akan inda zai nemo ɗansa ga Maysun a halin yanzu gazawar sa take gani. Har ta kai ta kawo kullum sai ta ɗora masa laifi akan ɓatan ɗan nasu. Tana gani cewa don shi na da wasu 'ya'yan ne shiyasa bai damu da ya nemo mata nata ɗan ba. Ga baki ɗaya ta bi ta tashi hankalinsa bashi da natsuwa ko kaɗan, ga kuma Anaal da a yanzu ya rasa gane kanta sakaci iri-irin take masa a kamfani daman can ita ce jajirtacciyya a kamfanin ita ce mai kokarin kawo cigaba a koda yaushe saɓani yanzu da ko ayyukan office ɗinta ta daina kulawa dasu. Wani lokaci ma bata zuwa kamfani sai ta yi kwanciyar ta a gida idan ya yi magana sai ta ce bata jin daɗi. Ƙarfaffiyar ajiyar zuciya Aliyu na Uku ya sauke ya kai dubansa akan wayarsa dake ringing ya ga kiran daga Kamfani whitepaper ne dake Germany, jikinsa babu kuzari ya yi picking. "Hello, Mr. Aliyu, you're talking to the president of the white paper company Clark Andrew I heard that you canceled the business agreement between your company and the moonlight automobile industry company.May I know your reason for canceling the agreement. With shock Aliyu na uku ya miƙe tsaye domin shi iya saninsa bai san sanda hakan ta faru ba. Amman dole Anaal tana da cikakkiyar masaniyar domin ita ce CEO na kamfanin dole sai da sa hannunta za a iya soke yarjejeniyar ɗin. Cikin sanyi murya ya shiga faɗin "sorry mr clark i don't know about that but give me time I'll talk to the CEO I'll contact you later thank you very much. Bai jira me Clark ɗin zai faɗa ba next ba ya kashe wayar saboda ransa ya fara ɓaci har yana tambayar kansa yaushe Anaal ta sami power har haka da za ta zantar da hukuncin irin wannan with out his consent zuciyarsa sai tafarfasa take yi a fusace ya koma ya zauna ya dauki wayarsa ya kira layin Anaal sai dai wayarta bata shiga, secretary ɗinsa ya kira ya ce ta kira masa Anaal a office ɗinta jim kaɗan ta dawo "Sir, her office was closed and I asked her secretary and he said that she came in the morning and she left in a hurry. "did he tell you where she went? "No sir! he said that she didn't tell him where she was going, but she left in a hurry. "Okay! You can go back to your work. "Yes sir! Ta faɗa cike da ladabi ta juya tare da ficewa, landline na office ɗin Zaheed ya kira ya ce ya zo yana so ganinsa. After some minutes sai ga Zaheed ya nemi kujerar dake gaban desk ɗin Aliyu na uku ya zauna. "Zaheed ko kasan inda Anaal ta je na kira layin ta baya shiga, sannan kuma kana da masaniyar akan cancelling partnership ɗinmu da kamfanonin moonlight da ta yi?" "Ban san inda ta je ba Abbu tun safe rabona da ita dangane da cancelling partnership shi ma basan komai akai ba. Amman za ka iya bincikar Zayeed maybe shi ta gayamasa. Batareda Aliyu na Uku ya ce komai ba ya kira Zayeed. "Ga ni Abbu! Zayeed ya faɗa cikin russunawa. "Zauna Zayeed. Abbu ya faɗa tare da pointing kujera da hannunsa jikin Zayeed ne ya yi sanyi ya zauna tare da kallon Zaheed yana kifkifta masa ido alamar me ke faruwa?" Shi ma alamar ya yi masa da jira Abbu ai zai gayamasa, sai da Abbu ya ja iska da bakinsa ya fesar kamin ya yi wa Zayeed irin tambayar da ya yi wa Zaheed. "Eh! Na haɗu da ita a parking lot za ta fita yadda naga tana sauri ya daure min da kai domin iya tsayin zamana da ita bata taɓa ganinta tana irin wannan saurin ba, shiyasa na yi sauri fitowa daga motata na tambaye ta me ke faruwa take sauri haka. Sai ta cemin tafiyar gaggawa ce ta kama ta zuwa Kano. Mamaki ne ya kama ni za ta je yi a Kano kuma cikin gaggawa kamin na yi mata wannan tambayar har ta ja mota ta tafi. Amma dangane da partnership ɗin ne bani da masaniyar nima. "Kano?" Aliyu na uku ya maimaita sunan cikin mamaki. "Eh! Abbu. "Anaal ce ta tafi Kano? To me za ta je yi a Kano?" "Wallahi Abbu nima bansani ba. Zayeed ya yi magana yana lankwasa yatsunsa. "Abbu wannan al'amari da ɗaure kai yake iya sanina da Anaal bata da ƙawa a Kano balle mu ci ko gun ƙawarta ta je. Zaheed ya faɗa da dimbin mamaki shimfiɗe akan fuskarsa. Shiru ne ya biyo baya kamin Abbu ya ce su koma bakin aikinsu. Ya zurfafa tunaninsa me Anaal za ta je yi Kano batareda da neman izininsa ba. Shi kansa yasan Anaal ta canza ba haka yasan ta ba dole da akwai abun da yake damunta to mene ne wannan abun ɗin?" Rashin sani amsa yasa ya ƙara gwada kiran wayarta still bata shiga. *KANO NIGERIA* Kafin mutane su kawowa Ab agaji motarsa ta kama da wuta, wani irin ci take yi da wuta bata daina ci ba har sai da ta dawo toka babu abin da mutane ke yi sai kalmar shahada akan idonsu motar ta cinye duka. Aydah da Rumaisah har dare basu samun labari inda Ab yake ba tun Aydah tana kira Daddy da Mami suna dauka har suka daina daukar kiranta wanda hakan ya ƙara jefa ta cikin damuwa, ga Rumaisa sai amai take sheƙawa hatta da ruwa ta sha sai ta dawo dasu cikin lokaci guda sun fice daga hayyacinsu. Zaune suke a parlorn ƙasa sun yi zugu-zugun lokaci zuwa lokaci Aydah take goge hawaye da suka kasa daina fita daga idanunta, Rumaisah ce mai ɗan karfin hali rarrashinta suna cikin wannan halin Abdulkarim ya zo tare da wani abokin su Jabeer yadda Abdulkarim yaga Aydah da Rumaisah manne da junansu sai suka yi bala'in basa tausayi shi da Jabeer suka dinga rarrashesu da kwatar musu da hankali, suna baro gidan suka wuce police station suka kai report daga nan kuma suka nufo gidan Mami. Sun sami gani Daddy sai dai har Abdulkarim ya gama basa labari duk inda yake saka ran gani AB ya je bai sami shi ba hasali ma an ce bai je ba. Daddy ya dafe goshinsa yana tuna abubuwan da suka faru tsakaninsa da AB, wata irin nadama haɗe danasani marar adadi Daddy yake ji yana kama shi cikin rauni murya ya ce "Abdulkarim ku hutar da kanku da neman abokinku domin baya ciki garin kano a halin yanzu Allah kaɗai yasan inda yake. Abdulkarim bai san me ya hau kaina ba na kora Abba da kaina ni na umarce shi da yabar rayuwata da ta iyalina batare da ya yi min laifin komai ba. Abdul ni na kore ɗa na da kaina ni kam wane ne irin uba ne? Daddy ya ƙarashe magana hawaye na bin kumatunsa daga Abdulkarim har Jabeer sun kasa cewa komai wannan al'amarin ba ƙaramin daure musu kai ya yi ba. Sun rasa ta ina za su fara ga kuma tarin tambayoyi da suka cika musu ciki daga ƙarshe dai sai sallama suka yi wa Daddy tare da basa yakinin cewa in shaa Allahu za a gansa. Har washegari babu labarin Abba zuwa lokaci Rumaisah da Aydah sun ci kuka har sun godewa Allah, Kwata-kwata daren jiya babu wacce ta runtse a cikin su. Misali karfe 11:20am Abdulkarim ya sami kira daga police headquarter saboda da ya kai report har hoton ab da na motarsa ya bar hoton motar yana dauke da plate number jami'an tsaro sun sami gani motar AB iya bincike da bin kididdiga da suka yi ya tabbatar musu da motar AB ce da Abdulkarim ya isa inda motar take, yana ƙare mata kallo cikin abun da bai wuce twenty seconds ba ya gane motar AB ce faduwar ƙasa ya yi ya dafe kansa, sai ga Abdulkarim yana kuka da hawaye duk Abdulkarim yana cikin wannan halin hakan bai hana masa kiran Daddy ba ya sanar dashi mummunan labari kamin ka ce kwabo mutuwar Ab ta zagaya ko'ina, suman Aydah biyu Rumaisah kuma jini ya ɓalle mata sai asibiti aka wuce da ita cikin hukuncin ubangiji cikin nata bai zube duka ba aka yi nasarar tsayarda bleeding ɗin tare da bata gado har aka yi addu'ar uku Rumaisah tana kwance asibiti. Ko Mami da ta zama silar barin Abba gida da labarin mutuwar sa ya riske ta, ta shiga tashin hankali musamman yadda taga yaranta suna kuka Sadiya kamar za ta yi hauka sai sambatu take yi Siyama ce mai ɗan karfin halin rarrashin Aydah tare da yi mata nasiha. *BAYAN WATA BIYAR* A cikin watanni biyar ɗinan abubuwa da dama sun faru daga ciki har da dawowar Aydah gidan Daddy bayan ta kammala takabarta yayin da Rumaisah ta koma nasu gida, aka rufe gidan AB. Rayuwar Aydah ta dawo abar tausayawa ta dawo miskila ƙarfi da yaji kullum tana ƙunshe a ɗaki gashi sai shirye-shirye bikin su Sadiya ake yi wanda za a fara shagalin bikin nan da kwana biyu, duk wannan bidiri da ake yi babu Aydah a ciki a duk sanda ta zauna ta dinga shafar cikinta kenan tana ji ina ma ita ma ace tana dauke da cikinsa kamar dai Rumaisah. Idan kewarsa ta addabe ta sai ta dinga kallon pictures dinsa dake cikin wayarta. Mami ta yi faɗa ta yi rarrashinta har tagaji ta zuba mata ido yayin da shi ma Daddy yake cikin matsananciyar damuwa ya ɗauki laifin faruwar al'amarin ya ɗorawa kansa idan kaga Daddy yarda ya zabge ya yi wata irin rama kullum jininsa ƙara hawa yake yi baya jin lafiya ko kaɗan a jikinsa ƙarfin hali kawai yake yi burinsa ya aurar da su Siyama tun da raguwar numfashinsa don ji yake yi jikinsa kamar da wuya a wannan karon ya kai labari. Cikin amincewar ubangiji aka yi bikin Siyama da Sadiya lafiya kowacce aka kaita gidan mijinta sai dai fatar Allah ya basu zaman lafiya. Tun bayan bikin su Siyama abubuwa suka ƙara caɓewa Aydah ga kadaice zaman gida ga kewar yayanta da har ta kasa sabawa da rashinsa. Tun last week aka yi resuming school ta kasa komawa gashi har an fara hada-hadar zana waec da neco, da kyar Daddy ya samu ta amince za ta koma on monday. Ta ɓangaren Rumaisah cikin jikinta ya zo mata da laulayi mai wahala ga damuwar mutuwar mijinta sai abubuwa suka taro suka yi mata yawa, idan kaga Rumaisah sai ka zubar mata da hawaye duk ramar da Aydah ta yi Rumaisah ta fi ta. Kullum sai Aydah ta kira ta, ta ji yanayin jikinta duk ranar juma'a idan an sauko daga masallaci direba yake kai Aydah gidansu Rumaisa yanzu wata irin shaƙuwa ta ban mamaki ta shiga tsakanin su. Mutuwar Ab ta koya musu ƙaunar junansu a duk sanda suka haɗu basu da hira sai ta irin zaman da suka yi dashi wani abu idan suka tuno dashi sai ya basu dariya, wani kuma sai su fashe da kuka a duk sanda irin haka ta faru Ammi ce ke zama a tsakiyar su ta dinga rarrashinsu bala'in tausayi suke bata. Yau ma kamar kullum bayan Aydah ta dawo daga school kasancewar ranar juma'a ce ƙarfe 12 suke tasowa a main parlor ta tarar da Mami da Hajiya Zeenah suna hira ta gaishe su a takaice ta haura ɗakinta hajiya Zeenah ta dubi Mami tana murmushi tare da faɗin "Wai Mariya haka za ki zubawa Aydah ido kina kallo yarinya za ta kashe kanta akan wanda tuni aka shafe babinsa a doron duniya wallahi Mariya ki yi wa kanki faɗa ki ɗora 'yarki kan hanya ina amfani badi ba rai wanda ya mutu ya mutu kenan har abada ba zai taɓa dawowa ba. "Bari kawai Zeenah ba kisan irin halin takaici da nake ciki akan lamarin Aydah da mahaifinta sun ɗauki soyayyar duniya sun ɗorawa matatcce ina lure da Alhaji kwata-kwata ya daina bacci sai uwar rama da yake yi da zarar ya buɗe bakinsa baya da wani zance face na Abba, haka zalika Aydah. Magana ta gaskiya Zeenah na kashe maciji ne ban sare kai ba. Na kawar da Abba daga zuri'a ta amma na kasa cire musu shi a zuciya hatta da Siyama da Sadiya basu da zance idan bana sa ba. "Uhm! Lallai Mariya Daddyn su Sadiya ya ɗauki miki kara da kiyashi daukar marar sani anya kuwa Abba ɗinan bai haɗa tsatso da mayyu ba?" Yaro ya mutu amma be bar mutane suka huta ba. Da haka suka ci-gaba da hirar su wacce dukkanta akan Abba ne. Bayan Aydah ta yi wanka ta shirya cikin milk colour ɗin Abaya ta yi rolling da mayafin rigar ta fito da ƙaramar purse ɗinta a hannu koda ta fito Mami da Zeenah sun koma ɗakin Mami saboda haka ta fice abin ta direban Mami ne ya sauke ta gidansu Rumaisa ta ce ya dawo da yamma ya dauke ta. Da sallama ta shiga parlorn gidan Rumaisah na zaune a ƙasan rug tana cin kwado zogale yau da sha'awar cinsa ta tashi shi ne Ammi ta yi mata. Sallamar Aydah da ta ji yasa ta ɗagowa tare da fadada fara'arta ta amsa mata, ita ma Aydah murmushi ta sakar mata ta nemi kujerar da ke kusa da ita ta je ta zauna tana faɗin "Yau kuma me ake ci ne haka maman twins?" Dai da Rumaisah ta galla mata harara kamin ta ce "wai Baby ba za ki daina zance twins ɗinan ba ko?" "Akan me zan daina bayan kullum addu'ata akanki ki haifa mana 'yan biyu ki ɗauki ɗaya ki bani ɗaya. "Uhm! Aydah kenan ai na gayamiki guda ɗaya ne an yi min scanning an tabbatar da hakan kuma in shaa Allah zan ba ki shi. Dariya Aydah ta yi tare da zamewa daga kan kujera ta zauna dab da Rumaisah akan rug tana faɗin "Kin ga aunty Rumaisah kar ki shafa min zuma a baki sai bayan kin haihu ki ce ba kisan da zance ba. Musamman idan kika haifu mai kama da Yayanmu. Murmushi kurum Rumaisah ta yi sai ta ƙarashe cinye kwado ta kana ta kai plate kitchen ta wanko hannu da bakinta ta dawo ta zauna kusa da Aydah ta kama hannayenta "Da gaske nake yi baby duk abun da na haifa wallahi zan ba ki shi domin nasan za ki so shi za ki kaunace shi ba za ki taɓa barinsa ya yi kukan maraici ba. Wani irin farin ciki ne ya lulluɓe Aydah yayin da idanunta suka cicciko da ƙwalla bata baro gidansu Rumaisa ba sai yamma lis. *LAGOS NIGERIA* A fusace Aliyu na uku ya shiga ɗakin Anaal wacce ke zaune akan stool ɗin dressing mirror ta ɗora laptop akan lap ɗinta tana wani aiki, yadda Abbu ya turo ƙofar ɗakinta yai masifar haifar mata da faɗuwar gaba tai sauri rufe laptop ɗin ta yada ganinta akan fuskarsa wacce ke murtuƙe "Me kike zuwa yi Kano?" Abbu ya faɗa babu annuri ko alamar wargi akan fuskarsa. Anaal ta haɗiye wasu busassu miyau tare da kauda fuskarta tana lankwasa yatsunta daman tasan dole sai hakan ta faru saboda jiya ta dawo daga Kano wanda yanzu zuwa garin Kano ya zama matar kamar dole. "Anaal dake nake magana ki buɗe baki ki faɗamin abun da kike zuwa yi a Kano iya sanina daga ni har mahaifiyarki ba mu da wasu dangi a garin kano bare na ce ko ziyara kike zuwa idan ma akwai dangin acan ba zai yiwuwa ba ace ki dinga zuwa akai-akai ki faɗamin gaskiyar abun da kike ɓoyewa Anaal idan har kika bari na binciko da kaina wallahi sai nayi mummunan saɓa miki. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. [2/5, 2:01 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 096. Shiru Anaal ta yi ta kasa furta uffan sai faman lankwasa yatsunta take yi tamkar su ne za su kawo mata mafita. Wanda hakan da ta yi yai masifar kular da Abbu ya hasala iya hasala sai huci yake yi, ji yake tamkar ya rufe ta da duka tana 'ya mace za ta dinga yawon banza da na wofi. "Za ki buɗe baki ki bani amsa ko sai na taɓa lafiyar jikinki?" "Abbu ka yi haƙuri. Anaal ta faɗa cikin rawar murya "Ba zan haƙura ba har sai kin gayamin abun da kike zuwa yi a Kano. Duk yadda Abbu ya kai da nuna fushinsa a fili akan Anaal ta faɗa masa abun da take zuwa yi a Kano amman yarinya nan ta tsuke bakinta ta yi shiru sosai ya harzuƙa har bai san sanda ya yi kanta da nufi ya rufe ta da duka ta arce toilet ta rufe ƙofa da key, da Abbu ya gaji da bambamin faɗansa ya fice daga gidan dukka. Ya nufi the george hotel wurin Maysun duk da ko ita a yanzu ba daɗinta yake ji ba saboda ta sako shi a gaba akan sai ya nemo mata ɗanta. Musamman a kwana nan da take yawan mummunan mafarki akansa, duk ta bi ta addabe Aliyu na Uku damuwa tana neman ta kassara shi. Ya yi parking motarsa a parking lot din hotel ɗin ya nufi receptionist hankalinsa Kwata-kwata baya jikinsa ko kaɗan bai lura da Alhaji Ƙasim Birema ɗaya daga cikin abokan Ciroma dake zaune a receptionist ɗin yana amsa waya yayin da Alhaji Ƙasim Birema yana ganinsa ya washe haƙora ya yi sauri kashe wayar ya bishi a baya daman yana neman wanda ya sani a garin Lagos ɗin wani muhimmin abu ne ya kawo shi sai dai babbar matsalar sa da ya kasance bai san wasu wurare a cikin garin na Lagos ba. Shi ne yana gani Aliyu na Uku ya ji damuwarsa ta kau yana da yaƙini zai taimake sa ko don albarkacin yayansa Ciroma da yake abokinsa. Ya tashi da sauri yana baza babbar rigarsa ya bi bayan Aliyu na Uku sai dai kafin ya cimma masa ya ɓace masa saboda haka ya dawo receptionist ya kasa ya tsare yana jiran fitowarsa, jim kaɗan sai ga Maysun ta fito a fusace zuwa cikin receptionist ɗin yayin da Aliyu na uku yake bin ta a baya yana rokonta ta tsaya ta saurare shi bata tsaya ba ɗin har sai ta dangana da parking lot zuciyata tana tafarfasa ta shiga zazzaga masa masifa tana kuka. Alhaji Ƙasim yana ganinsu ya taso ya biyo su a baya daga nesa ya tsaya yana kallon su da kyar Aliyu na Uku ya rarrashe Maysun ta haƙura ta koma ɗakin hotel ɗin. Tun daga fitowarsu har komawarsu ciki akan idanuwan Alh Ƙasim yana mamakin miye gamin Aliyu da wannan balarabiyar mata kodai Aliyu ya fara bin matan banza ne. Nan da nan zuciyarsa ta cika da kokwanto Alh Ƙasim Birema yana cikin jinsin mutane masu azababben sa'ido da munafuci haɗe da anamimanci wannan halayyar tasa tun daga yarinta yake dauke da abarsa har zuwa girmansa da abun ya cigaba da habbaka, saboda haka jikinsa yana rawa ya lallaɓo numbern Ciroma don ya fesa masa labarin abun da idanunsa suka gane masa, musamman da yasan cewa babban laifi ne ga jini masauratar kudu ya kulla haramtacciyar alaka da, idan hakan ta faru aka kuma gabatar da gamsasu hujjoji za a kore wannan jinin sarautar daga masaurata idan yana da sarauta za a tube rawaninsa. Saboda haka Ciroma yana picking da kyar ya bari suka gaisa ya kwashe ƙarya da gaskiya ya gayamasa farin ciki ya lulluɓe Ciroma ya ce dashi ya yi kokari ya dauko masa hotunan Aliyu ɗin tare da balarabiyar akwai kyauta ta musamman da zai masa. Saboda haka Alh Ƙasim ya bazama neman yadda zai ɗauki hotunan su sai a washegari ya sami damar aiwatar da burinsa.Ta hanyar biyan daga cikin ma'aikatan hotel ɗin, ba iya hotunan su ba har da video ya ɗauka kala daban-daban, cike da alfahari Ƙasim Birema ya turawa Ciroma ta hanyar whatapp lokacin da Ciroma ya yi arba da hotunan haɗe da video sai da buga ihu idan Allah ya taimake sa, shi kaɗai ne zaune a turakarsa da faɗa ne da mutuncin sa ya gama zubewa. Batareda da sani Aliyu na uku ba Anaal ta haɗa kayanta, ta bi jirgin safe sai Kano ta dabo tumbin giwa sai wani dan gajeren message da ta tura masa "Abbu kada ka sha wahala nemana, na tafi Kano" Abbu yana gama karanta text ɗin nata ransa ya yi mummunan ɓaci yasan ko ya gwada kiran wayarta zai tarar da ita a kashe kamar dai yadda ta saba yi a duk sanda ta yi irin wannan tafiyar ta sirri Allah kaɗai yasan abun da Anaal take aikatawa a ɓoye. *MASARAUTAR KUDU* Wannan ita ce dama ta ƙarshe da Ciroma ya samu da zai tarwatse rayuwar alhalin mai babban ɗaki ba wai Aliyu kaɗai ba suma zunubin Aliyu ya shafe su domin hukuncin su kora daga masaurata. Ciroma ya kira Galadima ya nuna masa video da hotunan wata irin dariyar mugunta Galadima ya kece da ita ransa wasai don har ya fara hango kansa a matsayin sarkin sabon birnin kudu. Kilishi ta kalli amintacciyar jakadiyarta ta ce "Jakadiya burukana ga baki ɗayansu sun gama rugujewa a yanzu banida sauran mafita, tun sanda boka mai Gundulelliya ya juya min baya ya ci amana ta na daina gani haske a almurrana a duk sanda na ƙyala ido naga Ciroma ne a matsayin da nake so jinina ya kasance akai na rantse miki da Allah Jakadiya sai na ji tamkar na haɗiye zuciya na mutu. "Allah ya ƙara miki lafiya da tsawon rai mun riga da mun ɓata kyau tun ran wanka, da mun sani ba mu aikata abun da muka aikata shekaru talatin da takwas a baya da duk haka bata faru damu ba. Yanzu dole mu yi haƙuri mu cigaba da karɓar Ciroma a matsayin ɗan da kika haifa kamar yadda duniya ta daɗe da sani kece