~*BOSS LADIES WRITERS*~_ *_💋KURKUKUN ƘADDARA💋_* _The Prisoners🔥💫_ ~Middle step~ _A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty._ *Episode 1* Zaro ido su Parveen su ka yi bakunansu a sake, yayin da su ke kallon ƙofar, Wani irin farin Ciki ne Mara misaltuwa ya bayyana akan fuskokinsu Har sun wage baki zasu Fasa ihu Angel Tai saurin Dakatar da su ta hanyar cewa"Kun manta abunda na faɗa ma ku? Komi za ku gani ku ja Baki ku yi shiru idan ba haka ba asirin mu zai tonu har su gane abunda mu ke ƙoƙarin yi' Fuskokinsu Haris da alamun ruɗu donsu basu son kan me ta ke magana ba, sun dai ga murfin ƙarfe jikin bango, bayan haka sunji batul tace ƙofar da su ke nema. Naufal ne yai ƙoƙarin buɗe baki Yace"Angel Kun bar mu a duhu, bamu san kan me ku ke magana ba" ya ƙarasa maganar idanunshi akan fuskarta, har lokacin bata daina sakin murmushi ba, Haka zalika su parveen Bakin su awashe ya ke Kamar Gonar audugu Ji su ke kamar ma Har sun fuce daga Cikin kurkukun. "Ki yi mana bayani mana, Wannan murfin ƙarfen na menene a jikin bango"? javed ne yai maganar, sautin Muryoyin su daƙyar ya ke fita saboda rashin ƙarfin jikin su, har ƙwara sauran mazan akan mubeen ko da su ka shigo toilet ɗin kan shi na asaman Kafaɗar Hannah, Sam babu kuzari a jikin shi. "Na ruɗe Angel Ki fada mana mun ƙosa Mu ji," acewar Gabriel. duk wanda yai magana acikin su idanuwanta na akan la66ansa, Sai bin su ta ke yi da kallo, farin Ciki Ya hana ta yi magana. "Idan ba zata Iya yi mana Bayani Ba, Deeja Ku faɗa mana Meke faruwa ne'? Haris ne yai maganar idon shi akan su Deeja dake a tsaitsaye Cirko Cirko. Ganin sun fara fusata Yasa ta haɗiyi yawu tare da sauke nauyayyar Ajiyar zuciya, Cikin sanyin murya ta soma kora masu jawabi sannu a hankali ta fayyace masu komai dangane da ƙofar sai dai ta 6oye masu Game da tattaunawar da su ka yi Ita da Salsabeel. Tsabar mamaki yasa su ka dinga jefawa junansu kallo Lokaci ɗaya wani irin Annurin farin Ciki Mara misaltuwa ya lullu6e zukatan su, Har basu san lokacin da suka ƙarasa gaban Angel suka ɗago da ita daga zuƙunnan da take abakin Bango, gaba ɗaya su ka rungumeta, Kamar zasu Karya ƙasusuwan Jikinta, Musamman Gabriel da ya fi kowa burin son ku6uta daga kurkukun ƙaddara, zafafan hawaye ne su ka soma gangarowa ta saman fuskarta, ta rasa gane hawayen menene? Shin na farin Cikin da ta ke yi ne ko kuwa na baƙin Ciki? Ɗaya bayan ɗaya ta ke kallon su Bayan sun sake ta, Maganar da ke yi mata yawo acikin kanta itace"kada ku sanyawa ranku cewa dukkan ku za ku Rayu! wannan maganar ta yi matuƙar tsaya mata aranta, ta ta6a zuciyarta, fatan ta Allah yasa Mutuwar kada ta rusƙe su agidan kurkukun ƙaddara, ba zata so wani daga Cikin su ya ƙara rasa ran shi a wannan Ƙazamin Ginin ba, Duk idan ta tuna Matasan Yaran da ta gani awannan ɗakin lokacin da ta dura taga taje ta gane ma idonta su Rataye Saman igiyoyi kamar dabbobi sai ta ji duk jikin ta ya mutu, Haƙiƙa ta yi matuƙar girgiza ganin yadda Suke feɗe Cikin mutun mai rai su kwashe sassan Jikin shi........" Hankalin su ba ƙaramin tashi yai ba, ganin yadda Angel ta fashe da matsanancin kuka tamkar ranta zai fita har wani jiri ta ke gani acikin idanuwanta, Daƙyar ta jingina bayanta Jikim bango, taci gaba da riskar kukan ta Fuskarta jaga jaga da hawaye. Murnar da su ke yi ce ta koma Ciki, Damuwa ta bayyana Akan faces ɗinsu, Har suna haɗa baki wurin furta Sunanta "Angel! Why are u shedding ur tears? Dan Allah kada kisa zuciyoyin mu su karaya, Baki ji irin farin Cikin da mu ke yi ba, saboda Kin gano mana ƙofar da zamu bi, don mu ku6uta daga kurkukun ƙaddarar, Gidan da aka ƙuntata rayuwar mu aka hana mu sakat, Shekara da shekaru tun muna jarirai har zuwa lokacin da muka fara mallakar hankalin mu, Angel dukkan mu nan babu wanda bai haura shekara sha wani abu ba a gidan kurkukun Nan, Ta ya ya ba zamuyi farin Cikin Ganin ƙofar nan ba? muna so mu tsira kodan Muga ya wajen kurkukun nan ya ke, Muna so muga hasken dake awajen shi, koda da numfashin mu na ƙarshe ne, mu dai burin mu, shi ne mu ga mun ku6uta, Idan ma kina tunanin ba zamu Iya tsira mu dukkan mu ba, Zamu roƙi Allah da ya ara mana lokaci mu bar kurkukun nan wlh bamu fatan mu yi wulaƙantacciyar mutuwa acikin shi! Mun fi so Mutuwar ta risƙe mu acan inda zamu je koma akan hanyar Guduwar mu ne......." Kalamansu sun ƙara karya mata zuciya, kallon da take binsu da shi da rinannun idanuwanta waɗanda suka canza launi kallo ne da ke nuni da tsantsar ƙaunar su, tausayin su da ta ke ji, Ko ɗaya daga Cikin su ba ta son ta rasa, sai dai tasan ba abune mai yiwuwa ba, Mutuwa dole ce! Tsawon lokaci Suna ta shan kukansu musamman Batul da su Azeeza in ka cire mazan da ke a cikinsu, hawaye ne kwance acikin fararen idanuwansu. "Muna 6ata lokaci Angel, Ni zan fara jaraba 6alle ƙofar," Gabriel ne yai maganar, Shi da ba ƙoshin lafiya ba. A haka ya nufi ƙofar ya zuƙunna yana tatta6a Jikinta. "Nima zan ta ya ka" acewar Naufal, yai maganar tare da matsawa kusa da Gabriel Ya zuƙunna, Atare suka dunga bugun ƙofar da niyar ta buɗe, sun haɗa uban gumi akan fuskokin su, murfin ƙarfen ko motsi bai yi balle su sa ran zai buɗe. Matsawa Haris yai kusa dasu Shima ya sanya hannun shi, Hada matan kowa Ya shiga gwada ƙarfin shi akan ƙofar don ta buɗe, Duk wannan budurin da ake yi Jemimah Tana acan cikin ɗakin su kwance saman gado, ta lullu6e kanta da bargo baccin ne bai ishe ta ba. Sun ɗauka cewa abun wasan yara ne shiyasa su ka dage akan sai sun buɗe ƙofar, Mayen ƙarfe ne murfin da ke ajikinta Yana da ƙarko Shekara da shekaru wurin yana adatse ta ya ya zasu iya buɗe shi? Yaran da ba lafiya gare su ba, Ganin yadda suke ta gabzar ƙofar ko sautin bugun da su ke yi mata bai fita sun Dage sun nace akan dole sai sun buɗe ta.. "Haris! Gabriel! Ku daina wahalar da kanku, Ƙofar ba zata ta6a buɗewa ba, saboda babu babban mukullin da zamu Iya buɗe ta da shi,". Jin wannan maganar da Angel ta yi ne yasa su ka mimmiƙe tsaye sai nishi suke fitarwa ta ko'ina sufa ke tsastsafo masu a jikin su Atare suka haɗa baki wurin faɗin"Makulli? A ina zamu same shi? Dan Allah ki faɗa mana inda ya ke" Zuciyarta ba ƙaramar karaya ta yi ba a yayin da su ke tambayarta ina makullin , wani abu da ta lura dashi gaba ɗaya hankalin su ba'a kwance ya ke ba, duk sun furgice burinsu kawai su bar kurkukun. "Angel kin yi shiru baki amsa mana ba" Jan numfashi ta yi tare da sanya tongue ɗinta ta ɗan lashi lower lip ɗinta da ya bushe Cikin sanyi murya ta soma yi masu magana "Danish! Shine makullin Da zai Iya 6alle mana ƙofar, gashi baya atare damu Yana acikin kurkuku, Yanzu dole sai mun nemo shi idan har muna son mu ku6uta ......." a matuƙar ruɗe su ke jefa mata kallo, Dole su yi mamaki, Ta ya ya Danish da ya kasance Ragon Namiji acikin su zai zama Makullin buɗe ƙofa? How that can be possible? Ta ina Danish ya ke da ƙarfin yin hakan? ganin irin kallon da su ke binta dashi yasa ta fahimci cewa Basu gasgata maganarta ba. Suna buƙatar ƙarin haske. "Bazan Iya yi ma ku dogon bayani ba, because you won't understand me, but definitely Danish is the key to open the door, just believe my words, he can open it," Lamarin ya yi matuƙar ɗaure masu kai, Musamman Haris shi da yafi kowa sanin Danish, mutumin da ko ƙwaro Tsoron shi ya ke ji yau shine Angel ta ke kira da makullin buɗe ƙofa. "Maganar ki gaskice! Ni shaida ne akan hakan! Danish ne kaɗai zai Iya buɗe ƙofar! kusan atare suka ɗaura Idanuwansu akan fuskar Gabriel da yayi maganar. "Nasan za ku yi mamaki, Dalilin da yasa nace haka, Saboda kokawar da muka ta6a yi dashi, lokacin da Danish Ya shaƙi wuyana da hannun shi, Shaƙar da bana tunanin cikakken mutunne yayi mini ita, Ni nasan mai naji a lokacin da har yaja na naushi idonshi, ƙarfi ne dashi naban mamaki, tabbas shi zai iya buɗe ƙofar......" tunkan ya ƙarasa rufe baki Haris yace"Kun rikita mini tunani na, Taya mutumin daya rasa idon shi ɗaya zai Iya yin hakan? Bayan ni asani na Danish bashi da wani ƙarfi," Fuskar shi da alamun ruɗu yai maganar. "Danish Ya rasa ido"! Batul ce ta ambaci hakan Idanuwanta azazzare hankalinta ba ƙaramin tashi yai ba jin abunda Haris yace don ita bata san da zancen rasa ido da Danish yai ba, sun6oye mata don karsu tayar mata da hankalinta. "Danish bai rasa idonshi ba, Sun samu sa6ani da Gabriel ne, Har takaiga ya naushi idon shi, wanda silar hakan Giant yazo ya tafi dashi, Na 6oye maki hakan ne saboda bana son hankalin ki ya tashi, Kuma Ni da kaina Danish ya faɗa mini cewa Lafiyar shi qalou ba abunda ya same shi, ' Angel ce ta kora mata jawabi, Hankalin batul yaƙi kwanciya da kalamanta, jikin ta yayi sanyi, hawaye tuni sun soma yin sintiri saman kuncin ta. "Shikenan Yanzu ki faɗa mana Taya za'ae mu ga ɗan uwan mu Danish? Idan ma ta kama Ni zan bi ki mu shiga prison ne don mu nemo shi" Gabriel ne yai maganar da ƙwarin gwiwarsa, Har yanzu yana nan da rashin tsoronshi. Girgiza kai Angel tayi"wannan aikina ne, Ni kaɗaice zan Iya dawo da Danish Cikin mu, In sha Allah, " "But how could you do that? Bayan babu wata ƙofa da zaki Iya shiga prison"? Har ta buɗe baki da niyar Ta amsa Ma Naufal tambayar da yai mata, kwatsam! ba zato ba tsammani Kunnuwanta su ka jiyo mata motsin buɗe ƙopar ɗakin su, hakan yasa tai saurin Katse maganarta, Idanuwanta azazzare Take kallon su. "Kamar buɗe ƙofar ɗakin Mu ake yi? Mun shiga uku, Asirin mu zai tonu, wlh mu gudu daga Cikin toilet ɗin nan," Parveen ce tai maganar, hankalinsu idan yai dubu toh ya tashi, Gaba ɗaya duk sun bi sun ruɗe, a sukwane Angel ta juya da gudu ta nufi Ƙofar toilet ta buɗe ta, Fucewar ta keda wuya suma suka bi bayanta, garin gudu har suna bangaje juna, Adai dai lokacin da suka faɗo tsakiyar ɗakin, kowannansu ya tsaya da tafiya, Idanuwansu azazzare su ke bin benan da kallo, sai faman haki suke yi babu mai sauran kwanciyar hankali acikin su, babban abunda su ke jima fargaba kada ace Tsohuwa zafreen ce, Ilai ko hasashen su Ya zama gaskiya, ƙofar na ƙarasa buɗewa kunnuwansu suka soma jiyo masu takun takalmanta Har wani sauti su ke badawa ƙwas ƙwas! Jikinsu Ya hau kakarwa zufa ta dinga tsastsafo masu ta ko'ina a jikin su. Cikin muryar raɗa Deeja tace"Mun shiga uku Angel mun manta bamu maida tukunyar fulawar nan ba! Yanzu idan ta shiga toilet ɗin ya zamu yi? Ƙasa ƙasa da murya Angel ta ce"In sha Allah ma ba zata shiga ba, Idan ma tai yunƙurin yin hakan zan dakatar da ita," ita kanta da ta ke yin maganar a tsoroce ta ke furtata, ƙarfin halin ne kawai. Ahankali ta ke tunkaro in da suke atsaye Cikin shigarta ta jajayen kaya, Yau babu mask a kan fuskarta, Daga bayanta Giants ne Guda Biyu masu ƙirar Samudawa, ko da ta ƙaraso dab dasu saita dakata da yin tafiyar A tsanake ta ke binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya, Saboda tsabar ruɗu da kama kai, Jikin Angel na 6ari ta russinar da kanta Ƙasa muryarta babu natsuwa ta furta"Ina kwana" Tun da tsohuwa zafreen ta kafe ta da ido sam ta kasa motsawa, Lamarin ne ya ɗaure mata kai, Yadda Angel ta duƙa mata wurin gaishe da ita..... Da sauri su Haris suka russinar da kansu tare da gaishe da ita Cikin girmamawa. Babu wanda ta amsamawa a cikinsu, Tsawon mintuna biyar kafin ta ɗan yi gyaran murya tare da basu Umarnin su ɗago da kawunansu, bayan sun ɗago ta tsare fuskar angel da blue eyes ɗinta, Suspicious looking ta ke binta dashi Hatta tsigar jikin Angel sai da ta tashi haiƙam, Sam takasa yarda su haɗa ido da tsohuwa zafreen, ta dage tana ta wasa da yatsun hannunta, ta harɗe su acikin na juna, Su ta ƙurawa ido. Su Deeja duk sun sha jinin jikin su, ganin irin kallon da tsohuwa zafreen ke bin Angel da shi, Kuskuren da Angel ta tafka shine gaishe da zafreen da ta yi, Mace Dattijuwa irin zafreen wadda taga jiya taga yau, Taya zata Iya yi mata wayau? Yarinyar da bata ta6a gaishe da ita ba, sai yau Hakan ya ƙara sanya mata zargin wani abu na faruwa a ɗakin nasu, A hankali takawar da idanuwanta daga kan fuskar Angel ta soma bin fuskokin su Batul da kallo, Sai faman zazzare idanuwansu suke yi, sam babu alamun gaskiya atattare dasu, duk wani motsinsu akan idonta. Ba zato ba tsammani suka ga ta tuntsire da dariya mai sautin gaske hankalinsu ya ƙara ɗugunzuma, a firgice su ke bin ta da kallo, Lokaci ɗaya ta dakata dayin dariyar ta ɗaure fuskarta tamau babu annuri. "Meyasa ki ka yi gaggawar gaishe dani tun kafin in buƙaci hakan? Kamar daga sama Angel taji ta jefa mata tambayar. Yawu ta haɗiya kutt a maƙoshinta, Idanuwanta na kallon Ƙasa azazzare ta soma magana Cikin rashin natsuwa "Nagane kuskure na, kuma Na yi danasanin rashin kunyar da na yi maki a kwanakin baya, inaso