[20/05, 11:37 pm] +234 813 644 0264: *If you should come across this post plss say a prayer for my late father, Allah ya sabunta masa rahama, ya gafarta masa da duk musulman da suka riga mu gidan gaskiya, Allah ya kyautata makwancinsu gaba daya, ya sa mutuwa hutu ce a garesu, Allah ya yafe masu kurakurrensu, Allah ya bamu guzurin tar da su* 🥺 **All thanks to Allah S.W.T for the chance and privilege to commence this new book, yanda muka fara lafiya Allah ya sa mu idar lafiya* _Hmm ga fa Halysaah, Allah ka bani ikon delivering babu cece ku ce_ *This first page goes to all the members of Mayraah Conversation, i love and appreciate you all*🥰 ✨✨HALYSAAH✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 1.... Tsaye take ta jingina da trunk din bishiya a wani babban garden dake dauke da shukoki iri iri da suka kawata wajen, tsuntsaye sai shawagi suke a garden din happily making a chirping sound as the sun set slowly, the view was so beautiful and breathe taking, duk da yanda ta kafe view din da ido gaba daya hankalinta baya gun, she was just staring at the setting sun absentmindedly, tayi nisa cikin tunanin da take, daga gefenta wata ma'aikaciyar asibiti ce in her mid 40, likitar ta dafa ta tana kallonta cikin kwantar da murya tace "Magariba ya gabato mu je kiyi alwala ko" Kallon likitar kawai take babu ko kiftawa kamar bata fahimci abinda take cewa ba, sai ga hawaye ya fara taruwa idonta tana sauke numfashi a hankali, likitar ta kama hannunta ta jawota jikinta calmly tace "C'mon sweet heart, are you breaking ur promise already?" ta kwantar da kanta jikin likitan hawaye wasu na bin wasu a fuskarta, likitan ta lumshe ido tana patting dinta duk jikinta a sanyaye, a tare suka juya jin footstep a garden din, ya tsaya daga inda yake bai karaso ba yana kallonsu, likitan ta fara gaishesa cikin girmamawa, zame jikinta tayi daga na likitan ta juya masa baya alamar ko ganinsa bata son yi hawaye na zuba idonta, ji take kamar numfashinta zai dauke kamar ko da yaushe, ta fashe da matsanancin kuka ta dafe trunk din bishiyar dake gefenta, ko amsa gaisuwan likitar bai yi ba ya juya ya fice daga garden din, da sauri likitan ta kamota ganin faduwa zata yi, ta fara kokarin zaunar da ita akan lallausan carpet dake shimfide wajen trying to calm her down tace "Haba kanwata, me yasa baza ki cika min alkawarin da kika daukar min ba?" Muryarta na rawa tace "Kiyi hakuri bazan iya ba wallahi" Rungumeta likitan tayi tana bubbuga bayanta a hankali wani mugun tausayinta na shigarta, tayi attending to different cases in her career as a medical Doctor amma babu wanda ya taɓa daga mata hankali ya tsaya mata a rai irin na baiwar Allahn nan, she wish she can take away her pains, she wish she can make her happy once more, she wish she can make her forget the past and face the present, a hankali likitar tace "Halysaah...." khaleesat ta daga rinannun idonta tana kallon likitan, likitan tace "Kiyi hakuri Halysaah, kiyi hakuri" Khaleesat ta sauke idonta bata ce komai ba, likitan ta daga ta tana rike da hannunta suka bar garden din zuwa babban compound din gidan. Few years back! "Talk to Abdul about it, nasan bazai taɓa yarda da haka ba, and he will definitely find a way out for u immediately..." Khaleesat ta daga manyan idanuwanta tana kallon kawarta Safiyyah, kamar bazata ce komai ba sai kuma ta sauke idonta a hankali tace "That will be another huge burden Safiyyah, u know how expensive apartment can be in this state, gida da akwai tsada sosai, kuma na fa ce maki ni bazan sake tambayarsa komai ba, ko kuma ince yayi min wani abu...." Safiyyah tace "Cabdi, to in ba ki tambayesa ba kina da wanda zaki tambaya? Balle ma kinsan halinsa lokaci daya tsaf zai juya situation din nan against you, i think gwara kawai ki sanar masa yafi maki kwanciyar hankali" Khaleesat tayi shiru tana nazarin abinda Safiyyah ta ce, sai kuma ta sauke ajiyar zuciya tana girgiza kai tace "It's fine Safiyyah, ba sai na gaya masa ba i will cope in sha Allah, after all we have just a year and a half to go" Safiyyah na kallonta ta kamo hannunta tace "Ko zaki dawo wajena sai in gaya masu kawata zata zo ta ɗan zauna da mu zuwa wani ɗan lokaci?" Khaleesat ta girgiza kai tace "Let not inconvenience them Safiyyah, kar ki damu kawai, i will sort my self out...." Safiyyah tace "No, i will talk to Ya Musty about ur current situation khaly, nasan bazai ce a'a ba, matarsa ce dai gagarumar er iska, and do i even care? Ba ki ma san me take min ba yanxu a gidan, duk dare bata girki da ni sai dai in nemi abinda zan ci tunda kinsan Ya Musty night shift yake, ni kuma dama kin san i prefer junk food, kawai sai in hada cornflakes in sha abu na" Khaleesat tayi murmushi tace "Shine kike son in bi ki zuwa gidan a haka ko? You are very funny" Safiyya ta juya ido tace "So what? Naga ai ba kanta zaki zauna ba in kin dawo gidan, Yaya Mustyn nan fa is my cousin brother ko kin manta ne? Saboda haka ko taki ko ta so dole in zauna a gidan har in gama karatuna, very wicked and self centered woman, wallahi kar ki wani damu in dai nayi ma Ya Musty magana kawai ki dauko kayanki ki dawo gidan ko zuwa gobe ne...." Khaleesat tace "Aa gaskiya don't even start that Safiyyah, i will cope with my present situation with time, nasan zan saba gradually, beside it's something that is normal kawai dai ni ce nake damun kai na saboda addinina da culture dina da dai wasu abubuwan da baza a rasa ba, any way... it's fine Safiyyah" Tana fadin haka ta kalli wayarta dake hannunta jin shigowar notification, tace "I think my Lyft is here Sophie, sai gobe in Allah ya kai mu" Safiyya ta sauke ajiyar zuciya tace "Ohk then, take care of ur self, i will stroll home too" a haka suka rabu, Khaleesat ta nufi Lyft din da tayi ordering zai maida ta gida. Khaleesat na kitchen wajen karfe goma na dare ta gama girka Noodles da zata ci for dinner kenan taji alamar an bude kofar parlor, a hankali ta karasa juye Indomie dinta a plate ta dau fork ta saka sannan ta wanke pot din ta ajiye, ta bude fridge ta dau bottle water ta fita daga kitchen din, hanyar dakinta ta nufa direct, dai dai corridor aka bude kofar wani room that is just few steps away from her own room, ko kallon direction din bata yarda tayi ba tana kokarin bude kofar dakinta taji ance "Hi, good evening, we didn't get to meet when i was here in the morning I guess you've already left for school then, you can call me Jay, and i am ur new House mate, I moved in this morning...." Sai a sannan Khaleesat ta juya ta kallesa amma bata ce komai ba, ya gyada mata kai yace "Jay" babu yabo babu fallasa tace "I see" Ganin zata shige daki yace "A minute pls" Ta juya ta sake kallonsa da wani expression, a takaice yace "Ke bahaushiya ce?" Ta ɗan hade rai tace "I don't know what u are talking about" Yace "Oh ohk, i am asking for a permission..." Ita dai kallonsa kawai take, Ya gyara tsayuwarsa yace "As u can see it's late already now, can i use some of ur portable water and Beverages before i get mine tomorrow if you don't mind?" Khaleesat ta dauke kanta a takaice tace "Ohk" Yace "Alright" Daga haka ta shige dakinta ta kulle kofar ta saka key, ko da ta gama cin Indomie din bata ji zata iya bude kofa ta fita kai plate din kitchen ba, daga karshe kawai ta bar shi a wajen bayan ta shiga bandaki ta wanke bakinta ta dauro alwala ta fito ta zauna edge din gadon dakin ta dau wayarta, Miss calls din Abdul ta gani har biyu wanda yayi mata tun karfe shidda, ta sauke ajiyar zuciya tana duba agogon wayarta dake nuna mata karfe goma da kusan rabi, meanwhile karfe kusan biyar kenan na asuba agogon Nigeria, bude WhatsApp dinta tayi ta dubasa taga yana online, hakan yasa ta masa WhatsApp call, yana dagawa tayi kasa da murya ta gaishesa a hankali, Bai amsa ba yace "Yanzu kika ga kirana?" Ta sauke boyayyen ajiyar zuciya tace "Kayi hakuri, yanzu naga kiran wallahi" Yace "You mean tun daxu wayarki baya gun ki kenan?" Tace "Not really, tun dai da na dawo schl nake karatu, in few months time zamu fara exams" Yace "I see, shi ne yasa kika ga ban yi deserving lokacin ki ba don zaku fara exams, ta yaya ma wayarki zai yi ring ki ce baki sani ba in ba rainin hankali ba?" Rasa abinda zata ce masa tayi, don wayar a silent yake kuma ya hanata barin waya a silent on several occasions, to avoid further issues sai bata ce masa wayar a silent yake ba, a hankali tace "Kayi hakuri, wallahi ba haka bane, i am sorry..." Yace "Sorry for ur self, malama so nake ki gaya min kina ina har wayarki rang twice baki ji ba? ur lectures today terminated by 4pm Baltimore time, so ina kika je daga nan?" Ta rufe ido ta bude don ta fara gajiya da tuhumar tasa, After few seconds ta marairaice tace "Ina parlor ne ina karatu, wayar kuma na daki" Yace "Kin fara zaman parlor kenan, when did that start? House mate din taki ta dena shigowa da saurayinta ne gidan?" sai da gaban Khaleesat ya fadi, A hankali tace "Bata nan, taje LA jiya" Yace "Sau uku kenan ina kiranki a satin nan baki dagawa sai sanda kika ga dama ki biyoni, that nonsense shouldn't repeat it self again, a kanki aka fara karatu ko ni zaki gaya ma karatun Exams?" Shiru Khaleesat tayi lkci daya hawaye ya cika idonta, a ɗan fusace yace "Baki ji na ne?" Cikin sanyin murya tace "Naji, kayi hakuri hakan bazai sake faruwa ba in sha Allah" Yace "Good, you can go to bed" Tana goge hawayen da yaki tsaya mata tace "Nagode, sai da safe" Shi ya katse call din ta ajiye wayarta gefen gadon ta dora kanta a pillow hawaye na zuba idonta, after a while ta mike ta tafi bandaki ta wanke fuskarta ta dawo ta kashe wutan dakin tayi addu'an bacci ta kwanta.... Washegari Friday da wuri Khaleesat suka gama lectures dinsu, suna zaune a exact spot din jiya ita da Safiyyah dake waya, sosai Khaleesat tayi nisa tunanin da take har bata san sanda Safiyyah ta gama waya ba, dafa kafadarta da Safiyyah tayi ne ya dawo da ita duniyar tunanin da ta shiga, Safiyyah tace "What is wrong Khaleesat, ina ta magana baki ma san ina yi ba, tunanin me kike haka?" Khaleesat ta ɗan kirkiri murmushi tace "Kawai ina kewar Ummanmu ne da siblings dina" Safiyyah ta girgiza kai tace "Ban yarda ba, there is definitely something that is bothering you" Khaleesat ta kauda zancen tace "Ke da George ne ke waya ko?" Safiyyah tayi kasa da murya tace "Pls gobe weekend ki shirya mu tafi Virginia Leesat, George is throwing a party for his birthday tomorrow, kuma za mu je Beach, don Allah kar ki ce a'a, we need to take a break and rest our brain, ba ko da yaushe karatu ba kamar mu muka kawo boko duniya...." Khaleesat dake ta kallonta tace "Ke yanzu sai ki kama hanyar Virginia Safiyyah??" Safiyyah ta hade girar sama da ta kasa tace "To menene, it's just a 4 hours ride from Maryland, kamar fa ace daga kaduna zuwa kano shi ma in mota bai yi gudu ba, pls for once ki zama social mana Khaleesat, ke baki gajiya da zama guri daya ne a kasar nan? Baki gajiya da karatu? ranan Monday fa za mu dawo in sha Allah, kuma babu wanda zai san mun je wani Virginia, dama Ya Mustapha na riga na gama plan din abinda zan ce masa, ke da ba ma ki da wanda zai sa maki ido kike mis using opportunities haka, da mun koma Nigeria fa shikenan, tafiyar nan maza ne hade da mata" Khaleesat ta girgiza kai tace "Lallai... Ni dai ina baki shawara kar ki je Safiyyah" Safiyyah tace "Bana ma son shawaran, abinda mu goma za mu je" Khaleesat tace "Toh Allah ya tsare hanya ya dawo da ku lafiya" Safiyyah ta mata wani kallo tace "Baza ki je ba kenan dai?" Ba tare da Khaleesat ta kalleta ba tace "Kema kin san bazan je ba ai" Safiyyah tace "Ke kika sani, mu dai za mu je wallahi" Safiyyah na kai wa nan ta mike tace "Sai ran Monday" Khaleesat na kallonta a hankali tace "Wai tafiya za ki yi? Da sauran time fa Safiyyah" Safiyyah tace "Aa toh me za mu zauna yi a schl bamu da aji? Yau kuma kece ke cewa da sauran time duk son ki da komawa gida da wuri? Ikon Allah" Khaleesat ta kasa cewa komai, ita har ranta take jin ta tsani gidan nata yanzu, she no longer see the home as her comfort zone, and she don't think she can cope staying together with an Hausa Guy under same roof, da ma bature ne ko kadan bazata damu ba kamar yanda ta damu yanxu, har ta taho school bata hadu da sabon Housemate din nata ba da safe, Safiyyah ta ɗan buda ido ta koma ta zauna tace "Ohh now i remember, wai saboda new House mate dinki? To wai ke meye damuwarki ne da shi? Yayi harkan gabansa kiyi naki ne fa a gidan, ko magana in baki son ya maki you just call the cops a maki iyaka da shi, just dial 911 and that's all, balle nasan kilan da kyar aka kukuta masa ya taho makaranta kasar nan to kuwa ina zai tsaya bata lkcnsa akan abinda ba shi ya kawo sa ba, don dai in wani Shege ne shi bazai zauna a shared apartment ba a USA, kuma 'ya yan masu kudin nan sun fi iskanci su kuwa talakawa abinda ya kawo su kawai suke yi, kiyi ta kanki kawai shi ma yayi ta kansa, kar kiyi mamaki ta scholarship ya zo kasar ma" Khaleesat dai kallon Safiyyah kawai take, Safiyyah ta kyabe baki tace "Tashi mu je gidan, ni banda Ya Musty bazai yarda ba da ba sai in tattaro in dawo gidan naki ba mu zauna kawai" Khaleesat ta marairaice tace "Plss ki sake masa magana ko zai bar ki mana, ai sanda ya hanaki kinga bamu dade da fara makarantar ba" Safiyyah tace "Kar ma ki bata bakinki mutumin nan bazai yarda ba, tashi mu je in raka ki, in House mate din ma yaga kina wani yin abu a tsorace renaki zai yi wallahi, yi zaki yi kamar kema er gari ce kawai sai ki ga ya fara shakkar ki a gidan" Khaleesat ta mike tace "Kar fa muje kiyi ta Hausa, just pretend we are not Hausa" Safiyyah tayi dariya tace "Kece dai is not Hausa, ni kam Bahaushiya ce cikakkiya kuwa" A haka dai suka bar makarantar suka nufi gidan da Khaleesat take.... Khaleesat ta bude handbag dinta ta ciro makulli ta bude kofar shiga gidan suka shiga parlor Safiyyah na biye da ita a baya, Safiyyah na gyada kai jin wani kamshi da parlon yake tace "Da alama bai dade da fita ba ma" Khaleesat dai bin parlon take da kallo ganin duk reading materials dinsa ne saman kujera ya tula a kai, Safiyyah tace "Kinga don Allah ki saki ranki ki ci gaba da harkokin ki Khaleesat, a Maryland fa kike a Amurka ba Kano Nigeria ba, ki dinga abu irin na wayayyu mana pls" Wani kallo Khaleesat tayi mata ta ajiye handbag dinta tace "Ance maki in bature ne ko wani yare ni zan damu, kawai my issue here is about him being a Hausa Guy, har fa tambayata yayi jiya ko ni bahaushiya ce" Safiyyah tace "Ohh kun ma yi magana kenan...." Khaleesat tace "Ni ban kulasa ba kuma ban nuna masa ni Bahaushiya bace, i will just pretend i am from Morocco" Safiyyah ta dinga dariya har da saukowa daga kan kujera tace "Gashi kuwa an ma fi saninsu da fararen mata kyawawa na ajin karshe, tsaf zai yarda daga can kike, kinga da larabci ya zauna daram a bakinki sai kiyi ta zabga larabci nasan ba lallai yana ji ba, daga haka zai kama kansa yayi zaton ke balarabiyar gaske ce... sai ma Abdul yaji kuna gida daya da Bahaushe kilan Baltimore yayi maku kadan wallahi, shi sa nace ki gaya masa kika ki" Khaleesat ta ajiye jakarta bata sake kallon Safiyyah dake ta dariya ba tayi wucewarta kitchen tana tunanin me zata dafa masu dama ko breakfast bata yi ba ta fita daga gidan, tsaye tayi kitchen din tana kallon cartons din bottle water kusan bakwai wanda duk yafi tsada a state din, sai kuma ta juya ta kalli beverages masu yawa da ya ajiye kan cabinet, ta karasa cikin kitchen din ta bude babban fridge zata dau kwai da za ta dafa masu Noodles, kallon fridge din ta dinga yi ganinsa fully stocked with everything, tun daga tsadaddun drinks kala kala, fresh milk, varieties of fruits, with many eggs, muryar Safiyyah taji a bayanta tace "Kai kai kai, shi ya zuba abubuwan nan a fridge Leesah?" Khaleesat ta juya ta kalleta looking speechless, can dai ta dau eggs din da zata dauka ta kulle fridge din ta tafi inda foodstuffs dinta suke shi ma taga kayan abinci ya siyo, Safiyyah ta rike haɓa tace "Duk a kudin scholarship din yake facakan nan? Ko dai bashi da hankali ne bai san bin komai ake a sannu a kasar nan ba" Khaleesat dai ta dau Noodles dinta ta bar wajen tana kallon Safiyyah tace "Ga Indomie ki dafa mana, ina son inyi magana da Ummanmu kafin Aunty Sha'awa ta fita kasuwa" Safiyyah tace "Ohk to" Khaleesat ta bar kitchen din ta dau jakarta ta wuce dakinta, WhatsApp dinta ta bude ta shiga contact din makociyarsu Sha'awa tayi mata voice note kamar yanda ta saba a duk sanda take son magana da Ummanta. Sai kusan karfe hudu na yamma Khaleesat ta raka Safiyyah zuwa gun Lyft din da tayi ordering don tun daxu Cousin brother dinta ke kiranta ganin bata dawo gida ba, Safiyyah ta shige motar ta kulle tana daga ma Khaleesat hannu, sai da Lyft din ya bar wajen sannan Khaleesat ta juya tana tafiya a hankali ta nufi apartment dinta, dai dai apartment din taga mota yayi parking a space din da aka tanadar don parking for that apartment, bata karasa ba ta jingina jikin fence din dake inda take tsaye tana kallon motar ta little space din dake between the wooden fence din, taga ya fito daga motar ta bi sa da ido har ya shiga apartment din yana danna wayarsa, ta fi minti biyar tsaye a inda take, daga karshe tana tafiya a hankali ta karasa apartment din ta murda kofar parlon taji ya kulle, hade rai tayi tana kallon kofar, daga karshe da ta gaji da tsayuwa kawai tayi knocking, sau uku tana knocking sannan ya bude kofar, yana ganinta yace "Hi" ita dai ko kallonsa bata yi ba fuskarta babu yabo babu fallasa ta bi gefensa ta shiga parlon, direct gun wayarta dake kan kujera ta nufa ta dauka tare da reading materials dinta dake saman kujeran, har zata dakinta sai kuma ta dawo ta tafi kitchen ta dau goran ruwa daya sannan ta nufi dakin, sai da ta bude kofar tayi masa kallon gefen ido taga he is just busy sorting out some textbooks that were inside a carton he came with, har ta shiga dakin nata bai juya ba balle ya kalli direction dinta.... 07087865788✍🏻 [20/05, 11:37 pm] +234 813 644 0264: https://chat.whatsapp.com/KVY8hjs3iNq5ntSN4Z5g6V ✨✨ HALYSAAH ✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 2..... Washegari har karfe sha daya Khaleesat na dakinta bata fito ba duk da yunwan da take ji, tayi tagumi don gaba daya ta ma rasa what is her problem particularly, ta dau wayarta jin shigowar WhatsApp message, tun daxu suke chatting ta VN da Ummanta ta wayar makociyarsu Sha'awa, da taji shiru ta ma zata an maida ma Aunty Sha'awa wayar nata ne, ta bude VN din tana sauraren voice din mahaifiyarta, Addu'a Ummanta ke mata tana mata fatan nasara a karatun ta, sannan kamar ko da yaushe ta sake jaddada mata ta kula da mutuncinta ta kula da kanta, daga karshe ta ƙare da cewa za a kai ma sha'awa wayarta don zata fita kasuwa, Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya ta ajiye wayar a hankali sannan ta mike ta dau hijab din sallanta ta saka ta nufi kofa ta bude a hankali ta fita daga dakin don ta gaji da horan kanta da yunwa ita da ke breakfast da wuri, kitchen ta tafi almost bumping into her new House mate shi kuma yana kokarin fitowa daga cikin kitchen din, komawa baya yayi at the same time yace "Good morning" Bata yarda su hada ido ba ta matsa gefe allowing him to pass, ya fito daga kitchen din yayi wucewarsa without looking at her, sai a sannan ta shiga ciki, tsaye tayi tana kallon littered cups da plates din da yayi amfani da su ya bari a sink din wanke wanke without washing them, ga bowl din fruit salad da shi ma ya ajiye bai sha ba, bin kofar kitchen din tayi da kallon mamaki, to wa ya bari yayi masa wanke wanke? Ta fi minti daya tsaye a inda take da tunani iri iri a ranta, wata zuciyar ta ce mata kawai tayi abinda ya kawota ta fita daga kitchen din ta bar unclean utensils din a yanda ya bar su, amma dai kawai ta jawo liquid wash da sponge fuskarta a daure ta fara wanke kayan wanke wanken kawai, bayan ta gama ta goggoge kitchen din ta hada shayi ta debi cookies a plate sannan ta fita daga kitchen din ta wuce dakinta. Wajen karfe uku Khaleesat ta fito daga dakinta, tun da ta gama breakfast take karatu sai sallah kawai ta tashi tayi da azahar, jin ko ina shiru and to be sure baya gidan ta nufi kofar parlon zata bude taji an kulle da makulli, dakinta ta koma ta dauko makullinta ta bude kofar tana duba garage taga babu motarsa a ciki, komawa cikin gidan tayi ta kulle kofar sannan ta tafi kitchen, tun shekaranjiya take son cin shinkafa da miya amma kasancewar she is not comfortable tun da ya dawo gidan yasa ta hakura da girkawa, yanzu da taga baya nan kawai tayi deciding tayi shinkafa da miyar, bayan ta daura shinkafar, ta fara hada miyar dama tana da sauran chicken thighs a fridge, fitowa parlor tayi da sweeper zata yi shara, ta ajiye sweeper din hannunta to tidy the couch first, dukawa tayi tana kallon takardun Housemate din nata da ta gani, sai kuma ta kyabe baki ta bar su nan yanda ya bari a kan kujeran, share rug din parlon ta fara yi bayan ta dauke makullin da ta gani a kasa, ta dinga juya makullin ganin kamar na Bedroom ne, kafin minti arba'in ta gama girkin da take ta tsaftace ko ina na gidan, ta debi abincinta ta tafi daki da shi, sai da ta fara yin sallahn Asr sannan ta dau wayarta tana dubawa, sosai gabanta ya fadi ganin miss call din Abdul, nan da nan taji abincin ya fita ranta gaba daya, ta zauna gefen gado a hankali tana kallon wayar, ta fi minti goma zaune a haka, she was soo worried, to yanzu me zata ce masa ma in ta kirasa, daga karshe ta daure tayi dialing number nasa, har ya katse bai daga ba, ta sake kira nan ma bai daga ba, duk da yunwan da take ji haka nan taji abincin ya fita ranta, ta tsani duk wani abu da zai sa Abdul ya daga mata hankali, haka tayi forcing din kanta ta ci abincin sannan ta kwanta side din gado, bata san sanda bacci ya dauketa ba a haka.... knocking kofar dakinta da ake yi ne ya farkar da ita daga baccin da take, ta mike zaune da kyar tana murza idonta tana kallon kofar at the same time tana mamakin me zai sa ya dinga bubbuga mata kofa haka, to ko dai bashi da kai ne?? ta jawo wayarta tana duba agogo taga karfe shidda da mintuna, bata yi tunanin ta dade tana bacci haka ba, sake knocking da aka yi yasa ta mike tsaye ta saka hijab fuska daure tace "What is that??" Ta ji yace "Ohk i think i misplaced my keys, just want to know if you saw it while tidying up the parlor?" Sai a sannan ta tuna makullin da ta gani a parlor daxu da take shara, tana tafiya a hankali ta karasa kofar dakinta ta murda key din jiki sannan ta bude door din, tuni har ya bar corridor din ya koma parlor ya tsaya yana jiranta, da alama dawowarsa gidan kenan a lkcn, ta karaso cikin parlon ba tare da ta kallesa ba, shi dai duba message din da ya shigo wayarsa yake with all his attention, ta tafi inda ta ajiye makullin sannan ta dawo ta ajiye masa kan takardunsa dake kan kujera tace "Here" Yace "Ohk" dakinta ta koma ta shiga tana mamakin wai Ohk, ba ma thank you ba kamar irin ya ajiyeta din nan, kwafa tayi ta saka ma kofarta key, bayan Khaleesat ta idar da isha ta sake kiran Abdul bai daga ba, sau hudu kenan tana kiransa tun karfe bakwai bai yi responding ba, yanzu dai tafi tunanin yana bacci don dare ne sosai a can kasar, even at that tasan she is in soup, mikewa tayi ta dau plate din da ta ci abinci daxu ta nufi kofa ta fita daga dakin, a parlor ta ga sabon Housemate dinta yana tattara takardunsa at the same time yana answering phone call taji yana cewa "I am on my way now" Daga haka ya katse wayar ya mayar aljihunsa ya dau takardunsa da makullin mota ya mike tsaye, ido hudu suka yi for the first time tunda ya dawo gidan, ita dai ta dauke kai kamar bata ma gansa ba ta karaso cikin parlon zata tafi kitchen taji yace "I ate a little out of the food you cook, and...." Yayi pointing takeaway din da ke kan kujera yace "I am taking some to my frnd too" duk wannan abun bai kalli inda take tsaye ba yake magana, sai ita ce ma da ta dinga kallonsa da mamaki babu ko kiftawa, ya dau takeaway din ya nufi kofa cikin hanzari, yace "Good night" Ta bi sa da kallo har ya fita ya kulle gidan da makulli ta waje, mamaki yasa ta kasa karasawa kitchen din, after some seconds ta tafi kitchen din, da plate din da ya ci abincin, da cup din da ya sha coffee, da bowl din da ya sha fruits salad duk suna ajiye a sink babu wanki, ta jingina da kofar kitchen din ta rungume hannu tana kallon sink din kamar zata fashe don bakin ciki, can ta karasa ciki tana duba shinkafar da ya bar mata, taga da kyar in zai yi spoon uku, gashi duk yayi littering din wajen da shinkafar wajen diba kuma ya bar shi haka, haka nan ta juye er shinkafar da ya rage a karamin bowl, ta wanke duk utensils din, ta gyara ko ina ta goge sannan ta hada shayi ta koma daki da bowl din sauran abincin, zaunawa tayi gefen gado ta dau wayarta tayi dialing number Safiyyah, sai da ya kusa katsewa Safiyyah tayi picking daga daya bangaren tace "Allah da gaske baki da kirki Khaleesah, to ko baki kira ba dai na isa Virginia cikin koshin lafiya" Khaleesat ta ɗan yi murmushi tace "Dama nasan kin isa lafiya ai, hope you are doing good?" Safiyyah ta tabe baki tace "Oho dai, wannan ba matsalar ki bane" Khaleesat tace "Amma don Allah ina kika ce ma Ya Musty za ki?" Safiyyah tace "Ahaf tsaya wasa, sai kace baki san ni ba, munafukar matarsa da yake ba son zamana a gidan take ba ita ce ma ta kara convincing dinsa, duk zatonsu ina gidanki muna group reading with some of our Coursemate" Khaleesat tayi murmushi tace "To ai shikenan, yanxu yaushe zaki dawo?" Safiyyah tace "Gobe ne birthday din ai, in sha Allah i will be back on Monday" Khaleesat tace "Toh Allah ya kai mu, kinsan mene?" Safiyyah tace "Aa" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "Wallahi in gaya maki Abdallah ne ya kirani nayi missing call dinsa as i am speaking to you now tun daxu nake kiransa yaki picking, nasan fushi yayi sosai, ni kuma...." Safiyyah ta dakatar da ita tace "Ke kuma me? Shikenan rayuwa babu uxuri dama?" Khaleesat tayi kasa da murya tace "He warned me times without number kar in sake missing call dinsa Safiyyah, kuma wallahi ina kitchen sanda ya kira wayar kuma na daki ba da gangan nayi missing kiransa ba" Sounding so pissed off Safiyyah tace "Wai don Allah me yasa kika dauki tsoron duniya kika dora ma mutumin nan ne Khaleesat? For how long will things continue this way? Yaushe za ki fara nuna masa ke fa mace ce? yanzu haka za ku yi auren ya maida ki slave a gidansa tunda kin nuna masa kina mugun tsoronsa tun a waje? wannan wani irin gantalallen relationship ne? Gaskiya ina jinjina maki Khaleesat, don wallahi in nice bazan iya ba Allah ma ya gani sai dai duk abinda zai faru ya faru" Cikin sanyin murya Khaleesat tace "I have no choice nor option Safiyyah...." Tana fadin haka hawaye ya fara gangarowa idonta, a ɗan fusace Safiyyah tace "To wai ke kadai ce mace a gidanku ne da ya gani? Naga ga Labibah da Lamisah, ina ce sati biyu kika ba Labibah a shekaru, ita kuma Lamisah wata daya, ga kuma yayyinki Samira da salamatu, to wai halan su ba mata bane sai ke??" Khaleesat dai bata ce komai ba tana goge hawayen dake zuba idonta, Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya tace "Ai shikenan, but u really need to speak up for ur self Khaleesat, ni dai nasan their worst mistake is sending you to school abroad, aje dai zuwa, ke kuma in har baki waye kin kwatar ma kanki 'yanci daga karshe ba to sorry to say this, wallahi u will live a miserable life in the nearest future Khaleesat, this is just the fact i am saying, na gaji da lamarin so called Abdul din ki" Cike da karfin hali Khaleesat tace "Ki daina cewa haka pls Safiyyah, ke me tayani addu'a ce kan Allah ya kawo min komai da sauki amma ba ki dinga fadin wa ennan maganganun ba...." Safiyyah ta taɓe baki bata dai ce komai ba, a hankali Khaleesat tace "Pls ko zuwa gobe da safe ki masa magana ta Whatsapp ki tayani basa hakuri cause nasan bazai daga kirana ba no matter what..." Safiyyah tace "To naji, Allah ya kai mu goben" Khaleesat tace "Ameen" Sallama suka yi, Khaleesat ta ajiye wayarta. Karfe goma saura na safe Khaleesat ta fito daga dakinta rike da wayarta don kar ma Abdul ya kira by mistake tayi missing call dinsa, tun jiya take makale da wayar duk don kar ya kira bata sani ba, kuma sau uku tana kiransa bayan da tayi sallan asuba bai daga ba still, yanzun ma da ta tashi sae da ta kirasa sau daya nan ma no answer, zaune taga new Housemate dinta a ɗan reading nook da aka tanadar a living Room din studying with a huge textbook dake gabansa, she had no idea ma ya shigo gidan, don bayan da tayi sallan asuba ta fito ta hada shayi ta sha da cookies a nan parlon sannan tayi karatu har zuwa bakwai na safe, daga nan ta shiga daki ta kwanta sai kuma yanzu da ta tashi feeling hungry, sau daya ya kalleta yana ci gaba da duba Textbook din gabansa yace "Good morning" Ta karaso cikin living room din a takaice tace "Ok" Ajiye wayarta tayi kan 1 sitter ta nufi kitchen, Ya daga kai yana kallon direction din da ta bi da harshen turanci yace "In baki yi breakfast ba, ga wani nan ki dauka....." Tsayawa tayi sai kuma ta juya ta kalli Centre table da yake nuna mata, ledan abinci ne kan table din duk da bata san wani kalan abinci bane a ledan, ta kallesa taga ya ci gaba da karatun da yake, girgiza kai tayi with no interest tace "No, tnx" Daga haka tayi wucewarta kitchen, ta fi minti uku tsaye kitchen din tana tunanin me zata yi, seeing her House mate sitted in the living room yasa ta zama uncomfortable to cook anything, hakan yasa kawai ta dauko kwalin cereals da bowl zata hada cornflakes, wayarta ta ji yana ring a parlor don tun jiya ta cire wayar a silent, bata san sanda ta saki both d bowl and the Cereal din hannunta ba ta fito daga kitchen din within few seconds, House mate dinta ya bi ta da kallo har ta nufi gun wayarta ta dauka da sauri, sai da gabanta ya fadi ganin Abdul ne ke kiranta, babu bata lokaci ta daga call din, zuciyarta na bugawa tayi masa sallama, jin shiru tace "Hello" kallon wayar tayi ta sake maidawa a kunnenta har sannan bata daina cewa Hello ba, House mate dinta dai ya ajiye Textbook dinsa gefe ganin yanda ta rude ya maida duk concentration dinsa akan ta, Khaleesat ta sake kallon Screen din wayar jin shiru Abdul ya ki ce mata komai kuma tana jin maganar mutane a background, marairaicewa tayi ta duka nan kasan living room din ta saka wayar a handsfree tace "I know u can hear me pls, don Allah kayi hakuri, i am making u this promise hakan bazai sake faruwa ba wallahi, don girman Allah kayi hakuri" Sai a sannan yayi magana da husky voice yace "Hold on to ur promise malama, sau biyar kenan kina missing call dina within a short period, are you out of ur senses or is anything wrong with ur brain?" Da sauri ta girgiza kai kamar zata yi kuka tace "Wallahi ina kitchen ina girki san da ka kira jiya, kuma...." Cutting dinta yayi yace "ke, bana bukatar jin komai daga gare ki, none of ur lies and excuses will convince me, naga kamar u are beginning to take me for granted this days.... Kinsan Allah kika sake missing call dina zaki sha mamakina wallahi cause it will take me nothing to be in America...." Hawaye ya cika idonta cikin sanyin murya tace "Amma me yasa baka min uxuri?" Yace "Baza ayi uxurin ba, ni za ki gaya ma uxuri? A kanki aka fara karatu?" Shiru tayi bata ce komai ba, yace "Wato ke kin fi karfin ki bude baki ki bada hakuri ko" Kasa cewa komai Khaleesat tayi don tun da ta daga kiransa ta fara basa hakuri bata kuma san wani hakurin yake nufi ba, A takaice yace "Anyway, i called to warn you to stop disturbing me with unnecessary calls, na biyu kuma ki ja ma kawarki kunne she should never come into my DM and tell me nonsense again don zan dau mummunan mataki a kanta, ke kuma duk sanda yayi suiting dina i will call you, don't try calling my line again" Yana kai wa nan ya katse wayar, Khaleesat ta dinga kallon screen din wayar hawayen dake makale idonta ya gangaro, House mate dinta ya ɗan yi murmushi wanda iyakarsa lips after paying attention to their conversation, mikewa Khaleesat tayi tana share hawayen dake sauka idonta, sai a sannan ta lura da shi a parlon, dauke kai tayi da sauri bayan sun hada ido, gaba daya ta ma mance yana parlon, taji yace "Is that ur Father?" Wani kallo ta jefa masa tayi wucewarta dakinta wasu sabbin hawayen na zuba idonta, ruf da ciki tayi kan gadonta tana kuka har da shessheka, ta kusa minti arba'in kwance a yanda take, zuwa sannan ta dena kukan da take kawai ta lumshe ido, knocking din kofar dakinta da taji anyi at the same time aka bude ne yasa ta mike zaune da sauri don bata san bata kulle kofar ba, hada ido suka yi da new Housemate dinta, yayi dropping ledan hannunsa ya jingina jikin kofar dakin ya rungume hannu yana kallonta da kyau, calmly yace "Like seriously, Namiji kika kwanta kike yi ma kuka?" Ta wani hade rai ta kauda kanta zuwa wani direction din daban, how did he even know she understands Hausa?? yana juya counter din hannunsa as if counting his words yace "It's... funny" Ta juya ta kallesa har sannan fuskarta a daure tace "Excuse you, why will u barge into someone else's bedroom just like that?" Ya daga kafadarsa yace "Zan yi shisshigi in baki shawara ni dai, run for ur dear life cause u are dating a monster as a boyfriend" Yana kai wa nan ya juya ya fita daga dakin closing the door behind him, Khaleesat ta dafe kanta da yayi mata nauyi, daga karshe ta mike ta kulle dakinta da makulli sannan ta shiga bandaki, karfe sha biyu da yan mintuna ta gama shiryawa don wanka tayi, kallon ledan da ya ajiye mata tayi ta dauke kai sannan ta nufi kofa ta bude ta fita, satan kallon kofar bedroom dinsa tayi ta karasa living room, tana tafiya a hankali ta tafi kofar parlon ta murda taji a kulle an sa makulli, leka windon parlorn tayi taga babu motarsa a garage alamar ya fita, tana tafiya a hankali ta shiga kitchen, ta jingina da kofa tana kallon Cereal da bowl din da ta dauko daxu an ajiyesu kan cabinet din kitchen din, juyawa tayi ta fita daga kitchen din ta koma dakinta, ledan da ya ajiye mata ta dauka ta zauna kan kujeran dake dakin tana duba abinda ke cikin ledan, Breakfast Sandwiches ne sai fresh fruit smoothie a ledan..... 07087865788✍🏻 [20/05, 11:34 pm] +234 813 644 0264: https://chat.whatsapp.com/KBwGIidDZY683SzzudJ0zc ✨✨ HALYSAAH✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 3..... Bayan magrib Khaleesat ta fito living room saboda yunwan da take ji, har sannan bata ji alamar House mate din nata ya dawo gidan ba, gaba daya haka ta wuni ranan babu walwala, all of a sudden yau ta ji a zuciyarta ta fara gajiya da attitude din Abdul da abubuwan da yake mata, da ta tuna Housemate dinta overheard all her conversation with Abdul da kuma maganar da ya gaya mata sai taji wani bakin ciki da takaici ya tokareta at the same time tana wishing that never happened, zaunawa tayi kan kujera ta jinginar da kanta jikin kujeran ta afka duniyar tunanin rayuwarta, after a while ta sauke ajiyar zuciya ta mike tana tafiya a hankali ta shiga kitchen tana tunanin abinda zata dafa ta ci, absently ta fara wanke few utensils din da yayi amfani da shi ya bari a sink sannan ta kunna gas, stir fry pasta ta girka, bayan ta gama ta debi kadan da zata ci ta fita daga kitchen din, dai dai corridor din dakunan ta kusa cin karo da House mate din nata, a firgice tace "Innalillahi...." Sai kuma tayi shiru ta hade rai, ya koma gefe yana kallonta, har ranta taji tsoro don bata san yana gidan ba amma tayi pretending ta hanyar daure fuska, ya daga kafada ya bar wajen ta bi sa da kallon gefen ido.... reading nook dake cikin living room din ta ga ya nufa yana kwashe takardunsa dake kan table, ta dauke kanta ta shiga cikin dakinta ta kulle da makulli, karfe takwas da few minutes ta gama duk abinda zata yi ta dauro alwala sannan kwanta don gobe Monday tana da aji da safe, tana lumshe ido bacci ya dauketa. Cikin bacci Khaleesat taji ana knocking kofar dakinta, ta mike zaune da kyar tana murza ido ta jawo wayarta tana kallon agogo taga karfe goma saura minti biyar, kallon kofar tayi da mamakin dalilin da yasa yake mata knocking by this time, can dai ta daure fuska tace "Waye wannan?" Taji yace "I could use ur help if u don't mind" Bluntly tace "I beg ur Pardon?" A takaice yace "Nayi misplacing makullina again" Da farko rasa ma me zata ce masa tayi don mamaki, she was mute for almost a minutes, taji yace "Hello" Sosai ta hade rai tace "I don't understand kayi misplacing makullin ka?" Yace "Look, ni fita zan yi yanzu idan na fita sai ki kulle gidan" Bata san sanda tace "Idan fita zaka yi ka fita mana, me yasa zaka tambayeni makulli? ko makullinmu a hade yake?" Shiru yayi at first, sai kuma yace "Ta yaya zan fita nace maki ban ga makullin kofa ba" Tace "But our keys are separate isn't it?" Yace "Sai yanzu da kika fada na sani ai, fito ki bude min kofa zan fita" Wani bakin ciki taji ya tokareta, yace "I am waiting at the parlor" Bata tanka sa ba, can tayi tsaki ta sauka daga kan gadonta ta dau hijab ta sa, ta bude handbag dinta ta dau makullinta ta nufi kofar dakin, fuskarta a daure ta bude ta fito ta karasa living room ta gansa tsaye bakin kofar parlon yana jiranta, ko kallonsa bata yi ba kamar yanda shi ma din wayarsa yake dannawa bai kalli inda take ba, ta karasa ta bude kofar parlon da makullin hannunta tace "You weren't given a needle as key da zai dinga ɓata kullum, and i shouldn't be responsible always for someone else carelessness" Shi dai bai ce mata komai ba ya fita without looking at her yace "Na zata ai needle aka bani Housemate" Da ido ta bi sa har ya isa inda motarsa take, wato godiyar da zai mata kenan? Ta gyada kai ta kulle kofar parlon a ranta kuma tayi vow bazata sake masa amfani da makullinta ba sai dai kar ya fita, banda ma rainin hankali me yasa baya misplacing makullin motarsa sai na gida, next time sai dai ya fasa zuwa inda za shi don bazata sake sharing key dinta da shi ba, fuska daure ta koma cikin parlor, sai kuma ta tsaya tana kallon plate din da ya ci abinci ya bari a parlon da container din soft drink ga goran ruwa, tsabar mamaki bata san sanda ta nemi waje ta zauna ba, is this guy okay? After fetching her food without asking for permission he still have the mind to leave the plate for her at the parlor, anyway... she believe he didn't leave it for her, he left it for himself instead, don ko sati daya zai yi bai dawo gidan ba zai dawo ya tarar da plate din at that same spot don bazata daukesa ba, tashi tayi ta tafi daki fuskarta a daure. Da safe Khaleesat ta gama shirin fita makaranta, har a lkcn bata dauke plate din da ya bari a parlon ba, amma fa zuciyarta kawai ta kai nesa don ta tsani ganin abu ba inda ya kamata ba, zata kai cup din da ta sha shayi kitchen taji ta taka makulli a kan ash carpet din parlon, dukawa tayi ta dau makullin tana kallo taga nasa ne, he is just careless, tabe baki tayi ta mike ta ajiye makullin nan kan kujera, ta kalli plate din jiya da ya bari, tsaki tayi ta dauke tare da gwangwanin soft drink din da na ruwa, ta hada da cup din hannunta ta tafi kitchen, bayan ɗan lokaci ta dawo parlor ta dauki handbag dinta tana duba wayarta, ganin Lyft din da tayi order ya kusa isowa ta nufi kofa ta fita. Wajen karfe sha biyu Khaleesat na zaune tare da Safiyyah warce shigowarta makarantar kenan, Khaleesat na kallonta tace "Kun sha birthday" Safiyyah tace "Oho dai tunda ke baki je ba, yau me ku ka yi a aji?" Khaleesat tace "Nothing much" Safiyyah ta bude handbag dinta ta ciro cake tana mika ma Khaleesat tace "Gashi ba don halin ki ba" Khaleesat tayi murmushi ta amsa tace "Nagode" Safiyyah tace "Kun yi waya da Abdallan ne?" Khaleesat ta sauke idonta a hankali tace "Sophie me kika ce masa ta chat?" Safiyyah ta dau wayarta tayi unlocking cikin few seconds ta shiga DM din Abdul sannan ta mika ma Khaleesat wayar, Khaleesat ta amsa tana duba chat din, it was nothing worth taking personal Safiyyah ta gaya masa a chat din, Khaleesat dai tayi shiru bata ce komai ba tana kallon wayar hannunta, Safiyyah tace "Me yace maki halan?" Khaleesat ta mika mata wayarta tace "Nothing, kawai yace min kin masa magana" Safiyyah ta tabe baki tace "Kin dai ga yanda yake amsa min chat din ma kamar wani ɗan sarki, wallahi Abdallah bai yi deserving dinki ba, u are too good to be Abdul's or to end up with him, Allah ya maki sauyi cikin ruwan sanyi ya kawo maki mafita" a hankali Khaleesat tace "Ki tashi mu je aji" Safiyyah tace "Oh baza ki ce Ameen ba??" Murmushi Khaleesat