mahaifiyarsa. "Uhm! Ba za ki fahimci halin takaici da baƙin ciki da nake ciki faratt ɗaya ba jakadiya kasancewar Ciroma a raye barazana ce babba a gareni, da kike ganinsa wutar ƙaiƙayi ne zai iya bankado dadadden sirri da muka yi haƙa muka binne, saboda haka kafin ya tona mana asiri ki nemo Dogara lokaci ya yi da za mu yi amfani da wancan ɓoyayyen sirri da muka daɗe muna adanawa yanzu ne ya dace mu yi amfani dashi domin tarwatsa Ciroma, kin ga daga Ciroma har Galadima za su ƙare rayuwarsu a maƙargama yayin da ni kuma zan yi amfani da wannan damar na sanya Ahmadu ya ɗane karagar mulkin kudu wannan ita kadai ce damar da nake da ita domin cimma burina. "Wannan haka yake uwardakina a wannan karon ƙarshen Ciroma ya zo shi kenan ruwa ya karewa ɗan kada. Ranki shi daɗe ban da ma Ciroma da watau taya za ki raine sa sannan ya fi ki sani kundin sharri. "Kamar yadda kika faɗa watau da rashin sani wacece ainihin Kilishi shiyasa ya tafka irin wannan kuskure. Jakadiya ta tashi daga durƙuso da ta yi a gaban Kilishi ta fice da sauri. Duk wani mai faɗa aji dake cikin masauratar kudu sai da Ciroma ya kira sa tare da 'yan uwansa dukka ga baki ɗaya faɗa ta cika ta yi makil, yasa aka shigo da Ƙasim Birema wanda daren jiya Galadima ya kawo shawarar shi ne ya fadi haramtacciyar alaka da Aliyu na uku yake aikata wa a boye gudun kada ace sharri suka yi masa.Babu kunya balle tsoron Allah Ƙasim Birema ya karkace kai ya shiga fadar ƙarya da gaskiya, nan da nan faɗa ta hartsune da surutu musamman yan uwa Aliyu da suke uwa ɗaya suna fadar ba su yarda ba sharri ne aka yi wa dan uwansu kowa yasan Aliyu kamili ne ta ya zai aikata irin wannan mummunan kaba'ira. Ciroma kamar wani mutumin kirki ya yi gyaran murya tare da daka musu tsawa wanda hakan yasa fada ta yi tsit! Ya shiga faɗin "A matsayina na sarkinku, shugaba agareku ina mai matukar ba ku haƙuri a bisa faruwar wannan murɗaɗɗen al'amari sanin kanku ne duk wani jinin sarautar Kudu ba za a taɓa kama shi da aikata mummunan zunubin zina duba da irin kyakkyawar tarbiyyar da iyaye da kakannin mu suka ba mu wacce har kawo wannan ƙarni da muke ciki muna kanta. Idan har Ƙasim Birema yana da kwakkwarar huja da zai iya gabatar wa da fada domin ta gasganta, abun da ya zo mana dashi gaskiya ne ko karya. Ƙasim Birema gyara zaman sa yana ƙara sadda kansa ƙasa "Allah ya taimake ka sarki mai adalci tun farko da nayi tunani faruwar hakan duba da yadda mutane suke kallon Aliyu na uku a matsayin mutumin kirki, domin gujewa ka-ce-na-ce sai na yi amfani da waya ta a boye na dauke shi hoto tare da videoYa ciro wayarsa aka jona da ƙatuwar plasma sai ga Aliyu na Uku tare da Maysun waɗansu wurare a cikin video har yana rungumarta da sauri Ciroma ya ce aka kashe tv ɗin muni abun ya yi yawa, tsananin baƙin ciki ya rufe magaji ƙarami ya fashe da kuka zuciyarsa ba za ta iya jurewa ba domin yasan shiryayyen al'amari ne aka shirya domin taɓa kima da daraja yayansa, ya miƙe ya baro cikin fada kaitsaye ɓangaren mai babban ɗaki ya nufa yadda ya shigo yana gunji kuka ya yi bala'in ɗagawa mai babban ɗaki hankali zubewa ya yi a gabanta cikin muryar kuka yake faɗa mata abun da ya faru wani irin bugawa zuciyarta ta yi sai ga mai babban ɗaki ta zube a sume, tashin hankali goma da ashirin aka kwashe ta zuwa asibiti kamin ka ce kwabo, video Aliyu na Uku tare da karuwarsa kamar yadda suka ce ya fara trending a social media wanda aka rasa waye ya saki video. Yaya Gimbiya ce ta ɗaga waya ta kira Aliyu tana kuka tana tsine masa, tare da faɗin idan ya zama silar mutuwar mahaifiyarsu ba za su taɓa yafe masa ba. Cike da tashin hankali ya shigo jirgin yamma shi da twins suka nufo birnin kudu, twins ke kwatar masa da hankali. *KANO NIGERIA* Cikin hukunci Ubangiji su Aydah suka kammala zana jarabawa yanzu tana zaman jiran fitowar result ne. Rumaisa har ta wuce EDD ta wanda hakan ya ɗaga mata hankali ga ciki har ya shiga watanni goma amma babu alamar haihuwarsa, yau da ta je awo sai riƙe ta suka yi aka yi inducing ɗinta Rumaisah tasha bakar wahala domin haihuwa taki zuwa sai azaba take sha daga ƙarshe jini ya ɓalle mata ga baki ɗaya ta fita hayyancinta, dole sai cs aka yi mata aka fito da baby girl wani abun tashin hankali idan ana ƙara mata jini tana bleeding likitocin sun kasa gane idan matsalar take. Aunty Raliya ce ta kira Aydah ta sanar da ita halin da Rumaisah take ciki a haukace Aydah ta iso asibitin, bayan kuka babu abin da Aydah, Ammi da Aunty Raliya wata nurse ce ta fito ta kira Ammi tazo a ruɗe Ammi ta shiga ɗakin tun daga yadda taga numfashin Rumaisah na hawa da sauka ta tsinke, hannunta Ammi ta kama ta jinke cikin nata, idanunta na ambaliyar hawaye "Ammi ki yafe min ki roƙa min gafara wurin Abba da aunty Raliya da yaya Safwan har ma Aydah. Ammi mutuwa zan yi. "Ba za ki mutu ba Rumaisah in shaa Allahu Allah zai tashi kafaɗarki, ki raini 'yarki da hannunki ki bata ingantacciyar tarbiyya. Murmushi kurum Rumaisah ta yi tare da girgiza kai "Ammi ko bayan na mutu don Allah ki cika min alkawarin da na daukar wa Aydah ki bata abun da na haifa nasan za ta kula da ita za ta bata tarbiyyar da kike hasashen zan bata dan Allah Ammi ki cika min wannan alƙawari. Kasa magana Ammi ta yi a dalilin kukan da ya ci karfin ta nurse ɗin da ta shigo da ita ta ja ta zuwa waje, hannun Rumaisa dake cikin nata tasaki har ta isa bakin ƙofa tana waiwayen Rumaisah. Bayan fitar Ammi aka sakawa Rumaisah oxygen, babu jimawa numfashinta ya tsaya cak! Hatta da likitocin dake kanta sai da mutuwarta ta girgiza su, sai dai babu yanda suka iya duk mai rai sai ya dandani mutuwa. Farin mayafi suka ja tare da lulluɓeta kana babba daga cikinsu ya fito yana goge zufa dake ta tsatsafo masa a goshi cikin rauni murya ya faɗa musu rasuwar ta. Daga Ammi har su Aydah rushewa da matsanancin kuka har aka wuce da gawar Rumaisah zuwa gida Aydah ta kasa daina kuka da kyar ta iya kiran Mami da Daddy ta faɗa musu hatta da Sadiya da bata jituwa da Rumaisah mutuwarta ta girgiza ta. Misali karfe 4:30pm aka yi jana'izar Rumaisah aka kaita gidanta na gaskiya, duk wanda ya zo ta'azziyya zai tarar da Aydah rungume da baby a jikinta, ta yi kuka har idanunta sun kumbure mutuwar Ab ta dawo mata sabuwa ji take kamar yanzu ne ta rasa shi, idan kuma ta tuno da irin zaman da suka yi da Rumaisa shi kenan sun tafi sun barta sai ta sake fashewa da kuka. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. [2/6, 1:54 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye. 097. Har aka yi sadakar bakwai Aydah bata daina kukan mutuwar Rumaisah ba. Yadda ta yi kukan mutuwar Rumaisah bata yi ta Ab haka ba saboda duk sanda ta kalli Babyn Rumaisah sai tausayin yarinyar ya kamata sai ta ji mutuwar mamarta ya dawo mata sabuwa. Ammi bata hana wa Aydah tafiya da little Rumaisah wacce suke yi wa lakabi da Baby Noor sai dai Mami ce ta nuna ƙin amincewarta a cewarta yaushe aka gama rainon Aydah ballantana ta raini wani ko ma wanin jinjira sabuwar haihuwa.Haka Mami,ta murje ido renon baby Noor ya koma hannun Ammi,Amman kullum Aydah na hanyar zuwa gidansu Rumaisa ganin Baby Noor,idan Mami tace abun baya daga mata hankali tayi karya.har shawara Hajiya Zeenah ta kawo mata akan ayiwa Aydah asirin da Baby Noor za ta fice mata arai ta ji ta tsani yarinyar Ga baki ɗaya Mami taki yadda da haka. Tun da ta yi wa Daddy asiri ya kori AB bata kara ganin kwanciyar hankali cikin gidan aurenta ba ga Daddy ya zama wani iri tun faruwar al'amarin iyakasa ya riqa bin kowa da kallo bai cika magana ya dawo mata miskilin ƙarfi da ya ji, shi kan murmushinsa ba ma za ta iya tuna sanda ya yi mata shi ba. Ga kamfaninsa da ya sakarwa su Alhaji Sanusi da Alh Umaru,sunayin yadda suka ga dama abun duniya duk ya yiwa Mami,yawa karo na farko da ta tsani laifukanta karo na farko da ta yi da danasanin raba Abba Bashir dasu,da tasani da tabarsa, gashi nan dukiyar da take hange tana dab da subuce musu ga bangaren auren Sadiya da Alh samanni kullum cikin tashin hankali suke uwargidanta Hajiya Saratu ta hana Sadiya walwala acikin gidan,tun da ta shigo gidan basu taɓa haɗa shimfida da Alh sammani ba duk lokacin da yazo kusantar Sadiyar sai yaji an mayar dashi kamar ba namiji ba sannan duk lokacin da yake tare da Sadiya,sai yaji tana wani irin mummunan warin jaba har ta kai ta kawo baya kwana a gidan Sadiya,iyakarsa su yi waya idan tana bukatar wani abu ya tura mata kudi ta account ta siya. ba ƙaramin damuwa Sadiya ta shiga ba. wata rana Siyama,ta kai wa Sadiya ziyara ganin halin da Sadiyar take ciki yayi mugun ɗagawa Siyama,hankali dakyar Sadiya ta buɗe baki ta yi wa Siyama bayanin matsalarta da Alh.samanni tun lokacin da ta tako kafarta acikin gidansa bata kara samun farin ciki ba,haka take fadawa Siyama wata rana jin take kamar ta kashe kanta saboda bakin ciki har wurin malamin dake mata aiki ta koma ta tarar ya mutu. Dan tasan ba haka Hajiya Saratu tabarta ba. Siyama ,ta girgiza kai tana faɗin."Yaya Sadiya har yanzu duniya bata koya maki hankali ba?"baki tuna irin hakkokin mutane dake kanki ba keda Mami,nasan duk irin biyar malamman da kuke yi yaya Sadiya ki godewa Allah tun da Allah ya fara nuna maki ishara tun anan duniya. Da shock Sadiya ke kallon Siyama,bata taɓa tunanin duk tasan irin abubuwan da suka aikata ta karkashin ƙasa ita da Mami ba, Siyama ta gyada kai tana faɗin."nasan komai yaya Sadiya,ko asirin da kika je kika saka gidan yaya Abba ni da kaina naje na cire,yaya Sadiya tun kafin lokaci ya kure maki ki tuba ki komawa Allah. Wata irin nasiha Siyama, keyi wa Sadiya mai shiga jiki har dare suna tare da Sadiyar haka Sadiya ta dauki alkawarin duk irin shawarwarin da Siyama ta bata za ta yi amfani dasu tun daga lokacin Sadiya,bata barcin dare ita ce azumi Litinin da Alhamis,ita ce zuwa makarantun islamiyya a boye tana bada sadaka cikin watanni ukku Sadiya ta yi wani irin sanyi na ban mamaki, haka zalika taga canji sosai a al'amurranta musamman yanzu Alhaji sammani da yake zuwa gidanta yana kwana,shima tana masa addu'a sosai dan ta lura ba haka nan kawai matarsa tabarsa ba,itama tana sa yayi sallolin dare da yawan azkar da azumi,shi kansa yaga canji sosai ajikinsa duk wannan tsoron matar tasa Saratu da yake yi ya ragu sosai a zuciyarsa har takai ta kawo wani dare ya nemi Sadiya da karfin addu'oin da suke yi daga shi har ita a ranar yasan Sadiya a matsayin 'ya macce. Hawaye ta rika sharewa afakaice tana godiya ga Allah da yaganar da ita kuskurenta tun anan duniya. Ita ma Mami,sosai tayi murnar yadda Sadiya hankalinta ya kwanta. Yau tun karfe bakwai Siyama ta kira sadiya a waya suka gaisa,cikin sanyi murya Siyama ke faɗin."yaya Sadiya ko mu je mu lallashi Mami,tayi hakuri tabar Aydah ta karbi Baby Noor. Naga yadda Aydah take cikin damuwa hanata karɓar ta da ta yi,kina ganin yadda Aydah ta zabge tayi wata irin rama lokaci ɗaya, don kawai Mami ta hanata daukar Baby Noor ina tsoron wani ciwo ya je ya shige ta, ga Daddy yaki yace komai a maganar. Siyama ta karasa maganar da karaya a muryarta Sadiya ta sauke numfashi tana faɗin."ki fito da wuri sai ki biyo tana nan ki daukeni da mota,ni kaina damuwar Daddy tana damuna. Da haka suka yiwa junansu sallama,kusan karfe goma na safe sai ga Sadiya da Siyama,sun zo gida bangaren mahaifinsu suka nufa kai tsaye Aydah suka samu wurin Daddy, Daddy ya daga kai ya kallesu har suka karaso cikin falon cike da girmamawa suka nufi mahaifinsu suka durkusa a kasa suka gaishesa da respect ,ya amsa yana tambayarsu mazajensu,acan kasan ran Daddy ,yaji dadi yadda yaga ya'yan nasa sun natsu lokaci ɗaya,musamman Sadiya bai taɓa kawowa ransa zata canja haka cikin sauki ba. "Auta yau baki fita school ba?"Aydah ta mairairai ce masu tana faɗin."bata da lecture sai zuwa karfe biyu, murmushi dukansu suka yi mata. Shiru ya ratsa a tsakaninsu na kusan sakan biyar,kafin Siyama ta daga kai ta kalli Daddy,da yayi nisa a tunaninsa kallon wani gefe daban yake zuciyar Siyama taji tana wani irin bugawa. Cikin sanyin murya Siyama,ke faɗin."Nasan damuwarka Daddy, Kai musulmine ya kamata ka karbi ƙaddara mai kyau ko marar kyau a duk sanda tazo maka. Daddy yaya Abba addu'ar ka yake bukata koda yaushe. Wanda ya mutu ba zai dawo ba har abada Daddy,ka yadda da wannan komai ya canja saboda rasuwar yaya Abba, Daddy ya kamata ka buɗe ido ka fuskanci harkokin kasuwanci ka kamfaninka ga baki ɗaya ka saki. "Yaya kake so muyi ne Daddy,muna son ganin walwala a fuskarka. Sadiya ta karɓe itama tana masa nata kalar nasihar kafin suyi magana akan abunda ya kawosu. "Daddy kayi wa Mami magana dan Allah tabar Aydah ta riƙe Baby Noor tun da aka fara wannan maganar har yau kaki kace komai. "munafukai dama shiya kawoku kuka dokomin samakko a gida.?" Mami ta faɗa so pissed up a muryarta "ku saboda kuna wawaye ba ku san inda ke maku ciwo ba kamar Aydah ita za tayi rainon jaririyar yarinya?"da karatun da ta fara za taji koda rainon jinjira?" Yadda ta haukace tana faɗa yasa Daddy,ya daga kai yana kallonta "mariya!"ki zauna. Yadda daddy ya kira sunanta cikin wani irin yanayi mai wuyar fassarawa yasa ta nemi wuri ta zauna Amman ga baki ɗaya ranta a ɓace yake."idan cikin zamana dake na taba cutarki ko na rana ɗaya ne Allah ya saka maki tun anan duniya nima idan kin cuceni acikin zamanmu Allah ya sakamin. kalaman Daddy ba ƙaramin razana Mami,suka yi ba ya dubi Aydah yace Mamana da yaushe zaki dawo makaranta?"yaushe lectures ɗinki zai kare.?"cikin rawar murya ta faɗa masa zuwa 6 na yamma ya gyada kai ya kalli Siyama da Sadiya yace ku jira har ta dawo zuwa bayan magarib za muje mu karbo Noor ɗin. Da wani irin farin ciki suke kallon mahaifinsu Aydah ce ta fara matsawa kusa dashi ta Rungumesa haka Siyama kafin Sadiya tabi bayansu. Baki buɗe Mami ta saki tana kallonsu,wani irin mugun sanyi jikinta yayi lokaci ɗaya,kalaman Daddy,ba ƙaramin ruguzata suka yi ba. Tana jin yadda Daddy ke sakawa 'ya'yan nasa albarka. Tun rasuwar AB bata kara ganin Daddy,yana farin ciki ba sai a wannan lokacin. *MASARAUTAR KUDU* Hankali tashe ya iso masarauta kansa tsaye ya wuce kingdom hospital inda mai babban ɗaki take kwace magashiyam! Batasan wanda yake kanta ba. Jininta ne ya yi mummunan hawa Aliyu yana isa ɗakin da take yaya Gimbiya ta taso ta wanke sa da mugun mari cikin tsanani fushi da fusata ta soma zazzaga masa masifa babu kalar zagin da bata yi masa ba. Duk iya ƙoƙarinsa na gani ya fahimtar da ita ya warware mata kurman allo da suke ciki amman taƙi basa haɗin kai, daga ƙarshe ma cewa ta yi ya fice bata son ganinsa. Duk abun da ke faruwa Safiya tana gefen a zaune ko a bisa kuskure bata kalli gefen da Aliyu yake ba. "Yaya Gimbiya Dan Allah ki tsaya ki saurareni koda na mintuna biyar ne. "Bakada sauran abun da za ka faɗa har ni ɗin nan na saurare ka Aliyu, ka ci mutuncin mu ka tozarta mu a idon duniya ka wulakanta martaba ta wannan gidan, amma kasani kanka ka yi wa. Dafe goshinsa ya yi ga baki ɗaya ji yake duniya ta yi masa zafi tare da yi masa juyin ɗan mangwaro. "Yaya Gimbiya wannan video da ake yawo dashi ta cikin video mata ta ce da muka yi aure tsawon shekaru talatin da biyu.. "What?? In shock yaya Gimbiya ta furta tare da zaro idanuwanta waje tana kallon Aliyu, wani irin juyowa Safiya ta yi tare da miƙewa tsaye har kujera da take zaune akai ta fadi jikinta ne ya ɗauki rawa sai kakkarwa take yi tamkar mai jin sanyi, tsabar kaɗuwar da ta yi har dishi-dishi take gani kallon Aliyu take ta faman yi babu ko kyaftawa ta kasa yarda da abun da kunnuwanta suka ji. Lallai namiji munafuki ne sai yau da asirinsa ya gama tonuwa sunansa ya ɓaci a idon duniya kowa yana masa kallon fasiki mazinaci sannan zai gayamusu wannan daɗadden sirri wato da asirinsa bai tonu ba yana nufi kenan zai yi ta boye musu ne. Nan da nan ƙwaƙwalwarta ta soma tunano mata irin kalar ƙunci da ta dinga shiga tun aurenta dashi, da irin halin ko in kula da yake nuna mata. Yes! Tasan ta yi haƙuri yayin zamanta dashi ta yi juriya haɗe da haɗiye tulin baƙin ciki da yake jefa ta ciki, daidai da rana ɗaya bata taɓa tuhumarsa ba ko ta ji haushinsa kullum burinta ta kyautata masa kuma tana masa uzuri ga zamantakewar su. Sanadin baƙin cikinsa yasa depression ya kamata, kuma har kawo yau ɗinan da yake tsaye a gabanta bata taɓa kai karar sa wurin kowa ba. Ashe duk wannan baƙin wulaƙanci da yake mata saboda wata macce ne duk da bata ganta ba tana da yakini ba za ta fi ta nagarta ba. Akanta ne ta ɗauki tsawon shekaru ashirin da bakwai bata gane kan mijin da take aure ba sai nuƙurƙusar baƙin ciki da zaman haƙuri take yi, iyakacinta tana amsa sunan matar aure ne ba don tasan daɗi dake cikinsa ba. Cikin wani yanayi ta tako ta iso gaban Aliyu na uku ta tsaya tana ƙare masa kallo from head to toe kamin ta girgiza kai hawaye masu masifar zafi suka wanke mata kumatu, cikin sarƙewar lafazi ta furta "ina so ka sake maimaita abun da ka faɗa yanzu nan Aliyu. A rikice Aliyu na uku ya jefa ƙwayar idonsa cikin nata zuciyarsa tana wani irin bugawa domin ba zai iya tuna sanda Safiya ta kira ainihin sunansa ba tun kafin ta haifi Anaal take kiransa da Yallaɓai bayan haihuwar Anaal ne ta sauya masa suna zuwa Abbu amma a yau gata tsaye a gabansa tana kallonsa ido cikin ido ta kira sunansa na yanka lallai wannan al'amari babba ne ya zarce yadda yake tunani. "Mata ta ce Safiya sunanta ma.... "Bana so jin sunanta bana kuma buƙatar sake ji komai akanta. Safiya ta faɗa tare da juyawa a fusace ta nufi ƙofar fita da sauri Aliyu na uku ya cimmata ya riƙo hannunta "Kafin ki tafi Safiya ki tsaya na ba ku labarin yadda al'amarin ya wakana. "Don girman Allah ka cika min hannuna Aliyu a halin yanzu ina cikin yanayi da ni kaina tsanar kaina nake to balle kai da ka kasance makasudin da yasa nake ji wannan tsanar. Sannu a hankali ya sakar mata hannu ta juya tare da barin asibitin, komawa ya yi gaban yaya Gimbiya ya mugun kallon da take masa kaɗai ya isa ya gamsar dashi ita ma ba za ta saurare shi, saboda haka ya bar asibitin ya nufo gida ba. Tun kafin ya shiga gidansa ya tarar da ɗan aike fada tana nemansa, ko kadan bai tsorata da kiran da ake masa ba duk tsiyarsu bai wuce su ce sun sauke shi daga sarautar sa ba. Daman can ba damuwa da sarautar ya yi ba damuwarsa ɗaya ce mai Babban ɗaki ya za ta ji idan ta farfaɗo ta tarar da baya matsayin sarki Allah kaɗai yasan irin halin da za ta sake shiga. Fada ta cika ta yi makil duk wani mai faɗa a ji acikin masauratar kudu yana cikin fada, malam Liman ya buɗe taro da addu'a kana magatakarda ya karanto laifin Aliyu, daga nan waziri ya ɗaga hannu alamar yana so abashi dama zai yi magana. Sarki Hashim Ciroma ya ɓata fuska domin ya kwana da sani Waziri baya tsagin zalunci kuma tun da ya nemi abashi dama ya yi magana tabbas akwai wani abu a ƙasa, cikin daurarriyar fuska Ciroma ya gyaɗa kansa don bai isa ya hana sa magana ba a fada ba hakan zai iya kawo kananun maganganu. Waziri ya kalli Aliyu yana faɗin "Kafin zantar da kowanne irin hukunci yana da kyau mu tsaya mu saurare bangarori biyu, Aliyu fada tana tuhumar ka da zubar mata kima da daraja ta hanyar ajiye wata macce kana fasikanci da ita, ka kuma san irin hukunci da aka tanadarwa duk wanda aka sama da aikata zunubi irin wanda kai ɗinan ka aikata. Karo na farko da Ciroma ya ji waziri ya burge sa ko kaɗan bai yi tsammaci irin wadannan maganganu ne za su fito daga bakinsa ya zaci ko zai nemi ya kare Aliyu. Kafin Ciroma ya gama tunani ya tsikayi muryar Waziri yana cigaba da faɗin "inaso ka faɗa mana hakikanin gaskiya abun da ya faru shin da gaske ne ka aikata abun da fada ke tuhumarka dashi?" Aliyu ya yi shiru batareda ko ɗaga kansa ya kalli duk wanda ke cikin fada ba waziri da yaga shiru na Aliyu yana neman ya yi yawa ya sake kwatar da muryarsa, ya ce "Na haɗa ka da girman Allah Aliyu ka buɗe baki ka yi magana ka tuna girman wannan al'amari idan ba ka yi magana ba, fada za ta yanke maka hukunci marar daɗi. Ina ji a jikina Aliyu ba ka aikata wannan al'amari ba dole da akwai wani kurman allo da kai kaɗai kasan da wanzuwar sa. Karo na farko da Aliyu na Uku ya ɗago ya bi mutane dake zazzaune a faɗa da idanunsa, kafin ya sauke numfashi ciki maganarsa mai cike da zallan izza ya ce "Ina mai ba wa fada haƙuri da sauran jama'a tabbas wannan video ɗin babu ƙarya ni ne a ciki. Nan da nan fada ta hartsune da surutu mutane sai sallati da tafa hannuwa suke yi, sai da sarkin fada ya tsawata musu sa'annan suka yi shiru, waziri ya kalli Aliyu na Uku ya ce "Kai muke saurare ranka shidade ko iya abun da za ka ce kenan. "Shuɗadden al'amari ne da ya faru tun lokacin da na je karatu a London, anan na haɗu da ita a wancan lokaci tana amsa sunaye guda biyu domin iyayenta suna bin mabanbanta addinai, mahaifinta ya kasance musulmi ne ɗan ƙasar Qatar shi yana kiranta da Maysun, mahaifiyarta kuma 'yar asalin Rasha ce Christan ce shi yasa take kiranta da Elissa. Koda muka yi aure tana matsayin christan. Sake harsunewa fada ta yi da surutu, kowa da kalar abun da yake fada. Hakan yasa Aliyu na Uku ya dakata da basu labari ya ja bakinsa ya tsuke. Ga baki ɗaya mutane dake fada mamaki ne ya lulluɓe su an ɗauki lokaci kamin sun yi shiru in da Aliyu na uku ya cigaba da basu labarin yadda soyayyarsa da Maysun ta fara har izuwa aurensa tare da ɗa da suka haifa har ɓatansa da irin fafutukar nemansa da suke yi, domin ya sami wata majiya mai doshe wanda suke zargin ɗansu yana wurinsa yana zaune a garin Katsina. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO. [2/6, 1:54 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 098. Bayan ya gama basu labari fada ta yi shiru yayin da baƙin ciki ya lulluɓe Ciroma ji yake yi kamar ya haɗiye zuciya, ga takaicin Waziri da ya gama cika sa duk shi ne ya rugaza masa plan da so ya yi da zarar Aliyu ya amsa kiran fada ba zai tsaya sauraren wani banzan labarinsa ba zai sa a tube masa rawaninsa ya cikawa Galadima alkawarin da ya ɗaukar masa amma wannan ɗan bagidajiya waziri ya lalata masa komai. Amma duk da haka zai nuna shi yake da ƙarfin iko a masaurata yana wani muzurai ya ɗago ya ƙarewa fada kallo, kana ya kara ɗaure fuska tamau ya murza zoben tsafi da boka mai Gundulelliya ya mallaka masa a duk sanda yake so ya aiwatar da wani zalunci wanda babu wanda ya isa ya musa masa yake amfani dashi da zarar ya murzarsa shi kenan magana ta kare. Cikin kakkausar murya ya ce "wannan labarin naka Aliyu duk wani mai cikakken hankali ba zai yarda dashi ba, idan har da gaske kun yi aure da ita dadiron taka ka faɗa mana ina shaidunka, da waliyain ka,ko kana nufi haka sidam kun ka yi aure har da haifar ɗan shege. Wani irin ɗagowa Aliyu na uku ya yi kiran ɗansa da suna shege da Ciroma ya yi ya taɓa sa matuƙa, nan da nan idanunsa suka fara canza colour. Tsanani ɓacin rai yasa ya yi shiru ya kasa bashi amsa, daman abun da Ciroma ke so kenan ya harzuƙa sa saboda yasan Aliyu akwai zuciya da zafin kai. "Ka ba mu amsa Aliyu idan kuma ƙaryayyakin naka sun ƙare sai mu sani. Nan ma Aliyu bai tanka sa ba sai ajiyar zuciya yake saukewa tare da furza da zazzafar iska daga bakinsa, waziri ne ya taso da gun zamansa ya koma kusa da Aliyu ya sassauta murya ya ce "Kada ka bari fushinka ya zama makamin da za a cutar da kai Aliyu, ka tuna girma da martabar da wannan masauratar take da babban abun takaici ne ace yau an kore ka daga cikinta. Ka tuna halin da mahaifiyarka take ciki da irin abun da zai iya faruwa da ita idan ta farfaɗo ta sami mummunan labarin korar ku daga masaurata. Runtse idanuwa Aliyu na Uku ya yi shi kadai yasan irin zogi da raɗaɗin da yake ji ciki da wajen zuciyarsa, amman da ya tuna da mai babban ɗaki ya tuna da irin yadda ta dauki gidan sarauta tamkar rai da numfashinta tabbas idan aka kore su za ta iya haɗiye zuciya ta mutu. Tunawa da haka da ya yi yasa ya ɗan sassauta fushinsa ya ce "Allah ne kaɗai shaida ta, sai kuma church ɗin da aka ɗaura mana aure, domin gudun faruwar hakan yasa muka yi marriage certificate idan fada tana bukata zan iya gabatar mata da certificate ɗin tare da waɗansu daga cikin pictures da muka ɗauka a ranar daurin auren mu. "Wadannan ba za su taɓa zama gamsasshiyar hujja a garemu Aliyu, ka kawo mana shaidu na mutane da suka ga lokacin da kuka yi aure, tsawon shekaru talatin har da doriya ba wasa ba. Idan har ba ka da shaidun gani da ido kasani za mu hukunta ka, kamar yadda yake acikin kundin tsarin mulkin masauratar Kudu. "Ina da shaidun gani da ido ahalin yanzu bansan inda suke ba, sune mutane da yarona Muhammad Azhar yake hannunsu ina rokon fada da tabani dama zan nemo Bashir da mai ɗakinsa Maryama a wancan lokaci a gaban idonsu aure ya wakana tsananina da Maysun, zan kuma kawo Maysun fada ku ji ta bakinta. Aliyu na uku ya ƙarasa magana yana ƙoƙarin danne zuciyarsa don ji yake kamar ya gaggayawa Ciroma baƙaƙen maganganu sai kuma ya tuna da matsayin Ciroma a yanzu. Ciroma ya ƙara daure fuska, alamar zai zantar da hukunci da yake da burin zantarwa da Aliyu na Uku. "ina son kasani Aliyu mu ba jahilai bane muna da ilimin addini da na zamani kuma Allah ya yi mana basirar fahimtar gane gaskiya da karya. Kasani ka ci mutuncin masaurata ka zubarwa da ahalin wannan gidan daraja sabida haka ba za mu bar haka ba dole sai mun hukunta ka domin ya zama izzana ga 'yan baya. Na tabbata da mahaifin mu na raye ba zai kyaleka ba a bisa wannan mummunan zunubi da ka aikata. Don haka mu ma da shi muke koyi ba za mu lamunta ba jini wannan alhali ya je yana aikata fasikanci a fili har mutane suna dauka ana yaɗawa akan kafafen sada zumunta, lallai kasani ba za mu kyale ka ba Aliyu Ina sarkin fada? "Gani Allah ya ƙara ma lafiya. "Ka tube mana rawani da ke kan Aliyu na Uku daga yau mun cire shi daga karagar sa ta mulki daga yanzu shi ba sarkin sabon birnin kudu bane. Kuma ya tattara shi da ahalinsa dukka su fice daga masarauta ba ma bukatarsa kuma yasani daga yau mun cire shi daga zuri'ar mai martaba sarki Usman na Uku. Hatta da mahaifiyarsa dake kwance akan gadon asibiti ba ma bukatarta acikin masaurata. Nan take sarkin fada ya tube rawani Aliyu na uku, magatakarda ya rubuta takardar korar Aliyu sarki Hashim Ciroma ya buga hatimin masaurata akai. "Akwai wanda yake da ja akan hukuncina?" Ciroma ya faɗa yana zare ido fada ta yi shiru kowa ya kasa koda kwakkwaran motsi, hatta da waziri dake kare Aliyu na Uku ya kasa magana sai sadda kansa ƙasa da ya yi yana jin baƙin ciki akan abun da aka yi wa Aliyu zuciyar Aliyu tana farfasa ya karɓi takardar ya fice daga fada Magaji ƙaramin ne ya biyo shi a baya "Yaya ka yi haƙuri kowanne bawa da kalar tasa ƙaddara idan muka yi haƙuri komai zai wuce babbar damuwata yaya Gimbiya domin ita mutum ce mai zafin gaske marar karɓar uzuri dole ka toshe kunnuwanka domin Allah ne kaɗai yasan adadin maganganu da za ka ji daga bakinta. "Karka damu magaji ƙarami nasani na aikata laifi mai girma amman duk da girman laifina a tsaye a dubi lamarina da idon basira na faɗi hujjojina da dalilai da yasa na yi aure batare da sanin alhalina ba, na kuma ɓoye hakan tsawon wasu shekaru haka sidam ba zan boye wannan al'amari mai girman gaske. "Haka ne yaya ni dama jikina ya bani da dole akwai dalilinka na yi hakan. Aliyu bai ƙara cewa komai ba ya cigaba da tafiya kamin ya isa ɓangaren sa ya sami kira daga ɓangaren mai babban ɗaki dole ya juya ya nufi can koda ya iso parlornta 'yan uwansa su biyar da suke uwa ɗaya uba ɗaya sun yi zaune zugu-zugun ƙanwarsa Hauwa da yaya Gimbiya sun sha kuka har idanuwansu sun kumbure, babban ƙasƙanci ne ga jinin sarauta ya waye gari an kore sa daga masaurata musamman Aliyu idan ya kasance ya aikata fasikanci. Jikinsa ya yi bala'in sanyi ya nemi wuri ya zauna yaya Gimbiya ta taso a mugun fusace ta yi kansa ta rufe shi da duka tana dukansa tana kuka tare da fadar maganganu marasa daɗi "Ka cuce mu Aliyu ka dasa mana baƙin ciki da har mu kwanta dama ba zai fita daga zukatanmu ba. Ka ja mana abun kunya da tozarci a zuri'ar mu, kasani ba za mu taɓa yafe maka ba. Abdallah na Uku ne ya taso ya kama yaya Gimbiya ya maida ta wurin zamanta, daman Abdallah kusan halinsa ɗaya da marigayi Mahmood na Uku, halin dattaku da haƙuri da matuƙar wahala su biyu nan su yi fushi haka zalika mubashir wanda suke kira da magaji ƙarami, kasancewar shi ne ƙarami daga cikin 'ya'ya Usman na uku shiyasa ake kiransa da magaji ƙarami, sai kuma Gimbiya Hauwa wacce daga Aliyu na Uku sai ita. Ita ma Hauwa tana da sanyi hali sosai bata da hayaniya sai dai akwai ta da izza da taƙama, kusan halin mai babban ɗaki ta dauko. "Dan Allah ya isa haka yaya Gimbiya wasu matsaloli ba a iya magance su acikin fushi, kamata ya yi ki tsaya mu ji ta bakinsa. Abdallah na uku ya faɗa yana kallon cikin idanuwan yaya Gimbiya, wacce sai huci take yi tare da jin tsanar Aliyu. "Babu buƙatar hakan Abdallah, tun da har ya zabi ya ci mutuncin mu ya tozarta mu, ya sani muma bama buƙatarsa daga cikinmu daga mun cire ka daga cikin yayan da mahaifiyar mu ta haifa, daga yanzu mu huɗu ne. Aliyu ya ɗago ransa a ɓace yake kallon yaya Gimbiya kafin ya miƙe tsaye, idanunsa sun yi jajir "Daman can ban tsammaci sassauci ko tausayawa daga gare ki ba yaya Gimbiya, ga kowanne irin al'amari kanki kawai kika sani bakisan ki yi waninki uzuri ba, idan har barin cikinku shi zai sa ku rage jin raɗaɗi da zafin ɓata muku suna da nayi to albishirinku zan yi nesa daku har izuwa lokacin da gaskiya za ta yi halinta a wannan lokaci ku ne za ku nemi ni da kanku. Domin nasan wannan hukuncin da Ciroma ya yanke min kaitsaye akwai maƙarƙashiya acikinsa tare da munakisa, dole da akwai wata boyayyar manufa da yake so ya cimma. Zan koma Lagos ku yi haƙuri a bisa ɓata muku suna da nayi. Yana karashe magana ya juya "Abbu mu ma za mu bika mu koma tare Lagos ɗin. Zaheed ya faɗa cikin sanyi murya a rikice Fulani babba ta ɗago tare da daka masa tsawa "Ku koma ina? Ai ku da sake zama dashi hayatan-hayatan ko su kike yi ya ɗora ku a bakar hanyar da yake kai. Kashin kaji da ya shafa muku ya isa haka. Daidai kofar fita Aliyu na uku ya tsaya cak! cikin kaɗuwa ya juyo yana kallon Fulani babba, bai taɓa tsammani fitar irin wannan maganganu daga bakinta ba duba da yadda take mace mai kawaici da kauda kai, ashe akwai ranar da za ta zo duk masoyansa su koma makiyansa. Ya juya da sauri ya fice, tafe yake yana haɗa hanya don har wani dishi-dishi yake gani. Aliyu yana ficewa yaya Gimbiya tasa aka haɗa kayan sawar mai babban ɗaki tare da waɗansu muhimman abubuwanta, suka bar cikin masaurata daga nan suka wuce Abuja da ita. Aliyu yana shiga ɓangarensa ya tarar da Safiya ta gama hada kayan sawarta da na yaranta dukka a manyan trolleys hatta da na Anaal ta haɗa bata bar ko ɗaya ba. Duk da tun zuwan Aliyu bata ga Anaal tare dashi ba taga twins amman babu Anaal acikinsu tashin hankali da take ciki ya hanata tambayar twins ina take. Yana shigowa tambaya ta farko da ta fara masa "Ina Anaal?" Yadda tai masa tambaya da daurarriyar fuska yasa jikinsa ya ƙara yi wani irin cikin sanyi murya ya ce "Tana Kano. "Na kira wayarta bata shiga idan akwai wani layi ka gayamata idan tana bukatar gani na ta same ni a Bauchi. "Bauchi? Safiya me za ki je yi a Bauchi? A tunanina za ki bini Lagos. "A'ah! Bauchi zan koma gaban iyayena gara mu ba wa junanmu space Aliyu wata kila ta hakan za mu iya gane muhimmancin junanmu. "Kina nufi kema za ki guje ni Safiya kema kina min kallon fasiki?" "Ba ko ɗaya kawai dai ina gani lokaci ya yi da kowanne mu ke buƙatar hutu. "Karki min haka Safiya Dan Allah karki guje ni adaidai lokacin da kowa yake guduna, ina tsananin buƙatarki kusa dani. "Kada ka cilasta min Aliyu zuciyata ba za ta iya jurewa ba,ka tuna da adadin baƙin ciki da na dinga shanye wa akanka a wannan karon ka zo min da babban al'amari da nake bukatar nisanta kaina daga gare ka koda na ɗan wani takaitaccen lokaci ne Dan Allah ka bani wannan damar, ita kadai nake buƙata gareka. "Safiya Dan Allah! "Ya isa Aliyu kada ka cigaba da rokona saboda na rika na yanke hukunci, zan tafi. Tana karasa magana ta juya idanunta na fidda zafafan hawaye, da sauri ya riƙo hannunta tana juyowa ya rungumeta sosai, cikin rauni murya mai cike da ban tausayi ya ce "Kamin ki tafi ki barni na ji ɗumin jikinki Safiya bansani ba ko shi ne abu na ƙarshe da zai sake kasancewa tsakanina dake, in fact ina buƙatar kafaɗar da zan ɗora kaina na yi kuka kuma a tausaya min har a rarrashini ina da yaƙini ke kaɗai ce za ki yi min wannan. Kukan da Safiya take dannewa ne ya subuce mata ga baki ɗaya, tsananin tausayin mijinta ya lulluɓeta har batasan sanda ta ƙanƙame shi tana bubbuga gadon bayansa, wani irin jan numfashi Aliyu ke yi idanunsa sun ri ga da sun soye jaruntarsa ba za ta barsa ya zubda hawaye ba. Amma yana jin wani irin tuƙuƙi a kasan zuciyarsa. Sun ɗauki lokaci rungume da juna kamin ta janye jininta daga nasa ta juya da sauri ta nufi ɗakin yaranta Amal da Amatullah tarar dasu zaune sun yi zugu-zugun kowacce taci kuka wanda har zuwa lokaci basu daina yin sa. "Ku taso mu tafi. Ta faɗa cikin muryarta mai ɗauke da kuka, su Amal suna fitowa suka ga Aliyu da gudu suka rungumesa, tare da ƙarawa kukansu sauti. "Ku yi haƙuri my little princesses Barbie Abbu bai kyauta muku ba ya zama silar zubda hawayenku. "Ka daina faɗar haka Abbu dukkan mu, mun sani sharri aka yi maka kuma in shaa Allahu duk wanda yake da sa hannu wurin bata maka suna Allah ya tona masa asiri. Amal ta faɗa tana shasshakar kuka. Murmushi kurum Aliyu ya yi tare da sumbatar forehead ɗinsu, ya ce "Za ku tafi Bauchi tare da umminku idan komai ya daidaita zan zo gare ku, ku kula da umminku. Safiya da kasa jure cigaba da jin kalaman Aliyu ta juya da sauri ta fice daga parlorn idan ta cigaba da tsayuwa zai iya karya mata da zuciya ta fasa tafiya, alhali tana gani tafiyarta ita ce zai basa damar fahimtar amfaninta cikin rayuwarsa. Ta hakan ne kaɗai za ta san matsayinta a wurinsa. Har parking lot ya rakasu yana tsaye har motarsa ta fice daga masarauta, sai da ya daina hange su kana ya juya jiri na dibar sa, sai lokacin ya ji wasu ruwa masu zafi sun sauka a kumatunsa a tsorace ya kai hannunsa ya shafi kumatun nasa, hawaye ya gani a tafin hannunsa. Da saurinsa ya koma ɓangarensa yana jin tsoron ya haɗu da wani yaga hawayen idonsa garesa wannan babbar kasawa ce. Cike da jarunta da ya ara ya yafa kansa ya harhada muhimman abubuwansa, ya yi parking ɗinsu a trolley biyu. Direbansa ya umarta da ya kaisa Airport har ya isa airport yana gwada kiran layunka Anaal, still dai a kashe. Misali ƙarfe 4:00pm jirgin da zai shiga ya ɗaga zuwa Lagos. Amintacciyar jakadiyar Kilishi ce ta zo mata daddaɗan labari na korar alhalin mai babban ɗaki da Ciroma ya yi a maimakon ta ga farin ciki akan fuskar Kilishi sai taga saɓanin tunaninta, domin kuwa wata kalar zabura Kilishi ta yi, jikinta ya ɗauki rawa tana kakkarwa "Lallai ki sani Jakadiya Ciroma ya tafka babban kuskure wanda ba shi kaɗai ba har mu ɗinan sai ya shafa shiyasa tun farko na hane sa da hawa karagar mulkin kudu amma yaƙi ji, to tun da yaƙi ji lallai baya ƙi gani ba, a wannan karon bana tunani bokansa zai iya cetonsa daga wutar dashi ya kunnowa kansa ita. "Ban fahimci wannan kurman allo naki ba ranki shidade shin ko za ki iya warware min zare da abawa?" "Lokaci ne zai warware miki hakan jakadiya sai dai ina miki albishir da komai ya lalace ki tuna da maganar da jiya malam na kan tudu ya faɗa. A rikice Jakadiya ta faɗi zaune daga durƙuso da take idanunta suka firfito waje "Na shiga uku uwargijiyata yanzu mene ne mafita?" "Bana tunanin muna da wata mafita Jakadiya kawai dai yanzu ki yi kokari ɗan abun da ya rage mana ki fito dashi, gara ayi mutuwar kasko. *ALH BELLO MADAWAKI MANSION* Daga Daddy sai yaransa suka zo gidan su Rumaisa Mami kasa biyo su ta yi, saboda tsananin kunyar abun da ta aikata take ji. Kyakkyawar tarba Ammi ta yi musu cikin sa'a suka tarar da mahaifin Rumaisa yana gida a mutunce suka gaisa da Daddy, kana Daddy ya faɗa musu makasudin zuwansa. "Babu komai Alhaji daman can wasiyyar da Rumaisah ta bari kenan 'yarta ta taso a hannun Aydah saboda haka ni ba zan hana ku tafiya da baby Noor ba sai dai Dan Allah a dinga kawo mana ita akai-akai muna ganinta. Ammi ta yi magana tana share hawaye da gefen hijab ɗinta "karki damu Hajiya indai dan wannan ne bakida matsala. Daddy ya faɗa da murmushi akan fuskarsa sun ɗan daɗe a gidan Daddy da Alh Bello Madawaki suna hirar yaushe gamo, kamin Ammi ta haɗa kayan Baby Noor wacce tun zuwansu Aydah ta goye abarta, har wurin mota su Ammi suka rako su. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. [2/7, 3:02 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 099. "Daddy ya kamata a samowa Auta mai Reno,saboda ba zai yiwuwa ba ta rika zuwa da Baby Noor a school ba hankalinta zai rabu gida biyu. Sadiya ta faɗa tana kallon Daddy,Siyama ta amsa zancen da faɗin "Hakane Daddy,da Mami, zata bar Huwaila sai ta dawo gidan ta rika kula da Baby Noor kafin Aydah ta dawo school. "wannan ma shawara ce mai kyau. Daddy ya faɗa yana kallon Aydah yana cigaba da faɗin."ki kiramin Huwaila a waya ki faɗa mata gobe da safe ta taho ta sameni kafin na fita aiki ina ganin gobe zan koma office. kallon mahaifinsu suke yi cike da farin ciki acikin fuskokinsu. Da gaske za ka koma office Daddy?" Aydah ta faɗa sounding so very happy a muryata. "In shaa Allahu zan koma auta. "mungode sosai Daddy. Siyama ta faɗa wearing a loverly smile "Allah ya dafa maka ya shiga lamurranka a duk inda zaka taka kafafunka. Cewar Sadiya ita ma da murmushin kwance a fuskarta. "Ameen duka suka amsa har suka isa gida hirar farin ciki suke ba zasu iya tuna wane lokaci ne suka zauna suka yi farin ciki irin wannan tare da mahaifinsu ba ,tun kafin ayi zancen auren Sadiya da Abba. Sai da suka ci abincin dare tare da mahaifinsu cikin nishadi da annashuwa Mami,dai sai binsu take da kallo. ga baki ɗaya jikinta a mace yake sai da suka gama Daddy,ya koma bangarensa Aydah ta nufi ɗakinta da luggage ɗin Baby Noor. Sadiya da Siyama,suka nufi bangaren Mami suka cimmata har ɗakinta sai da suka kwankwasa kofar tai masu izinin shiga sa'annan suka shiga da sallama a bakunan su kallo daya,Mami tayi masu ta dauke kanta ta cigaba da danna wayar hannunta. Daga Sadiya har Siyama jiki a sanyaye suka karaso cikin ɗakin,kan Soofa suka zauna. "Mami dan Allah kiyi hakuri bamu da niyyar mu bata maki rai kema muna son muganki cikin farin ciki kamar yadda muke so muga dayddy. Mami abubuwa sun ta faruwa marar dadi ji da gani tun akan auran yaya Abba Mami tunaninki ya canja imaninki yayi karanci duk da haka Allah ya nuna maki karfin ikonsa ya tabbatar da sai yaya Abba yayi zaman aure da Aydah. tau yanzu duk wannan rigingimun da ake yaya Abba baya ma duniyar sai idan mun tunasa muyi masa addu'a sai kuma gudan jininsa da yabar mana wanda ba zamu iya gudunta ba dole mu kaunaci abun da yafito daga jikin yaya Abba. kuma Mami,Noor kawai ce zata cirewa Aydah kewar yaya Abba kina ganin yadda damuwa tayi mata yawa duk adalilin yaya Abba,yanzu mun samu abunda zai cire mata kewa miyasa ba zamu karbesa da hannu bibbiyu ba? Sadiya ta nisa ta cigaba da faɗin."Mami Ni kaina naga ishara tun a duniya?"nayi aure sama da watanni uku babu kwanciyar hankali duk akan sanadin abubuwan da kika yiwa yaya Abba ne Allah ya jarabceni haka nima abubuwan da nayi masu ne Allah ya nuna min kuskure na tun anan duniya ko makiyina bana son yayi irin rayuwar da nayi a gidan aurena watanni uku da yawuce,ga yar uwata nan Siyama ita ta nutsar dani ta nuna min illolin abubuwan da na dinga aikatawa a baya. Saboda Allah yana sona da rahama, nan take na tuba na nemi gafara wurin Ubangiji,hatta da Aydah sai da na sameta na nemi gafarta har yanzu kin san cewa Mami,bana bacci cikin farin ciki a kullum tunanina yaya Abba da Rumaisa da suka koma wurin mahalicci su ban nemi gafarar su ba a duk kwanan duniya girman laifin dana aikata masu yana hanani samun walwala. Ina addu'a ina yimasu sadaqa Allah ya kai haske kabarinsu. Mami ki nemi Daddy afuwa duk irin laifukkan da kika yi masa a baya. Na san zai yafe maki Mami,kawai muna son ki tuba ki komawa Allah. Sadiya ta karashe maganar cikin rawar murya kasa daurewa tayi saboda wani irin kuka da ya zo mata batare da ta shiryawa zuwansa ba, da gudu tabar ɗakin kuka na fitar hankali na fitowa tun daga karkashin zuciyarta. Haka Siyama ta tashi ta tabi bayanta ita ma da nata hawayen dake son zubowa. Suka bar Mami zaune a ɗaki tamkar an dasata hawayen idonta sun kasa tsayawa,tana jin girman laifukkan data aikata suna wani irin danneta ,bata san kuma tana ina za ta fara ba. Washe gari karfe tara huwayila ta kwankwasa kofar falo sabuwar mai aikinsu ce mai suna Hanne ita ta zo ta buɗe mata ganin Huwaila zata girmeta yasa ta gaisheta Huwaila ta amsa tana fadar wurin Aydah ta zo ko ta tashi bacci?"Dan ita kanta Huwaila tsoron shiga cikin falon take tana gudun haɗuwa da Mami,dan bata san irin tarbar da za ta yi mata ba. "Ki zauna bara na kira miki ita. Hanne ta faɗa tana katsewa Huwaila tunanin da ta tafi lokaci ɗaya,kan rug Huwaila ta zauna. Hanne ta je ta kwankwasa kofar ɗakin Aydah,Aydah ta yi mata izinin shiga ta shiga baby Noor ce goye a bayan Aydah dukansu sun yi wanka gwanin ban sha'awa zaka rantse Aydah ce ta haifeta a lokacin saboda ita ma Aydah jikinta ya buɗe ta cika komai na girma ya gama bayyana a jikinta "Hanne ya aka yi ne kin gama jera komai ne akan dinning ɗin?"Aydah ta faɗa tana kallon Hanne, Dan tare suka shirya breakfast ita da Hanne ganin yau Mami bata sauko kasa ba tunda ta yi sallar asuba bata koma bacci ba. Tun bayan rasuwar AB da ta dawo gida ta zage ta koyi girki kala-kala a wurin Rumaisa da Mami har wani catering school ta shiga,idan taje gidansu Rumaisa haka zata mannewa Ammi suyi girki tare saboda Ammi ta kware a fannin girke-girken gargajiya,yanzu duk wannan sakarcin na son jikin Aydah tabarsa ta yi hankali tare da wata irin natsuwa ta ban mamaki. Yawan aikin da take yi har ya daina bai wa Mami,mamaki ita ke gyara ɗakinta batareda ta nemi taimakon yar aiki ba. "kin yi bakuwa tana kasa tana jiranki. Hanne ta faɗa tana kallon Aydah, ɗan jim Aydah ta yi tana juya maganar Hanne aranta tana mamakin bakuwa? Kafin tunaninta ya tsaya akan Daddy,yace Aunty Huwaila ta zo,cike da murna Aydah ta kalli Hanne tana faɗin."ki ce mata ina zuwa da haka Aydah ta ɗauki ƙaramin hijab ɗinta ta saka saboda kar sanyi ya yi wa Baby Noor yawa Ta sauka downstairs gabanta na faduwa wannan karon bata san kalar tarbar da mami,zata yi wa Aunty Huwaila ba idan kuma taki amincewa da ita fa?" Wata zuciyar Aydah ta bata amsa sai ta ji jikinta ya yi sanyi lokaci ɗaya,har ta karasa cikin parlor ta ware ido da murna ta nufi Huwaila tana gaisheta ita ma Huwaila da murna ta amsa tana ƙoƙarin duba Baby Noor. "Ai bacci take yi Aunty Huwaila na samu nayi mata wanka. Fitowar Mami,ya katse musu zance kowacce ta shiga hankalinta cikin rawar murya Huwaila ta gaisheda Mami,Mami ta amsa adakile. "Daman Mami Daddy ne yace yau Aunty Huwaila ta samesa kafin ya fita office. Sai da zuciyar Mami ta ɗan buga da ta ji Daddy ne yake neman Huwaila to tayi masa me?"nan take Mami ta shiga tashin hankali tunani na farko da yazo mata ko dai Daddy Huwaila zai aura dan ya rama abubuwan da ta yi masa abaya Girgiza kai Mami ta yi a ranta take faɗin "ai ba zai ma yiyuwa ba. "Ki zauna bari nayi masa magana. Mami ta fadawa Huwaila da rashin walwala a fuskarta kai tsaye bangaren Daddy ta nufa ta samesa har yayi wanka mami ta zauna ta gaishesa cikin sanyi murya ya amsa batareda ya kalli bangaren da take ba. Sa taji jikinta yayi bala'in sanyi saukowa tayi akan kujera ta haɗe hannunta wuri ɗaya cikin wani irin murya take faɗin."Dan Allah dan Annabi Daddy ,ka yafemun duk irin laifukkan da nayi maka a baya wallahi-tallahi sharrin zuciya ne da sharrin shaitan kai ma kasan ban taɓa ƙin Abba ba ni kaina bai san meya shiga kaina ba sai dai na danganta hakan da yadda abubuwa suka dinga yi min zuwan bazata. Na yi nadamar waya'nnan abubuwa na aikata sosai wallahi dan Allah ka yafe min Alhaji. Mami ta faɗa hawayen idonta na gudu akan fuskarta. "Ni bani kika cuta ba Mariya wanda kika zalunta ya riga da yabar duniyar kawai ki je ki cigaba da addu'a da istgifari ko zaki ga daidai a Rayuwarki. ɗan sanyi Mami,taji aranta,kafin ta daura da faɗin "Huwaila na falo tana jiranka,ban san kuma meyasa kake nemanta ba,nasan nayi maka laifi Alhaji karka haɗani kishi da Huwaila zuciyata za ta iya bugawa! Nasan halinku ku maza da zarar macce tayi maku laifi za ku nemi ku karo aure. Dan Allah karka yimin haka. Wani murmushi Daddy,ya saki miyesa tun farko tunanin kara aure bai zo masa ba dan ya hukunta Mami sai yanzu data an karar dashi?wani kallo Daddy ya rika aikawa Mami ta saitin ta kafin yace "Idan ma na aureta ina ganin hakan ba haramun bane mariya?" Da shock Mami ke faɗin."Huwaila fa zata zo sa'ar Sadiya me za kayi da yarinyar daka haifa kuma wadda ta gama sanin sirrin gidan ka 'yarka aikinka wannan ba daidai bane Alhaji. Mami ,ta faɗa a rude Daddy ya mike ya nufi kofar fita batareda ya kula Mami,ba ita ma a gigice tabisa zuciyarta banda rawa babu abunda take duk ranar da Daddy ya yi mata kishiya ita kam za ta iya mutuwa kishiyar ma kamar Huwaila. Har kasa Huwaila ta zube tana gaisheda daddy, Banda uwar harara babu abunda Mami ke aikawa a saitin da Huwaila take."Huwaila yarinya nakeso ki samowa Aydah mai hankali wacce zata tayata rainon Baby Noor. Da sauri Aydah ta kalli Daddy a shagwabe tana faɗin."Daddy nazata Aunty Huwaila fa za kace ta tayani raino ita kaɗai na yadda da ita idan aka dauko muguwa fa ta yi ta cin zalin Baby Noor. Aydah ta karasa maganar tamkar za ta yi kuka , murmushi Daddy ya yi yana faɗin."ai mai hankali zata samo wacce tasan halinta. Ita ma Huwaila ta dauka Daddy zai ce ita. murmushi Huwaila ta kirkira tana faɗin "in sha Allah za'a samu Daddy akwai wata yarinyar makotanmu sunanta Bintalo zasu zo sa'annin juna da Aydah idan na koma za yiwa Babarta magana idan sun amince shi kenan gobe na kawo ta. Huwaila ta faɗa da respect a muryarta, murmushi kurum Daddy keyi yana kallon yadda Mami,ta ɗan saki ranta ganin ba Huwaila ce zata taya Aydah rainon Baby Noor ba. Daddy ya kirga kuɗi dubu goma ya bai wa Huwaila ta yi na mota,sai godiya take masa. Bayan tafiyar Huwaila suna karin kumallo Aydah ta dubi mahaifinta tana faɗin."Daddy miyesa?"sai wata banccin ga Aunty Huwaila ni nafi sabawa da ita na kuma fi yadda da ita. A mugun fusace Mami,ke faɗin."to ba za'a dauketa ba ɗin idan an kawo maki wata ki korata Huwaila kanwar uwarki ce kota ubanki.? Mami,ta faɗa tamkar zata rufe Aydah da duka,ga baki ɗaya ta ji ta tsani Huwaila. Da haka Aydah ta koma daki tana hawaye ta kira Siyama,tana faɗa mata yadda Daddy ya ce, hakuri Siyama ta bata tana faɗin."ta yi wa Daddy uzuri maybe yana da dalilin sa, da haka Aydah ta haƙura,kwana biyu tsakani Daddy yana ta shawara a zuciyarsa ba wai yana jin son Huwaila bane sai dai aurenta shi zai sa ya zama izina ga Mami,har ga sauran mata masu irin halinta dan ya cigaba da zama da Mami haka bai hukunta taba yabarwa sauran mata kofofin da zasu rika yin yadda suke so a gidan mazajensu har su cigaba da shirka saboda son zuciya. ba'a yi sati ba Huwaila ta kawo Bintalo haka ta fadawa Aydah tana da hankali sosai ta kwantar ta hankalinta,nan ma Daddy wasu dubu goma ya bata yace ta yi na mota.Ya kasance ranar assabr kusan sati ɗaya da zuwan Bintalo gidan, Daddy ya kira Siyama da Sadiya a waya yace su haɗu a office ɗinsa da misalin karfe goma na safe akwai maganar da zasu tattauna. Haka ma Aydah kuma ya gargadeta karta sake ta fadawa Mami,da yake ranar tana da lecture zuwa 12 sai ta fita karfe goma bayan ta yiwa Baby Noor duk abubuwan da take mata dan ko wanka ita take yi mata iyakaci Bintalo ta yi mata wankin kaya tayi rainonta. Idan lokacin cin abincinta ya yi ta bata shikenan,da kuma Aydah ta dawo school zat a karbi abarta su shige ɗaki wani irin so take wa Baby Noor dukka soyayyar da take wa Ab ta tattaro ta, ta dawo da ita kan Baby Noor ko kuka ta yi yanzu Aydah za ta bi ta tashi hankalinta. Yadda Mami taga Aydah tana kula da tattalin Noor sai ta dinga tuna lokacin da Abba yake rainon Aydah haka yake mata tarihi dai yana neman ya maimaita kansa. Kai tsaye office ɗin mahaifinta ta nufa da motar da AB ya siyamata wanda driver ne ya koya mata motar saboda zuwa makaranta. Wurin ta samu tayi parking motarta, ta fito tana kallon motocin yan uwanta cike da mamaki ta ƙarasa office ɗin Daddy,ta gaisheda yayunta suka amsa Siyama tana tsokanarta da faɗin "Auta dai yanzu kin zama ustaziyyah wannan dogon hijab da kike sakawa har suna ja ga kasa kin dauka shi zai sa samari su daina kula ki muslim ƙanin Saleem yana nan yana min naci kin ki kulasa. Yar fara'ar dake cikin fuskar Aydah nan take ta ɓace batt a tabare ta kalli mahaifinsu dake kallonsu cike da farin ciki, Daddy a can kasan zuciyarsa yana jin kewar Abba. "Daddy kaga yaya Siyam ko?" Siyam ta buɗe ido tana faɗin "Daga faɗar gaskiya sai kai ƙarata lallai auta kina da abin mamaki. "Siyama ki daina tun da bataso. Daddy ya faɗa cike da kashedi daria Sadiya ta yi tana faɗin. "To wai Daddy haka za a zuba mata ido ta zauna bazata yi aure ba?" Fashewa da kuka Aydah ta yi babu kalmar da tafi tsana a duniya a furta mata irin kalmar aure. Ganin da gaske kuka take yi sai suka hau rarrashinta wannan karon har da Daddy, sai da suka tabbatar ta daina kukan ta natsu sa'annan Daddy,ya dubesu yana faɗin."Shawara nake so ku bani a matsayinku na 'ya'yana wani gefe kuma abokanina duk duniyar nan babu wanda ya kamata na nemi yaddarsa da shawararsa baya ga ku ɗinan kune kaɗa dole na. Duba da nayi yadda duniyar ta zama yanzu babu amana,ko ƙanƙani ku kaɗai na yarda daku nasan kowanne ku zai bani shawarar data dace kafin na yanke hukunci. Dukkansu natsuwa suka yi suna sauraren mahaifinsu."Har yanzu na kasa manta irin rashin kyautatawa da mahaifiyarku tayi min ita gani take yi bansan cewa ita silar shiga tsakanina da Abba tai min asirin da na kori Abba da kaina wannan abun da mahaifiyarku ba zan taɓa iya mantawa dashi cikin sauki ba. Duk sanda na tuna haka sai naji wani iri araina duk da na yafe mata har cikin zuciyata kawai dai na kasa mantawa ne. Kuma wani bangaren na zuciyata ina son na hukuntata cikin ruwan sanyi yadda zata kara yin nadamar haka zalika ya zama izina ga masu hali irin nata. Ga baki ɗaya sai suka yi shiru sun tattara hankalinsu akan bayanin da mahaifinsu keyi duk cikinsu babu wacce hankalinta bai tashi ba duk tunaninsu ya tsaya akan mahaifinsu zai rabu da mahaifiyarsu ne. Kamar daga sama suka ji Daddy,na faɗin."zan kara aure auren kuma bada kowa ba sai da Huwaila ita kaɗai ce nake ganin ya kamata na aura hankalina ya kwanta ganin mun yi kusan shekaru goma a tare da ita. A wani irin razane suka daga kai suna kallon mahaifin nasu da sauri Aydah ta shiga girgiza kai duk da mahaifiyarsu mai laifi ce wannan hukunci yayi mata tsauri da yawa. "Daddy miyasa sai Huwaila kana gani ba zai zama cin fuska a wurin Mami ba a matsayin Huwaila na 'yar aikinta? Daddy ka canja wata dan Allah banda ita. Kusan su duka suka furta suna haɗa baki da wani yanayi shimfide akan fuskokinsu. "Aure babu fashi nayi niyya kuma ba gudu ba jada baya ba, ai don naci mata fuska yasa nace aure mai aikin nata. To amman meyasa bakwa son Huwaila ba ku san halinta bane ko yaya ko kun fiso naje na dauko wacce ke shirka wacce bata yarda da ƙaddara ba irin mahaifiyarku? Dukkansu shiru suka yi Daddy ya cigaba da faɗin "dukkan ku kun fini sanin halin Huwaila da tana da wani mugun hali da ko kaɗan ba zan yi wa kaina sha'awar aurenta ba don haka na shirya tsaf sai na hada mahaifiyarku kishi da wannan dai 'yar aikin nata Huwaila. "Allah yasa haka shi yafi zama alkhairi Daddy,ina goyon bayanka dari bisa dari. Sadiya ta faɗa tana jin wani iri a zuciyarta har ga Allah tana taya mahaifiyarta kishi, Siyama ma ta yi wa Daddy fatan alkhairi kafin Aydah ita ma tayi nata duka jikinsu a sanyayyen, nasiha sosai Daddy ya yi masu akan jin tsoron Allah kafin su yi masa sallama su fita. Aydah ce ta fara tafiya kafin Siyama ta kalli Sadiya tana faɗin "tsoron Allah ya ƙara shigata yaya Sadiya ni Babu wanda nake ji irin Mami. Allah yasa hakan ya canjata gabaki ɗaya. Sadiya ta faɗa duk jikinta a mace kafin kowace ta shige motar ta ta wuce. Tun daga nesa Marwan Garkuwa ya hangota sai dai yanayin dake shimfide akan fuskarta yayi bala'in tsinka masa zuciya yau ko baccin kirki bai samu ya yi ba saboda kawai dan ya ganta ya shigo makarantar kafin su fara lecture rabon shi da ita tun shekaran jiya. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO [2/8, 2:43 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love story #Gwagwarmaya #Team tagwaye Novels 100. Ganin yadda ya tunkarota gadan-gadan yasa lokaci ɗaya Aydah ta haɗe rai tana ƙoƙarin canja wata hanyar sai dai ta makara jin ta yi an rike hannunta sosai an nufi inda tayi parking motarta,kallonsa ta yi cike da ƙarfin hali waye ya basa ikon ya rike mata hannu har haka?" Ta lura Marwan Garkuwa bashi da hankali a yan kwanakin nan yana takura mata yana mata naci akan abun da yasan ba zai taɓa faruwa ba a tsakaninsu ko a mafarki Barantana a gaske,har ta kai ta kawo tana tsoron ta shigo makaranta taci karo da fuskarsa ,duk inda ta shiga idonsa na kafe akanta. Ta gaji ta gaji da wannan nacin nasa,lokaci ɗaya ta fisge hannunta cikin nasa cikin tsiwa da ɓacin rai take faɗin."meke damunka ne? wai meyasa duk inda na shiga sai ka bini?"kai babu zuciya ne dashe a kirjinka ne wai? Ta ƙarasa maganar cike da wani yanayi a muryarta harɗe hannu ya yi a ƙirjinsa yana kallonta. Sai kace babu wani abu da zai gabatar a rayuwarsa baya ga kallon nata,girarsa ta sama ya tattare ya haɗe wuri ɗaya. "Buɗe motar da hannunki ki shiga magana za mu yi. baki buɗe take kallonsa "Saboda ga ka ubana. Ta faɗa so pissed up a muryarta. "karki yi trying ɗina da safen nan ko break fast ban tsaya nayi ba na fito dan kawai na zo na ganki shi ne kike so ki ɓatamin rai shiga nace. Ya ƙarasa magana da ɗaga murya yana wani haɗe girar sama da ƙasa. Dariyar rainin hankali ta fashe dashi wallahi abubuwan Marwan Garkuwa dariya suke bata mutum sai shegen manyyance tasan shekarun Marwan ɗin ba za su wuce 20 years ba tsawon kafa kawai ne ke jansa da girman jiki yana bata umarni sai kace ubanta. "Idan naki ɗin me za kayi?" hannun rigarsa ya shiga tattarewa lokaci ɗaya ya fisge car key ɗin dake hannunta ya danna motar ta buɗe ganin ya nufota gadan-gadan da gaske daukarta zai yi yasa ta nufi motar cikin tsiwa take faɗin "me kake shirin yi haka?"Marwan wai kai sai kace wani mai shekaru kayi ta abubuwa irin na manya yaro da kai. Ta faɗa tana buɗe bangaren driver ta zauna fuskarta a murtuƙe,shiga ya yi ya zauna frontseat yana rufe ƙofar hannu yasa ya dannawa kowace ƙofa lock,kallonsa kawai take. "kara maimaita abun da kika ce a waje? Wani kalar zaro ido tayi ganin yadda yake kokarin haɗe fuskarsa da tata har tana jin saukar numfashinsa saman fuskarta wani irin bugawa zuciyarta ta shiga yi da sauri ta matsa ɗan murmushi ya saki ya riko hannunta duk yadda take kokarin kwacewa ya kasa sake mata hannu Da wata irin murya yake faɗin."fadamun shekaruna basu kai nayi aure ba da kike rainamin shekaru?"wannan karon cikin ido take kallonsa ta fincike hannunta da karfi cikin nasa "ka daina tabani bana so. Da gaske kai ɗin yaro ne dan ba zan iya aurenka ba ka min kankanta. maganarta ya ji tana bata masa rai rigarsa yake kokarin cirewa a gabanta wani irin ihu ta sakar masa tana wani rufe idanunta babu inda jikinta baya rawa. "ki buɗe ido ki kalleni ki ga jikina idan akwai yarinta acikinsa. "Wallahi Marwan zan maka ihu ka buɗe min mota na fita wai meyasa kake min haka ne"?rigarsa ya mayar yana kallonta da wani yanayi acikin idanunsa yake faɗin."ki bani dama naje gidanku na gabatar da kaina a wajen iyayenki,ko yanzu suke so ayi miki aure iyayena basu da matsala ,daga nan idan aka yi auren zan baki ciki na tabbatar maki dani ba yaro bane. "Wallahi ka daina wannan mafarkin ba zan taɓa auren yaro kamar ka ba. "wai an faɗa maka bani da aure ne balle ka dame ni da zance aure? Wallahi ka fita sabgata ko na haɗaka da mijina Marwan. Wani murmushi mai ciwo ya yi yana faɗin "nasan mijinki ya rasu ki daina yimin karya magana na karshe komai zai faru baz an iya rabuwa dake ba zyulaiha ki rubuta haka ki aje,kuma ki cigaba da kirana yaro watarana sai kin fusatani nayi maki abun da baki taba tunani ba wanda mu dukanmu ba za mu ji daɗinsa ba ki kiyaye karki kure hankurina. "To ubana budemin kofa naji. Ta faɗa cike da tsiwa tana tura masa bakinta Murmushi ya yi yana shafa sumar kansa,kusan tare suka fito motar ya danna key motar ta rufe ya karbi handbag ɗinta ya saka mata key ɗin "Mu je ki rakani nayi break fast ko cikin cafteria ne babu komai acikina. Duk kin bin kin hargitsa min lissafi. Sanin halinsa na naci yasa tayi gaba yana bin ta a baya duk yadda zata yiwa Marwan Garkuwa wulaƙanci ba zai daina nace mata ba. Haka yake ko cikin class suke suna daukar lecture baya son yaga wani namiji ya zauna kusa da ita,abu ɗaya take so a tare dashi ƙoƙarinsa yana da wani irin ƙoƙari na ban mamaki dan shi ne class rep ɗin ajinsu.Yammatan class ɗinsu kuwa kowace so take Marwan Garkuwa ya kulata wanda ita haka baya gabanta tasan dai ba zata taɓa son Marwan ba,namiji ɗaya ke da wannan matsayi a zuciyarta matsayinsa ba zai taɓa canja ba har tsayawar numfashinta. Yinin ranar duk inda ta sauke kafa anan Marwan ke