na gyara tsakanina dake ne saboda nasan ban kyauta ba.." tunkan ta kai ƙarshen maganar tsohuwa zafreen ta soma sakin bazawarin murmushi, wanda silar hakan yasa ta kasa ƙarasa zancen da ta kamo. "Saboda meyasa kike son gyara tsakanina da ke"? Ras taji gabanta ya faɗi, Daƙyar ta tattara natsuwarta kafin ta ci gaba da magana"Mahafina bai koyar dani rashin kunya ba, Tunkafin rasuwar shi yana yawan yi mini nasiha akan girmama na gaba dani, amma saboda rashin jin magana irin nawa ban bi abinda yake koya mini ba nayi danasani........" Sosai ta fashe da kuka gaba ɗaya idonsu Hibba akanta, Tsabar mamaki yasa suka saki bakunansu suna kallon Fuskarta, Ba ƙaramar ƴar drama bace. Da buɗar bakin tsohuwa zafreen sai cewa tai"well done Unaisah! Dila sarkin wayau! Da ace ke ƴar film ce tabbas zaki iya cin gasar wadda tafi kowa Iya wasan kwaikwayo, Tun da nake ba ata6a rainin mini wayau irin na yau ba, Ƴar ƙaramar yarinyar da na yi jika da ita...." maganar tsohuwa zafreen ba ƙaramin ƙara ɗaga masu hankali ta yi ba, duk sun sha Jinin Jikin su. "Ku faɗa min Me ku ke shiryawa ne" Shiru su ka yi ƙirjinsu na bugawa , Mirmushin gefen fuska ta saki tare da cewa"Dama nasani ba za ku faɗa mini ba, Idan naso zan iya yin anfani da sihirin da nake dashi wurin jin abunda zuciyarku ke saƙa maku, Ko in sanya ku yi mini magana da kunan ku,' Yanayin yadda suka zazzare Ƙwayar idanuwansu tamkar zata faɗo ƙasa, tsoro da firgici ne tsantsa akan fuskokin su. Ganin tana ƙoƙarin buga sandarta ƙasa Yasa Angel tai saurin cewa"Zan faɗa maki gaskiya, " tsayar da ido zafreen tayi akan fuskarta. "Tattaunawa mu ke yi akan yadda zamu ku6uta daga Cikin kurkukun nan saboda mun gaji da rayuwar kulle, Muna so mu ma mu yi rayuwar ƴanci kamar yarda sauran mutane su ke Yi" Daƙyar ta kai ƙarshen maganar tana mai haɗiyar yawu, Su Batul duk suna sauraronsu babu wani mai natsuwa a cikin su. "Ban yarda da maganar ki ba, A iya sani na prisoners basu da hankalin Yin tunani mai kyau irin wannan balle har su baki haɗin kai ku tattauna da junanku, Ke ce kika tsara komai Unaisah, saboda kina son karkatar da hankalina don In yarda da maganar ki, " Tun kan ta ƙarasa maganar ta soma bin ɗakin nasu da kallo, Kamar sakarkaru haka suka dinga binta da ido Cike da fargabatar karta faɗa sashen toilet ɗinsu asiri Ya tonu, A hankali take tafiya tana ƙarewa ɗakin Kallo Kafin Ta Juyo a sukwane Ta tun kari sashen toilet ɗin su, Tashin hankalin A matuƙar tsorace suke kallon bayanta, Giants ɗin dake atare da ita basu motsa ba, suna atsaye Kamar gumaka Su Angel Ido ya raina fata, Sai faman Cizon yatsa ta ke Yi, Ji take kamar ta watsa aguje tasha gaban zafreen. "Innalillahi Ya Allah ta makance kafin ta shiga, Ya Allah ka taimake mu! ya Allah ka hanata gani" Acikin zuciyoyinsu suke furta hakan, Suna ganin ta shige Ciki, Zufa ta soma wanke fuskokinsu, Azeeza tuni ta fara matse kwallo, sun san dole Taga abunda suke aiwatarwa, Idan kuwa harta gano zasu ɗanɗani kuɗarsu ne, Kowa zaiji a jikin shi, Babban abunda yafi damun Angel gargaɗin da Salsabeel ya yi mata akan su yi takatsantsan Yanzu idan asiri ya tonu gaba ɗaya taja masu masifa da bala'e. Runtse idanuwanta ta yi sosai, hawaye ta ko'ina suka shiga wanke fuskarta, idanuwansu Deeja akanta, Tausayin kansu ne ya kama su, Har sun fara hasashen irin Azabtarwar da za'ayi masu kafin akashe su, Sai bin Juna su ke yi da ido babu mai magana saboda Giants ɗin da ke tsaye akansu. Fitowa tsohuwa zafreen ta yi daga sashen toilet ɗinsu, Fuskarta ɗauke da shu'umin murmushin nan nata mai wuyar fassaruwa, girgiza mata kai su ka dinga yi ba tare da sun iya furta komai ba, Sun riga da sunsan taga ƙofar nan shikenan ta faru da ta ƙare, Watan Cin ubansu ya tsaya, sun kirawa kansu mutuwa tunkafin lokacin su yayi. "Wallahi Allah!....' Azeeza ce ta yi su6ul da baka, da sauri Gabriel Ya toshe mata bakinta da hannun shi, ruwan hawaye ne kwance acikin idanuwansu, duk sun ƙagara su ji wani hukunci zata yanke masu tun da ta gano plan ɗinsu. Walking magestically ta ƙaraso gabansu Tare da tsaida sandarta a ƙasa, Daya bayan ɗaya ta ke kallon su tsawon mintuna Uku kafin ta soma magana atsanake "Furennin da ku ka shufka sunyi kyau sosai, Wanene ke basu ruwa A cikin ku? Zaro ido su ka yi akan fuskarta Mamaki Ya kamasu, Aransu suka shiga ayyana cewa" ko dai bata ga ƙofar ba ne? Ko kuwa Allah ne yaji kokensu ya hanata ganin komai. "Kun yi shiru baku bani amsa ba"? Yawu Angel ta haɗiya Muryarta Na rawa ta ce"am..um..ni..nice..Ni nake bata ruwa, tare da ƴan uwana," Murmushi tsohuwa zafreen ta saki tare da cewa"Ku cigaba da bata ruwa inason furenni, Nan da wani lokaci zan ɗauke tukunyar fulawar in mayar da ita ɗakina..." tsabar zalama tunkan ta ƙarasa maganar Angel tai wuff wurin cewa"idan ma kinaso Yanzu saina ɗauko maki ita ki tafi da ita, ai mu mun fi son duk wani abu da zai faranta maki rai" kallonta tsohuwa zafreen ta yi da tsoffin idanuwanta"Kamar baki da gaskiya? Ina magana kina katse ni"! A kausashe tayi maganar. Sunnar dakai ƙasa Angel tayi a tsananin ruɗe Batul ta ɗaura da cewa"Ae tun lokacin da aka canza mana abinci zuwa ganye, Angel ta soma Fita hayyacinta, sam babu natsuwa atattare da ita, Hakanan zaki ga ta zauna tana sambatu ita kaɗai" ta ƙarasa maganar hada murmushinta, (Yara sun zama ƴan wasan kwaikwayo) "Eyyah Hakane ashe, " jinjina kai Angel tayi"dama ni tun ina agida idan na ci abincin da aka haɗa da ganye zaucewa nake yi, Bana son Cin ganye yana affecting ɗina" Fuskarta amarairace ta yi maganar. Shiru tsohuwa zafreen ta yi a yayin da ta ke ƙare masu kallo kamar tana son gano wani abu da ke 6oye akan fuskokin su sai dai Allah bai bata ikon fahimtar komai ba, Abun da ya ɗaure mata kai yadda su ke yi mata magana ba tare da jin shakkarta ba. "Da za ki bamu dama Yau na rana ɗaya kawai, Ki zauna muyi fira da ke, A matsayin ki na kakarmu....." gaba ɗaya sun ruɗar da ita, sai kallonsu take yi tana faman jinjina kai kamar ƴar ƙadangaruwa Sun kashe mata bakin magana, A hanzarce ta juya ta nufi bene Giants dake take mata baya suka juyawa tare da bin bayanta, Suna jiyo sautin rufe ƙofar ɗakinsu, Gaba ɗaya suka daka uban tsalle tare da rungume junansu fuskokinsu ɗauke da farin Cikin nasarar da su ka yi akanta, yau sun kashe tsohuwa zafreen da mamaki "Alhamdulillah Ya Allah, Mun gode da taimakon ka agare mu, " Angel ce ta furta hakan. "Mun ji jiki yau Allah, ba kiji yadda gaba na ke faɗuwa ba, tun da ta shigo hankalina yaƙi kwanciya" acewar Yasmin, Hibba tace"Ae ba ke ka ɗai ba, ni kaina ƙiris ya rage in saki fitsari a wando, matar can bala'e ce' Kowa yana tofa albarkacin bakin shi "Amma wai ya akai da ta shiga toilet din bata ga komai ba? Kuma har ta ga Tukunyar fulawar"? Naufal nai yai tambayar mamaki ya ishe shi "Ae Allah muka roƙo shine ya makantar da ita, shiyasa bata ga komai ba" Deeja ce tai maganar, "Pls kudaina maganar nan kada Suji mu tunda suna ganin mu, Inaso mu yi magana amma dole mu jira zuwa anjima idan marece Ya nutsa, sai mu shiga sashen toilet dinmu saboda idan su ka ga zaryar Tayi yawa zasu fahimci wani abu" Atare suka hada baki wurin furta mata "Toh" "Yanzu kowa yaje ya kwanta, Inaso ku huta, kafin zuwa anjima " ɗaya bayan ɗaya suka nufi gadajen su tare da haye saman suka kwakkwanta, Mutun uku ya rage a tsaye, Zuciyoyin A cunkushe suke da tunanin taya zasu Iya 6alle murfin ƙofar nan? Taya zasu iya Gano Danish? Fatansu Allah yasa adawo masu da shi ba tare da sun sha wahala ba, A tunanin su Haris kenan su da basu san komai game da zamanshi giant ba. Mutun uku da suka rage atsaye Gabriel ne sai Batul tare da Angel, Sunƙi tafiya ga dukkan alamu suna buƙatar jin wani bayani ne daga gare ta. Kallon su ta ɗanyi kafin ta soma magana "Gabriel nasan me ka ke son ji, Ka ƙara haƙuri zan yi maka bayanin komai" amsa mata yai da toh tare da juyawa ya nufi gadon shi. "bugun zuciyata me kike tunani ne"? Lumshe ido batul ta yi tare da ware su kan fuskar Angel"har yanzu ban fahimci komai ba, dangane da abunda ya faru da ɗan uwana Danish, hankalina bai kwanta da abunda kika faɗa mini ya faru dashi," Matsawa Angel tayi kusa da ita sosai har numfashinsu na kokawa dana juna "Kin damu dashi"? Jinjina mata kai tayi alamar eh, ta ƙara da cewa"taya bazan damu dashi ba Angel, bakisan yadda nake jin shi acikin zuciyata ba, da ace ina da hanyar da zanbi inje gare shi nothing would stop me from going." Angel ba ta yi mamakin jin abunda batul tace mata ba, saboda sanin irin shaƙuwar dake a tsakaninsu, Hakan yasa ma taƙi sanar da ita cewa Ya zama Giant, gudun kada ta sanya damuwa Ruwan hawayen da ya taru acikin idonta ne yaci gaba da gangarowa "Ki kwantar da hankalin ki bana son kina shedding tears din ki, Ko dan saboda farin Cikin ki zan yi ƙoƙari wurin ganin Danish ya dawo gare mu," kwantar da kanta tayi saman kafaɗar Angel taci gaba da yin shessheƙar kuka tana faɗin"Amma ai bashi da lafiya, An cire mashi ido ɗaya, bansan awani hali yake ciki ba, " "Ki daina kuka batul so kike hankalinsu Ya ƙara tashi? Nace ma ki lafiyar shi ƙalau shi da kanshi Ya faɗa mini cewa babu abunda ya samu idonshi" lallashinta Angel taci gaba dayi har saida ta samu ta lafa, Abun da yaɗaure ma Angel kai, zazza6in da taji a jikin batul lokacin da ta kwantar da kanta saman kafadarta, Jikinta zafi sosai. Hannayenta biyu ta ɗaura saman shoulders ɗin batul, ta ɗago da kanta, Idanuwansu acikin na juna, "Baki da lafiya ne?naji jikin ki da zafi"? Muryarta adisashe ta ce"Lafiyata qalou, idan ma bani da lafiya damuwar rashin Danish ne" shiru Angel tayi kamar an ɗauke mata sautin muryarta, ta rasa tunanin me za ta yi, Ruƙo hannun batul tayi acikin nata Calmly tace "You need to take a bath, mu je in raka ki toilet, girgiza kai batul tayi"A'a bana iya wanka, nafi so na kwanta zuwa anjima idan na tashi zanyi," Gyaɗa kai Angel tayi"shikenan muje mu kwanta da anjima nima zanyi wankan" Atare suka nufi gadajen su, tafiya su ke yi kamar waɗanda aka zarewa laka, babu kuzari a jikin kowaccensu, Ita dai Angel akwai wani abu dake damunta acan ƙasan zuciyarta, Fatan ta Allah yasa hasashenta karya zama gaskiya don kuwa ba ƙaramar matsala za'a samu ba. Ta yi niyar ta kwanta asaman Gadon Danish ganin Jemimah kwance saman nata gadon, sai dai kafin ta gama yanke shawara da zuciyarta batul ta riga ta kwanciya saman gadonshi, da ido ta bita da kallo ganin ta rungume pillow dinshi a ƙirjinta tare da lumshe idanuwanta, Jiri Angel ta gani acikin idanuwanta kamar zata faɗi kasa adaddafe ta nufi gadonta daƙyar ta haye gefen jemimah ta kwanta tana faman sauke ajiyar zuciya, lokaci ɗaya ta ji yanayin jikinta ya canza zuwa zazza6i, hakan yasa ta soma ambaton sunan Allah, sama sama ta fara jin bacci yana fisgarta har ya ci nasara akanta sosai ta nutsa tana bacci............... Ɗakin ya yi tsit babu mai magana a cikin su, kamar masu bacci alhalin kuwa likimo su ka yi, sai da marece ya nutsa Angel ta umarce su akan su je su yi wanka saboda wunin ranar jikin su baiga ruwa ba, ba tare da 6ata lokaci ba kowannansu Yayi wanka, ta ɗauko masu sababbin uniform ɗinsu kowa ya zura nashi a jikin shi, tsaffin kuma suka cire su Angel ta kar6esu ta ninke su ta ajiye saman table. Lokacin da dare ya gabato, dubara su ka yi wurin kashe Floor lamps ɗin da ke a ƙasan ɗakin su, Duhu Ya mamaye idanuwansu, saboda sabon da su ka yi da ɗakin yasa su ke iya gane hanya ko a cikin duhu, Kamar yarda Angel ta tsara masu mutun Uku ne zasu Haɗa masu kayan su A cikin akwatin da zasu gudu da shi, Rai da burin sufa shirin matafiya su ke yi tun kafin su gano Makullin Buɗe ƙofa, Babu wanda yai bacci acikin su Hatta Jemimah idonta biyu tun ɗazu da marece da ta farka Angel tayi mata bayanin komai dangane da gano ƙofa da kuma shirin su na guduwa, abunda yasa tayi mata bayani don kada ta basu matsala, da ya ke yarinyar tana da wayau ta fahimce ta sosai, yanzu haka suna kwance saman gadon Angel ita da azeeza sun rungume juna sunata saƙa wasiƙar jaki game da rayuwar da za su yi agidan daddyn Genie ɗinta. Sauran Ƴan uwan nasu duk suna a zaune gefen gadajen su, duk wani motsin su Angel akan kunnuwansu. "Bamu san Girman ƙofar ba Angel Kada mu gaza wuce wa da akwatin kayan mu" Gabriel ne yai maganar, Cikin duhu suke magana, zurfin tunani ta yi acikin kwakwalwarta, A Labarin da Salsabeel ya bata Na mahaifin shi habibullah ya tabbatar mata da cewa Ƙofar sai da rarrafe mutun zai Iya giftawa ta cikinta, mutun zai Iya rarrafawa ko ya zauna, Amma babu zancen miƙewa tsaye, abun zai zo masu da sauƙi tun da basu da girman jiki, yawancinsu dogaye ne amma babu