tayi tace "Wani mafita kenan Safiyyah? Cewa zaki yi Allah ya canza min halayyarsa kawai...." Safiyyah ta tabe baki ta mike tace "Mu je" Khaleesat ta mike suka bar wajen a tare... Khaleesat na sauka Uber din da ya dawo da ita gida ta nufi apartment dinta, dai dai sanda Co-tenant dinta ya fito daga cikin motarsa dake inda aka tanadar domin parking, sau daya ta kallesa ta dauke kai tana ci gaba da tafiyarta toward their apartment, ya bi bayanta yace "I've waited all day long, i forgot some paperwork a cikin gidan gashi zanyi Submitting tun daxu" Ba tare da ta juyo ba tana ci gaba da tafiya tace "Serves you right" Kallonta yake yana biye da ita, ta ciro makulli a jakarta ta bude kofar ta zare makullinta sannan tayi shigewarta ciki ta nufi dakinta da makullin... Bayan Khaleesat ta idar da sallah ta sauya kaya ta fito parlor don daura girki, bata gansa a parlon ba, kuma bata ji alamar ya shiga dakinsa ba, ta nufi tagar living room din tana leka parking space, ganin babu motarsa ta karasa gun kofa ta murda taji a kulle, kallon inda ta ajiye makullinsa daxu da safe tayi taga ya gani har ya dauke, wucewarta tayi zuwa kitchen. Wajen karfe tara na dare Khaleesat ta gama karatun da take ta jawo wayarta ta bude WhatsApp dinta don ganin ko Neighbor dinsu Aunty Sha'awa tayi replying sakon da ta tura mata amma sai taga bata yi reply ba har sannan kuma ta bude message din, ajiye wayar tayi ta mike ta dauke darduman da take zaune kai, ta dau hijab ta saka sannan ta fito parlor zata debi abinci, Zaune taga House mate dinta a parlon yana operating laptop dinsa, without looking at him ta tafi kitchen, after some minutes ta fito, ya daga kai yana dubanta yace "Can i have some of ur food if you don't mind?" Mamaki ma ya bata, har da baza ta tanka sa ba sai kuma ta tsaya tace "Duk na baya da kake diba gaya min kake halan?" Ya ɗan buda ido yana gyada kai yace "Haka ne kuma fa, i just decided to ask politely today" Bata sake bi ta kansa ba tayi tafiyar ta daki, in har sai tace ya diba to ashe bazai ci ba. Washegari da safe Khaleesat na kitchen tana ma kanta snacks da zata kai school don har yamma suke da Lecture gashi suna da er jarabawan da za su yi ranan da safen, Housemate dinta ne ya shigo parlon, tun jiya da daddare da ya fita sai a sannan ya dawo gidan, har zai tafi dakinsa sai kuma ya tsaya yana kallon Handbag dinta da makulli dake ajiye gefen jakar, karasawa yayi ya dau makullin sannan ya juya ya fice daga parlon gaba daya closing the door gently ya kulle da key, Khaleesat tafi minti sha biyar tana duba makullinta bayan ta fito daga kitchen, tun daga dakinta har parlor zuwa kitchen babu inda bata duba ba amma bata ga alamar makullin ba, she can't even tell ko ta fito da shi parlor, she was so confuse gashi tayi latti, daki ta koma sai da ta birkice ko ina amma babu alamar makullin, how comes will her keys disappear just like that, tunda ta fara karatu a kasar bata taɓa misplacing makulli ba banda wani lkci da Safiyyah ta yar mata guda daya, ko gyara dakin da ta birkita bata yi ba ta dawo parlor looking so frustrated, tsaye tayi trying to calm her brain ko Allah zai sa ta tuna inda ta ajiye keys din, ta ɗaga kai da sauri tana kallon kofar parlon jin ana budewa, House mate dinta ne ya shigo living room din da wasu takardu a hannunsa, sai da ya kulle kofar ya zare makullinsa sannan ya karasa cikin living room din ya ajiye takardunsa kan kujera without looking at her yace "Good morning Housemate...." Bai tsaya yaji amsarta ba yayi wucewarsa daki yana cire jacket din jikinsa, Khaleesat ta bi sa da kallo har ya shige daki ya kulle, zaunawa tayi gefen kujera ta dafe kanta da taji har ya fara ciwo, yanzu ina ta jefar da mukullin nan for God sake gashi lokaci na ta wucewa, after few minutes sai gashi ya sake dawowa parlon, har sannan bai yarda ya kalli direction dinta ba, taga yayi wucewarsa kitchen ya fito rike da ruwan gora ya sake komawa dakinsa ya kulle, wayarta dake jaka ne ya fara ring ta bude jakar ta ciro wayar taga Safiyyah ce, dagawa tayi ta kai kunne Safiyyah tace "Ya baki shigo schl ba har yanzu, duk latti na yau na riga ki shigowa makaranta, ko kin manta muna da test ne" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "Ina sane Safiyyah" Safiyyah tace "Na fa ce akwai tutorial da zaki min kafin mu shiga test din" a hankali Khaleesat tace "Zan taho yanzu" Safiyyah tace "Don Allah ki taho, wallahi ba abinda na sani a course din kema kin sani" Khaleesat ta ajiye wayar bayan Safiyyah ta katse, agogon wayarta ta kafa ma ido, bayan wasu yan mintuna ta mike after gathering courage to do what her mind is telling her, walking slowly ta nufi dakinsa, tsaye tayi tana facing kofar, a hankali ta kai hannu kofar tayi knocking tana turo baki, Yana jin knocking din ya kalli kofarsa, gyada kai yayi letting out a grin, sai da ta sake knocking din sannan yace "Waye wannan?" Exactly yanda take yawan fada, Shiru tayi bata ce komai ba ta kara turo baki, ya mike ya tafi gun kofar ya bude yana kallonta daga sama har kasa da alamar mamaki, tuni ta kauda kai, still keeping a surprise face yace "Madam hope nothing??" Trying to sound a little polite tace "I need you to open the door for me" ya gyara tsayuwa yace "I don't understand, dama a hade makullinmu suke? Where is ur key?" A takaice tace "It's fine, no long talk" Juyawa tayi zata bar wajen, yace "Ko baki ga naki bane?" Ta wani kallesa tace "Banda haka ai da ban zo nan nace ka bude min kofa ba" Yace "Ohh i see, does this mean u are careless too?" Barin wajen tayi ta koma parlor ta zauna, ya gyada kai with smile of satisfaction sannan ya koma daki ya dauko makullinsa ya fito, sai da ya shigo parlon yace "Ta yaya ma zaki yi misplacing a whole bunch of key sai kace allura, this is kind of weird" Daukar handbag dinta tayi ta nufi kofar yana budewa ta fice daga parlon tayi wucewarta without turning her back, ya gyada kai yace "Zaki dawo ai, zan ga ta inda zaki shigo gidan" Kulle kofar parlon yayi still smiling, ko ba komai ya rama abinda ta masa jiya. Safiyyah na kallon Khaleesat tace "To ko ya shige cikin Couch ne makullin?" Khaleesat tace "Ta yaya zai shiga kujera?" Safiyyah tace "Kuma har kitchen din kin duba?" Khaleesat tace "Babu inda ban duba ba fa" Safiyyah tace "Toh kawai kiyi ma agent din gidan magana su baki wani makullin mana" Khaleesat tace "Gani nake kamar dogon process ne hakan, kuma ai biyu ne makullin kika yar min da daya shine na dauko spare key din nake using, to shima gashi ban gansa ba yanzu" Safiyyah tace "Kar ki wani damu kanki, makullin na nan zaki gansa, kawai kin mance inda kika jefar ne, amma definitely it's either in ur room ko kuma parlor, yanzu jira zaki yi sai sanda housemate dinki ya dawo ki koma gidan kenan?" Khaleesat tace "Wani housemate? Shi da ba kwana ma yake a gidan ba, kuma ba shi da exact time da yake zuwa" Safiyyah tace "Kai haba, to a ina yake kwana?" Khaleesat ta zaro ido tace "Kin ji ki da wani tambaya, ta yaya ni kuma zan sani? what is my business with him da zan san inda yake kwana" Safiyyah tace "To kawai mu je gidanmu ki kwana" Khaleesat tace "Kina ganin babu matsala hakan?" Safiyyah tace "Wani irin matsala? To gidanta ne ko na ubanta da za a samu matsala? ta shi mu tafi jare" Safiyyah na gaba Khaleesat na biye da ita a baya suka shigo parlor da sallama, Surayya matar cousin brother din Safiyyah dake zaune parlorn ta daga kai tana kallonsu, Safiyyah tace "Sannu da gida Mom Aslam" Surayya ta ci gaba da danna wayar hannunta tace "Yauwa" Khaleesat ta zauna kan kujera ta gaisheta, Surayya ta amsa without looking at her tana danna wayarta, Safiyyah tace "Ai kin ganeta Mom Aslam, kawata ce kuma Coursemate dita Khaleesat" Surayya tace "Ohk" Safiyyah tace "She will be passing the night here, makullinta ne ya ɓata" Surayya ta daga wayarta da ya fara ring ta kai kunne hade da amsa sallama ta mike ta bar masu parlon, Safiyyah ta kalli Khaleesat tace "Tashi mu je ciki" Mikewa Khaleesat tayi ta bi bayan Safiyyah zuwa dakinta, Safiyyah na idar da sallah ta canza kayan jikinta tana kallon Khaleesat dake zaune saman darduma tace "Bari in samar mana abinda za mu ci a kitchen" Kai kawai Khaleesat ta gyada mata, Safiyyah ta fita daga dakin... Khaleesat was so uncomfortable a gidan cause it's a home that she is not welcome, ko daga irin tarban da aka mata tasan she isn't welcome, karatun da take ta yi na boko ne ke while din mata lokaci, Safiyyah kuwa tun da suka ci abinci take ta bacci har yanzu da magrib yayi, Khaleesat tayi alwala sannan ta fito ta tasheta, bayan sun idar da sallah Safiyyah tace "Bari in je in ga me waccan matar ta girka" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba tana ci gaba da azkar dinta, Safiyyah ta fita daga parlon, Surayya na parlor tana ba yaronta Cereal da ta hada masa, Safiyyah ta karasa parlon tace "Aslam yanzu ya tashi ne, ban gansa tun daxu ba" Surayya tace "Ehh" Safiyyah ta ɗan masa wasa sannan ta wuce kitchen, abinci ne iya cikinta taga Surayya ta ajiye mata a kitchen din, Safiyyah ta fi minti biyu tsaye kitchen din tana kallon abincin, can tayi kwafa ta dau plate ta juye ma Khaleesat kawai ita idan ya so ko cornflakes ne sai ta sha anjima, ta fito kitchen din kenan sai ga Cousin brother dinta ya shigo parlor, gaishesa tayi ta amshi ledan hannunsa yace "Leave it, kije ki ci abincin ki" Tace "Ai ba nawa bane ba ma, kawata zan kai ma, ni sai dai in sha cornflakes tunda abincin iya wannan ya rage" Surayya dai kallonta kawai take, Musty yace "Wace kawarki?" Safiyyah tace "Khaleesat, she lost her house key shine ta zo zata yi spending night din a nan" Musty yace "Oh Allah sarki, ba ayi abincin da yawa bane?" Safiyyah ta karkace masa plate din sosai tana nuna masa tace "Iyakarsa kenan aka bari a kitchen, tun da rana muka dawo kuma" Musty yace "Ohk, me ku ke son ci let me get it yanzu a restaurant" Safiyyah ta ɗan yi murmushi ta ajiye plate din saman center table kusa da Surayya tace "Bari in tambayi Khaleesar abinda zata ci" Surayya ta bi ta da wani kallo har ta shige daki, Safiyyah na shiga dakin tace "Khaleesat ki fito ku gaisa da yaya Musty nace masa kina nan" Khaleesat ta daga kai ta kalleta tace "Is it necessary Safiyyah?" Safiyyah tace "Ban gane is it necessary ba, yayana ne fa, kuma nace masa kina nan, ai ya kamata ki gaishesa dai ko" Khaleesat tayi shiru, can ta mike suka fito daga dakin tare, tana tsaye daga jikin kujera ta gaida Musty ba tare da ta kallesa sun hada ido ba, ya amsa da fara'a yana kallonta, Surayya dai fuskarta babu yabo babu fallasa take tura ma yaronta Cereal a hanci maimakon baki ba tare da ta sani ba, Khaleesat ce kadai ta lura da hakan, Safiyyah na murmushi ta kalli Khaleesat tace "Wai yaya yace me za mu ci zai fita yanzu ya siyo mana" Khaleesat taki cewa komai, Safiyyah tayi fari da ido ta fara lissafo masa abubuwan da zai siyo masu, Surayya ta ajiye bowl din Cereal din hannunta kan Centre table ta ciro Aslam daga kekensa tace "Mu je in maka wanka Aslam" Daga haka ta bar parlon tayi wucewarta daki, Khaleesat dai ta sunkuyar da kanta, Muryar Musty da taji yana mata magana yasa ta daga kai ta kallesa, yace "Su kenan iya abinda Safiyyah ta lissafo za a siyo maku Khaleesah?" Kai kawai Khaleesat ta gyada masa, bayan nan ta juya ta koma dakin Safiyyah jiki a sanyaye. 07087865788✍🏻 [20/05, 11:38 pm] +234 813 644 0264: ✨✨ HALYSAAH ✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 4..... Khaleesat ta zauna gefen gadon dakin Safiyyah duk jikinta a sanyaye, jawo wayarta tayi tana duba agogo taga karfe bakwai har da rabi, sam bata ji zata iya kwana gidan nan ba, tasan probably yanzu House mate dinta na gida, to ya ta iya? Hakan dai zata koma gidan tayi masa knocking, the thought of this made her weak, shigowar Safiyyah dakin yasa ta daga kai, Safiyyah ta rike haɓa tace "Kinsan kuwa shegiyar matar nan bata ajiye mana abinci ba, ai ko sai ga yaya Musty kamar an jefosa kuma night shift fa yake yi wallahi, kinga ko ba komai sai ta hadiyi zuciya ta mutu don bakin ciki yau, abincin da na lissafo masa ko rabinsa baza mu iya ci ba kuma kwalelenta sai dai in har shi yayi dubaran siyo mata nata daban, ban taɓa ganin me tsinannen hali kamar matar nan ba tirr, ni ai na zata in mutum zai taho wata kasar barin baƙin halinsa yake a gida, to ita dai da nata ta taho wallahi" Khaleesat tayi murmushin karfin hali tace "Lallai kam, kinga ni kuma tafiya zan yi fa, da ma bai siyo abincin ba, yanzu Housemate dina ya kirani yace he is back home" Safiyyah ta bude baki da mamaki tana kallonta, can tace "Ban gane ba, yaushe kika samu number Housemate dinki har ya kira ki? Wallahi ban yarda ba kawai so kike ki tafi, bari ki ji in dai don Surayya ce nima fa zaman hakuri nake da ita a gidan nan Khaleesat, mugun halinta bai da part 2, gwara kawai kiyi zamanki in ma shekara zaki yi a nan babu yanda ta iya tunda ba gidan ubanta bane kuma warmly Ya Musty zai yi welcoming din ki" Khaleesat tace "Sophie ni fa tunda Housemate dina ya dawo bazan kwana a gidan nan ba, dama bani da kayan da zan canza sannan na ma manta na bar kaya a washing machine kin ga bani kadai bace a gidan, may be zai yi laundry shi ma" Safiyyah ta hade rai tace "A takaice me kike nufi kenan? Kina ji ina lissafa ma Ya Mustapha abinda zai siyo mana don walakanci ki ce ke zaki tafi? shima ai bazai ji dadi ba idan ya dawo da abincin yaga kin tafi kuma saboda ke ya fita ya siyo don in dan ta nice sai dai yunwan ya kasheni in bai ga dama ba" Khaleesat ta ɗan yi murmushi tace "Zan jira ya dawo, sai in tafi da abincin gida kawai" Safiyyah da har ranta ya ɓaci tayi mata banza ta tafi ta dau wayarta tana dannawa, Khaleesat dai bata sake cewa komai ba, komin fushin Safiyyah ita kam baza ta kwana gidan nan ba, after a while Ya Mustapha ya dawo gidan da abincin da ya siyo masu, Safiyyah ta mike ta nufi kofa bayan ya kirata a waya, Khaleesat ta bi ta da kallo har ta fita sannan tayi murmushi, Safiyyah ta karasa dinning table ta dau abincin da Cousin din nata ya ajiye masu ta koma daki, iya wanda zata ci ta cire ta bar ma Khaleesat duk abincin, Khaleesat tace "Ya zanyi da abincin nan me yawa Sophie?" Ba tare da Safiyyah ta kalleta ba tace "Wannan kuma ke kika sani" Khaleesat bata son jan maganar yayi tsayi kawai ta mike ta dau veil dinta da handbag sannan ta dau ledan abincin tace "Sai mun hadu gobe, thank you so much dear" Safiyyah tace "Kinyi order din ride ne?" Khaleesat tace "Sure" Mikewa Safiyyah tayi suka fito dakin a tare, dai dai fitowar Mustapha parlor shi ma, yana kallonsu da mamaki yace "Ya aka yi kuma?" Safiyyah ta langwabar da kai tace "Her Housemate is back, shine kawai zata tafi gida wai" Yace "Isn't it late?" Safiyyah ta kyabe baki tace "Nima dai haka nace mata" Ya kalli Khaleesat da ta sunkuyar da kanta, yace "Kiyi hakuri ki bari gobe mana Khaleesah, yanzu ai dare yayi...." Khaleesat ta ɗan yi murmushi ta dago kai cikin sanyin murya tace "Akwai abinda nake son zan yi ne idan na koma gida" Mustapha ya daga kafada yace "While, if you insist...." Ta gyada masa kai tace "Nagode" Safiyyah ta wani harare ta, Mustapha yace "Zan koma aiki ne dama, mu je sai inyi dropping din ki ko" Khaleesat bata yi expecting offer din nasa ba, ta ɗan kallesa tace "Na riga nayi order din Lyft ai...." Safiyyah ta mata wani kallo tace "Haka kuma you can cancel it ai ko...." Kasa cewa komai Khaleesat tayi, lkci daya ta zama uncomfortable, Mustapha dai kallonta kawai yake, after few seconds a hankali tace "Ohk" in response to Safiyyah, Kofa Mustapha ya nufa, Safiyyah tayi kasa da murya tana kallonta tace "Ke in zaki saki jiki ki saki jiki, a ko da yaushe sai kin nuna ke er.... Ya ma sunan wannan unguwan naku a kano?" Khaleesat ta dinga kallonta, can ta juya ta nufi kofa tana tafiya slowly, Safiyyah ta fara dariya kasa kasa tace "Good night girlfriend" Ko tankata Khaleesat bata yi ba. Yana zaune cikin motarsa yana jiranta har ta karaso, ta bude gaban motar ta shiga, sai kallon entrance din gidan take tana fatan kar matarsa ta fito ta gansu, ya tada motar suka bar garage din, sai a sannan ta sauke boyayyen ajiyar zuciya tayi fastening seat belt dinta a ranta ta dau alwashin wannan shine zuwanta na karshe gidansu Safiyyah, bayan sun hau saman hanya taji yace "Where do u stay?" Idonta na kan titi ta gaya masa, yace "Co-living kike yi kenan?" Tace "Um" Yace "Menene yasa baki dawo ku zauna gidana tare da Safiyyah ba instead of living alone with a stranger?" Ko rufe baki bai yi ba tace "Ai yawanci ni kadai ce a gidan, my Housemate is not always around" Yace "Ok then" After almost a minute yace "Kema er kano ce?" Tace "Um" Yace "Wani anguwa?" Tayi shiru, sai kuma ta ɗan kallesa ta gefen ido taga kallonta yake at the same time yana tuki, ta sauke idonta kasa ta gaya masa, she is so uncomfortable with him, Yana gyada kai yace "Ohk, i am also from kano, Sharada to be precise" Ita dai tayi shiru bata ce komai ba, cikin minti 13 ya kawota gida, ya juya yana kallonta bayan yayi parking, daukar ledan abincin tayi tace "Nagode sosai, Allah ya saka da alkhairi" Wayarsa taga ya mika mata, ta daga kai ta kallesa, yace "Ki sa min digit dinki sai mu dinga gaisawa, in kina bukatar wani abu kuma feel free to ask me anytime" Khaleesat ta sauke idonta, ita da ta sani babu abinda zai kai ta gidansa yau, da kawai dawowarta tayi ta zauna bakin apartment dinta ta jira har sanda Housemate dinta ya ga daman dawowa ya bude mata kofa, muryarsa ya dawo da ita duniyar tunanin da ta tafi ta daga kai da sauri ta kallesa, bata ma san me yace ba taga dae yana kallonta, da kyar tayi stretching hannu ta amshi wayar ta sa masa digit din nata, yayi dialing, ita dai kanta na kasa, wayarta dake cikin jaka ya fara vibrate, yace "Kiyi saving nawa digit din" Tace "Um" Yace "Good night, take care Khaleesah" Tayi karfin halin cewa "Nagode" Daga haka ta bude motar ta sauka, kallon window din kitchen na apartment dinta tayi ganin wuta a kunne, sannan taga mota a Garage, she felt relieved sanin cewar her Housemate is around, ta zaga zuwa gaban apartment din tana jin sanyi na shigarta sosai don sanyi ya fara shigowa kasar, knocking din kofar parlor tayi gently, sai da ta kwankwasa sau uku sannan taji muryarsa yace "Who is there?" Ta kauda kai a takaice tace "Somebody" Yace "Somebody? I am not expecting somebody this late" Ta wani hade rai tace "Ni ka bude min kofa in shiga gida" Yace "Ke wa zan bude ma kofa?" Kin cewa komai tayi cause she is already provoke, yace "Ohk then, i am going back to my room after all i am not a door keeper" Tana jin haka a fusace tace "Don Allah ka bude min" Yace "Ke wa?" Tace "Ban gane ni wa ba?" Yace "Ohh, tsawa ma kike min?" Ta kara marairaicewa tace "Don Allah ka bude mana" Yace "To ai ni ban san wacece ba, baki da suna ne?" Shiru tayi tana kallon kofar kamar zata fashe da kuka, Yace "Ke zan fa yi tafiyata daki in baza ki fadi sunanki in san wa zan bude ma kofata ba cikin daren nan" Ta sauke idonta kasa, after a few seconds ta dake tace "Khaleesat" Yace "Halysaah..." Wani harara ta zabga ma kofar, Kamar yana counting harufan sunan yace "Ha.. lee...saah" A fusace kamar zata yi kuka tace "Sanyi fa nake ji ka ki bude min kofa, ko don ba kai bane tsaye cikin sanyin?" Bude kofar yayi yace "Baki san da sanyin ba kika je kika yi dare a titi?" Ko kallonsa bata yi ba ta kusa bangajesa ta shige parlon fuskarta a murtuke, yace "Wajen saurayinki kika tafi kenan kika yi dare, naga ma shi ya ajiye ki a mota, Allah sa ba me sa ki kukan nan bane dai" Direct dakinta ta nufa without even looking at him abinda ya fada na sinking zuwa cikin kanta, ya bi ta da kallo yace "Ok.... ga Door keeper dinki ya bude maki kofa ko? Tomorrow is another day, better look for ur lost key in ba so kike ki kwana a waje ba next time" Tuni ta bude kofar dakinta tayi shigewarta ta sa makulli tare da jan dogon tsaki. Da safe tunda Khaleesat ta tashi take zaune tana tunanin how today will be like, taje schl din ne ko ta hakura kawai tunda bata da makulli yanzu, zaro ido tayi bayan ta tuna lecture din da za su yi ranan, she just can't miss that class don course din is a bit complicated, mikewa tayi ta shiga bandaki, wajen karfe tara ta fito parlor hoping house mate dinta bai fita ba, don jiya wajen karfe sha biyu da rabi na dare ta fito don saka abincin da bata iya ta ci ba a fridge ta gansa kwance a parlor yana bacci, har ta gama abinda zata yi a kitchen ta fito bai farka ba, tun zuwansa gidan ranan ne rana na biyu da taga ya kwana a gidan, babu kowa parlorn ta karasa kusa da tagan parlon tana leka Garage ko zata ga motarsa taga motar na nan alamar he is around, ajiyar zuciya ta sauke don da ya fita shkkn babu tafiyarta makaranta kenan, kitchen ta tafi ta hado shayi ta debi cookies ta dawo parlon, har ta gama breakfast bai fito parlor ba, sai kallon agogo take don goma ta kusa gashi bata son tayi latti, kuma ita dai bazata taɓa masa maganar ya bude mata kofa zata fita ba, goma saura minti goma ya fito parlorn, ita dai bata dago kanta ba tana ci gaba da danna wayarta, taji yace "Good Morning, Halysaah" Without looking at him tana ci gaba da danna wayarta kamar tana ma kanta magana tace "Ok" Ta gefen ido ta bi sa da kallo ganin ya nufi kofa ta mike ta bi bayansa, yana lura da ta biyosa sai ya fasa bude kofar, ya juya yana kallonta keeping a serious face yace "Me ya faru?" Ta kauda kai taki cewa komai, mayar da makullin yayi aljihunsa zai bar wajen ta wani kallesa tace "Ni dai ka bude min kofa zan tafi makaranta" Yana gyada kai yace "Ohhh, ohk kin boye makullinki ne don in zama door keeper dinki dama?" Taki kallonsa don bata ma san me zata ce masa ba, ganin da gaske barin wajen zai yi ta marairaice tace "Makaranta zan tafi fa" Ya juyo yace "Be a good girl and beg politely first....." Shiru tayi tana bin sa da kallo har ya koma cikin parlor ya zauna kan kujera, Ta dake da kyar tace "Please ka bude min. i am going to school" Yace "Ban ji ba" Takaici yasa ta dauke kai taji ranta ya kara ɓaci, ganin lokacinta kawai take ɓatawa ta sake juyowa trying to be calm tace "Plss ka bude min kofa i am going to school" Ɗan murmushi yayi ya mike ya dawo bakin kofar ya ciro makullin a aljihunsa yace "Never knew u can be this Obedient" Ita dai bata kallesa ba, ya bude kofar yace "In kika sake yin dare baza ki shigo gidan nan ba sai dai ki kwana bakin ƙofa ko kuma a Garage..." Bata tankasa ba ta fice daga parlon with annoyance almost brushing his shoulders, ya bude baki yana bin ta da kallon mamaki yace "Ohh, is this ur thank you??" Tuni har ta kusa titi abun ta, ta ja tsaki feeling so fed up with him. Bayan Khaleesat sun fito daga aji Safiyyah tace "Kinsan me Khalee?" Khaleesat ta juya ta kalleta, Safiyyah tayi dariya har da kyakyatawa tace "Wai Ya Musty ke tambayata ko kina da saurayi" Sai da gaban Khaleesat ya fadi, Safiyya bata fasa dariyar da take ba tace "Wallahi kuwa, he chatted me up yesternight wajen karfe sha biyu, bari ma in nuna maki ki ga, ni ko nace masa baki da kowa wallahi" Sai a sannan Khaleesat ta kalleta tace "Ban gane bani da kowa ba Sophie?" Safiyyah tace "To kina da shi ne? To in kallon saurayinki kike ma Abdul to ni wallahi kallon ɗan daba nake masa, ni dai nace ma Ya Musty bakya kula kowa saboda karatu don haka baki da saurayi, kema kin dai san da Ya Musty na da mugun hali da tuni na fesa maki ni da bakina baya shiru, ai ko don wannan er banzar matar tasa zan so ya kara aure, kuma ace kawata ya aura huhuhu za a ga rashin nasiha da jahilci wajena" Khaleesat ta mike tana gyara Veil din jikinta tace "Zan tafi gida sai gobe" Safiyyah ta tsuke fuska tace "Ban gane zaki tafi gida ba daga na kawo maki maganar arziki" Khaleesat tace "Wallahi da na sani babu abinda zai sa in bi ki gida jiya Safiyyah, haba fisabilillah, put ur self in the wife's shoe in kece aka ma haka zaki ji dadi?" Safiyyah tace "Godforbid, her shoes will never size me sef kafin in sa kafata ciki Khaleesat, ai ni bani da mugun hali kamar ta, kina ga fa ko tsayawa ta amsa gaisuwarki bata yi ba ta wani ƙara waya a kunne ta wuce daki ita er iska, sannan bari kiji jiya iya cikina ta ajiye abinci a kitchen bayan nace mata nan zaki kwana kuma ta sani, ni dai wallahi in kika ce baki son yayana nice kawai baki so, Ya Musty bai da wani aibu wallahi, ga arziki ga Ilimi ga kyau, baza ma ki ce ya taɓa auren wata er iska ba wai ita Surayya, ɗan saurayi da shi" Khaleesat tace "In matarsa kike son tura ma haushi ai kema zaki iya aurensa tunda he is ur cousin brother kuma da aure tsakanin ku" Daga haka Khaleesat ta bar wajen tayi wucewarta, Safiyyah tace "Oho dai wallahi ce masa zan yi kin amince sai dai ki mutu, haka kawai kin makala ma kanki ɗan daba kina kiransa da wanda zaki aura, ki auresa ki ci uwar me da shi, wannan har duka sai ya dinga nakada maki babu me kwatarki in ku ka yi aure" Khaleesat na isa gida taga babu motar Housemate dinta a parking space, jingina tayi jikin entrance din apartment din nasu, gashi ta gaji sosai ga yunwar da take ji, babu wanda ta saba da shi a Neighborhood din balle ta shiga gidansa, balle su turawa basu yarda da hakan ba ma, ta kusa twenty minute a tsaye sai ga motarsa ta hango, sunkuyar da kanta tayi har yayi parking ya karaso kofar entrance din, gefe ta koma without looking at him, tun kan ya karaso kofar apartment din ya sa hannu a aljihunsa yaji babu makullin, ya ɗan bude ido still yana laluba duk aljihunsa, sai a sannan ta daga kai tana kallonsa, juyawa yayi ya koma motarsa ta bi sa da ido, ya gama dube dubensa a motar bai ga makullin ba, ai tana ganin yanda yake dube dube tasan kilan ya yar da makullin, shikenan ta shiga uku, she is soo tired, har wani jiri take ji a tsayen da take, dawowa yayi yana kallonta yace "Look Halysaah, i think i left the key at where i am coming from" Ita dai bata ce komai ba kuma bata bari ta hada ido da shi ba, yace "Ko zaki shiga apartment din Neighbor dinmu kafin in dawo" Sunkuyar da kanta tayi still keeping mute, yace "Or ain't you familiar with them?" A takaice tace "Eh" Yace "Ok i will be back as soon as possible" Juyawa yayi ya koma gun motarsa ta bi sa da wani kallo.... Khaleesat na ta tsaye har bayan wani minti sha biyar sai gashi ya dawo, yana kallonta yace "Allah ya taimake ki na gani" Wani kallo tayi masa wato ita Allah ya taimaka ma, yana bude kofar tayi shigewarta ciki ta nufi dakinta ba tare da ta juya ba, sai da ta kwanta na kusan minti sha biyar sannan ta mike a hankali ta shiga bandakinta, bayan Khaleesat tayi wanka tayi sallah tana zaune kan darduma taji yayi knocking kofar dakinta, kallon kofar take bata ce komai ba kuma bata amsa ba balle ta tashi, taji yace "Halysaah" Bluntly tace "Me ya faru?" Jin ya murda kofar dakin ta zaro ido ta mike tsaye da sauri tace "What?" Tuni ta isa gun kofar ta bude tana masa kallon tuhuma, ledan hannunsa ya ajiye mata yace "I got you food, naga kin yi laushi" Ta kalli ledan, ya juya ya bar wajen ta bi sa da kallo har ya koma parlor, sauke idonta tayi, bayan few seconds ta duka ta dau ledan ta juya ta koma dakin. Khaleesat ta bude abincin da ya kawo mata ta fara ci kenan wayarta ya fara vibrate, mikewa tayi ta bude handbag dinta ta ciro wayar, sosai gabanta ya fadi ganin Abdul ke kiran ta, zaunawa tayi gefen gado tana kallon screen din wayar har sannan gabanta na bugawa, kafin kiran ya katse tayi karfin halin dagawa ta sa handsfree sannan tayi sallama cikin sanyin murya, maimakon ya amsa sai ji tayi yace "Wato all this While ni kike jira in kiraki ko Khaleesat?" Ta sauke idonta a hankali tace "To ai cewa kayi duk sanda kake son magana da ni zaka kirani amma kar in sake in kira ka" Yace "Don nace kar ki kirani sai ki ki kiran nawa? Me yasa baki reason ne?" A sanyaye tace "Kayi hakuri" Yace "In ban hakura ba ya zan yi da ke? Ai saboda baki damu da ni bane yasa kika zama comfortable without calling me all this while, ko da bazan daga ba ai kamata yayi ki kira" Cikin sanyin murya tace "Kayi hakuri" Yace "Yaushe za ku fara jarabawa?" Tace "Probably nan da 6 to 7 weeks" Yace "I can't wait har zuwa nan da sati bakwai ban gan ki ba Khaleesat, idan na samu lokaci zan shigo anytime from now in sha Allah" Shiru Khaleesat tayi as if trying to process what he just said, yace "Hello" Da sauri ta kifta ido tace "Na'am ina ji" Yace "Me yasa kika yi shiru? Ko baki son in zo ne?" Tayi yake tace "Aa ban yi shiru ba network ne, ban ji me kace ba" Yace "Ohk, nace you should expect me any moment from now" A hankali tace "Toh Allah ya kai mu" Yace "Ameen, me kike yi yanzu?" Tace "Abinci nake ci" Yace "Ohk switch to video call" A hankali tace "Toh" Mayafinta ta jawo sannan tayi yanda yace mata. 07087865788 for more info✍🏻 ✨✨ HALYSAAH ✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 5...... Wajen karfe biyar na yamma Khaleesat ta fito parlor daga dakinta, window ta nufa tana leka garage ta ga motar Housemate dinta alamar yana gidan, juyawa tayi ta tafi kitchen zata yi disposing takeaway din da yayi mata daxu, ta window din kitchen din ta hangosa zaune a Lawn din dake bayan kitchen din waya ƙare a kunnensa alamar he is making a phone call, komawa baya tayi don kar ya hangota ta window din kitchen din, ta ajiye ledan hannunta a hankali ta juya ta fita daga kitchen din ta dawo parlor, tsaye tayi tana kallon handle na kofar living room din, sai kuma ta tafi gun da ya ajiye takardun karatunsa ta hau bincika Books din da sauri, har ta gama dube dubenta bata ga abinda take nema ba, ta koma kitchen din tana kara lekansa, seeing he is still on call ta dawo da sauri ta tafi corridor din dakunansu, tsaye tayi gabanta na faduwa as if contemplating on whether to do what is on her mind or just forget it, ganin she is just wasting time ta runtse idonta ta bude, sai kuma ta kai hannu handle din kofar dakinsa a hankali ta bude ta shiga ciki zuciyarta na bugawa, bin dakin that was neat and tidy ta fara yi da kallo kafin ta karasa can ciki da sauri, har sannan tana kallon ko ina na dakin, ta ma rasa daga inda zata fara duba abinda ta shigo nema, zagaye dakin ta fara yi tana dube dube with confusion, daya wayarsa dake gefen gado yayi haske alamar shigowar sako, kallon screen din wayar take yi ganin wani matashi kamarsa a shekaru ne a fuskar wayar, ta juya ta kalli Trouser dinsa, gabanta na faduwa ta dauka ta kai hannu aljihun wandon, Dollar ta ciro masu yawa tayi saurin ajiyesu gefen gado, sannan ta duba daya aljihun, zaro ido tayi jin makulli da Counter a ciki, ta ciro da sauri tana kallon makullin taga makullin kofar parlor ne, bata san sanda tayi murmushi ba ta ajiye wandon a inda ta dauka sannan ta juya da sauri, ƙamewa tayi a spot din da take ganinsa tsaye bakin kofar dakin ya rungume hannu yana kallonta daga sama har kasa, kawai ta juya masa baya zuciyarta na bugawa taji kamar ƙasa ya bude ta shige ta huta, after some seconds taji yace "Sannu da aiki" Ita dai ta kasa juyowa, she felt so ashame at that moment, she wish this never happened, sai juya makullin hannunta take with shame, Calmly yace "Give me the key" Ta wani turo baki taki juyowa tace "To ba amfani zan yi da shi ba" Yace "Dama in bana nan bincike kike shigowa ki min a daki?" Bata san sanda ta juyo tana kallonsa babu ko kiftawa ba jin abinda yace, sai kuma ta ajiye makullin a gefen gado ta nufi kofa ta bi gefensa ta fice daga dakin ta shiga nata ta tura kofar, nan da nan taji hawaye ya cika idonta ta zauna gefen gado, sai kuma ta ɗora kanta saman pillow hawaye na sauka idonta har da shessheka. Karfe bakwai da few minutes Khaleesat na zaune kan darduma, tun da ta idar da sallah take zaune wajen, da ta tuna abinda Housemate din nata yace mata sai taji hawaye ya cika idonta, gaba daya taji ta tsani zaman gidan, kuma bata jin zata iya ci gaba da zama as far as he is here, ta yanke shawaran kawai zata gaya ma Abdul ya canza mata gida kamar yanda Safiyyah ta bata shawara tun farko taki dauka, wayarta dake gefen gado ta dauka jin ana kira, tana dubawa taga Mustapha ne ke kiranta, ajiye wayar tayi gefenta taki dauka har ya katse, ya sake kira nan ma taki dagawa, bayan ɗan lokaci aka sake kiranta kallon wayar tayi a bit fed up thinking it's still Mustapha sai taga Abdul ne ke kiranta this time around, ta jawo wayar a hankali tayi picking ta kai kunne, sallama tayi masa sannan ta gaishesa, yace "Ya naji muryarki haka?" Tayi shiru tana tunanin ta inda zata fara sanar masa the situation at hand, muryarsa ya dawo da ita tunanin da take, a ɗan tsawace yace "Ke, baki ji na ne zaki min shiru?" Kasa gaya masa tayi don bata ma san yanda zai fara daukar lamarin ba barin yanda taki gaya masa tun farko, Ta ɗan yi yake tace "Ina jin ka, kawai muna da wani jarabawa ne gobe, kuma ina jin ciwon kai, and I haven't covered up, shi yasa nake damuwa" Yace "Na ce ki dena stressing kanki da karatu, u are not dull to be studying as if ur life depends on it, read a little and get enough rest, nasan za ki yi passing ko ma me za kuyi gobe" Tana murmushin karfin hali a hankali tace "To" Yace "Kin ci abinci ne?" Ta girgiza kai tace "Ban ci ba" yace "Ohk get something to eat, idan kin gama sai ki kirani ina jiran ki" Tace "Toh" Katse wayar yayi, ta bude WhatsApp dinta tana duba ko Neighbor dinsu ta mata reply taga ta hau WhatsApp din amma still bata yi reply ba, yau kwana uku kenan basu yi magana da Ummanta ba, Dialing din Number Sha'awa tayi ta direct call, har ya katse ba a daga ba, sai da ta sake kira aka daga, sallama Khaleesat tayi mata sannan ta gaisheta, Sha'awa ta amsa tace "Lafiya lau Khaleesah, ya karatu?" Khaleesat tace "Alhamdulillah ya gida ya su Kamilu?" Sha'awa tace "Duu lafiyansu lau wallahi" Khaleesat tace "Su Ummanmu suna lafiya..." Sha'awa tace "Kwana biyu kinyi magana ta wassap kinji shiru ko, to Ummanku dai bata da lafiya amma da sauki yanzu" Nan da nan Khaleesat taji hankalinta ya tashi don dama tun da taji shiru for days tasan ba lafiya ba, don ko bata yi ma Ummanta magana ba ita zata mata ta wayar Sha'awa taji ko tana lafiya, Hankalinta a tashe tace "Aunty Sha'awa tun yaushe?" Sha'awa tace "Ina jin yau kwana uku, ai an ma ce kar a gaya maki, shi yasa ko mayar maki da sakon da kika yi ta wassap din ma ban yi ba, yanzun ma kar ki wani ce zaki kira kowa kiyi ta mata addu'a kawai Allah ya bata lafiya" Khaleesat taji hawaye na sakko mata ta kasa cewa komai, Sha'awa tace "Wai daga ta tashi zata fito daki tayi alwalan magariba shi ne fa ta yanke jiki ta fadi a bakin kofar dakin, duk kwanan nan ina rabata da saka ma kanta damuwa tunda tasan matsalarta na hawan jini, to kinga ai irin haka ake gudu gashi kuma ya faru, Farida ma ta taho daga legas tun jiya ta iso, kar ki wani tada hankalinki don jikin da sauki" Cike da karfin hali Khaleesat tace "Suna asibiti ne yanzu?" Sha'awa tace "Wani asibiti? To har sai da Farida ta zo sannan ta kai ta asibiti jiya in gaya maki, amma duk kwanakin nan tana gida gashi ko taɓata kika yi a daya barin jikinta bata ji wai, ko magana ma in tayi sai kin sa kunne sosai zaki ji, ke abun fa ba kyau, har yanzu hankalinmu a tashe yake, an dai ce kar a gaya maki kar hankalinki ya tashi...." Khaleesat in hankalinta yayi dubu ya tashi a lkcn, ta kalli Screen din wayarta jin kiran ya katse alamar katin ta ya kare, ajiye wayar tayi ta fara rera kuka kamar an sanar mata da mutuwa... Har karfe goma na dare Khaleesat ta kasa tashi daga kan darduman da take, sosai ta shiga damuwa ba kadan ba, a inda take zaune Abdul ya kirata sau biyu amma ta kasa picking call din nasa, karfe goma da rabi taji anyi knocking kofar dakinta, ta juya ta kalli kofar tana share hawayen dake idonta amma bata tashi ba sai ma hade rai da tayi, after a while ya sake knocking still dai bata tanka ba, sai kuma taji yace "Assalamu alaikum" kawai ji tayi ya bude kofar dakin ta juya da sauri daga inda take zaune suka hada ido, daga nan bakin kofar ya tsaya yana kallonta, ita dai taki yarda ta sake hada ido da shi, ya karasa ciki ya tsaya still leaving enough distance between them, calmly yace "Maganar da na maki yasa kike kuka? But i was only pulling ur legs Halysaah, i am sorry about that, was just joking" Wasu hawaye suka cika idonta sai kuma ta fara kuka, bude ido yayi alamar mamaki sosai yana kallonta, can dai ya kwantar da murya yace "Look, do not take my words serious Halysaah ni wasa nake maki wallahi" Ta rufe fuskarta da Hijab din jikinta tana kuka a hankali, dukawa yayi da mamaki sosai yana kallonta ya ma kasa cewa komai, after few seconds da taji shiru ta ɗan bude fuskarta don tunaninta ya fita daga dakin, suna hada ido ta daure fuska tace "Ni saboda kai nace nake kuka?" Yace "Toh why are you crying?" Shiru tayi bata ce komai ba wasu sabbin hawayen na cika idonta, Yace "Tell me Halysaah, what is making you cry?" Kamar bazata ce komai ba sai kuma tace "My mother is sick" Yace "Hasbunallah, what's wrong with her?" bata sake ce masa komai ba tana goge idonta, After few seconds ya sauke ajiyar zuciya yace "Amma ai ba kuka zaki zauna kina yi ba, addu'a zaki mata Allah ya bata lafiya" Nan ma dai bata ce komai ba, ya mike yace "Allah ya bata lafiya" Sai a sannan tace "Ameen" Yace "Are you going back home to check on her?" Ta daga kai ta kallesa amma bata ce masa komai ba, yayi shiru shima, can yace "Are you from kano?" Ta gyada masa kai, Yace "Allah Ubangiji ya bata lafiya, and try getting something to eat for Dinner" Ta sunkuyar da kanta kawai, ya juya ya fita daga dakin ya kullo mata kofar gently. Wajen karfe sha biyu na dare Khaleesat na kwance taji ya sake knocking kofar dakinta, juyawa tayi ta kalli kofar, bayan wasu yan sakwanni ta mike zaune tana kallon kofar, sai da ya sake knocking sannan ta sauka daga saman gadon ta dau hijab dinta ta saka ta nufi kofar ta bude, yace "Are you still crying?" Ta hade rai ta girgiza kai without looking at him, yace "Ok naga baki fito kinyi dinner ba and it's past 12, ki nemi abinda za ki ci kar ki kwanta haka" Ita dai bata ce komai ba, yace "Hello" Daga kai tayi ta kallesa tace "Naji" Yace "Good" Kullo kofar dakin nata tayi ta nufi kitchen tana tafiya a hankali, sai da yaga ta shiga kitchen din sannan ya shiga dakinta yana bin ko ina da kallo, after a while Khaleesat ta fito daga kitchen din with a cup of tea and some cookies, tsaye ta gansa corridor, bayan ta karaso yace "Kin ga nima Ummi na bata da lafiya amma ban zauna ina kuka ba kamar yanda kika yi" Khaleesat bata kallesa ba ta shige dakinta ta kulle kofa, tana gama shan shayin ta koma saman gado ta kwanta, tasan yau da kyar ta iya bacci, she wish she can just see herself in Nigeria, but how?? Wasu hawaye ne suka zubo idonta ta lumshe ido, after a while ta jawo wayarta a hankali tayi dialing number Abdul bayan ta tuna ya kirata har sau biyu daxu bata iya tayi picking ba, har kiran ya katse bai daga ba, ta sake kiransa nan ma bai daga ba, tasan as usual yayi fushi kenan, ko uxuri bazai mata ba, ajiye wayar tayi ta juya zuwa daya side din gadon. Washegari da safe Khaleesat na zaune daki tana ta kokarin kiran Aunty Farida amma baya shiga, har Sha'awa sai da ta kira ita ma wayarta baya shiga, ta rasa wa kuma zata kira, ta kalli agogon wayarta dake nuna karfe goma sha daya ta ajiye wayar tayi tagumi, tun daga daren jiya har yau bata da sukuni, ko schl din ma yau tasan bazata iya zuwa ba, juyawa tayi jin knocking a kofar dakinta, tana dai zaune har sai da ya kwankwasa kofar sau uku sannan ta sauka daga saman gado, walking slowly ta tafi ta bude kofar, Yace "Good morning Halysaah, how was ur night?" Without looking at him tace "Fine" Yace "Ya jikin Mama? Kun yi communicating da su?" Kai kawai ta gyada masa bata ce komai ba kuma bata kallesa ba, Paper da pen din hannunsa ya mika mata yace "Can i get ur Email Address?" Ta daga kai ta kallesa da mamaki tace "I don't understand" Yace "I mean ur Email Address" wayarsa ne ya fara ring ya mika mata takardan da pen ya daga kiran sannan ya juya ya bar wajen, ita dai ta bi sa da kallon mamaki, can ta juya ta koma daki ta ajiye takardan da pen da ya bata, after some minutes sai gashi ya dawo yayi knocking yace "Can i get the paper" Tasowa tayi ta bude kofar bayan ta dau pen da takardan tace "Why are you asking for my Email Address?" Yace "Ki dae rubuta ki bani" Shiru tayi, sai kuma ta jinginar da paper din jikin kofa ta rubuta sannan ta mika masa ya amsa ya juya ya bar wajen, yana fita da few minutes taji message ya shigo wayarta, ta dau wayar ganin E-mail ne ya shigo ta bude, kallon Image din da ta gani as Email din ta dinga yi babu ko kiftawa, she