sauke tasa har ta gaji da yimasa magana ta zuba masa ido. Bayan ta koma gida da dare kawai tayi tunanin turawa Daddy,lambar Aunty Huwaila. Sai dai acan kasan ranta tana son ganin mahaifinta cikin farin ciki, sai dai bata san ya Mami za ta ɗauki al'amarin ba. Kusan sati ɗaya da maganar Huwaila da Daddy,kuma tun ranar Daddy yaga Aydah ta tura masa lambar sai dai bai dauka ba barantana ya kira, yau yana office wuraren karfe biyu ya kira Aydah ita ma fitowarta kenan daga lecture,yace idan ta gama lecture ta samesa a office kai tsaye can ta nufa idanunta har rufewa suke saboda yunwar da take ji, kallo ɗaya Daddy ya yi mata yasan yunwa take ji masinjansa ya akai yayo mata take away anan cikin office ɗin Daddy ta shiga cin abinci kamar Allah ya aikota, sai bayan da ta natsu Daddy ya kalleta yana faɗin "wurin Auntynki zamu je tun da har yanzu kin yi shiru kinki gabatar mata dani,baki buɗe Aydah ke kallon Daddy,kafin tace "na fa tura maka lambar tun ranar Daddy kuma naga ka buɗe ba kace komai ba. "Idan na kirata nace mata me?"mu dai je kiyi mata bayani kafin nawa ya biyo baya. Idan ta yarda zata auri tsoho kamata shikenan idan kuma bata yarda ba ba zan mata dole ba, dariya Aydah ta fashe dashi tana faɗin "Daddy ba ka fa tsufa ba infact kana da kuɗi kuma tsoho da kuɗi yaro ne. murmushi kurum Daddy,ya yi acikin motar Aydah suka nufi gidansu Huwaila Ita dai Huwaila tamkar a mafarki take sauraren Aydah jin wani zance da take kamar almara,da sauri Huwaila ta shiga girgiza kai tana faɗin."wannan cin fuskar ya yi yawa Auta ba zan iya ba bakya tunanin irin abun da zai biyo baya daga wurin Mami. Ni dai tsoro nake ji wallahi. "tsoron me za ki ji Aunty Huwaila Daddy ne fa Daddyna kin san halinsa fa kuma da kike tunanin Mami,Mami bata da matsala ta canja wallahi. Haka Aydah ta yi ta fama da huwaila har ta amince,dakyar tace ta je taga Daddy yana zauren gidansu yana jiranta ita zata zauna anan ta jira har su gama Wani irin nauyin Daddy Huwaila ta rika ji bayan ta fita ta samesa komai ganinsa take tamkar a mafarki haka Daddy,yace kar ta damu ba zai takura mata ba ya bata sati ɗaya ta je tayi shawara idan ta amince zai turo da magabatansa da haka suka rabu. Cikin sati biyu Huwaila ta sake da daddy har ya tura da magabatansa an tsayar da magana baya son bikin ya dauki lokaci aka saka sati biyu za'a daura aure sati biyu daga baya sai ta tare,Daddy Sadiya ya turawa kudi ta account ɗinta akan ta haɗa lefen Huwaila haka ta kira Siyama,a waya suka saka rana suka shiga kasuwa suka rika haɗa kayan lefe suma sai da suka saka gudummuwarsu aciki dan lefe nagani na faɗa suka haɗa,haka Daddy ya shiga gyaran gida ya canja furnitures duka,Mami nata murna yanzu komai ya daidaita tsakaninta da Daddy,suna zaunawa suyi hira kuma yana sake mata fuska sosai. Ana sauran kwana huɗu a daurawa Daddy,aure da Huwaila da dare Daddy ya yanke shawarar ya sanar da Mami ya kirata a waya kafin ta zo sai da ya tura mata miliyan biyu a account ɗinta ,da fara'a Mami ta shigo falon na Daddy dan tana riƙe da wayarta taga alert kuma daga wurin Daddy ta samu wuri ta zauna, "Daddy naga ka turamin saƙo yanzu Allah ya kara budi da daukaka. Mami ta faɗa sounding so happy, "Ameen ameen! Daddy ya faɗa kafin ya karkace kai ya fara yimata bayani duk cikin bayanan da yake mata daurin aurensa sauran kwana huɗu shi kaɗai ta fahimta. A gigice ta miqe tsaye hawaye suka wanke mata fuska "tozarcin da ka shirya yimin kenan Alhaji da shekaruna za ka yi min kishiya?"wallahi sai dai ka zaba koni ko ita ba zan zauna da kishiya ba watau shine ka hau gyaran gida kou?"namiji munafuki wallahi ba zan zauna da kishiya ba. Mami ta ƙarasa magana a fusace tana ficewa fuuuuuu tabar Daddy ,sake da baki Aydah na kwance a ɗakinta ta saka baby Noor a gaba tana yimata wasa taji an turo kofar ɗakinta da mamaki ta daga kai suka yi ido biyu da Mami, ganin yanayin Mami ya kayar mata da gaba da sauri ta sauko daga kan bed ta nufi Mami,tana tambayarta lafiya?"kuka Mami ta fashe dashi tana samun wurin zama anan gefen bed ɗin Aydah. A tsorace Aydah ke faɗin."Mami ki faɗamin wani ya mutu ne?" "Ba kara ace mun mutuwa aka yi ba da abun da Daddynku keso ya yi min ba so yake Ya kunyatani cikin kawayena da yan uwana da tsufan Daddynku zai ce zai kara aure. Shiru Aydah tayi aranta take faɗin "Daddy ya fasa kwan kenan. Cikin sanyin murya Aydah ke fadin"to Mami meye aciki dan Daddy ya kara aure kinga ba haramun bane? baki buɗe Mami ta juya tana kallon kalaman dake fitowa daga bakin Aydah."Banyi mamakin jin fitowar wa'yannan kalaman daga bakin ki ba. Daman can ba kaunata kike ba kinfi kaunar mahaifinki akaina munafuka muguwa marar tausayi waya sani koda ke kuka haɗa kai keda mahaifin naki aka munafuce ni. To wallahi babu shegiyar da ta isa ta shigo gidan nan a matsayin kishiyata. A fusace Mami tabarwa Aydah ɗakin,Mami na shiga ɗakinta ta saka key a kofarta ta dauki wayarta ta kira Sadiya. Sadiya na dauka Mami ta fashewa Sadiya da kuka. hankalin Sadiya a tashe ta shiga tambayar Mami meya faru."Mahaifinku yake so ya tozartani Sadiya,da yarintata ba ai min kishiya ba sai yanzu. Shiru Sadiya ta yi ta rasa me zata cewa Mami,sai ta fara rarrashin Mami, tana faɗin "gobe Mami zamu zo nida Siyama ,dan Allah ki kwantar da hankalinki komai zai zama daidai. Sadiya ta rika rarrashin Mami, da kalaman kwatar da hankali. Har ta samu ta haƙura tace ba za ta je ko'ina ba. Washe gari Mami ko kallon Daddy ba tayi ba barantana ta kawo masa break fast Aydah ce ta shiga kitchen ta yiwa Daddyn komai. Banda harararta babu abunda Mami keyi. Daddy,yana gama break fast ya wuce office ita ma Aydah karfe 10 ta fita school har daki ta sami Mami,tace mata ta tafi school banza Mami tayi mata haka ta gama tsayuwarta ta wuce makaranta bata dade da tafiya ba sai ga Sadiya da Siyama banda faduwa babu abunda gabansu keyi basu san ya mami zata dauki zancen ba,cike da karfin hali Sadiya ta shiga yiwa Mami,bayani tun neman shawarar da Daddy yayi a wurinsu haka Siyama,ta ɗora da nata with shock Mami ke kallon ya'yan nata watau da ya'yanta na cikinta aka haɗa baki akaci amanarta, batareda Mami tace komai ba ta mike tsaye ta nufi toilet da ido suka bi ta,har kusan minti goma ba su ji Mami ta fito ba Siyama ta ƙarasa kofar toilet tayi knocking tana kiran sunan Mami,muryar Mami ta ji tana faɗin "kafin na fito dake da Sadiya ku barmin gidana na kar na fito na yi maku baki. kalaman Mami ba ƙaramin razanasu ya yi ba ko minti biyu basu kara ba suka bar gidan, Siyama ta kira Daddy a waya tana kuka tana faɗin "ko Daddy za ka fasa auren nan Mami bata dauki al'amarin nan da sauqi ba? "ki kwantar da hankalin ki Siyama, ni ba ƙaramin mutum bane aure babu fashi idan taga an daura dole za ta hakura. Da haka Daddy ,ya kashe wayar batareda ya tsaya jin me Sadiya za ta faɗa ba. Ranar juma'a da misalin ƙarfe biyu na rana bayan an tashi masallaci dubban mutane suka shaida daurin auren Alh Bashir da Huwaila akan sadaki Naira dubu dari. #JEEDDAH ALIYU #ASMY B ALIYU #KURMAN ALLO [2/9, 7:41 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 101. *LAGOS NIGERIA* Duk tsawon kwanaki da Aliyu na Uku ya dauka da dawowa Lagos, Anaal bata dawo ba kuma wayarta a kashe wannan al'amari ya daga masa hankali matuka har ya fara tunani ko masu garkuwa da mutane ne suka yi masa awon gaba da 'ya, to idan sune miyasa har yanzu basu kira sa sun faɗi kuɗin fansa ba?" A halin yanzu ya yanke shawarar zai tafi Kano ya je police headquarter dake Kano ɗin ya kai report jirgin karfe biyu zai bi zuwa Kano ɗin. Sai gashi yau yana zaune a ofishin sa kiran ya shigo wayarsa na mutumin da ya ba wa aiki ya binciko masa Bashir shamaki, da farko ya yi bincike aka ce yana Katsina koda suka je Katsina ba shi bane sunan ne kawai ya zo ɗaya. Cikin sanyi jikin Aliyu ya yi picking, wani kalar miƙewa tsaye Aliyu ya yi "Ka tabbata Kabir Umar kada ka yi min irin na wancan lokaci kasa min hope sai da na je naga ba haka bane? "To shikenan daman yau zan je Kano sai mun haɗu. Agaggauce Aliyu ya baro kamfani ya wuce gidansa wanda yanzu, Maysun ce ke zaune a ciki a main parlor ya tarar da ita zaune akan two seater ta rafka tagumi ga baki ɗaya ta rame ta zage, burinta taga ɗanta ba karamin so take yi wa Azhar shi ne rayuwarta. Rashin samun takamaiman inda Bashir shamaki da Maryama suke ya yi bala'in daga mata hankali, kullum da sabuwar karya da Aliyu zai zo mata da ita duk kokari da yake yi bata gani, sai ma ta danganta hakan da karya. Dauke mata tagumin da ya yi tare da zaunawa gefenta ya ɗan rungumo kafaɗarta "Ki yi haƙuri my love in shaa Allahu komai ya kusan zuwa ƙarshe yanzu nan na sami kira mai muhimmanci Bashir shamaki yana zaune a garin kano hatta da address ɗin gidansa Kabir Umar ya turomin, ki kwantar da hankalinki in shaa Allahu za a ga Azhar ɗinki cikin ƙoshin lafiya. A maimakon Maysun ta yi farin ciki da jin kalamansa sai ta fusata ta ɗago kodaddin idanuwanta, ta dube shi dasu "Ka ga Ali ka barni na ji damuwar da kai ɗinan kaine silar jefa ni acikinta. Kullum cikin bani fake hope kake idan har ka salwantar min da ɗa dan Allah ka fito fili ka faɗa min gaskiya, na tattara na koma Qatar da ka dinga bani karya cewa za a gansa, ina saka raina akan hakan gwara nasan gaskiya nayi kokari fitar dashi daga raina. Tun sanda Maysun ta fara magana Aliyu na Uku ya yi mutuwar zaune yana kallonta, babban abin da yafi bashi haushi da takaici bai wuce cewa da ta yi idan ya salwantar mata da ɗa. Me take nufi da wannan kurman allon nata ko tana nufi shi da kansa zai ɓatar da ɗansa na cikinsa. Miyasa a koda yaushe Maysun bata masa uzuri kamar yadda Safiya take masa. Kodai Maysun ta daina sonsa ne shi kaɗai ke wahalar banza akanta? Ransa ya yi mugun ɓaci ya miƙe tsaye tare da jefa idanunsa cikin nata, cikin fusata ya ce "Duk kokari da nake yi bakya gani Maysun karka fa ki manta kace sanadin shiga ta dimbin matsaloli da har kawo yanzu na kasa warware su, idanuwanki sun rufe kin kasa fahimtar irin halin da naki ciki kanki kawai kika sani idan kina magana dangane da ɓatan ɗanki mai shekara ɗaya, ni kuma yata mai shekaru ashirin da biyar a duniya na nema na rasa yau kwananta takwas bansan inda take ba. Saboda haka ba zan bari akan wani self-interest dinki ki ƙara haifar min da wata damuwa don haka ki tattara ki koma Qatar na yi miki alƙawari zan cigaba da neman ɗanki har izuwa ƙarshen numfashina, idan da rabo na gansa a raye zan kai miki shi har Qatar na damki miki shi a hannunki. Wani irin zaro idanuwa Maysun ta yi cikin kaɗuwa take kallonsa lallai Ali ya canza mutumin da yake lallaɓata da rirrita ta, tamkar kwai akan spoon wai yau shi ne yake mata magana da kakkausar murya mutumin da a shekarun baya, ko wani ya daga mata murya sai inda ƙarfinsa ya ƙare yau shi ne tsaye a gabanta yana faɗa mata maganganu marasa daɗi har yana iƙrarin ta tafi kasar su. Wani irin kuka mai cin rai ta fashe dashi kallonta ya yi tare da girgiza kansa ya juya rai ɓace ya haura sama ɗakinsa ya shiga ya canza kaya zuwa farar shadda dimkin babbar riga, jikinsa na fidda ƙamshin turarensa har ya dawo cikin parlorn Maysun na rera kuka gabanta ya tsaya still fuskarsa a haɗe ya ce "Ni zan wuce Kano jirgin karfe biyu zan bi idan za ki cigaba da zama dani ƙofa a buɗe take idan kuma Qatar ɗin za ki koma ina miki fatan sauka lafiya. Ya karashe magana tare da juyawa zuciyarsa tana masa tuƙuƙi, da sauri Maysun ta taso ta rungumesa ta baya tare da zagaye hannayenta a cikinsa ta ɗora kanta a gadon bayansa "Ka yi haƙuri Ali na kasa riƙe kaina ne gani nake yi kowanne lokaci zan iya tafiya batareda da idanuwana sun yi tozali da Muhammad Azhar ba. Ta ƙarasa magana tana wani irin kuka mai taɓa zuciya da sauri ya juyo ya ƙanƙame ta yana bubbuga bayanta "ko tafiya kika yi Maysun na yi miki alƙawari zan kai miki shi har Qatar. "Ba za ka gane bane Ali kai dai ka yi kokari na gansa banaso na mutu batare da na ga tilo dana ba. Wani irin bugawa zuciyar Aliyu na Uku ta yi jikinsa ya ɗauki rawa, da sauri ya ɗago fuskarta yana kallon tsakiyar idanunta "me kike so ki ce Maysun?" Wani murmushi mai ciwo ta sakar masa "I've terminal blood cancer kowanne lokaci zan iya mutuwa Ali banida lokaci mai tsawo Dan Allah ka taimake ni ka haɗa ni da dana kamin na mutu ina so na gansa wannan shi ne kadai burina a duniya. "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Hasbunallahu wal-imaal wakil! Aliyu na uku ya faɗa tare da sakin kafanɗun Maysun da yake riƙe dasu ya dinga ja da baya wani irin jiri ne ya ɗebe shi ya faɗi zaune dabass! Ji ya yi numfashinsa na ƙoƙarin fita daga gangar jikinsa take ƙwaƙwalwarsa ta dinga tunano masa da kalolin magunguna da koda yaushe yake gani Maysun tana sha, idan ya tambaye ta sai ta ce mishi na blood pressure ne bai damu sosai ba saboda yasan hawan jini ya zama gama garin ciwo tun da ko Safiya tana dashi haka zalika mai babban ɗaki, ko kaɗan bai taɓa kawowa ransa cewa tana ɗauki da gaggarumar cuta irin wannan ba. A hankali Maysun ta zo ta zauna kusa dashi cikin muryarta da baya fita sosai ta ce "Ka yafe min boya maka da nayi Ali banaso ka shiga damuwa ne lokacin da muka haɗu a hamburg, na je gani likita ne anan yake tabbatar min da ciwon ya gama zagaye jinin jikina ba zan wuce three to four months a raye ba. Banaso na faɗa maka na dantse maka farin ciki da ka ɗauki shekaru masu yawa ba ka yi ba. Cikin wani yanayi ya rungumo ta wasu hawaye masu zafin gaske ya ji suna sauka akan kamatunsa, ya ɗauki lokaci mai tsawo rungume da Maysun kamin ya kamata ya nufi kujera da ita ya zaunar da ita ji ya yi ba zai iya tafiya ya barta ba yana gani kamin ya dawo wani abu ya faru da ita dole sai fasa tafiya ya yi saboda ya nema mata ticket ta online bai samu ba sai a washegari suka nufo Kano. ******** Mami hauka ne kaɗai bata yi ba da ta ji ɗaurin auren Daddy ya tabbata, gaba ɗaya yaranta daina amsa musu gaisuwa ta yi dukkansu fushi take dasu yayin da Zeenah ke ta faman zugata tare da yi mata hudubar shaitan tana faɗin Daddy ya zubar mata da mutunci ya rasa wacce zai aura sai 'yar aikinta karta sake ta yarda da wannan wulaƙancin nasa, a takaice babu kalar zuga da bata yi mata ba. Da yake kai nan na Mami sai a hankali sai ta hau ta zauna daram. *SKYLINE UNIVERSITY* Aydah suna kammala lecture ta fito daga hall da saurinta da nufi ta ɓacewa Marwan, ta gaji da nacin da yake mata ya bi ya takura ta ya hana mata rawar gaban hantsi. Duk saurin da take yi batasan cewa yana bayanta ba sai murmushi yake abinsa domin yasa, shi take so ta gujewa "Zulaiha wai sauri me kike yi haka?" Da sauri Aydah ta waiga bayanta fuskarta ta dawo kalar tausayi saboda duk abin da take wa gudu bata tsira ba, karasowa Marwan ya yi yana wani miskilalan murmushi "Mu je yau ƙafana ƙafarki ko bakyso dole sai kin gabatar dani ga yan gidanku shiyasa ma ban zo da motor na ba. Zaro idanuwa ta yi tare da faɗin "Wallahi Marwan kana da matsala wannan takurawa da kake min ba shi zai sa ka sami gurbi acikin zuciyata ba. "Kin ga malama ki wuce mu tafi dan ni na yi nisa ko kaɗan bana jin kira. Harara ta watsa masa haɗe da yi ƙwafa ta juya ya bi ta a baya, bata da yanda za ta yi da rigimarsa dole ta lallaɓa shi su rabu lafiya. Anaal zaune a Gusto restaurant tana ci abinci da ta yi order, tun zuwanta Kano ta rufe wayarta saboda abun da ta zo gabatarwa asirance. Bayan ta kammala cin abincinta ta yi order wani as usual don duk sanda ta zo cin abinci a Gusto sai ta yi order wani a takeaway ta tafi dashi. Tana fitowa ta tari adaidaita ta faɗa masa inda zai kaita tafiya sosai suka yi kafin su iso wani plat house ɗan madaidaci dashi a bakin gate aka sauke ta, ta yi knocking mai gadi ya buɗe mata ƙofa ɗaya daga cikin ledar takeaway ɗin ta zo dashi, ta miƙa masa kana ta wuce entrance ɗin gidan a main parlor ta tarar da doctor Maheer yana amsa waya bayan ta yi sallama ta ƙaraso ta zauna kujerar dake facing ɗinsa, ya kammala wayar tare da zuba mata fararen idanunsa cikin sanyi muryarsa ya ce "Alhamdullah! Abubuwa sai tafiya suke yi cikin nasara ina tunani nan da ɗan wani lokaci za a samu abun da ake so. Sanyayye murmushi Anaal ta yi tare da faɗin "Ina fatan haka doctor ina kuma kara godiya da kokarinka bantaɓa haɗuwa da mutum mai kirki da tausayi irinka ba, ba zan taɓa mantawa da taimakon ka ba,ga abinci na zo ma dashi bansani ba ko kana jin yunwa. Ta ƙarashe magana tare da aje masa takeaway ɗin hannunta akan centre table. Jirgin na landing Aliyu ya kira Kabir Umar shi ya zo da mota ya ɗauke su da fari sai da suka fara neman masauki a hotel suka yi wanka suka ci abinci tare da yi sallah, Kabir Umar ya ɗauke su zuwa gidan Bashir shamaki. Babu kalar rigamar da Mami bata tsiro wa da Daddy dashi ba ita fa a son ranta gara Daddy ya sake ta da ta yi zaman kishi da Huwaila a ganinta zama da Huwaila zai taɓa mata ƙima gara ta bar masa gidansa kawai. Shi kuma Daddy bashi da burin sakinta ya fiso ya haɗa ta da Huwaila don ya kuntata mata, so yake ya gasa mata 'ya'ya gyaɗa a tafin hannunta wannan ita kadai ce hanyar da zai bi domin yasata ta gurbe abun da ta shuka. Aydah lallaɓa Marwan ta dinga yi da kyar ya barta ta nufo gida shi ma sai ta daukar masa alƙawari ta daina ignoring ɗinsa sannan fa ya barta ta tafi, Aydah tana isowa gida ta wuce ɗakinta ta yi wanka saboda gajiya da ta ɗebo ta saka gown na cotton material mai gajeren hannu, kana ta dawo main parlor, ta kira Bintalo ta kawo mata Baby Noor ta ce ta zubo mata abinci ta kawo mata ɗakinta. Bayan ta kammala cin abinci ta ɗora Baby Noor a cikinta tana mata wasa ita kuma tana dariya a duk sanda ta kalli Baby Noor sai ta ji kewar iyayenta ya lulluɓeta. Horn ɗin da ake ta faman yi ga Balmo maigadi ya ɗan zagaya banɗaki yau tun safe ya tashi da ciwon cikin sai gudawa yake yi, da sauri ya fito yana ɗaure mazargin wandonsa da gudu ya je ya buɗe gate baƙuwar mota ya gani don tsawon zamansa a gidan bai taɓa ganinta ta zo gidan ba, Kabir Umar ya nufi parking lot ya yi parking jikin Maysun sai wani irin rawa yake yi zuciyarta tana bugawa da ƙarfi. Suna fitowa daga mota Balmo maigadi yana ƙarasowa ya yi musu sannu da zuwa, kana Aliyu ya tambaye shi maigidan yana nan kuwa? Balmo ya amsa da baya nan amman matar gidan tana ciki. Aliyu na uku ya ce ya yi musu iso a wurinta ya faɗa mata baƙi ne daga nesa. Balmo jikinsa har rawa yake yi ya je ya isar da sako saboda abubuwan mamaki guda biyu da ya ci karo dasu, wannan balarabiya mata mai kama da Abba ga kuma wani dogon mutumin shi ma yana yanayi da Abba tsayin su kusa ɗaya, ga maganarsa sak irin ta Abba don wannan mutumin da ya gani da ace shekarun sa ɗaya da Abba da ya ce Abba ɗin ne ya dawo. Balmo ya danna door bell Hanne ta zo ta buɗe masa ya ce ta gayawa Mami ta yi bakin larabawa. Hanne ta nufi ɗakin Mami dake upstairs a kwance ta tarar da ita duniya ta yi mata juyin ɗan mangwaro, cikin kwanaki ƙalilan Mami ta zabge ta yi mummunan rama. Cikin girmamawa Hanne ta faɗa mata sakon Balmo cike da mamaki ta furta "baƙin larabawa? "Eh! Mami haka dai ya cemin. "Shi kenan ki ce ya shigo dasu gani nan zuwa. Hanne ta fice ta je ta gayawa Balmo sakon Mami kana ta koma kitchen shi kuma ya je ya gayawa musu, tun sanda suka shigo parlorn Maysun ta haɗe tafukan hannayenta tana mutsutsuka su, wani irin take ji a jikinta. Footsteps ɗin Mami da suka ji tana saukowa daga kan stairs ya saka su kallon upstairs ɗin, ga mamakin su ba Maryama suka gani ba wata baƙuwar fuska ce ta daban da sauri Maysun ta kalli Aliyu don har idanuwanta sun ciko da hawaye "Abu Azhar wannan ba Maryama bace matar Bashir shamaki kodai ba nan ne gidansa ba?" Maysun ta yi magana da rauni a muryarta. Hannunta Aliyu na Uku ya riƙo yana ɗan girgiza mata kai alamar ta kwantar da hankalinta, Mami tana sakkowa idanunta suka yi tozali da mutane da ke mata kama da Abba, wani Irin shock ta ji ya kamata ko bata tambaya ba waɗannan mutane suna da alaƙa mai ƙarfi da margayi Abba, don duk tsawon zamanta da Abba ko a hoto bata taɓa gani masu kama dashi irin wadannan mata da miji dake zaune a parlornta, cikin mutuwar jiki Mami ta ƙaraso tare da yi musu sallama, Aliyu na Uku ne ya yi ƙarfin hali amsa mata ta nemi wuri ta zauna tare da kikkiro murmushin dole ta yafa wa fuskarta Hanne ta shigo ɗauke da tray mai ɗauke da drinks da ruwa ta ajiye musu kana ta sake komawa kitchen. Mami ta dube su gabanta na faɗuwa ta ce "Sannunku da zuwa ku yi haƙuri ban waye ku ba idan babu damuwa zan iya sani daga ina kuke wa kuma kuke nema?" "Sunana Aliyu na Uku wannan matata ce sunanta Maysun mun zo neman Bashir shamaki da matarsa Maryama, sai dai kamar an ba mu wrong address. Murmushi Mami ta yi tare da faɗin "Ba a ba ku wrong address ba nan ne gidan Bashir shamaki sai dai Matarsa Maryama Allah ya yi mata rasuwa tsawon shekaru talatin kenan da rasuwarta. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. [2/9, 7:42 AM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye. 102. Sai da Aliyu na uku ya ja dogon numfashi tare da saukewa ya ce "Allah ya jiƙanta da rahama. "Amin! Mami ta faɗa cikin sanyi murya. "Maigida fa?" Cewar Aliyu yana jin gabansa na faduwa, don baisan kalar amsar da za ta fito daga bakin Mami ba. "Yana office bara na kirasa a waya na sanar dashi zuwanku. Gyada kai kurum Aliyu ya yi yana mai ƙara damƙe hannun Maysun acikin nasa. Mami ta miƙe tare da komawa ɗaki ta kira wayar Daddy, kira uku tai masa amma bai yi picking ba kuma yana gani kiran nata, kawai dai baya da ra'ayin ɗauka fitinarta ya ishe shi cigaba da kira Mami ta yi a fusace Daddy ya ɗaga yana faɗin "Wai ke miye matsalarki ne kin fara kaini bango fa? "Ka yi baƙi da dukkan alama suna da alaƙa ta jini da margayi Abba idan kaga dama za ka iya zuwa ka gansu. Abun da Mami ta faɗa kenan tana mai kashe wayarta,ta dawo parlor wurinsu ta zauna. Anaal ta miƙe tsaye tare da kallon Dr Maheer tana faɗin "Dr bara na shiga ciki na duba sa. Dr Maheer ya gyada kansa Anaal ta juya cikin salon tafiyar ta natsuwa wacce tana ɗaya daga cikin abubuwan dake jan hankali maza akanta, Dr Maheer ya bi ta da kallo yana ji soyayyarta tana ƙara huda sassan jikinsa sai dai har kawo yanzu ta ƙi karɓar tayin soyayyar tasa. Yanzu ma da ta nemi taimakon sa domin kula da mutumin da ta ce dashi ɗan uwanta ne da fari asibitin sa ya fara jinya daga baya ya dawo dashi ɗaya daga cikin gidanjensa domin ta ce masa bata so, asan mutumin yana raye saboda tsananin son da yake mata ne yasa shi biye mata ya yi mata abun da take so yake kuma cigaba da kula dashi. Dukka bai fi 30 minutes ba sai ga Daddy ya zo yana arba da Aliyu na Uku gabansa ya yi mummunan faɗuwa ƙafafuwansa suka ƙasa daukarsa anan ya zube guiwayoyinsa, yana sauke numfashi yayin da idanunsa suka fara canza colour, gani Aliyu na uku da ya yi yasa abubuwa da dama suna dawowa masa a ƙwaƙwalwa musamman mutuwar Abba, a yanzu baisan da wane ido zai kalle su ya gayamusu ɗansu ya mutu. Cikin sauri Aliyu na uku ya taso yana zuwa shima ya zube guiwayoyinsa gaban Daddy tare da kama kafanɗun Daddy "Ba...Ba Ba..shir...ina ɗana Muhammad Azhar nasan yana wurinka ko Bashir dan Allah karkace min baya tare da kai?" Aliyu na Uku ya faɗa cikin raunatacciya murya, wani marayan kuka ne ya subuce wa Daddy, ya ɗora hannunsa kan na Aliyu dake kan kafaɗarsa tun kafin Daddy ya yi magana Aliyu na Uku ya kidime yayin da Maysun ta miƙe tsaye, cikin kaɗuwa take kallonsu "Ka yi haƙuri Aliyu Allah ya yiwa Abba rasuwa watannin biyar da suka wuce, har yanzu ban daina kukan rashinsa ba. "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Abun da Aliyu ke ta faman nanatawa gani haka yasa, Maysun ta zo ta dafa kafaɗarsa cikin harshen turanci take tambayar Aliyu me ya faru, kukan da yake kokarin dannewa ne ya subuce masa a lokaci guda, cikin muryar kuka yake fadawa Maysun Azhar ya rasu jiri da take ji tun ɗazu ne ya zo ya kwashe ta, daman can ƙarfin hali take yi tare da sawa ranta son ganin ɗanta yanzu kuma da ta ji ya rasuwa sai ta kasa jurewa, wani irin duhu ya mamaye ganinta ta fadi ƙasa a some kusan a tare Aliyu, Daddy har ma da Mami suka yi kanta jini suka gani yana fita ta ƙofofin hancinta da sauri Aliyu ya ciccibe ta ya nufi ƙofar fita, Daddy da Mami suka bi su a baya kaitsaye, asibitin Softcare da su Daddy ke zuwa aka wuce da Maysun. Sannu a hankali Anaal take ƙare masa kallo gaba ɗaya an naɗe kansa da bandage, haka ma ƙafarsa ta hagu wacce ke nuni da kariya ce ya yi sai wasu sassan jikinsa dake ɗauke da tanbuna na warkewar ciwuka, hannunsa na dama manne da cannula ana ƙara masa drip. Ba don na'urar da ke nuni da bugun numfashin sa za ka zaci gawa ne. Tsawon watanni biyar kenan yana cikin coma, har yau ko ɗan ya tsansa bai taɓa motsawa ba. Gashi nan dai ya zama gawa kin ƙi shiga rami. Anaal ta ja kujerar dake facing fuskarsa ta zauna, a hankali ta ɗora tafin hannunta akan nasa, tana shafawa a hankali yayin da hawayen tausayinsa suka cicciko mata a idanuwa "Tun farkon ganina da kai jikina ya bani kai ɗin jinina ne saboda wasu abubuwa da nake ji a duk sanda idanuwana suka kalle ka, ban tabbatar da hakan ba sai da na fara bibbiyarka har na yi nasarar samun gashinka ta hanyar wurin wanda kake zuwa aski a wurinsa, bayan Dr Maheer ya yi gwaji akansa ya tabbatar min da kai ɗin ɗan Abbu ne. Na ji haushi matuƙa da faruwar hakan, domin ina gani kalar soyayya da Abbu yake maka, tun kafin ya ganka kishinka nake yi yayana ina jin tsoron idan ka shigo rayuwarmu za ka kwace min fada a wurin Abbuna, mahaifiyarka za ta kara mamaye zuciyar Abbu ummina za ta zama kara zama bora a dalilin wannan gurgun tunani nawa, sai na yanke shawarar na haddasa gaba a tsakaninka da mahaifinka da ba kasan da zamansa ba. A ranar da zan gabatar da plan b ɗina na kira ka da zimmar aiwatar da manufata, a maimakon na ji muryarka sai na ji wata baƙuwar murya tana cewa dani yau kwana uku kenan da yi mummunan hatsari, shi ma tsintar kai ya yi amman ya kai ka asibiti idan ina da alaƙa da kai na zo asibitin da ya kai, ka. Da farin nace banida alaka da kai sai kuma na yi wani tunani wanda hakan ne yasa na zo Kano, da na zo naga hali da kake ciki yayana sai na ji zuciyata ta karye duk wani haushinka da kishinka da nake ji na nemi shi na rasa dan haka dan Allah ka tashi yayana,idan har ba ka tashi ba, ba zan iya gabatarwa da Abbu kai a wannan halin ba. Mahaifiyarka ta zo bata da buri face ta yi tozali da kai, banaso dukkansu biyu su ganka cikin wannan hali, na tabbata zuciyoyin su ba zai iya dauka ba. Domin kai na dawo Kano na tare batareda da sanin iyayena ba na cigaba da kula da kai, na kuma kashe waya ta saboda bani da hujja da zan gabatar musu da ita da za su bar ni na zo kano na zauna. Shiyasa nake rokon da ka tashi Abba Bashir ka tashi yayana ka buɗe idanunka ka kira ni da sunan da ka saba kirana dashi me ma kake kira ni dashi? Uhm! Mss Anaal! Ka kira ni da suna nan yayanmu. Har wani sheɗewa Anaal take yi saboda kuka, da yaci ƙarfinta sai kawai ta kifa kanta a ƙirjinsa ta cigaba da kukanta. Kusan awannin biyu likitoci suka dauka kan Maysun kamin su samu ta farfaɗo, sai dai tun sanda ta farfaɗo ɗin take kira sunan Azhar allurar bacci aka sake yi mata, bacci mai nauyi ya ɗauke ta sai lokacin Daddy ya sami damar ba wa Aliyu labarin Ab, ya yi matuƙar farin ciki da ya ji Abban ɗin yabar tsatsonsa da za su gani su ji sanyi. *MASARAUTAR KUDU* Tuni masauratar ta dauki sabon zance sarautar sabon birnin kudu da Ciroma ya ba wa Galadima, wanda hakan ba ƙaramin ce-ce-kuce ya kawo ba, sai dai babu mai karfin gwiwar da zai iya tunkararsa da maganar sai dai su koma gefe suna ƙanana maganganu. Kilishi ta kammala kallon video da ɗaya daga cikin amintattun bayinta ya taɓa yi wa Ciroma da Galadima a gidan gona wanda suka tsara kashe sarki Mahmood na Uku, daman Kilishi ta adana wannan video ne domin zuwan irin wannan rana, sai gashi yau zai mata amfani tana kammala kallo tasaki shu'umin murmushi tare da yada ganinta akan fuskar jakadiya tana faɗin "Jakadiya lokaci ya yi da za ki fallasa wannan sirri na Ciroma da Galadima baki ɗayansu za su ƙare a maƙarma da zarar mu yi nasarar zuwansu can zan nemi wasu daga cikin amintattun bayina su je har can gidan kaso ɗin su kawar min da damuwata, domin mutuwar Ciroma shi ne kadai hanyar da rufafffen sirrina zai cigaba da zama a rufe, domin duk ranar da wani ko wata a masauratar nan yasan da cewa bani na haifi Ciroma ba, kashina ya bushe domin daga ni har ke da kika taimaka min a lokacin da na haihu 'yata bata zo da rai ba, cikin hukuncin ubangiji hidima Rahane ita ma a wannan daren kika sami labarin ita ma tana kan gwiwa (nakuda)bayan ta haihu sai jini ya buge ta, ta fita hayyancinta batare da tasan me ta haifa ba, wannan ne ya ba ki damar haɗa baki da mijinta hidimi Bawa ta hanya kwadaita masa dukiya mai tarin yawa da nuna masa da kika yi anan gaba dansa ne magajin masaurata, tsabar kwadayin hidimi Bawa yasa kamin hadima Rahane ta farfaɗo ya musanya mata, ɗanta da matatcciyar 'yata daga nan muka yi sanadin mutuwar hidimi Bawa domin mu rufa wannan sirri, haka zalika muka kawar da matarsa hadima Rahane domin dai wannan sirri ya cigaba da rufuwa, a yau kuma za mu bi wata hanya don kawar da Ciroma amfaninsa ya ƙare a halin yanzu na haife 'ya'ya maza, yanzu Ahmadu ne kaɗai magajin masaurata domin zuri'ar mai Babban ɗaki rankatakaf ɗinsu ba za su sake yin sarauta a Kudu ba. A dalilin abun kunyar da Aliyu ya janyo musu, hakikanin gaskiya Jakadiya mun sha doguwar tafiya kamin cikar burinmu lallai kisani idan har burina ya cika Ahmadu ya zama sarkin wannan daula tukuicin ki babba ne. Don haka ki yi maza ki je ki aiwatar da abun da na umarce ki. "Allah ya taimake ki ya ƙara miki lafiya, uwargijiyata, uwa ga sarkin gobe. Jakadiya ta faɗa tare da mikewa jikinta yana rawa ta fice daga masaurata, wata bakar van ce ta sha gaban jakadiya, wasu zaratan maza biyu ne suka fito daga van ɗin masu sanye da leather jacket fuskarsu lulluɓe da baƙin facemask, suka yi mata daukar amarya kamin ta yi wani yunkuri sun rufe mata baki da salatif, wani baƙin daji mai duhun bishiyoyi suka nufa da ita sai da suka yi mata dukan mutuwa kafin su tambaye ta ina wayar da Kilishi ta bata, anan take faɗa musu ta fadi sa'ili da suka dauko ta, ta ji sanda ta faɗo daga cikin zaninta. Wannan furuncin na ta ya fusata ɗaya daga cikinsu ya buga kanta a jikin motar nan take kanta ya fashe daga nan bata sake motsawa ba. Da suka fahimci ta mutu duk sai hankalinsu ya tashi gashi basu karɓi wayar ba, ta mutu basu san me za su ce da Ciroma ba. Daga baya suka yanke shawarar a tsakaninsu su nemo wata waya su kai masa a matsayin wacce suka karɓa hannun jakadiya, haka kuwa aka yi Ciroma ya yi murmushin mugunta yana hasaso irin mummunan kisan gillar da zai yi wa Kilishi. *SOFTCARE PRIVATE HOSPITAL* Aliyu na Uku zaune a gaban gadon da Maysun take kwace magashiyam! Tsananin tausayinta ya gama cika sa, musamman idan ya tuna da wa'adin da ya rage mata a duniya duk da yana gani, faɗa ce kawai irin na likitoci ba fadar Ubangiji ba. A duk sanda ya tuna da haka sai ya ji hankalinsa ya ɗan kwanta, duk da yana cikin jimamin ciwon Maysun hakan bai hana masa zurfafa tunaninsa ba Idan har da gaske Azhar ya mutu a labarin da Daddy ya basa miyasa ko burbushin gawarsa ba a gani ba, ya kamata ace koda tokar sa ne sun gani don duk yadda mutum ya kone dole za a ga wata alama tasa, wani irin bugawa zuciyarsa ta yi bai san sanda ya miƙe tsaye ba jikinsa yana rawa idan har hasashe sa ya tabbata gaskiya to tabbas kuwa Azhar ɗinsa yana raye. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. [2/11, 2:28 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye. 103. Da taimakon Hanne Mami ta kammala girka abinci da za ta kai hospital, tun sanda ta ji irin cutar dake damun Maysun ta fara jin nadamar abubuwan da ta aikata. Yanzu kam ta gama fahimtar rayuwa dan adam ba a baki komai take ba, har kwatanta kanta take yi da Maysun da ita ce ke dauke da wannan ciwo ba lallai bane ta sami tausayawar mijinta kwatakwacin yarda Aliyu ke nunawa Maysun, saboda tasan a halin yanzu bata da kyakkyawan hali ko ɗaya wanda za a iya tausaya mata saboda shi. Wannan yasa tun sanda suka baro asibiti jikinta ya yi sanyi ta ji nadama ta kamata. Har ta kudurta aranta za ta roke Daddy gafara ita rayuwa gajeriya ce idan babu cuta akwai mutuwa wacce za ta iya ɗaukar mutum a kowanne lokaci da wannan tunanin Mami ta kammala arranging abincin da za ta tafi dashi a food basket kana ta nufi bangaren Daddy jikinta a sanyayye ta tura ƙofa. Daddy ta gani tallaɓe da kamatunsa ya ya zurfi a tunani, bayan ta gama ƙare masa kallo ta zauna kusa da ƙugunsa tana jin ita ce silar shigar mutane da dama a cikin damuwa da bata yi abun da ta yi ba da wata kila har yanzu Abba yana raye sosai da sosai take tuhumar kanta tare da ba wa kanta laifi ta kuma jefa kanta a matsayin mai azababben son zuciya. "Ka yi haƙuri Alh ka yafe min domin ni ce silar jefa ka cikin wannan yanayi, ga kuma iyayen Abba da nake ji ta dalilina suke acikin wannan matsanancin hali. Hakika ni bana cikin jerin mutane nagari, ni kaina Alh ina mamaki ta yarda na bari shaitan ya yi wasa da imanina bansan miyasa na juye daga Mariya ta mai haƙuri da takwalli mai son farin cikin iyalinta? Na tuba Alh wallahi na yi nadama Dan Allah ka yafe min ba don halina ba. Mami ta ƙarashe magana tare da sakkowa ƙasa ta zube guiwayoyinta ƙasa, sosai mamakin sauyawarta lokaci ɗaya ya lulluɓe Daddy, sai kuma ya tuna Allah ne mai shiryarda wanda yaso a lokaci da yaso to wannan ba abun mamaki bane daga cikin kudirar ta ubangiji. Tunawa da haka da ya yi yasa ya ɗago kafanɗun Mami ya mayarda da ita kan kujera tare da kama hannunta faɗin "Al-hamdullilah! Dukkan godiya da yabo sun tabbata ga Ubangiji talikai mahaliccin sammai bakwai, da ya bani aron rai da numfashi da har naga wannan ranar da Mariya kika yi nadama kana kika tare da da fahimtar kurakuranki. Hakika shaitan ya yi amfani da rauninki na mace ya yi wancagali da imaninki sai gashi cikin hukunci Ubangiji kin yi yaƙi da wannan zuciyar taki da shaitan ya yi kane-kane acikinta. Na yafe miki Mariya daman tun can asali na kudurta araina na yafe miki, a yanzu ma na kara faɗa na yafe miki Mariya duniya da lahira. Je kika kira min Aydah yana da kyau nai mata bayani kamin mu tafi asibiti ɗin. Mami ta amsa tare da miƙewa ta fice koda ta shigo ɓangarenta Aydah tana zaune a falon ƙasa goye da baby Noor, mami ta isar da sakon Daddy tare suka nufi ɓangaren Daddy still yana zaune inda Mami ta barshi. Cikin natsuwa ya shiga ba wa Aydah da Mami haɗuwarsa da Aliyu na uku a garin London har zuwa yadda AB ya zo hannunsa, lokaci da Aydah ta ji irin cutar da mahaifiyar AB ke ɗauke da ita sai ta ji wani irin rauni a zuciyata har ta kasa riƙe kanta ta dinga zubda hawaye hakikanin gaskiya ta tausayawa Maysun yadda ta ji ta ƙwallafa ranta akan Ab sai gashi Allah ya yi ikonsa ba zasu haɗu ba. Bayan sallar isha Daddy da Mami tare da Aydah suka nufi software koda suka isa Maysun ta farfaɗo har Aliyu na uku ya bata labarin Baby Noor ta kagara su zo ta ganta, suna shiga ɗakin da take Aydah ta yi arba da fuskar Maysun mai kamanceceniya da ta yayanta bata kara rudewa ba sai da taga Aliyu na Uku koman sa sak na AB, cike da farin ciki Maysun ta karbi Baby Noor a hannun Aydah ta rungumeta tsam a ƙirjinta tana jin ɗumin jikinta, ji take yi tamkar Ab ɗin ne ta rungume. Mutuwar Ab ta dawowa Aydah sabuwa sosai ta ci kuka sai da Maysun ta gama shasshafa baby Noor kana ta maida ganinta kan Aydah ta ya fito ta da hannu, hawayen idanun Aydah sun kasa tsayawa da sauri ta je ta rungumeta dukkansu biyu suka fashe da kuka, sun dau tsawon lokaci suna koke-kokensu daga bisani suka haƙura, Daddy da Aliyu na Uku suka fita hakan ne yasa Maysun ta umarci Aydah da ta bata labari Ab halayarsa abubuwa da yake so da wanda bayaso, Aydah tana kuka tana faɗa masa sai ya zamana ita tana kuka Aydah tana yi Mami dake zaune a gefe tana kallonsu tare da tayasu kukan. Cikin ɗan lokaci ƙanƙani Aydah da Maysun suka yi bala'in sabo tamkar sun shekara da sanin juna daga ƙarshe ma anan asibiti Daddy da Mami suka baro Aydah za ta kwana tare da Maysun Mami ta dawo gida da baby Noor Aliyu kuma ya nufi hotel ɗin da suka y masaukinsu. Tun haihuwar baby Noor karo na farko da Mami ta kula da ita har ta kwana ɗaki ɗaya da ita nan da nan kaunar yarinya ya sami muhalli a zuciyata, sai yanzu ta daina ganin laifin yaranta da maigidanta yadda suke bala'in son Baby Noor ashe bala'in shiga rai ne da ita, a wasu lokuta har haushi mutane take ji yadda suke nuna mata ƙauna yanzu haka kusan sai Abdulkarim ya zo duba ta kuma sai ya ɓata dogon lokaci yana mata wasa, wani lokaci ma har ya fita yake yi da ita ga yawan kyaututtuka da take samu daga wurin abokan Ab, ga 'yan uwan margayiya Rumaisah koda yaushe cikin zarya zuwa ganinta suke yi hatta da yayan Rumaisah Safwan da baya Nigeria amma kullum cikin kiran vid call yake yi Aydah ta haɗa shi da ita ya kan bata lokaci yana kallonta kamin ya kashe wayarsa. A takaice baby Noor tana da farin jini na musamman kowa sonta yake yi babu ma kamar Sadiya da duk wani kudinta ga shopping ɗin kayayyakin Baby Noor suke ƙarewa. *MASAURATAR KUDU* Yaran Ciroma da suka tabbatar da jakadiya ta mutu sai suka haƙa rami mai zurfin gaske suka binneta a dokar daji, daga nan suka dawo gidan gonar Ciroma suna jiran ƙarasowarsa suka nemi waya fairly used siya suka cewa Ciroma ita ce wayar da suka karbe a hannun Jakadiya, kuma sun goge duk wani vid dake ciki saboda haka ya kwantar da hankalinsa don kuwa matsalarsa ta zo. Kuɗi masu yawan gaske ya basu kana ya koma masaurata, can cikin dare ya yi ɓanda kama ya fita zuwa bangaren Kilishi, cikin kwarewa ya dinga sanɗa har ya isa ɗakinta ta yi kwance rashe-rashe tana sharar bacci duk tana cikin damuwar rashin dawowar Jakadiya amma hakan bai hana mata baccin ba.Ciroma ya yi tsaye yana kare mata kallo yana saki murmushin mugunta, sannu a hankali ya hau gadon Kilishi ya kai hannunsa ya dalla mata mugun mari, can cikin bacci Kilishi ta ji saukar mari a kumatunta ta zabura ta tashi zaune tana zare ido tana tozali da Ciroma wanda ya murtuƙe fuska hanjin cikinta ya hartsune, tsoro ya mamaye ta ko ba a faɗa mata ba ta gama wassafa abun da ya kawo sa shiyasa tun kamin ya kai da aikwatar da manufarsa akanta ta fara magiya "Dan Allah ka yi haƙuri Ciroma naci darajar rainon ka da nayi koda ban kasance wacce ta kawo ka duniya ba na ci darajar kula da kai da nayi har ka girma, na ba ka gata wanda ni ce sanadiyyar zamanka sarkin kudu. "Haka zalika ke ce sanadiyar mutuwar iyayena ba, kuma kike ƙoƙarin fallasa sirrina, to amma kamin ki kai da yin haka ni ɗin nan zan aika ki garin da kika aika iyayena Kilishi. "A'ah! Ciro..... Kamin ta karasa ya cafke wuyanta ya danne ta da dukkan ƙarfinsa tun tana ƙoƙarin kwatar kanta har ƙarfin ta ya ƙare abun ka da jikin girma Ciroma bai sake ta ba har sai da ya tabbatar da cewa ta mutu, kana ya gyara mata kwanciyarta har da rufe ta da duvet ta yadda ya shigo cikin sanɗa haka ya fice zuciyarsa wasai yana gani ya kawar da damuwarsa. ***** Tun sanda Anaal ta shiga ɗakin da AB yake bata motsa ba ko nan da can tana kwance a ƙirjinsa, sai da aka yi kiran sallar magarib sannan ta tashi ta je ta yi alwala ta gabatar da sallah rabin addu'arta duk akan ab ne ta kagara taga ya motsa koda ɗan yatsansa ne, a yanzu wata irin ƙaunarsa Allah subhanahu wata'ala ya dasa mata, tana so ya tashi su haɗa kan alhalin su domin duk abun da ke faruwa a masaurata tasani ta hanyar twins da su kaɗai take waya su ma ɗin sai in ta ce ta kira su, tana sallama sallar isha ta miƙe ta dauko ruwan zam-zam da koda yaushe take addu'a acikinsu ta bin jikin Ab ta shafa masa yau bayan ta kammala shafa masa ta kamo Alqur'ani dake cikin wayarta, ta shiga karanta masa a hankali tana kyautata yaƙini ta hanyar karatun Alkur'ani da take masa wata rana zai farfaɗo daga doguwar suman da ya shiga. Sannu a hankali AB yake motsa hannunsa mai ɗauke da drip, tun yanayi a hankali har ya shiga motsawa da karfi na'urar da ke nuna bugawar zuciyarsa ta shiga ƙara wanda hakan yasa Anaal tai sauri ta ɗago idanunta ta sauke su akansa sai taga idanunsa suna marmadi alamar yana so buɗe su. Cikin kidima ta miƙe tsaye tun idanunsa suna rawa-rawa har ya buɗe su kaɗan sai kuma ya sake rufe su cikin sauri wanda hakan yasa sautin ƙarar na'urar ya ƙara yawa, da gudu Anaal ta nufi parlor tana kwallawa Dr Maheer kira da sauri ya nufo ta dawowarsa daga kenan masallaci Anaal tana kiransa bugun zuciyarsa Dr Maheer ya fara dubawa, da sauri ya ja wata allura a syringe ya yi masa a hannunsa ya ɗauki tsawon lokaci yana duba sa ƙafin ya ja wani kalan numfashi ya ciro handkerchief daga gaban aljihunsa ya goge gumin da yake ta faman tsatsafo masa a goshi. Ya juya kalli Anaal yaga sai zarar idanuwa take yi jikinta yana rawa wani irin tausayinta ya dirar masa bayaso ya faɗa mata abun da zai ɗaga mata hankali domin yadda yaga tana zarar idanu dole ya ji shakku faɗa mata. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. [2/11, 2:29 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye. 104. Wasu busassu miyau Anaal ta haɗiye jikinta duk yai sanyi tana fargabar abun da za ta tambaya da kuma kalar amsar da Dr Maheer zai bata duk da irin fargabar da take ciki daurewa ta yi ta ce "me ke faruwa Dr Maheer me ya sami yayana?" Ajiyar zuciya Dr Maheer ya yi cikin sanyin muryarsa mai matuƙar daɗi ya furta "Bugun zuciyarsa ya ragu da kashi takwas bisa goma idan har ya kai 24hours bugun zuciyar nasa bai daidaita ba I'm sorry to say za mu iya rasa shi. "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Dr Maheer please ka ceci rayuwar ɗan uwana dan Allah kada ka bari ya mutu shi kaɗai ne ɗa namiji a wurin Abbuna shi ɗin hasken idaniyar mahaifina ne cigaba da rayuwarsa shi ne zai dawo da farin ciki da walwala ahalina, mutuwarsa kuwa za ta iya kara dagular da komai. "Anaal ki cigaba da masa addu'a rayuwa da mutuwa duk suna hannun Allah, iyakacin mu kula da majiyaci idan kwanakin sa sun kare likita bai isa ya basa wata rayuwa ba. Wani irin kuka Anaal ta fashe dashi tare da kama hannun Dr Maheer, cikin dushewar murya ta ce "likita ba ubangiji bane amma ubangiji ne ya basa baiwa da fikra ceto rayukan mutane idan suna cikin hali irin na jinya, jikina yana bani za ka iya Dr Maheer kada ka bari gwarin gwiwa da nake dashi akanka ya tafi a wofi idan har ka yi nasarar ceto rayuwar yayana na yi ma alƙawari zan aure ka. "Me kika ce?" Dr Maheer ya faɗa yana zaro ido domin abun da ya daɗe yana jiran ya fito daga bakinta ne, yau ta furta masa. "Yes! Maheer zan aure ka zan rayuwa da kai za ka zama uban 'yayana muddin dai za ka ceci rayuwar ɗan uwana. Sanyayyen murmushi Dr Maheer ya yi wani irin gwari gwiwa ya dinga shigarsa da sauri ya nufi Ab ya shiga baje duk wata kwarewar sa akansa, yana kuma gani nasara dan yanzu Ab sosai yake responding treatment ɗin, saɓani can baya da sai ya sha wuya kamin ya yi respond. Ga yadda Dr Maheer ke hasashe idan har ya cigaba a haka zuwa gobe zai iya tashi. ******* Aydah ta fito daga bathroom riƙe da kafaɗar Maysun ta taimaka mata ne ta yi wanka, da yake har yanzu babu kuzari a jikinta komai Aydah ke mata zaunar da ita Aydah ta yi akan plastic rubber chair, kana ta jawo food basket ta zuba mata kunun gyaɗa da Mami ta aiko direba ya kawo musu breakfast, kamin zuwa anjima ita ma ta shigo. Aliyu na uku ne ya turo ƙofa ya shigo cikin shigarsa ta babbar riga ash color ɗin shadda wacce ta ji aiki da dark ash ɗin zare hular kansa kalar aikin jikin shaddar, as usual sai ƙamshi tsadadden turarensa yake. Ya yi bala'in kyau tun da ya shigo Aydah ta tsinci kanta da faduwar gaba ba inda ya baro Abbanta, abu gudu Ab zai gwada masa kuruciya amma komai nasu iri ɗaya ne kamar tasu har ta ɓaci kamar an tsaga kara. Yadda Aydah ta saki baki da hanci tana kallonsa ba ko kyaftawa yasa shi sakar mata murmushi don ya gama gano abun da take kallo saboda hotunan Ab da aka nuna masa shi kansa yaga yadda suka yi bala'in kama "innalillahi wai'inna illahim raji'un! Hatta da murmushin su iri ɗaya. Aydah ta faɗa a bayyane wanda ita a tunaninta cikin zuciyarta ne ta yi magana batasan cewa a bayyane ta faɗa ba sai da ta ji sautin murmushin Aliyu na Uku yana faɗin "Kai my daughter yaushe za ki haɗa murmushina da na mijinki bayan kisan na fisa iya murmushi ke fa da bakinki kika gayamin bai cika dariya ba sai in tayi masa daɗi ni kuma koda yaushe fuskata cike take da fara'a. Wata irin mashahuriyar kunya ce ta lulluɓe Aydah, tai sauri zamewa daga kan kujerar da take zaune akai ta durƙusa ta gaishesa "Ina kwana Abbu?" "Ina kwana my daughter hope kin tashi lafiya ya jikin ummin taki?" "Jiki al-hamdullilah! Don kuwa har ta yi wanka breakfast ma take yi yanzu. "Ma shaa Allah! Allah Ya ƙara mata lafiya ya tashi kafanɗunta. "Amin Abbu! Aydah ta faɗa idonta na cikowa da ƙwalla domin ta ji irin cutar da ke damun Maysun ɗin da kuma wa'adin da likita ya faɗa akanta. "Sababul khairi Abu Azhar. Maysun ta faɗa idanunta akan fuskarsa murumshi ya sakar mata tare da karasa kusa da ita ya ɗago fuskarta yana kallon tsakiyar idanunta "Sababul khairi oum Azhar ya jikin naki akwai inda yake miki ciwo na kira likita ya duba ki kafin na wuce Gombe??" Girgiza kai ta yi tana faɗin "A'ah! Bana ji komai kuzarin jikina ne kawai bai dawo ba shi ma nasan sannu a hankali zai dawo ka gaishe min da Safiya ka bata haƙuri a madadina, ka kuma roka min alfarma a wurinta da ta zo mu ga juna kamin na mutu. Da sauri ya rungume ta yana bubbuga bayanta zuciyarsa tana masa wani irin ji yake da ba a gaban Aydah yake ba da abun da zai hana masa taya Maysun kukan da take yi, da sauri Aydah ta tashi ta fice waje zuciyata ba za ta jure kallonsu a haka ba koda ta isa parking lot kuka ya ci karfin ta a jikin wata mota ta kifa kanta tana shasshekar kuka. Aliyu na Uku ya ɗauki dogon lokaci yana rarrashin Maysun tare da nuna mata rai fa da mutuwa duk na Allah ne sau nawa mai lafiya zai mutu ya bar mai ciwo, da zarar ya dawo zai kai ta India akwai kwararrun likitoci da suka kware akan cuta irin ta, ta wani murumshi mai ciwo Maysun tai masa cikin raunatacciya murya ta ce "kada ka wahalar kanka Abu Azhar mutuwa dole ce koda da cuta ko babu dole wata rana sai mun mutu kawai ka cigaba da yi min addu'a mutuwata ta zo min cikin sauki na tafi cikin salama. Aliyu na Uku ya ji zuciyarsa ta karye duk yadda ya kai da jarumta sai da kuka ya kubce masa, sosai yake kuka yana ƙara matse Maysun a ƙirjinsa "Kada ki tafi ki barni Maysun ina ji a jikina Azhar yana raye bai mutu ba ko jiya nayi mafarkinsa yana faɗamin zai dawo gare mu. Idan kika tafi wa zai kula mana dashi ki sani Azhar yana bukatar mu a tare dashi. "Ubangijin da ya ba mu shi lokacin da ba mu yi tsammani ba ya kuma raba mu dashi a lokacin da yake da watanni biyar a duniya ya kuma hada shi da iyayen nagari suka raini shi cikin da so da kauna na tabbata idan har yana raye za su cigaba da kulawa dashi. Sosai kalamanta suka kayar mai da zuciya ya ji ba zai iya cigaba da zama a ɗakin ba saboda rauninsa ga baki ɗaya ya gama bayyana, ya sumbaci forehead ɗinta ya juya da sassarfa ya fice daga ɗakin. A parking lot ya tarar da Aydah, tana ganinsa tai sauri goge hawayen fuskarta ta kakkalo murmushin dole tai masa daga shi har ita idanuwansu sun jajir alamar sun yi kuka. "Har ka fito Abbu?" Aydah ta tambaya tana kokarin ɓoye damuwarta. "Eh! Daughter zan tafi Gombe wajen ɗayar mamar ta ku, ki kula da ita sosai idan kin ga jikin nata yana so tashi ki yi gaggawar kiran likita. "To Abbu in shaa Allahu zan kula Allah ya tsare ya kai ka lafiya. "Amin my daughter! Ya yi magana tare da shiga mota Kabir Umar ya ja sa zuwa airport. Aydah kuma ta koma ɗaki wurin Maysun hira Maysun take ta faman jan ta da ita har sai da taga ta saki jikinta. *MASARAUTAR KUDU* A yau kuma suka tashi da mummunan labari na mutuwar Kilishi, tuni 'ya'yanta na nesa da kusa sun iso masaurata aka yi mata sutura kamar yadda addini ya tanadar aka kaita gidanta na gaskiya, kana aka ci gaba da zaman makoki. Ciroma ya fi kowa shiga tashin hankali duk da matsayinsa kuka ya dinga yi Ahmadu ne ya dinga rarrashinsa. Ta ɓangaren mai babban ɗaki ta ji sauki sosai sai dai a yanzu bata iya taka ƙafafuwanta, bayan an sallame ta daga asibiti yaya Gimbiya ta dawo da ita gidanta tana cigaba da kula da ita. Da mai babban ɗaki ta yi zaune tai nazari akan Aliyu sai tai masa uzuri duk da tasan wani bangare yana da laifi na ɓoye musu babban al'amari irin wannan da ya yi amma a matsayinta na uwa sai tai masa uzira, tun tana asibiti take zancensa ta ce Magaji ƙarami ya kira mata shi yayin da yaya Gimbiya da Gimbiya Hauwa suka yo mata caaa! Suka hanawa Magaji ƙarami kiran nasa har yaya Gimbiya tana faɗin idan har mai babban ɗaki ta kafe lallai sai Aliyu ya zo to ita za ta bar asibitin ɗin don bata ga amfani da Aliyu zai mata bayan duk irin abun kunyar da ya jawo musu. Mai babban ɗaki tana ji tana gani yaya Gimbiya da Gimbiya Hauwa suka hana ta magana da ɗanta. Ga magaji ƙarami daman can Allah ya dora masa tsoron yaya Gimbiya yasan halinta har yanzu bai wuce duka a wurinta ba, shi mutum ne mai sanyi hali bayaso hayaniya shiyasa ya bi su a yarda suke so don kawai a zauna lafiya ba don haka ba shi ma Aliyu yana cikin ransa. Misali ƙarfe 12:44pm Aliyu na Uku ya isa masauratar Gombe sai da ya fara zuwa fada ya kwashe gaisuwa wurin yayan Safiya mai martaba sarki Haroon wanda ya kasance yaya ga Safiya. Daga nan ya nufo gidan mahaifiyar ta, ko kaɗan ban tsammaci kyakkyawar tarba daga gare su ba duba da irin girman laifinsa a wurin 'yarsu amma sai yaga sabanin tunanin nasa hatta da Safiya sai nan-nan take dashi bini-bini ta sakar masa tattausan murmushi bayan sun kebance ta dube shi cikin sanyi murya ta ce "Abbu duk ka bi ka rame dan Allah ka rage saka damu a ranka kada hakan ya shafi lafiyarka. Ƙasa da murya ya yi ya ce "I'm sorry Safiya ban kasance mai adalci agare ki ba ka yi haƙuri ki yi min afuwa a wancan lokaci ina tunani irin abun da zai faru idan na faɗi aurena da Maysun sai dai duk abun da na yiwa gudu a wancan lokaci shi ne ya faru a yanzu. Cigaba da rarrashinta da daddaɗan kalamai ya yi har ya bata labarin abubuwan da suka faru mutuwar Azhar da halin da Maysun take ciki, sai ga Safiya tana sharɓe hawayen tausayin mijinta abun ka da mace mai haƙuri da hangen nesa nan take ta yafe masa ta kuma yi masa alƙawari gobe za ta bishi su tafi Kano ɗin. "Har yanzu ban sami wani labari akan Anaal ba bansani ba ko ta kira ki a waya ni dai ko kira ɗari zan mata bana samun ta a waya?" Numfashi Safiya taja ta sauke tana ɗan murmusawa ta ce "Tana lafiya ko yau da safe ta kira ni. Cike da mamaki ya furta "Ta kira ki fa?" To ni kuwa laifin me na yiwa Anaal da za ta ƙi kirana a tunaninta ita kadai ce bana iya ɓoyewa halin da nake ciki, hatta da mai babban ɗaki ban gayamata labarin Maysun ba amman ita Anaal tuntuni na sanar da ita. Bani da wani abokin shawara a rayuwata sai Anaal haka zalika ita ma bata ɓoye min komai nata, wannan shi ne karo na farko a rayuwarta da ta boye min abun da ke faruwa da ita. Jikina ya bani tabbas da akwai wani gagarumin al'amari da take kainta Kano. Ko kin san me take yi a Kano Safiya?" Aliyu ya ƙarashe magana fuskarsa na nuna tsananin damuwa da ɓacin rai, Safiya cike da kulawa ta kama hannunsa ta haɗe da nata ta kalle shi tana faɗin "Karka yi fushi da ita Abbu Anaal yarinya ce mai matukar biyayya agareki ta kasance tana son farin cikinka fiye da komai da kowa, duk abun da za ta yi kaine abu na farko mai muhimmanci agareta, ni kam iya tsawon rayuwata ban taɓa gani uba da 'ya irin kai da Anaal ba. Wasu 'ya'ya sun fi so iyayensu mata amma ni tuni na dade da sani Anaal ta fi sonka akaina ta fi ƙaunar farin cikinka akan nawa, ita ɗin fura ce mai matuƙar daraja muddin tana raye ba za ta kasance mai share maka hawaye. A duk sanda nai mata ƙorafin aure ba zan manta da kalaman a koda yaushe take faɗa ba Ummi ba aure ne banaso ba, ba kuma masu sona na rasa ba, ummi tausayin Abbuna nake ji idan na yi aure dole ragamar kula da mijina zai dawo kaina, taimakawar da nake yiwa Abbuna a kasuwancinsa zai ragu, da zarar kuma na haihu na fara tara yara shi kenan nauyi ya ƙara yi min yawa, gashi ni ce koman Abbu bashi da wani ɗa da zai taimaka masa twins basa son aikin kamfani shiyasa basa maida hankali, na tabbata da zarar na bar kamfani su ma tafiyar su za su domin suna zaune a kamfani saboda ni ba wai dan suna ji daɗinsa ba. Ga Amal da Amatullah yanzu suke tasowa kuma kowacce su tana da nata ambition banaso wahala ta yiwa Abbuna yawa. Dan Allah ki ƙara daga min ƙafa akwai wani babban al'amari da na saka a gaba wanda nake tunani zai taimake rayuwar Abbuna da zarar na cika burina na yi miki alƙawari Ummi zan fito da miji na yi aure. Tun sanda Safiya ta fara magana Aliyu na uku yake bin kalamanta yana bin su yana ɗora su a mizanin na auna fahimta, sai dai yadda ƙwaƙwalwrsa ta toshe ya kasa fahimtar kalaman Anaal. Washegari Aliyu ya juyo Kano tare da Safiya, koda suka iso hospital ɗin Mami da yaranta dukka suna asibitin kowanne yana ƙoƙarin ganin ya sanya Maysun farin ciki ta hanyar bata labarin yaya Abba, domin shi kadai ne kesa ta farin ciki har ta yi dariya zamansu Sadiya da asibitin ba ƙaramin kawar wa da Maysun damuwa suka yi ba. Shigowar Aliyu na uku da Safiya ya katse musu hirar da suke yi, Maysun da Safiya suka rungume juna tamkar sun shekara da sanin junansu komai cikin ilimi da wayewa suke gudanar dashi, tamkar ba kishiyoyi ba gwanin ban sha'awa wanda hakan ba ƙaramin burge Mami ya yi ba, har ta kudurta aranta za ta zauna lafiya da Huwaila wanda hakan yasa da dare da suka koma gida ta yi wa Daddy zance tarewar Huwaila ta ce ya kamata zuwa gobe ko jibi matarsa ta tare, sosai Daddy ya yi farin ciki yadda Allah ya shiryar masa da matarsa don dama ba ƙaramin so yake wa Mami ba ita ce dai bata zamar masa 'ya ba. Washegari da kanta ta gyarawa Huwaila ɗakunan biyu dake downstairs, ta zuba mata furnitures sababbin da dare Huwaila ta tare. Lokacin da Zeenah ta ji labarin abun da Mami ta yi tattaki ta yi ta zo gidan da zimmar ta zuga Mami sai ga Mami ta bata mamaki dan kuwa zage ta Mami ta yi tass daga ƙarshe tai mata korar kare ta kuma gargadi Balmo maigadi kada ya sake bari ta shigo mata gida. Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. [2/11, 2:29 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye. 105. Sannu a hankali AB yake motsa jikinsa kafin ya shiga ware idanunsa har Allah ya bashi ikon buɗe su dukka, ya bi ɗakin da yake da kallo sai kuma ya shiga tunano abun da ya faru dashi gani ƙafarsa da kansa da bandage ya kara yarda da accident ya yi sai dai wannan ɗakin da yake ko kaɗan bai yi masa kama da ɗakin asibiti ba. A hankali yake furta "innalillahi wa'inna illahim raji'un! Daidai Anaal tana buɗe kofar bathroom ta fito da raguwar ruwan alwala a fuska da hannayenta, sauti buɗe ƙofa yasa shi juyawa da sauri a maimakon yaga Aydah ko Rumaisa ko dai wani makusancin sa, sai ya yi tozali da mss Anaal wanda hakan ba ƙaramin girgiza shi ya yi ba. "Mss Anaal! Ya faɗa sai dai sautin bai fita sosai ba a dalilin muryarsa da take a dusashe, wani kalar zaro idanu Anaal ta yi kafin kuma ta kalli gabas ta yi sujjudi-shukur duk abun da taka yi Ab bai ɗauke idanunsa akanta ba sai mamaki ke ƙara rufe shi miye alaƙarsa da ita da har za ta kasance dashi daidai wannan lokacin?" Sai kuma ya tuna da korarsa da Daddy ya yi, sai ya lumshe idanuwansa Anaal ta ɗago da sujjadar da ta yi ta nufo wurinsa ta mai ƙara hamdallah ga Ubangiji "Sannu yayana ya kake ji jikin naka?" "Yayana?" AB ya furta da madaukakin mamaki iya saninsa da ita da mr Abba Bashir take kiransa dashi miyasa yau za ta kira sa da sunan da ƙannansa Sadiya, Siyama da Aydah ke kiransa dashi. "Bara na kira Dr Maheer na sanar dashi kyakkyawar labari ka farka bayan tsawon watanni da ka dauka acikin doguwar suma. Anaal ta faɗa tare da nufar gun da wayarta take ta dauko ta kira Dr Maheer dama ba nisa ya yi ba ya shiga asibitinsa ne kuma asibitin bashi da nisa sosai da gidan. Daf dashi Anaal ta tsaya tana kallon kyakkyawar fuskarsa da yake ta bin ta da kallon mamaki, gani yadda yake kallonta ta sakar masa murmushi ta bashi labarin yadda aka yi har ya zo nan ɗin, kyakkyawar ajiyar zuciya ya sauke kamin ya yi magana sai ga Dr Maheer ya shigo nan da nan ya shiga duba sa yaga komai nasa ya zama normal ya juya ya kalli Anaal dake ta murmushi farin cikinta ya gaza boyuwa ya ce "Congratulations Mrs Maheer m Hamza yayanki ya farfaɗo kuma cikin ƙoshin lafiya ciwon dake ƙafarsa kaɗai ya rage ya ƙarasa warkewa. "Uhm! Gaskiya Dr Maheer ka cika zumudi duk saurinka dole dai ka jira yayana ya gama dawowa natsuwarsa domin shi ne zai ba ka aurena. Anaal ta yi magana tana dariya shi ma Dr Maheer dariya ya yi, yayin da maganganunsa suka yi bala'in daurewa Ab kai. Dr Maheer ya yi musu sallama ya koma asibiti saboda yana da surgery ɗin da zai shiga, bayan fitarsa AB ya kalli Anaal cikin dushewar murya ya ce "mss Anaal na ji kina waɗansu maganganu wanda nake da tabbaci suna da alaƙa dani sai dai ban fahimci komai ba, shin ko za ki ɗaure ki warware min wannan kurman allo?" Murmushi Anaal ta yi tare da latsa wayarta ta kamu hoton Abbu ta miƙa masa wayar, daman kafin Dr Maheer ya fita ya tashi shi zaune yana jingine da pillow ne ya karɓi wayar idanunsa suka yi masa tozali da wani mutumin mai kama dashi sak kamar