ƙiba, haris ɗin ma da ke da jiki yanzu ya zabge ya koma kamar su Javed. "Ae akwatin zamu Iya kwantar dashi mu dinga tura shi ta cikin hanyar, Ni abunda nake Jiye mana kada mu kwasa mu tafi zai Iya kasancewa ƙurmin daji ne bamusan ya weather ɗin shi zai kasance ba, Zafi ko Sanyi, Zamu sha wahala akwai sanyin da ma zai Iya kisa Haka zafi ma, Ni nafi so mu tafi da bargunan mu saboda tsaro, shiyasa nake so mu ɗauki akwati ɗaya sai Backpack ɗin Unaiza dole mu tafi da ita saboda gadon mu ce. Duk maganganun da suke tattaunawa cikin duhu akan kunnan ƴan uwansu da ke zaune gefen gado Sun natsu suna sauraron su. "Mu fara ɗaukar uniform ɗin mu jera su ciki, " batul ce tai maganar, Angel tace"Ki je toilet ki ɗauko mana fitila ɗaya amma ki fara kashe ta tun acan dan kada su gan mu, a ɗakin tsohuwa tamira zamu aiwatar da komai" ta amsa mata da toh, kafin ta nufi hanyar sashen toilet ɗinsu cikin duhu har ta samu ta cimma ƙofar makewayin nasu, da hannu ta tura ƙofar ta kutsa kai ciki ta shiga ta ɗauko fitilar tare da kashe ta, Kafin ta dawo ɗakin tunkan ta ƙaraso tace dasu gata nan tafe, Ruƙo hannunta Angel tayi acikin nata ta kuma ruƙo hannun Gabriel da ɗayan hannun atare suka shige ɗakin tsohuwa tamira, "Ki kunna fitilar yanzu, Ni kuma zan shiga ɗaki In ɗauko Akwatin kayan mu da backpack ɗin" ta amsa da toh, Batul na kunna fitilar Haske Ya gauraye ko'ina na ɗakin tsohuwa Tamira, Zazzaro ido su ka yi ita da Gabriel da mamaki akan fuskokinsu suke bin Bedroom ɗin da kallo, basu ta6a sanin haka ya ke ba, Yau ne rana ta farko da batul ta fara shigowa ɗakin tsohuwa tamira. Kallon Juna su ka yi ita da Gabriel Murmushi ne ya bayyana akan fuskokinsu ba tare da sun yiwa juna magana ba. Turo ƙofar ɗakin akayi da sauri suka kalli mai shigowa, Angel ce janye da akwati ɗaya na kayansu, Ta goyo back pack ɗin Unaiza saman bayanta sai ta yi tamkar Ɗalibar makaranta, A tsakiyar ɗakin tsohuwa tamira ta ajiye akwatin saman floor, ta kwanto jakar bayanta ta ɗaura ta saman table. "Angel Har yanzu ba ki yi mana bayanin ta ya ya akai kika gane inda ƙofar nan ta ke? Waye ya faɗa maki kiyi amfani da ruwan zafi don shafen wurin ya tsage? after that Mun yi mamakin yadda akai kika buɗe ɗakin tsohuwa Tamira ko dai itace duk ta faɗa maki hakan"? Batul ce tayi mata tambayar a ƙagare da son jin amsarta. "Zan baki amsar tambayarki amma kafin nan inaso ki kira mini su Haris su shigo ayi komai agabansu" har ta juya zata fuce da fitilar hannunta da sauri Gabriel Ya cafko damtsen hannunta tare da janyo ta baya yana fadin"So kike asirin mu ya tonu? Ina zaki da fitila"? Murmushi ta ɗan saki tare da cewa"Na shafa'a ne" kar6ar fitilar yayi ita kuma ta fuce Jim kaɗan Su kaji an turo ƙofar Haris Ne agaba Deeja na abayan shi dasu Hibba a jere suka shigo Hada azeeza Hannah ce ta ruƙo hannunta. "Wa ya ce ku zo da Azeeza? Ba a kwance ta ke ba"? Gabriel ne yai maganar Yana kallonta, Naufal yace"kasan halinta da rigima tafi son komai za'ayi ayi agabanta mutun na fama da makantar dare," Ranta ne ya 6aci sosai jin abunda suke cewa, fusge hannunta ta yi daga ruƙon da Hanna tayi mata, A ƙasa ta zuƙunna tana rera masu kuka. Angel tace"Dan Allah ku rarrashe ta idan ba so ku ke ta tona mana asiri ba" Gabriel ne ya nufi wurin da ta ke a zuƙunne ya kai hannu ɗaya ya ɗago da ita kamar jira ta ke yi ta faɗa saman laps ɗinshi tana cigaba da kuka, Murmushi ya saki yana kallonta har mamakin Ƙarantarta ya ke yi, "Its ok Share hawayen ki My Azeeza, kinsan bana son zubar hawayenki, Ko so ki ke Ajiyo sautin kukan ki asirin mu ya tonu"? Muryarta da shessheƙar kuka tace"A'a" yace"okey wipe ur tears, zan Goya ki abayana don bana son kisha wahalar neman ɗan jagora," yai maganar tare da miƙa ma Batul fitilar hannun shi, bayan ta kar6a ya zuƙunna Azeeza ta haye bayan shi ta ƙanƙameshi sosai, Ya miƙe ɗauke da ita" Angel na ƙoƙarin fara yi masu bayani muryar jemimah da suka bari ita kaɗai acikin ɗaki ya karaɗe kunnuwansu ta kware baki Tana ƙwala mata kira"Genie! Genie! " da sauri Angel ta nufi ƙopar ta buɗe ta fuce, Bayan fitarta Hankalinsu Ya koma kan ɗakin da su ke a ciki na tsohuwa Tamira Sai faman wurwurga ƙwayar idanuwansu su ke yi, Parveen Acici Tana Hango Wannan Tea pot ɗin da ƴan kofuna biyu jiki na rawa ta nufi table ɗin dake ɗauke dasu, ta zauna saman kujera tare da ɗaukar pot ɗin tana jijjigata don taji idan akwai ruwan shayi aciki, "Kada ki kuskura ki ce zaki sha, Kawai daga ganin abu bakisan tsawon lokacin daya ɗauka a ajiye ba kin ɗauka zaki sha da ya ke ba ki da linzami indai akan abinci ne" Deeja ce ke yi mata magana, Saboda kafiya irin ta parveen ko kallo bata isheta ba hada cewa"dama kin daina wahalar da kanki wurin yi mini magana don wlh saina sha tea ɗin nan" Tsawa haris ya daka mata"Zaki tashi ko saina 6ata maki rai"? Murguɗa mashi ƙaramin bakinta ta yi"Wai ku ina ruwan ku dani ne? Cikina ne ko naku"? dafe kai Hannah ta yi tare da cewa"ku ukun nan kunfi kowa jaraba dake da Azeeza sai waccan ƴar jemimah, Ni inaga Idan mun tashi tafiya mu bar su a kurkukun domin kuwa nan yafi da cewa dasu, in ba haka ba zasu ja mana ne" Jin maganar Hannah yasa azeeza dake kwance bayan gabriel ta ƙara fashewa da wani sabon kukan, saboda ance za'a barsu a kurkuku "Pls Hannah stop saying that, na samu na rarrasheta gashi yanzu kinsa ta kuma fashewa da wani kukan" acewar Gabriel, ta6e baki hannah ta yi ba tare da ta tanka mashi ba. Daƙyar ya samu yashawo kan Azeeza ta daina yi mashi kuka, Parveen kuwa harta Tsiyaya Shayin A cikin Cup hada lashe baki zata fara sha, Kamar daga sama taji an damƙi wuyan rigarta daga baya, da sauri ta ɗago don taga wanene, dama saida ranta ya bata cewar shi ne Harara ta shiga jefa mashi tare da murguɗa mashi baki, Ya ɗaure fuskarshi sosai babu annuri "Tashi ki bar wurin" kaitsaye ya bata umarni, tasan halin shi sarai miƙewa ta yi ranta a6ace, bata so ya hana ta shan tea din ba, ta ƙwallafa rai. Acikin hannunshi ya ruƙe nata sosai don kada ta kufce mashi ta koma shan shayin, Naufal kenan. "Angel shiru bata dawowa ba, Tabar mu atsaitsaye cirko cirko, Ni bari ma in haye saman gadon tsohuwa in kwanta" Rubina ce ta yi maganar, bata kai ga zuwa ta hau gadon ba, Angel ta turo ƙofar hannayenta biyu rungume da uniform dinsu, Jemimah na kwance saman bayanta, Ta ƙanƙameta da hannayenta, abunda ya jawo har suka daɗe Jemimah ce ta buƙaci ta rakata toilet zata zazzage cikinta, Shiyasa basu dawo da wuri ba, Sai da Angel ta jira ta gama tukunna ta kamota suka dawo ɗakin. Ataƙaice Cikin daren suka jera uniform ɗinsu acikin akwatin kayan, Hada barguna Deeja ta ɗauko masu guda takwas daƙyar akwatin ya iya ɗauke su, Har saida suka rage uniform din dake a ciki suka turasu cikin backpack ɗin Unaiza tukunna ya ishe su, Bayan sun kammala sanya kayan suka datse shi, daga cikin abubuwan da suka dauka bayan uniform da barguna hada cotton scarves dinsu da Hulunansu sai rigunan sanyi da takalmansu, A cikin jakar unaiza suka saka Madubin da tsohuwa Tamira ta basu kyauta, ba su bar cikin ɗakin ba saida Angel ta fayyace masu komai dangane da tattaunawarsu da Salsabeel.Abu ɗayane bata fada masu ba komawar Danish Giant bata so su sani gudun kada su tayar da hankulansu. Haƙiƙa tsohuwa tamira ta kafa tarihi acikin zukatansu, A yau ta amsa sunanta na mahaifiyar su wadda ta raine su, basu ta6a yarda cewa tana sonsu ba sai yau da Angel ta labarta masu komai dangane da taimakon da ta yi masu, sun ji ƙaunarta sosai har suna fatan Allah ya haɗa su da ita kafin subar kurkukun, sai da su ka kammala shirya komai tsaf na kayansu, Angel ta kalle su ɗaya bayan ɗaya Azeeza tuni bacci ya ɗauke ta abayan Gabriel, hankalinta kwance sai sharar bacci ta ke Yi, Jemimah kuwa Idonta biyu Sai faman baza ido ta ke yi Hannunta na a ruƙe dana Angel. "Me yakamata Mu yi yanzu don ganin An dawo mana da ɗan uwan mu Danish"! Haris ne yai maganar "I'll go and get him back tonight!" da ƙwarin gwiwa Angel ta yi maganar. "Ta yaya hakan zai yiwu? Angel muna jin tsoron wani abu ya same ki, Me zai hana mu tafi gaba ɗayan mu"! batul ce ta yi mata maganar fuskarta da alamun damuwa "Zan bi ki Angel Mu tafi atare"! Gabriel ne Ya yi maganar" girgiza kai ta yi"Bana so wani abu ya samu ɗaya daga Cikin ku, Bazan bari ka bini ba Gabriel ni kaɗa nake so na jefa kaina cikin hatsari Zan roƙi Allah ya tsare ni....." muryarta na ɗan rawa ta ambaci hakan kamar akwai rauni atattare dani, tabbas tana matuƙar fargabar abu biyu, Na farko tafiyar da zata Yi tabar su da jimamin Awani hali take a ciki, Na biyu Haɗuwarta da garkuwar kurkuku, Wani irin azababben tsoron shi ta ke ji tun kafin ta yi tozali da shi. "Genie Pls don't leave me Ki tafi dani..." cikin shessheƙar kuka Jemimah ta yi maganar tana ƙara damƙe hannun Angel dake ruƙe da nata. "Wlh Angel hankalin mu ba'a kwance ya ke ba, Gani mu ke kamar wani abu zai faru da ke idan kika tafi kika barmu" Deeja ce ta yi maganar, ta fahimci kowannan su atsorace ya ke da tafiyarta. "Angel bazamu ta6a yafewa kan mu ba idan har wani abu ya faru dake ta silar taimakon mu da ki ke ƙoƙarin Yi," Javed ne yai maganar, Tuni zafafan hawaye sun wanke fuskokin kowannan su, La66anta sai kerma su ke yi sam ta kasa buɗe baki ta yi masu magana sai binsu ta ke yi da ido, Zuciyarta ba ƙaramin karaya ta yi ba, Ita kanta tana ji a jikinta cewa wannan karan zaiyi wuya ta dawo cikin su ba tare da wani mummunan abu ya faru da ita ba. "Idan har muka ji kin daɗe baki dawo ba, Zamu biyo ki ne"! Hibba ce tai maganar hawaye kwance saman kuncinta Daƙyar Angel Ta iya tattara natsuwarta tare da cewa"Ku daina sanyawa ranku cewa wani abu zai faru dani, idan ma ya faru dani to ku sani ƙaddarata ce wadda ban isa in sauyata ba, Ni da Allah na dogara wani mutun ko Aljan ɗaya daga cikinsu bai isa ya cutar dani ba face da izninsa, ƴan uwana addu'arku kawai nake buƙata akan Allah ya bani Sa'a akan abunda zan je nema......." Sautin shessheƙar kukansu ne ya gauraye Ɗakin tsohuwa. Muryarta adisashe tace"Tunkafin ma na tafi kun fara kuka? Meyasa? Dan Allah ku daina kamar fa kuna discouraging ɗina ne, Nafi so inga kuna ƙarfafa mini gwiwa, ganin hawayenku da nake yi ba ƙaramin raunata mini zuciya ya ke yi ba. "Ba zamu iya jurewa rashinki atare damu ba Angel, wlh muna ƙaunarki fiye da yarda muke son kanmu, bamu son wani abu ya same ki, saboda mu kike ƙoƙarin jefa kan ki ga halaka taya ba zamu yi kuka ba? Angel ke uwace agare mu, Kin fiye mana iyayenmu da su ka yi watsi damu, Dan Allah Angel karki bari mu rasa ki" Sosai suka sanya mata kuka Itama ta fashe masu da matsanancin kuka mai cin rai tamkar ana zare ranta Cikin muryar kuka take magana "Shiga prison Ya zamar mun dole, Idan har ban je ba rayuwar mu tana a cikin haɗari, sannan Alƙawari ne na ɗauka Dole na cika shi ku daina raunata mun zuciyata kada kusa Na gaza......" Kasa ƙarasa maganar ta yi saboda raɗaɗin da ta ke ji a cikin zuciyarta. Tsawon lokaci suna kallon kallo a tsakanin su kafin ta tsagaita da yin kukan tace da batul"Ga amanar jemimah, Ki rungume mun ita a ƙirjin ki har sai ta yi bacci, da zarar na dawo zan kar6i abuna" cikin sanyin murya batul ta amsa mata da cewa In sha Allah zan bata kyakkyawar kulawa har ki dawo Angel, murmushin yaƙe ta ƙaƙaro kan fuskarta tare da kallon su Parveen da ke atsaitsaye tace"Zan tafi ba za ku rungume ni a jikin ku ba"? Jin haka yasa da sauri suka matso kusa da ita, Ɗaya bayan ɗaya suka dinga rungumeta a ƙirjin su, kamar karsu sake ta, a ƙarshe Ta Soma tafiya tana ja da baya tana kallon su idanuwansu akanta, Jiki amace ta juya tare da buɗe ƙofar ɗakin tsohuwa tamira, Da gudun gaske Cikin duhu ta nufi sashen toilet ɗinsu tana faɗowa Hasken sauran fitilun dake a cikin toilets Ya haskaka idanuwanta, buɗe ƙofar toilet ɗin ta yi tare da shigewa Ciki. Yatsun hannunta na kerma ta sanya jamlock ta datse ƙofa don kar su yi gigin cewa zasu bi bayanta, A jikin ƙofar ta jingina bayanta sosai ta fashe da kuka gudun kada su ji sautin kukanta yasa ta toshe bakinta da tafin hannunta, tsawon mintuna goma shabiyar tana sharar ƙwalla kamar ruwan hawayenta zasu ƙare sai da tayi mai isarta kafin ta soma tafiya tana tunkarar Tagar da zata dura, har zata gifta tukunyar fulawar nan ta ɗan dakata da yin tafiya kafin a hankali ta kalli inda ta ke a jingine jikin bango, duk da halin da take aciki na fargaba sai da tayi mamakin ganin an maida tukunyar a mazauninta na asali, shiyasa ɗazu tsohuwa Zafreen bata samu damar ganin ƙofar ba saboda an toshe ta, ajiyar zuciya ta sauke tare da lumshe idunuwanta daga bisani ware su sosai akan furen Danish da ganyayyakin shi su ka bubbuɗe gwanin ban sha'awa, Kyakkyawar fuskarshi ta ke imagining acikin idanuwanta, aranta kuwa tana ayyana koya Zata Ganshi a yanzu daya koma Giant? Da wannan tunanin Angel Ta ƙarasa gaban glass window ɗin Ta janyo bokitin Ta haye sama A hankali ta 6a66ako glass ɗin tare da curo shi ta dire shi ƙasa kafin ta daddage ta haura Saman tagar bakinta ɗauke da Bismillah. Zuƙunna tayi a jikin bangon da ta faɗo, wani irin Sanyi ne ya mamaye sassan Jikinta, Ga tsoro daya mamaye zuciyarta, Biji biji take ƙarewa doguwar hanyar kallo, duhu sosai babu haske sai dai da alamun haske a ƙarshen hanyar Inda Babban filin nan ya ke. miƙewa Tayi tsare tare da Sanya hannayenta Biyu ta ruƙo duguwar sumar kanta tare da nannaɗeta ta jefar da ita saman gadon Bayanta, tunawa da addu'oin da ta karanta a jiya da tayi fitar nan yasa a yanzu ma ta soma ambaton su acikin zuciyarta, A yayin da take tafiya tana nufar cikin kurkukun........ *Boss Bature✍️ Mu haɗu Monday Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game neman ƙarin Bayani Ya tuntu6i Layina na whatsapp 08103884440 banda Kira just message😊* _~*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*~_ *KURKUKUN ƘADDARA* _The Prisoners 2🔥💫_ *Daga alƙalamin Hafsat Bature* ~Middle step~ _A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._ Bayin Allah su Batul zullumi da fargabar Halin da Angel zata shiga Ya hana su runtsa a daren ranar, A ɗakin tsohuwa Tamira su ka zazzauna saman floor, zuciyarsu na harbawa da faɗuwar gaba, Sun yi shiru kowa da a bun da ya ke saƙawa acikin ranshi. Deeja ce tai ƙoƙarin tunasar dasu akan su yi mata addu’a. Su ka amsa mata da toh, nan fa kowan nan su ya soma karanto addu’o’in da Angel ta koya ma su. Dare ya nutsa sosai Azeeza tuni ta koma bacci, a saman ƙirjin Gabriel ta kwantar da kanta, Hannun shi na dafe da bayanta kamar zai mai da ta cikin sa. Jemimah tana a kwance saman cinyoyin Batul ta ƙi yin bacci, ba yadda ba su yi da ita ba akan ta runtse idon ta ta yi bacci amma ta kafe akan sai Genie ɗinta ta dawo, a ƙarshe ma da su ka matsa mata sai ta sanya masu kuka, Tsananin tausayinta ne ya kama su, Haris yace ku bita a hankalin ni banga laifin ta ba, saboda ita yarinya ce ta saba kwana rungume da Angel dole taji ba daɗi, Rarrashin ta ya kama ta mu yi, Amsa mashi su ka yi da toh, atare su ka haɗu suna rarrashin jemimah daƙyar su ka shawo kanta. Parveen sai hammah ta ke yi Ga yunwa ga Bacci, Naufal da ke zaune a gefenta Yace da ita Ki kwanta ki yi bacci mana, Kin ishe ni da hammah” harara ta ɗan jefa mashi tare da cewa”in yi bacci fa ka ce? Sai kace bansan ciwon kaina ba, Ta ya zan iya runtsawa bayan yan uwar mu tana acikin kurkuku....” ta6e la66ansa Yai”Naji daɗi da ki ka yi Hankali” bata tanka mashi ba sai ma ɗaura kanta da ta yi asaman laps ɗinshi. “Batul mu tashi mu bi Genie mu ɗauko ta” Muryar Jemimah ce ta yi maganar Fuskar ta ta yi sumtum saboda kukan da tasha, Lallashinta Batul ta yi” Ki yi haƙuri kin ji, In sha Allah zata dawo Cikin Mu, Badajimawa ba,” Zumbura ba ki ta ɗanyi “Toh idan ta dawo zamu gudu ko”? gaba ɗaya hankalinsu Haris ya dawo kanta Murmushi Batul ta sakar mata”Eh mana da zarar ta dawo zamu gudu mubar kurkuku....” tunkan ta kai ƙarshen maganar Jemimah ta katse ta da cewa”Zamu koma gidan daddyn Genie Ko? In da zamu sakata mu wala mu yi rayuwar mu babu takura Allah yasa genie ɗin mu ta dawo da wuri na ƙosa muje inga gidan daddyn ta” farin cikin da su ka gani akan fuskar jemimah a yayin da ta ke yin maganar yai matuƙar karya masu Zuciya, Har sai da suka ji hawaye sun cika idanuwansu, cikin rauni na murya Deeja tace da ita “Jemimah Pray for Her! Tana buƙatar addu’ar mu, mu dage da yi mata addu’a har sai ta dawo Cikin mu” jinjina kai jemimah ta yi tare da cewa”tom zan mata addu’a” ta ambaci hakan tare da lumshe idanuwanta, acikin zuciyarta tana ambaton Ya Allah ka dawo min da Genie ɗita in dai kana son farin ciki na....” “Gabriel Ka tada azeeza ta tashi Mu haɗu mu duka wurin yi mata addu’a ba yadda za’ae muna acikin tashin hankalin nan ita tana bacci, ko dai jemimah da ta ke ƙarama a cikin mu ta kasa runtsawa balle ita” Rubina ce ta yi maganar, Girgiza mata kai Gabriel yai alamar Bazai tayar da ita ba “I’m sorry to say I can’t wake her I don’t want to worry her, Just Let her sleep.” ɗaure fuska Rubina ta yi jin a bun da yace, ita haushinta yadda suka tashi hankalin su akan Angel amma ita Azeeza ta lafe jikin shi Hankalin ta kwance ta ke sharar bacci. “Akwai matsala fa! Dare Yana ƙara nutsawa babu alamun Angel zata dawo” Sarah ce ta yi maganar tana daga zaune Ta jingina bayanta jikin bango, Ta saki dogayen ƙafafuwanta ƙasa. “Duka yaushe ta tafi da har za ki fara tunanin akwai matsala! Pls mu yi mata fatan Alkhairi, Ni gajan haƙuri ke bana so” acewar Haris. To jama’a abu fa kamar wasa A ƙalla Angel ta ɗauki tsawon awanni babu ita babu alamarta, Idanuwansu sun kaɗa sunyi jawur dasu ga bacci ga yunwa ga zullumin rashin ta atare da su, sun dage sai addu’a Su ke Yi mata, Ba zato ba tsammani Hasken Ɗakin su ya gauraye ko’ina, ta jikin ƙofar ɗakin tsohuwa da bata ƙarasa datsewa ba su ka hango hasken da ke kurɗaɗowa, Hankalinsu Ba ƙarami tashi yai ba, A kiɗime su ka mimmiƙe tsaye hatta Azeeza da ke bacci sai da ta farka tana faman murza idanuwanta da yatsun hannayenta. kallon kallo suka shiga jefawa junansu fuskokinsu ɗauke da matsananciya damuwa “Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un;’ shine kalmar da ta fara fitowa abakunansu Deeja, Yayin da su ke a tsaitsaye cirko cirko, Bakomai ne ya tayar masu da hankali ba face ganin Safiya ta yi ba tare da Angel ta dawo ba. Nan ta ke ransu ya basu cewar wani abu ya faru da ƴar uwarsu................. Shine meke Faruwane ata 6angaren Angel!? Ai tun lokacin data watsa da gudu ta nufi Cikin kurkuku, Sautin kururuwa Mai ƙaraji da gurnani ya cika kunnuwanta, ga wani azababben San yi da ya addabe ta, kamar jaura ta gifta Cikin duhu ta ke gudu Adai dai lokacin da ta ɗaura ƙafarta saman ground floor ɗin nan Inda ke kewaye da dogayen benaye Ba zato Ba tsammani idanuwanta su ka sauka akan ƙafafuwan Tsohuwa Zafreen Lamarin yai matuƙar gigitar da ita, sam Ba ta yi tsammanin Zata ci karo da wani abu ba ita kawai ta sanyawa ranta cewa Danish ne kaɗai mutumin da zata haɗu da shi. Mummunar faɗuwa gabanta yai, ƙirjinta ya hau bugu da ƙarfi da ƙarfi A firgice ta ɗago da idonta akan tsohuwa zafreen da ke a ruƙe da sanda, Kasancewar Filin Yana da Fitilu masu haske can saman silin ya gauraye ko’ina, daga ƙasa har sama shigar Jajayen kaya ne a jikinta kamar kullum Fuskarta na asanye da takuntumi. “Ya Allah saida nayi addu’a kafin in fito but why na fara Cin karo da mummunar tsohuwar nan Ina lillahi.....” acikin zuciyarta ta ambaci hakan, Kafin ta yi wani yunƙuri tsohuwa Zafreen ta soma tunkarota sautin takalmanta ƙwas ƙwas har cikin dodon kunnan Angel, Duk ta ku ɗaya idan ta yi sai gaban Angel Ya faɗi, tauraruwa mai wutsiya ganin ki ba alkhairi ba. Ko da ta ƙaraso gabanta, Bata tanka mata ba, Sai bin ta da tayi da wani matsiyacin kallo irin na marasa imani, Shuɗayen idanuwanta sun Ciza launinsu. “Ban yi mamakin Ganin ki ba Unaisah! Ina ji arai na ba yau ba ne rana ta farko da kika fara ƙetare Iyakar Ki, Taurin kan ki da kafiyar ki da kuma rashin tsoron ki su ne suka ƙarfafa maki gwiwar shigowa Cikin prison! Ko a tarihi ba a ta6a samun prisoner ɗin da ya ta6a ƙetare Iyakar shi ba sai Akan Ki”! Magana ta ke yi muryarta na fita da sauti mai amo. yawu Angel ta haɗiya, tuni tasha Jinin jikinta, Ido ya raina fata sam ta kasa magana, Zufa sai tsastsafo mata ta ke yi kan fuskarta har ɗiɗɗiga ta ke a ƙasa. “Ko za ki Iya faɗa min menene Ya fito da ke? Kuma Ta yaya akai Kika tsaga bangon ɗakin ku kika fito”? Muryar Angel na rawa ta soma magana”Tsautsayi ne da ƙaddara, dan Allah kada ki cutar dani, Zan koma inda na fito, Kawai Inason ganin ɗan uwana Danish ne shiyasa na fito neman shi.....” kasa ƙarasa maganar ta yi sakamakon sautin Dariyar tsohuwa zafreen da ya tari numfashinta. Tsagaitawa ta yi da yin dariyar, ta soma matsawa tana ƙara kusanta kanta da Angel, A tsananin tsoroce Angel ta ke Ja da baya tana girgiza mata kai “Tun jiya dana shigo ɗakin ku Raina ya bani cewar Wani abun ku ke shiryawa kuma ke ce jagora a cikin tafiyar, Saboda prisoners basu da wayan da zasu Iya ta6uka wani abu, Unaisah ke ce ƙwarin gwiwar su, Babban kuskuran da ki ka aikata shi ne ƙetare Iyakarki! Hakan Ya sa6awa dokar Kurkuku! Na yi imanin babu mai Iya ƙwatarki daga hannu na! Saina rushe duk wani sashe na Jikin Ki da ke da ƙarfi zuwa mai rauni......” Zazzare ido Angel ta yi tamkar ƙwayar zata faɗo ƙasa Jikinta sai kerma ya ke yi. “Kin jama kan ki bala’i da masifa! Not only u! Hatta Ƴan uwan ki da Ki ka baro ɗaki, suna cikin masifa, Zanje gare su Bayan na gama da ke, duk saina tarwatsa farin Cikin da ku ke da shi” Muryarta a kausashe ta ke furta maganar. Hawayen da su ka taru a cikin idonta ne suka soma gangarowa saman kuncinta da wani irin rauni na murya ta furta”duk horon da za ki yi mani kada ki haɗa da ƴan uwana, Ni ce mai laifi don haka Ni za ki hukunta” Fuskar Tsohuwa Zafreen a murtuke ta jinjina kai tare da cewa “Umarni ki ke Bani? In yi abunda kike so”? A ruɗe Angel ta girgiza kai ba tare da ta iya furta mata komai ba. “Zan jaraba Ki inga idan zaki Iya ceton Kanki, Nasan baki ta6a shaƙar ƙamshin mutuwa ba amma yau zansa ki shaƙeta sosai, waɗannan Idanuwan naki launin ruwan toka yau zansa su koma launin Ja, Hawayen da ke fito wa ta cikinsu zansa su janza launi zuwa na Jini, La66an ki da su ka saba gaya wa Mutane magana Ayau ɗin nan zan canza masu kamannin.....” Hankalin Angel idan yai dubu to ya tashi tarasa gane inda kalaman tsohuwa Zafreen suka dosa. Ja da baya tsohuwa zafreen ta soma Yi yayin da ta ke sakin Shu’umin Murmushin nan nata na tantiran Ƴan duniya waɗanda su ka ga jiya su ka ga yau Juyawa Baya ta yi tare da nuna ma Angel Third floor da sandar hannunta “Ɗan Uwan ki da ki ke nema Yana a hawa Na Uku, Za ki Iya zuwa gare shi, Fatan Nasara” Kalmar ƙarshe da ta furta mata kafin Ta buga sandar hannunta ƙasa, Nan ta ke hayaki Mai kamar an watsa tiya gas Ya cika idanuwan Angel, bata Iya ganin komai amma taji aranta cewa tsohuwa Zafreen ta 6ace daga wurin da ta ke a tsaye, a hanzarce ta kamo sunan Allah taci gaba da ambaton duk wata addu’a da tazo bakinta, Cikin ƙankanin lokaci ƙurar ta washe Idanuwan ta suka dawo dai dai. A lokacin ta riga ta yanke shawarar komawa ɗakin su gurin ƴan uwanta saboda gudun kada tsohuwa zafreen ta cutar mata dasu kamar yarda ta furta mata cewa zata je gare su, A hautsine Ta juya da niyar tabi hanyar da ta 6ullo don ta koma ɗakin su, Rass gaban yai mugun faɗuwa ganin babu corridor ɗin kwata kwata kamar ba’a ta6a yinta ba, Yawu ta haɗiya zuciyarta na harbawa da sauri da sauri tamkar zata faso ƙirjin ta. A fujajen ta mayar da dubanta ga dogayen benayen da tsohuwa Zafreen ta faɗa mata cewa ɗan uwanta na anan A hankali ta ke tafiya tana tunkarar benan Yayin da ta ke cigaba da karanta addu’o’in neman tsari a cikin bakinta, firgita ta yi sakamakon Jin sautin shessheƙar kukan Su Azeeza a cikin kunnanta, ta ko’ina sautin kukansu ne kamar zasu zautar da ita, Tunawa da barazanar da aka yi mata acan lokaci na farko data ta6a shigowa prison yasa ta yardarwa kanta cewa ba kukan su bane Anayi ne don a tsoratar da ita, hakan yasa ta samu ƙwarin gwiwa, Watsawa ta yi da gudu ta Haura saman benan Har ta yi tsakiyarshi Taji ya soma motsawa Matakalarshi ta dinga komar da ita baya kamar dai yadda ya faru a jiya, Gudu ta dinga yi tana haurawa, wata uwar zufa ta wanke fuskarta, daƙyar ta samu ta haye saman Second floor. Numfashi taja tare da fetsar dashi, sai faman yin haki ta ke yi, Tsawon mintuna takwas kafin taci gaba da tafiya tana bin hanyar, wani abu daya ƙara rikitar da ita, Ginin wurin ya dinga canza mata hanyar da take bi, Sai ta yi nisa taga an dawo da ita Baya, hakan ba ƙaramin gigitar da ita yayi ba. Tarasa ina zata dosa, Tamance ma hanyar da zata bi ta isar da ita hawa na Uku, tana Cikin yin tafiyar kamar zautacciya ita kanta batasan inda ta ke jefa ƙafafuwanta ba, Cikin rashin sa’a ta faɗo cikin wani ɗaki. Idanuwanta basu sauka a ko’ina ba sai akan wasu tsoffin mata da ke agaban manyan tukwanan girki, An ɗaura su saman murhu Wuta sai Ci ta ke, Hannuwansu ruƙe da ludayi Suna Juya naman da ke a cikin Tukunyar girkinsu, Gabanta ne ya faɗi ganin Naman mutun yatsun hannun da ta gani ne cikin romar miyarsu ya tabbata mata da cewa Naman mutunne