look shocked and confused at the same time, ta daga kai tana kallon kofar dakinta babu ko kiftawa, dai dai sanda taji sallamarsa, kasa tashi tayi daga inda take zaune, har sai da yayi knocking sau biyu tayi karfin halin mikewa ta isa kofar ta bude tana kallonsa, Yace "I don't know if you find this okay and a good idea" Ita dai bata fasa kallonsa ba looking speechless, Yace "Hope they won't be Mad at this back home Halysaah?" Jin bata basa amsa ba ya gyada kai yace "I guess it's a bad idea, I should have ask for ur opinion first before doing this" Nan da nan hawaye ya cika idonta ta sunkuyar da kanta, yace "Ok it's fine, i will get the ticket cancelled" Daga kai tayi da kyar tana kallonsa hawaye na zuba idonta tace "Thank you so much, i appreciate" Yace "Sure??" Ta gyada masa kai, yace "Ohk, u can order a Lyft that will be taking u to the airport later, ur flight is at 3pm today" Sauke idonta tayi cause she is totally speechless, ya mika mata travelling documents dinta, amsa tayi cike da mamakin how he got them, ya juya ya bar wajen, komawa cikin daki tayi ta kulle kofar tana kallon inda take ajiye travelling doc din nata a dakin, did he come to her room to check ne, to ai throughout babu inda taje, ta karasa gefen gado har sannan jikinta a mugun sanyaye ta zauna, kallon screen din wayarta ta sake yi tana kallon ticket din don ganin abun take kamar a mafarki, tana kara duba taga tun daren jiya ya siya ticket din and kamar yanda yace the flight is by 3pm today, ta ma rasa ko farin ciki zata yi ko kuma wani reaction zata yi, amma da ta tuna she is going back home to see her Mom which was her wish since yesterday sai taji wani farin cikin da tunda take bata taɓa jin irinsa ba a rayuwarta, 80% a cikin dari na damuwarta ya ragu cikin lokaci kankani, kallon agogo tayi taga sha daya ya wuce sosai, the weakness she is been feeling since this morning immediately vanished, mikewa tayi tana share hawayenta ta dau medium box din kayanta.... Karfe biyu Khaleesat ta gama duk abinda take, har sallan zuhur tayi, Lyft din da tayi ordering kawai take jira, tana zaune gefen gado xuciyarta fal da tunani kala kala, babban burinta a yanzu bai wuce ta ganta kusa da mahaifiyarta ba, in yaso koma me zai faru daga baya sai ya faru, kallon wayarta tayi taga Safiyyah ce ke kiranta, tun daxu da safe ta kirata amma sbda damuwar da take ciki ko picking bata iya tayi ba, Khaleesat ta daga kiran ta kai kunne, Safiyyah tace "Khalee me yasa baki shigo schl ba yau? Are you okay?" Khaleesat ta sauke boyayyen ajiyar zuciya tace "Ummanmu ce bata da lafiya Sophie" Safiyyah tace "Subhanallah, amma ya jikin yanzu?" Khaleesat tace "Da sauki" Safiyyah tace "To Allah ya bata lafiya, plss nasan ki kar ki sa ma kanki damuwa kawata addu'a kawai zaki dinga mata, nasan kilan kina nan kina ta kuka ko?" Khaleesat dai tayi shiru bata ce komai ba, Safiyyah tace "In sha Allah in mun gama lectures zan taho" Khaleesat tace "I am sorry ban kira ki na gaya maki ba i will be leaving for Nigeria by 3pm" Da mamaki Safiyyah tace "Zaki tafi Nigeria? Abdul ne ya siya maki flight ticket?" Khaleesat ta sauke idonta tace "Uhm" Safiyyah tace "Is it that critical Khaleesat?" Khaleesat tace "To da sauki dai, amma kinsan bazan samu rest of mind ba in ban je ba" Safiyyah tace "To kina airport yanzu ne?" Khaleesat tace "Aa ina jiran Lyft ne yanzu zan tafi" Safiyyah tace "Toh shikenan mu hadu a can kawai sai mu yi sallama, bari in nemi Uber nima" Khaleesat tace "To nagode Sophie" Da haka suka gama wayar, Khaleesat ta mike bayan Lyft dinta ya iso, tana rike da trolley dinta da handbag ta fito daga dakin ta kulle kofa, sanye take da Maroon Abaya sai veil dinta, tana tafiya a hankali ta karaso cikin parlorn, ya ajiye wayar da yake yace "Kin shirya?" Without looking at him tace "Eh" yace "Kin yi ordering ride ai?" Tace "Eh" yace "Ohk" Mikewa yayi ya ciro 1000 Dollars ya mika mata yace "Sort ur self out with this" Girgiza masa kai tayi tace "Aa Nagode" Yace "C'mon, u didn't beg me Halysaah" Ƙin kallonsa tayi kuma taki amsan kudin, ya dau handbag dinta da ta ajiye saman trolley din gabanta ya bude zip din jakar ya sa mata kudin tare da wani farin takarda, ta ɗaga kai tana kallonsa, ya koma ya zauna yace "Allah ya tsare, my regards to ur Mom and everyone back home, Allah ya bata lafiya" Da kyar tace "Ameen nagode" Yace "Zaki ga digit na rubuta maki a takarda, idan kun sauka Airport sai ki kira number kice masa kun sauka" Ta kasa cewa komai, after few seconds ta dau handbag dinta cikin sanyin murya tace "Nagode " Yace "U are welcome, wishing u a Safe trip" Tana jan trolley dinta a hankali ta nufi kofa, tana bude kofar ta fita ta daga kai tana kallonsa taga Idonsa na kan wayarsa da yake dannawa, kulle kofar parlon tayi, taga Lyft din dake jiranta ta nufi wajensa. A Airport Khaleesat suka hadu da Safiyyah, Safiyyah na rike da hannunta tace "Tun yaushe ne Umman bata da lafiya?" Khaleesat tace "Jiya Aunty sha'awa ke gaya min" Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya tace "To Allah Ubangiji ya bata lafiya" Khaleesat tace "Ameen" Safiyyah tace "Lallai Abdul ya fara hankali da yayi tunanin biya maki jirgi kije ki duba Umma, nayi mamaki sosai wallahi" Khaleesat ta ɗan yi murmushi da iyakarsa lips, Safiyyah tace "Yanzu kwana nawa za ki yi?" Khaleesat tayi shiru at first, sai kuma tace "Sai dai naje tukunna in sha Allah" Safiyyah tace "Toh Allah ya kai ku lafiya, don Allah ki gaida min Umma da jiki" Safiyyah na fadin haka ta jawo handbag din Khaleesat ta saka mata dala dari tace "Plss manage this kawata" Khaleesat ta ɗan bude baki tace "Haba meye haka Sophie" Sophie bata tsaya ta saurareta ba ta daga mata hannu tana murmushi ta bar ta tsaye wajen, Khaleesat dai ta bi ta da kallo. Khaleesat was more than shock bayan ta amshi boarding pass dinta ganin ticket din Business Class ya siya mata, Business class fa? Kikkifta ido tayi ta sake kallon ticket din sosai to confirm, taga Business class din dai ne still, sosai jikinta yayi sanyi, tana jan kafa da kyar ta shiga jirgin, this is the first time she will be traveling Business class, wata Flight Attendant that gave her all the maximum attention ta yi leading dinta har zuwa Seat dinta a cikin jirgin da fara'a tana welcoming dinta, bayan wani ɗan lokaci jirgin ya tashi, Khaleesat ta ajiye Amenity kit da aka bata ko duba abinda ke ciki bata yi ba tana bin ko ina na Business class din da ido, the Flight from Baltimore Washington International to Amsterdam Schiphol Airport in North Holland for Layover was smooth and comfortable, duk zuwanta Amurka bata taɓa tafiya feeling so comfortable like this ba, bayan few hours aka sauya masu jirgi zuwa Nigeria a nan North Holland, Khaleesat tayi shiru da mamaki jin announcement na cewar Lagos Nigeria jirgin ya nufa, ticket dinta ta sake dubawa taga ashe haka ne a jiki, bayan tafiyar kusan awa bakwai jirgin nasu ya sauka a MMI Airport Lagos. 07087865788✍🏻 ✨✨HALYSAAH✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 6..... Bayan Khaleesat ta dau trolley dinta a cikin airport after going through custom ta tsaya cikin airport din tana tunanin yanda zata yi cause karfe shidda saura ne na asuba, should she check for available flight to Kano? To nawa ne ma a account dinta before she think of doing so, ko dai kawai ta tafi Motor park ta hau mota zuwa kano, dollars din da Housemate dinta ya bata ne ya fado mata a rai don gaba daya ta ma mance, ta bude handbag dinta ta ciro kudin tana kallo, takardan da ya saka mata hade da kudin a jaka ya fadi kasa, ta duka ta dau takardan tana kallon numbers din jiki sai kuma ta mayar cikin jaka tare da Dollars din, masallacin dake cikin Murtala Muhammad International airport ta tafi don yin sallan asuba, tana ta zaune cikin masallacin bayan ta idar da sallah tana azkar dinta, can ta ciro wayarta a handbag ta duba agogo taga karfe bakwai da minti goma, dollars din jakar ta sake cirowa ta kirga taga dala dubu ce, kallon kudin ta dinga yi jiki a sanyaye don bata yi tunanin har haka ya bata ba, ta dau white paper din dake dauke da digit tana tunanin to ko digit dinsa ne wannan din, kati ta siya ta Ussd sannan tayi dialing number a wayarta, sai da ya kusa katsewa aka daga, daga daya side din aka yi sallama ta amsa, amma sai taji kamar ba muryarsa bane, ta dai ce "Ina kwana?" Yace "Hajiya ko kece kika taho daga America?" Tace "Eh" Yace "To barka da isowa Hajiya, ina ta sauraren kiran naki dama tun daxu, kina cikin airport din ne yanzu?" Tace "Eh" Yace "Ohk to gani nan tahowa ba da dadewa ba in sha Allah" Bayan ya katse wayar ta kalli screen dinta, to waye kuma wannan, maida kudin tayi jaka ta ciro nose mask dinta ta saka sannan ta mike ta fito daga Masallacin da trolley dinta with handbag, bayan wasu mintoci sai gashi ya sake kiranta, ta fito outside of the airport, yana hangota ya nufota ya gaisheta da ladabi har da bowing kansa yace "Ya hanya Hajiya?" Ta sauke idonta tace "Lafiya Alhamdulillah" With respect yace "Ga mota can Hajiya, zaki je hotel ki huta zuwa karfe daya na rana don Flight dinki zuwa kano na karfe Biyu ne in sha Allah..." Khaleesat was speechless ta dinga kallonsa babu ko kiftawa cike da mamaki, can kuma ta kalli lafiyayyen motar da ya nuna nata, tuni ya karasa ya amshi trolley dinta ya tafi ya bude booth ya saka, sannan ya bude mata bayan mota yace "Bismillah Hajiya" Sauke idonta tayi kasa taji kafafuwanta sun mata nauyi amma a haka tana tafiya a hankali ta tafi ta shiga back seat sannan ya kulle motar, ya zaga ya shiga driver seat, Hotel me tsada sosai that isn't far away from the airport ya kai ta, sai da ya tabbatar tayi check in har zuwa dakinta sannan ya bar hotel din, tana shiga babu jimawa wata ma'aikaciyar hotel din ta kawo mata lafiyayyen Breakfast, ita dai Khaleesat ba um bare um um, gaba daya kanta ya gama kullewa, tashi tayi ta bude trolley dinta ta dau Shower gel zata yi wanka. Khaleesat na bacci wajen karfe daya da minti ashirin vibration din wayarta ya tasheta, ta jawo wayar a hankali tana duba me kiranta taga mutumin da ya kawota Hotel ne, ta mike zaune sannan tayi picking call din ta kai kunne tayi shiru, daga daya bangaren yayi mata sallama sannan yace "Hajiya fatan kin shirya in taho in dauke ki, flight din naki nan da minti talatin ne in sha Allah" a hankali Khaleesat tace "Toh" Yace "Gani nan tahowa yanzu da izinin Allah" Yana katse wayar Khaleesat ta sauka daga saman gado taje tayi alwala a bandaki, tana idar da sallan Azahar sai ga kiransa, ta dau trolley dinta da handbag ta bar dakin hotel din ta sauko downstairs, yana hangota a Reception din hotel din ya tafi da sauri ya amshi trolley din hannunta, ya karbi makullin dakin ya kai ma Receptionist, sannan suka fita haraban hotel din ya bude mata back seat bayan ya saka trolley dinta a booth, cikin mintuna kadan suka isa MMI Airport, sai da ya tabbatar ta amshi boarding pass dinta sannan yayi mata sallama da murmushi fuskarsa yace "Toh Allah Ubangiji ya tsare Hajiya, idan kun sauka kanon za a karasa dake gida in sha Allah... We will keep in touch" a hankali Khaleesat tace "Toh Nagode, Allah ya saka da alkhairi" Yace "Ameen Hajjaju, nagode kwarai, Allah Ubangiji ya kai ku lafiya" A haka suka rabu ta nufi Departure lounge walking slowly, bayan kusan minti ashirin jirginsu ya tashi zuwa garin kano. Suna sauka kano Khaleesat ta fito daga cikin airport gabanta na faduwa, sai gyara nose mask din fuskarta take tana waige waige, yanzu ina ma ta nufa tukun, tasan ko da wasa bazata nufi gida ba dai, wayarta ya fara ring ta duba da sauri gabanta na ci gaba da faduwa, wata lamba ce ke kiranta tayi picking tayi shiru, taji an mata sallama ta amsa, mutumin ya gaisheta yace "Hajiya Hamisu ne ya aiko min lambarki, naga jirgin ku ya sauka yanzu, yace za a karasa dake gida, kina ta ina yanzu?" Tace "Na fito outside of the airport" Tahowa taga mutumin yayi zuwa inda take tsaye bayan ya hangota, nan ya kai ta har motar dake jiranta, motar shigen wanda ta shiga a Abuja ne, mutumin ya bude mata back seat ta shiga tace "Nagode" Yayi bowing kansa yayi mata sallama yace "Allah ya kai ku lafiya" Tace "Ameen Nagode" Drivern dake mazaunin driver ya gaisheta yana tambayarta ya hanya sannan ya tada motar suka fita daga airport din yace "Ina muka nufa Hajjaju?" Khaleesat ta ɗan yi shiru kamar me nazari, sai kuma tace "Hotoro zaka kai ni" Yace "To Allah ya kai mu lafiya" Suna isa dai dai kofar gidan da ta nuna masa ya tsaya, ya bude motar ya sauka don fiddo mata Trolley dinta a booth, bude motar tayi ita ma ta sauka tana gyara facemask dinta, ta amshi akwatinta a hannunsa sannan tayi masa godiya ta shiga cikin gidan da sauri, Baaba Gaje dake zaune tana tankade garin tuwo ta daga kai tana kallonta, Khaleesat ta ɗan sauke Facemask dinta tana murmushi tace "Baaba sannu da aiki" Baaba Gaje ta ajiye rariyar hannunta tace "Khaleesatu? Daga ina kuma haka?" Khaleesat ta duka nan gabanta har sannan tana ɗan murmushi tace "Makaranta" Baaba Gaje tace "Ikon Allah, to ai ko minti ashirin banyi da dawowa daga gidanku ba kuma ba ace min kina hanya ba" A hankali Khaleesat tace "Baaba ya jikin Ummanmu fa?" Baaba Gaje tace "Kaddai ba a san kin biyo hanya ba kika taho Khaleesatu?" Khaleesat ta gyada mata kai kawai, Baaba Gaje tace "Ikon Allah, to ai jikin nata da sauki er nan, shi Awdul din ne ya biya maki kudin jirgi kika dawo?" Khaleesat ta girgiza kai gabanta na faduwa tace "Bai san na dawo ba Baaba" Baaba Gaje tace "Ikon Allah, to bari in kira Parida, ko kuma ke ki kirata da kanki, Gwara da kika yi dubaran zuwa nan kada Salubabben uban nan naki ya sa ki a bakin duniya mu shiga uku, Ga tabarma taho ki zauna ki huta, irin wannan tafiya me nisa haka, naji ance Amurkan har yapi legas nisa ko? Kira Paridan mu ji yanda za ayi" Khaleesat ta zauna gefenta ta bude handbag ta ciro wayarta, duk da yanda gabanta ke faduwa haka tayi dialing din lambar kanwar Ummanta Aunty Farida, Baaba Gaje tace "Auu to ai Parida ba waya a hannunta wai an sace a mota" Khaleesat ta daga kai tana kallonta, Baaba Gaje tace "Abinda zai faru kawai ga garin tuwon nan ki karasa tankade min ga can murhu na dora ruwan tuwo in yayi ki min talgi ki tuka tuwon in ya silala ki kwashe, ga kuma kayan miya can bai dai da yawa ki jajjaga ki kada min miyar kuka, ni kuma sai in koma can Mariri yanzu in sanar ma Ummanku kin zo" Khaleesat tace "Toh Baaba" Mikewa Baaba Gaje tayi ta figi yakunennen gyalenta a igiyar shanyan dake ɗan karamin tsakar gidan ta yafa tace "Bara inje, dama ina da canjina dari da hansin sai in roke masu ɗan sahu su kai ni ko Farawa ne sai in karasa Maririn da kafa ta" Khaleesat ta bude handbag dinta amma sai taga Dollars kawai, ta daga kai ta kalli Baaba Gaje tace "Wallahi bani da kudin Nigeria a nan Baaba, amma bari in ciro a POS yanzu sai in baki kudin adaidaita sahun" Baaba Gaje tace "Aa yi zamanki kiyi aikin da na sa ki, minti nawa ne nan da Mariri, kawai dai ga wanke wanke can bakin kwararo ki wanke min har su, ki share tsakar gidan nan, in yaran nan suka dawo islamiyya ki dauraye masu Uniform dinsu, dakin ma na nan sunyi kaca kaca da shi babu kyan gani" Daga haka ta fice daga cikin gidan bayan ta saka slippers dinta, Khaleesat ta cire mayafin abayan jikinta ta dora kan akwatinta sannan ta ci gaba da tankaden da Baaba Gaje ta bar mata, Baaba Gaje makociyarsu ce a can unguwansu Mariri kafin 'ya yanta su siya mata wani ɗan kararramin gida a nan Hotoro Tsamiyar boka ta dawo tana zaune da jikokinta biyar tana dubasu, zaman mutunci da amana Baaba Gaje suka yi da Mahaifiyar Khaleesat da ta dauki Gajen tamkar uwa. Wajen karfe shidda saura Khaleesat ta gama duk aikin da Gaje ta loda mata sannan ta dora ruwan da zata yi wanka a sauran rushi, zaunawa tayi kan tabarma ta jingina da bango don ta gaji likis, Housemate dinta ne ya fado mata, ta dai yi shiru staring into space, after a while ta sauke idonta a hankali ta mike ta shiga da kwanukan da ta wanke cikin dakin Gaje, dai dai nan Gaje ta shigo cikin gidan da Aunty Farida, Khaleesat ta tafi da gudu ta rungume Aunty Farida cike da murnan ganinta, Aunty Farida na kallonta tace "Ke kuma da wa kika yi shawara kika biyo hanya Khaleesah? Abdul din ne yace ki taho?" Gaje ta daga hannu sama da sauri tace "Aaaa tace bai ma sani ba" Aunty Farida na kallon Khaleesat da mamaki tace "Ban gane bai sani ba??" Khaleesat ta marairaice ta kauda zancen ta hanyar cewa "Aunty ya jikin Ummanmu?" Aunty Farida ta kamo hannunta suka zauna saman tabarma tace "Ai jikin Umma da sauki sosai Khaleesat, gashi har an sallamemu a asibiti, wa yace maki bata da lafiya ne ma tukun?" Khaleesat da har hawaye ya ciko idonta tace "Aunty Sha'awa" Gaje tace "Lahh ha ila, wato Sha'awa bazata dena munafurci ba ko? Wato bazata canxa hali ba ko? Da kaina fa sai da na jaddada mata kar ta gaya maki ko kin mata sako ta wassol don kar hankalinki ya tashi, ashe sai da munafukar ta zaga ta fada maki" Aunty Farida tace "Toh Allah ya kyauta, kwata kwata Sha'awa bazata canza ba" Khaleesat da hawaye ke cika idonta tace "To Aunty ta yaya zan ga Ummanmu yanzu?" Aunty Farida tace "Kar ki damu kiyi zaman ki nan wajen Baaba Gaje, gobe da safe in za mu tafi asibiti sai mu fara biyowa ta nan da Umman tunda asibitin Malam Aminu kano ne" A hankali Khaleesat tace "Toh Allah ya kai mu Aunty" Sai bayan Magrib Aunty Farida ta bar gidan bayan ta ci tuwon da Khaleesat tayi ma Gaje, sosai Khaleesat taji ta samu rest of mind bayan taji jikin Ummanta da sauki, bayan Isha Gaje ta gyara mata ɗan lungun da zata kwanta a dakin ta daura mata net din sauro tace "Allah dai ya rabaki da cinnaku" ita dai Khaleesat tayi murmushi kawai bata ce komai ba, ita matsalarta ma zafi, ko ya zata yi da zafi yau gashi karamin dakin wani ɗan mitsitsin window ne kawai ke garesa, su bakwai kuma zasu kwana a ciki, Khaleesat ta gama shirin kwanciya don tayi wanka sannan ta shiga net din ta kwanta, ta amshi maficin da gaje ke mika mata ta cikin net din, tun dawowarta sai a sannan tayi subscription ta shiga WhatsApp dinta, Message din Safiyyah dake tambayarta ko ta isa lafiya kadai tayi ma reply, bata yi mamakin rashin ganin message din Abdul ba don she isn't even expecting his message, ajiye wayar tayi ta gyara kwanciyarta ta lumshe ido, Housemate dinta ne ya fado mata, she have no access to him balle ko godiya ma tayi masa, bata yi tunanin da ta fito zata tafi airport bazai tambayeta phone number dinta ba, ko Airport din ma bata yi tunanin bazai yi offering yace zai kai ta ba, juye juye kawai take yi a net din idonta a rufe, after a while of thinking bacci ya dauketa. Washegari Khaleesat ta gama yi ma Baaba Gaje duk aikace aikacen gidan, ta hura gawayi ta daura ruwa tayi ma kananun jikokinta wanka sannan ta dama kunu, Baaba Gaje ta fita siyo masu kosai a titi, har karfe goma Khaleesat bata ga Aunty Farida sun zo gidan da Ummanta ba, gaba daya ta damu taga Ummanta, Baaba Gaje tace "To ke sai ruwan ya salance zaki je kiyi wankan? Ba fa wani gawayin" Khaleesat tace "Zan yi" Daga haka ta mike ta tafi yin wankan, tana fitowa daga wanka taga takalmin da Aunty Farida ta zo da shi jiya a bakin kofa da wani takalmin daban wanda ko ba a fada ba tasan na Ummanta ne, da sauri ta shiga dakin Baaba Gaje taga Ummanta da Aunty Farida a zaune, tsallake Aunty Farida tayi ta tafi gun Ummanta da gudu cike da farin cikin ganinta ta durkusa gabanta ta rungumeta, Aunty Farida tace "Ko dai baki da hankali ne?" Baaba Gaje tace "Toh da sauki dai kam" Ita dai Umman sai kallon Khaleesat take, gaba daya Khaleesat ta ma mance wai Umma bata da lafiya tsabar farin cikin ganinta, a hankali Umma tace "Meyasa zaki biyo hanya Khaleesah? Abdul din ne yace ki dawo?" Khaleesat ta kamo hannunta cike da damuwa tace "Umma ya jikin?" Umma tace "Naji sauki Alhamdulillah" Khaleesat tace "Aunty Sha'awa tace min ko magana fa baki yi" Baaba Gaje ta rike haɓa tace "Oh ni 'ya su, kun ji er iska ko? Wallahi Sha'awa da kyar taga annabi, babu yanda bamu yi da ita ko da wasa kar ta gaya maki ba ashe sai da ta zaga ta fada, har ce mata nayi tace maki tayi tafiya ko da zaki buga nata wassol" Khaleesat ta daga kai ta kalli Baaba Gaje tace "Ni ce na kirata don ina ta magana bata min reply ba" Aunty Farida tace "Ai tsabar munafurci yasa ta gaya maki ba wani abu ba" Khaleesat ta ɗan yi murmushi ta gaida Aunty Farida, Aunty Farida ta amsa tace "Amma shi Abdul yasan Umma bata da lafiya shine ko kira ya dubata bai yi ba?" Khaleesat ta sauke idonta kasa tace "Ni fa bai san na dawo ba Aunty" Aunty Farida tace "Wai ban gane bai san kin dawo ba, wa ya biya maki kudin jirgin?" Khaleesat ta daga manyan idanuwanta tana kallonsu, Sai kuma a hankali tace "Wani ne ya biya min ba Abdul ba" Umma ta kalleta da sauri tace "Wani?" Da mamaki Aunty Farida tace "Wani a ina?" Khaleesat na kokarin mikewa tace "Neighbor dina ne" Umma ta bude baki tana kallonta, sai kuma tace "Ko baki da hankali ne, waye ya biya maki kudin jirgi Khaleesah?" Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, Gaje tace "Bude baki zaki yi ki mana bayani dalla dalla, waye shi zai biya maki zunzurutun kudi na jirgin da naji ance ya fi miliyan daya? A ina kika san sa?" Still dai Khaleesat taki cewa komai, Aunty Farida tace "Ke bana son rainin wayo uban wa zaki ma shiru ana maki magana? Ko baki ji tambayar da ake maki bane?" Umma dai kallon Khaleesat kawai take da mamaki, Khaleesat ta koma baya ta ɗan sunkuyar da kanta a hankali tace "Ni fa nace makocina ne ya biya min, kuma ai gani yayi ina ta kuka Ummana bata da lafiya shine ya biya min jirgi in dawo in dubota" Cikin sanyin murya ta kare maganar, Baaba Gaje tace "Atoh dama ai ko ina ana samun na Allah, Allah ya masa albarka, Bature ne ko?" A takaice Khaleesat tace "Um" don bata son ma a ci gaba da zancen, Baaba Gaje tace "Ko da naji, ai sai baturen dama, wani baƙin fata ne zai biya maki jirgi don yana makocinki, ai ko mutuwa uwar taki tayi iyaka ya maki gaisuwa ya kama gabansa, to Allah ya saka masa da alkhairi, abinda ma baturen kudin jirgin ba wani kudi bane a wajensa, ji zai yi kamar naira dubu goma ya kashe fa" Khaleesat na kallon Aunty Farida tace "Aunty yanzu za aje asibitin ne?" Aunty Farida tace "Aa mu har mun dawo daga asibiti sai kuma na gobe in Allah ya kai mu" a hankali Umma tace "Toh da ya biya maki kudin jirgin zuwa wa zai maki na komawa yanzu? Kinsan dai ko hauka kike baza ki bari Abdul yaji wannan batun ba ki ja mana masifa ko?" Sai da gaban Khaleesat ya fadi, a hankali ta sunkuyar da kanta, ita gaba daya ta ma mance ashe biyan jirgi za ayi a koma, nan da nan jikinta yayi mugun sanyi, yanzu ina zata samu kudin ticket din komawa, she became so weak at once, Aunty Farida tace "Toh shi Abdul din baki ce masa Umma bata da lafiya bane?" Khaleesat da har sannan jikinta yake a sanyaye ta girgiza kai tace "Baya nan ne" Daga haka ta mike ta tafi zata shirya don zanin da tayi wanka ne daure jikinta har a lkcn, Khaleesat na cikin saka kayanta da ta fiddo a akwati 1000 dollar din da Housemate dinta ya bata suka fado mata a rai, ta zaro ido lkci daya taji hankalinta ya kwanta har sai da ta sauke ajiyar zuciya, tasan probably in ta canza har da 100 dollar din da Safiyyah ta bata kudaden za su iya maidata Amurka, she felt so relieved, nan da nan walwalarta ya dawo, tana jin Baaba Gaje na tambayar Aunty Farida ko kishiyoyin Ummanta sun shiga dubata yau, Aunty Farida tace "Jiya ma basu shigo dubata ba sai yau Baaba Gaje" Baaba Gaje tace "Shegu matsiyata, so fa suka yi ace ta mutu, to shi Malam Alin ya ku ka ƙarke da shi? Ya bada kudin?" Aunty Farida tace "Aa ni fa ban bi ta kansa ba Baaba Gaje, dama me ya tsinana kafin in zo kanon? daxu ma aka turo min sauran kudin adashina da nake jira, duk na siya sauran magungunan" Baaba Gaje tace "Atoh dai bai taɓuka komai ba a takaice, shi ma da zaki basa yanxu tsaf zai amshe" Har aka yi azahar su Umma da Aunty Farida na gidan, Umma har tayi bacci ta tashi saboda maganin da take sha, har a sannan da kyar take taka kafarta daya, hannunta dai ya sake ya dawo normal tun a jiya, Khaleesat ta shigo dakin da shinkafa da waken da ta dafa, Baaba Gaje kuma ta shiga makota dubiya, Aunty Farida dai sai bin Khaleesat take da kallo, sosai taga ta kara kyau tayi fresh, duk da dai tana nan a yanda take babu kiba, komawa tsakar gida Khaleesat tayi ta dauko man gyadan da ta soya ta dawo dakin, ta fara zuba ma Umma da Aunty Farida abincin, Umma dake zaune kan darduma tana kallonta tace "Kun fara jarabawan ne?" Aunty Farida tace "Haba dai sun fara jarabawa zata taho? Ai bazai yiwu ba, ko ana haka ne?" Khaleesat dake sauraronsu ta girgiza kai tana ɗan murmushi tace "Da sauran lokaci bamu fara ba tukun" Aunty Farida tace "To yanzu dai tun kan wani munafukin yasan kina garin nan mu shiga uku yaushe za ki koma Khaleesah?" Khaleesat ta daga kai a hankali tace "Cikin satin nan in sha Allah" Aunty Farida tace "Toh inji dai Abdul din ya rage abubuwan nan nasa da yake maki?" Khaleesat ta ajiye masu abincin a gabansu kamar bazata ce komai ba sai kuma tace "Babu abinda ya fasa, ni na gaji da halinsa ma yanzu" Umma ta daga kai tana kallonta, Aunty Farida ma kallonta take don bata taɓa cewa ta gaji da halin Abdul ba, Aunty Farida ta sauke ajiyar zuciya ta fara cin abincin gabanta tace "Na dai gaya maki babu me canza maki shi sai ke da kanki, ke macece ya kamata ace zuwa yanzu kinsan wanene Abdul kinsan kuma yanda zaki zauna da shi" Mikewa Khaleesat tayi without saying anything don ita yanzu taji ko zancen nasa ma bata so har cikin ranta, tun shekaranjiya da yayi fushi har yau bai kirata ba ita kuma as far as tayi masa miss calls har biyu to bata ji zata iya sake kiransa ba unlike before da ta dinga kiransa kenan ko da bazai daga ba, ko kuma tayi ta masa magana ta WhatsApp, to yanzu kam bata ji zata iya ba..... 07087865788✍🏻 *Still on free pages* ✨✨HALYSAAH✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 7..... Kwanan Khaleesat hudu yau a garin kano, kuma har a sannan babu wanda yasan da zuwanta a cikin yan gidansu, ko nan da can bata fita a gidan Baaba Gaje don ma kar tsautsayi ya sa ta hadu da daya daga cikin yan gidan nasu, a kwanaki hudun nan sau biyu Ummanta da Aunty Farida suka zo gidan Baaba Gaje dominta, zuwa sannan Umma ta warware gaba daya tafiyarta ya dawo normal, tun kwanaki biyu da suka wuce ta gama amsan treatment dinta a hospital sai magunguna da take sha kawai, har zuwa ranan kuma Abdul bai kira Khaleesat ba, ita kuwa kawai taji ko a jikinta da ya kira da kar ya kira, there wasn't an atom of disturbance a tattare da ita, ko ta WhatsApp bata yi gigin yi masa magana ba Unlike before da bazata iya hakuri ba sai ta masa, tana bakin murhu tana dafa shinkafa da wake ga turmi gabanta tana ɗaka yajin da za ayi amfani da shi wajen cin shinkafa da waken, Su Ummanta da Baaba Gaje kuma na can uwar ɗaka, tunanin yanda zata fara shirye shiryen komawa USA take don suna da wani presentation nan da kwana uku, daxu da safe ta duba available flight da farashinsu online and she is hoping in ta canza dollars din da Housemate dinta ya bata zai isheta ta koma, Khaleesat ta bar daƙan yajin da take yi bayan taji Aunty Farida na kwalo mata kira, mikewa tayi ta wuce dakin tana amsawa, tun da ta zo gidan Baaba Gaje ta sakar mata aikin komai, hatta jikokinta ita ke masu wanka kan su tafi makaranta, ita taga kamar har ta ɗan yi duhu tsabar girki cikin rana da take yi tun zuwanta, Aunty Farida tace "Ana kiran wayarki" nan da nan mood din Khaleesat ya canza ta karasa gun wayar without much interest, duk tunaninta Abdul ne cause she isn't expecting any call from anybody, Number mutumin da ya tarbeta a Airport din Lagos ta gani a gaban Screen din wayarta, ta dinga kallon number bata ko kiftawa, duk da bata yi saving ba amma ta gane nasa ne, daukar wayar tayi ta fita daga dakin ta koma bakin murhun sannan tayi picking ta kai kunne, sallama yayi ya gaisheta da ladabi, tace "Ina yini?" Yace "Alhamdulillahi Hajiya, ya jama'ar gidan?" Tace "Alhamdulillah" Yace "To maa sha Allah, dama na bugo ne inji ko zaki kara kwanaki nawa nan gaba kan ki koma America?" Khaleesat tayi shiru trying to understand why he is asking her that, yace "Hello?" Tace "Ina jin ka, ban gane tambayar bane" Calmly yace "Aa so nake in san ranan da zaki koma ne Hajiya, in ya kama ayi rescheduling din ticket dinki sai ayi hakan in sha Allah" Khaleesat was speechless, a ranta tace Ticket kuma? Kasa cewa komai tayi with surprise, taji ta ma kasa ci gaba da tsayuwa, jin ya sake cewa "Hello" ta kifta ido da kyar ta duka kusa da turmin da take daka yaji tace "Ina ji" Yace "Ina ga a bari duk sanda kika shirya zaki nemeni ta waya ko Hajiya?" Sauke idonta tayi kasa, lokaci daya jikinta yayi sanyi sosai, cikin sanyayyen murya tace "Ranan Lahadi nake son zan koma idan Allah ya yarda" Yace "To Maa sha Allah, dama booking din ranan aka maki da zaki taho, flight din karfe daya ne, za ku tashi ta Airport din Abuja in sha Allah" Ita dai Khaleesat ta kasa cewa komai, yace "Sai kin ji ni in sha Allah Hajiya" A hankali Khaleesat tace "Nagode" Khaleesat na zaune dakin Baaba Gaje tana jujjuya shinkafa da waken dake gabanta da cokali, gaba daya ta kasa cin abincin, ita kanta ta rasa dalili, ko tsabar yanda jikinta yayi sanyi ne tun bayan da suka yi waya da mutumin daxu da ya sanar mata da ticket dinta na komawa America sannan tana gama aikin da take ta bude WhatsApp taga ya aiko mata da Flight Ticket dinta which was also business Class kamar dai yanda ta zo, this made her so weak, gaba daya ta ma rasa gane feeling din dake ranta a lokacin, bata taba tunanin Housemate din nata zai mata ticket din komawa ba, Duk Ummanta na lura da sauyawanta lkci guda, Aunty Farida ta gama shafa powder din da take zata leka gidan wata kawarta Maman Fu'ad a nan hotoron, ta dau jakarta da mayafi tana kallon yayarta tace "To sai na dawo Umma" Umma tace "Amma kar ki dade don Allah Farida" Aunty Farida tace "Haba ai yamma tayi bazan zauna ba Umma" Daga haka ta fita daga dakin tayi ma Baaba Gaje dake waje tare da bakuwarta sallama sannan ta fita daga gidan, Umma ta daga kai tana kallon Khaleesat tace "Menene kika saka abinci a gaba kika kasa ci Khaleesat?" Khaleesat ta daga kai da sauri tana kallon kyakkyawan fuskar Ummanta, babu wanda zai ce Umma ce ta haifeta sai dai ma yayi tunanin yayarta ce don kama suke ba na wasa ba kamar an tsaga ƙara, Khaleesat tayi murmushin yake ta kai shinkafa da waken baki tace "Babu komai fa Umma" Umma tace "Yaushe za ki koma? Kuma yaya za ayi da batun kudin jirgi? Har yanzu Abdul din bai san kina nan ba?" Khaleesat ta girgiza kai tace "Umma ai nace baya nan kuma ba a samunsa ta waya, ranan lahadi zan koma in sha Allah" Umma tace "Ranan Lahadi? To ina za ki samu kudin komawa?" Khaleesat ta gyara zamanta tace "Makocin nawa ai tare ya biya min na zuwa da dawowa" Kallonta Umma ta dinga yi da alamar tuhuma ga mamaki kwance fuskarta, Khaleesat taki yarda ta bari su hada ido sai tura abincin gabanta take, Umma tace "Khaleesah" Da kyar Khaleesat ta daga kai gabanta na faduwa, Umma tace "Meye tsakaninki da wannan mutumi da ya biya maki kudin jirgin zuwa har da na komawa?" Khaleesat ta hadiye sauran shinkafar da ya makale a throat dinta da kyar tace "Wallahi Umma babu komai, makocina ne kawai shi, kuma don yaga yanda na daga hankali baki da lafiya shi ne yasa yayi hakan, ni kaina sai bayan da ya biya min na sani, amma ki yarda dani Umma babu komai tsakanina da shi" Kamar zata yi kuka ta kare maganar, Ummanta ta sauke ajiyar zuciya tayi shiru, bayan some seconds tace "Toh shikenan, amma dai kinsan in Abdul ya samu labarin nan da matsala ko?" Khaleesat ta sunkuyar da kanta bata sake cewa komai ba, jin Umma tayi shiru alamar ta fada duniyar tunani Khaleesat ta daga kai a hankali tace "To ai Umma babu wanda yasan na zo kano har yanzu, don haka bazai sani ba" Umma ta sauke wani ajiyar zuciyar tace "To gudun kada hakan ya sake faruwa kar ki sake yarda ko wata mu'amula ta hadaki da shi makocin naki Khaleesat, ki rufa mana asiri" Khaleesat bata ce komai ba sai kuma ta jawo handbag dinta ta ciro dala dubu dayan da Housemate dinta ya bata ta nuna ma Umma cikin sanyin murya tace "Wannan ma shi ya bani da zan taho" Umma ta dinga kallon kudin duk da bata san ko nawa bane ta dai ce "Ki kula don Allah Khaleesat kar ki ja mana magana kin dai san wanene Abdul kin san kuma waye Babanki" Khaleesat dai tayi shiru, tasan Umma bata san har nawa bane Dollars din in an canza zuwa Naira, ita dai tayi shiru bata gaya mata ba kar ta kara daga mata hankali. Washegari da wuri Khaleesat ta shirya ta saka Nikab dinta ta fita don zata je canza dollar din nata ta dan yi siyayya, bayan ta canza dalolin taga har ya wuce yanda take tunani a Naira, nan ta fara zuwa inda zata siyi waya, ta siya ma Ummanta da Aunty Farida sabbin wayar Android iri daya na dubu dari da hamsin each, Ganin Baaba Gaje ma bata da waya kuma ba iya amfani da Android zata yi ba ta siya mata karamar waya na dubu ashirin, daga nan ta karasa kasuwa tayi siyayyar yan abubuwan da zata koma USA da shi, ta siya ma siblings dinta twins mata sabbin school bag da schl shoe da socks, ta siya masu atamfofi kala uku each da mayafai da takalma masu kyau da inner wears, jikokin Baaba Gaje ma ta siya masu takalma da inner wears gaba dayansu, pharmacy ta shiga da takardan da aka rubuta magungunan Ummanta ta siya mata na wata biyu duk da tsadar magungunan, kusan Azahar ta koma gidan Baaba Gaje ta tarar su Ummanta basu zo ba. Washegari asabar Khaleesat na shanya kayan jikokin Baaba Gaje da ta wanke, Baaba Gaje kuma na shirin fita kasuwa Ummanta suka shigo gidan tare da Aunty Farida da Siblings dinta yan biyu Islam da Noor that are just 11 years old, da gudu suka tafi suka rungumeta suna mata oyoyo, sosai kannin nata ke kama da ita, Khaleesat was so happy seeing her twins Siblings wanda su uku kawai Ummansu ta haifa, Baaba Gaje tace "Basu tafi islamiyya bane?" Umma tayi kasa da murya tana kallon Gaje tace "Sun ma kwana biyu rabonsu da zuwa, ba a biya kudin wata ba" Baaba Gaje tace "Ikon Allah to Alin ca yayi bazai biya ba kenan?" Umma tace "Cewa yayi in dora masu talla kamar yanda yan uwansu ke yi tunda su ba 'ya yan Gwal bane, dama ba fa shi ke biya masu ba wannan karan ne bani da kudi duk jarin ya lalace shine nace su tambayesa" Baaba Gaje tace "To Allah ya kyauta, amma Ali dai haƙƙin 'ya ya da kyar ya bari ya jiyo kamshin aljanna balle yaje kusa da ita" Ita dai Khaleesat a sanyaye ta kama hannun kannin nata zuwa dakin Baaba Gaje, tana jin Baaba Gaje na cewa "Amma de suna zuwa bokon?" Umma ta sauke ajiyar zuciya tace "Ina fa, islamiyya ma da ya zama dole ba aje ba sae wani boko" Aunty Farida ta girgiza kai cike da takaici tace "Allah de ya kyauta, shi fa bakin cikin bata dora ma yaran talla kamar yanda sauran matansa ke dora ma nasu 'ya yan talla ba yake" Sosai jikin Khaleesat yayi sanyi don duk sanda ta tambayi Ummanta ko kannen nata na zuwa boko da Islamiyya ta wayar Sha'awa sai tace mata eh suna zuwa, ashe basa zuwa, Umma dai bata ce komai ba suka shiga dakin gaba daya, Baaba Gaje tace "Kun ga bari inje kasuwa in dawo" Su Umma suka mata Allah ya kiyaye ta figi gyalenta ta fita daga gidan, Khaleesat ta fiddo duk siyayyan da tayi jiya, daga Ummanta har Aunty Farida kallonta suka tsaya yi, Aunty Farida ta rike haɓa tace "Haka kudin suke da yawa da kika canza? Kuma wa ya aike ki kashe kudi haka mu da muke da sabga a gabanmu Khaleesat? Maimakon ki bada a ajiye maki ko kujeru da setin gado ne da kudaden? Kin de san ko tsintsiya mahaifinki ba lallai ya siya maki da sunan a kai ki dakinki da shi ba ko?" Khaleesat tayi murmushin karfin hali bata ce komai ba, Umma dai ta ma rasa abun cewa, Aunty Farida tace "Ni da kin yi shawara da ni duk baza ki yi wannan siyayyan ba, iyaka ki siyi abinda zaki koma can Amurka da shi, in suka tado da maganar aure me garemu da za a kai ki da shi Khaleesah?" Khaleesat na murmushi tace "Allah zai rufa asiri zuwa sannan Aunty" Aunty Farida tace "Yanzu duk kudin sun kare kenan?" Khaleesat ta girgiza kai tace "Aa, saura dubu dari biyar" Daga Aunty Farida har Umma bude ido suka yi sosai suna kallonta with shock, Aunty Farida ta gyara zama tana zaro ido tace "Har nawa ya baki haka? Ko dai baki da hankali ne" Khaleesat ta kauda zancen ta hanyar cewa "Har fa da kudadena duk na canxa" handbag dinta ta jawo ta bude ta ciro sauran kudaden da suka rage don har wanda Safiyyah ta bata ta canza, ta kirga dubu dari a ciki ta ware, sannan ta kirga dubu dari da hamsin shi ma ta ware, kallonta kawai Umma da Aunty Farida suke, ta ba Aunty Farida dubu dari tace "Aunty kiyi kudin mota da wannan idan zaki koma Lagos sannan ki kara jari" Ta ajiye ma Umma 150k tace "Umma ki rike wannan a biya kudin makarantar su islam da Noor a kuma canza masu Uniform" Umma tace "Ko dai baki da hankali ne Khaleesah? baki ji shawaran da Farida ta kawo bane halan?" Aunty Farida ta mayar mata da 100k din tace "Aa gaskiya ban ga alamar da kan nan ba Umma, ina ga hakoranmu za mu je mu jera mata a gida idan bikin ya tashi...." Khaleesat bata san sanda tayi dariya ba tace "Akwai fa kudade a account dina wanda Abdul ke bani kuma suna da yawa za su isa ayi duk abinda za ayi sannan Aunty" It took Khaleesat almost an eternity to convince her Mother and aunt akan su rike kudin da ta basu, nan kuma bata da wani kudin a zo a gani a account dinta sai miliyan 10 na Abdul da ya ajiye a account din wanda nashi ne ba nata ba, iya kudin foodstuff kawai yake tura mata duk karshen wata sai kuma kudin Uber na zuwa makaranta, sai house rent dinta da yake biya at due time, iya abinda kawai yake mata kenan amma naira biyar dinsa baya bata a matsayin kyauta, instead sai dai ya siya mata kaya masu tsada, monthly kuma yake mata subscription a waya, apart from this bai bata kudi da sunan kudin kashewa, a haka dai ta samu tayi convincing Umma da Aunty Farida suka amshi kudin da ta basu, Aunty Farida na kallon Umma tace "To kinga sai kiyi kaffa kaffa da wayar nan kar su sace maki tunda sun saba maki haka, kin dai ga ba dan karamin kudi aka siyo wayar da shi ba" Umma na kallon Khaleesat tace "To shi Malam din me kika siya masa?" Aunty Farida ta wani kalli yayarta, Khaleesat ma dai kallon Ummanta tayi bata ce komai ba, Aunty Farida ta kyabe baki ta kauda kai, Umma ta kalli Aunty Farida tace "Wai saboda hakki, naga ta siya min waya shima da sai ta nemi abinda ta siya masa kwatankwacin wayar, kuma bashi da wayar shi ma wallahi" Aunty Farida na kallon yayarta da kyau tace "Umma in kinsan zuwa za kiyi ki kyautar da wayar nan da ta siya maki to gwara dai ki bar mata kayanta, ina ce kwanaki can matansa ya siya ma Atamfa yar gadagalle lkcn bikin Salisu ke ya siya maki?" Umma tace "Aa ba ruwanta da wannan Farida, ai ubanta ne, kuma don ta siyi abu ta basa ai ba faduwa tayi ba" Aunty Farida bata sake tanka Umma ba ta fara harhada ma Khaleesat kayayyakin abinci da ta siyo waje daya, Sai kusan la'asar su Umma suka bar gidan kuma har sannan Baaba Gaje bata dawo ba, a boye Khaleesat ta ba Siblings dinta 50k wanda ta saka a karamin jakar Islam tace masu in sun je gida su ba Umma kuma ta ja masu kunni sosai kan daukan sabon wayar da ta siya ma Umma kar su lalata mata. Washegari da safe Khaleesat ta fito wanka wayarta ya fara ring tana dauka taga mutumin nan ne dai, bayan ta daga suka gaisa sannan yace "Hajiya nan da karfe tara da rabi wani driver zai kiraki sai kiyi masa kwatancen inda zai zo ya daukeki ya kai ki airport, don flight dinki zuwa Abuja na karfe sha daya ne, in kun iso Abuja kuma jirgin da zaki bi zuwa Amurka jirgin karfe biyu saura ne" Khaleesat tace "To ba damuwa Nagode" Aunty Farida kadai ce ta zo gidan Baaba Gaje yi ma Khaleesat sallama, Khaleesat bata ji dadin da Umma bata biyo ta ba, duk jikinta yayi sanyi sosai, a haka drivern da zai kai ta airport ya iso, Baaba Gaje ta dinga sa mata albarkan wayar da ta siya mata da abubuwan da ta siyo ma jikokinta, bayan an kai akwatin kayanta cikin mota su Aunty Farida da Baaba Gaje suka rakata har bakin motar, bayan Khaleesat ta shiga motar ta daga masu hannu a sanyaye tana murmushin karfin hali, har cikin ranta bata ji dadin da bata yi sallama da Ummanta ba, a haka suka kama hanyar airport da drivern da ya zo daukarta, suna sauka Abuja karfe daya da minti 40 jirgin su ya tashi. The flight to the United state was so comfortable for Khaleesat in her business class seat, don throughout bacci tayi, karfe hudu saura na asuba jirginsu ya sauka Maryland, It was soo cold in Maryland gashi bata da sweater a kayanta, bayan ta fito da luggages dinta tana duba Uber da zai kai ta gida tana rike da wayar kamar ance ta daga kai taga motar da yayi parking, kallo daya tayi masa sai kuma ta sauke kai kasa, ya karaso har inda take yace "Jirgin ya dade da sauka ne?" Sai a sannan ta kara kallon Sleepy face dinsa, sai kuma ta girgiza kai tace "Aa" Yace "Ohk let me drop you home" Daga haka ya koma gun motarsa ta bi bayansa with both of her luggages, ya bude booth ya amshi daya trolley dinta ya sa a booth, ita ma ta sa dayan, ya zaga ya shiga driver seat, tana jan kafa ta karasa front seat ta bude motar sannan ta shiga tana kallonsa da gefen ido, jinginar da kansa taga yayi da kujeran motar idonsa a lumshe, ta kulle motar gently, after few seconds ta sake kallonsa ga mamakinta sai taga kamar fa bacci yake, kallonsa ta dinga yi, and they seated for almost 3 minutes a haka ita dai bata tashesa ba kuma bata ce komai ba, Vibration din wayarta ne ya sa ya bude ido, ya wara ido ya fara kokarin tada motar, bude jakarta tayi to stop the alarm din da ya sa wayarta ke vibrate, bayan ya ja motar sun bar wajen, still not sounding normal yace "Ya jikin Mama?" Ta sauke idonta tace "Alhamdulillah, You shouldn't have bothered coming tunda akwai Lyft ko Uber" Without looking at her yace "The house key is with me, shi yasa na taho, cause i estimated when u are arriving" Bata sake ce masa komai ba shi ma haka, a haka har suka iso gida yayi parking, ya sake jinginar da kansa da kujeran motar, ita dai ta bude motar gently ta fita, jin fitarta ya sa ya bude ido, shi ma ya sauka daga motar, Entrance din shiga gidan ya nufa ta bi bayansa, Pajamas ne jikinsa sai Jacket da ya saka saboda sanyi, yana isa kofar ya kai hannu aljihu alamar zai ciro makulli, still taga yayi a bakin kofar, ita dai kallonsa kawai take, after some seconds ya juya yana kallonta, zuwa sannan his eyes are very clear gaba daya baccin ya gudu jin babu makulli jikinsa, ko bai gaya mata ba ta fahimci baya tare da makullin gidan, ya ɗan sosa kai yace "I think.... I think, i left the key at where i am coming from, i am sorry about that Halysaah" Sauke idonta tayi without saying anything, ya juya ya nufi motarsa ta bi sa da kallo, sai da ya isa gun motar ya juyo, da sauri ta dauke kanta daga kallonsa, yace "Mu je in dauko makullin, ba wani nisa zuwa can, kinga it's cold out here baza ki iya tsayawa cikin sanyi ki jirani in dawo ba" Bata yi musu ba ta koma gun motar don yanzun ma sanyin take ji sosai, sai da ya shiga sannan ita ma ta shiga, his car was so warm, ya tada motar suka bar garage din, inda yace mata babu wani nisa taga sunyi tafiyar kusan 15 mins basu kai ba, nan taji gabanta ya fara faduwa, lkci lkci take ɗan satan kallonsa ta gefen ido, wani unguwa suka shigo wanda ko wani gida da gate dinsa unlike some houses in US, daga karshe taga yayi parking ba tare da ya kashe motar ba yace "Let me get the keys" Bude motar yayi ya sauka ta bi sa da kallo taga gate din kusa da su ya bude ya shiga, tsaf take iya kallon hadadden gidan dake ta cikin gate din don ba irin gate dinmu na gida bane, ita dai sai bin unguwan take da kallo wanda ko ba a fada maka ba kasan na masu hannu da shuni ne a Amurka din, ba a wani dau lokaci ba sai gashi ya fito da wani Huge Dog dake biye da shi yana shisshige masa, wani faduwa gabanta yayi don a duniya tana mugun tsoron kare, ya duka yana patting Dog din yana masa magana at the same time, wani matashi ne dogo just like him ya fito daga cikin gate din gidan sanye da Pajamas shi ma, Khaleesat ta dinga kallonsa as if ta taɓa saninsa amma kuma bata san sa from anywhere ba, tana kallonsa tana gyara mayafin kanta kar ma ya kalli direction dinta su hada ido da shi, gabanta kuwa sai faduwa yake kamar mara gaskiya, matashin ya jingina da gate crossing his both legs yana kallon Housemate dinta taji yace "Daga ina kake?" Ƙin basa amsa Housemate din nata yayi instead ya mike yana tura masa ƙaton karen don karen tsaf zai ce zai bi sa, Calmly matashin yace "Ina za ka?" Housemate dinta ya kallesa yace "You have any issue with that?" Matashin ya ɗan kalli motarsa calmly yace "Is that a lady in ur Car?" Housemate dinta yayi kamar bai ji sa ba still pushing the Dog to him, Matashin ya sake kallon motar, Khaleesat tayi saurin kauda kanta, tabe baki yayi yace "Enjoy" Daga haka ya ja karen suka koma cikin gidan, Khaleesat da duk taji conversation din nasu taji ranta ya baci, House mate dinta ya dawo cikin motarsa ya kulle without looking at her yace "Sorry for keeping u waiting Halysaah" Yana fara driving ta hade rai tace "Mene yasa bazaka gaya masa i am just ur housemate ba da kuma dalilin da yasa ka kawo ni nan din?" Housemate dinta yace "Never mind, ba wai yana da hankali bane" 07087865788✍🏻 ✨✨HALYSAAH✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 8....... Har suka isa gida babu wanda ya sake cewa komai a cikinsu, yana parking a garage ya bude motar ya sauka, ita ma ta sauka tana satan kallonsa, kofar entrance din parlor taga ya nufa without looking at her, hakan yasa tana tafiya a hankali ta bi bayansa, ya bude kofar parlon ya juya ya kalleta, ita ta fara shiga parlorn sannan shi ma ya shiga ya kulle kofar, dakinta ta tafi bayan ta bude kofa ta juya ta kallesa, kwanciya taga yayi a kan 3 seater ya lumshe ido, ta shiga dakinta kawai ta kulle. Washegari da safe karfe takwas da 'yan mintuna Khaleesat ta fito daga dakinta, zaune ta gansa da text books a gabansa alamar he is studying, yana daga kai tayi saurin dauke idonta daga kallonsa, har ta karaso cikin parlon ta tsaya jikin kujera tana wasa da edge din mayafin jikinta, a hankali tace "Ina kwana" Ya ajiye pen din hannunsa yace "Good morning Halysaah" Still bata dago kanta ba kuma bata fasa wasa da gefen gyalenta ba, yace "How was ur trip?" Ta ɗan kyafta ido tace "Alhamdulillah" Yace "Sorry jiya ban tambayeki jikin Mama ba, i was sleepy hope she is better now?" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa, tace "She is fine Alhamdulillah" Yace "Hope ur mind is now at rest?" Sunkuyar da kanta tayi bata ce komai ba, sai kuma ta ɗan gyada masa kai, wayarsa ne ya fara ring ya dauka sannan yayi picking ya kai kunne, ta ɗaga kanta tana kallonsa, taga shiru yayi alamar yana sauraron abinda ake gaya masa a wayar, after few seconds yace "It should be upstairs then" Daga haka ya katse wayar ya ajiye ya daga kai, da sauri Khaleesat ta dauke kanta daga kallonsa, Yace "Hope nothing Halysaah?" A hankali tace "Kawai, i want to appreciate you, thank you so much, Allah ya saka da alkhairi...." Cikin calm voice yace "No, You need not to Halysaah, iya abinda zan yi ma kanwata na maki ai" Cikin sanyin murya tace "To Nagode Allah ya saka da alkhairi" Ya ɗan yi murmushi yace "To Ameen, so u can be this calm?" Ta wani kallesa, yace "Makarantar zaki tafi baza ki bari ki huta from ur long journey ba?" Ta sauke idonta tace "I am having presentation today" Yace "Ohk then, Allah ya bada sa'a" A hankali tace "Ameen" Ya nuna mata Trolley dinta da ya shigo mata da shi parlon yace "Ga boxes dinki can" Ta kallesu tace "Thank you" Yace "You are welcome" Daga haka ya ci gaba da abinda yake, Sai da ta kai su dakinta sannan ta dawo ta nufi kitchen, Tea kawai Khaleesat ta sha da Cookies sannan ta dauko jakarta zata wuce makarantar, makullin gidan ya mika mata yace "The house key...." Ta tsaya tana kallonsa, sai kuma tace "Ain't u using it?" Ya daga kafada yace "Will sort my self out" Shiru tayi at first, can kuma ta nufesa ta amshi makullin tace "Thank you" Yace "You are welcome" Daga haka ta fita daga gidan ta kullo masa kofar. Khaleesat na tafe tare da Safiyyah dake mata mitar Ya Mustapha yace bata daga kiransa, ita dai Khaleesat tafiyarta kawai take bata ce komai ba, Safiyyah ta tsaya tace "Ohh ga gantalalliya na maki magana ko?" Khaleesat ta tsaya tana kallonta tace "To me zan ce Sophie? Ke kanki kinsan ina da wanda zan aura to menene amfanin in daga wayar Yaya Mustapha? Beside wallahi ko da bani da wanda zan aura ni bazan kulasa ba, ai ana barin halaq ko don kunya" Da wani expression Safiyyah tace "Ban gane ba, as per cewar Surayya cousin sis dinki ce ko kuma kawarki ce? Where did u know her from? Meye hadinki da ita da har za a bar halal don kunya? Can you hear ur self pls? If you are not interested in my cousin brother ba sai kin ta corner corner ba kina kawo zancen da hankali ma bazai dauka ba, meye hadinki da wata Surayya da zaki bar halal don kunya?" Khaleesat tace "Ni dai don girman Allah ki ma bar wannan zancen, Ya Mustapha kuma kiyi ma Allah ki gaya masa i am engage, ni bazan daga kiransa ba" Safiyyah tace "Wallahi bazan fada ba ai kina da baki ki gaya masa da kanki, ke da wa aka yi engaging da zance masa u are engage? Ai as far as i am concern ni ban san wannan batun ba, kawai nasan kina da wanda baki da wani option sai na aurensa, but as time goes on ke kanki zaki san kina da option, za kuma ki ji baza ki iya auren ba sai dai duk abinda zai faru ya faru" Khaleesat ta taɓe baki tace "Kin ga ni yunwa nake ji zan tafi gida, sai gobe in mun hadu" Safiyyah bata tanka ta ba ta ci gaba da tafiya ta bar ta tsaye a wajen, Khaleesat ta bi ta da kallo, to wai ma ta yaya zata daga kiran Ya Mustapha, ita a rayuwarta abinda tasan in an mata bazata ji dadi ba ko by mistake ne bata yi ma wani, ita Safiyyah in ita ce a shoe din Surayya ya zata ji, wannan ai son zuciya ne ma kawai, bin bayanta Khaleesat tayi tace "Ni dai tunda ba mu da aji mu je gida pls ki mana girki i am very hungry and at the same time tired from yesterday's journey" A haka ta samu ta lallaba Safiyyah dake jin haushinta suka kama hanyar gidanta, suna sauka daga Uber ta nufi apartment dinta tana kallon Garage taga babu motar Housemate dinta, does this mean a bude ya bar kofar tunda makullin na hannunta, tana murda kofar taji sa a kulle, to ina ya samu key? ko dai magana yayi aka basa wani makullin, bude jakarta tayi ta ciro key ta bude kofar suka shiga cikin living room din tare da Safiyyah dake biye da ita, Safiyyah ta dinga bin parlon da kallo ta lumshe ido tace "Kai amma wannan turaren Housemate din naki ba dai dadin kamshi ba, the perf is so cool" Khaleesat dai bata ce mata komai ba, ta ajiye jakarta da mayafi ta zauna saman kujera tana ciro wayarta a jaka, Safiyyah ta zauna ita ma kan kujera tace "To kun hadu da Abdul din a Nigeria?" Khaleesat tayi shiru cause kawai taji ita ko maganar Abdul ma bata son ana mata yanzu, ganin yanda Safiyyah ta tsareta da ido, a takaice tace "Eh... me zaki dafa mana pls, wllhi yunwa nake ji" Safiyyah ta mike tace "Toh bari in je in ga what is available in the kitchen" Daga haka ta mike ta nufi kitchen, tana shiga bayan few minutes sai ga ta ta fito, tana kallon Khaleesat da mamaki tace "Kee wai Housemate din naki ne ke maku restocking abubuwa a kitchen haka? Look how ur kitchen is stocked up with costly food items, where is he getting the money to buy all this from?" Khaleesat tace "Baza dai kiyi girkin ba kenan in zo inyi?" Safiyyah tayi dariya tace "No wallahi mamaki nake naga abubuwa masu tsada yake siya, don ni dai nasan kudin da Abdul ke turo maki bazai taɓa siya maki wnn uban abubuwa dake kitchen din nan ba, anya bazan dawo gidan nan ba kuwa Khaleesat? Kinga wasu tsadaddun cookies da drinks da na gani, even the table water in this kitchen ba na yara bane wallahi, the fridge is full to the brim" Khaleesat taki tanka ta tana danna waya, hakan yasa Safiyyah ta juya ta koma kitchen tana kara jaddada anya bazata dawo gidan ba kuwa, Lafiyayyen girki Safiyyah ke yi a kitchen din komai baja baja malam, Sallah kawai Khaleesat tayi a daki ta dawo ta kwanta kan 3 seater tana danna wayarta waiting for the food to be ready, kiran Abdul ne ya shigo wayar hannunta, sosai gabanta ya fadi lkci daya mood dinta ya canza ta hade rai, ta dinga kallon screen din wayar fuskarta babu fara'a tana jiran sai ya kusa katsewa kafin tayi picking call din, dai dai nan taji alamar ana bude kofar parlon, ta mike zaune tana gyara scarf dinta sai ga Housemate dinta ya shigo parlon, sallama yayi ganinta zaune living room din, ta ajiye wayar hannunta ta fasa picking call din Abdul din ta amsa sallamar House mate din nata, yana cire takalman kafarsa yace "Good evening" Ta sauke idonta tace "Ina yini" Yace "Alhamdulillah, bakuwa kika yi?" Double foot wear da ya gani bakin kofar yasa yayi tambayar, tace "Um she is my course mate" Yace "Good" Daki ya nufa, sai a sannan ta kalli wayarta taga kiran Abdul har ya katse tuntuni, she wasn't bothered at all kuma bata yi attempting bin kiran nasa ba ta ajiye wayar kawai, mikewa tayi ta wuce kitchen, tare suka fito kitchen da Safiyyah bayan Safiyyar tayi dishing masu abincin a plate daya, Safiyyah na bin parlon da kallo tace "Ko dai Housemate din naki ya dawo ne kamshin turaren nake kara ji a parlon" Khaleesat ta dau spoon ta fara cin abincin tace "Ko dai kin san sa ne Safiyyah?" Dariya Safiyyah tayi tace "Ina kuwa na san sa, kawai so nake in gansa ne wallahi, irin wannan kayan alatu a kitchen haka, where is he even getting the money shi da ya zo ta scholarship" Khaleesat dai cin abincin gabanta kawai take taki ce mata komai, Safiyyah ta dau spoon ta fara cin abincin ita ma, basu jima da fara cin abincin ba sai ga shi ya fito daga dakinsa, bai kalli direction din da suke ba ya nufi kofa rike da laptop dinsa, Safiyyah ta bi sa da kallo kamar idonta zai fita ya bi sa, ita dai Khaleesat kallo daya tayi masa ta ci gaba da cin abincinta har ya fita daga parlon ya kulle masu kofa, Safiyyah ta ajiye spoon din hannunta tace "To fa, shi kuma haka yake? Ji wani ɗaga shoulders da yake ko kallon inda muke bai yi ba, haka yake maki a gidan dama?" Khaleesat tace "You can be funny Safiyyah" Safiyyah ta hade rai tace "No like seriously haka yake feeling kansa? Ko don abincin da yake ajiye maki na yan gayu a kitchen ne ya ja haka? Ta yaya zai wani wuce mu babu ko Hi, ni fa bana son harkan walakanci" Khaleesat tace "Look Safiyyah ni ba shi ya ajiye min duk abinda kika gani a kitchen ba, shi baya ma zaman gidan nan, jifa jifa kawai nake ganinsa, beside ai mun gaisa da ya shigo kina kitchen, to kuma kallon me zai yi mana don zai fita?" Safiyyah zata yi magana wayarta ya fara ring, mikewa tayi ta dauko wayar, ta ɗan buda ido tana kallon Khaleesat tace "Ke Abdul ne ke kirs" Sosai gaban Khaleesat ya fadi ta ajiye cokalin hannunta ta dinga kallon wayar Safiyyah, Safiyyah ta rike haɓa tace "Ikon Allah, ko ya kiraki baki daga bane? Let me pick dai inji me zai ce" Da sauri Khaleesat ta kamo hannunta zuciyarta na bugawa tace "Safiyyah kar ki ce masa naje Nigeria plss cause bai sani ba wallahi" Safiyyah ta saki baki tana kallonta hangangan, da mugun mamaki tace "Ban gane bai sani ba? To wa yayi sponsoring tafiyar taki? Ina kika samu kudin tafiya" Sosai hankalin Khaleesat ya tashi a lkcn, tana girgiza ma Safiyyah kai tace "Just don't tell him pls, nace maki bai sani ba" Safiyyah da mamaki ya kasa barin ta tace "Ai kiran nasa ma ya katse" Khaleesat taji gaba daya abincin ya fita ranta, sai ga kiransa ya sake shigowa wayar Safiyyah, Safiyyah ta gwalo ido tace "Abdul ne da kirana har sau biyu? Anya lafiya" Khaleesat tayi gathering courage tace "Just pick, in ya tambayeki ni kawai kice masa bani da lafiya yanzu ma kika baro gidana" Safiyyah tace "Ohk" Picking call din tayi ta saka handsfree, ita ta masa sallama ya amsa yace "Ya kike?" Safiyyah tace "I am good" yace "Are you together with Khaleesat?" Babu bata lkci Safiyyah ta sanar masa exactly abinda Khaleesat tace ta gaya masa, ya dan yi shiru at first, sai kuma yace "Tun yaushe ne bata da lafiya?" Safiyyah ta kalli Khaleesat, da sauri Khaleesat tayi mata alamar sati daya da fingers dinta, Safiyyah tace "Yau ina jin sati daya kenan" Daga daya bangaren yace "Sati daya? Me yasa ba a gaya min ba, and what's wrong with her?" Safiyyah tace "Oh ni na zata ai ta gaya maka" Abdul yace "Wani irin rashin lafiya take haka dake hindering dinta from picking calls?" Safiyyah ta wani yamutse fuska jin useless question din da yake yi taki basa amsa tana kyabe baki, ita dai Khaleesat gabanta sai faduwa yake, Yace "Where is she now?" Sounding uninterested with the conversation Safiyyah tace "Tana gidanta mana" Da sauri Khaleesat tayi typing a wayarta sannan ta nuna ma Safiyyah, bayan Safiyyah ta ga abinda Khaleesat ta rubuta tace "Jikin nata dai da sauki sosai fa" A takaice yace "Thanks" Daga haka ya katse wayar, Safiyyah ta ajiye wayarta tace "Tirrrr, ki ji wani magana gatsau gatsau kamar dan daba, ko tashi hankalinsa fa bai yi ba, ni wallahi da ina da yanda zanyi ku rabu rabuwa na har abada da Abdul din nan wallahi yi zan yi, ko kadan bashi da features din miji na gari, babu caring babu tausayi babu affection, so pompous and full of himself always, nonsense and ingredient, wallahi in wani mutumin kirki ne da yanzu hankalinsa ya tashi duk ya birkice min a waya amma kiji yanda yake magana a tsattsaye kamar ubana daga karshe wai Thanks, kamar wanda nayi ma albishir me dadi wai Thanks, ke ki ji fa wai thanks" a hankali Khaleesat tace "Baza ki gane ba Safiyyah, nima naji i am fed up with him, na gaji da halinsa yanzu" Safiyyah ta rike haba da sauri tace "Ke Khaleesat, anya kece ke fadin haka kuwa?" Khaleesat ta wani taɓe baki ta jawo abinci ta fara ci tace "Kawai naji na gaji all of a sudden wllhi" Safiyyah ta sako baki tana mata kallon mamaki, can tace "Ni ba wannan ba ma, Khaleesat wa yayi sponsoring flight dinki zuwa Nigeria?" Khaleesat ta daga kai tana kallonta amma tayi shiru, Safiyyah tace "Kin yi shiru, waye ya biya maki kudin jirgi?" Khaleesat ta sauke idonta kamar bazata ce komai ba sai kuma tace "Housemate dina ne ya siya min Ticket" Safiyyah ta gwalo ido da wani expression na mamaki sosai tace "Ban fahimta ba Khaleesat, Housemate dinki as how?" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "Eh shi ne ya biya min ticket din jirgin...." Khaleesat bata boye ma Safiyyah duk yanda aka yi Housemate din nata yayi sponsoring tafiyarta ba, Safiyyah was totally speechless and Surprise, after few seconds tace "Did you know what flight ticket is saying from USA to Nigeria Khaleesat?" Khaleesat tace "I went to Nigeria in business class and came back in Business class Sophie" Buda baki Safiyyah tayi ba tare da ta san tayi hakan ba tana kallon Khaleesat kamar idanuwanta za su fito, a hankali tace "Business class fa kika ce Khaleesat?" Khaleesat ta gyada mata kai, Safiyyah ta fara bin gidan da suke ciki da kallo that is for the average here in America, da wani Expression tace "Business class? To me yake yi a wannan gidan if he is doing this well that he can afford to pay for business class to and fro? Dama ni tun daga irin abubuwan da na gani a kitchen nasan wannan mutumi might be trying to disguise himself for a reason best known to him, idan ba haka ba why share an Apartment bayan zai iya affording shi kadai ya zauna a gidan, beside zai iya samun wanda ma yafi wannan in a more better area" Ita dai Khaleesat kallon Safiyyah kawai take ganin yanda tayi concluding lokaci daya, Safiyyah ta wani juya ido tace "Or did he have any mission here da bamu sani ba?" Khaleesat ta girgiza kai tace "Daga sanda nayi misplacing makullina ne ya fara kwana gidan nan tunda yasan bani da makulli, amma tun da yayi move in zuwa gidan nan i can count sau nawa ya kwana if i remembered well, baya kwana nan wallahi, ba har na gaya maki ba...." Safiyyah tayi dariya tace "But i am trying to understand me yasa yake zaune a gidan nan, ko dai ya sanki from somewhere ne shine ya dawo nan saboda ke?" Khaleesat tace "Ji fa wani magana, bai san ni a ko ina ba wallahi, ni bamu taɓa haduwa da shi ba, ranan da suka fara zuwa gidan i overheard him asking if his housemate is a Male or female, lkcn ina dakina, kilan he is in a haste to settle down ne shi yasa kawai he opt for this, amma bai san ni ba wallahi" Safiyyah dai tayi wani murmushi tace "Ae shikenan we shall see" Sai kusan karfe bakwai Safiyyah ta bar gidan shi ma saboda azababben kiran da Ya Mustapha ke mata ne, tana mita haka ta bar gidan, bayan Khaleesat ta rakata ta dawo tayi sallahn magarib a nan parlon tana zaune saman darduma bayan ta gama azkar ta dau wayarta don dubawa ko Ummanta tayi mata reply, tun Safiyyah na nan suke Voice chat da Ummanta da kannenta, ganin Umma bata yi reply ba ta gane wayar ya mutu don dama Umma tace mata babu caji wayar ta kusa mutuwa, mamakin Abdul kawai Khaleesat ke yi a ranta, duk da ce masa da Safiyyah tayi bata da lafiya amma har yanzu bai kira wayarta ba, ko ta Whatsapp bai mata magana ba, tana cikin wannan tunanin taji an bude kofar parlon, juyawa tayi Housemate dinta ya shigo, sallama yayi ganinta a parlon, ta dauke idonta ta amsa, ya karaso cikin parlon without looking at her ya tafi inda Books dinsa suke yace "Kawar taki ta tafi kenan...." Khaleesat tace "Ina yini" Yace "Good evening Halysaah" Bayan ya gama daukan text books da zai dauka ya dawo cikin parlon yace "Alright Good night" Ta bi sa da kallo, sai da ya nufi kofa ya sake juyowa yace "Sai da safe" Ta sauke idonta tace "Allah ya kai mu lafiya" Daga haka ya bude kofar ya fita tana jin ya kulle kofar da makulli daga waje. Washegari Khaleesat bata da karatun da za su yi a makaranta, don haka har karfe goma bata fito parlor ba tana kwance, ita har sannan fa ta kasa daina mamakin Abdul don har sannan bai kirata ba, tashi tayi daga karshe ta shiga bandaki tayi wanka ta shirya, wajen karfe goma da minti arba'in ta fito daga dakinta, kwance taga Housemate dinta saman 3 seater yana bacci, kulle kofar da tayi ne yasa ya bude ido a hankali, walking slowly ta karaso cikin parlon, juyawa yayi bayan ya sake rufe idonsa as if murmuring yace "Good Morning Halysaah" Tace "Ina kwana" Bai bude ido ba bai kuma amsa ba alamar ya ci gaba da baccinsa, ita dai ta wuce kitchen. After an hour Khaleesat ta fito daga kitchen bayan ta gama girkin da take, zaune ta gansa a parlon ya dafe kansa, tsayawa tayi tana kallonsa, ya daga kai suna hada ido ta ɗan koma baya tace "Is everything okay?" 07087865788✍🏻 [20/05, 11:33 pm] +234 813 644 0264: ✨✨HALYSAAH✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 9..... Still bai dago kansa ba yace "Tashi na kika yi" Ta ɗan bude ido tana kallonsa tace "How?" Ya koma ya kwanta ya rufe ido yace "With the noise ur utensils were making in the kitchen" At first kamar bazata ce komai ba, sai kuma tace "To ai ba nan ya kamata ka kwanta kana bacci ba" Ya bude ido yace "Ok u intentionally woke me up kenan?" tace "Ni ban ma san kana parlon ba ai..." Murmushi kawai yayi bai ce mata komai ba, tana ɗan kallonsa a hankali tace "I made some breakfast, you can have some" Yace "Ok thanks, baki je schl yau ba?" Tace "Ba mu da lectures" Yace "Ohk, wani school kike?" Shiru tayi tana kallonsa, ya mike zaune yace "University of Maryland Baltimore? Loyola University Maryland? Morgan state University? Stevenson University? Johns Hopkins University?" Tace "Duk kuma a nan garin su ke?" Yace "Ohh, kina gari baki san makarantun dake garin ba?" Ta girgiza masa kai kawai still looking at him, shi dai bai kalleta ba yace "To ke wanne kike zuwa a cikinsu?" Ta sauke idonta tace "Na karshen da ka kira" Ya ɗan yi murmushi yace "John Hopkins kenan? Buh ni ban taɓa ganin ko me kama dake a schl din ba ai" Yayi dariya yace "Just joking kafin ki fara min kuka" Ta wani kallesa, duk wannan abun bai kalli direction dinta ba yana magana ne yana kallon agogon wrist dinsa, yace wani course kike yi?" Tace "Pharmacology" Sai a sannan ya kalleta yace "Really?" Ta gyada masa kai, yace "That's a very good course, year what kike yanzu?" Calmly tace "Year 3" Ya gyada kai yace "Good, Allah ya bada sa'a" Ta sauke idonta tace "Ameen" Yace "Ban yi tunanin makarantar kike ba da na dinga dropping dinki in zan je ai, ko da yake ba lallai sanda zan je kina da Class ba...." Sunan wani lecturer dinsu ya kira mata, kawai ta ɗan yi murmushi tana kallonsa cause he is one of her favourite lecturer, yace "He took us during our Undergraduate Degree, and Master's degree also, that was 3 years back, and he is still among my Supervisors currently...." Khaleesat dai sai kallonsa take, ta kasa hakuri har sai da tace "And you are still a student till date?" Ɗan murmushi yayi yace "I am a Medical Dr, pursuing my PhD on Cardiology" Khaleesat couldn't stop staring at him, Yace "I have been studying since i was a baby" Tace "Amma lecturer kake son zama?" Er dariya yayi yace "Not at all Halysaah...." Khaleesat dai tayi shiru bata ce komai ba tana kallonsa, ya dau wayarsa da ake kira ya mayar ya ajiye yace "Kin ci abincin ne a kitchen naga ban ganki da plate ba as usual?" Ta wani kallesa bata ce komai ba ta juya tayi wucewarta daki, shayi ta sha da cookies a kitchen sanda take girki, bayan ta gama girkin kuma taji bata ma jin yunwan shi sa bata zuba abincin ba, Khaleesat ta koma dakinta da kusan 45 minutes tana duba wani course dinsu ta laptop taji kamar ana knocking din kofar parlor, ta mike ta fito parlorn, tsaye taga Housemate dinta bakin kofar living room din har ya bude kofar, Safiyyah ce ta shigo parlon tana kallonsa tace "Hello" Ya dauke idonsa yace "Hi" Komawa daki Khaleesat tayi, Safiyyah tace "Pls is Khaleesat around?" Yace "Sure...." Dakin Khaleesat ta nufa, shi kuma ya tafi ya ci gaba da karatun da yake a parlor, Khaleesat ta mike tana kallon Safiyyah bayan ta shigo dakinta tace "Why are you looking this way Sophie?" Safiyyah tace "Wallahi kwanan nan zaki ji nayi ma matar can duka a kasar nan" Khaleesat tayi murmushi tace "Me kuma tayi maki again?" Gefen gado Safiyyah ta zauna kana ganinta kasan ranta a bace yake tace "Tun fa da kika je gidan mugun halinta ya ninku akan wanda take min a baya Khaleesat, she is trying all possible best to make the house miserable for me, dama yanzu ta dena ajiye min abinci kwata kwata, cornflakes da Golden morn sai ta boye a dakinta da sunan taje hada ma yaronta ne duk don kar in sha...." Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "To Allah ya kyauta, ko zaki dawo nan?" Safiyyah tace "In dawo nan for what reason? ashe ma riba ta ci kenan idan na bar mata gidan, ai we die together with her in that house, babu inda zan dawo wallahi, kawai rabon ta ci duka ne ba wani abu ba" Lkci daya expression din Safiyyah ya canza daga bacin rai ta kamo hannun Khaleesat tana washe baki tace "Kee naga Housemate dinki ido da ido yau, dama haka yake gayen? Wallahi he is so well flavoured komai yaji, ina masa magana ma ko kallona bai yi ba amma ya amsa min cikin girmamawa, wallahi ya burgeni" Tana blushing ta karasa maganar nata, Khaleesat dai ta saki baki ta kasa cewa komai, can ta kalli kofar dakinta da sauri don ta tabbatar a kulle yake kar ace yana jiyo Safiyyah, sai kuma tayi kasa da murya fuska daure tace "Meye haka Safiyyah what if yana jin ki?" Safiyyah tace "Wallahi raina a bace yake amma yana bude kofar kawai na mance da abinda er iskar matar can ta min, a very calm gentleman, yace min Hi nace Hello... kuma kuna Hausa da shi ko turanci ku ke? Ni sai nake ga kamar ba bahaushe bane ba fa" Khaleesat ta hade rai sosai tace "Don Allah ki rufa mana asiri Sophie, What's all this?" Safiyyah tayi dariya tace "Ni dai kinyi girki? Don wallahi yunwa nake ji" Khaleesat ta mike ta nufi kofa ta fita daga dakin, a corridor ta gansa zai shiga dakinsa, bai kalli ma wanda ya bude kofa ba yayi shigewarsa daki, Khaleesat ta tafi kitchen ta dibar ma Safiyyah abincin da ta girka, jin alamar har ya fito daga dakin nasa ta dawo parlor ta tsaya sai gashi ya shigo parlon, makullin motarsa taga ya dauka da wani littafi, ya daga kai suka hada ido ta fara kame kame tace "Ain't you eating the food?" Yace "Oh, ok na manta" Kitchen din taga ya nufa ta bi sa da kallo, sai da ya shiga sannan ta bi bayansa zata gaya masa kar ya bar mata plate bai wanke ba, tsaye ta gansa kusa da abincin ya dau spoon ya bude tukunyar sannan ya debi shinkafar kadan ya kai baki, kallonsa kawai take da mamaki, ya juya ya kalleta yace "Bad habit right?" Sake dibar abincin yayi ya kai baki, daga haka ya rufe tukunyar yace "Kinga ni ba yunwa nake ji ba, I am full" Ta dinga kallonsa, bata san sanda tace "Ko in zuba maka ka tafi da shi?" Ya bude fridge ya ciro bottle water yace "Aa in na dawo anjima zan ci" Daga haka ya fita daga kitchen din ya nufi kofar living room ya bude, sai a sannan ya juya, ta dauke idonta, yace "See yah" Fita yayi ya kulle kofar daga waje. Sai wajen karfe shidda na yamma Khaleesat ta raka Safiyyah zata hau Uber da tayi ordering, Safiyyah na kallonta tace "Ya Mustapha dai ya hakura dake, jiya nake gaya masa gaskiya kina da wanda zaki aura a gida, don nima na gaji da damuna da yake yi shi sa kawai na gaya masa, ai ko ina gaya masa yace to shikenan dama tun farko ai da kin gaya masa he will understand" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "To ai kinga gwara haka" a haka suka rabu Khaleesat ta koma cikin gida, har goma na dare bata ji shigowar housemate din nata ba hakan yasa ta gane bazai dawo gidan ba ranan. Washegari da safe ta shirya ta tafi makaranta, bata dawo gidan ba sai kusan karfe hudu na yamma, tana shiga living room ta gane ya dawo gidan da bata nan, bedroom dinta ta wuce bayan tayi wanka tayi sallah ta canza kaya ta fito kitchen zata yi ɗan wake don shi ne a ranta, bayan ta gama hada duk ingredients din taji an bude kofar parlor, ta dai ci gaba da abinda take, kitchen din ya shigo ya ajiye ledan hannunsa yace "Good evening Halysaah" Tace "Ina yini?" Yace "Lafiya lau, Are you baking?" Ta kalli flour din da take kokarin kwabawa tace "No" Yace "What are u using flour for?" Bata yarda su hada ido ba tace "Dan wake" Da mamaki yace "Meye shi?" Ta wani kallesa ganin da gaske jiran amsarta yake tace "Dan waken ne baka sani ba?" Yace "Ban san shi ba" Tace "Toh zaka gansa" Turning stick ta dauko ta fara kwabin danwaken shi dai yana tsaye yana kallo, yace "Hey, why did it change to that color? Ko dai ba flour bane?" Ta ɗan kallesa amma taki basa amsa, yana ta kallo with astonishment har ta gama kwabin, sannan ta wanke hannu ta fara saka dan waken a ruwan dake tafasa kan gas, shi dai kallonta kawai yake, can yace "To haka ake cin sa?" Tace "Aa da bread ake ci" Sounding amused ya kalli sauran bread din dake a kitchen din yace "Really?" Bata san sanda tayi murmushi ba batare da ta sake ce masa komai ba don taga da gaske ya yarda da Bread za a ci ɗan waken, he couldn't stop looking at her and the food har ta gama, ya ga ta soya man gyada, sannan tayi dishing din abincin a plate, ta saka eggs din da ta bare a gefe, ta dauko roban yaji, yace "Dama wai wannan abincin ne? To ai na san sa when i was a kid, idan munje wajen Grandma dinmu tana mana" Without looking at him tace "Da ka girma ne ka dawo America ka mance sa kenan" Dariya yayi ya karasa cikin kitchen din yace "Ohk, Can i taste some inji yanda yake?" Komawa gefe tayi bayan ta saka cokali a danwaken, ya dau cokalin ita dai kallonsa kawai take har ya ɗan juya ɗan waken ya debi seed biyu ya kai baki, she couldn't stop looking at him yana tauna abincin gently as if trying to figure out the taste, can ya karyar da kai yace "It's nice, i like it, i still remember the taste, it's nice" Murmushi kawai tayi, ya sake diban abincin ya kai baki, tace "To kaje da shi, i will make another one" Yace "Aa bazan iya cinyewa ba ai" Yana fadin haka ya dauko wani plate din ya debi ɗan kadan a ciki yace "Thank you" Ta karasa ta amsa cokalin a hannunsa ta kara masa ɗan waken ta saka masa kwai daya, ya kalleta ya ɗan bude ido yace "Thanks Halysaah, but seriously I can't finish all this" Tace "Eat and remain" Ruwa ya dauka a fridge ya fita daga kitchen din. Khaleesat na idar da sallan Isha'i ta fito parlor zata dafo black tea don tana son tayi karatu har zuwa karfe dayan dare, tunda ta shiga daki daxu da yamma bata sake fitowa ba sai lkcn, bacci ta tarda Housemate dinta yake yi a 3 seater, da mamaki take kallonsa ganin wai bacci yake bayan Isha'i, ita bata ma san yana gidan ba sai yanzu da ta fito, kallon wayarsa dake gefensa tayi ganin yana haske, ta leka screen din taga an rubuta A-jay, kiran na katsewa taga 5 miss calls aka yi masa, kamar ta tashesa sai kuma dai bata yi hakan ba, ta dau wayar kawai tana dubawa taga babu password balle pin a jiki, cire wayar tayi a silent mode sannan ta mayar inda ta dauka tayi wucewarta kitchen, ta gama dafa shayi ta fito parlon kenan taji wayar ya fara ringing loudly, da kyar ya bude idanuwan sa, ita dai ta koma kusa da kofar kitchen din ta makale a jiki, ya ɗan kalli wayarsa ya jawo yana duba screen din, ɗaga kiran yayi ya kai kunne yayi shiru har sannan yana lullumshe ido, can ya ja tsaki ya ajiye wayar sannan ya mike zaune, har sannan bai ganta ba ita ma bata bar jikin kofar da ta makale ba, mikewa tsaye yayi daga karshe yana lumshe ido, gani tayi kamar baccin yake yi a tsayen, ta wara ido tana kallonsa with shock , sai da yaga ya kusa faduwa sannan ya bude idonsa sosai, ta kai hannu bakinta saboda dariyar da taji ya taho mata, tafiya yayi ya isa jikin pillar dake parlon ya jingina ya rufe ido, kasa daina kallonsa tayi da mamaki, he stood there for almost 3 minutes yana bacci, ringing din wayarsa ne yasa ya bude ido da sauri as if frightened, kitchen ta shige don bata son yin dariyar da ya taho mata a wajen, sai a sannan ya ganta bayan ta shige kitchen da sauri, ya fara bin parlon da kallo as if trying to understand what was happening, lkci daya idonsa yayi clearing gaba daya ya fara sosa kai, at first bai yi niyyar bin ta kitchen din ba, can kuma dai ya nufi kitchen din, ta ajiye kofin shayin hannunta ta dafe cabinet tana dariya ciki ciki, tana ganinsa ta hade rai tana juya shayinta da cokali as if nothing happened, fridge ya bude ya dau ruwan gora yana kallonta yace "You are still awake?" Ta ɗan kallesa tace "To karfe nawa ne yanzu da zan yi bacci, as if i am you" Bai ce komai ba ya fita daga kitchen din, murmushi tayi ta bi sa da kallo, daukan shayin tayi ta bi bayansa, taga ya dau makullin motarsa da waya without looking at her yace "Good night Halysaah" Bata san sanda tace "To kar fa kaje kana driving bacci ya dauke ka a kan steering" Bai kalleta ba sai murmushi da yayi kawai ya nufi kofa, ta bi sa da kallo har ya fita sannan ya kulle kofar ta waje, karasawa kusa da window tayi ta ɗan bude curtain kadan tana kallonsa har ya shiga motarsa a garage yayi reverse, sai da ta daina hangen motarsa sannan ta sake curtain din a hankali, tafi minti uku a tsaye wajen ta jingina da window, daga karshe tana tafiya a hankali ta wuce dakinta bayan ta kashe wutan parlon..... Washegari Khaleesat na sauka daga Lyft bayan ta dawo school taga motar Housemate dinta heading toward the garage, kafin ta karasa apartment din nasu har ya shiga ciki, murda kofar tayi taji a bude ya bar mata alamar ya ganta shi ma, tana shiga parlon yana fitowa daga kitchen rike da Lemon gwangwani me sanyi, ya karaso cikin parlon yace "Are you just coming back from school?" Gaishesa tayi, yace "Good evening Halysaah" Bedroom dinta ta wuce ta bar sa a parlon, it's almost 6pm na yamma kuma Safiyyah ce ta bata masu lkci tana mata bayanin wani course dinsu da tace bata ganewa, wanka Khaleesat tayi ta sauya kayan jikinta zuwa kananun kaya sannan ta saka hijab ta fito parlor, yana parlon har sannan yana operating laptop dinsa, ganin zata shiga kitchen yace "Ki bari ki hutu, zan fita sai na siyo abinci" Khaleesat ta kallesa tace "I am cooking noodles" Yace "Ohk then" Tana fadin haka ta wuce kitchen, Ya mike ya wuce dakinsa da laptop dinsa, cikin mintunan da basu da yawa Khaleesat ta gama dafa noodles din da take, ba da yawa ta dafa ba don bata san ko zai ci ba, zata yi dishing din abincin a plate taji ana knocking kofar parlor, ta ajiye plate din hannunta sannan ta fito daga kitchen din, Housemate dinta ta gani har ya fito shi ma to check on who is at the door, amma ganinta kawai ya juya ya koma dakinsa, karasawa tayi ta bude kofar, lkci daya taji komai ya tsaya mata cak ta dinga kallonsa babu ko kiftawa kamar ranan ta fara ganinsa, Yana kallonta daga sama har kasa yace "Meye kike kallo na haka Malama?" Tayi wani yake zuciyarta na bugawa tana in-ina da kyar tace "Ya Abdul, I.. I.. was surprised, san..nnu da zuwa" Da sauri ta juya ta koma parlon, ya bi bayanta yana duba wayarsa dake vibrate a hannunsa alamar ana kiransa, ita dai ta koma bayan kujera ta tsaya kamar munafuka tana kallonsa zuciyarta na bugawa sosai, kana ganinsa kasan ba a lkcn ya shigo America ba, probably tun daxu ya shigo ya sauka hotel, ya ɗaga kiran da ake masa ya kai kunne, tana ganin haka ta juya ta nufi corridor din dakunan apartment din tana waige waige, ganin attention dinsa na kan wayar da yake ta bude kofar dakin Housemate dinta ta shiga da sauri ta kulle kofar, Housemate dinta ya juya yana kallonta da mamaki, gaba daya a rude take ta nufesa tana yarfe hannu ta duka kusa da shi, ya mike still looking at her with surprise yace "Are you alright Halysaah?" 