an tsaga kara, a matsayin sa na mutum mai cikakken hankali ko bai tambaya ba yasan wannan mahaifinsa idan ba mahaifinsa babu ta yadda za a yi su yi irin wannan kama domin duk tsawon rayuwarsa bai taɓa cin karo da mai kama dashi ba sai wannan mutumin na cikin wayar Anaal ɗagowar da ya yi da zimmar ya tambaye Anaal alaƙar ta da mutumin sai idanunsa suka sauka akan fuskarta da ke yanayi da tasa, hancinsa da nata ɗaya haka zalika shape ɗin fuskarta don kawai ta kasance ta mace shiyasa ya kasa gane kamanninsu ɗaya sai fa yau da ya yi mata kallo a tsanake, wani irin bugawa zuciyarsa ta yi daman duk tsawon wannan lokaci Anaal 'yar uwarsa ce?" Kamar Anaal tasan tambayar da yake yiwa zuciyarsa sai ta gyada masa kai cikin raunin murya ta ce "Ni ƙanwarka ce Abba Bashir wannan na jikin waya mahaifin mu ne Aliyu na Uku, ni da kai baban mu ɗaya. Da sauri Ab ya runtse idanunsa ya kasa yarda da abun da kunnensa ke ji masa, gani yake yi tamkar mafarki yake da zarar ya farka shi kenan, ya sake buɗe idanunsa akan fuskar Anaal wacce ke kallonsa tana hawaye. "Na kasa gasganta abun da kike faɗa Anaal gani nake yi tamkar mafarki ne nake yi. AB ya faɗa cikin sanyin murya. "Yanzu kuwa zan tabbatar maka da zahirin gaskiya ta zare wayarta dake hannunsa ta cire airplane mode da take saka ta, ta yi dialling numbern Aliyu na Uku, a lokacin su dukkansu suna zaune a asibiti, har da Alh Bashir wanda shigewarsa kenan Anaal tana kira, Aliyu na Uku yana ganin sunan wacce ta kira sa jikinsa ya ɗauki rawa, ya yi saurin picking "Anaal kina ina faɗamin ina kika shiga shin kinsan irin tashin hankali da nake ciki a bisa rashin sani takamaiman inda kike?" Kuka Anaal ta fashe dashi cikin muryar kuka ta ce "Albishirin ka Abbu. "Bana so shirmen banza Anaal ina tambayarki inda kike ke kuma kina min shirme. Aliyu na ukku ya faɗa ransa ɓace. "Abbu yayana ya farfaɗo gashi nan zaune yana kallona Abbu ina tayaka murna ɗanka Muhammad Azhar yana raye... "Me kika ce Anaal? Aliyu na Uku ka katse ta cikin kidimewa kana kuma ya saka wayar a speaker "Abbu na ce ɗanka sanyin idaniyarka Muhammad Azhar yana raye duk tsawon lokaci nan ina tare dashi bayan doguwar sumar da shiga sai yau Allah ya yi ikonsa ya farfaɗo, babban abin farin ciki yana cikin ƙoshin lafiya, Abbu nasan kana garin Kano zan turo ma da address ɗin gidan da muke ka zo ka gansa. Abbu kamar ka ɗaya dashi sai dai yafi ka kyau. Anaal ta ƙarashe magana tana kuka tana dariya. Gabaki ɗaya ɗakin rudewa ya yi da ihun farin ciki, Aydah kasa motsawa ta yi daga idan take zaune hatta da Maysun mai fama da kanta, ta ɗaga hannu sama tana godewa Allah. Siyama ta zo da sauri ta girgiza Aydah ita kaɗai ta fahimci suma Aydah ta yi, Mami ta ɗauki robar ruwa ta shafawa Aydah ta ja doguwar ajiyar zuciya tana bin kowa da idanu can ta furta "Gaske ne abun da kunnena ya ji da gaske ne Yayanmu yana raye bai mutu ba?" Siyama da Sadiya ne suka tabbatar mata da hakan. Aliyu na Uku yana gani Anaal ta turo masa da address ya ce Daddy ya zo su je, nan da nan kowa ya ce zai je hatta da Maysun basu baro ta, tashi ta yi Mami ta kamata suka fito sauƙin su ɗaya Sadiya da Siyama da motocin su suka ga ta Daddy. Tafiya suke yi kowanne su gabansa na faɗuwa koda suka isa gidan Aydah ji take kamar ta buɗe ido ta ganta gaban AB. Anaal tana ji dirar motocin su ta kalli AB tana murmushi "Ka gani ko yayana dama na gayama Abbuna yana matukar ƙaunarka kai ɗin ɗan gata ne gaba da baya. Daddy ne a gaba sai faman saɓa babbar rigarsa yake yi tana zamewa, ya riga kowa isa dakin da AB yake yana arba dashi da sassarfa ya isa kan gado da yake ya rungume shi ya fashe da kuka shi ma Ab ƙanƙame Daddy ya yi, ya saki nasa kuka, sun ɗauki lokaci rungume da juna kamin Daddy ya sake shi ya kalli yadda su Aliyu suka yi cirko-cirko Anaal ta ruga ta rungume Aliyu tana "Faɗin Abbu na samo shi na samo maka farin cikinka, nasan daga yau ka yi bankwana da damuwa. "Nagode Anaal Allah ya yi miki albarka yadda kika faranta min ke ma Allah ya faranta miki ya ba ki 'ya'ya nagari masu saki farin ciki. "Amin Abbuna! Anaal ta faɗa very excited, kamin ta je ta rungume Safiya. Daddy ya kalli Aliyu na Uku dake tsaye yana kallonsu da murmushi akan fuskarsa "Zo mana Aliyu ku matso kusa ku ga ɗan nawa. Kamin Aliyu na Uku ya cira sanyayyu ƙafafuwansa har Maysun ta ruga ta rungume AB, gan-gan kamar za ta mayar dashi ciki sai sumbatar sa take yi. Aliyu na Uku ya karasa ya zauna kusa da AB yana kallonsu yana murmushi hawaye na sauka a kamatunsa ga baki ɗaya ɗakin rikicewa ya yi da koke-koke musamman da AB ya tambaye Rumaisa da Aydah cikin raunin zuciya Daddy ya gayamasa Rumaisa ta rasu wurin haihuwa sai dai ta bar 'ya koda ya duba bai ga Aydah ba Daddy ya tambaye Siyama ina Aydah ta fice da sauri ta je ta dubata koda ta fito tana rakuɓe jikin bangon parlor tana kuka haiƙan "haba Aydah ke da ya dace ki yi farin ciki ki godewa ubangiji ya dawo miki da farin ciki da kika rasa. "Yaya Siyam na kasa yarda shin mafarki nake yi ko kuma da gaske ne Yayanmu yana raye bai mutu ba?" "Aydah a zahiri ba mafarki kike yi ba ta so mu je sai tambayarki yake yi. Girgiza kai Aydah ta yi "Ba zan iya shiga ba idan su Daddy na ciki zan iya aikata abun kunya a gabansu zuciyata ba za ta iya jurewa ba dole sai na rungumesa na ji ɗumin jikinsa da na ɗauki tsawon lokaci ban ji ba. Duk yadda Siyama taso Aydah ta, zo su shiga ciki taƙi. Bayan sun gama koke-kokensu suka yi shirin barin gidan kuma har zuwa lokaci Aydah bata shigo ba tana parlor farin ciki da suke yi yasa ba wanda ya damu da sai ta shigo saɓanin Ab dake rungume da Baby Noor, ga baki ɗaya hankalinsa yana ga ƙofar shigowa yana kallon shigowar Babynsa, ita kadai zuciyarsa take mararin gani ya kosa ya ganta yaga ta canza ko tana nan yarda yasan ta. Anaal ta kira Dr Maheer fitowarsa daga ɗakin tiyata ta kira sa, agaggauce ya canza kaya jikinsa ya zo shi kansa ya yi farin ciki da ganin iyayen Anaal ya ƙara duba Ab ya basu tabbacin za su iya tafiya dashi, Siyama ce ta fara fitowa daga ɗakin ta kalli Aydah wacce har zuwa lokaci ta kasa tsayar da hawayen idonta. Sai gashi su Daddy su dukka Dr Maheer da Anaal kaɗai aka bari a ciki suma dan za su taimaka masa ne saboda ba zai iya taka ƙafafuwansa ba duba da yarda ya daɗe a kwace ga ƙafarsa guda mai ciwo bata ƙarasa warkewa ba. Aliyu na Uku ya kalli Aydah dake sharar hawaye yana murmushi ya ce "Shi ga ki gansa kamin a fito dashi tun da kunyar mu ta hana miki zuwa inda mijinki, sai rabon idanuwa yake yi yana kallon ta inda za ki fito. Da sauri Aydah ta sadda kanta ƙasa, cikin yanayi na jin kunya ta nufi ɗakin Siyama da Sadiya suka bi ta dariya. Cikin wani irin yanayi mai matukar wahalar fassarawa ta shiga ɗakin AB da ke kokarin sakkowa daga gado ga Dr Maheer da Anaal sun kama gefe kafaɗarsa Anaal tana riƙe da bangare hagu Dr Maheer dama, AB yana ganinta zuciyarsa ta yi wani irin bugawa da mugun ƙarfi ya koma ya zauna har ta ƙaraso kusa dashi bai ɗauke idanunsa daga kanta ba. Sosai yake mamakin girmanta kamar wacce aka zubawa fertilizer, ga wasu butt da ajiye ƙirjinta kuma ya ciko mayataccen kallo da yake mata yasa Anaal da Dr Maheer suka fice suna murumshi, yadda yake kallonta ita ma haka take kallonsa duk ya yi muguwar rama fuskarsa ta cika da gashi ga wani uban gemi da ya yi hakan bai dusashe kyawunsa ba sai ma Aydah taga gemun ya yi bala'in yi masa ya kyau kamar wani Sheikh, cike da zallan kewarta ya ware mata hannayensa a hankali ta shige jikinsa ya yi mata kyakkyawan masauki a faffadan ƙirjinsa, a lokaci guda suka sauke ajiyar zuciya cikin muryar kuka ta kira sunansa "Yayanmu an gayamaka aunty Rumaisa ta rasu ko? Ka ga kyakkyawar 'yarmu da ta bar mana?" Gyaɗa kansa kurum yake yi yayin da hawaye ke bin kumatunsa yana jin kewar Rumaisah a can kasan zuciyarsa addu'a yake mata. Sun ɗauki lokaci rungume da juna ya ɗago fuskarta yana lashe hawayen dake bin kumatunta kana ya haɗe bakinsu yana kissing ɗinta passionately, lallai kuwa sun yi kewar juna dan su Daddy tafiyarsu suka yi suka ce dasu Sadiya idan sun fito su yi gaba su same su a gida, da kyar Ab ya iya rarrashin zuciyarsa ya bar Aydah suka fito zuwa gidan Daddy. *ALH SALISU GARKUWA MANSION* Yau tun safe mai babban ɗaki ta tsira kuka taƙi cin komai kamar wata yarinyar goye sai kiran sunan Aliyu na uku take yi tana faɗin yaya Gimbiya ta kira mata shi ya zo ta ganshi kafin ta mutu wannan furuncin da take ta nanatawa, yasa jikin yaya Gimbiya ya yi sanyi ta kalli Marwan wanda jiya ya zo hutu daga Kano da yake a kano yake karatu "Marwan je ki ɗakina ka dauko min wayata na kira mata fitinannen yaro nan dama irin su Aliyu sun fi shiga ran iyaye, kana gani dai duk kulawar da muke nuna mata zuciyarta bata daina mararin sa ba. Murmushi Marwan ya yi ya je ya dauko mata wayar ta kira layin Aliyu wanda isowarsu kenan gidan Daddy yana ganin kiranta sai da gabansa ya faɗi, cikin mutuwar jiki ya yi picking "Assalamu alaikum yaya Gimbiya! "Kai fitinannen ka zo mahaifiyarka tana so ganinka tun da kai ka manta da ita. Ita kam ta kasa mantawa da kaine silar kwanciyarta gadon asibiti. "Ki yi haƙuri yaya Gimbiya ta ya kike tunani zan iya mantawa da wacce ta kawo ni duniya, ki tambaye Magaji ƙarami babu ranar da bana kiransa na ji lafiyarta. Kuma koda ba ki kirani ba in shaa Allahu gobe zan zo tare da iyalina dukka. #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo. [2/11, 2:29 PM] Asmy B Aliyu: *KURMAN ALLO* (A beautiful Love story) NA JEEDDAH ALIYU & ASMY B ALIYU #Love Story #Gwagwarmaya #Team Tagwaye 106- 🔚 Su Aydah suna isowa Daddy ya ce a wuce da AB part ɗinsa dake gidan ya yi wanka, a bedroom aka zaunar dashi Aydah ta wuce bathroom dinsa ta haɗa masa ruwa wanka. A hankali AB yake bin ɗakin da kallo yana tuna irin rayuwar da ya yi acikinsa. Sai kuma ya dawo da ganinsa kan baby Noor dake cinyarsa dan har Anaal za ta wuce da ita bangaren Mami ya karɓe ta, wata irin ƙaunarta yake ji hannunta ya kama ya kai bakinsa ya sumbata. Aydah ta fito ta zo kusa dashi tana faɗin "kawo ta ka je ka yi wankan na hada ruwa. A maimakon ya miƙa mata ita sai rikon hannun Aydah ta zauna daf da ƙugunsa yana kallonta yana lumshe idanuwansa tamkar dai mai jin bacci "Baby kin canza ga baki ɗaya. "Uhm! Aydah ta faɗa tana murmushi. "Me kike ci ne haka da kika kiɓa abubuwa nan sun fito. Yana magana yana shafa duwawunta "wadannan kamar za su tsone min ido Allah baby kamar ba ke ba. Ya ƙarashe maganar tare da ɗora hannunsa a boobs ɗinta, ture hannunsa ta yi tare da daukar Baby Noor "Da can ba raina su ka yi ba. "Kai, kai! Baby me kuma ya kawo wannan zance?" "Ka je ka yi wanka Yayanmu su Daddy na jiran mu kada mu barsu su ta jira. "Ki ajiye Baby Noor ki zo mu je ki tayani wankan. Batareda da tace komai ba ta shimfiɗe baby Noor akan gado ta kama shi ya miƙe ya sakala hannunsa a wuyanta ɗayan hannun yana can akan duwawunta yana matsawa, a zuciyar Aydah sai mamaki jarabarsa take yi kai da ka farfaɗo yau ban da jaraba me zai yi da mace. A wurin wanka sai da suka kwashe daro dan kuwa matseta ya yi ya dinga luguiguta ta, da kyar aka yi wanka koda suka fito baby Noor ta gaji da wasanta ta yi bacci, kasancewa dama akwai raguwar kayansa a ɗakin Aydah ta dauko masa wani filtex material brown colour ya saka, sosai kayan suka yi masa kyau, suka yo bangaren Mami Ab baya iya taka ƙafarsa sosai sai da taimakon sanda, hadaddun girke-girken da Huwaila ta yi musu suka haɗu a dining suka ci Daddy da Aliyu na uku aka kai musu nasu a bangaren Daddy, lokacin da AB ya sami labarin Daddy ya aure Huwaila addu'ar fatan alkhairi ya yi musu. Washegari ga baki ɗayansu suka dunguma suka yo garin Zaria gidan yaya Gimbiya, mai babban ɗaki tana gani Aliyu ga kuma Ab sai kurum ta fashe da kuka tare da godewa ubangiji, da ya kasance ɗanta yana da magaji saboda 'ya mace 'yar gidan wani ce ta kuma san rashin mai tallafa masa ne yasa ya zubawa Anaal ido batareda ta yi aure ba. Duk masifar yaya Gimbiya tana ji cutar da ke damun Maysun jikinta sanyi yayi ta jinginar da masifarta a gefe. Marwan Garkuwa yana arba da Aydah zuciyarsa saura kaɗan ta buga bai ƙara shiga tashin hankali ba sai da aka gabatar masa da ita a matsayin matar cousin ɗinsa, ɗakinsa ya shige duk hidimar da ake yi yana can kudundune cikin duvet zazzaɓi mai zafi ya rufe shi. Aydah kuma yi tayi kamar bata taɓa saninsa ba, a zuciyarta sai ƙara godewa ubangiji take yi da yasa bata karɓi soyayyarsa ba da yanzu shi da ita ne za su shiga wani hali. Kwanan su ɗaya a Zaria Aliyu na Uku ya sami kira daga waziri, masarauta tana nemansu da kyar suka yi convince mai babban daki ta amince da zuwa kudu a cewarta ta bar masauratar Kudu bari na har abada. Wayar da Jakadiya ta jefar wani daga cikin bayi ya tsinta lokacin da yaga video dake cikin wayar ya girgiza matuƙa, sai kawai ya je ya kai ma shugaban bayi dake gidan shi kuma ya ba sarkin fada har dai wayar ta zo hannun waziri kasancewar ga baki ɗaya fada basa ƙaunar Ciroma, sai dai basu da yarda za su yi yanzu kuma da Allah ya kawo musu hanyar da za su tsige shi sai farin ciki suke yi. Yayin da Ciroma bai san wainar da ake toyawa ba sai shirye shiryen-shiryen naɗin Galadima yake yi wanda a tsarinsa gobe ne naɗin sarautar. Sosai Aliyu na Uku ya girgiza da jin Ciroma ne ya kashe sarki Mahmood na Uku don kawai ya hau karagar mulki wannan yana ɗaya daga cikin dalilai da yasa ya tsani sarauta. Ciroma yana gidansa jami'an farin kaya suka yi awon gaba dashi zuwa ofishin su, gani video yasa bai da wata mafita da ya wuce ya faɗi gaskiya wata kila zai sami sassauci daga hukunci da za a yi masa, nan da nan ya warware musu duk wani tuggu da muguye abubuwa da ya aikata nan take aka kamo Galadima da Fulani ƙarama duk wanda ya ji abun da suka aikata sai ya tsine musu albarka musamman da suka ji cewa Ciroma ne ya kashe Kilishi saboda ya gano ba ita bace ta haife shi. Kotu aka wuce dasu aka yanke wa Ciroma hukuncin kisa ta hanyar rataya, Fulani ƙarama da Galadima life imprisonment. Ab ya yi farin ciki da ya haɗu da ahalinsa, shi ma dai kamar mahaifinsa ko kaɗan gidan sarauta baya burgesa tuni aka dawowa da Aliyu na Uku da sarautarsa ta sarkin sabon birnin kudu yayin da aka naɗa Ahmadu a matsayin sabon sarkin kudu saboda cancantarsa da sanin ya kamata sa yau ga Ahmadu a matsayin sarkin kudu Kilishi kuma tana lahira tana girbar abun da ta shukka da ta yi haƙuri da wata kila ta ga zuwan wannan rana sai ta bi son zuciya gashi nan inda ya kaita. Aliyu na Uku ya zaunar da AB ya faɗa masa irin cutar da Maysun take damunta, sosai AB ya shiga damuwa ranar ko bacci kirki bai yi ba, tun daga lokaci yake ba wa mahaifiyarsa kulawa ta musamman anan Kudu su Daddy suka baro su shi da Aydah suka dawo Kano, ɗan zaman da Ab ya yi da Maysun wata irin shaƙuwa mai ban sha'awa ta shiga tsakaninsu, sai suka yi sati biyu a kudu sannan Aliyu na Uku ya tattara dukka iyalinsa suka koma Lagos har da AB da Aydah sai satin su ɗaya a Lagos suna cin amarci sannan suka dawo Kano inda sukafi wayau domin har gobe Ab Daddy da Mami yake kallo a matsayin iyayensa ga baki ɗaya hankalin ahalin ya kwanta yanzu basu da wata matsala kowa yana gudanar da rayuwarsa cikin farin ciki. AB da Aydah sun koma gidansu sai zuba soyayya ta fitar hankali suke yi rayuwarsu gwanin ban sha'awa. *BAYAN WATA BIYU* A yau iyalin Aliyu na Uku suka waye gari cikin tashin hankali ciwon Maysun ne ya tashi, sun je asibiti likita ya tabbatar musu ciwonta ya zo matakin karshe su yi mata addu'a kawai domin babu sauran wani abu da za su iya mata. Wannan dalili yasa Aliyu na uku ya kira Ab ya faɗa masa, cikin tashin hankali ya siye tacket ya nufi lagos kamin ya iso Allah ya karbi rayuwar Maysun sun yi kuka rashinta sai dai kawai su bi ta da addu'a. Bayan sati biyu da rasuwar Maysun Ab ya yi musu visa shi da Aydah da baby Noor suka tafi Qatar wurin dangin Maysun sosai suka yi farin ciki da gani AB anan ya sami labarin tun bayan tafiyar Maysun Nigeria mahaifiyarta, ta mutu ya dai hadu da yayunta da ƙannanta tare da iyalansu watan su ɗaya a Qatar suka dawo Nigeria a lokaci Aydah tana ɗauki da ciki sai dai bata laulayi Ab sai kara shagwaɓa ta da rirrita ta yake yi. Siyama ce ta fara haihuwa ta haifi ɗa namiji ana gobe suna Sadiya ta haifi 'ya mace tun sanda suka haihu Aydah bata zauna ba sai hidima take gashi sauran sati guda a fara bikin Anaal da Dr Maheer Ab sai korafi yake mata wai tana wahalar masa da Babynsa. An yi bikin Dr Maheer da Anaal lafiya amarya da ango sun tare a katafaren gidansu anan Kano. Rayuwa tana ta tafiya yau daɗi gobe akasin haka wasu suna farin ciki wasu suna baƙin ciki kamar dai yadda ta faru akan Alh Sanusi da Zeenah akan hanyar su na zuwa Katsina sun sami labarin wani mashahurin boka a wani ƙauye dake cikin Katsina so take ta kowanne hali sai sun ga bayan Daddy da iyalinsa dukka, Musamman da suka ga Ab ya dawo nan da nan hankalinsu ya yi mummunan tashi suka bazama yawon gidan bokaye da Malaman tsibu sai dai babu nasara, jiya suka sami labarin wannan bokan da za su kaima ziyara, anan suka haɗu da masu garkuwa da mutane sun tare hanya a kokarin Alh Sanusi da ya gudu suka harbe shi ko shurawa bai yi ba ya mutu, Zeenah tana gani haka ta ruga wurin gawar mijinta ita ma suka sakar mata harsashi a ciki ta fadi matatcciya. Duk da Zeenah ta gano Ab ɗan mijin ƙanwarta ce Safiya da iyayensu mata suke ɗa wa da ɗa ƙani amma bai sa Ab yaci wannan darajar zumunci dake tsakaninta da Safiya ba, kullum burinta ita da mijinta su kawo ƙarshen sa, sai gashi basu kawo karshen nasa ba kidnappers sun kawo karshen su. Allah yasa mu cika da imani yasa mu fi karfin zukatan mu ya tsare mu da mummunan ƙaddara. Cikin hukunci Ubangiji Aydah ta haifi ɗa namiji kyakkyawan gaske mai kama da Ab, ranar suna yaro yaci sunan Daddy lokacin da Aydah ta ji sunan yaro kallon tuhuma ta riqa bin Ab dashi "Baby wannan kallon fa?" AB ya faɗa tare da zaunawa kusa da ita, ƙara tanke fuska ta yi tare da faɗin "nayi tunani Abbu za ka yi wa takwara, kai Bashir Daddy Bashir yanzu kuma ka sake sakawa ɗan mu Bashir, haba abin ya yi yawa. Ta ƙarashe magana tana turo baki dariya Ab ya yi tare da rungumeta "Baby baki san daɗin nake ji ba a duk sanda Daddy ya yi min kirari da Bashir ɗan Bashir to kin ga yanzu idan ya tashi zai ce min Bashir ɗan Bashir baban Bashir. Aydah ta fashe da dariya sosai take dariya yana tayata "ina sonka Bee da ba ka dawo rayuwata ba ina jin ba zan sake aure ba har in mutu. Kyakkyawan murmushi ya sakar mata tare da haɗe bakinsa da nata duniya ta yi musu daɗi rayuwarsu sai san barka. *ALHAMDULILLAH* _A nan muka kawo ƙarshen wannan littafi suna KURMAN ALLO, muna roƙon Allah da ya yafe mana kurakuran da muka rubuta a cikinsa, ya kuma yafe muku wanda kuka karanta kuma ya bamu ikon aiki da duka abubuwan alkhairi dake cikinsa_ _Haka zalika muna miƙa saƙon gaisuwa ta musamman da kuma godiya ga dukkanin waɗanda suka sayi littatafan mu na 'yan tagwaye biyar, mun yaba muku kuma mun jinjina muku Allah ya ƙara muku buɗi, lafiya da kuma daukaka, mun gode. Allah ya haɗamu a wata tafiyar cikin aminci_ #Love Story 2023/2024 #Jeeddah Aliyu #Asmy b Aliyu #Team tagwaye novels #Kurman Allo.