su ke yi. farfe sun shi. Basu lura da ita ba sai da ta daddage ta kwatsa ƙara Mai sautin gaske silar hakan Ya janyo hankulansu ga kallonta, zaro ido waje ta yi ganin sun ganta, a kiɗime ta manne ma bango ɗakin, jikinta sae kerma ya ke yi Tamkar a mafar ki ta ke kallon su. Halittarsu gwanin ban tsoro Munanan gaske, ga Uban tamoji tamojin akan fatar fuskokin su, kamar jijiyoyin jikin bishiya ƴan rigunan da ke sanye a jikin su launin Ja Kamar yar shara ta maza da su ke sanyawa, Ga uban gashi a hammatocinsu sai ɗoyi suke Yi. a ƙalla sun kai su Shida, uban fason da ke a tafin ƙafafuwan su kamar Kwanannar Fura da ta bushe ta tsastsage. Kamar mahaukata haka suka fashe da dariya mai sautin gaske Muryoyinsu ne suka Cika mata kannuwanta. “Laah ga Unaiserh Ta kawo mana ziyara, yau zata sha farfesun Ƴan Ci ki, Zonan Unaisah Yarinyar mu, Zo ki sha roman nama” La66anta na kerma ta furta”Bazanci ba, Ni ba wurin ku nazo ba, Dan Allah Ku ƙyale ni In tafi....” Tun kan ta ƙarasa maganar ɗa ya daga Cikin tsoffin ta ɗebo farfesun a cikin ludayi hada Yatsun hannun mutun, tunkaro Angel ta yi tare da miƙa mata Ludayi” Kar6i nan ƴata ki sha Roman Farfesun Mutun akwai daɗi” Tashin zuciya ne ya farma mata, a matuƙar firgice ta juya tana ƙoƙarin buɗe ƙofar ɗakin don ta gudu, sai dai kash ƙofar ta ƙi buɗuwa. Fashewa ta yi da matsanancin ku ka tamkar ranta zai fita, da hannu ta dinga Bugun ƙofar kamar zata 6alle ta ko motsi ƙofar ba ta yi ba har sai da tsoffin nan suka cimmata, Ta ƙarfi Suka zaunar da ita tare da rurruƙe mata hannayenta da ƙafafuwanta ta yadda ba za ta Iya ƙwatar kanta ba. Tsohuwar da ke a ruƙe da Ludayin ce ta zuƙunna agabanta tare da tsoma hannayenta masu zaƙo zaƙon akaifa ta ɗebo Ƴan hanjin Cikin sai tiri suke Yi, runtse ido Angel ta yi sosai ta guntse bakinta zucuyarta na tashi kamar zata yi hauka, Bata ta6a ganin masifa ido da ido ba sai yau da Allah ya haɗa ta da tsoffin nan, Duk yadda tazo ta kufce masu abun ya faskara kamar zata haɗiyi zuciya ta mutu, Ta ƙarfi suka 6are bakinta har saida gefe ya dinga fitar da jini, baiwar Allah taji raɗaɗin azaba, duk ta ciccije la66anta da tsiya su ka dunga tura mata ƴan hanjin abakinta, don dole ta dinga haɗiyarshi da zafinshi harshenta duk ya sale haka la66anta ma sun yi suntum. Kamar zautacciya haka tsoffin nan su ka maida ta, Sai da su ka gama azabartar da ita kafin suka saketa Anan ƙasa ta shiga kwarara amai suna kallonta suna dariya, kaf saida ta amayar da ƴan hanjin da su ka bata, wani azababben ciwon kai ya farmata, Ga jiri da ta ke gani acikin idanuwanta “Lami ba ta ƙoshi da farfesun ba, A ƙaro mata wani” maganar su taji a cikin kunnanta, a galabai ce ta miƙe jiki ba ƙwari ta dinga bugun ƙofar ɗakin har sai da ta samu daƙyar ta buɗe ta, gudu ta ke yi jini na wanke rigar Jikinta saboda bakinta da suka sanya ƙarfi wurin 6are shi gefe ya tsage bleeding ya ke kamar jinin jikinta zai ƙare. Baiwar Allah ga zazza6i mai zafi daya rufar mata, Jikinta sai kakarwa ya ke yi, ta gama fita hayyacinta, Neman hanyar da zata koma cikin ƴan uwanta ta ke yi saboda ta riga da ta sare da kurkukun, mutuwa ka ɗai ta ke gani acikin idanuwanta gashi ba ta son ta mutu ba tare da ta yi bankwana da ƴan uwanta ba. Tsabar raɗaɗin da bakin ta ke yi mata ne ya jaza mata rauni da rashin kuzari a jikinta Ƙaffuwanta suka harɗe Gaba ɗaya ta kife saman floor, kanta ya daki ƙasa sosai, runtse idanuwanta ta yi yayin da hawaye ke cigaba da wanke fuskarta miryarta babu sauti take ambaton sunan ƴan uwanta tana neman taimakon su akan su zo su taimake ta, kada ta mutu ba tare da sun gana da junan su ba, Babu alamun hankali atattare da ita, sai sambatu ta ke yi ita kaɗai, Addu’o’in da ta ke ƙokarin yi yanzu sun kufce mata...... Sautin tafiya ta soma Ji kamar motsi motsi saman jikinta, a daddafe ta miƙe tana faman yin nishi, Ras taji gabanta Ya faɗi ganin wasu Girgizo kwafta kwafta a kewaye da ita, Tashin hankalin da ta shiga ne yasa ta fasa ƙara tare da yunƙurawa ta miƙe da gudun gaske ta miƙi hanya tana gudu tana waiwayon su gaba ɗaya sumar kanta mai tarin yawa ta rufe mata idanuwanta, Cikin rashin sa’a Ta 6urma cikin wani ɗaki tare da Jan ƙofa ta datse, ba tare da ta ankara da inda ta faɗo ba, Jikinta sai kerma ya ke Yi. “Barka da zuwa Ɗakin Fiɗa, Ga dukkan Alamu mun samu wata sabuwar ma’aikaciyar” Muryar matashin saurayi taji acikin kunnanta, Tun kafin ta juya ta kalle su Jikinta ya hau tsuma, A furgice ta waiwaya tare da sanya hannu ta nannaɗe sumar kanta da ta rufe mata idanuwanta, Inna lillahi wa’inna ilaihirraji’un bakomai ne yasa ta ambaton hakan ba face Matasan ƴan matan da ta gani kwance saman gadaje kalar na marasa lafiya, zindir babu kaya a jikin su hada masu Ɗauke da juna Biyu, gwanin ban tausayi, Giants ne tsaitsaye akansu Hannayensu ruƙe da kayan theater suna acikin shigarsu ta baƙaƙen Kaya. “Ƴar uwa dan Allah ki taimake ni, ki fitar dani daga wurin nan kada su kashe ni” waro ido sosai Angel ta yi akan matar da ta yi mata magana, Ita ce mai ɗauke da juna biyu Daga ganin cikinta tsoho ne Ya shiga wata na tara. Sun tu6e mata kaya tsiraicinsu duk abayyane, Wannan wata irin masifa ce? Hasbunallahu wa’ni e mal wakeel Lahaula wala ƙuwata Illa Billah, Allahumma ajirni fil musibati wa aklif ni khairan min ha,’ adabarbarce Angel ta ke ambaton hakan. Matar sai kuka take yi tana rokonta akan ta taimake ta ko dan saboda yaron da ke a cikinta, rushewa Angel ta yi da kuka ba tare da ta Iya furta magana ba. Ɗaya daga Cikin Giant ɗin dake a ɗakin tiyatar ne Ya tunkarota Hannun shi ruƙe da wuƙa, Tunkan yai magana ta fahimci abinda ya ke nufi, aiko Jiki na 6ari ta juya tana ƙoƙarin buɗe ƙofar ɗakin don ta gudu, sai dai ina kafin ta yi hakan ta ji Ya damƙi hannunta, ruƙo bana wasa ba, ta ƙarfi ya dinga janta har sai da ya kai ta bakin gadon da matar nan me ciki take kwance. Zura mata wuƙar ya yi a cikin hannunta Ya damƙe shi da nashi hannun, Ta ƙarfi ya soma ƙoƙari sanyata farke cikin matar, Kamar zata zauce saboda tsabar kiɗima har Allah ta dinga roƙo akan ya ɗauki ranta kafin faruwar hakan, Bata ta6a danasanin zuwanta duniya ba sai yau, ta yi fatan ace bata ta6a wanzuwa acikinta ba, ta yi kuka kamar ranta zai fita tayi haukan tayi borin duk abanza, ta ƙarfi giant din nan ya ɗaura hannunta saman cikin matar nan da ke ta kuka tana roƙonta akan ta taimake ta, Saboda rashin imani Ya yi amfani da hannun Angel wurin farke cikinta Kamar an fasa pipe ɗin ruwa Haka jini yadinga tsastsafowa yana wanke fuskar Angel har ta cikin bakinta ya dinga fallasa yana shiga. Hatta jaririn da ke acikinta bai tsiri ba, Biyu suka raba shi da wuƙar, Allah sarki Angel Gani ta yi kamar ita ta aikata kisan kan, Wata irin kururuwa ta saki da iya ƙarfinta na karshe ta bangaje giant ɗin da ke a ruƙe da ta ita Amakance ta dinga Tafiya tana neman Hanyar fita, muryarta da sautin kuka ta ke faɗin. “Nashiga Uku na bani na lalace Inalillah wa’inna ilaihirraji’in Na aikata kisan kai! na yi kisa da hannayena Shikanen Na mutu, nasan Allah ba zai ƙyale ni ba, Na kashe mashi baiwarshi da bata ji ba bata gani ba, Wayyo Allah Na......” Yatsun hannayenta ta ɗaura asaman kanta kamar Aljanna Jinin matar duk ya canza mata kamanninta, duhu ya mamaye idanuwanta da zuciyarta. Giants ɗin da ke Yin aikin fiɗar sai tiƙar dariya su ke Yi, Hankalinsu kwance su ke Cigaba da gudanar da aikin su, yadda su ke farke cikin mutun kamar dabba babu imani ko misƙala Zarratin. Da wata irin raunatacciyar murya ta ke faɗin”Allah ba zai ta6a barin ku ba, Mugaye Azzalumai, Tun agidan duniya za ku fara gir6ar abunda ku ka shuka ƴan iska fasiƙai masu zuciya irin ta kafuran farko, In sha Allah Ni ce Ajalin ku, Sai kun ɗanɗani kuɗar ku sai kun gane ba ku da wayau, kamar yarda kuka sa na zubar da hawaye na in sha Allah kuma za ku zubar da naku hawayen Na jini ma, Yadda ku ka cutar dani ku ka sa na aikata kisa kuma sai an yi maku mafiyin shi......” ƙululun baƙin Cikine ya tokare maƙoshinta, silar hakan yasa ta kasa ƙarasa maganar. Hannayen ta biyu ta sanya saman wuyanta, ta shaƙe shi sosai cikin fitar hayyaci kamar zata kashe kanta, tsabar raɗaɗin da ƙunar da zuciyarta ke yi mata ne yasa ta ke ƙokarin aikata hakan, tana a cikin wannan mawuyacin halin taji An sunkuce ta kamar Ɗiyar roba haka aka ɗauke ta sama, wani gabjejen giant ne yai mata wannan ɗaukar, fucewa yai da ita daga Cikin ɗakin Ɗauke saman kafaɗarshi bai nufi ko’ina da ita ba sai cikin wannan Ƙaton palourn Da taron matsafa su ke gudanar da Bautar su, Wasu dogayen mutane masu sanye da jajayen kaya ko’ina na jikin su arufe ya ke, sun kai su talatin, Agaban dodon tsafin su, Anan Ya sauke ta saman floor, a durƙushe ta kife kasa saboda rashin ƙwarin Jikinta, Hatta numfashinta a hargitse yake fita Jikinta yai zafi rau kamar wadda aka tsomo daga cikin wuta. A lokacin ta kai maƙura bata iya ta6uka komai, motsin hannun mutun ta ji ajikinta, saboda duhun da idanuwanta su ka yi mata yasa ta makance, bata ganin komai, kayan Jikinta suka cire mata gaba ɗaya iya pant ɗin ta su ka bar mata, duk da bata acikin hayyacinta sai da ta shiga matsanancin tashin hankali tunawa da robar ruwan zamzam ɗin da ke a cikin wandonta, rarrafe ta dinga tana laluban suturarta don ta mayar dasu a jikinta sai dai kash bata samu damar ganin inda aka jefa mata kayanta ba. Kukan zuci ta dinga yi, duk wani motsinta akan idon matsafan, ita damuwarta ba akan tsiraicinta da suke kallo ba, robar ruwan Zam zam ce damuwar ta, Ya za ta yi idan ta rasa ta? Ita kaɗai ce damar da suke da ita. Kunnuwata ne suka soma Jiyo mata Sautin muryoyinsu Marasa daɗin ji magana su ke yi da yaren su na matsafa gur6ataccen yare mara daɗin ji, kamar zata haukace, Lallai yau Angel ta shaida tana acikin kurkukun ƙaddara. Ƙwaryoyin ne ruƙe a hannun matsafan masu ɗauke Da zallar Jinin mutane mai ƙarni, Layi suka jera agabanta suka tsaya tare da Kwarara mata Jinin A saman kanta, Wa’iya zubillah Numfashinta ya gauraye da Ƙarnin Jinin Nan ta ke Ta ƙara sa faɗuwa ƙasa tana fitar da numfashi sama sama, basu ƙyale ta ba sai da su ka yi mata wankan tsarki da jinin da ke a hannunsu, wani kalar Jini mai wari da ƙarni daga gani sun tsuma shi sosai, ba ƙaramin zautar da ita su ka yi ba, Kwakwalwarta bazata Iya jure abinda suke yi mata ba, Tana jin motsin hannayensu a jikinta saƙo da lungu su ke cuccuɗata kamar suna yi mata wanka, Sun goga mata najasa a jikinta sun wulaƙanta Martabar jikinta. Allah ne bai nufa Angel zata mutu ba da tuni ta jima da mutuwa lokacinta ne bai yi ba, domin kuwa warin jinin da suka yi mata wanka dashi kaɗai ya isa ya halakar da ɗan adam. Bayan sun kammala yi mata wankan tsarkin nasu na matsafa, Giant ɗin da ya kawota Ya sanya hannu tare da tattareta kamar tsumma Ya ɗauke ta, Ya fito da ita daga Cikin Falon Ya nufi Hawa Na uku da ita, ba tare da sun mayar mata da uniform ɗin ta ba, ko yatsun hannunta bata Iya motsawa, Sautin tafiyar shi ka ɗai ta ke iya ji acikin kunnuwanta, ƙofar Wani ɗaki Ya tura da ƙafarshi Ya shigar da ita, Katafaren bedroom ne na zamani kamar ba’a cikin kurkukun Ya ke ba, Da jinin jikinta da komai Ya jefar da ita saman gadon tare da Juyawa Ya buɗe ƙofar Ya fuce. Kaɗan daga Cikin Abunda ya faru da Angel kenan A cikin Daren ranar, Shin me kuke Tunani zai biyo Baya? Bayan gaba ɗaya Shirinsu Ya tarwatse Babu alamun zata haɗu da Danish, Ko da ta haɗu dashi daƙyar ma Ta iya gane shi saboda bata a cikin hayyacinta babbar matsalar babu ruwan zamzam ɗin da zata Iya shawo kanshi, saboda kwalbar tana a cikin aljihun uniform ɗinta, Ya salam!! Wannan wace irin mummunar ƙaddarar rayuwace!!! Me zai faru da su Azeeza? Me tsohuwa zafreen zata yi masu🥺 *Boss Bature✍️ Mu haɗu Gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08103884440, Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ *KURKUKUN ƘADDARA* _The Prisoners E3🔥💫_ *Daga alƙalamin Hafsat Bature* ~Middle step~ _A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._ A yayin da Angel ta ke A Cikin mawuyacin Hali Idan muka koma 6angaren ƴan uwanta da ke ta tsammanin dawowarta, wani mummunan abu Ya faru dasu!! Tun lokacin da suka fuskanci cewa gari ya waye bata dawo ba, Hankulan su su ka tashi matuƙa, Sun kasa fitowa daga Cikin ɗakin tsohuwa Tamira, gudun kada asirin su Ya tonu, tun da ana kallon duk wani motsinsu. “Yanzu ya zamu Yi? Nifa ina tsoron mu fito daga ɗakin tsohuwa Agan mu dole su zargi wani abu” Deeja ce tai maganar Haris yace”Zaman mu kuma acikin ɗakin yafi komai haɗari, Idan Giant su ka zo kawo mana abinci zasu ga babu mu aɗaki zasu Iya zargin mu” Damuwace