07087865788✍🏻 ********************** ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** ************************* ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels WhatsApp Number: 08138873799 Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafinmu ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ************************** [20/05, 11:33 pm] +234 813 644 0264: ✨✨ HALYSAAH ✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 10..... Khaleesat ta gyada masa kai tana rufe bakinta da hannunta murya can kasa tace "Plss i have a visitor, i want u to plss pretend you are not staying here, just pretend u came to drop some books for ur Female friend living here plssss" Kamar zata yi kuka ta kare maganar tana kallonsa, yayi shiru shima yana kallonta at first, sai kuma yace "As in how Halysaah?" Ta marairaice masa tace "Kawai dai kayi kamar ba a gidan nan kake ba don girman Allah ka rufa min asiri, u know my former housemate mace ce, act as though u are her friend, kayi kamar wajenta ka zo pls, don Allah ka taimake ni" Bata jira cewarsa ba ta mike ta juya da sauri ta fice daga dakin kafin Abdul ya biyo ta, ya bi ta da kallon mamaki baya ko kiftawa, can kawai yayi murmushi ya zauna ya ci gaba da abinda yake yi a Laptop dinsa, parlor Khaleesat ta dawo suka kusa cin karo da Abdul da ya nufo corridor yace "Me kika je yi a ciki? You didn't even get me something to drink" Ta ɗan yi murmushi a hankali tace "Why didn't you let me know u are coming? Me yasa baka gaya min zaka zo ba?" Yace "Sai na gaya maki in zan zo? Ko ke zaki biya min ticket din jirgin?" Ta girgiza kai cikin sanyin murya tace "Aa ba haka nake nufi ba, ya hanya?" Yana kallonta daga sama har kasa yace "What is wrong with you, why were you sick?" Ta sauke manyan idanuwanta kasa a hankali tace "I don't know too, but i am much better now, naji sauki Alhamdulillah" Yace "Rashin lafiyar ne yasa kika dena daga kirana all this while?" Ta marairaice masa tace "Don baka san yanda nake ji bane a sannan, let me get you water to drink" Daga haka ta wucesa da sauri, ya bi ta da kallo har ta shiga kitchen, Khaleesat ta jingina jikin cabinet din kitchen din ta dafe kirjinta that was heaving so fast, after few seconds ta sauke numfashi sannan ta dau tray ta bude fridge ta dauko ruwa da lemo da glass cup sannan ta fito daga kitchen, zaune ta gansa a parlon yana danna wayarsa, ta karasa ta duka gabansa ta ajiye masa ba tare da ta bari sun hada ido ba, shi dai tunda ta fito kitchen din yake bin ta da ido, ta zauna kan carpet ta tankwashe kafarta ba tare da ta bari sun hada ido ba tace "Ya su Mumy da Daddy?" Jin yayi shiru ta daga idanuwanta ta kallesa taga kallonta kawai yake, a hankali ta sauke idonta kasa, yace "Duk kwana biyun nan kin canza Baby, you don't look critically ill da har zaki kasa daga kirana, menene yasa kika dena kirana kuma idan na kira ki ki dagawa? Common WhatsApp kin dena min magana yanzu" Ta kasa kallonsa, tana wasa da gefen hijab dinta a hankali tace "To kwanan nan sai kayi ta min fada ta waya baka considering dina, ga kuma course dinmu da wahala ka sani" Ita kanta ta rasa dalilin da yasa hawaye ya cika idonta, He let out a sigh har a sannan yana kallonta, sai kuma ya dagota sitting her down by his side, gabanta ne ya fara faduwa, in da akwai abinda ta tsana kuma take fargaba a rayuwarta bai wuce Abdul ya zo America wajenta ba, duk da yawanci zuwan da yake it's either tare da Mom dinsa or his Dad, amma duk da haka a dar dar take da shi saboda wasu abubuwan da ya tsira wanda a baya baya mata haka, duk zuwansa kasar sai ta kirko wani abu da zai maidata unhealthy wani lkcn har sai an kai ta hospital, ita da tasan zai kamo hanya ya taho da bata fara ce ma Safiyyah tace masa bata da lafiya ba, yana caressing fingers dinta yayi kasa da murya yace "But you know i love you Khaleesah, ke ce kike jawowa nake maki fada a ko da yaushe" Ita dai bata ce komai ba hawayen dake makale idonta ya gangaro bisa kuncinta, ya kai hannu yana goge hawayen a hankali yace "Ohk, but you know i love you so much right?" ta gyada masa kai kawai, a hankali yace "Housemate dinki fa? Is she around?" Sosai taji gabanta ya fadi, taki barin su hada ido tace "No ban sani ba, i saw she had a visitor daxu ya zo nemanta, probably her friend...." Yana kallonta yace "Friend? Namiji kenan?" Khaleesat ta gyada masa kai, lkci daya ya hade girar sama da ta kasa yace "Yaushe ta fara kawo namiji gidan? When did that start?" Khaleesat tayi karfin halin cewa "Dama tana kawowa time to time ai but not frequently, sai in kilan sun kawo mata reading materials ko bata da lafiya sun zo dubata" Yace "Kuma mazan na kwana a nan?" Khaleesat ta hadiye wani abu da kyar tace "Ni ban sani ba gaskiya, tunda ina dakina always a kulle ai" Kallonsa tayi to cut short the conversation tace "Na dafa noodles yanzu bari in kawo maka kar ya huce" Tana fadin haka ta mike da sauri zuciyarta na bugawa, dai dai nan Housemate dinta ya fito daga dakinsa, Khaleesat taji zuciyarta ya kusa shigewa cikinta tsabar kidimewa, tayi saurin dauke kai tayi hanyar kitchen, Abdul ya juya jin an bude kofar daki, hada ido suka yi da Housemate din nata da ya shigo parlon yana tafiya slowly waya kare a kunnensa duk da ba magana yake a wayar ba hannunsa daya rike da wani Textbook, idonsa kuma na kan Abdul, hannu ya daga masa calmly yace "Hello" Abdul ya bi sa da kallo babu ko kiftawa without replying to his Hello, shi dai Housemate din nata yana tafiya calmly ya nufi kofa ya fita daga parlon, tuni Khaleesat har ta shige kitchen hankalinta a tashe ta dafe kirjinta tace "Na shiga uku....." A haka dai ta fara zubo noodles din a plate, cike da karfin hali ta dawo parlon, Abdul dake ta kallonta yace "Who is he Baby?" Khaleesat ta ɗan yi fari da ido tace "Ni ban ma taɓa ganinsa ba sai yanxu, Nancy ya kawo ma littafi ina ga" Abdul ya mike yace "Ta yaya zaki dinga rayuwa under same roof da wani gardi Baby? Yaushe Nancy din ta fara shigo da samari gidan nan? All this while dama yana cikin gidan nan?" A hankali Khaleesat tace "Na fa ce maka ban taɓa ganinsa ba, i have never seen him before sai yanzu" Ajiye abincin hannunta tayi cike da karfin hali tace "In dafo maka black tea?" Komawa yayi ya zauna yaki cewa komai, kana ganinsa kasan he is boiling inside, ita dai ta juya tana tafiya kamar munafuka ta koma kitchen, mikewa yayi ya bi bayanta har zuwa kitchen din yace "Ta yaya wani banza can zai dinga shigowa yana kalle min ke anyhow Khaleesah?" A hankali Khaleesat tace "Ya Abdul kar ka manta communal living muke a gidan nan, this is America.... this isn't my apartment alone, bazan iya cewa ga wa enda za su shigo gidan ba tunda ba gidana ni kadai bace" Tsawa ya mata yace "And so what??? An gaya maki bazan iya kama maki hayar gidan ke kadai bane? Banda kince kina tsoron zama ke daya a gida do you think u will be sharing an Apartment with anyone in America? Do u think I can't afford a full apartment for you??" Har jikin Khaleesat ya fara rawa ganin how fiercely he was speaking to her yana huci, ga idanuwansa sun fara sauya launi, sosai take jin tsoron Abdul ita kam, hawaye ya fara gangarowa idonta muryarta na rawa tace "Ka fara kuma ko?" Kamo hannunta yayi fuskarsa a murtuke suka fito daga kitchen din, ta fashe masa da kuka a hankali har suka dawo cikin parlon, cike da fada yace "Ya bazan fara ba naga wani katon banza under same roof with you? Me yasa tun tuni baki gaya min Housemate dinki na shigowa da gardawa cikin gidan nan ba in samar maki other alternative? Me yasa baki da hankali baki da tunani ne ke a rayuwarki?" Zaunawa tayi ta fashe da kuka sosai ta hade kanta da kujera, ya zauna yana huci, ita dai kuka kawai take tana shessheka, after few minutes ya koma kusa da ita ya dagota drawing her closer to him kamshin turarensa ya cika mata hanci, nan da nan ta hadiye kukan da take tana zare ido, Gently yake caressing dinta murya can kasa yace "I am sorry Baby, amma da kin gaya min da na samar maki wani apartment din ai...." Ta fara kokarin komawa baya tana son kwace kanta daga hannunsa, kin saketa yayi a fusace yace "Why do u always act like a Bush gal Khaleesah? Har yanzu rayuwar Ghetto bazai fita a kanki ba? What is the meaning of this nonsense?" Ta ki barin su hada ido, da kyar tace "To ai... This is a promise you made, amma kuma sai ka dinga..." Cikin tsawa yace "So f what if i break the promise? Ko ance maki tsoronki nake ne? Ko kuma wani ne zai aure min ke dama?" Ta marairaice masa kamar zata yi kuka tace "Ni dae bari in kawo maka black tea" zata mike ya fixgota har sae da fado kansa, ya fige hijab din jikinta yace "Naga alamar kin ma maida ni wani gara don kinga ina biye ki" Ta takure waje daya wasu hawayen na taruwa idonta taki yarda su hada ido tana kokarin kwatar kanta daga grip dinsa, skirt karami ne sosai jikinta sai half vest shi sa ma take ta yawo da hijab tun daxu da ta dawo schl, ya sake fixgota sosai jikinsa, kuka ta fara yi muryarta na rawa tace "Don Allah ka bari plss, this wasn't our deal, you are not keeping to ur promise" Kallonta ya dinga yi saboda yanda tayi provoking dinsa, duk da shi bai yi niyyar mata komai ba da ya wuce ya lallasheta amma tsabar yanda ta hasala shi sai ya fara kokarin kissing dinta, ƙin yarda tayi tana kiciniyar kwace kanta tana kuka, House mate dinta ne ya shigo parlon a lkcn, ya kalli yanayin da suke da kuma yanda take struggling din kwatar kanta daga jikinsa, direct ya nufi cikin parlorn har inda suke without a second thought ya cakumo Abdul yana kallonsa da kyau "Hey, this is America guy, what sort of molestation is this??" Mikewa Abdul yayi yana kallonsa da wani irin Expression na mamaki, bai yi wata wata ba kawai ya sauke masa fist dinsa a kirji har sau biyu, ya wani cakumosa yace "Are you insane? How dare you??" Khaleesat ta zaro ido ta mike cikin tashin hankali ta riko Abdul tana zaro ido with shock, lkci daya ta kalli Housemate dinta da ya tsaya yana kallon Abdul baya ko kiftawa kuma bai yi attempting rama abinda yayi masa ba, da kyar tace "He is my boyfriend, I don't think u have any problem with this, who are you? And where do you know us from? You have no right to intrude!" Housemate dinta dake kallonta ya sauke idonsa kamar bazai ce komai ba, sai kuma calmly yace "My bad! And i am sorry, i thought u were in danger, i am only here to drop some books, sorry about that plss" Khaleesat ta wani kallesa tace "Do i know u from anywhere that warrant u intruding?" Ya girgiza kai yace "Not at all... I am sorry" Kallon Abdul yayi, bowing his head gently at the same time yace "I am sorry, dude" Daga haka ya ajiye book din hannunsa ya juya ya nufi kofar parlon ya fita waje, that was when Khaleesat realized she was half dressed all this while, dukawa tayi ta fara kuka a hankali ta hade kanta da kujera tana jin kanta na wani irin sara mata, wani kallo Abdul yayi mata yana huci, kawai ya dau wayarsa ya nufi kofa ya fice daga parlon kamar zae tashi sama, ta bi sa da kallo hawaye na sauka idonta, mikewa tayi da sauri ta nufi window tana duba waje taga babu motar Housemate dinta har ya tafi, sae Abdul da ta hango yana tafiya down the street, dawowa parlon tayi tana goge hawayen dake sauka idonta ta dau Hijab dinta ta wuce daki da sauri, har wajen karfe tara na dare Khaleesat ta kasa tashi daga saman darduman da take zaune ga wani ciwo da kanta yake mata, jawo wayarta tayi a hankali, tun daxu take son kiran Abdul amma ta kasa kiransa saboda tsoro, daga karshe tayi gathering courage tayi dialing numbersa har ya katse bai daga ba, ta sake kira nan ma bai ɗaga ba, tasan ba lallai ya ɗaga ba dama, ajiye wayar tayi ta kwanta gefen gado wasu sabbin hawayen na zuba idonta. Da safe duk da yanda Khaleesat ke jin ta wani iri kamar zata yi rashin lafiya haka nan tayi shirin makaranta ta saka Facemask dinta sannan ta bar gidan, ta kusa awa daya a makarantar kafin Safiyyah ta shigo, Khaleesat ta zauna gefenta tana kallonta tace "Why are you sitted here Khalee? Is the lecturer not around?" Khaleesat ta sauke idonta bata ce mata komai ba, Safiyyah ta sauke Facemask dinta ganin swollen eyes dinta cike da damuwa tace "Subhanallahi, what is wrong Khaleesat? Kukan me kika yi? Ko jikin Mama ne?" Khaleesat ta girgiza mata kai hawaye na taruwa idonta, hankalin Safiyyah ya tashi tace "Innalillahi, don Allah me ya faru? Is everything ok?" Khaleesat ta girgiza mata kai tana goge idonta a hankali tace "Abdul ne ya zo" Safiyyah ta gwalo ido tace "Abdul kuma?? Yaushe? Kuma me ya maki kike kuka?" Khaleesat tace "He came yesterday evening" Safiyyah tace "Ji jaraba, to me ya zo yi? Kuma me ya faru da ya zo din?" Safiyyah na jefa mata wannan tambayar taji hankalinta ya tashi lkci daya, let it not be what just crossed her mind now, tunda tasan ko wanene Abdul, ta kamo hannun Khaleesat da sauri cikin tashin hankali tace "Ko ya maki wani abu ne? A gidanki ya kwana???" Khaleesat ta girgiza mata kai a hankali tace "A'a" Safiyyah bata san sanda ta sauke wani ajiyar zuciya ba, can tace "Toh meye kuma na kuka don ya zo, ko rashin mutuncin da ya saba ya shuka maki?" Khaleesat na shessheka a hankali tace "He met my Housemate" Safiyyah ta bude baki tace "Kai don Allah, cikin gidan ya gansa? To ke ma dai wallahi baza ki iya karyan kare kanki ba kice masa kawai baƙon Housemate dinki ne shi tunda bai san Nancy ta tashi a gidan ba, to sai kika ce masa me?" Khaleesat na gyada mata kai tana goge hawayen da yaki tsaya mata tace "Haka nace masa, amma ai kin sansa kinsan halinsa, he even fought with my Housemate" Safiyyah ta zaro ido tace "Fight? To akan wani dalili?" Khaleesat tace "Kema kinsan yanda yake yi ai Sophie, kawai wai zai yi kissing dina ni kuma naki yarda sai ga Housemate dina ya shigo shine yayi approaching dinsa seeing what he was doing to me, hakan da yayi ne yasa Abdul yayi fada da shi, he hit him so hard" Safiyyah tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, to Housemate din ya rama ne?" Khaleesat ta girgiza kai a hankali tace "Bai rama ba, kawai hakuri ya basa" Safiyyah tace "Wallahi in ance min Abdul na shan giya ni bazan musa ba, cause his actions portray that, kawai daga ganin mutum ka fara fada da shi kamar wani ɗan daba, kuma in banda rainin wayo zai zo me yasa bazai ce maki zai zo ba kawai sai dai ki gansa kamar an jefosa a gidan?" Khaleesat tace "Wai fa ce masa da kika yi bani da lafiya shine yasa ya taso ya taho, da na sani da ban ce kice masa haka ba" Safiyyah ta bude baki tana kallon Khaleesat don ita ma sai a sannan taga da basu ce masa haka ba tunda ba isasshen hankali ke garesa ba, Safiyyah ta sauke wani ajiyar zuciya tace "To yanzu Housemate din naki fa? Hope he didn't hurt him?" Khaleesat ta fara goge wasu sabbin hawayen idonta tace "Kinsan menene ya dameni?" Safiyyah ta girgiza kai, a hankali Khaleesat tace "Maganganun da na gaya ma Housemate din nawa, meanwhile he was just trying to be protective ganin kamar Abdul molesting dina zai yi, ni kuma abinda yasa nayi masa haka don kar Abdul din ya zargi mun san juna da Housemate din nawa, cause i told him frnd din Nancy ne kuma ni ban taba ganinsa ba" Safiyyah da ta kasa rufe baki tace "Wasu irin maganganu ki ka gaya ma Housemate din naki?" A hankali Khaleesat ta gaya mata duk bakaken maganganun da ta gaya ma Housemate din nata, Safiyyah ta dinga mata wani kallo cike da takaici, can tace "To shi katon banzan da kika fadi bakaken maganganun a kansa hope yayi considering dinki at the end of everything?" Khaleesat ta girgiza kai tace "He walk out on me, na kirasa sau biyu jiya yaki dagawa, kuma har yanzu bai kirani ba" Safiyyah ta ja tsaki tace "In ma ya ɗaga shi babban ɗan iska ne, kada Allah yasa ya daga, kuma shi Housemate din naki kun sake haduwa bayan abinda ya faru jiya?" A hankali Khaleesat tace "Shi ma tunda ya bar gidan jiya har yanzu bai dawo ba" Safiyyah tace "To wallahi ki kirasa don mutumin nan yafi karfin walakanci a wajen ki" Khaleesat ta fara wani hawayen tace "I don't have his Number" Safiyyah tace "Ban gane baki da lambarsa ba?" Khaleesat tace "Wallahi, even when i was going to Nigeria kawai hadani yayi da wani mutum ya bani number mutumin amma bai bani lambarsa ba" Safiyyah tayi shiru, can ta sauke ajiyar zuciya tace "Ki tashi kawai ki koma gida kilan Allah zai sa ya dawo sai ki basa hakuri, Abdul kuma kar ki kuskura ki sake kiransa in ba haka ba in tsine maki wallahi" Duk da bakin cikin da Khaleesat ke ciki sai da ta ɗan yi murmushi, a haka ta koma gida ta bar Safiyyah a school din bayan Safiyyah tace ta kirata duk abinda ake ciki, in ma Abdul din ne ya sake dawowa gidan ta kirata zata taho..... Throughout ranan Khaleesat bata ga Housemate dinta ya dawo gidan ba har karfe takwas na dare, ta rasa me yasa ta kasa samun nutsuwa hankalinta yaki kwanciya, ko tunanin Abdul bata saka a ranta ba tun bayan barin ta school daxu da safe da Safiyyah tayi encouraging dinta kar ta sake kiransa, but she was so restless ganin Housemate dinta bai zo gidan ba, she wish she had his number ta kirasa, wajen karfe goma saura wayarta ya fara vibrate ta jawo a hankali tana duba screen din taga Safiyyah ce, Safiyyah ta kirata yayi sau 6 daga barinta school da safe har zuwa yanzu, Safiyyah tace "Is he back Khaleesat?" Khaleesat ta girgiza mata kai a hankali tace "A'a bai zo ba" Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya tace "Kilan sai gobe zai zo gidan, ki kwantar da hankalin ki pls" Khaleesat dai tayi shiru bata ce komai ba, Safiyyah tace "Plss kar ki wani damu kanki da yawa kawata, hope kin ci abinci?" Khaleesat tace "Na ci" Safiyyah tace "To kiyi kwanciyarki, good night" A haka suka rabu, Khaleesat ta ajiye wayarta ta lumshe ido duk da tasan ba baccin zata yi ba....... *Continue making your payment before the end of free pages fanss, in ba haka ba aji shiruuu...*😃 07087865788✍🏻 [20/05, 11:38 pm] +234 813 644 0264: ✨ ✨HALYSAAH✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 11..... Tun da gari ya waye Khaleesat ta kira Safiyyah tace mata bazata shigo school ba don tana son tayi bacci, Safiyyah tasan sarai bata yi baccin kirki ba kenan daren jiya, har mamakin yanda Khaleesat ta iya saka abu a rai ya dameta take, Safiyyah tace "Shikenan kawata, after our classes zan zo ko da yamma ne in sha Allah" a hankali Khaleesat tace "To Allah ya kai mu, Nagode" Daga haka suka yi sallama ta ajiye wayar ta koma ta kwanta. Wajen karfe hudu na yamma Khaleesat ta tashi daga baccin da take, bandaki ta shiga ta wanke baki sannan tayi wanka ta dauro alwala ta fito, tun wayewar gari babu abinda ta ci har zuwa sannan, rabonta da abincin kirki zae yi kwana uku yau tun dai faruwar incident din few days ago, bayan ta idar da sallah ta shirya cikin kaya marasu nauyi ta fito parlor ta tafi kitchen ta hada shayi kawai sannan ta koma dakinta, laptop dinta ta jawo ta kunna zata saka movie ko zata ɗan samu nutsuwar abubuwan dake damun ta a rai ta hanyar kallon film, daga karshe ma ta fasa kallon ta dauko takardunta ta fara karatu, nan ma taji bata fahimtar komai a karatun, rufe takardan tayi ta kwantar da kanta gefen gado ta lumshe ido with different thoughts running her mind, it's not as if she is disturb don Abdul bai daga kiranta ba ko bai kirata ba, kawai dai bata ma san abinda ke damunta bane in particular, bayan lokaci me tsawo ta sauke ajiyar zuciya ta bude idonta ta jawo wayarta ta bude WhatsApp, status taga Abdul yayi updating few hours ago, ta bude hoton da yasa taga har ya ma koma Nigeria cause a field din kwallo yayi hoton da abokansa dukkansu sanye da jersey, ko kadan bata yi mamakin komawarsa Nigeria ba don zai ma iya abinda yafi hakan, da taji shiru har kwana uku dama ta zargi ya koma, dai dai nan taji an bude dakin that is opposite her's, sosai gabanta ya fadi don tun ranan sae yau Housemate din nata ya zo gidan, ta kalli agogon wayarta taga karfe biyar har ya gota, ta ajiye wayar ta dago kanta, tana ta zaune har bayan 15 mins da shigarsa daki sai kuma ta mike tsaye tana jin jikinta ba karfi ta dau gyalenta tana tafiya a hankali ta nufi kofarta ta bude ta fito corridor, sai kallon kofar dakin nasa take gabanta na faduwa, ta rasa courage din karasawa bakin kofar, she stood der for some minutes daga karshe ta lumshe ido ta bude tana tafiya slowly ta isa bakin kofar nasa ta tsaya, ta kai hannu tayi knocking a hankali kamar tana tsoron kofar, komawa gefe tayi kamar mara gaskiya waiting for his response, jin shiru bai amsa ba ta sake knocking din a hankali, ta jira for like a minute again taga dai ba a amsa ba, babu abinda yayi crossing mind dinta sai ko yana bacci ne, but bacci da yamma haka? handle din kofar ta kai hannu gently without thinking twice ta bude kofar tana kallon cikin dakin with throbbing heart, a edge din gadon dakin ta gansa a duke yana operating laptop dinsa da alamar abinda bai gama ba ranan da ya bar gidan yake karasawa, ya daga kai ya kalleta sai kuma ya ci gaba da abinda yake yi, she felt really really bad, ashe yana ma jin tana knocking din, da tasan yana ji ya kyaleta da bazata fara bude kofar dakin nasa ba, ya mike tsaye yace "Good evening Halysaah" Taki amsawa kuma taki yarda ta kallesa, da kyar tace "Dama kana ji kaki amsawa?" Har muryarta ya fara rawa, ya ɗan bude ido yace "To na sani ko saurayinki ne Halysaah?" Nan da nan hawaye ya cika idonta ta juya ta bar bakin kofar ta kullo masa dakin ta koma nata, dukawa yayi ya ci gaba da abinda yake yi a laptop, tana komawa daki ta fara kukan da bata san dalilinsa ba, she felt really hurt kuma tayi da ta sanin zuwa dakin nasa, tana nan a yanda take har shidda saura sannan taji yayi knocking kofar dakinta gently, daga kai tayi tana kallon kofar sai kuma ta hade rai, lkci daya ya bude kofar tare da sallama, sai dai daga nan bakin kofar ya tsaya yana kallonta yace "I was trying to finish a power point Housemate, how are you doing?" Ta sauke idonta a takaice tace "It's fine" Yace "Baki je makaranta ba yau?" Ta gyada masa kai looking toward a different direction, yace "Why?" A takaice tace "Ba komai" Yace "Ok, hope everything is okay?" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa sai kuma ta dauke kai don kar ma ta fara kukan dake taruwa idonta, bayan like 10 seconds yace "Saurayin da ke maki fada a waya ne guy din nan ko?" Ta kasa cewa komai at first, sai kuma muryarta na rawa tace "Kayi hakuri da abinda ya faru" Ya ɗan buda ido yace "No it's fine Halysaah, ai ba ma abinda ya faru, but where did you know him from?" Tayi shiru ta kasa cewa komai tana share hawayen idonta, yace "I am intruding ko?" Ta girgiza masa kai kawai, yace "Ohk can we talk if you are comfortable Halysaah" She kept mute Kamar me nazari, can kuma a hankali tace "Ohk" yace "Then meet me at the parlor" Daga haka ya juya ya fita, ko da Khaleesat ta fito parlon bata tarda sa ba a ciki, ta zauna kan kujeran parlon tunani iri iri na yawo a kanta har ta rame a kwana ukun nan, bayan some minutes sae gashi ya fito daga kitchen with a cup of coffee, ya karaso cikin parlon ya zauna yana kallonta yace "You look pale Housemate, are you okay? Ko ya maki wani abun ne?" Khaleesat ta daga kai ta kallesa, sai kuma ta girgiza masa kai a hankali tace "He left immediately u left too" Yace "Oh really? That's weird" Ita dai tayi shiru, ya ɗan yi murmushi ya ajiye coffee din hannunsa yace "Amma baki ci abinci ba" Nan ma tayi shiru tana kallonsa, yace "Naga kamar its been a while da kika yi girki a kitchen, so me kike ci a gidan?" Ta sauke idonta, he could see tana cikin damuwa sosai, yace "Tun ranan da ya tafi bai dawo ba kenan?" Tace "Um" Ya kalli agogon wrist dinsa yace "Do u mind me taking u out for dinner?" Kallonsa Khaleesat take babu ko kiftawa kuma bata ce komai ba, ya mike yace "Get ready, let me get my car key" Yana fadin haka ya mike ya tafi dakinsa ta bi sa da ido, Khaleesat ta fi minti uku zaune parlon tana contemplating on weather to go out with him or not, what if Abdul bai bar kasan ba kawai old picture yayi uploading a status dinsa? The thought of this sent her quivers all over, Tana cikin wannan tunanin sai gashi ya fito daga dakinsa, yana shigowa parlor ta mike ba tare da ta bari sun hada ido ba ta wuce dakinta, canza kaya tayi ta dau veil dinta ta yafa sannan ta zauna gefen gado tana tunane tunane iri iri, bayan 15 mins da shigowarta dakin taji yayi knocking yace "Baki shirya ba Halysaah?" A hankali ta mike ta dau wayarta ta nufi kofa ta bude ta fita, ta samesa har ya koma parlor yana jiranta, tana isowa parlon yana kallonta yace "Where u contemplating inside the room?" Bata san sanda ta dan yi murmushi ba bata dai ce masa komai ba, yace "To mu je, this is after 6 already" Shi ya fara nufar kofar fita living room din sannan ta bi bayansa, yana tsaye bakin kofar bayan ya fita ya jira har ta fito daga parlon sannan ya kulle kofar yana kallonta yace "Why this much Deodorant Housemate?" Ta wani kallesa tace "Ni nace maka na sa?" Bai bata amsa ba ya nufi garage tana biye da shi a hankali, ita dai bata sa turare yanzu ba sai tun wanda ta saka da tayi wanka daxu, sai in ko kamshin kayanta yaji amma ba dai ita ba, bude mata motar yayi tun bata karaso ba sannan ya zaga ya shiga motar yana jiranta, bayan ta shiga suka bar Garage din, wani babban restaurant sananne ya kai ta a Baltimore, bayan yayi parking ta dinga kallon restaurant din da ta ga an rubuta The Capital Grille, sai da ya fara sauka daga motar sannan ita ma ta sauka, tana biye da shi suka shiga ciki, shi yayi offering dinta seat bayan ta zauna shi ma ya zauna ya dau food Menu dake saman table yana nuna mata na kusa da ita yace "Ki duba abinda za ki ci" Ita dai bata dau Menu din ba, yace "I am talking Halysaah" Without looking at him tace "Ko ma meye zan ci" Yace "Ohk" Tana danna wayarta yayi masu ordering abincin, mamaki Khaleesat ta dinga yi ganin amount of different type of foods that he ordered kamar za ayi karamin feast a wajen, abinci kuma masu tsadan gaske, da yawa cikin abincin da aka kawo masu sai a ranan ta fara ganinsu, duk da dai abincin turawa ne, drink ma ya kusa kala hudu ya siya masu, ta daga kai ta kallesa a karo na farko tace "Su waye za su cinye duk wannan?" Orange Crush ya dauka yana sha bai ce mata komai ba, after a while ganin bata fara cin abincin ba shi kuma sai cin abinda zai ci yake ya daga kai ya kalleta yace "Ko babu abinda kike so a nan ne?" A hankali ta dau Tacos daya, shi ko ya ci gaba da cin abincinsa, ƙasa ƙasa Khaleesat take kallonsa, ta lura yanda baya wasa da bacci haka baya wasa da abinci, because he didn't even mind she was in front of him abincinsa kawai yake ci sosai, ganin ko kallonta baya yi ta abincin gabansa kawai yake yasa ta ɗan saki jiki kadan ta fara cin abincin duk da ba sosai ba, ta ci iya abinda zata iya ci ta dau drink tana sha a hankali, sai a sannan ya daga kai ya kalleta after almost finishing his food yace "Ko dai a maki packaging abincin ki ci a gida, naga kamar kina kunyan ki ci abinci cikin mutane, or should i give u privacy?" Tana kallonsa a hankali tace "Privacy in an open restaurant? Ni nace ina kunyan in ci abincin?" Ya ɗan bude ido yace "Naga u ate just the Tacos bayan ga abinci da yawa a gabanki" Ta sauke idonta tace "Nafi son sa ne" Yana goge lips dinsa da tissue alamar ya koshi yace "Ohk, so now can i talk to you?" Shiru tayi na few seconds, sai kuma ta kallesa a hankali tace "Ohk" Ya karasa shanye drink dinsa yace "A nan America kika hadu da saurayin naki ko a Nigeria?" Khaleesat was silent, sai kuma ta sauke idonta tace "Nigeria" Yace "Ohk, but me kike tunanin yake janyo maku matsala tsakaninku?" Ta girgiza kai tace "Nima ban sani ba" Yace "Saboda ke ya taho nan daga Nigeria or he have a business here?" Ta gyada masa kai tace "Saboda ni ya zo" ya gyara zama yace "Kinga yana sonki kenan, sosai ma kuwa yake sonki, he left everything he was doing and came over just to see you, in na fahimta bai son kiyi sharing apartment da namiji a kasar nan ko?" Ita dai Khaleesat bata ce komai ba tana wasa da gefen mayafinta, yace "Sure... yana da gaskiyarsa, don ko ni bazan bar budurwata tayi communal living ba" Khaleesat ta daga kai ta kallesa, Yace "Yanzu dai kiyi kokari ki basa hakuri ku dai daita kanku, ni kuma i will think of another alternative for peace to reign between u and ur boyfriend, sannan shawaran da zan baki shine try all possible best ki dinga nuna masa abinda baza ki yi tolerating ba tun kafin kuyi aure, ya kamata ace akwai mutual understanding tsakanin ku, he look cool though kawai yana da hot temper ne and i notice insecurity na daya daga cikin matsalarku da shi, but you can definitely change him gradually Halysaah, so last maganar da zan maki ina ga ba abinda ya shafeni bane, kawai dai zan tunatar da ke Do's and don't din addininki ta bangaren relationship tsakanin mace da namiji" Khaleesat dai sauraronsa kawai take without looking at him, kuma taki ce masa komai tana kokarin fahimtar abinda zancensa na karshe ke nufi, shirun da taji yayi yasa ta daga manyan idanuwanta ta kallesa, at the same time ta kalli wa enda yake kallo a cikin restaurant din, 3 Guys ne suka shigo restaurant din gaba dayansu yan Africa, amma daya ne ɗan Nigeria a cikin su, guys din da ba yan Nigeria ba suka daga ma Housemate din nata hannu alamar girmamawa, and he waved back at them with smile on his face, Khaleesat ta dinga kallon daya mutumin da ya nufo su don ta ma ganesa, su sauran biyun kuma suka tafi yin abinda ya kawo su restaurant din, Mutumin na isowa kusa da table dinsu yana kallon Housemate dinta yace "Done with the power point?" Tuni kamshin turarensa ya cika wajen, Housemate dinta ya daga kai ya kallesa yace "Yau kuma har da kai za a ci abinci a nan kenan...." Yace "Not at all, i am getting some Steak for legend, meanwhile ashe kana nan" Housemate dinta yace "Yea, i came with my friend for Dinner" Khaleesat dai danna wayarta kawai take don mutumin yi yayi kamar bai san da Allah yayi ruwanta a wajen ba, ita ma ko kallon direction dinsa bata yi ba, Housemate dinta ya nuna masa bill dinsu yace "Get the bill cleared" juyawa mutumin yayi ya bar wajen yana tafiya irin ta ƙasaita, Khaleesat ta bi sa da kallon gefen ido, he was wearing a Jogger and a white Polo, ta dai ci gaba da danna wayarta, muryar Housemate dinta taji yace "That's my gee Halysaah, we share the same name with him...." Khaleesat ta daga kai without interest tace "Ohk" Yace "Sorry about his attitude, he isn't friendly, but i promise you he is good" Khaleesat tace "Likewise myself" Murmushi housemate dinta yayi sannan yayi excusing kansa ya mike ya nufi gun wanda ya kira da gee dinsa, daga inda take zaune taji mutumin na cewa "Kai kuma ina ka samo waccan yarinyar dake zaune kamar gunki bata iya gaisuwa ba, duk wani harkar raini ka iya ja ma mutane, that was how the other day da ka kawota karfe ukun dare a mota ta dinga kallon mutane kamar statue da aka dasa a gaban motar" Definitely yayi maganar ne ta yanda zata ji, Housemate dinta dake kallonsa yace "Ban gane bata iya gaisuwa ba, ba kai ka sameta a wajen ba, kayi mata magana ne kaga bata amsa maka ba?" Maimakon ya ba Housemate dinta amsar abinda yace sai taji yace "Na kai Legend gun Veterinary daxu" Taji Housemate dinta yace "Hope he is better now?" Mutumin yace "Let me get the bill cleared mu tafi gidan Mike yanxu...." Housemate dinta yace "No kayi tafiyarka zan yi dropping frnd dina first" Taji mutumin yace "Like seriously kai ko wani irresponsible being sae kace friend dinka, why are you stooping your self soo low Jay" Taji Housemate dinta yace "C'mon Ajay, come off it, this is so harsh..." Mutumin da ya kira da Ajay ya tafi ya bar sa gun a tsaye, Dawowa Housemate din nata yayi inda take, tuni ta mike tana gyara gyalenta without looking at him tace "Thanks for the dinner, kawata na kirana zan tafi gida" Housemate dinta yace "Ke kika kawo kanki da za ki koma ke kadai?" Taki kallonsa tace "Ae naga ur responsible frnds are here, so let me get going" Yace "Halysaah" ta daga kai ta kallesa, yace "Jira ni inyi clearing bill dinmu in yi dropping dinki gida" Yana fadin haka daya daga masu aiki a restaurant din ya nufosa da ladabi ya sanar masa anyi clearing bill din su, ya bi A-jay da ya fita daga Restaurant din da kallo, wa enda suka shigo tare na biye da shi a baya. Khaleesat bata yarda ta hada ido da Housemate dinta ba har suka fito daga Restaurant din zuwa inda yayi parking motarsa, sai da ya shiga motar sannan ita ma ta shiga ta zauna tana danna wayarta, bai tada motar ba ya kalleta, speaking calmly yace "Hope you are not offended Halysaah?" Without looking at him tace "Offended at what?" Yace "I don't really know" Ta kada baki tace "Ai ni ban yi kama da someone that isn't responsible ba balle in zama Offended at what a random stranger spew out, out of his ignorance, shi dai da bashi da manner shi ne babban irresponsible being, ai da ya fada a gabana yaji abinda zan gaya masa" Housemate dinta ya bude baki yana kallonta da mamaki looking completely speechless, bai yi tunanin taji abinda Ajay din ya fada ba, bai kuma yi tunanin tana ma da baki haka ba, after few seconds yayi kasa da murya yace "Pls kiyi hakuri Halysaah, bana son wannan yasa ranki ya bace, i purposely brought you out to cheer you up and make you lively don naga kamar kina cikin damuwa, amma ba don a kara bata maki rai ba, plss ignore Ajay's attitude, wani lkcn yana da problem i think today is one of those days" Khaleesat bata sake cewa komai ba but she is trying hard not to cry, ya ci sa'a ba yana tsaye gabanta ya fadi haka ba da tsaff zata mayar masa da baƙar magana dai dai da abinda ya gaya mata a wajen, Housemate dinta ya tada mota suka bar Restaurant din, hakuri ya dinga bata kamar shi ne yayi mata laifi har suka isa gida, direct dakinta kawai ta wuce, after like 40 mins ta fito wanka tana duba sleeping dress din da zata sa taji yayi knocking kofar dakinta, hijab din da tayi sallah ta dauka da sauri ta saka, bai bude kofar dakin ba har sai da taje ta bude tana kallonsa, yace "Sae da safe Halysaah, pls ki kwantar da hankalinki and get some rest, gobe kuma ki je school" ta sauke idonta bata ce komai ba, taji yace "Take care" Sai da ya juya ya bar wajen sannan ta daga kai ta bi sa da kallo cikin sanyin murya tace "Thank you so much, for..." Sai kuma tayi shiru, ya juya yace "For?" Ta langwabar da kai tace "The Dinner" Ya ɗan buda ido yace "My pleasure Halysaah" A hankali tace "But.... i don't... know, ur name" Yace "Oh really, amma ranan da na fara zuwa gidan nan ai nayi introducing kaina sai dai in kin manta, I am Ahmad Jawwad Yusuf, my frnds call me Jayy" Kallonsa Khaleesat ta dinga yi without blinking, yace "Are you okay with that?" Ta sauke idonta tace "Alright, i really appreciate you" Ya sakar mata murmushi yace "See yah tomorrow" daga haka ya bar wajen ta bi sa da ido har ya fita daga gidan gaba daya sannan ta juya a hankali ta koma dakinta ta kulle kofar. *Make ur payment before the end of free pages, kar a ji shiru* 07087865788✍🏻 [20/05, 11:38 pm] +234 813 644 0264: ✨✨HALYSAAH✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 12..... Washegari da safe Khaleesat ta gama duk abinda zata yi a gida ta shirya ta tafi makaranta, tana zaune favourite spot dinsu ita da Safiyyah bayan sun fito daga aji, Safiyyah na facing dinta tace "Tsakaninki da Allah ina kika je jiya da yamma da naje gidan baki nan? Ni dai nasan babu inda kike zuwa a garin nan, ba kuma frnds gare ki ba, So where did u go?" Khaleesat da idonta ke kan jotting da tayi a aji tace "To ke meye na zuwa da yamma likis, i was expecting you around 5pm not 7pm" Safiyyah ta amshi takardan hannunta tace "Ina maki tambaya kina min tambaya, ko akwai abinda kika fara boye min ne Khaleesat?" Tagumi tayi tana kallon Khaleesat din da tuhuma, sai a sannan Khaleesat ta daga kai ta kalleta, dariya ta bata amma bata yi ba, kamar dai bazata ce mata komai ba sai kuma ta bude baki tace "Mun fita zuwa restaurant ne da Housemate dina" Safiyyah ta buda baki tana kallonta with surprise, can tace "Waw, really? Housemate dinki fa kika ce?" Sai kuma tayi dariya tana gyara zama idanuwanta kamar za su fito tace "Anya Khalee babu magana a kasa kuwa? Restaurant fa kika ce? How did he convince you har kika bi sa zuwa restaurant?" Khaleesat ta tabe baki tace "Toh meye kuma a kasa? Daga dai ya kai ni restaurant mu ci abinci? Kinsan yaushe rabon da inci abincin kirki a gidan?" Khaleesat ta sauke idonta a hankali tace "He notice i haven't been eating shi ne yasa har ya kai ni restaurant" Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya tace "Ai kece da dora ma kanki abinda Allah bai dora maki ba kawata, akan Abdul din da naga yayi updating status da jersey jiya alamar har ya koma Nigeria ya ci gaba da harkokin gabansa ke kina nan kina neman kashe kanki, wallahi in zaki ajiye lamarin gayen nan a gefe da zai fi maki alkhairi a rayuwarki, very very heartless guy with no conscience, dubi tsabar zuciyarsa ta dutse ne ya gwammace ya kara siyan ticket yayi juyawarsa ya koma Nigeria, Allah ma yasa yayi maki ya jiki zuwan da yayi" Khaleesat dai tayi shiru tana kallon Safiyyah, Safiyyah ta daga kafada tace "Ga dai Housemate din nan naki duka duka yaushe har ma ku ka san juna? Amma ya gane kina cikin damuwa har da kai ki restaurant for dinner, to this is how a caring and understanding Boyfriend and a Gentleman should be" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya a hankali tace "Ni babban damuwata kar ya sake dawowa kasar ban sani ba Sophie, ce masa nayi Housemate dina frnd din Nancy ne fa, kinsan bai san Nancy bata gidan ba ai har yanzu, to kar ya sake dawowa unexpectedly ya gansa" Safiyyah tace "Abinda zai faru kawai kiransa zaki yi ta yi har sanda ya ga daman daga kiranki, ki basa hakuri ki samu ku shirya, in har ku ka shirya duk wani movement dinsa zaki dinga sani, yanzun ma ai don baku communicating ne all this while shi yasa kawai ya taho kamar an jefosa, banda haka ai duk sanda zai zo yana gaya maki" Khaleesat tace "Haka ne, amma kin san irin zuciyarsa wallahi zan iya kiransa sau goma ma bazai daga ba, ko na masa magana ta WhatsApp bazai yi reply ba" a sanyaye ta kare maganar, Safiyya tace "Bari in kirasa ta wayana yana picking zan ce ya kirani, daga nan in ya kira sai in baki wayar ku yi settling dispute din karyan ku" Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba, amma tasan hakan kadai shi ne way out, Safiyyah ta ciro wayarta ta fara kiran Abdul, har ya katse bai daga ba, ta sake kiransa sai gashi ya daga, sallama tayi masa ta gaishesa tace "Pls in ba damuwa ka kirani" Katse kiran yayi sai gashi ya kira tayi picking sannan ta mika ma Khaleesat wayar, Khaleesat ta amshi wayar gabanta na faduwa ta kai kunne, Safiyyah ta tashi ta bar ta a wajen ta koma wani waje ta zauna, a hankali Khaleesat tace "Don Allah kayi hakuri ka saurareni..." Shiru yayi da yaji muryarta, nan da nan hawaye ya cika idonta muryarta na rawa tace "Pls kayi hakuri da abinda ya faru, i promise you hakan bazai sake faruwa ba" Yace "Dama akwai abinda ya faru ne?" Tayi shiru bata ce komai ba, yace "I am asking you, akwai abinda ya faru ne dama?" Ta sunkuyar da kanta tace "Don Allah kayi hakuri, i am truly sorry plss" Yace "Look i am super busy now, idan kin shirya gaya min abinda ya faru kike ban hakuri sai ki kirani ta layin ki anjima" Cikin sanyin murya tace "Toh Nagode" Katse wayar yayi, ta juya tana kallon Safiyyah, Safiyyah ta kyabe baki ta dawo kusa da ita ta zauna tace "Ya ku ka yi da shi?" Khaleesat ta ja tsaki tana tattara reading material dinta tace "An gaya masa banda ina tsoron kar ya dawo without notice ni zan sake magana da shi ta waya ne" Safiyyah ta bude baki tana kallon Khaleesat tana tunanin yaushe bakinta ya fara budewa haka akan Abdul ne wai, Dariya Safiyya tayi tace "Shi Abdul din naki Khalee?" Khaleesat ta ki bata amsa, har ranta ita fa yanzu tana jin bazata iya ci gaba da tolerating abubuwan Abdul ba, ita kanta bata san daga inda wannan liver din yake zuwa mata ba, sai dai duk abinda zai faru ya faru but she is not tolerating anymore. Wajen karfe biyu ta koma gida, bayan tayi wanka tayi sallah ta sauya kayanta ta kwanta, sai bayan da tayi la'asar ta shiga kitchen ta jingina da cabinet tana tunanin abinda zata girka, tuwo taji take son ci, kawai daga karshe tayi deciding tayi tuwon since tana da duk ingredients din girka tuwon, kan kace me ta gama girka tuwo da miyar kuka with enough obstacles a ciki, ta gama goge gogen kitchen din sannan ta fito parlor wajen karfe biyar, dai dai shigowar Housemate dinta gidan, ita dai tana tsaye kusa da kitchen, ya juya ya kalleta bayan ya kulle kofar parlon yace "Good evening Halysaah" Tace "Good evening" Yace "What are you cooking with such a nice Aroma" Tace "Tuwo ne" Ya karaso cikin parlon yace "Really, it's been long na ci tuwo fa" Tana kallonsa tace "In kawo maka?" Ya dan buda ido yace "Ok thank you" Juyawa tayi ta koma kitchen din, ya zauna saman kujera hoping ba da yawa zata saka masa ba, ba a dau lokaci ba sai ga ta ta dawo parlon da plate dauke da tuwo with a diff bowl of soup, tun da ta duka ta ajiye abincin yake kallon bowl din miyan babu ko kiftawa, can dai ya daga kai ya kalleta yace "Wani miya ne wannan Halysaah?" Ta koma gefe tace "Miyar kuka ce" Lkci daya yayi yaƙe yana shafa kansa yace "Wow, but bana cin irin miyan, i thought vegetable soup ne, baki yi stew ba?" Ta wani kallesa, a takaice tace "Babu, kuma kayi tasting miyan ne kafin kace baka cin irin sa?" Ya jingina da kujera ya sauke ajiyar zuciya yace "Na ma ci abinci few minutes ago fa" Dukawa tayi ta dau bowl din ta mika masa miyan tace "Taste it first before concluding" Ya dan kalleta yana murmushin dole yace "Ok, where is the spoon?" Tace "Shi ba a cin sa da cokali ai, da hannu zaka sha" Yayi shiru sai kuma yace "Then bari in wanke hannu" Yana fadin haka ya mike, ta koma gefe don basa hanya sannan ta bi sa da kallo har ya tafi bandakin dake parlorn ya wanke hannu sai gashi ya dawo, bayan ya zauna ta mika masa miyan tana kallonsa, shi dai bai yarda ya hada ido da ita ba, tun da ya kai finger ya lasa miyan ya kai baki ya kasa dago kai, ita dai kallonsa kawai take bata ko kiftawa, can dai yana murmushi da kyar ya dago yace "It's sooo nice amma na ci abinci wallahi Halysaah" Duk da dariyar da ya bata ta dake tace "To ai tunda ka sa na zuba sai ka ci ko kadan ne cause i am not throwing it away" Bata jira cewarsa ba ta juye masa miyan a kan tuwon dake plate ta dau plate din ta mika masa tana kallonsa, he was totally speechless and confuse at the same time, tana kallonsa da kyau tace "Karba" Ya kai hannu a hankali ya amsa plate din tuwon, in ya debi tuwon sai ya dangwala miyar kamar yana tsoronsa sannan ya kai baki, sosai ya bata dariya amma fa bata yi ba, instead sai murmushi take, sau uku yana diban tuwon yana ci kuma har sannan yaki yarda su hada ido da ita, kana ganinsa kasan da kyar yake cin abincin, his facial expression says it all, wayarsa ne ya fara vibrate, ya ajiye tuwon da sauri ya fiddo wayar yana kallon screen, sai kuma ya kalleta yace "This is an urgent call Halysaah bari in shiga daki in daga" Kasa basa amsa tayi don kar ma tayi dariyar da take dannewa, ya mike ya nufi dakinsa da sauri don ko jiran jin abinda zata ce bai yi ba, tana ji ya sa ma kofar dakin makulli bayan ya shiga, sai a sannan ta zauna gefen kujera ta rike kanta tana dariya, after some minutes ta mike ta dau plate din tuwon still smiling ta wuce dakinta. Khaleesat na Voice call ta WhatsApp da Ummanta wajen karfe tara da rabi na dare taji Housemate dinta na knocking kofar dakinta, bayan tace ma Ummanta tana zuwa ta ajiye wayar sannan ta sauka daga kan gado ta saka hijab ta tafi ta bude kofar, yana jingine jikin