ƙarara akan fuskokinsu, Kowa yana tofa albarkacin bakin shi, jemimah da ke a ruke da hannun Batul idanuwanta sun kumbura suntum saboda rashin baccin da bata samu damar yi ba adaren Jiya, jikinta hada zazza6i, “Mun tsaya muna kallon juna, Yakamata Muyi wani abu akai,” eve ce ta yi maganar, fuskokin su duk sun kumbura musamman idanuwanta saboda rashin baccin da ba su yi ba a daren jiya. Numfasawa Batul ta yi tare da cewa”mu fita kawai” ta ambaci hakan tare da ɗaukar jemimah saman Jikinta, ƙofar fita ta nufa ta sanya hannu ta tura ta, Zura ƙafarta ke da wuya Cikin ɗakinsu Ta yi arba da tsohuwa Zafreen A tsaye hannunta ruke da sandarta fuskar nan ɗauke da murmushi, A gigice Batul ta koma Cikin ɗakin Zuciyarta na bugun uku uku, Ganin yadda ta Faɗo masu yasa su ka haɗa ba ki wurin tambayarta”Lafiya? Me yasa ta dawo”? Muryarta na ruwa ta ambaci sunan tsohuwa Zafreen! “Wlh ita ce naganta a cikin ɗakin mu, Wayyo Allah mun shiga uku”! Cikin shessheƙar Kuka ta ƙarasa maganar, Kafin wani ya kuma cewa wani abu tsohuwa zafreen ta faɗo cikin ɗakin da su ke a ciki, A firgice Azeeza ta 6oye bayan Gabriel Jikinta nata kerma, Tashin hankali ne tsantsa akan fuskokinsu. Ɗaya bayan ɗaya ta ke bin su da shu’umin kallon nan nata “Halan Ƴar uwar ku ku ke Jira ta dawo”? Shiru su ka yi babu wanda Ya tanka mata,” Idanuwan su azazzare jin ta gane me su ke jira, hakan ya tabbatar masu da cewa Sun yi aran gama da Angel, Zuciyoyin su ba ƙaramin karaya su ka yi ba. Dama saida ransu ya basu cewar fitar Angel ba alkhairi bace. Tuntsirewa ta yi da dariya mai sautin gaske kamar zata fasa masu kunnuwan su, har saida suka sanya tafin hannayen su wurin toshe kunnuwan su. Lokaci ɗaya ta dakata da yin dariyar tare da ɗaure fuskarta tamau babu annuri ko misƙala zarratin. Wahalallan Yawu su ka haɗiya, Daƙyar Deeja ta samu damar buɗe baki Muryarta na kakarwa ta soma magana”Dan Allah Ki yi haƙuri kada ki cutar mana da ƴar uwar mu, duk abunda ta aikata ba laifinta bane, Laifin mu ne, ta yi ne saboda mu.....” bata ƙarasa maganar ba, Haris yai saurin toshe mata bakinta gudun kada ta tona masu asiri, A hasashen shi Tsohuwa zafreen bata san zancen shirin guduwar su ba, Iya abunda ta sani shine Shigar Angel kurkuku. Muryar jemimah Cikin shessheƙar kuka da 6acin rai tace”Wlh idan ki ka ta6a mini Genie ɗina saina rama mata, bata ma ku komai ba ku ke cutar min.....” a hanzarce Batul ta toshe mata bakinta da hannu, Hankalin su yai matuƙar tashi ganin irin kallon da tsohuwa Zafreen ta ke bin Jemimah. “Dan Allah Ki yi haƙuri da kalaman da ta yi maki, yarinya ce bata son komai ba, kuma bata acikin hayyacin ta,” Atare suka haɗa baki suna bata haƙuri, da buɗar bakin ta sai cewa ta yi”Sorry for ur self! Ku ya cancanta in ba haƙuri saboda kune rayuwar ku ta ke acikin matsala, Ni bani da damuwa” A matuƙar ruɗe suke binta da kallo Cigaba da yin magana ta yi cikin shaƙiyanci da izgilanci”Na jima inason kasancewa tare da ku ban samu damar Yin hakan ba sai yau, Ganin ku da nayi ahaka yayi matuƙar tayar mini da tsohon tsumina, ya za’ai? Zaku bani haɗin kai ko kuwa zan ƙwaci haƙkina ta karfi”? Ta yi tambayar tana ɗage masu gira. Kallon kallo su ka soma jefa ma junan su, sam basu fahimci me ta ke nufi ba. “Au Na manta kufa dabbobine ba ku san komai ba, dole sai ana yi ma ku magana da yaren da zaku iya ganewa,” ta ambaci hakan tare da tunkarar su, bayin Allah sai ja da baya baya suke Ke yi. “Abunda na ke nufi shine zan kwanta da ku In biya buƙatata, idan ku ka bani haɗin kai salin alin zamu rabu lafiya, har ma In bada umarnin akawo maku lafiyayyan abinci, kuma daga rana irin ta yau za’a daina baku ganye kuna Ci” Hankalinta akwance ta ke kora masu Bayani, Cikin shessheƙar kuka Deeja tace”Wlh ba zamu ba ki haɗin kai ba” ta ambaci hakan tare da kallon su Hibba “Kada ku yadda da ita so ta ke ta yi mana irin abunda akayiwa unaiza wanda yaja har ta mutu tabar duniya......” Maganar da Deeja ta yi ne ya fargar dasu, sai yanzu su ka fahimci abunda tsohuwa zafreen ta ke nufi. Ƴan matan cikin su tuni sun fashe da kuka suna roƙonta akan karta ta6a su ta ƙyale su, Baiwar Allah Azeeza ta ƙanƙame Gabriel kamar zasu koma mutun ɗaya. tsananin tausayin kansu ne ya kama su, don basu ga alamun sassauci akan fuskarta ba. Tsawa ta daka masu tare da nuna mazansu da sanadar hannunta”Maza ku fuce ku bani wuri, ba da ku zanyi ba, Matan na ke kwaɗayin kasancewa dasu” kaitsaye ta basu umarnin fita, kamar sakarkaru haka suka haura ƙafafuwan su su ka nufi ƙofar fita, Azeeza da ke ruƙe da Gabriel tuni ya yi wurgi da ita ƙasa saboda basa acikin hayyacin su, ta yi amfani da sihirine wurin basu umarni su fita, fucewar su ke da wuya ƙofar ɗakin ta datse ta yadda ba zasu Iya tsere mata ba. Jikin su sai kerma ya ke yi, da gudu Azeeza ta shige ƙarƙashin gadon tsohuwa tamira, ganin ta yi hakan yasa Batul sauke Jemimah tare da turata ƙarƙashin gadon, tace da azeeza ta rungumeta a jikinta, bayan ta ɗago ta jera da sauran ƴan uwanta suka haɗu suna yi mata magiya akan ta ƙyale su kada ta cutar dasu. Shu’umin murmushi ne ya bayyana akan fuskarta, A hankali ta jefar da sandar hannunta, Dama lafiyar ƙafarta lau, ruƙe sandar da ta ke yi na ado ne. Yatsun hannayenta ta ɗaura kan doguwar rigar da ke a jikinta, Ta zame ta nan take tsiracinta Ya bayyana babu kyan gani jikin ta duk tamoji tamoji kamar jikin faskaran Icce, Undyn da ke a jikinta shara shara ya ke kamar net kana iya ganin komai, uban gashin gabanta gwanin ban ƙyama, Tsayin shi ya kai na ciyawa, wani abun tashin hankalin ma Halittar gabanta sak irin na Namiji ce hakan na nufin tsohuwa zafreen Mata maza ce! Nonuwanta kamar silifas har saman Cikinta. Runtse idanuwansu su ka yi don ba za su Iya jurar kallon tashin hankalin nan ba. Ajikin bango suka ƙanƙame juna kamar zasu tsaga shi su shige ciki saboda tsabar yadda su ka manne mashi. Bayan ta kammala cire doguwar rigar ta jefar da ita ƙasa. “Ku kwantar da hankulan ku Ni ba da ku zan fara ba, Na ƙarƙashin gadon su nafi sha’awa” jin wannan maganar yasa suka bubbuɗe idanuwansu azazzare suke kallonta, Kafin su ka kai idonsu kan gadon tsohuwa Tamira da ƙarfi Deeja ta furta sunan Jemimah da Azeeza, Kafin su yi yunƙuri zuwa gare su tsohuwa zafreen ta cimma ƙarƙashin gadon da hannu Ta janyo ƙafar azeeza da ta jamimah da ƙarfi ta fusgosu waje kawunansu ba ƙaramin buguwa su ka Yi ba, A saman gado ta kwantar dasu Sai faman lashe baki take tana ƙokarin cure masu kayan jikin su. Kukan kura Su Batul su ka yi da gudu gaske suka haye saman gadon, Da iya ƙarfin su na ƙarshe su ke kai mata naushi duk don ta ƙyale masu Ƴan uwansu, sai dai ina ko kaɗan tsohuwa zafreen bata Ji bugun nasu ba, batasan ma su na yi ba don tuni ta tsuduma cikin biyan buƙatarta dasu azeeza, ta raba su da kayan jikin su, sautin kukansu Ya karaɗe Cikin ɗakin wani irin raɗaɗin azaba su ke ji a jikinsu, sai da ta tabbatar ta lala masu rayuwa, tun numfashinsu na fita a wahalce har ta kai ga sun daina motsi, gaban su sharkaf da jini, tukunna ta ƙyalesu ta koma kansu Batul da ke bugun bayanta, wata irin wawura ta kai masu da hannayenta masu faɗi ta dinga Rabasu da kayan jikinsu Zir ta yi masu Mutun biyu ta damƙa acikinsu Sarah da Yasmin Ta kwantar dasu ƙasa ta hau kansu taci gaba da biyan buƙatarta, wa’iya zubullah Tashin hankalin da suka fuskanta Bazai misaltu ba, basu ta6a ganin Masifa ido da ido ba sai yau, Suna ji suna gani ta gama amfani dasu sarah ta koma kan su Rubina ɗaya baya ɗaya ta ke kwantar dasu ƙasa ta hau kansu tana Biyan buƙatarta. sautin koke kokensu da gurnanin tsohuwa zafreen Ya cika kunnuwansu Haris, waɗanda tuni sun jima da haukacewa, Don tun bayan fitar su daga cikin ɗakin ƙofar ta datse, Tunaninsu ya dawo, Sun yi kuka har sun gaji, yayin da su ke jiyo sautin muryoyin su Deeja cikin mawuyacin hali su ke ƙwala masu kira donsu zo su cece rayuwar su sai dai sun gaza yin hakan, basu da wata hanya da zasu iya taimakon su, ji su ke kamar su haɗiyi zuciya su mutu, sun yi fatan ace mafarki ne ba gaske ba. Mutun ɗaya ce ta rage A tsaye Fuskarta jaga jaga da hawaye ta rasa ya za ta yi don tasan itama zata dawo kanta ne idon ta gama dasu Deeja gani ta ke kamar ƴan uwan su sun mutu saboda wasu daga Cikinsu babu numfashi atattare dasu Musamman jemimah da Azeza zaiyi wuya su rayu. zafreen ta gama kashe masu rayuwarsu ta wulakanta su kamar dabbobi. A haukace Batul ta nufi table ɗin da ke ɗauke da Tunkunyar shayin nan ta ɗaɗɗago shi da hannu biyu, tana haki ta nufi tsohuwa zafreen da ta duƙufa asaman su Rubina, ta daddage ta buga mata shi, Ko gizau batayi ba, Komawa ta yi tare da ɗauko kujerar table ɗin ta dawo ta kuma buga mata ita saman kanta, still bata ɗago ba. A fujajan ta koma cikin ɗakin tana neman abunda zata ƙwala mata, Duk ta bi ta haukace sai waige waige ta ke yi fuskarta sharkaf da hawaye, har zata juya ta wutsiyar idonta ta hango Rigar wuƙa da ke a so ke a tsakanin littattafan cikin Book shelves ɗin ɗakin. Tsohuwar ajiye ce wuƙar da tsohuwa Tamira ta ba Danish Kyautarta a lokacin da ya buƙaci yana son datse sumar kan shi, ashe ya maida mata ita shiyasa ko lokacin da Angel ta yi mashi magiya akan ya bata wuƙar Yaƙi bata saboda bata atare da shi, da gudu Batul ta nufi book shelves din ta zura hannu ta ɗauko rigar wukar ta zaro ta Jikinta har salƙi ya ke yi saboda tsabar kaifinta, wuƙar sihiri ce mai haɗarin gaske, Cikin zafin nama ta watsa aguje bata nufi ko’ina ba sai kan Tsohuwa Zafreen a lokacin ta gama da su Rubina juyowar da za ta yi ke da wuya Batul ta daddage ta Luma mata wuƙar Cikin idonta, kafin ta yi wani yunƙurin yin amfani da sihirinta Batul ta ja wuƙar Tun daga kan idonta har zuwa saman wuyanta ta tsartsarga mata Jikinta, Wani irin ƙarfine yazo mata, Dama jinin ta akan akaifa ya ke, Zuciyar ta bushe, Gaba ɗaya tsohuwa zafreen ta gigice saboda azabar zafin da taji na shigar wuƙar, Ta yi ƙoƙarin Buge Batul sai dai Allah bai bata Ikon Yin hakan ba, ba ƙaramin Illah Batul ta yi mata ba, Sai dai duk da haka wani abun mamaki babu ɗigon Jini da ya fito daga idonta, duk inda Batul ta fasa mata da wuƙar kamar ana ɗinke fatar wurin haka ta dinga haɗewa tamkar ba’a ta6a tsaga ta ba. So ta ke ta lalubo sandar hannunta saboda ƙarfin sihirinta yana a jikin sandar, Idan har babu ita Sauran sihirin da ke a jikinta ba lallai Ya iya yi mata tasiri ba, Daƙyar ta samu ta yi wurgi da Batul gefe ɗaya gaba ɗaya ta kife ƙasa kanta ya daku, wuƙar hannunta ta kufce mata, yunƙurawa zafreen ta yi tare da miƙewa tsaye Jikinta na kakarwa ta soma tafiya tana tunkararta, so ta ke kawai ta kashe ta har Lahira, Cikin fitar hayyaci Batul ta miƙe zaune daga kwancen da ta ke a ƙasa, Ja da baya ta dinga Yi har sai da ta ƙurewa bango. Tuni tsohuwa zafreen ta cimmata, tafin ƙafarta ta ɗaura saman Yatsun hannun Batul ta murjesu, tsabar raɗaɗin da Batul ta ji ne yasa ta fashe da matsanancin ku ka na fitar hayyaci, wata irin zufa ta soma tsasstafo mata “Kafin ki kashe Ni, Ni zan fara kashe ki, Dabba kawai, Kin yi kuskure da ki ka soka mini wuƙa A cikin idona, Angaya maki cewa Ni Mutunce da zan mutu farat ɗaya? Tana huci ta yi tambayar, janye tafin ƙafarta tayi daga kan yatsun hannun Batul ta ɗaura ƙafar saman jikinta da ƙarfi ta danna shi tare da murza ƙafar, Jini ne ya soma gangarowa ta cikin bakin batul Nan ta ke Numfashinta ya soma kokawar ɗaukewa..... Ba zato ba tsammani tsohuwa Zafreen Taji an buge mata kanta da ƙarfi gaba ɗaya ta kife ƙasa, ta baya aka shammace ta, A hanzar ce ta ɗago don ta ga wanene, a matuƙar ruɗe ta ke kallon fuskarta, Ba kowa bace face TSOHUWA TAMIRA. “Ban yi mamakin ganin ki ba Dama na jima da zargin cewa ba ki atare damu Tamira!” zafreen ce tayi maganar muryarta akausashe, saboda tsabar 6acin rai facial musles din tsohuwa tamira har kerma su ke yi, Hankalinta yai matuƙar tashi ganin yadda zafreen ta lalata rayuwar Yaran da ta raina gaba ɗaya ta gama da rayuwarsu, ta yi danasanin zuwan da ta yi amakare da duk hakan bata faru ba, idanuwanta sun yi jawur dasu tamkar garwashin wuta, wani irin hu ci ta ke futarwa Yunƙurawa tsohuwa zafreen ta yi tare da miƙewa tsaye, Ido cikin ido su ke kallon juna babu sassauci akan fuskokin kowannan su. “Ni dama ba ki ta6a burgeni ba, Muguwa azzaluma baƙar kafura, Ban ta6a ganin dabba Jahila daƙiƙiya irin ki ba, Wai ke baki da hankali ne? Ke fa mutunce waɗannan yaran da kika lalata rayuwar su mutanene fa ba dabbo bi ba, Laifin me su ka yi maki da har su ka cancanci wannan hukuncin daga gare ki”? Rai amutuƙar 6ace ta jefa mata tambayar. Ɗaure fuska tsohuwa zafreen Ta yi, idanuwanta sun kaɗa jawur dasu, Babu ko alamun imani akan fuskarta Tana magana tana huci kamar mayun waciyar zakanya” Ni kike gayawa magana? Ka da ki manta ke bakowa bace a gidan kurkukun nan face ƙasƙantacciya mai rainon Yara, dole Ki yi mini biyayya saboda ni ke agaba da ke, Nafi ƙarfin ki Tamira nesa ba kusa ba, Idan har kina son ki tsira da ranki to ki gaggauta barin wajen nan tunkafin In yi maki mummunar Ill......”Bata kai ga ƙarasa maganar ba, tsohuwa Tamira ta daka mata tsawa har saida ta furgita, karo na farko kenan da taga Rashin tsoro acikin idon Tamira. Nuna ta ta yi da yatsan hannunta”ko da can baya da na ke girmamaki ba dan ina jin tsoron ki bane sai don Ƙudirin da na ke dashi na son Rushe Baƙin tarihin da kuka kafa, Ajali ne ke kiran ki shiyasa har ki ka yi gigin shigowa cikin ɗakina, A yau inaso in nuna maki ƙarfin ikon da na ke shi wanda na samu awurin rainon yaran da nake yi, Zafreen Yau zaki yaba ma aya zaƙinta, Ko da zan rasa raina ne saina fara ganin bayanki wulaƙantacciya kawai”a fusace ta ambaci hakan idonta akan fuskar zafreen ga dukkan alamu mamaki da al’jabi ne ya hana ta mayarwa Tamira martanin maganarta. bata ta6a tsammanin tsohuwa Tamira zata Iya yada mata magana ba tare da jin shakkarta ba. “Tsautsayi da ƙaddara ne suka jefo waɗannan Watsastsun ƙafafuwan naki cikin ɗaki na, Kin ga babu mai kallon mu bare aji sautin mu, Yau zan huce haushina akan ki....” Tunkan ta ƙarasa maganarta, tsohuwa Zafreen ta 6ace ma ganinta, Hankalin tsohuwa Tamira Ba ƙaramin tashi yai ba, babban abunda ta ke ji ma tsoro kada ace ta bar ɗakin, In kuwa haka ta faru zasu fuskanci azabtarwa domin kuwa za ta je ne ta fallasa su. Jin motsin mutun abayanta yasa ta yi saurin Juyawa, Har saida gabanta Ya ɗan faɗi ganin tsohuwa Zafreen ta bayyana cikin shigar jajayen kayanta hannunta ruƙe da sandarta, ashe 6acewar da ta yi don ta ɗauko sandar hannunta ne ta kuma mayar da suturarta. “Na yi tsammanin kin ji tsoro kin gudu ne”; acewar tsohuwa Tamira Mahaukaciyar dariya zafreen Ta saki tare da cewa”Babu tsoro a cikin zuciyar tsohuwa Zafreen! Tamira kin shiga Uku! Kin tsokanowa kanki Bala’e da masifar da ba za ki Iya jurarsu ba, Zan kashe ki har lahira bayan na gama da ke zan ƙarasa kashe waɗanda basu mutu ba a cikin Yaran can naki, Zan sha Jinin su In ci tsokar naman su” Tana kai ƙarshen maganar ta, ta yi kukan kura tare da Afkawa tsohuwa Tamira, gaba da gabanta Aljani Ya taka wuta, Domin kuwa Zafreen tafi Tamira ƙarfin sihiri, Faɗane ya kaure a tsakanin su kamar dawakai, ba ka iya jin komai sai sautin buge bugen su da gurnaninsu uwa namun dawa, Ƙura ta karaɗe cikin ɗa ki, Kusan atare su ka canza suffofin su, Tsohuwa Zafreen ta rikiɗa ta koma Damusa, Tamira ta koma kura, Ko a namun dawa Damusa ba abokiyar karawar Kura bace, Faɗan nasu Ya canza salo, kamar a filin daga su ka cigaba da kaima junan su Hari duk suka raunata kawunan su. *ANGEL* Tsawon lokaci tana a sume saman Gadon da aka kwantar da ita, fatar jikinta jawur da Jinin da su ka yi mata wanka dashi duk ya daskare mata, zai yi wuya yabar Jikinta, saukar ruwan sanyin da ta ji ajikinta ne ya farkar da ita a firguce ta farka, sai dai ta kasa buɗe idanuwanta saboda nauyin dasu ka yi mata, hatta bakinta Yaƙi buɗuwa la66anta sun kumbura suntum wani irin zogin azaba su ke yi mata. Ba zato ba tsammani kunnuwanta su ka jiyo mata muryar SALSABEEL. “Meyasa ki ka yi gaggawa? Kin manta me na faɗa ma ki? Sai da nace ku yi takatsantsan idan ba haka ba za ku ja ma kan ku ne damu kan mu....” Sam ta ƙasa motsa bakinta, Idanuwanta kaɗai ta iya samun damar buɗe su akan jikin shi, Yana atsaye Cikin shigar Giant ko’ina na jikin shi arufe kamar yarda ta ganshi a shekaran Jiya. Ta yi mamaki sosai saboda a tattaunar da su ka yi da ita ya faɗa mata cewa ba zata sa ke ganin shi ba, sai ga shi Ya dawo yau, hakan ya tabbatar mata da cewa suna acikin haɗari gaba ɗayan su, taja masu bala’e. Rushewa ta yi da matsancin kuka raunin da ke abakinta yaci gaba da fitar da jini Tsananin tausayin ta ne Ya kama shi, ganin yadda suka raunata Jikinta sun gur6ata mata tsaftatacciyar fatarta, tsabar takaici da danasanin gaggawar da ta yi ne yasa ta yin kukan, tana so ta yi ma shi magana sai dai ta kasa saboda sautin muryar ta yaƙi fita ko da tana yin kukan babu sauti. “Ban faɗi hakan don na fama maki ciwon da ke acikin zuciyarki ba, Nasan kina yi ne duk don ki cece rayuwan ƴan uwan ki, don kuma ki cika mana alƙawarin da ki ka ɗaukar mana, sai dai kash gaggawar da ki ka yi ta yi silar jefa rayukan mu cikin haɗari, Zai yi wuya mu tsira sai dai bazan bari Ki rasa ran ki ba, Zan yi maku ƙoƙari Ayau ɗin nan ku fuce daga cikin kurkukun nan kafin Hankalin Matsafan ya dawo kanku, Mun ci sa’a shuwagabannin kurkukun basu aciki, Sauran da suka rage Giant ne masu haɗarin gaske, Ni kaina da na ke da sihiri a jikina bazan Iya ja dasu ba, A yanzu haka da nake Yin magana da ke nayi ƙoƙarin Sarrafa ɗakin Da ke ɗauke da madubin tsafin su shiyasa ba zasu Iya ganin mu ba, Nan da Awa ɗaya Zamu Aiwatar da komai Idan har lokacin nan ya cika kuna acikin kurkukun nan mu dukan mu zamu Mutu bayan azabtarwa da zasu Mana.” Baiwar Allah duk da raɗaɗin da bakinta ke yi mata ahaka ta daure ta cije ta soma Yi mashi magana muryarta araunace daƙyar sautin ma yake fita “Sun cire min uniform ɗina, Ruwan zamzam din Yana a cikin aljihun wandona bansan Ya zanyi ba” cikin ƙunar rai ta ambaci hakan “Zanje na ɗauko maki Uniform ɗin ki, cikin minti ɗaya” Yana ambaton hakan ya 6ace ma ganinta. Yunƙurawa ta yi daƙyar ta miƙe zaune, Ƙarnin Jinin jikinta ya addabi hancinta, bargon da ke shimfiɗe saman gadon ta janyo ta yafa ma jikinta, Zuciyarta acunkushe take da damuwar halin da ƴan uwanta su ke a ciki, Ita ba ta damu da kanta ba, sune damuwarta. Fatanta Allah yasa tsohuwa zafreen bata cutar dasu ba kamar yarda ta faɗa mata. Durowa Cikin ɗakin salsabeel Yayi hannu shi ruƙe da uniform ɗinta, Jar vest ɗinta da wandon ta Ya miƙa mata su, yatsun hannayen ta na kerma ta kar6e su, Agaban shi ta zura kayan bayan ta kammala sanya su ta zaro ƴar ƙaramar robar zamzam daga cikin aljihun wandonta, Idanuwanta acike tab da ƙwala ta kalle shi tare da cewa”Ta ya ya zan Iya ganin Danish har in bashi ruwan zam zam ɗin”? “Bamu da isasshen lokaci, A saman bayana zan goya ki in kai ki inda Ya ke kuma zan taimaka maki mu bashi ruwan, ya kai ƙarshen maganar tare da Juya mata baya ya zuƙunna daga bakin gadon, matsowa ta yi tare da kama bayan shi ta haye, Ya yunƙura Ya miƙe, Daga inda ya ke goye da ita Ya 6ace 6att.... Ba su dura a ko’ina ba sai A wani katafaren Ɗaki mai tsawo da faɗi komai na cikin shi launin Ja ne, hatta dogayen labulayen da ke a kewaye dashi red colour ne. wani irin sanyi ne ke ratsa sassan Jiki acikin ɗaki kamar sanyin A.c, daga gani special room ne na kurkukun ƙaddara, Tsadaddun furniture ɗin da ke a cikin ɗakin kaɗai abun kallo ne. Jin shiru bata motsa daga saman bayan shi ba yasa shi yi mata magana muryarshi cikin raɗa ya furta” Mun ƙaraso, Ki tashi ki ga ɗan uwanki” yanayin yadda ya yi mata maganar ne yasa taji gabanta Faɗuwa shi kanshi Salsabeel ɗin A tsorace Ya ke da abunda zai Biyo baya balle ita kuma da ta ke Ƴar ƙwaruwa wadda bata taka kara ta karya ba. Tsoro ya hana ta ɗago ta kalli inda Danish ɗin Ya ke duk irin kewar shi da ta yi, Sosai ta runtse idanuwanta Hannayenta ƙanƙame da Salsabeel. “Na faɗa maki bamu da isasshen lokaci ki sauka mana” yai maganar tare da zuƙunnawa don ta sauka, Kamar wadda ƙwai ya fashe mawa akai jiki na kerma ta sauko daga saman bayanshi, sai lokacin ta samu damar Ware idanuwanta sosai Tana ƙarewa ɗakin kallo tun daga kan labulayen dake a cikin shi har zuwa kan shimfiɗaɗen Carpet ɗin dake a ƙasa Ga wani ƙayataccen table mai ɗauke da Dinner set, plate ta gani na tangaran mai ɗauke da kayan marmari, ga wani apple da aka datsi saman shi, hada sawun haƙoran mutun, Ga wani glass cup mai ɗauke da wani abu acikinsa ruwane amma launin shi yayi bright red kamar an surkashi da wani abu. Duk fa wannan kalle kalle da ta ke yi ba ta yi tozali da shi ba, saboda ta hana idonta kaiwa gare shi, Har sai da Sabsabeel yai mata gyaran murya tukunna ta soma Juyar da ƙwayar idanuwanta a hankali ta ɗaura su kan katafaren king sized bed ɗin da ke kafe a cikin ɗakin, Gado ne irin na sarakuna launin shi Golden Colour an shimfiɗe shi da lallausan Bedsheet launin Ja, slowly ta sauke idonta akan dogayen ƙafafuwanshi wa’iya zubilla tsabar ruɗu yasa ta dabarbarce saboda ta kasa yadda cewa shine, Halittar Jikin shi gaba ɗaya ta canza, Ya zama jibgegen ƙato, Samun Namiji mai irin ƙirar ƙarfin shi zaiyi wuya, ƙira ce mai matuƙar tsoratarwa, rikitarwa da kuma jan hankali, Ga dukkan alamu bacci ya ke yi a giant ɗin ma bai bar halin shi na yin bacci ba, Dogon wandone Baƙi A jikin shi, Sai Jar t shirt ta matse jikin shi, ta bayyana ainihin surar shi, musamman damtsen hannayen shi tamkar zasu fasa rigar saboda tsabar ƙarfi. Sun canza shi sosai Farar fatar wuyan shi hada zanen tattoo launin baƙi da Ja wanda ya kasance Tambarin kurkukun ƙaddara ne duk wani Giant yana da Zanan a wuyan shi, sun rage mashi tsayin sumar kanshi, Anyi mashi kitson zane guda shida, wutsiyar kitson ta sauka har saman Broad-shoulders ɗin shi, Ya koma kamar ƴan iskan turawan nan, waɗanda tun daga suffarsu zaka shaida cewa, ba bu Ɗigon Imani A zuciyar su. Zafafan hawaye ne su ka wanke fuskarta a yayin da ta ke ƙare mashi kallo, Ta gaza yarda da abunda idanuwanta su ke Nuna mata, Wai Danish ɗinta ne Ya koma haka? Hankalin shi kwance ya ke sharar bacci babu alamun damuwa atattare da shi, duk irin kewar shi da ta yi shi baisan ma da zaman ta ba balle sauran ƴan uwan shi, saboda zalunci na mutanan nan sun rabasu da ɗan uwansu. Cikin shessheƙar Kuka Ta furta Sunan shi”Da..Nish..” walking nervously ta nufi bakin gadon ta zauna daga gefe tana ƙare mashi kallo, Ya yi wani irin haske mai kyan gaske, tsabar kyan fuskarshi tamkar zai kashe mata ido, la66ansa sun yi jawur dasu kamar na Jinjiri, Dogon hancin shi ya tafi tsaye ba lanƙwasa, kwarin idon shi ta zuba ma ido, dogayen eye lashes dinshi masu kyau da tsari. “Don’t waste Our time! Mintuna kaɗan suka rage mana,” Muryar Salsabeel ce ta fargar da ita, Ji ta ke kamar ta faɗa mashi ta rungume shi a jikinta ko ta samu sassauci a cikin zuciyarta. Matsawa kusa da ita sabsabeel yai “Ki buɗe murfin robar, Ni zan hau saman gadon In ruƙe shi gudun kada ya farka ya ham6are ki, naushin giant yana da haɗari sosai Bugu ɗaya su ke Yiwa mutun ya mutu In ba wani iko na Allah ba’ Wannan maganar da ya yi ta ɗaga mata hankali, ta ƙara jin tsoron shi. Yatsun hannunta na kerma ta soma ƙoƙarin buɗe murfin, tana dab da zata Ƙarasa cire shi, Kamar An ce ta kalli fuskarshi taga ƙwayar idon shi na motsi ta saman kwarin idon shi, da ƙarfi ta furta”Ya farka” Sautin miryarta ne ya daki dodon kunnanshi, Aiko kamar an zungure shi Ya ware manyan idanuwanshi launin russet brown akan fuskarta, wani irin ƙwar jini yai mata a furguce Ta miƙe daga gefen gadon Tana ja da baya, idanuwanta azazzare, Salsabeel da ke yunƙurin ruƙe kafaɗun shi don Ya hana shi miƙewa A zafafe Yai wurgi dashi tun daga saman gadon Ya ƙundumo ƙasa Ji ka ke tummm, Hankalin Angel fa ya ƙara tashi ganin yarda ya jefar da babban mutun kamar Salsabeel yadda kasan kallon tamola haka ya jefar dashi wanda a haife salsabeel zai Iya haifarshi, Durowa yai daga saman gadon Yana huci Kamar mayunwacin zaki, breast ɗin shi har motsi su Ke yi, Wani matsiyacin kallo da taga yana binta dashi yasa ta haɗiyi yawu mai zafin gaske, kallon da Danish ke yi mata kamar ma baisan wace ce ita ba, Tunkararta Ya soma yi Yana gurnani har wani jijjiga jikin shi ya ke yi, babban abunda ta ke ji ma tsoro kada Ya rikiɗa Ya canza halitta don ta fahimci abinda ya ke shirin Yi kenan, Juyawa ta yi da gudu tana neman inda zata 6oye kanta don kada ya cimmata, saida ta gama shan wahalar kewaye ɗakin Kwatsam taga Ya bayyana agabanta. Ɗagowa ta yi a tsananin tsorace ta ke kallon shi tana girgiza mashi kai haɗi da marairaice mashi fuska don Yaji tausayin ta amma ina ai ko kallo arziƙi bata ishe shi ba, Muryar Salsabeel ce ta karaɗe kunnuwanta a kausasace ya ke bata Umarnin ta gudu daga gabanshi kada ta bari ya Damƙe ta. kafin ta yi yunƙurin Canza hanya Cikin rashin sa’a ta ji Ya damƙi qugunta Kamar ɗiyar roba Ya ɗaga ta sama Muddin kuwa Ya bugata da kasa sai qugunta Ya 6alle saboda ƙarfin dake gare shi bana Mutun bane na baƙin shaiɗanin aljani ne, Yana ƙoƙari makata Da ƙasa Salsabeel ya cimma shi Gaba ɗaya yai wurgi da