bangon opposite din dakinta idonsa a kulle, yana jin bude kofa ya bude idon da sauri, kana ganinsa kasan daga bacci ya tashi, tun da ya shige daki daxu yace ana kiran wayarsa bata sake ganinsa ba sai yanzu, yace "Zan tafi sai da safe Halysaah, but pls ki dan kulle kofar i can't find my key" Ita dai bata ce komai ba tana kallonsa, he look so sleepy, ya ciro wayarsa dake ta vibrate a aljihu, tsaki yayi after picking yace "Kai dalla ina hanya" Daga haka ya mayar da wayar aljihu ya sake yi mata sai da safe ya juya ya fara tafiya, ta bi sa da kallo har ya isa parlor, jingina taga yayi ta bayan kujera ya rungume hannunsa ya rufe ido, Khaleesat ta sauke idonta sannan ta fito daga dakinta tana tafiya a hankali ta tafi parlon, bude ido yayi da sauri jin tafiya, sai kawai ya nufi kofar fita daga parlon, tace "Since u can't control ur self a ko ina ka samu bacci kake, be it standing, sitting, driving and even walking, then why not sleep over?" Ya dan kalleta jin abinda tace, nan da nan kuwa yaji baccin ya bar idonsa gaba daya, yana mata kallon mamaki at the same time yana sosa kai yace "Yaushe kika ga nake yin duk wannan da kika lissafa Housemate?" Ita dai ta rungume hannu tana kallonsa bata ce komai ba, ya dauke kai yace "I was only meditating ba wai bacci nake ba, in dai kika ga na rufe ido to i am meditating" Yana fadin haka ya nufi kofa ya bude yace "Good night, kar ki manta ki kulle kofar" Daga haka ya fita ya tura mata door din, ɗan murmushi tayi tana tafiya a hankali ta isa kusa da window ta dan bude curtain din tana lekansa, parking space taga ya nufa ya bude motarsa ya shiga, she is just hoping yana shiga bazai fara wani baccin ba a cikin motar, after few seconds taga ya fara reverse, ta sauke ajiyar zuciya tana kallonsa har ya bar Garage din ya dau hanya, sake curtain din tayi slowly, ta dan tsaya for few minutes sai kuma ta tafi daki ta dauko key dinta ta kulle kofar ta wuce dakinta, sake kiran Ummanta tayi ta WhatsApp, bayan Umma ta daga Khaleesat tace "Ko kin fara bacci ne Umma?" Umma tace "Aa idona biyu ina jiran ki, Abdul ya maki wata magana ne?" Khaleesat tayi shiru jin abinda Umma tace, ta girgiza kai tace "A'a bai ce min komai ba, me ya faru Umma?" Umma tace "Daxu Hasiya Matar Malam Saleh ta zo gidan nan" Sosai Khaleesat taji gabanta ya fadi, Malam Saleh aminin mahaifinta ne, yawanci abubuwa da yawa a bakin matarsa Ummanta ke ji tunda ba gaya mata baban nasu ke yi ba, abu da yawa ma sai dai taji a duniya ba dai a bakinsa ba, Khaleesat tayi karfin halin cewa "Me tace Umma?" Umma tace "Wai ko an tsaida maganarku da Abdul, haka dai tace min" Khaleesat was short of words, lokaci daya jikinta yayi sanyi, sosai maganar ta zo mata a bazata, she could feel her self tearing up, hankalinta yayi mugun tashi cikin lkci kadan, Umma tace "To ina jira dai in ga ko Malam din zai yi min magana, in ba ayi hankali ba kuma in ji a bakin matansa tun da su zai gaya masu ai, kuma kin ce Abdul din bai ce maki komai ba har yanzu ko?" Khaleesat ta goge hawayen da ya gangaro idonta, tana gyada kai da kyar kamar Umma na ganinta amma ta kasa cewa komai, Umma tace "Khaleesah?" Da kyar Khaleesat ta bude baki ta amsa don bata son Ummanta tasan kuka take, Umma tace "Naji kinyi shiru ne" Khaleesat ta dake tace "Ba komai Umma, ina duba wani karatu ne a takarda" Umma tace "To shikenan, kiyi karatun ki ma yi magana washegari ko?" A haka suka rabu, Khaleesat ta ajiye wayar hannunta ta kwantar da kanta saman pillow hawaye na sauka idonta, bata san menene ya sa all of a sudden taji she can't marry Abdul ba unlike before da har cikin ranta tasan bata da option dole ne aurenta da shi, tana kuma masa fatan ya canza wataran, yanzu kam bata jin haka a ranta, instead ji take bazata iya aurensa ba ma, Khaleesat bata yi wani baccin kirki ba daren ranan nan fargabanta daya kar ma yace a daura auren nan take, tasan in har suka ce ma iyayenta haka babu abinda zai hana a daura auren nan sai wani ikon Allah. Da safe Khaleesat ta tashi da ciwon kai sosai, kana ganinta kasan tana cikin damuwa ba kadan ba, haka dai ta shirya ta fita zuwa makaranta, warce take son tayi ma magana ta dan ji saukin abinda ke damunta sai bata shigo school ranan ba, wayarta ta ciro kawai tayi dialing number Abdul cause she can't hold it anymore, kiran na shiga ya katse ya kirata, ta daga ta kai kunne a hankali ta gaishesa, amsawa yayi yace "Ya aka yi?" At first tayi shiru, sai kuma tace "Ba komai i only called to greet you" Yace "Which side of the bed did you wake up from today da kika kirani ki gaisheni?" Tayi masa shiru, yace "ke dai fadi abinda kike so Malama, foodstuffs din ki ne ya kare ko me?" Ta hade rai tace "Yaushe ka siya da har zai kare?" Yace "Bazai kare ba dama mana tunda baki wani cin abinci sai cookies da kayan kwadayi" Ta wani turo baki bata ce masa komai ba, after few seconds tace "Kawai naji a jikina ne kamar da wani abu dake shirin faruwa shi sa na kira ka" Yace "Wani abu kamar me fa?" She was mute bata basa amsar tambayarsa ba, yace "Anyway, ko ma me kika ji a jikin ki haka ne, zan shiga meeting yanzu sai anjima" Katse wayar yayi a nan take, ta dinga kallon screen din wayarta wani tsanarsa na yawo a zuciyarta, a baya duk abubuwan da yake mata bata taba jin tsanarsa ba sai dai haushinsa yanzu kuwa kawai ji tayi ta tsanesa, ta ja tsaki ta mayar da wayarta jaka tana jin wasu hawaye na cika idonta, rashin zuwan Safiyyah makaranta ya sa bata tsaya su gama karatun ranan ba ta kama hanyar gida kawai cike da damuwa, tana jiran Lyft din da tayi ordering sai ga kiran Safiyyah ya shigo wayarta, tun daxu ta kirata bata daga ba sai yanzu ta biyo ta, Khaleesat ta daga ta kai kunne tana jin muryar Safiyyah tace "Baki da lafiya ne?" Da kyar Safiyyah tace "Tun jiya da daddare, na ma zata rasuwa zan yi kawata" Khaleesat ta ɗan bude ido tace "Me ya sameki?" Safiyyah tace "To ina ma na sani Khaleesat, Allah sa ba poison dina matar nan tayi ba don tun jiya sai yanzu nasan mutanen dake kaina" Khaleesat tace "Subhanallah, kina gida ne yanzu?" Safiyyah tace "Har da karin ruwa kuwa" Khaleesat tace "To bari in taho gidan yanzu" Khaleesat na maida wayarta jaka ta nufi gidansu Safiyyah, bayan tayi knocking kofar Surayya ta bude mata, Khaleesat ta sauke ido ta gaisheta, in ba kasa kunne sosai ba ma baza kasan Surayya ta amsa ba, Khaleesat taji muryar Mustapha na tambayar matar tasa wanene, ji tayi kamar ta juya ta fasa shiga cikin gidan, amma kasancewar a bude Surayya ta bar kofar yasa ta karasa ciki walking slowly, without looking at Mustapha dake parlor ta gaishesa, ya amsa yace "Ya karatun Khaleesat?" Khaleesat tace "Alhamdulillah, ya jikin Safiyyah?" Yace "Alhamdulillah, she is inside her room" Khaleesat ta juya ta nufi dakin Safiyyah, da gasken ruwa ta tarar ake kara mata don ta zata kawai tace mata haka ne don ta zo, Khaleesat ta zauna gefenta da damuwa tace "Sannu Sophie, ya jikin?" Safiyyah tace "Ba sauki Khaleesat, wallahi kilan abu matar nan ta saka min a abinci" Khaleesat tace "Don Allah ki dena cewa hka, kin ga yayanki ai bazai ji dadi ba in kina wnn magana" Safiyyah tace "Wallahi ita ce don lafiya na dawo gida jiya, ni na zata ma na rasu, sai da na farfado naga ba haka ba" Khaleesat tace "Allah dai ya baki lafiya, kin ci abinci?" Safiyyah tace "Ni bazan ci abincinta ba gaskiya tun daxu sai fruit kawai nake ta sha da lemon kwali" Khaleesat tace "Ko in je gida in maki girki? Me kike son ci?" Safiyyah tace "Ko tuwo da miyar kuka ne ki min in kina da ingredient, kawai shi naji nake so wallahi" Khaleesat tace "To ba damuwa, bari inyi sallah sai in tafi in maki girkin" A haka Khaleesat tayi sallahn azahar ta bar gidan bayan tayi ma Surayya da mijinta sallama, Mustapha ne ma ya tambayeta har zata tafi, Shine tace masa zata dawo anjima, Khaleesat na isa gida taga motar Housemate dinta a Garage, tana bude kofar ta shiga parlor ta gansa kwance kan 3 seater yana bacci, har ta kulle kofar bata ga ya bude ido ba, ta nufi dakinta ta shiga ciki ta canza kaya sannan ta fito ta shiga kitchen, tuwon ta dora har zata fara hada ingredient na miyar kukan sai kuma ta fasa taji gwara tayi vegetable soup kawai, ita kanta bata san menene yasa take son yin vegetable soup din ba duk da bata wani son cin miyar ganye she prefer slimy soup, sai da ta gama tuwon sannan tayi ordering lyft da zai kai ta nearest African store da zata iya siyan ingredients din miyan Vegetable. *Make ur payment before the end of free pages* _Halysaah is just 500 naira_ 07087865788 ✍🏻 [20/05, 11:45 pm] +234 812 308 8480: Read My Book "HALYSAAH" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6 ✨✨ HALYSAAH✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 13.... Har Khaleesat ta fita daga gidan zuwa Supermarket Housemate dinta bai tashi ba, bayan ta dawo sai bata gansa a parlor ba alamar ya shiga dakinsa, kafin karfe hudu da rabi na yamma Khaleesat ta gama miyan da take, tayi dishing ma Safiyyah abincin a warmer din da zata kai mata, kan kace me aroma din girkin ya cika gidan, ko tuwon bata ci ba ta tafi dakinta tayi wanka tayi alwala tayi sallan la'asar sannan ta shirya, fitowa parlor tayi ta nufi kitchen, tsaye ta ga Housemate dinta ya jingina da cabinet din kitchen din idonsa a lumshe, ya dora lipton a gas, tace "Bacci kake a kitchen din?" Bude ido yayi ya juya ya kalleta yace "Not at all" Tace "To me kake yi?" Ya dan shafa kansa yace "I am having a terrible headache" Tayi kasa da murya tana kallonsa tace "Ka sha magani?" Ya kashe gas din yace "Zan sha" Tace "To in sa maka abinci?" Yace "What did you cook?" Tace "Tuwo...." Bai jira ta karasa ba da sauri yace "A'a, Alhamdulillah, am full" Murmushi tayi tace "To ai ba miyar kuka bane, vegetable soup ne" Tana fadin haka ta bude masa tukunyar miyar tana kallonsa, bayan ya ga miyar a hankali yace "Ohk, but let me dish the food my self" Ita dai bata ce masa komai ba ya dau plate ta nuna masa inda tuwon yake, kallon dan tuwon da ya zuba ta dinga yi, sai kuma tace "Wannan dan kadan din?" Without looking at her yace "Zai isheni" bata sake cewa komai ba ya zuba miyar a gefe with just one protein ya saka spoon a gefe, sannan ya dau mug ya debi lipton da ya dafa ya dau plate din tuwon yace "Thank you" Bin sa tayi da kallo har ya fita daga kitchen din. Ko da ta fito parlor da abincin Safiyyah ta samesa zaune kan kujera bai fara cin abincin ba, ya daga kai ya kalleta, ta dau handbag dinta dake saman kujera, yace "Are you going out with food?" Tace "Yea, kawata zan kai ma abinci she is sick" Yace "Ohk Allah ya bata lafiya" Tace "Ameen" Daga haka ta fita daga gidan. Har kusan Magrib Khaleesat na tare da Safiyya, sosai jikin Safiyyah yayi sauki sai labari take ma Khaleesat da tayi shiru hankalinta baya kan hirar, da ta tuna maganar da Ummanta tayi mata jiya da kuma abinda Abdul yace mata da ta kirasa daxu sai taji duk duniyar tayi mata zafi babu abinda ke mata dadi a rai, Safiyyah da ta kula da yanayin Khaleesat tace "Wai me ke damun ki ne kawata?" Khaleesat ta kalleta, sai kuma ta dan yi murmushi tace "Bakomai Sophie, kawai na gaji ne sosai har na fara jin bacci" Ba don khaleesat bata son gaya mata damuwarta bane yasa tace mata haka sai don bata son fadin damuwar tata a wnn lkcn, but tasan dole zata gaya ma Safiyyah abinda ke faruwa, Safiyyah tace "To ki kwana a nan mana tunda bamu da lectures gobe, it's already pass 7 yanzu" Khaleesat ta dan bude ido tace "In kwana a ina? A'a ni dai kin ga tafiyata" duk yanda Safiyyah ta so convincing Khaleesat ta kwana gidan, khaleesat ta ki sauraronta tayi sllhn magariba ta kama hanyar gida, dama tun da ta kawo tuwon da tayi ma Safiyyah daxu Mustapha ya shigo har dakin ya diba ta zama uncomfortable zama a gidan, matarsa kuwa ta kasa ta tsare a parlon gidan, ko da ta fito parlorn ita kadai ta samu zaune fuska a murtuke, Khaleesat tayi mata sallama ita dai har ta fita daga gidan bata ji ta amsa mata ba. Khaleesat na isa gida ta kulle kofar parlon ta karasa ciki tana kallon plate din dake saman kujera da yayi covering with another plate, mug din shayin ma na ajiye bai sha ba, ta tafi ta bude plate din tuwon taga bai ci ba, abinda ya fada mata a kitchen ne daxu ya fado mata that he is having headache, ta juya tana kallon kofar dakinsa, tana tafiya a hankali ta nufi dakin tayi knocking gently, sai da ta sake knocking jin bai amsa ba ta ɗan bude kofar slightly, bacci ta gansa yake yi saman gado, ta sauke idonta kasa, lkci daya ya bude ido yana kallonta, ta ɗan koma baya kamar mara gaskiya tana kame kame tace "Are you okay?" Kansa kawai ya nuna mata ta karasa cikin dakin ta duka ta side dinsa da damuwa tace "Baka sha maganin bane?" Bai yi responding ba hakan yasa ta kai hannu kusa da forehead dinsa sai dai bata taɓa sa ba, amma she could feel he is running temperature, a hankali tace "Should i order an Uber ride sae kaje asibiti?" Ya girgiza mata kai idonsa a lumshe, rasa abinda zata yi tayi, lkci daya taji hankalinta ya tashi, mikewa tayi ta fita zuwa dakinta ta dau karamin towel tayi soaking dinsa da ruwa bayan tayi squeezing ta dawo dakin, ta nufi inda yake kwance ta duka kusa da shi ta dora karamin towel din da ta linke saman forehead dinsa, ya bude idonsa, cikin sanyin murya tana kallonsa tace "In yi ordering ride din?" Ya dafe towel din da ta dora masa a forehead yace "Don't worry Halysaah" ita dai kallonsa kawai take, can ta tuna tana da pain reliever a daki, mikewa tayi dai dai nan taji kamar ana kwankwasa kofa a parlor, ta juya ta nufi kofar ta fita zuwa parlorn, tsaye tayi bakin kofar parlon tana tambayar waye at the same time tana bude kofar, ta ɗan koma baya tana kallonsa with surprise, shi ma daga sama har kasa yake kallonta hannunsa rike da wayarsa, su biyu ne tsaye bakin kofar, lkci daya ta hade rai tace "How may i help you?" Kai tsaye shi wanda yake mata kallon sama da kasa ya shigo parlon har sai da ta matsa gefe da sauri kar ya bangajeta, shi dayan mutumin dake tsaye bakin kofar calmly yace "Hello, plss is Jay in here? Ahmad Jay...." Mutumin da ya shiga parlon ya juya yana masa wani kallo yace "Kaii wajenta ka zo halan?" Shi wanda ke waje ya ɗan yi murmushi ya shiga parlon ya sauke kai kasa, amma sai ya tsaya daga bakin kofar bai karasa can cikin parlon ba, shi ko wanda ya fara shigowa har ya nufi hanyar dakunan dake apartment din, da sauri Khaleesat ta nufesa a fusace tace "How will you just barge into someone's apartment without excuse or an explanation?" Juyawa yayi ya kalleta from head to toes, ita kanta bata san me yasa ta tsaya ɗan nesa da shi ba taki ci gaba da bin sa ba amma bata fasa masa kallon da take masa ba fuska a daure, ya gyada kai ya ci gaba da tafiyarsa kamar yasan dakin, kawai taga ya bude ya shiga ciki, ta juya ta kalli mutumin dake tsaye har sannan a parlor tace "Ku haka ake yi daga inda ku ka fito?" Cikin nutsuwa mutumin yace "We are sorry Madam, location shi Jay din ya tura masa wai bashi da lafiya and here is the location sannan mun ga motarsa a garage din apartment din nan, hope we are in the right place?" Khaleesat tace "Sai bayan kun shigo za ka tambayeni ko kuna right place din?? Where Is it done this way?" Mutumin ya hade hannunsa biyu alamar bada hakuri yace "Kiyi hakuri dai" Yana fadin haka ya bi bayansa ya shiga har cikin dakin shi ma, bin su tayi amma ta tsaya a corridor, ji tayi wanda ya fara shiga dakin da farko na cewa "Jay me kake yi a gidan nan da wannan karamar yarinyar da bata da manners? Is this the reason why ka dena zama 24/7 a gida yanzu? When did u start this useless life? First of all who is the little brat i want to know?" Da wani expression yake kallon Jay dake fama da kansa a kwance yaki basa amsa, shi dai mutumin da ya shigo a karshe na tsaye daga daya gefen Jay yana masa sannu, sai kuma ya kalli Ajay calmy yace "Kaga dai bashi da lafiya yanzu Ajay, all this question isn't necessary now" Da kyar Jay yace "Ka kyale ɗan iska mana, laifina ne da na tura masa location" Ajay dai sai bin dakin da kallon mamaki yake yi ganin property din Jay duk a dakin, can ya kallesa yace "To ma menene yasa za ka kirani? in baka da lafiya ita yarinyar ta kai ka hospital mana, ba tare ku ke zama a gidan ba" Mikewa zaune Jay yayi yace "Kai wai did you know how i am feeling? Ka wani zo nan ka isheni da unnecessary surutu, pls get out Ajay, gerrout pls" Khaleesat dake sauraron conversation dinsu ta wani taɓe baki ta juya ta koma parlor ta zauna wani mugun haushin mutumin da taji ana kira da Ajay take ji a ranta, taga Abdul ma balle shi, Salem ya mika ma Jay hannu zae taimaka masa ya tashi, Jay yace "Pls kace mata ta kawo min bottle water, or you check the kitchen ka dauko min" Salem ya juya ya fita, Ajay dake taɓe baki ya juya ya fice daga dakin shi ma, direct ya nufi kofar fita daga apartment din yayi ficewarsa ya koma can waje ya tsaya jikin motarsa, Salem dai ya bi sa da kallo ya sauke ajiyar zuciya ganin fita yayi, sannan ya kalli Khaleesat ya gaya mata ta dauko ma Jay ruwa, ta mike ta tafi kitchen ta dauko ruwan ta basa, ba a dau lokaci ba sai ga shi sun fito tare da Jay, mikewa tsaye tayi tana kallonsa, Jay ya zame hannunsa a na Salem ya zauna saman kujera ya jinginar da kansa da kujeran ya lumshe ido, a hankali Khaleesat tace "Amma hospital zaku je ko?" Da kyar yace "No, gida za mu je ya min treatment" Khaleesat tace "To Allah ya sauwake, Allah ya baka lafiya" Ya gyada mata kai sannan ya mika ma Salem hannu ya mike tsaye, Khaleesat na son tambayarsa abu amma ta kasa, ganin za su fita daga parlon ta dake tace "Can i get ur digit so i can be checking up on you?" Salem dai ya juya ya kalleta da ɗan mamaki jin tambayar da tayi, does this mean basu san juna ba kenan tunda har bata da lambarsa, Housemate din nata ya juya ya kalleta yace "Ai zaki gane gidan da muka je ranan da na mance makulli da daddare bayan kin dawo Nigeria, that's our home, zaki iya zuwa at anytime...." Khaleesat dai ta dinga kallonsa, sai kuma yace "Salem give her my digit, ko kuma ka bata nata kar ta kira bata sameni ba" Salem yace "Ohk bari in bata nawa" Khaleesat ta dauko wayarta sannan ta amshi number Salem, bayan ya gama bata suka fita daga parlon tare da housemate din nata, tana tafiya a sanyaye ta karasa gun window ta bude labule tana kallonsu, sae da suka fito Ajay ya shiga motarsa, bayan sun shiga yayi zoom off. Khaleesat ta sauke idonta sannan ta juya a hankali ta koma cikin parlon. Bayan kwana uku Khaleesat sun fito daga aji tare da Safiyyah dake waya, ita dai Khaleesat na tafiya ne amma gaba daya hankalinta na wani gun daban, Safiyyah tace "Wai ya jikin Housemate din naki yanzu? Ko ya dawo ne baki gaya min ba?" Khaleesat ta kalleta tace "Har yanzu ai bamu yi magana da shi ba" Safiyyah tace "To wanda ya baki number sa fa ko har yanzu bai daga kiran naki ba?" Khaleesat tace "Aa ya daga jiya, amma sai yace min he is much better, da na tambayesa ko yana kusa sae yace min a'a yana bacci, kawai ni dai i hope da gasken jikin nasa da sauki..." Safiyyah tace "Shegen mutumi in ba kinibibi ba me yasa zai wani ƙi baki lambar Housemate din naki sai na shi, me za kiyi da lambarsa when u have no business with him, in ni ce ke cewa zanyi a'a ba nasa zai ban ba gaskiya, amma fa har yanzu abun na ban mamaki ace duk mutuncin Housemate din nan naki bai taɓa requesting phone number din ki ba ko sau daya, ji ma sanda kika je Nigeria, to ko me yasa oho" Ita dai Khaleesat kallonta kawai take bata ce komai ba, Safiyyah tace "To wai ma ba kince har cewa yayi ki je gidan nasu ba, tun jiya nake ce maki mu shirya mu je kin ki, in baki je kin dubasa ba ta yaya zai san kema kin damu da halin da yake ciki, ai ance gaida me gaisheka, beside da bakinsa ya maki kwatancen gidan nasu ai, to me yasa baza ki je ba, da Nigeria muke sai mu ce ai bai kamata ba saboda yan sa ido da yan fassara lamari but this is USA Khaleesat, kuma abu ai kamawa yake for 3 days baki san halin da mutumin nan yake ciki ba gashi ke kanki kina testifying kyawawan halayyarsa, wallahi ki shirya in rakaki mu je ki dubasa da jiki, kuma kafin nan mu fara biyawa ta shopping mall kiyi masa shopping da zaki kai masa, shi ma sae yaji dadi wallahi" Khaleesat tace "Kawai sai in kama tafiya har gidan nasu duba shi? Ai bai ma dace ba sai kace wasu marasa kamun kai Safiyyah, be it in USA still bai dace ba, mu mata ne fa" Safiyyah ta mata wani kallo, can tace "Ai da naki matsalar ya taso haka ya cire kudadensa sama da miliyan goma sha biyar ko fin haka if i am not mistaken yayi solving maki matsalar ki, shi kuma bai da lafiya rai kwakwai mutu kwakwai kince zuwa dubasa rashin kamun kai ne, to rashin dacewa ya wuce zaman da ku ke yi gida daya? Shi wannan me za ki ce masa? Wani lokacin baki ma nazarin maganar dake fitowa bakin ki Khaleesat, in zuwa dubasa bai dace ba to zamanku gida daya ma ai bai dace ba be it in USA" Khaleesat dai sai kallonta take ta kasa cewa komai, can dai tace "Ban gane ba, Miliyan goma sha biyar for what??" Safiyyah ta mata wani kallo tace "Ohh for what ko? da yake business class ticket din da ya siya maki an gaya maki na wasan yara ne ai, to bari ki ji Business class ticket kusan 5000 dollars ne base on Airline, ki lissafa 5000 ko 4000 dollars kudin Nigeria kiga nawa zai baki" Khaleesat was speechless after realizing Safiyyah is saying the truth, banda dala dubu dayan da ya bata da zata tafi, sannan ga kuma domestic flight ticket from lagos to kano, and from kano to Abuja, bata mance irin hotel din da ta zauna na few hours a garin Lagos ba, sauke idonta kasa tayi bata sake cewa komai ba, Safiyyah ta ja tsaki tace "Wallahi ki ajiye wnn kauyancin naki ki zama wayayyiya ki dinga yin abun da ya dace, komai a rayuwar nan kamawa yake Khaleesat, to wai ku ka zauna apartment daya ba ace rashin kamun kai ba sai don zaki je dubasa bai da lafiya? ni abinda ke daure min kai kenan" Khaleesat dai taki cewa komai with many thoughts running her mind, a haka dai suka rabu kowa ya tafi gida... The next day sai da Safiyyah tasan duk yanda tayi convincing din Khaleesat da dadin baki da masifa da bacin rai, daga karshe Khaleesat ta yarda su je can inda Housemate dinta yace gidansu ne su dubosa amma fa don babu yanda ta iya da Safiyyah ne don har cikin ranta tsoron zuwa anguwan take don unguwa ce na masu kudi a kasar, to in ma sun je su ce me ya kai su? What if iyayensa ko wasu yan uwansa mata na gidan sai su yi yaya kenan? Kasa hakura tayi har sai da tayi ma Safiyyah wannan tambayar, Safiyyah tace "Dai dai kenan in ma iyayensa na gidan, ai ba Nigeria bane nan USA ne, kuma tsaf za su amshe mu hannu bibbiyu su yi farin ciki da zuwan mu don duba ɗan su muka je yi bai da lafiya" Khaleesat ta sauke wani boyayyen ajiyar zuciya, Safiyya tace "Amma ni har raina ina son sanin dalilinsa na dawowa apartment dinki ya zauna bayan ga nasu gidan can, nace da wani abu a kasa kince min ba haka ba, wallahi kilan ya san ki from somewhere Khaleesat" Khaleesat tace "Sai kuma kiyi ai, nace maki bamu taɓa sanin juna da shi ba" Safiyyah tace "Ma ji ma gani dai" Sai da Safiyyah ta fara jan Khaleesat zuwa inda za su siya kayan ciye ciye sannan suka yi ordering Uber da zai kai su unguwan, tun da suka shigo Safiyyah ke kallon manyan Gidaje with fascination, Khaleesat kuwa gabanta sai faduwa yake sai addu'a take a ranta, ita banda Safiyyah tayi insisting da babu abinda zai kawota wai duba Housemate dinta, dai dai kusa da gidan Uber din ya tsaya duk suka sauka, Safiyyah dake zaro ido tana kare ma Glass house din kallo tace "Ke kin tabbata nan ne kar mu shiga gidan mutane a kira mana 911 mu shiga uku Khaleesat" Khaleesat bata san sanda tayi dariya ba amma bata tanka ma Safiyyah ba, Khaleesat ta ciro wayarta tayi dialing number Salem ita kanta zuciyarta bugawa yake gaba daya she is afraid, sai da kiran ya kusa yankewa ya daga, sai gashi a mota zai fito daga cikin gidan, sauka yayi daga motar ganinsu, yana kallon Khaleesat da mamaki yace "Ohh you are here, sannu da zuwa...." Gaishesa tayi ta sauke idonta kasa kamar munafuka, ya amsa da fara'a, Safiyyah ma ta gaishesa sannan tace "Dama ta zo duba jikin Housemate dinta ne shi ne na rakota" Yana gyada kai yace "Ohh that's so thoughtful of her, mu je ciki to...." Suna biye da shi suka shiga cikin katon gidan, Safiyyah dai sai gwale ido take tana bin gidan da kallo ta gefen ido, ita dai Khaleesat gabanta sai faduwa yake sosai ko daga kai ta kasa, after walking briefly sai gasu sun iso entrance din shiga parlon gidan, kofar shiga parlon ma kadai sai ka kalla ka sake kalla, Safiyyah ta saci kallon motoci uku dake compound din kuma masu tsada, suna shiga parlon gidan Khaleesat ta hada ido da Ajay dake zaune kan kujera ga different fruits daga gefensa yana kallon abu a wayarsa at the same time yana cin apple dake hannunsa, 3 quarter ne baƙi a jikinsa with gray polo, tuni ta dauke idonta tsabar yanda ta rikice bata ma san sanda ta bude baki ta gaishesa ba tana makale bakin kofa, hade rai yayi ya dauke kai ya ci gaba da kallon abinda yake a wayarsa. 07087865788 ✍🏻 [20/05, 11:45 pm] +234 812 308 8480: ✨✨HALYSAAH✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 14.... Safiyyah ma dake kallonsa kamar munafuka tana in-ina tace "Good... good evening sir" Without looking at Safiyyah ya amsa yana cin apple dinsa, Salem na kallonsa speaking calmly yace "Ajay sun zo duba jikin Jay ne" Ajay ya ajiye apple din hannunsa, sai kuma ya kai wayarsa kunne alamar bashi da lkcn basa amsa, ganin haka Salem ya juya ya kalli su Khaleesat yace "Bari in masa magana a sama, za ku iya zama ku jira ni, have a sit pls" Daga haka ya nufi stairs, ko haurawa saman bai yi ba Khaleesat ta zaro ido tace "Innalillahi" da sauri ta koma bayan Safiyyah ganin wani jibgegen kare ya nufo su yana haushi, Safiyyah ta dinga buga ma karen jakar hannunta tana koransa ita ma a tsorace, Salem ya dawo parlon da sauri ganin haushin da karen ke yi zai yi attacking dinsu, Ajay ya mike ya nufi karen yana kiransa yace "C'mon Legend" Karen ya juyo da gudu ya dawo gun Ajay da yayi patting din kansa, Salem ya dawo kusa da su yana murmushi yace "Mu je saman kawai tunda tsoron kare ku ke, ai ba abinda zai maku kawai yaga baƙin fuskoki ne shi yasa" Khaleesat da jikinta ke rawa ta bi bayan Salem da sauri Safiyyah na biye da ita, a haka Salem yayi leading dinsu har sama zuwa Bedroom din Jay, knocking yayi yana tsaye bakin kofar, Khaleesat sai waige waige take tana ganin kamar karen zai sake biyo su saman, sai da Jay ya amsa ma Salem knocking din da yayi sannan ya kallesu yace "Bari in sanar masa yana da baƙi" Daga haka ya bude kofar dakin ya shiga ciki ya kullo, Safiyyah ta rike haɓa ta kalli Khaleesat murya can kasa tace "Ke wani tantirin ɗan iska ne wannan muka gaida a kasa ya mana walakanci haka?" Khaleesat bata tanka ta ba, har sannan kuma bata daina waige waigen da take ba don gani take fa karen nan zai iya biyo su har sama, sai ga Salem ya fito daga dakin yana kallonsu yace "Za ku iya shiga, ni zan ɗan fita sai na dawo" a hankali Khaleesat tace "Ohk mun gode" Bude kofar dakin tayi still gabanta na faduwa ta shiga cikin massive room din da sallama Safiyyah dake gwale ido na biye da ita a baya, wani ɗaddadan kamshi hade da sanyin Ac ne yayi welcoming dinsu a cikin babban dakin, Housemate din nata na zaune saman makeken gadonsa alamar Salem just woke him up, his room was just something else wajen tsaruwa da haduwa, Khaleesat taki yarda ta hada ido da shi zuciyarta na bugawa ta zauna nan ƙasan lallausan carpet din dakin, a hankali yace "C'mon Halysaah, ga gefen gado ku zauna, ko ku zauna kan kujera" Khaleesat bata dago kanta ba tace "I am comfortable here" Ya lura kamar she is frightened, ya kalli Safiyyah dake kallonsa bayan ita ma ta zauna, dan murmushi yayi mata yace "Hello...." Kana jin muryarsa kasan he is still recovering, Safiyyah ta gaishesa da fara'a tana tambayarsa jikinsa, yace "Alhamdulillah, ya karatu?" Tace "Alhamdulillah" Ya kalli Khaleesat yace "Ya kwana biyu Housemate? Hope you are doing good?" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa tace "Ya jiki?" Yana murmushi yace "Da sauki, Alhamdulillah" A hankali tace "To Allah Ubangiji ya sauwake ya kara lafiya" Yace "Ameen ya Allah" Safiyyah ta ajiye ledan hannunta kusa da gadon dakin tace "She got you this" Khaleesat ta kalleta, godiya yayi masu gaba daya, sai kuma ya fara kokarin sauka daga saman gadon yace "Bari in kawo maku ruwa" Edge din gadon ya zauna kamar bazai iya tashi ba, Khaleesat tace "Aa mun gode, we are okay" Ya kalleta a hankali yace "To ai ba ke kadai nayi offering ba Housemate" After some seconds ya tashi ya bude portable Fridge din dake dakin ya dauko masu ruwa da tsadaddun lemuka duk ya ajiye masu sannan ya fita daga dakin walking slowly, exactly irin kayan jikin Ajay ne a jikinsa shi ma, Safiyyah ta rike haba tana kallon Khaleesat bayan ya fita, sai kuma tayi kasa da murya tace "Khaleesat kin dai ga arziki ko? Gidansu kenan fa a Amurka ina ga Nigeria kuma?" Khaleesat ta hade rai tace "Pls stop this Safiyyah" Safiyyah ta rufe baki da sauri, sai kuma tayi kasa sosai da murya tace "Kuma haka fa, kar ace da Cctv a dakin mu ji kunya" Khaleesat ta wani kalleta tace "Ki ji kunya dai, tun da mun gaishesa ki tashi mu tafi kawai" a hankali Safiyyah tace "Gaskiya Housemate din nan naki is more than nice and calm, ni har naji yana burgeni wallahi, look how he welcomed us warmly duk da bashi da lafiya" Khaleesat ta daga ido ta kalleta sai dai bata ce komai ba, ita dai Safiyyah sai bin katon dakin take da kallo with fascination, tayi kasa da murya tace "In na samu irin wannan dakin ai mance me ya kawo ni kasar ma zan yi gaba daya, anya ma kuwa student ne Housemate din nan naki" Khaleesat ta hade rai tace "Tashi mu tafi tunda mun dubasa Safiyyah" Safiyyah tace "Amma ai kya jira ya shigo mu yi masa sallama ko, dadina dake a ko ina sai kin nuna halin ki, kamar ana koranmu daga shigowa gida kice mu tashi mu tafi" Budewar kofar dakin ya sa duk suka yi shiru, Housemate dinta ya shigo da sallama ya zauna kan kujeran dakin ya jinginar da kansa da kujeran, sai ga wani chef din gidan ya shigo da wasu tsadaddun cookies ya ajiye masu kusa da su, sannan ya juya ya fita, Jay na kallon Khaleesat yace "Naga kina son cookies sosai Housemate, here are some for you and ur frnd" Bata yarda ta kallesa ba tana wasa da gyalenta tace "I am okay, tafiya ma za mu yi" a hankali yace "So soon? Amma sai kun ci cookies tukun" Khaleesat ta ɗan kallesa suka hada ido a karo na farko tun shigowarsu dakin, sosai taji gabanta ya fadi tayi saurin sauke idonta, ya kalli Safiyyah yace "In bazata ci ba ke ki ci abunki... Amma ban san sunanki ba kawar Housemate" Safiyya tayi murmushi tana bude cookies din ta dau guda daya tace "Sunana Safiyyah Adam" Yace "Maa sha Allah, it's nice meeting you Safiyyah, i am Jawwad Ahmad, or you call me Jay" Safiyyah tace "Nice meeting you too Jay" ita dai Khaleesat wasa da gefen veil dinta kawai take kanta a kasa, Safiyyah ta bude handbag dinta saboda kiran wayarta da ake yi, tana dubawa taga Cousin brother dinta ne, ta mike tace "Let me pick a call pls" Jay yace "Alright Safiyyah" Kofa ta nufa ta bude ta fita sannan ta kullo masu kofar, ledan da suka shigo dakin dashi ya ɗan bude yace "You got me all this Halysaah" Khaleesat ta ɗan kallesa tace "Um" Yace "Ohk thank you so much i really appreciate" Tana kallonsa a hankali tace "Ya jikin?" Yace "I am getting better gradually, daxu sai naji ina sha'awar wannan tuwon da kika yi some days back" Tana kallonsa tace "Na vegetable soup?" Yace "No, wannan da na kasa ci, the dark soup, I can't remember the name" Bata san sanda tayi murmushi ba tace "Ok miyan kuka?" Yace "Shi... kawai naji shi nake son ci sincerely" a hankali tace "Ohk zaka je can gida anytime soon ne?" A hankali yace "Idan na samu lafiya in sha Allah" Ita dai Khaleesat kallonsa kawai take, shi kam idonsa na gun different direction, Ajay ne ya bude kofar dakin, kai tsaye ya shigo ya nufi Jay yana mika masa wayar hannunsa yana kallonsa, ita dai Khaleesat ta sunkuyar da kanta bata kalli inda yake ba, Jay ya amshi wayar yana duba screen din, sauke ƙafafuwansa yayi daga kan kujeran da yake zaune ganin wanda ke kan layi, ya kai wayar kunne da ladabi yayi sallama hade da gaisuwa, sai kuma yace "Alhamdulillah Abba da sauki, wayar a silent yake ne shi yasa" Sai kuma ya daga kai ya kalli Ajay jin abinda Abban ke ce masa, a hankali yace "A'a ba haka bane Abba, i do eat... but not much, ba gaskiya ya fada ba" Daga haka yayi shiru bai sake cewa komai ba, after a minute yace "To in sha Allah Abba, Allah ya kara girma" Sai da ya jira Abba ya katse wayar sannan yayi wurgi da wayar saman gadonsa yana kallon Ajay, wani kallo Ajay yayi masa ta gefen ido ya juya ya tafi ya dau wayarsa a kan gadon sannan ya fice daga dakin, Khaleesat ta gama tura ma Safiyyah text din da take na cewa tayi masu ordering Lyft su tafi gida, sai kuma ta daga kai ta kalli Jay, ganin mood dinsa ya canza, a hankali tace "Baka cin abincin ne ko?" Yace "Ki kyalesa mana, i took cereal daxu da safe kuma a gabansa, shi in bai bata min rai ba baya jin dadi a rayuwarsa" Khaleesat tayi shiru kamar bazata ce komai ba, can dai tace "To ai Cereal ba abinci bane, ka dai dinga ci ko kadan ne" Ɗan murmushi kawai yayi bai ce komai ba, tace "Shikenan, za mu koma, Allah Ubangiji ya baka lafiya" Yace "Baza ki bari Salem ya dawo yayi dropping din ku ba?" Tace "Aa, Safiyyah nasan brother dinta ne ke kiranta a waya, kaga tun daxu muka gama lectures bata koma gida ba" Yace "Ohk ni bari in ajiye ku" Khaleesat ta zaro ido tace "Aa kai da baka da lafiya, za mu yi ordering Uber do not worry about us pls" Khaleesat ta mike, yana ganin haka shi ma ya tashi, amma sai da ya dafa kujera for sometime saboda juya masa da kansa ya fara yi, A hankali Khaleesat tace "Pls kar kayi stressing kanka, just lie down and rest" Ya dago kansa yace "No, let me see you downstairs" Juyawa tayi ta nufi kofa, ya bi bayanta, ga mamakinta sai ta ga Safiyyah tsabar samun waje tana zaune parlon dake upstairs tana kallo tana cin cookies ga lemo a gabanta, to a ina ta samo lemun da cookies, Safiyyah ta washe baki ganin Khaleesat sannan ta mike tace "Shikenan mu tafi?" Jay da ta hango ne yasa tayi tsit, Khaleesat ta nufeta suka fara sauka downstairs a tare amma gabanta faduwa yake kar su kara ganin karen daxu, hakan yasa ta bari Safiyyah ta shiga gaba, Jay na biye da su a baya har suka sauko downstairs, ai ko karen na ganinsu ya nufo su da gudu yana haushi, Khaleesat ta juya a tsorace zata koma sama ta ci karo da Housemate dinta dake bayanta, ya rikota da sauri yace "C'mon, are you afraid of dog Halysaah?" Bayansa ta koma zuciyarta na bugawa, Safiyyah kuwa sai kora karen take da jakar hannunta fuska daure, shi dai Ajay na zaune parlor tun da ya kallesu sau daya ya dauke kai ya ci gaba da kallon Football da yake, sai da Jay ya kori karen sannan ya juya da gudu ya koma gun Ajay ya zauna saman kujeran kusa da shi, Jay ya juya ya kalli Khaleesat da ta marairaice ita ma tana kallonsa, ya ɗan yi murmushi yace "Ba abinda zai maku ai, bai san ku bane shi yasa...." ita dai bata ce komai ba, Jay ya jufi Ajay yace "Ajay ina makullin motana?" Ajay yace "Me zaka yi da makullin mota?" Khaleesat dai tuni ta nufi kofar fita parlon da sauri don ko kallon Ajay bata son yi, Safiyyah kam tana kallon Ajay tace "To sai anjima, Nagode sosai" Yace "Allah ya tsare" sallama tayi ma Jay shima sannan ta bi bayan Khaleesat, Jay yasan bazai basa makullin ba, hakan yasa ya duba aljihun Ajayn ya zaro few dollars sannan ya juya ya bi bayan Safiyyah, duk yanda yayi da Safiyyah ta amshi kudin taki amsa, Khaleesat tuni ta kusa fita daga gidan gaba daya, a haka Safiyyah ta bi bayanta. Safiyyah na kallon Khaleesat bayan sun shiga Lyft har sun fara tafiya ta rike haɓa tace "Ke ashe wannan gayen da muka yi misunderstanding da farko da muka shigo gidan yana da kirki sosai, in gaya maki da na zauna parlon nan na sama ni kadai ya zo wucewa ya ganni sai ya tsaya yayi powering min TV, har da kunna min wutan parlon, ya kuma nuna min fridge in dau lemo in sha, wallahi i never expect such kind gesture from him duba da yanda ya amsa mana gaisuwanmu da muka shigo parlon da farko, ashe mun yi misperceiving dinsa ne" Khaleesat tayi kamar ma bata ji abinda Safiyyah ke cewa ba. 07087865788 ✍🏻 [20/05, 11:46 pm] +234 813 644 0264: Read My Book "HALYSAAH" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6 ✨✨HALYSAAH✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 15..... Wajen karfe takwas na dare Khaleesat na zaune parlor tana duba wani reading material dinta wayarta ya fara vibrate, daukan wayar tayi taga number Salem, ita dai kallon screen din kawai take at first, after some seconds ta daga ta sa Hands-free tayi shiru tana saurare, daga daya bangaren aka mata sallama, muryar Housemate dinta ta ji, ta amsa sallamar tare da gaishesa, yace "Ya kika je gida Halysaah?" Tace "Lafiya lau" Yace "How about Safiyyah?" Tace "Tana can gidansu" Yace "Good, thank you so much for the visit" a hankali tace "Allah ya kara lafiya" Yace "Ameen Housemate" Daga haka yayi mata sallama ya katse wayar, bata kai ga ajiye wayar ba wani kiran ya sake shigowa ta ga Abdul ne, sai a sannan ta tuna damuwar da take ciki for days now, nan da nan mood dinta ya canza, tayi picking call din ta saka hands free sannan ta ajiye a gefenta tana ci gaba da duba reading material dinta a hankali ta gaishesa, yace "Didn't you see the money i sent to you?" Ta girgiza kai tace "Ban kula ba" yace "To ki duba" Katse wayar yayi ta jinginar da kanta jikin kujera with many thought running her mind.... Washegari da yamma bayan Khaleesat ta idar da sallah tana zaune tayi dialing number Salem, yana fara ring ya daga, bayan sun gaisa tace "Dama abinci ne zan ma Housemate dina yace min yana so, ban san ko zaka iya zuwa karfe biyar sai ka tafi masa da shi ba, that's if you are available and u don't mind doing so pls" Yace "Oops naje Pennsylvania daxu da safe, but za ki iya zuwa gidan ki kai masa ai, he is at home" A hankali Khaleesat tace "Ohk" Yace "Yeah, ki kai masa kawai can gidan" Tace "To nagode" a haka suka yi sallama ta ajiye wayar, Allah ya so bata dora girkin ba don ta san babu abinda zai sake maida ta gidan nan dai, tayi zuwan farko tayi na karshe. Khaleesat na zaune tare da Safiyyah bayan sun gama lectures din su na ranan, Safiyyah tace "Are you checking on ur Housemate even if ta waya ne kuwa Khaleesat?" Khaleesat ta kalleta tace "I don't have his number ai" Safiyyah ta dinga kallonta da mamaki, can ta girgiza kai tace "Ni ban san me yasa kike haka ba, why won't u ask that guy Salem ya baki? It's almost 10 days now da muka je gidan dubasa tunda kika ga har yanzu bai zo apartment dinku ba kinsan kilan ko bai ji sauki bane" Khaleesat tace "There was a time da muka yi waya da Salem din yace zai turo min lambarsa kuma bai turo ba shi sa har yau ban sake masa magana ba naga kamar baya son tura lambar ne, sannan kawai i assume kilan wannan arrogant guy din ne na gidan yayi stopping dinsa from coming to the house, i suspect they are kind of related or something like that" Safiyyah ta tabe baki tace "To ko in raka ki mu sake zuwa dubasa ne?" ko rufe baki bata yi ba Khaleesat tace "I am going no where, sai dai in ke zaki je sai in masa tuwo ki kai masa, dama ranan da muka je yace min yana son tuwo da miyar kuka, but for me babu abinda zai sake maidani gidan nan wallahi" Safiyyah ta dinga kallonta, can tace "Gaskiya zuciyarki kamar dutse yake Khaleesat, wato har ce maki yayi yana son cin tuwo amma kika kasa yi ki kai masa saboda wani banzan dalilinki, gaskiya you are not nice at all sorry to say" Khaleesat ta mike tace "Ki kirani ko ma me zaki kirani amma wallahi bazan koma wannan gidan ba as far as that bossy Man is in the house, kawai sai in kama hanya in sake komawa don yaji dadin kara raina min hankali ya walakanta ni, in dai ke zaki je zan yi girkin in baki, after all kince the arrogant guy is nice to you ai" Safiyyah bata tanka ta ba ta fara danna wayarta kawai, a haka suka rabu ko sallaman kirki basu yi da juna ba, har Khaleesat ta isa gida a lyft bata san sun iso ba, a duk kwanakin nan Allah ya sani Housemate dinta na ranta don babu ranan da zai zo ya wuce bata tunasa a zuciyarta, ba willingly taki zuwa gidan ta dubasa ba kawai wannan mutumin ne bata son ta sake haduwa da, sannan she is afraid of the huge dog in the house, kar ma taje mutumin ya sakar mata karen ta shiga uku, amma a ko da yaushe Housemate dinta yana ranta tana kuma son sanin how he is feeling, a hankali ta bude motar ta sauka duk jikinta a sanyaye ta nufi apartment dinta ta bude kofar ta shiga, turus tayi a living room din ganinsa kwance kan 3 seater yana bacci, juyawa taga yayi with his eyes still close yace "Good evening Halysaah" Sauke idonta tayi daga kallonsa, walking slowly ta karasa cikin living room din ta nufi can kusa da single sitter ta tsaya still looking at him, a hankali ya bude ido ya fara bin parlon da kallo alamar he is looking for her, suna hada ido calmly tace "Good evening" Mikewa zaune yayi trying to recover fully from his sleep yana shafa fuskarsa yace "How are you?" Tace "Alhamdulillah, ya jikin?" Yace "Naji sauki ai" Shiru tayi kamar me tunanin abinda zata ce, can kuma dai tana rike da edge din gyalenta cikin nutsuwa tace "Naga baka zo bane, i thought jikin ne har yanzu...." Ya girgiza kai without looking at her yace "Abbana ne yasa na je Nigeria, we spent 6 days in Nigeria, jiya muka dawo" Yana fadin haka ya daga kai yaga kallonsa take, da sauri ta kauda kanta tana nodding tace "Ohk" Daga haka ta juya ta nufi dakinta kamar munafuka, ya koma yayi kwanciyarsa. After almost an hour Khaleesat ta fito parlor, ta samesa zaune ya gama baccin yana danna laptop dinsa, kanta a kasa ta karasa cikin living room din ta dan kallesa suka hada ido tana kame kame tace "Dama tambayarka zan yi in maka tuwon ne yanzu zaka ci?" Yace "Tuwo kuma? Aa kinga you just came back from school, ki bari next time in sha Allah" Tace "Ohk" Daga haka ta tafi kitchen to make a light dinner, bayan ta gama girkin ta fito parlor, har sannan yana nan zaune, ta ɗan kallesa tace "You care for some?" Ya kalli hanyar kitchen din sai kuma yace "Let me dish it my self" Daga haka ya ajiye laptop dinsa ya mike ya tafi kitchen din, ita dai tana tsaye ta bi sa da kallo, bayan few minutes ya fito da bowl din pasta din ya zuba very little quantity, with another plate of the pasta, ita dai kallonsa take, ya mika mata na plate din ta sauke idonta ta amsa, ya zauna ya ajiye bowl din nasa, a hankali tace "Wannan ne zai isheka?" Yace "Eh" juyawa tayi zata bar wajen, yace "Bedroom za ki je ki ci abincin kenan" Ta gyada masa kai tayi tafiyarta daki. Wajen karfe tara na dare Khaleesat ta saka hijab dinta jin yana knocking kofarta sannan ta tafi ta bude kofar, yace "Sai da safe Halysaah, i am going home" at first shiru tayi, can kuma a hankali tace "Why are u having two home?" Ya ɗan buda ido yayi murmushi yace "One is a home, the other... a comfort zone" Ta langwabar da kai tace "U said two same thing ai, A Home is also known as a comfort zone" Dariya yayi yace "Not in my case Halysaah, they are two different thing to me" Shiru tayi kafin tace "So now, which is home and which is comfort zone?" Yayi murmushi yace "Kema dai kamar er jarida, how is ur frnd?" Tace "She is fine" Yace "And ur Bossy boyfriend, hope ya daina saka ki kuka dai yanzu?" Ta wani kallesa zata kulle kofarta da sauri yace "Wait, it's just a harmless question Halysaah" Tace "To da nace maka kuka yake sa ni?" Yace "Ohk, Allah sa kar in zo ina baki hakuri kwanan nan bayan ya saka ki kukan, and before i forget me yasa baki cin cookies dake kitchen?" Tace "Nawa ne da zan ci?" Yayi shiru kamar bazai ce komai ba, can kuma yace "To ki dinga ci daga yau duk abinda kika ga na siya ki dauka idan kina bukata, I didn't buy them all because of my self alone, ko da namiji ne a gidan nan ko wata mace daban in zan siya abu in ajiye zan siya ne in surplus not for only me, kin gane ko? Har bottle water ina siya mana ne mu biyu ba ni kadai ba, after all there is love in sharing" Ita dai idonta na kasa bata ce masa komai ba, Yace "Good night" juyawa yayi ta bi sa da kallo har zuwa parlor, sai kuma ta kulle kofar dakinta a hankali. Washegari Asabar Khaleesat ta gama laundry da take a kitchen, tayi tidying din duk gidan sannan taje tayi wanka ta fito parlor tana tunanin abinda zata girka kafin ta fara karatu cause it's almost 12pm, tun karfe goma Housemate dinta ya shigo gidan ya wuce Bedroom dinsa, ta ma san bacci, ita kam mamakin yanda baya gajiya da bacci take, knocking kofar parlon aka yi, she is expecting Safiyyah dama amma bata yi tunanin da wuri zata zo ba, ta karasa gun kofar ta bude a bit relieve ta samu me taya ta girki, da mamaki ta bi sa da kallo bayan ta koma gefe don da ta ci gaba da tsayuwa wajen taga alamar bangajeta zai yi ya shiga parlon, direct taga ya nufi dakin Jay ya bude ya shiga, kasa rufe baki tayi tsabar mamaki, tana jin sa yana ma Jay bala'i a dakin, ita dai bata ji muryar Jay din ba, Jay ne ya fara fitowa daga dakin, kamar yanda ta zarga kuwa baccin yake, laptop din da ya bari kan kujera da ya shigo daxu ne ya dauka, Ajay na fitowa ya mika masa laptop din, a mugun fusace Ajay yace "What the hell should i do what with it again bayan lokaci ya kure? Kasan implications din da abin nan da kayi zai ja min kuwa?" A karo na farko Jay yace "Kai dalla wayar a silent yake, kuma ni ban san akwai recent aikinka a ciki ba, da bazan taho da shi ba ai" Ajay dai kallonsa kawai yake kamar ya shaƙo sa, Jay ya zauna kan kujera ya jinginar da kansa tare da lumshe ido, banda hararan Ajay babu abinda Khaleesat da ke tsaye parlon take yi, lkci daya Jay ya mike yace "Hey let me see you off, wanka zan yi" a takaice Khaleesat tace "And pls Housemate warn him not to ever barge into someone else's apartment like this again, this isn't a shopping Mall da zai shigo kai tsaye" A tare suka juya suna kallonta gaba dayansu, Ajay yayi facing dinta calmly yace "Ke, da ni kike wannan maganar ko wa?" Ta wani kauda kai fuskarta a daure tace "In baka son ayi da kai kar ka sake shiga gidan mutane babu Excuse, after all ba tare muke renting apartment din ba da zaka shigo min gida without notice, idan wajen abokinka ka zo maturely sai ka jirasa a waje, you don't have to push ur way into people's apartment like it's a shopping complex" Ajay that was speechless ya kalli Jay, Jay ya shafa kansa yace "Why didn't u knock and wait for me outside, after all she is saying the truth" Khaleesat tace "Ni in ya sake shigo min gida haka wallahi 911 zan kira masa..." Ajay ya ciro wayarsa a aljihu yana mika mata yace "Call them immediately" Ta jefa masa wani kallo tayi hanyar dakinta, Yana kallonta da kyau yace "I will definitely deal with you" Ita dai tuni ta shige dakinta ta kulle kofar da makulli, Jay na kallonsa yace "Me yasa zaka shigo mata gida kamar tsohon barawo?" Ajay yace "Za kayi bayanin me kake yi da mace under the same roof in America, macen ma da ka kusa haifa, i promise to report you back home, ita kuma i will teach her the lesson of her life" Yana kai wa nan ya fixge laptop dinsa a hannun Jay, Jay dake murmushi yace "Babu abinda ka isa kayi mata don ta gaya maka gaskiya Malam, kai waye da baza a gaya ma gaskiya ba" Tuni Ajay ya fice daga parlon, Jay ya zauna kan kujera ya dafe kansa yana dariya, the incident was just funny to him, kallon kofar dakinta yayi yana mamakin dama wai haka yarinyar nan take amma take ma saurayinta kuka? Mikewa yayi ya nufi dakin nata yayi knocking kofar yace "Halysaah" sai da ya kirata sau uku sannan ta bude kofar a hankali tana leka parlon kana ganinta kasan a tsorace take, dariya yayi yace "Kinsan waye shi da kika masa rashin kunya Halysaah?" Ta wani turo baki tace "To ni ina ruwana da koma wanene shi, saboda me zai shigo min gida kamar wani barawo, where is it done that way? Ni dai wallahi kar ya sake zuwa min gidan nan in ba haka ba in kira 911" Jay dai sai sauraronta yake, can yayi murmushi yace "So dama kina da baki haka amma kike ma saurayin ki kuka?" Khaleesat ta wani kallesa ta hade rai tace "Ni bana son haka" still smiling yace "Ok, sorry" keeping a straight face tace "Ya tafi?" Jay ya juya zai bar wajen yace "Ya tafi mana" Da sauri tace "Plss ni dai kayi masa magana kar ya sake zuwa, if there is anything ai sai ya kira kaje can gidanku ka samesa kawai ba sai ya zo nan ba" Jay dai murmushi kawai yake yace "Ohk" parlor taga ya tafi, ta koma dakinta ta zauna bakin gado, har sannan gabanta faduwa yake, ita kanta bata san inda ta samu courage din gaggaya masa abubuwan da ta gaya masa ba, ko don dama tana jin haushinsa ne yasa ta samu irin wnn courage din oho, bata fito daga dakinta ba sai da tayi sallan zuhur, a hankali take tafiya ta shigo cikin parlorn, gani take kamar zai sake dawowa gidan at anytime, ai ko wallahi yan sanda zata kira masa, Zaune taga Jay a parlon yana danna wayarsa, tana tsaye bayan kujera tace "Did u warn him not to come back plss?" Jay yace "To ke meye damuwarki ba kin masa warning kar ya sake dawowa ba, ai bazai dawo ba" Kamar zata yi kuka tace "Wallahi zai iya dawowa, kuma in ya dawo baka nan ya zan yi?" Dariyar da yake dannewa ne ya taho masa yace "Ina kuwa zan san yanda za ki yi, ke wa ya aike ki yi masa rashin kunya? Da sai ki yi shiru da bakinki har in fitar da shi daga gidan, Laptop dinsa na dauko daga can gida yana bacci ban san akwai aikinsa da zai yi put foward ta email ba, yana ta kiran wayana kuma ina bacci na sa wayar silent, that was what brought him here" Zaunawa tayi kan kujera tace "That doesn't still warrant him ya shigo gidan mutane kai tsaye, ko magana bai min ba ina bude kofa ya kusa bangajeni fa ya shigo parlon, am i a joke to him?" Dariya Jay yayi yana gyada kai yace "This energy u used in attacking him Allah ya baki irin energy din kiyi using ma Boyfriend din ki" Wani kallo Khaleesat tayi masa, shi dai murmushi kawai yake still not looking at her yace "Naga kamar kin damu da abinda kika masa, ko in kirasa ki basa hakuri ta waya komai ya wuce?" mikewa tayi a takaice tace "Allah ya kiyaye" Daga haka tayi wucewarta kitchen, shi dai murmushi kawai yake looking at a different direction, yasan yau da kyar Ajay yayi bacci akan abinda tayi masa. Bayan Khaleesat ta gama girkin da take ta fito parlor tana kallon Jay ganin fita zai yi don har ya shirya yana saka agogon wrist dinsa without looking at her yace "I think sai gobe zan dawo in sha Allah" Ta marairaice amma bata ce masa komai ba, har cikin ranta ta fara jin tsoron kasancewarta ita kadai a gidan, ya ɗan kalleta yace "Any problem?" Ta hade rai tace "Toh ka bani makullinka idan ka zo goben sai kayi knocking in bude maka kofar" Da mamaki yace "Why?" Tace "So that baza kaje ka ajiye key din recklessly ba wannan mutumin ya gani ya dauka" Yayi dariya yace "To ya dauka yayi me da shi?" Ta nufesa tace "Bani" ba musu ya bata makullin ta amsa sannan a hankali tace "To abincin fa?" Yace "Abinci? Wani iri?" Bata tanka sa ba ta juya ta koma kitchen din, after some minutes sai ga ta ta dawo da plate din rice and stew, ya ɗan bude ido yace "Wa zai cinye duk wannan?" Tace "Kai mana" Ya zauna sannan ta mika masa abincin, yana girgiza kai yace "It's very plenty" tace "Should i get you water?" Yace "I will appreciate that" kitchen din ta koma ta dauko masa ruwan gora da drink din gwangwani, yace "Thank you Halysaah" dakinta ta wuce, after a while taji yayi knocking kofar dakinta, bayan ta bude yace "Zo ki bude min kofar zan tafi" Makulli ta dauko ta tafi ta bude masa kofar yace "Thank you, see yah tomorrow" ita dai bata ce komai ba ya fita daga parlon ya nufi garage, a hankali ta kulle kofar da makulli sannan ta tafi window ta ɗan bude labulen tana kallonsa har ya bar garage din after some minutes, Sake curtain din tayi, walking slowly ta tafi kitchen, bude abincin da ya rufe tayi taga kadan ya ci a ciki, Allah yasa yayi spoon hudu, naman ma kawai daya ya ci, kulle abincin tayi ta dawo parlor ta zauna, dai dai nan taji anyi knocking kofar parlon mikewa tayi da sauri tana kallon kofar a tsorace, da kyar tace "Waye??" Muryar Safiyyah taji, lkci daya ta sauke ajiyar zuciya sannan ta tafi ta bude kofar, Safiyyah tace "Har kin gama laundry din?" Khaleesat tace "Na gama" Safiyyah tace "Housemate din naki ya fita kenan?' Khaleesat tace "Eh" Safiyyah tace "Jiya da daddare da kika gaya min ya zo gidan ta chat wallahi nayi farin ciki, don mutumin na da kirki sosai" Khaleesat bata tanka ta ba, ta koma cikin parlon ta zauna tace "Ban gan ki da laptop dinki ba" Safiyyah tace "Abeg i will use urs, bani da strength din dauko laptop, kin yi girki kuwa? Don yunwa nake ji, wancen er iskar matar faten wake tayi saboda tasan ba na ci, hegiya dama bayerabiya ce ta wajen uwarta ai" Dariya kawai Khaleesat tayi ta mike ta tafi kitchen, abincin ta zubo ma Safiyyah, ita kuma ta dau wanda Housemate dinta ya rage, ta dauko masu ruwan gora da lemon kwali daya.... 07087865788✍🏻 [20/05, 11:46 pm] +234 813 644 0264: ✨✨HALYSAAH✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 16..... Ko da wasa Khaleesat bata ba Safiyyah labarin abinda ya faru tsakaninta da Ajay ba, amma fa bata da rest of mind gani take kamar zai iya dawowa gidan at anytime, upon all her restlessness bata ji tayi da ta sanin abinda tayi masa ba, dama haushi yake bata, Safiyyah na kallonta tace "Ke kwana biyu shiru banji kince ga abinda Abdul yayi maki ba ko dai ya fara canzawa ne? This is so unusual, ko baki gaya min ba in dai ya maki wani abu you are always moody in school, ta haka nake ganewa" Khaleesat na powering laptop dinta ta tabe baki tace "Ni ina naga wannan time din yanzu ga exams a gabana" Safiyyah tace "Atoh dai, wallahi naji dadin da kika fara daukar shawarata kina fita sabgarsa, sauranki abu daya yanzu" Khaleesat ta daga kai ta kalleta, Safiyyah ta gyara zama tace "Saura ki fara mayar masa da magana, in ya gaya maki daya ki gaya masa biyar" Ita dai Khaleesat bata sake ce mata komai ba tana neman softcopy na course din da za su yi studying tare da Safiyyah. Bayan tafiyar Safiyyah... Khaleesat ta wanke utensils da suka yi amfani da sannan ta wuce dakinta, wayarta ta dauka ta shiga WhatsApp don ganin ko Ummanta tayi mata reply din message da ta ajiye mata daxu, wajen karfe goma da rabi tana shirin kwanciya wayarta ya fara ring, dauka tayi taga Abdul ne ke kiranta, ta dinga kallon wayar, tun sanda Ummanta tace mata tana ganin kamar lkci aka tsayar take wani jin tsanarsa a zuciyarta, gashi yaki gaya mata ko da gasken an tsaida lkcn ko ba a tsayar ba don Ummanta ba wai ta tabbatar bane ita ma a gari ta ji, dama tana Nigeria din ne ta san gun warce zata je taji ko hakan ne ko ba haka ba, ɗaga kiran tayi kafin ya katse ta kai kunne, muryarta kamar me bacci ta gaishesa, ya amsa, a hankali tace "Ya aiki?" Yace "Lafiya lau" Shiru tayi bata sake cewa komai ba, yayi ƙasa da murya yace "I don't know, kawai ina missing din ki ne yau, i want to be with you Baby" Ta kauda kai kamar irin yana kusa da ita din nan tace "Um" Yace "Yaushe za ku fara jarabawan?" Tace "Nan da wata daya" A hankali yace "Ohk, sai da safe, naga kamar kin fara bacci" Tace "Um, ina son tashi inyi karatu ne anjima shi sa na kwanta da wuri" Yace "To ci gaba da baccinki, sai mun yi magana" Daga haka ya katse wayar, ta jefar gefenta ta ci gaba da chatting da take da Ummanta. Washegari lahadi Khaleesat na zaune dakinta tana morning Supplications dinta taji ana kwankwasa kofar parlor, wayarta ta jawo tana duba agogo taga bakwai ya wuce, ta daure ta mike tana tafiya a hankali ta fito parlor, bayan ta karasa bakin kofar with calmness tace "Waye?" Taji muryar Housemate dinta yace "Good morning" bude kofar tayi ta koma gefe ya shigo, sau daya ya kalleta yace "How was ur night" Ta kulle kofar tace "Alhmdlh" Materials din hannunsa ya ajiye saman 1 seater sannan ya kwanta kan doguwar kujera, ita dai bin sa tayi da kallo taga har ya kulle idonsa yana gyara kwanciyarsa alamar bacci zae yi, tana tafiya a hankali ta koma dakinta, ta karasa azkar dinta sannan ta kwanta. Har wajen karfe daya na rana Khaleesat bata fito dakinta ba, ta ɗan juya daga kwancen da take tana kallon kofar dakinta jin ana knocking, kiranta taji Housemate dinta ke yi, mikewa zaune tayi still tana kallon kofar amma bata sauka daga kan gadon ba, Calmly tace "I can hear you" Yace "Are you alright? Naga kamar baki yi breakfast ba ko?" Shiru tayi bata ce komai ba, bude kofar taga yayi, ta gyara blanket din jikinta tana kallonsa, ya tsaya daga bakin kofar dakin yace "Hope nothing?" Ta langwabar da kai tace "Nothing" Yace "To me yasa baki fito kinyi breakfast ba or are you fasting? Beside today is sunday" Ta kauda idonta tace "Kawai dai..." Sai kuma tayi shiru, ya karasa cikin dakin yace "Kawai dai me?" Kamar baza tace komai ba sai kuma dai tace "Ina jin ciwo a kafana ne" Yace "Ciwo a kafa kuma? Yana maki haka ne?" A hankali tace "Once a while" Shiru yayi jin abinda tace, can yace "Then what is the cause?" Ta ɗan kallesa, sai kuma ta bude hannu alamar bata sani ba, yace "Kun taɓa zuwa hospital a kan hakan?" Ta dai yi shiru without looking at him, sai kuma tace "It's fine, i will get better before evening in sha Allah" Ya juya as if trying to diagnose without examination the cause of her leg pain at her age, sau daya ya kalli gaban dressing mirror dinta sai kuma ya juyo yana kallonta yace "Ok i get, Allah ya sauwake..." Ta ɗan kallesa, yace "Try getting a hot shower, you will feel better" Juyawa yayi ya fita daga dakin, a hankali Khaleesat ta koma ta jingina da pillow, ko tashi tsaye bata jin zata iya a yanzu dai, kilan zuwa can anjima ta ɗan ji relieve before she can stand up and do anything, kiran Abdul ne ya shigo wayarta ta kife wayar taki dagawa don ko magana bata so, after some minutes ta kalli kofarta jin knocking at the same time ya bude kofar dakin ya shigo ciki rike da cup din hot chocolate, sauke idonta tayi daga kallonsa ya karasa har side din da take ya duka yana mika mata Mug din hot chocolate din yace "Try drinking this, will get u pain reliever now" Ta amshi Mug din without looking at him a hankali tace "Thank you" Yace "You are welcome" Daga haka ya fita daga dakin ta bi sa da kallo babu ko kiftawa, yana fita kiran Abdul ya sake shigowa wayarta still taki dagawa daga karshe ma tayi silencing wayar, khaleesat na gama shan hot chocolate din ta ajiye cup din a bedside drawer sannan ta koma ta kwanta tayi lamo kan pillow, kamar zata kira Safiyyah daxu wajen karfe sha biyu sai kuma ta fasa hoping the ache will subside, har ta fara bacci Housemate dinta yayi knocking wajen karfe biyu almost 20 mins bayan fitarsa daxu, sai da ta amsa sannan ya bude kofar, ita dai bata juyo ba, ya zaga ta inda take calmly yace "Are you sleeping Halysaah?" Ta bude ido tana girgiza kai, ya ajiye ledan abincin hannunsa da pain reliever da ya siyo mata yace "Baki yi hot shower da nace kiyi ba?" Tace "Zan yi" Yace "Ohk ga maganin sai ki ci abinci ki sha" Ta mike zaune without looking at him, a hankali tace "Thank you" Yace "Zan fita but i will come back around 6pm in sha Allah" Tana kallonsa tace "Toh makullin gidan fa?" Ɗan murmushi yayi yace "Ai a jikin kofar kika bar sa daxu da kika bude min da safe" Tace "Amma baza ka tafi da shi ba ai" Yace "To taso ki kulle kofar" Ta wani kallesa, er dariya yayi yace "Shi fa Ajay nasan yanxu kuma ya mance abinda ya faru tsakanin ku, may be sai ranan da ya kara ganinki zai tuna, but for now i am assuring you ya mance wallahi he is even busy with his upcoming defense, beside you misperceived him, Ajay is more than nice and calm, ba shi da matsala, kawai dai shaidan ne ya saka rashin jituwa tsakaninku tun a ranan da ku ka hadu" Khaleesat dai ta kyabe baki don ko duk jikinta kunnuwa ne bazata taɓa yarda da abinda yake fadi ba, Jay yace "Baki yarda ba ko?" Ta buda ido sosai tace "To dama saboda me zan yarda?" Dariya kawai yayi yace "Take care of ur self Halysaah, in kin ci abincin ki sha magani, let me get you bottled water" Daga haka ya nufi kofa ita dai ta bi sa da kallo har ya fita, sai gashi ya dawo mata da ruwan gora mara sanyi ya ajiye a inda ya ajiye mata ledan abinci da magani wato bedside drawer, yace "See yah later" a hankali tace "Thank you, and pls do not mishandle the key" Murmushi kawai yayi ya gyada mata kai ya fita daga dakin ya kullo mata kofar, ta sauke idonta kasa, after some minutes ta dau ledan abincin da ya ajiye mata a hankali tana budewa don ganin abinda ya siyo mata. Karfe shidda saura Khaleesat na zaune kasan dakinta ta kwantar da kanta jikin gado tana voice note da Ummanta, zuwa sannan she is feeling very much better don har ta gyara dakinta ta wanke bandaki tayi wanka, parlor ne dai taji bazata iya gyarawa ba, wajen karfe hudu suka yi chatting da Safiyyah tace mata zata zo karfe bakwai, Khaleesat ta dan yi jim bayan taji kamar an bude kofar gidan, gabanta ne ya fadi bayan Ajay ya fado mata, ta ajiye wayar hannunta a hankali tana kallon kofar dakinta, after few minutes taji an yi knocking kofar dakin, she felt a bit relieved, with calmness tace "I can hear you" Taji muryar Housemate dinta yace "Can i open the door?" Tace "Okay" bude kofar dakin yayi yana daga bakin kofar a tsaye yace "Good evening Housemate, how are you feeling?" Tace "Da sauki" Yace "Are you sure?" Sai a sannan ta daga kai ta kallesa, ta dan kwantar da kanta gefen gado tace "It's better than before" Yace "To Allah ya sauwake, where you able to go to the kitchen?" Ta gyada masa kai, yace "Ohk" Har zai kulle mata kofar sai kuma ya tsaya yace "Ko mu dan yi strolling as exercise, around the neighborhood, it will help you feel much better too" Khaleesat ta daga ido ta kallesa, yace "I will be waiting for you at the parlor, make sure to put on ur jacket cause it's freaking cold outside" Yana fadin haka ya fita daga dakin, Khaleesat dai na ta zaune kamar me nazari, it took her almost 5 mins of deciding kafin ta mike a hankali, veil dinta kawai ta dauka ta yafa ta dau wayarta tana tafiya a hankali ta fito daga cikin dakin, tsaye ta gansa ya jingina jikin pillar dake kusa da study area yana danna wayarsa daya hannunsa rike da jacket dinsa, yana ganinta yace "Are you ready? Where is ur jacket?" Karasawa yayi inda take tsaye yace "It's cold outside" Yana fadin haka ya ajiye mata Jacket dinsa kan kujeran dake kusa da ita yace "Use this, bari in dauko wani" Dakinsa ya koma ita dai ta bi sa da kallo, ba a dau lokaci ba sai gashi ya dawo parlon with another Jacket, ya saka a kan rigar jikinsa yace "Mu je" Ta sauke idonta ta dau Jacket din nasa, Kofar parlon ya nufa ta bi bayansa har suka fita daga parlon, ya kulle kofar ya kalleta yace "Na lura kina son so much perfume ke dai" Ta girgiza kai tace "A'a ni ban sa ba yanzu" Yace "Ohk" A tare suke tafiya with nobody saying anything, tun ba su kai ko ina ba taji tana jin sanyi sosai, hakan yasa ta ɗan saci kallonsa sannan ta saka jacket din hannunta yace "Ai na zata baza ki sa ba kina forming big gal" Kawai dai tayi murmushi bata ce komai ba, tana jin kamshin turarensa da ya cikata na jikin Jacket din, dai dai yake tafiya da ita to keep same pace with her, slowly suke tafiyar with absolute silence har suka yi nisa away from home, Jay yayi breaking silence din yace "Soon za a fara snow" Tace "In sha Allah kafin nan mun gama Exams dinmu" Zai yi magana wayarsa ya fara vibrate ya ciro a aljihunsa yana duba me kiransa, ta gefen ido ta kalli wayar tasa taga Ajay, yayi silencing wayar ya mayar aljihunsa, ta tabe baki tace "Shi dole sai ya dinga damunka da kira ne as if you are with his kidney?" Jay yayi dariya yace "Kidney ai me sauki ne, cewa za ki yi kamar life dinsa na wajena dai, a rana sai ya kirani sau ashirin in banyi hankali ba" Khaleesat ta kyabe baki sai ga shi ya sake kiran wayar, Jay ya kara ciro wayar yayi picking ya sa Hands-free yana tafiya yace "What again?" Daga daya bangaren Ajay yace"I need ur laptop, zan duba references dinka, na mance zan shiga schl gobe, i am outside with my frnd now" Jay yace "Da laptop din na fita ai, kuma i am not coming back home anytime soon" Ajay yace "Gidan wannan mara kunyan ka koma kenan? Wai are you even okay Bruh? Me kake yi da wannan yarinyar da ya sa kake zama gidanta? Ko iskanci ka fara ne? In ma iskancin zaka yi why with that little local brat pls?" Jay that was trying not to laugh yace "Kai kar ka bata min rai fa" Ajay yace "On a serious note idan baka daina zuwa gidan nan ba i promise you am gonna report you back home kasan karamin aikina ne hakan ko?" Jay yace "In ka fasa, kai duk takurani da kake da yan iskan abokanka a can gida ban kai report ba sai ni da na bar maka gidan for peace to reign shi ne zaka kai karata? To references din ma baza a nuna ba, go and sort ur self out" Yana kai wa nan ya katse wayar ya mayar cikin aljihu, ita dai Khaleesat bata kallesa ba kuma bata ce komai ba amma har cikin ranta take jin Ajay bai mata ba, she doesn't like him or anything concerning him, ta tsani mutum that is too pompous and proud of himself, Jay yace "Baya karatu fa, in ma wani aiki ne sai dai kai kayi ya gani sannan yayi nasa, har ma nasan yafi naka at the end" Khaleesat tace "To me yasa har yanzu ba a koresa ba daga makarantar?" Dariya sosai Jay yayi yana kallonta yace "Baya karatu doesn't mean he is dull Halysaah, kinsan Genius? That is who Ajay is, he is naturally gifted, he graduated as one of the best medical student during our degree program in this state and masters, kuma kar kice wani karatu yake, mu ne dai sai mun yi karatun za mu wuce" Yana murmushi ya kare maganar, Khaleesat ta wani kyabe baki kamar bazata ce komai ba, sai kuma tace "To ai gwara kai karatun kayi ka wuce, shi kuma banza kawai yake ci" Jay na dariya yace "Ai shi sa na bar masa gidan cause idan na ci gaba da biyesa da abokansa wucewa zai yi ya bar ni, su kansa abokan nasa ina tausaya masu biyesa da suke" Khaleesat tace "Shi ne yasa kake Co-living?" Yace "Yeah, shekaranmu na karshe kenan idan Allah ya yarda so i need much privacy to study very hard to earn my PhD, in kana tare da Ajay ba wani abun arziki da zaka yi in dai bangaren karatu ne, sannan baya barina inyi bacci sosai, nuisance ne shi fa, Ya Subhanallah" Khaleesat tayi shiru tana kallonsa, sai kuma ta sauke idonta, yace "Year nawa kike yanzu?" A hankali tace "Year 3" yace "Kince Pharmacy ko?" Ta gyada masa kai, yace "Kin kusa gamawa kema ai in sha Allah" ita dai tayi shiru bata ce komai ba suna ci gaba da tafiya slowly, ita ce tayi breaking silence din after almost 10 mins da ya biyo baya tace "You know him back home?" Jay ya kalleta yace "Wai Ajay? Yeah he is my favorite, yanzu ma dai kin ga budurwa nake nema masa bashi da mashinshiniya ko daya wallahi" Khaleesat tace "Ashe bazai taba samu ba, ai he is way too rude and full of himself, wacece zata yarda ta auresa in dai ba auren dole aka mata da shi ba, ko makala mata shi aka yi?" Jay dai dariya kawai yake yana kallonta yace "Ya kai Saurayin ki?" Nan da nan mood dinta ya canza, taki ce masa komai tana ci gaba da tafiyarta, yana kallonta yace "Naga kin yi shiru ko compare and contrasting kike yi a zuciyarki? Tell me pls ya kai saurayinki?" Without looking at him tace "Kamar lokacin sallah yayi, and it's getting dark already" Yace "Ke ina ruwanki da sallah tunda ba yi kike ba?" Khaleesat was dumbfounded jin abinda yace, ta kasa kallonsa kuma taki basa amsa still walking slowly, Roadside chair ta hango ta tafi ta zauna, ya karasa wajen yace "Ko har kin gaji ne?" Tace "To da bazan gaji ba, muna ta tafiya for almost an hour now" Yace "Akwai wani Eatry a area din nan, mu je sai mu yi dinner before going back home, the eatry isn't far away from here" Khaleesat tayi shiru, ta san Eatry din da yake magana don sun taɓa zuwa da Abdul kuma abincin wajen shegen tsada ne da shi, yace "Let go" Yana fadin haka ya juya ya fara tafiya, hakan ya sa ta mike ta bi bayansa, ya jira har ta iso inda yake sannan suka ci gaba da tafiya a tare har suka isa Eatry din, suna shiga ta kalli Jay that was grinning kamar yaga wanda ya sani a cikin Eatry din, lkci daya ta hango Ajay that was sitted da wata baturiya a cikin eatry din yana mata magana, ga abinci kala kala a gabanta, shi kuma ruwan gora ne kawai a gabansa, Khaleesat ta dauke idonta speaking calmly tace "I think zan tafi gida kawai, dama ba wani yunwa nake ji ba, i will order a Lyft in koma gida" Jay ya riko gyalenta don har ta juya zata fita yace "C'mon Halysaah, so kike ya kara raina ki, kina fita zai yi zaton tsoronsa ne yasa kika kasa shigowa kika fita and he will be very happy, kawai kiyi fuska ki tafi ki zauna" Khaleesat ta tsaya bayan ta ɗan yi nazarin abinda Jay yace, kuma fa haka ne zai yi zaton tsoronsa take, hakan yasa ta karasa Jay na biye da ita a baya ya jawo mata kujeran dake facing inda su Ajay ke zaune ta zauna, Jay ma ya zauna sannan ya kalli direction din Ajay dake kallonsu babu yabo babu fallasa, Jay ya daga masa hannu with smile all over his face alamar Hi, Ajay ya dauke kai kamar bai taɓa saninsa ba a rayuwa, Jay ya daga kafadarsa yana murmushi sannan ya dau menu dake saman table ya mika ma Khaleesat yace "Duba abinda zaki ci" Ta amshi Menu din tana kallo, cikin few minutes Jay ya saka masu order aka kawo masu abincin, duk da Khaleesat tana facing din Ajay ko da wasa bata yarda ta kallesa ba, tayi kamar bata san da shi a Eatry din ba, Jay kuwa cin abincinsa kawai yake with full concentration not minding her in his front, lkci lkci Khaleesat ke kallonsa, ta lura he doesn't joke with food and sleep for anything, dariya ma ita yake bata, ita kam a hankali take cin abincin gabanta, ya daga kai ganin bata wani ci Crab patatoe Chips din gabanta ba yace "Should i fetch some of urs?" Ta wani kallesa tace "Do you have an extra stomach?" Bai san sanda yayi dariya ba yace "I don't understand an extra stomach?" Tana kallonsa calmly tace "Naga duk kai ka kusa cinye abincin kan table din nan" Jay ya bude ido sosai yace "Har da sharri? Me da me na ci a table din?" Ta tallabi chin dinta tana murmushi tana kallonsa wanda har sai da dimples dinta ya lotsa, Mistakenly ta daga ido suka hada ido da Ajay dake kallonsu babu yabo babu fallasa, nan da nan murmushin dake fuskarta ya bace ta sha kunu, Jay bai ma san tana yi ba don tuni ya ci gaba da cin abincinsa har ma ya diba na gabanta, Khaleesat ta kalli wayarta dake vibrate kan table, sosai gabanta ya fadi ganin Abdul ne ke kiranta, Jay ya daga kai ya kalleta yace "Ba kiran ki ake ba?" A hankali tace "Na sani" Yace "Why are you not picking?" Tayi shiru, sai a sannan ta tuna fa ashe ya kirata severally bata daga kiransa ba, Jay yace "Ko de saurayinki ne?" Ta daga manyan idanuwanta ta kallesa, yace "Ki daga mana kar kiyi laifi" Sauke idonta tayi ta daga kiran a hankali ta kai kunne tare da sallama cikin sanyin murya..... 07087865788✍🏻 [20/05, 11:47 pm] +234 813 644 0264: Read My Book "HALYSAAH" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6 ✨✨ HALYSAAH✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 17.... Daga daya bangaren Abdul yace "What is wrong with you these days Khaleesat? Me yake damun ki?" Tunanin abinda zata ce masa ta fara yi, tayi shiru gabanta na faduwa, ita ta ma rasa me yasa take ƙin daga kiransa kwanan nan, kawai a zuciyarta take jin bata son waya da shi, Jay ya daga kai ya kalleta jin tayi shiru ga waya ƙare a kunnenta, amsar wayar yayi ta zaro ido tana kallonsa da mamaki with fear, ya sa wayar handsfree ya rage volume sannan ya ajiye saman table ya ci gaba da cin abincinsa, a fusace Abdul yace "Wai baki ji na ne, or is something wrong with you?" A hankali Khaleesat tace "Ina jin ka mana, na mance wayar ne a gidansu Safiyyah, i just got it now" Sounding so provoked yace "Ni zaki raina ma hankali? Ke ce zaki bar wayarki tun jiya gidansu Safiyyah?" Khaleesat ta wani kyabe baki ta kauda kai tace "Haka dai kawai bazan ki daga kiranka ba, me yasa baza ka min uxuri ba?" Abdul yace "Wait Khaleesat, where are you getting ur liver from these days? Who is ur vendor? Yaushe kika fara samun courage din mayar min da magana?" Khaleesat tace "Toh ni yanzu me nayi? Nace maka wayar baya wajena and u are trying to create an issue out of nothing, Nan da few weeks fa za mu fara jarabawa, you are only adding more pressure to the one i am already in, ka dinga considering dina mana pls" Jay ya ɗan daga kai ya kalleta, sai kuma yayi murmushi ya dau ruwan gora ya bude yana sha, Abdul yace "A kanki aka fara jarabawa? What is the big deal ah jarabawan da zaki yi? Ko dai Safiyyah ce ke dora ki akan abinda bazai fisshe ki ba? Safiyyah ce take zuga ki har kika fara samun courage din mayar min da magana ko? Switch to video call now" Khaleesat taji gabanta ya fadi sosai, Jay dai murmushi kawai yake, a hankali Khaleesat tace "Ohk i will, amma kayi hakuri let me dress up first..." A mugun fusace yace "Ki bar shi" Yana fadin haka ya katse wayar, Khaleesat dai tayi shiru tana kallon wayar nata, Jay yace "Ki gama cin abinda zaki ci mu tafi Halysaah, it's pass magrib now zan je inyi sallah" Khaleesat ta daga idanuwanta tana kallonsa, yace "Ko ayi maki takeaway din abincin?" Ta sauke idonta bayan sun hada ido da Ajay da ya mike daga inda yake zaune, Jay ya juya ya ɗan kalli Ajay yace "Hey man, ka hada har nawa bills din" Ajay yaki kallon direction dinsa kai kace bai san sa ba ma, Jay ya kira daya daga ma'aikatan wajen ta karaso, ya sa tayi masu packaging abincin da Khaleesat bata ci ba, ita dai Khaleesat har sannan taki cewa komai kana ganinta kasan she is a bit disturb, Jay ya bi Ajay da kallo har ya fita daga Eatry din da baturiyar da suke tare, shi bai ma taɓa ganinta ba sai ranan duk kwashe kwashen Ajay ne, bayan ma'aikaciyar wajen ta gama packaging abincin, yana kallonta ya tambayeta bill dinsa, nan ta sanar masa Ajay ya hada har nasu ya biya, Khaleesat ta daga kai ta kalli waitress din jin abinda tace, Jay yace "Ok then" Mikewa yayi ya dau ledan abincin Halysaah yana kallonta, ta tashi ta dau wayarta, yana gaba tana biye da shi suka fita daga wajen cin abincin, Lyft din da Jay yayi masu order har ya iso, ya bude mata back seat yana jiran ta shiga, Khaleesat felt somehow hakan da yayi, don duk fitar da suke yi da Abdul bai taɓa mata haka ba, yawanci ma shi yake fara shiga sannan ta shiga, bayan ta shiga motar Housemate dinta ma ya shiga, sai da suka kusa gida wayarta ya fara vibrate, ta kasa duba me kiranta sanin kila bazai wuce Abdul ba, Jay dake danna wayarsa ya kalleta yace "Kiran ki ake ai" Bata ce masa komai ba ta kalli screen din wayar sai taga Safiyyah ce ke kiranta, ta daga da sauri ta kai kunne tace "Hello Sophie" Safiyyah tace "Am at the door, nayi knocking shiru" Khaleesat ta ɗan saci kallon Jay, sai kuma a hankali tace "Ohk na ɗan fita ne amma ina hanya yanzu" Da mamaki Safiyyah tace "Kin fita? Ban gane kin fita ba, Ina kika je?" Khaleesat tayi shiru, Safiyyah tace "Ko da Housemate din ki?" Khaleesat tace "Um" Safiyyah tace "Hmmm i see, to in dai baku kusa dawowa ba bari inyi tafiyata kawai" Da sauri Khaleesat tace "Aa ki jirani am on my way" Tana fadin haka ta katse wayar, ajiyar zuciya ta sauke don tayi tunanin Abdul ne ya kira Safiyyah shine ta kirata, after some minutes suka isa gida, ta bude side dinta ta sauka daga Uber din, Jay ma ya sauka, Apartment dinsu ta nufa, ta ɗan rage pace dinta ganin kamar motar Mustapha a vicinity din, shi dai Housemate dinta na biye da ita a baya, sai ga Safiyyah ta fito daga motar Mustapha, da murmushi fuskarta ta nufesu ta gaida Jay, ya tsaya ya amsa mata sannan ya wuce cikin gida, Safiyyah ta kalli Khaleesat tace "Toh ki gaida ya Mustapha, dama girki na tsaya maki na zata har yanzu bakya iya tashi" Khaleesat ta kirkiro murmushi tace "Ohk bari in gaishesa" Zagawa tayi zuwa side din Mustapha taga yanda ya bi Jay da kallo har Jay ya shiga cikin gida, gaishesa tayi kanta a kasa, ya kalleta yace "Who is he Khaleesat?" A hankali Khaleesat tace "Housemate dina ne" Mustapha ya kalli Safiyyah yace "There was a time da kika ce min mace ce Housemate dinta?" Safiyyah tace "Eh wallahi the lady packed out shine shi ya shigo, ai bai wani dade sosai da dawowa apartment din ba" Mustapha ya kalli Khaleesat yace "Me yasa zaki dinga zama gida daya da namiji da sunan Co-living Khaleesat, why not come stay together with ur frnd Safiyyah in my house?" Safiyyah ta wani kallesa, sai kuma ta kyabe baki, sai kace ya gama kwatar mata 'yan ci gun shegiyar matarsa balle ya kwatar ma ita da kawarta, ita dai Khaleesat tayi shiru bata ce komai ba tana wasa da veil dinta, Mustapha yace "Wani yare ne Housemate din naki?" Caraf Safiyyah tayi tace "He is from Tanzania, yaren can kasar yake yi, beside shi baya ma wani zama a gidan once a while yake zuwa yayi karatu kawai" Mustapha ya wani kalleta yace "Ke na tambaya?" Gefe ta koma bata sake cewa komai ba, Mustapha yace "Daga ina ku ke da daddaren nan Khaleesat?" Khaleesat tace "I was sick tun da safe shine muka je ya siya min abinci yanzu" Mustapha dai sai kallonta yake, after some seconds yace "I will talk to my wife, sai ki dawo nan gidana kiyi zamanki tare da Safiyyah har ku gama Exams, i think the exam is by the corner...." Khaleesat tayi murmushi kawai bata basa amsa ba, Safiyyah tace "Mu je in kai maki abincin da na kawo maki ciki" Bude bayan motar tayi ta ciro abincin, Khaleesat tayi ma Mustapha sai da safe sannan suka wuce apartment dinta tare da Safiyyah, nan parlor Safiyyah ta ajiye abincin tayi kasa da murya tana washe baki tace "Ban gane wannan fitar da ku ke yi da Housemate dinki ba Khaleesat? Ina ku ka je?" Khaleesat tace "Abinci fa muka je ya siya min, kuma ba wai lapiyata lau muka je ya siya min abincin ba" Khaleesat ta ajiye ledan abincin hannunta ta zauna gefen kujera tare da sauke boyayyen ajiyar zuciya, Safiyyah dake washe baki tana ma Khaleesat wani kallo tace "To ya aka yi yasan baki da lafiya, kuma how did he know what was wrong with you?" Khaleesat tace "Kinga Sophie wnn ba shine damuwata ba yanzu, muna gidan cin abinci Abdul ya kirani" Safiyyah ta wani yatsine fuska tace "So? Da ya kiraki sai aka yi yaya?" Cike da damuwa Khaleesat ta bata labarin yanda aka yi da kuma call dinsa da ta ki picking tun jiya, Safiyyah tace "Haba, to ko ke fa da kika fara kokarin kwatar ma kanki 'yan ci, ni sai nake ga kamar Housemate din nan naki ne ke baki Liver kike wasu abubuwa yanzu, banda haka yaushe har kika yi bakin gaya ma Abdul magana haka" Tana dariya ta kare maganar, Khaleesat ta dinga hararanta ganin ta ma maida abun joke, Safiyyah tace "In ni ce ke ma bazan kirasa ba wallahi, gwara kawai komai ya ruguje kowa ya huta" Khaleesat tace "Kin manta abinda yayi kwanaki kawai muka gansa kamar an jefosa Sophie? Kinsan yanzun ma ba karamin aikinsa bane sai ya iya kamo hanya ya zo" Khaleesat ta dafe kanta tsabar she is confuse, Safiyyah tayi shiru, can kuma ta kyabe baki tace "Kuma haka ne ba kai ne da shi ba sai ya iya kamo hanya tunda ba su dau kudi bakin komai ba, kawai anjima ki kirasa sai ki kisa abinda zaki ce masa da zai gamsar da shi, kuma kina iya cewa baki da lafiya gantalallen ya kamo hanya, ni dama ya tafka wani tsiya America su kwace visan sa kowa ya huta" Duk da damuwar da Khaleesat ke ciki sai da tayi dariya, Safiyyah tace "Allah kuwa, ban ki ba ya zo ya maki hauka da kaina zan kira masa 911 wallahi" Khaleesat dai tayi murmushin karfin hali kawai, wayar Safiyyah ne ya fara ring ta duba taga Mustapha ke kiranta, turo baki tayi tace wannan mutumi yana takura rayuwata a kasar nan, wai daga cewa zan kawo maki abinci ya zata yawo zani shine fa ya biyoni, kema baki ji ba wai ki dawo gidansa da zama, salon wataran matar ta saka mana guba a abinci mu ci mu mutu gaba daya, yanzu haka fa ko ga maciji bama yi da ita, ɗan fitar nan da yayi da ni muna nan dake sai ya zamar masa matsala, tana can ta cika tayi fam tana jiransa, ko a jikina kuwa, sai na ma lallabasa ya kai ni ya siya min ice-cream ta yanda zata ga na dawo rike da leda" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya bata ce komai ba, Safiyyah ta mike tace "Bari in je, sai mun hadu Monday in sha Allah" Khaleesat ta rakata bakin kofa a hankali tace "Thank you Safiyyah" Safiyyah tace "No thanks kawata, ki ce ma Housemate dinki na tafi" Khaleesat ta gyada mata kai, a haka Safiyyah ta fita daga gidan, Khaleesat ta kullo kofar a hankali, abincin da Safiyyah ta kawo mata ta dauka ta kai fridge da wanda Housemate dinta ya sa ayi mata takeaway. Khaleesat ta fito wanka kenan taji Housemate dinta na knocking kofarta, ta dau Hijab dinta ta saka sannan ta nufi kofar ta bude tana kallonsa, yana rike da laptop dinsa yace "Good night Halysaah, i am sleepy" Khaleesat tace "To sai da safe, thank you for the dinner" Yace "No thanks.... kin kira BF din naki?" Khaleesat taki basa amsa, yace "Amma bari in tambayeki, a ina kika hadu da gayen nan ne? Don't know ko na taɓa tambayarki kwanaki...." Khaleesat ta jingina da kofa without looking at him tace "Back home" Yana gyada kai yace "I see, ni at first na zata you are not Nigerian, was thinking you are from Niger or Chad, probably Shuwa Arab" Khaleesat ta dinga kallonsa, bata san sanda tace "Why?" Yace "Na ganki kamar Buzuwa" Khaleesat ta sauke idonta bata basa amsa ba, yace "Ok, i will be on my way, good night" Daga haka ya juya ya bar wajen, a hankali ta sauke idonta sannan ta kulle dakinta ta jingina jikin kofar, she stood there for almost 5 mins kafin ta karasa cikin dakin ta cire hijab din jikinta ta ciro sleeping dress dinta ta saka, sanitary pad dinta dake gaban dressing mirror ta dinga kallo, sai kuma ta dauke daga wajen, sai da ta kwanta sannan tayi dialing number Abdul gabanta na faduwa, har ya katse bai daga ba dama tasan ba lallai ya daga ba, ta sake kiransa nan ma bai daga ba, ta bude WhatsApp tayi masa magana ta nan, reply yayi mata yace "I don't have ur time so do not border me" tabe baki tayi ta ajiye wayar ta kashe wutan dakin sannan tayi kwanciyar ta lumshe ido, nan da nan bacci ya dauketa. Washegari bayan Khaleesat ta gama azkar din da take yi, ta jawo wayarta a hankali, tunda ta tashi jikinta yake a sanyaye don mafarki tayi Abdul ya zo kamar yanda ya zo wancan lkcn still kuma ya sake haduwa da Housemate dinta a gidan, ba karamin daga mata hankali mafarkin nan yayi ba, WhatsApp dinta ta bude bayan tayi deciding zata masa message din ban hakuri duk da bata saka ran reply dinsa ba, cause it won't be funny if her dream comes true, tana shiga WhatsApp din ta ga ya turo mata hotuna kusan biyar tun 3 hours ago, bude message din tayi zuciyarta na bugawa don bata san hotunan menene ba, nan taga har da message yayi mata kafin yayi sending hotunan, ta fara downloading hotunan at the same tana duba message din da ya rubuto mata kamar haka "So now, kina kokarin nuna min cewa i made the mistake of letting you go to America to study right? Kin mance wacece ke ko? kin mance daga inda kika fito, then that is so foolish and stupid of you Khaleesat, amma ina me tabbatar maki idan har kika ci gaba da daukata for granted kamar yanda kike yi kwanan nan sai na sa kinyi da kin sani wallahi" Lkci daya Hawaye ya cika idon Khaleesat, ta sauke idanuwanta kan hotunan da ya turo mata, daya hoto ne da shi yayi mata a bakin kofar dakin Ummanta, yana zaune kan tabarma ta duka gabansa zata ajiye masa ruwa a Cup shine ya dauketa hoton, shekaru hudu da suka wuce kenan, she look so so young and meek a hoton, hoto na biyu kuma tana wajen debo ruwa a nan unguwansu ya zo ranan ya ganta a wajen, ita bata ma san yayi mata hoton ba ga zaninta duk a jike, hoto na uku kuma tana baƙin murhu a tsakar gidansu tana juye alalan siyarwan Ummanta a Cooler shi kuma ya zo gidan ranan, duk bata san ya mata hotunan nan ba sai yau da ya turo mata ta gani, hoto na hudu kuma ranan da ya kai ta zata zana Jamb ne, jamb din da bata ma yi amfani da shi ba daga karshe, sai kuma hoton karshe na ranan da zai kawota USA for the first time, looking at all the pictures da kuma looking at her now zaka ga banbanci me tazara sosai, infact the difference is very obvious don a yanzu she looks more beautiful, matured, nourished and well taken care of, yanzu skin dinta har wani glowing yake, in ma ba ka santa ba bazaka taba cewa ita ce a hotunan ba, bata san sanda ta fashe da kuka ba ta hade kanta da pillow tana kuka sosai, but like seriously Abdul bai yi deserving haka daga gareta ba, but did she also deserve irin abubuwan da yake mata? Kuma tun asali haka yake mata, Kuka sosai tayi babu me rarrashinta, bata ma san me take ji a zuciyarta ba a lkcn, she cried profusely for almost 30 mins, daga karshe tayi karfin halin mikewa zaune ta dau wayarta, she don't even know where to start from, Voice note ta fara masa muryarta na rawa trying to tell him she is sorry, amma bata kai ko ina a basa hakurin ba ta fashe da kuka sosai, cikin kuka ta ci gaba da basa hakurin, sai da tayi masa Voice note uku sannan ta ajiye wayar still crying.... 07087865788✍🏻 [21/05, 1:08 am] +234 813 644 0264: Read My Book "HALYSAAH" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6 ✨✨ HALYSAAH✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 18..... Wajen karfe goma na safe Khaleesat na kwance dakinta idonta rufe duk da ba bacci take ba, ji tayi ana kwankwasa kofa, kamar bazata iya tashi ba daga karshe dai ta mike ta sauka daga kan gadon ta dau hijab dinta ta saka, tana tafiya a hankali ta fito parlor, ta tagar parlon ta duba ta ga Housemate dinta ne, ta karasa ta bude kofar, Yace "Sorry na tashe ki kina bacci, i forgot the key at home" Ita dai bata yarda sun hada ido ba a hankali tace "Ina kwana?" Yace "Lafiya lau, how are you feeling now?" Ta juya going back to the parlor tace "Alhamdulillah" Ya bi ta da kallo sannan ya shiga parlorn, dakinta ya ga zata koma yace "Halysaah" Ta tsaya, after few seconds ta juyo but couldn't let her eyes contact his, shi dai kallonta kawai yake, ya karasa inda take tsaye yace "What happened?" Girgiza masa kai kawai tayi, lkci daya hawaye ya fara sauka idonta, ya dauke kai na 'yan dakiku kafin ya sake juyowa ya nuna mata kujera yace "Sit" Komawa tayi ta zauna, ya zauna shima yana kallonta yace "Tell me what's wrong" Ta sunkuyar da kanta, yace "Are you sick?" Ta girgiza masa kai, yace "Wannan saurayin naki ko?" Ta kasa basa amsa wasu hawayen na sauka idonta, sai kuma ta fashe masa da kuka, mikewa yayi yace "Waye ya hadaki da wannan mutumi ne? Why did u allow him know ur weak point? Why are you always crying because of him? Is he happy making u sad now and then?" Khaleesat dai kuka take a hankali, yayi shiru for almost 2 mins yana jin ransa na baci, can ya kalleta yace "Kee in zaki yi facing study dinki is better you do so, give that ur so called boyfriend space, ur exam is around the corner" Sai a sannan Khaleesat ta daga idanuwanta da suka yi ja ta kallesa, sae kuma ya kwantar da murya yace "Kiyi hakuri Housemate, zan dinga sa ki a addu'ata Allah ya maki mafita, i can't just intrude cause ban san sanda ku ka san juna da shi ba, ban kuma san me ya hada ku ba, i will only include you to my prayers i promise Halysaah" Khaleesat ta gyada masa kai da kyar, sannan ta mike cikin sanyin murya tace "Nagode" Daga haka ta juya ta nufi dakinta, Jay ya koma ya zauna yana mamakin irin son da take ma gayen da har ta kasa rabuwa da shi duk da musguna mata da yake yi a soyayya, bata da aiki sae yi masa kuka, da kanwarsa ce daga ita har saurayin zai hada ya ci ubansu, kuma ya rabata da shi na har abada, tausayinta yaji har cikin ransa don bai san wani irin so bane wannan take masa da har take iya tolerating abubuwan da yake mata, and ya lura the guy is taking advantage of this to hurt her always, mikewa yayi ya tafi kitchen kamar yanda ya zarga yaga alamar bata yi breakfast ba har sannan don kitchen din ma bata shigo ba, fridge ya bude ganin abincin da Safiyyah ta kawo mata jiya yayi mata microwaving dinsa ya hada mata shayi sannan ya kai mata daki, sai da yayi knocking ta amsa sannan ya shiga dakin, tun da ya shigo Khaleesat ke kallonsa har ya ajiye mata abincin, ta sauke idonta a hankali tace "Nagode" kai kawai ya gyada mata, sai kuma ta bi sa da kallo har ya fita daga dakin, karfe sha biyu saura Khaleesat ta jawo wayarta jin yana vibrate, tana duba screen din taga Abdul ke kiranta, ta sauke idonta kasa tayi picking call din ta kai kunne amma bata ce komai ba, yace "Khaleesah...." ta kasa amsawa hawaye ya fara sauka idonta, yace "Can you hear me?" Da kyar tace "Um" Yace "How was you night" tana share hawayen dake sauka idonta tace "Alhamdulillah" Tun daga wannan rana Khaleesat ta fara avoiding duk wani abu da zai hadasu fada da Abdul, she want just nothing but peace with him for her sanity, bin sa kawai take a yanda yake so for peace to keep reigning, in ma bala'i yake mata a waya zata yi shiru ta gama saurarensa sannan daga karshe ta basa hakuri kamar yanda take yi masa da, ranan da bai kirata ba kuwa ita zata kirasa, hakan kuma da tayi ya sa ta samu kwanciyar hankali har take concentrating a karatun ta, amma fa in ta tuna irin kulawar da Housemate dinta ke bata always wanting to make sure she is fine sai taji she isn't lucky having Abdul, ana haka har exams dinsu ya rage some days, ranan Wednesday tana kitchen da safe taji ana kwankwasa kofa, ta fito daga kitchen din don dama she is expecting Safiyyah, ta bude mata kofa, Safiyyah ta shigo tace "Ai na zata zan zo in tarar baki tashi ba?" Khaleesat tayi kasa da murya tace "Aa i am in the kitchen" Safiyyah tace "Ohk, why are you lowering ur voice?" Still Whispering Khaleesat tace "My Housemate is sleeping" Safiyyah ta sake baki tana kallonta, sai kuma ta rike haɓa tace "Ikon Allah gadinsa kike kenan?" Khaleesat ta hade rai tace "Ban gane gadinsa ba, daxu fa ya zo, and dama bacci yake zuwa yayi da safe don yace min baya bacci da daddare" Safiyyah couldn't stop smiling tana kallon Khaleesat, Khaleesat ta wani harareta ta juya ta koma kitchen, Safiyyah ta karasa ta zauna kan kujera har sannan bata daina murmushi ba, sai ga Khaleesat ta fito daga kitchen, still tana magana kasa kasa tace "Ko dai kawai mu je waje ki min gyaran gashin, kinga Hand dryer yana ƙara in ana using dinsa, it's noisy" Safiyyah ta buda baki tace "Ikon Allah, to akwai socket ne a wajen?" Khaleesat tace "Zan sa Extension a kitchen sai mu fito da shi ta window ai zai yi, kuma akwai tap a garden din sai mu wanke gashin ma a nan" Safiyyah dai murmushi kawai take bata ce mata komai ba, yanda Khaleesat tace haka din tayi duk don kar karan Hand dryer ya tada Housemate dinta or any of their noise kamar yanda tace, abinda bata sani ba ashe ba bacci yake ba aiki yake yi a Laptop dinsa a daki, bayan sun isa karamin Garden din dake bayan kitchen Khaleesat ta ajiye duk shampoo da Conditioner din hannunta sannan ta bude gashinta, Safiyyah na kallon gashin tace "Tab, Allah sa Shampoo din da Conditioner su isa dai" Khaleesat ta wani hade rai tace "Ban gane ba, saboda bargo za ki wanke?" Safiyyah tayi dariya tace "To meye banbancin wannan da bargon Khaleesat? Babancinsa kawai wannan akan ki yake, ni naga ma kamar karuwa gashin yake Tabarakallah Maa sha Allah" Khaleesat tace "Ba abinda ya karu yana nan yanda yake" A haka Safiyyah ta fara wanke mata gashin, suka dau time sosai bayan ta gama wankewa ta fara busar mata shi da Dryer, Jay ya shigo kitchen zai yi making Coffee drink ya dinga kallonsu ta window din kitchen, he was confuse seeing her hair, is all that Hair or what? long, full and black, kawai yaji bai yarda gashinta bane, ya juya ya fara yin abinda ya kawo sa kitchen din, Khaleesat ta kasa kunne sosai jin kamar sound a kitchen, ai ko ta jawo mayafinta da sauri ta rufe kanta bayan ta hangosa a kitchen din ya juya masu baya, Safiyyah dai sai kallonta take, Khaleesat ta mike ta isa kusa da window din kitchen din tana kallonsa tace "You woke up early today" Ya juya ya kalleta yace "This is to 12" Khaleesat ta zaro ido don bata san lkci ya wuce haka ba, ashe sun bata lkci sosai wajen wanke gashinta, yace "Me kike yi a nan?" Tace "I am together with my frnd Safiyyah" Ya ci gaba da abinda yake yi yace "Ohk my regards" Juyawa tayi ta koma gun Safiyyah, bayan Drying har Stretching gashin sai da Safiyyah tayi mata, Safiyyah tace "You know what Khaleesat, anjima ki zo can gida sai in maki Kalaba din, i think i can feel my period, i need to go home" Khaleesat ta juya ta kalleta tace "Da gaske?" Safiyyah tace "Wallahi, gwara in tafi gida kar ya zo" Khaleesat tace "Ohk, amma ki bari in dafa mana indomie ki ci tukun ki tafi" Safiyyah tace "Ke bazan ci ba, bari in tafi kawai i am uncomfortable" A hankali Khaleesat tace "To shikenan" Safiyyah tace "Sannan pls Khaleesat nace ma Ya Musty ran sunday zaki zo gidan tunda kinga Monday za mu fara exams, ko 2 days ne sai kiyi kafin matarsa ta fito da baƙin halinta gaba daya, kin dai ga bazai ce bamu ji maganarsa ba yace ki dawo gidansa baki dawo ba, even if it's just 2 days come and spend in his house pls" Khaleesat tace "Wallahi ba wai bana son zuwa bane ko kuma ban ji maganarsa ba Safiyyah, bana son issue ne da matarsa, i don't want any problem" Safiyyah tace "I know, shi yasa nace ko kwana biyu ne kawai ki zo kiyi ai bazai ce baki zo ba, ranan Sunday sai ki debi kayanki kala uku ki taho kawai, probably ma daga karshe nima nan gidan zan dawo mu yi karatu tare, ni nasan ba lallai ma kiyi kwana biyun ba matarsa bata kirkiro wata matsala ba, so just chill ba zama zaki yi a gidan ba Likewise myself" Khaleesat tayi shiru kamar me nazari, sau biyu Mustaphan ke mata magana da kansa ta WhatsApp akan dawowar da yace tayi gidansa, iyaka sai tace masa in sha Allah tana nan zuwa before exam, Safiyyah ma tayi mata magana yafi a kirga, ko don Safiyyah zata daure kawai taje tayi kwana biyun a gidan, let it not be as if bata jin magana, a haka ta raka Safiyyah bayan tayi order din Uber da zai maida ta gida, Khaleesat na dawowa parlor taga Housemate dinta ya shirya zai fita, yana kallonta yace "Wai duk gashinki ne wannan ko dai ƙarin gashi kike yi Halysaah?" Ta daga idanuwanta ta kallesa bayan tayi realizing ashe ya ganta kenan daxu, sauke idonta tayi tace "Ƙarin gashi kuma?" Yace "Naki ne? Ai na gansa kamar ba naki bane, sorry" Ɗan murmushi kawai tayi without giving him an answer, can yace "Wait, amma ba ki jin zafi na damun ki? I mean baya takura ki gashin? isn't it too much?" Tace "How?" Sounding so serious yace "Ki rage mana, just cut half of it off kema ki huta, sai kiyi azumi uku, wannan ai burden ne Halysaah, it's too much, ji fa sai da kawarki ta zo taya ki wankewa don kema baza ki iya wankesa da kanki ba, all this while ni na zata irin wannan acuci mazan da ku ke yi ne kike daurawa a kanki, i never knew gashin ki ne" Khaleesat tayi murmushi ba tare da tasan tayi hakan ba, can ta kallesa calmly tace "But i am not complaining, kuma ai ba nauyi gashin yake min a kai ba" Ya wara ido yace "Ohh! my bad, haka ne kuma fa, hope you are reading so well for ur exam, kinga in few days time zaku fara, i think monday ko?" Ta gyada masa kai, yace "Wishing you the very best of luck Halysaah" a hankali tace "Thank you" Yace "See ya later" Ta gyada masa kai, daga haka ya juya ya nufi kofa ya fita daga parlon.... Da yamma Khaleesat ta gama shiryawa bayan Safiyyah ta isheta da kira wai taje ta mata kitson, Khaleesat ta dau handbag dinta da mukullin gida bayan Uber din da tayi order ya iso sannan ta fita daga gidan ta kulle, tana hanya kiran Safiyyah ya shigo wayarta, ta daga tace "Ina hanya fa" Safiyyah tace "Allah in baki zo ba sai dai gashinki yayi ta zama haka bani da lokacin maki wani kalaba kuma idan aka fara jarabawa" Khaleesat dai tayi murmushi, tasan kawai Safiyyah so take ta je gidan, karfe hudu da yan mintuna ta isa gidan ta sauka Uber sannan tana tafiya a hankali ta nufi apartment din, tsayawa tayi bakin kofa ta danna bell, lkci daya aka bude kofar, sai da gaban Khaleesat ya fadi ganin Surayya ce ta bude mata kofa, ta sauke idonta tace "Ina yini?" A takaice Surayya tace "Wa kike nema?" Khaleesat ta daga kai ta kalleta tace "Wajen Safiyyah na zo" Bluntly Surayya tace "To bata nan, sai ki juya ki koma inda kika fito" Khaleesat was just looking at her babu ko kiftawa, sai ga Safiyyah ta fito daga daki fuuu, tana huci tace "Wajenta kika zo da zaki tsaya sauraronta baki bangajeta ba kinyi shigowarki?" Khaleesat ta bude baki tana kallon Safiyyah, wato ta bangaje matar gida ta shigo tsabar neman jifa'i, Surayya ta juya a fusace tana kallon Safiyyah tace "Tunda gidan na ubanta ne ko naki uban sai ta shigo mu ga" Safiyyah tayi cilli da wayar hannunta ta fige dankwalin kanta tace "Wallahi kar ki ga na raga maki daxu saboda yaya, to yanzu baya nan cin kaza kazanki zanyi la'ada waje" Khaleesat was shock, ta kasa rufe baki tana kallonsu, Surayya ta nufi Safiyyah tana kunduma mata zagi kamar dai yanda tayi mata few hours ago a gaban cousin brother dinta, instead sai cousin din ya dinga ba Safiyyah hakuri without taking any action, dama Safiyyah a wuya take, sbda bakin ciki ne ma yasa ta dinga kiran Khaleesat ta zo gidan, Khaleesat ta zaro ido ganin yanda Safiyyah ta finciko Surayya cikin zafin nama, ba ayi wata wata ba suka fara tikar dambe a wajen, Khaleesat ta karasa ciki da sauri tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, meye haka kuke yi Safiyyah? Don Allah ku bari" Yaron Surayya dake kan kujera sai tsala ihu yake, Khaleesat tayi kokarin rabasu taga an cillar da ita gefe har sai da ta kusa faduwa, bata sake gigin zuwa kusa da su ba, ta bude wayarta da sauri ta fara neman number Mustapha, tana kokarin kiransa taga Surayya na harin fixgo wani flower vase zata buga ma Safiyyah a kai, hakan yasa Khaleesat ta tafi da sauri ta dauke Vase din daga inda yake, Safiyyah tayi using opportunity din ta fixge vase din a hannun Khaleesat ta maka ma Surayya a goshi, sai ga jini kuma hakan bai sa sun fasa damben da suke ba, ko da Khaleesat ta kira Mustapha ashe yana hanyar dawowa, cikin few minutes sai gashi ya shigo gidan, sai shi ne ya rabasu bayan sun yi ma juna laga laga, Surayya bata daddara ba tayi kukan kura tayo kan Khaleesat zata cafkota tana cewa "Kika bata Vase ta buga min, wallahi kema sai na ci kaza kazan ki" A nan ne Mustapha ya sauke mata mari ya fincikota yace "Ko kin fara hauka ne Surayya? Me kike son mayar da ni a kasar nan ne?" Ita dai Khaleesat ta tsorata sosai, Safiyyah na huci tace "Shegiya bayerabiyar banza kawai jaka jahila..." Bata rufe baki ba ita ma Mustapha ya kai hannu zai gaura mata mari ta kauce da sauri tana harare harare tana huci, Surayya dake kuka wiwi ta figi ɗan ta zuwa sama tana cewa "Wallahi sai dai ka zaba ko ni ko Safiyyah a gidan nan yau, in ko ba haka ba ni zan bar maku gidan kayi zaman auren da ita" Safiyyah ta sauke ajiyar zuciya ko ba komai dai ta fasa mata kai hankalinta ya kwanta ta kuma ji dadi, Mustapha ya zauna saman kujera ya dafe kai, juyawa Khaleesat tayi sum sum ta fita daga parlon wishing dama bata zo gidan ba kilan da haka bai faru ba, da tasan bala'in da za ayi kenan babu abinda zai fara fitowa da ita daga gida, Safiyyah ta figi dankwalinta zata bi ta, Mustapha ya mata tsawa yace "Kar ki kuskura ki fita daga gidan nan" Safiyyah ta fashe da kuka tana bubbuga kafa tace "Ni wallahi yaya na gaji, na gaji kuma haka, na gajiiii, dubi cin mutuncin da matarka ta min daxu kace in kyaleta, yanzu kuma daga kawata ta zo wajena in mata kitso shikenan sai ta fara kunduma mana zagi ta kamani da dambe??" Yace "Wuce dakin ki nace" Ita dai Khaleesat tuni ta kara gaba ta bar gidan. That same day wajen karfe biyar da rabi sai ga Safiyyah ta zo gidan Khaleesat, Khaleesat ta zauna gefenta bayan sun shigo parlor tana kallonta tace "Ban ji dadin abinda ya faru ba yau Sophie, da na sani da ban je gidan ba ma wallahi" Safiyyah tace "Ai abun duniya ne ya dameni kamar in hadiye zuciya shi sa nayi ta kiranki ki zo daxu, wai fa bayan na gama yi maki gyaran gashi na koma gida matar nan kamar jirana take ta kama zagina ta uwa ta uba a gaban mijinta wai don me zan zubar mata da sauran miyarta dake kitchen, kuma fa kar kice da miya a tukunyar Khaleesat, wallahi ba komai ciki sai wani guntun miya da yayi tsami sai bugawa yake, ni kuma na wanke na dafa indomie na ci kafin in taho nan daxu in maki gyaran gashi, Ya Mustapha ya hanani cewa komai ya bani hakuri na wuce daki, a banza tunda dai shi ma har uwayensa ta zaga, shine bata daddara ba da kika zo zata sake hadamu ta zage ga yan iska sai muyi shiru muna kallonta, ni wallahi so nayi ace ma na cire mata hakora biyu ta dawo wawulo, amma dai a juri zuwa rafi wallahi sai na mata illar gaske kafin in gama karatu a kasar nan, dama tun 3 weeks ago da muka zo muka kawo maki abinci da ni da Y Mustapha ta kara kullatata ta kara tsanata tunda har yau tayi tunanin da akwai wani abu tsakaninki da Mustapha, ko ga maciji fa bama yi da ita a gidan" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya ta kamo hannunta tace "Ki dai dinga hakuri plss Sophie wataran sai labari, da ni ce ke ma wallahi bazan dinga biyeta ba a gidan nan" Safiyyah tace "To ai ba kowa ke da matattciyar zuciyar da kare ya lashe irin taki ba, amma wallahi tayi kadan in ki biye mata, tana ce min kule zan ce mata casss don ubanta, an gaya mata ita ta isa ta shiga tsakanina da Mustapha? Cousin dina ne fa, Uwarsa ce ta sha nono ta bar ma uwata, Babansa kuwa Cousin din babana ne halaq malaq, ina ga bai taɓa zaunar da ita ya mata bayanin nan dalla dalla bane, kuma ya ci sa'ar bana kai karar abinda matsiyaciyar matarsa ke yi min gida, don wallahi da tuni an dau mataki, amma dai bari mu yi hutu in koma Nigeria" Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya tace "Zancen gaskiya ke ma fa kina da naki Safiyyah, babu ta yanda za ayi kina zaune da mata ko ɗan wanke wanken nan da shara baza ki ke taya ta ba a gidan, Abinda fa idan an mana mun san baza mu ji dadi ba to kar mu yi ma wani, she is also human, kuma at times bacin rai ne ke triggering wani mugun halin mutum, kece kika yi triggering din halinta a gidan, babu ta yanda zaki ji dadi wataran kanwar mijinki ta zo gidanki ta zauna bata taya ki aikin komai sai dai in kinyi girki ta deba ta ci ta ajiye maki plate, ki duba wannan lamarin fa, mu mata muna da son kanmu wani lkcn..." Safiyyah ta dakatar da ita tace "Ohh wato goyon bayanta ma kike kenan Khaleesah? you are trying to say duk abinda take min yayi dai dai ko?? To nagode, dama ke baki taɓa goyon bayan mutum a duk halin da yake ciki, in dai mutum zai kawo maki damuwarsa to ya kara dulmiya kansa cikin damuwa ne, ni kuma ban taɓa kin supporting dinki ba no matter the situation, ko Abdul da nake zagi kullum kamar ɗa na nake goyon bayanki an gaya maki kema baki da naki baƙin halin ne wani lkci? Dama mistake nayi ma na zo gidan nan asirina a rufe da gidan Sandra na wuce da ba a kara bata min rai ba" Tana fadin haka ta mike ta figi jakarta ta nufi kofa kamar zata tashi sama, Khaleesat ta mike tace "Safiyyah" Banza da ita Safiyyah tayi har ta fice daga parlon ta kullo mata kofa, Khaleesat ta sauke ajiyar zuciya ta koma ta zauna, a hankali tace "Ae shikenan" 07087865788✍🏻 [21/05, 1:08 am] +234 813 644 0264: Read My Book "HALYSAAH" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=681294ff01c6bd900451c8e6 ✨✨ HALYSAAH✨✨ By _Khaleesat Haiydar_✍🏻 19.... Ranan friday wajen karfe sha daya na safe Khaleesat ta gama Laundry da take a kitchen ta fito, a reading nook din parlon ta tarar da Housemate dinta yana duba textbooks dinsa, cikin few seconds ya dau wanda zai dauka ya dawo cikin parlon yana kallonta yace "Har kin gama kenan" Kai kawai ta gyada masa ta fara tidying din parlon, rana na farko kenan da ta fara ganinsa yayi shiga irin ta Hausa cikin fararen kaya, Taji yace "Hope you are studying well Halysaah" kai kawai ta gyada masa, yace "Alright, till later" Ta ɗan kallesa tace "Are you Nigerian?" Ya buda ido yace "Why do u ask?" Tace "Kawai nayi zatan ko daga Chad kake, or Niger" Dariya yayi yace "Hope it's fine now tunda kin rama?" Hanyar dakinta ta nufa ba tare da ta basa amsa ba, ya dau makullin motarsa ya nufi kofar parlon, sai bayan da ya fita sannan ta dawo cikin parlon ta tafi gun window ta ɗan bude drapery din jiki tana leka garage, ganin har ya tafi ta ci gaba da aikin da take yi a parlor. Wajen karfe biyar na yamma Khaleesat na kitchen tana girki at the same time suna waya da Abdul, tun 40 mins ago ya kirata suke magana har sannan, duk kwanan nan dai lafiya suke waya da shi, ya kuma ɗan rage mata wasu abubuwan da yake mata, he is being a little caring these days, a rana sai su yi waya sau biyu wani lkcn har sau uku har hakan na bata mamaki kamar dai ba shi ba, yanzun ma shi ne yayi encouraging dinta ta tashi ta fara girkin da take yi don bata yi niyyar girki ba, for weeks now kullum Housemate dinta ke masu takeaway na dinner wani lkcn har lunch, this made her soo lazy to go to the kitchen, breakfast dama tea and cookies take ci yawanci ko kuma ta ci da bread idan Housemate dinta ya siyo, wani lkcn ta ci french fries da kwai ko ketchup, kwankwasa kofar parlor taji ana yi, ta ɗan zaro ido sanin bazai wuce Housemate dinta ba, kilan ya mance makullinsa ko kuma yayi misplacing dinsa as usual, ta kalli wayarta dake ajiye a kan kitchen cabinet har sannan Abdul was on the line kuma a handsfree ta sa wayar, tana ɗan kame kame tace masa "Can u excuse me pls, i will call u back in the next 2 minutes pls" Abdul yace "Why? Me zaki yi? Is the call hindering you from doing anything?" Da sauri tace "Noo" don bata son tayi laifi, sai kuma a hankali tace "Just want to round up the cooking ne, na kusa gamawa ai" Yace "But my call isn't preventing you from doing so, wayan ba a ajiye yake ba? Continue with ur work kawai" Knocking ta sake ji, ta ma san Housemate dinta ne cause haka yake knocking dinsa, ta kalli wayarta tace "Ohk then" Abdul ya ci gaba da maganar da yake mata, a hankali ta dau wayar ta fita daga kitchen din almost tiptoeing kamar tana tsoron yaji sound din tafiyarta, ta nufi kofar parlon ta bude at the same time tana kokarin yi ma Housemate dinta alamar da yayi shiru ta hanyar dora finger dinta daya a lips dinta, lkci daya taji komai nata ya tsaya cak, a hankali ta zame finger dinta daga lebbenta tana kallonsa bata ko kiftawa zuciyarta na bugawa, ta cire wayar dake kunnenta looking speechless and Surprise at the same time, Calmly yace "Ko in koma ne?" Ta zaro ido cikin in ina tace "No, no, not at all, i... i was just being surprise, sannu da zuwa" Da sauri ta koma gefe zuciyarta na bugawa da karfi, Ya katse wayar dake kare kunnensa sannan ya shiga parlon, ta bi sa da kallo still shocked, gani take kamar she is daydreaming, ta kikkifta idanuwanta ta bude to be sure but still she is still seeing him, har sai da ya karasa cikin parlon ya zauna sannan ta bi bayansa, a hankali ta duka kusa da shi tana yaƙen karfin hali tace "Wai dama all this while kana garin nan ne? I am so confuse" Yace "Gashi kin gan ni, in baki yarda ba sai ki taɓa ki ji don ki tabbatar" Still feigning smile tace "I am seriously surprise, this is the least thing i expected today wallahi..." Sai kuma ta tashi da sauri tace "Let me get u water" Kitchen ta tafi zuciyarta na bugawa, sai da ta jingina jikin cabinet ta dafe kirjinta a hankali tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku" Tasan at anytime Housemate dinta zai iya shigowa gidan don yamma yayi sosai, cikin hanzari ta bude fridge ta dauko masa ruwan gora da drink with glass cup sannan ta fita da sauri, tana kirkiran murmushi ta durkusa gabansa ta ajiye masa tace "Tun yaushe kake garin nan amma?" Ya dau ruwan goran yana kallo yace "You are buying expensive water now? Sannu er gayu" Tayi dariyar karfin hali tace "Not at all, miyar ma ya kusa yi sai in zuba maka abincin, ko dama shi sa kace sai nayi girki?" Kawai murmushi yayi bai bata amsa ba, ta mike ta koma kitchen, gaba daya she is confuse on what to do, ta fara dube duben wayarta ta tuna ta ajiyesa kan kujera a parlor, fitowa ta sake yi ta tarar Abdul yayi picking din kiran da ake masa ta waya, cikin dubara ta dau wayarta ta nufi dakinta da sauri tana kallonsa ta gefen ido taga attention dinsa na kan wayar da ya fara, bandakinta ta shige ta kulle tace "Na shiga uku" Da ta tuna bata ma da lambar Housemate din nata ta sake jin mugun tashin hankali, yanzu ya zata yi? Da sauri ta fara dialing number Salem, ai ko yana fara ring ya daga, murya can kasa ta gaishesa without waiting for his full reply tace "Plsss how can i get in contact with my Housemate? ina son zan masa magana ne urgently" Salem yace "Ohk, muna ma tare, gashi nan" Bata san sanda ta sauke wani irin ajiyar zuciyar relieve ba, taji muryar Housemate dinta yace "Hello Halysaah, is everything alright?" Ta girgiza masa kai da sauri kamar yana ganinta tace "Plss i am sorry amma kar kace zaka dawo yau, my fiance is around, he just came without notice" Yace "Tohhhh, haka kuma aka yi ashe?" Ta wani turo baki kamar yana ganinta, yayi murmushi yace "Alright Halysaah, keep ur cool, duk sanda ya tafi sai ki sanar min" A hankali tace "Thank you" Yace "Not a problem" Shi ya fara katse wayar, ta kalli screen din sannan ta sauke ajiyar zuciya ta fito da sauri bayan ta bar wayar a dakinta, har sannan ta tarar Abdul bai gama wayar da yake ba, da alama business call ne, Khaleesat na tafiya a hankali ta tafi kitchen don saka masa abincin da ta girka, har sannan she is shock, babban damuwarta yanzu kasantuwarsu su biyu kadai a gidan, a da bata jin tsoron kasancewa da shi guri daya and that was almost 4 years back, but not anymore, he is complete changed all of a sudden in just a year, da tunanin nan ta fito daga kitchen, ta karasa har gabansa ta ajiye masa abincin, yana kallonta yace "How about ur Housemate, bata nan ne?" Ta ɗan yi murmushin karfin hali tace "Yeah bata nan" Ta mike ta koma edge din kujera ta zauna kamar bakuwa a gidan, a hankali tace "Ya su Momy da Aunty Hafsah?" Yace "Lafiya lau" Bata sake cewa komai ba, Ya kalli abincin da ta ajiye masa yace "I am full, ki rufe sai dai anjima" A hankali tace "Ok tafiya zaka yi da shi?" Yana dubanta yace "In tafi da shi ina?" Ta kirkiri murmushi tace "A'a ai tambaya kawai nayi" Yace "Na riga nayi lodging out of the hotel, i was in Maryland since morning" Khaleesat was speechless, bata gane yayi lodging out of the hotel ba, to ina zai kwana ko kuma wani hotel din zai kama? kai bata ma yarda ba don in yayi lodge out to ina trolley din kayansa yake, Tana murmushi da kyar tace "To ina akwatin ka?" Yace "Tana cikin mota" Ta hadiye abu da kyar tace "Motar wa?" A takaice yace "Ban sani ba" sunkuyar da kai tayi bata sake cewa komai ba, yace "Ko kina da plans ne yau? Naga kinyi mamakin zuwana da gaske" Ta zaro ido tace "Not at all wallahi, ai kai ma kasan daga schl babu inda nake zuwa, kawai dai nayi mamakin muna ta waya tun daxu ashe kana garin nan" Ya mike yace "To ki dena mamaki tunda ba ke kika siya min ticket din ba" Ta sunkuyar da kanta tayi shiru, dakinta ya nufa yace "Let me take a shower" Khaleesat ta gyada masa kai kawai ta bi sa da kallo, a very tall and masculine guy he is, just like her Housemate, and they are all handsome in their own different ways kamar su suka yi kan su, sai dai ita tafi ganin kyan Housemate dinta ko me yasa, a zahiri duk macen da ta samu Abdul in dai mayyar kudi ce kuma tana son namiji me tsantsan kyau ga kuma qualities na cikakken namiji pertaining to body structure not behavior... to duk walakancin da Abdul zai dinga mata zata jure tayi ta shanyewa don mijin nuna ma sa'a ne shi din, that is if behavior isn't included, amma Khaleesat dai dai da rana daya qualities din nan biyu na Abdul bai taɓa dada ta da kasa ba, a haka stepsisters dinta ko ga maciji basa yi da ita all because of Abdul, kiri kiri suke nuna mata jealousy dinsu daga su har iyayensu a fili, ba su kadai ba hatta wasu daga sa'aninta a anguwa sun dena kulata saboda shi, basu san baƙin cikin da take kunsa day by day ba, she wish zai koma ma daya daga stepsisters din nata da ita kam ta huta, kwantar da kanta tayi jikin kujera tana jin hankalinta na kara tashi, yana nufin kenan bazai tafi anytime soon ba? kilan ma yace nan zai kwana fa? Sosai hankalinta yayi mugun tashi da tunanin hakan, after a while ta mike a sanyaye ta dau abincin da ta zubo masa ta tafi da shi kitchen ta rufe, ana haka har lkcn sallan magarib yayi bai fito daga dakinta ba, Khaleesat dake ta zaune a parlor kamar bakuwa a gidan ta kalli kofar dakin nata a sanyaye, sai kuma ta tashi walking slowly ta nufi dakin, a hankali tayi sallama sai da ya amsa sannan ta bude, ta samesa zaune saman darduma alamar sallah ya idar yana danna wayarsa, gaba daya dakin ya cika da kamshin turarensa, murmushin karfin hali ta kirkiro ta dau hijab dinta tace "Sallah zan yi" Sai kuma ta juya zata fita yace "Ina zaki yi sallan?" Ta sake juyowa cikin sanyin murya tace "Parlor" Mikewa yayi ya bar kan darduman yace "Pray here, dama kin saba sallah a parlon ne?" Ya koma gefen gado ya zauna still pressing his phone, da kyar ta karasa kan darduman ta fara sallan, bayan ta idar ta dinga addu'ar Allah ya taɓa zuciyarsa ya tashi ya tafi ya bar mata gidan ita dai, muryarsa taji yace "Make me a cup of hot chocolate" Ta gyada masa kai tace "To" Mikewa tayi ta nufi kofa ta fita zuwa kitchen, abinda yace tayi ta masa sannan ta koma dakin rike da mug din, bedside drawer ta ajiye masa tace "In kawo maka abincin?" Yace "Aa bazan ci abinci ba, me yasa kike yawo da Hijab kamar matar liman" Tana murmushin karfin hali da kyar tace "Aa ina jiran lkcn isha ne" Yace "Cire Hijab din nan" Ba musu ta cire a hankali ta linke ta ajiye, yace "Ke kin ci abincin ne?" Duk da bata ci ba ta gyada masa kai don gaba daya ta nemi appetite dinta ta rasa, gun reading material dinta ta tafi ta zauna ta kunna laptop dinta tayi kamar karatu take, ya gama danne dannensa a waya ya dau chocolate dinsa ya fara sha, gaba daya Khaleesat bata fahimtar me take dubawa a laptop din gabanta, sun kusa awa daya a yanda suke, ita dai har sannan tana gaban laptop taki tashi, ta gefen ido ta kallesa ganin ya mike daga inda yake zaune, taga sallan isha zai yi, sai da ya idar sannan ita ma ta tashi ta tafi tayi sallan, nan ma babu kalan addu'ar dabata yi ba kan Allah ya taɓa zuciyarsa ya koma hotel dinsa, after a while ta mike ta dauke darduman ta linke ta ajiye, ya mike ya kamo hannunta yana kallonta yace "Why are you uncomfortable kamar kina tare da stranger a gidan nan ne Khaleesat?" Tayi dariyar yake tace "Stranger kuma Ya Abdul? Ai kai ba stranger bane, kai yayana ne, kuma da ai ka sha kwana gidan nan farkon da na zo kasar, kana kwanciya a parlor ni kuma in kwanta a daki" Yace "Kinsan da haka kike dari dari?" Ta sunkuyar da kanta ganin kallon da yake mata, zuciyarta ya dinga bugawa, har ji take kafafuwanta suna neman kasa daukarta, ya matso da ita dab da shi har tana iya jiyo breathing dinsa, calmly yace "Kinsan menene yasa nake kwanciya a parlor a sannan?" Ta girgiza masa kai without looking at him don she is soo uncomfortable with him drawing her closer to himself, yayi kasa da murya yace "Saboda u were still a baby sannan" Ta daga idanuwanta da kyar ta kallesa amma ta kasa cewa komai, yace "Yanzu kuwa ke ba baby bace, how old are you?" Ta kasa basa amsa, ya ɗan mata tsawa yace "Tambayarki nake?" Ta hadiye wani abu da kyar tace "I am 20" yace "To a sannan ina keeping distance between us because i was still grooming you" Ta kauda kai seeing how closer he was coming to her, juyo da kanta yayi yace "Meye haka?" Muryarta na rawa tace "This is against the teaching of islam Ya Abdul, ni ba muharramarka bace" Yace "Oh really? Dama wani ne zai aure ki ba ni ba ashe?" Ta kasa ce masa komai lkci daya hawaye ya cika idonta, duk tsiyar da yake mata da yaga hawaye idonta yake calming down, ya jawota jikinsa yayi kasa da murya yace "Kin zata ke irin matan da zan yi using inyi dumping ne Khaleesat? You are diff from them, ke matar da zan aura ce" Ta kasa basa amsa hawaye na zuba idonta, ita kanta tasan Abdul so na aure yake mata, a shekarun da suka yi tare iyaka yakama mata hannu babu dadi babu kari, amma daga 2 years back labarin ya sauya har bata son ya zo inda take don sai ya mata wasu abubuwa dake damunta, in ya tafi ta sha kukanta kuma ta kan yi kwana da kwanaki bata dawo dai dai ba, amma bai taɓa attempting saninta ba, muryarsa ne ya dawo da ita daga tunanin da ta tafi, as if whispering yace "I have tried Khaleesat, i abstained from doing anything that will distabilize you all this years because i want you to have the best education ta yanda zan iya nuna ki a ko ina as my wife, amma kullum ina jin urge dinki a raina I've tried so many times to ignore the urge, but menene ya rage yanzu? You have just a year and few months to round up, aurenmu kuma ko yau aka ce a daura babu abinda zai hana daurasa, i came all the way from Nigeria because all this days my feeling for you is distabilizing me and making me go nut Khaleesat, so now trust me, relax and keep calm pls baby gal" Khaleesat ta dade bata shiga tashin hankalin da ta shiga a sannan ba, don sarai ta fahimci inda maganarsa ya dosa, kuma lkci daya yake magana yana cire mata hijab din jikinta, common ya taɓa ta idan taki ta karfi yake yi mata balle wnn, gashi gaba daya yanayinsa ya canza alamar ya fara fita hankalinsa ma, ta kamo hannunsa jikinta na rawa tace "But kwanakin da suka rage ai basu da yawa ko Ya Abdul, why not be patient pls..." Ya kalleta da idanuwansa da suka kada strictly yace "I can't wait any longer" Muryarsa kadai sai da ya tsoratata hakan yasa tayi gum da bakinta, tana jin zuciyarta kamar zai fito daga kirjinta tsabar tashin hankali, kafin ya rabata da kayanta tayi kasa da murya still holding his right hand tace "Ohk pls ka bari inyi wanka tukun, kai ma ai ka yi" Ya dinga kallonta da idonsa da suka yi ja, ta sunkuyar da kanta trying to control herself kar ta fashe da kuka tace "I won't take long" Saketa yayi ya koma gefen gado ya zauna, tana tafiya da kyar ta nufi bandaki tana kallon wayarta dake gaban dressing mirror, ta ɗan kallesa, taga bin ta yayi da kallo, ta dake da kyar tace "Zan dau shower gel dina" Gaban mirror dinta ta nufa, dai dai sanda ya fara cire rigar jikinsa da sauri ta dau wayarta da wani Container din lotion da tayi pretending shower gel ne sannan ta shige bandaki ta kulle kofa, tap ta bude jikinta na rawa hawaye na sauka idonta ta fara dialing number Salem, yana fara ring ya daga, da kyar tace "Plss i want to speak to my Housemate plss" Salem yace "Oops wllhi bama tare yanxu" Ko rufe baki bai yi ba tace "Don girman Allah ka turo min lambarsa yanzu" Yace "Ohk let me send you" Yana katse wayar ta dinga kallon screen dinta tana jiran shigowar lambar Housemate dinta, her body was just shaking, ga wani bugawa da zuciyarta yake, cikin few seconds sai gashi ya turo mata lambar, da sauri tayi dialing ya fara ringing amma har ya katse bai daga ba, ta sake kira nan ma bai daga ba, sau uku tana kiransa bai daga ba, ta saki kuka ta durkusa kasan bandakin tace "Na shiga uku" Sake dialing number Salem tayi, yana picking tace "Pls bai daga ba ko zaka..." Salem bai jira jin sauran bayaninta ba yace "Bari in tura maki number Ajay, nasan dama ba lallai Jay ya daga ba don ba ko wani kira yake dauka ba, sai kice ma Ajay ya basa suna tare yanzu" Tana gyada kai da sauri tace "Ohk to Nagode" yana katse wayar sai gashi ya turo mata number Ajay, tayi dialing number da sauri hannunta na rawa, ai kuwa yana fara ringing da few seconds aka daga, da kyar tace "Plsss ina son zan yi magana da Housemate dina ne" Shiru taji yayi as if processing the voice, sai kuma a takaice yace "Waye wannan?" Ta fara shesshekar kuka muryarta na rawa tace "Don Allah kayi hakuri ka rufa min asiri ka basa ina son zan masa magana" Yace "Me ya faru?" Cikin kuka tace "I need his help plss" katse wayar taji yayi, hankalinta in yayi dubu ya tashi a moment din nan, ta shiga uku ta lalace, yanzu ya zata yi, ko dai ta kira Safiyyah, number Safiyyah ta duba da sauri tayi dialing amma har ya katse bata daga ba, ji tayi kamar za a bude kofar bandakin tayi saurin tsoma wayar hannunta cikin ruwan da ta fara tarawa a bath tub a gigice, ashe kunnenta ne ma yaji kamar an taɓa kofa amma ba kowa gun kofar, ta ciro wayarta taga screen din yayi baƙi, ta dinga yarfe ruwan da ya shiga tana kokarin kunnawa amma yaki kunnuwa, hade kanta tayi da bath tub hawaye masu zafi na sauka idonta.... *End of free pages, za mu ci gaba da update a payment group* *For continuation of the book Halysaah, pay 500 into 3276052019 Fcmb Hauwa Bello Jiddah* _And ur evidence of payment via 07087865788_✍🏻 *My special thanks to those that have already patronized since the beginning of this book, Thank you so much and i appreciate you*🥺 ********************** ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** ************************* ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels WhatsApp Number: 08138873799 Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafinmu ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** **************************