ita ƙasa ta kife robar zamzam ɗin da ke a hannunta tuni ta gangara ƙarƙashin table ɗin da ke a ɗakin gashi murfinta ya fara zamewa zai cire saboda buɗeshin da ta fara Yi, ruwan da bai wuce Kur6a ɗaya ba Ya kare idan ya zube shikenan sun rasa damar da su ke da ita. Faɗane ya kaure a tsakanin Salsabeel tsohon ƙashi da Danish garkuwar kurkuku, Yadda Danish Ya ɗaga salsabeel Ya buga shi da kasa ba ƙaramin gigita Angel yai ba, lamarin ya tsoratar da ita babban abunda take jima tsoro kada Ya kashe shi da bugu, da ko ta shiga uku, ƙarfi ba ɗaya ba Danish ya zarce salsabeel Nesa ba kusa ba saboda shi matsayin babban giant ke gare shi masu haɗarin gaske, Salsabeel Kuwa Ko star ɗaya bai da ita a muƙamin Giant, ta inda Allah ya taimake shi ƙwarewar da ya samu A fannin sarrafa tsafi, ba don haka ba da tuni Danish ya jima da karkarya ƙasusuwan jikin shi, Bugun da ya ke yi mashi da ace Lafiyayyan mutun ya yi mashi wanda baida sihiri a jikin shi da tun a bugun farkon, ga6o6in jikin shi zasu daina aiki. Ta rasa ina zata tsoma ranta ta ji daɗi faɗansu ya yi matuƙar ta6a ƙwaƙwalwarta, Ku ka ta dinga yi hannayenta daddafe da kanta, wani irin matsanancin ciwon kai ne ya farmata, muryar Salsabeel taji a raunace ya ke faɗa mata ta ɗauko zam zam ɗin, da sauri ta rarrafa ta nufi table ɗin har ta kusa ƙarasawa Taji an Janyo ƙafarta da ƙarfi Yai wurgi da ita gefe ɗaya har saida kanta ya bugu da bango tsabar raɗadi Yasa nan ta ke ta sume. Sai faman huci ya ke yi yana gurnani, gaba ɗaya ya gama naƙasa ƙwarin gwiwarsu , shi kanshi Salsabeel Yana durƙushe ƙasa kanshi Ya bugu sosai ga6o6in jikinsa sun rauna, akan idon shi Danish Ya jefar da table ɗin da ƙafarshi, Kayan marmarin da ke asaman shi duk su ka tarwatse ƙasa, Ashe yana sane da robar Zam Zam ɗin hannunta, Kafarshi Ya ɗaga da niyar ya ta ke ta don ta fashe, A kiɗime Salsabeel Ya fasa ƙara tare da Miƙewa Yana jan kafarshi Ya nufi Danish. Shu’umin murmushi ne Ya bayyana akan fuskar shi hada juyowa ya kalli Fuskar Salsabeel Ya ɗaga mashi gira muryarshi tamkar ta mashayin giya ya furta”What?” “Kada ka fasa ta na roƙe ka ko dan saboda ƙaunar da ke a tsakanina da kai danish, Nifa ne Ya yan ka, Yau da hannun ka ka ke buguna kamar zaka kashe ni? Sai ka ce baka sanni ba? Laifin me muka aikata maka? Kalli kaga yadda ka Bugi ƴar uwarki Angel kamanta irin ƙaunar da ke atsakaninka da ita”? Ta6e la66ansa yai”who is she”? Tambayar daya jefa mashi kenan Muryar Salsabeel tamkar zai fashe da ku ka Ya ce “Ka kalle ta da kyau yar uwarka ce Angel, Ba ka yi kewarta ba? Idan bazan manta ba lokacin da ka ke rashin lafiya saboda matsalar da idon ka ya samu sunanta ka ke faɗi acikin sambatun ka ko ka manta ne”? Kwa6e fuskarshi yai Alamar bai tuna komai ba. Salsabeel sai Jan hankalin shi ya ke yi da surutu A yayin da ya ke tunkararshi duk don ya samu damar ɗauke robar zamzam ɗin da ya ke Yunƙurin fasawa. “you’re trying to deceive me” Danish Na ambaton hakan Ya dire ƙafarshi saman robar, kukan Kura Salsabeel Yai tare da cakumar Wuyan shi Da iya ƙarfin shi na ƙarshe Ya daddage Ya janye Danish gefe ɗaya, A gaban robar Sabsabeel Ya zuƙunna Yana Kallon Yadda ruwan Cikin ta ya tsiyaye ƙasa, Tsabar takai Ci yasa shi Fashewa da kuka kamar ƙaramin Yaro, ƙululun baƙin ciki ne ya addabi zuciyar shi, Damar da su ke da Ita ta ƙare, zaiyi wuya su tsira. Jikin Salsabeel na tsuma Ya yunƙura tare da miƙewa Ya ɗaura idanuwanshi akan Bayan Danish wanda ke ƙoƙarin Tunkarar Angel don Ya ƙarasa kasheta, A hankali ya ɗaura yatsun hannun shi saman rigar jikin shi ta kakin Giant, For the fast time da yai nufin bayyana ainihin suffar shi, Cire Rigar jikin shi yai tare da jefar da ita ƙasa, Faffaɗan ƙirjine dashi Irin na sadaukan Ya ƙi, 6an6are mask ɗin da ke akan fuskarshi Yai tare da jefar dashi saman rigarshi. Namijin Duniya Kyakkyawan gaske, fatar jikin shi Jawur ta ke, Ya fito a baturen shi, Idan ka kalli fuskar shi ba za ka ta6a yarda cewa shi jinin tsohuwa Tamira ne, saboda ita mummunace tsufa Ya 6oye kyanta. “Na bika ta lalama ka ƙi banin haɗin kai yan zu zan yi maka ta tsiya, Danish ko ni ko kai A yau ɗin nan” Jin miryarshi yasa Danish dakatawa da yin tafiyar, cikin Takun Qasaita Ya waiwayo yana kallon shi, ganin ya tu6e rigarshi yasa ya fahimci shirin faɗa Ya yi, jijjiga jikin shi yai nan ta ke ya rikiɗa ya koma Jibgegen zaki ƙosasshen gaske sai gurnani ya ke yi yana wage bakin shi. Hankalin Salsabeel Yai matuƙar tashi ganin ya rikiɗa, saboda shi sihirin shi bai kai ƙarfin da zai Iya rikiɗa ya canza halitta ba, ganin yadda ya ke tunkaro shi a fusace Yasa shi ja da baya ya soma tunanin me yakamata yayi don Ya dakatar dashi, idan ba haka ba A kashe zai kashe shi har lahira. Waige waige ya dinga yi yana bin ɗakin da kallo har idon shi ya sauka akan Wuƙar yanka kayan marmarin da ke yashe saman floor, Ba zai iya ɗaukarta ba don bai son Ya cutar dashi, Lallashinshi ya soma yi yana faɗin”Am sorry Danish ni ba faɗa zanyi da kai ba, Pls ka saurare ni Danish dan Allah ka canza halittarka zuwa ta mutane ina son yin magana da kai.....” Magiya ya dinga yi mashi amma ɗan tahalikin nan yaƙi sauraron shi, Juyawa yai da gudu ya nufi saman gadon ɗakin Ya daka Uban tsalle Ya haye saman shi tare da sanya hannu ya rarumo bargon dake nannaɗe saman shi, dai dai lokacin da Danish Yai kukan kura Ya daka tsalle da suffar Zaki Zai kai mashi hari Yai saurin Rufe shi Da bargon Ya nannaɗe shi a ciki, Allah ne ya taimake shi Ya bashi ƙarfin da shi kanshi yasan bana shi bane, a saman floor suka faɗo, Sosai Ya matse Danish Acikin bargon, ruƙo bana wasa ba kamar zai kashe shi, tun yana jin sautin gurnanin shi har ta kai ga yai shiru babu motsi alamar ya suma. Tsabar farin Ciki yasa shi sakin dariya yayin da hawaye ke bin fuskarshi, tunawa da lokacin su da ke shirin ƙarewa saura Mintuna 30 ya rage masu kacal, A hanzarce Ya zame bargon da ya lullu6e shi a ciki, har ya koma suffar shi ta mutane a ƙasa ya kwantar dashi, Miƙewa Salsabeel yai da sauri ya nufi robar zam zam ɗin da ya tsiyaye, Ya ɗauko ta a tsakiyar tafin hannun shi ya dawo ya zuƙunna agaban Danish, a hankali ya buɗe mashi ƙaramin bakin shi ya dinga matsar robar ta ƙarfi kamar zaiyi hauka daƙyar ya samu ɗigon Ruwan Ya faɗa bakin shi, Ɗigo ɗaya kacal, Gani ya ke kamar ba zai isa ya dawo hayyacin shi ba, hakan yasa shi cigaba da matsa robar duk don ya samu ruwan ya ƙara ɗigowa a ƙarshe da ya gaji ya jefar da robar ƙasa, ya dafe kanshi da hannu biyu zuciyar shi na harbawa da matsanancin sauri. faɗuwar da gaban shi ke yi ya tabbatar mashi da cewa wani mummunan abu na faru da wani nashi ko dai mahaifiyar shi, ko kuwa yaran da ya ke ƙoƙarin taimakon rayuwar su, Miƙewa yai a zabure Jiki ba ƙwari ya nufi Angel da ke yashe ƙasa tun ɗazu da Danish ya jefar da ita ta sume bata ƙara motsi ba, hannu biyu ya sanya tare da ɗaukar ta, Ya dawo ita gefen Danish Ya kwantar da ita, kafin ya ƙara miƙewa Ya nufi Kayan saman table da Danish Ya watsar dasu ƙasa, A cikinsu ya samu robar ruwa, ya ɗaukota tare da dawo wa gaban su Ya zuƙunna yana faman fitar da huci Shi kanshi a raunace ya ke daurewa kawai ya ke yi duk don ya samu ya ƙarasa taimakon su. A Saman fuskar Angel Ya watsa ruwan a Firgice ta farka haɗi da miƙewa tsaye tana Faman zazzare idanuwanta fuskarnan jawur ta kumbura suntum. “Unaisah” Cikin sanyin murya Salsabeel ya ambaci sunanta ko da ta kalle shi a tsoroce Ta furta”wanene kai”! Ras Ya ji gaban shi ya faɗi, Can kuma sai ya tuna da fuskarshi daya cire, shiyasa bata gane shi ba. “Salsabeel ne” kallon shi ta dinga yi kamar yau ta fara ganin shi, ita kanta ba haka ta yi tsammanin zata ga fuskarshi ba. “Ga ɗan uwan ki nan, Na yi ƙoƙarin ɗiga mashi ruwan zamzam ɗin sau ɗaya abakin shi bansani ba ko zai farka acikin hayyacin shi ko kuwa akasin hakan, Ba zan Iya jiran farfaɗowarshi ba, hankalina ba akwance yake ba, Ina tsoron wani abu ya sami mahaifiyata Don haka zan tafi wurin ƴan uwanki nasan tana atare dasu” Angel na ƙoƙarin buɗe ba ki tace mashi ya tafi da ita kada yabarta anan gudun kada Danish ya farka a matsayin Giant ya kasheta sai dai kash kafin tayi maganar Salsabeel tuni ya 6ace ma ganin ta... A 6angaren Su tsohuwa zafreen kuwa Dambe su ka yi bana wasa ba, Saboda tsabar zalunci sai da ta cire mata kunnuwanta duka biyun ta cinye su, Jini duk ya wanke jikin tsohuwa tamira, duk yadda taso ta ƙwaci kanta ta kasa saboda rashin ƙwarin Jikinta, har sai da zafreen ta kwantar da ita ƙasa ta dinga buga kanta Ga ƙasa tuntuna motsi har ta kai sumewa. Mahaukaciyar dariya zafreen ta saki ganin ta yi nasara akanta, Faɗa da aljani ba riba maganar da zafreen ta furta a yayin da take miƙewa ta nufi wuƙar da batul ta yi amfani wurin yi mata Illah, Jinin da ke a jikin wuƙar ta lashe kafin ta juyo ta dawo kan tsohuwa Tamira, Ta zuƙunna tana Shafa Jikinta da tsinin wuƙar”Na jiye maki baƙin Ciki, domin kuwa ayanzu ɗin nan zar farke Cikin ki, In kwashe ƴan hanjin dake a cikin ki In cinye su, idan kin isa Ki kwaci Kanki, ƙazamar banza har ni za ki kalli idona Ki gaya mini magana kamar bakisan wacece ni ba.....” ta ambaci hakan tana mai sakin murmushi Yunƙurin caka mata wuƙar ta yi ba zato ba tsammani taji an buge kanta da wani abu mai nauyin gaske tamkar dutse kafin ta yi yunƙurin juyawa don taga wanene taji an ƙara buga mata shi akanta, nan ta ke kanta ya juye Ta kife ƙasa,. Batul ce a tsaye Tana haki, Hannunta ruƙe da sandar Zafreen da ta jefar ƙasa, ƙarfin sihirin da ke a jikin sandar ne yasa har ta yi nasarar kwaɗeta da ita, daddagewa tayi da ƙarfi taci gaba da buga mata sandar, Jijiyoyin wuyan ta duk sun furfuto waje saboda tsabar 6acin rai, babu sassauci atattare da ita tun tsohuwa zafreen na motsi har ta kai ga idanuwanta sun Juye, Jefar da sandar Batul ta yi ƙasa tare da ɗaukar wuƙar da zafreen ɗin ta jefar, Saman ruwan cikinta ta haye ta daddage ta dinga luma mata wuƙar Jini yadin ga ambaliya kamar an kunna fanfo harta saman fuskarta, Kacaca tayi mata sai da ta farketa, A ƙarshe dai Baful ta yi nasarar kashe tsohuwa Zafreen ko shura wa ba ta yi ba nan ta ke rai yai halin shi, harta mutu batul bata daina farke jikinta da wuƙar ba, saboda bata acikin hayyacinta, kuka ta ke yi tamkar ana zare ranta. Farfaɗowa tsohuwa Tamira ta yi a hankali ta buɗe idanuwanta da suka ruƙida su ka yi jawur dasu, ta wurga su kan Batul da ke a zaune saman Zafreen tana aikin fiɗa. Muryarta na rawa ta ambaci sunanta”Ba..tul..” Sai lokacin ta jefar da wuƙar hannunta, jiki na rawa ta sauko daga saman jikin zafreen ta rarrafo Zuwa gaban tsohuwa Tamira. Fuskarta jaga jaga da hawaye hada majina, taci gaba da yin kuka tana faɗin”Ta zalunce mu ba mu yi mata laifin komai ba, ta kashe mana ƴan uwan mu ta gama da rayuwar mu.....” Hannun tsohuwa na kerma ta ɗaura shi saman sumar kan Batul da ke a tarwatse daƙyar take iya yi mata magana”Batul babu wasu kalmomi da zan iya yin amfani dasu wurin baku haƙuri akan irin jarabtar rayuwar da kuka fuskanta, Ku yi haƙuri kuyi haƙuri Allah yana atare da ku.......” Da numfashinta na ƙarshe ta ƙarasa maganar nan ta ke rai yai halin shi, A matuƙar kiɗime Batul ke Fuskarta......... *Boss Bature✍️ Mu haɗu Gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08103884440, Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*KURKUKUN ƘADDARA*_ _The Prisoners E4🔥💫_ *Daga alƙalamin Hafsat Bature* ~Middle step~ _A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._ wani sabon kukan ne ta kuma fashewa dashi ga matsanancin ciwon kai da ya takura mata, saboda tsabar kuka shatun jijiyoyin wuyanta sun fito ruɗu ruɗu kamar zasu fasa fatarta, hatta saman fore head ɗinta jijiyoyin ne.... A 6angaren su Haris kuwa da ke a cikin ɗaki, tun suna kuka har sun fidda rai da ƴan uwan su zasu rayu, Tun suna iya jiyo sautin shessheƙar kukansu har ta kai ga yanzu basu Iya jin komai, A bakin ƙofar ɗakin tsohuwa Tamira suka zuzzuƙuna, Zuciyoyin na tafarfasa Gabriel yasha kuka Idanuwanshi har sun ƙafe, Haka zalika Naufal da javed babu sauran mai walwala akan fuskokin su, Mubeen kuwa Dama ba ƙoshin lafiya ce da shi ba tun lokacin da aka dawo dashi kamar mutun mutumi ko magana bai Iya yi, Daƙyar ne yai tsawaicin kwana. A firgice su ka ɗago Da idanuwan su Jin Dirar mutun a Cikin ɗakin su, jiki na kerma suka miƙe suna kallon shi ba su san wanene shi ba, ganin su da Salsabeel ya yi ba ƙaramin karya mashi zuciya su ka yi ba, tausayin su ne ya kama shi, Cikin sanyin murya ya soma yi masu magana. “Ku kwantar da hankalin ku, Ba cutar da ku nazo yi ba, Nima ɗan uwan ku ne nasan ba ku ta6a gani na ba, Sunana Salsabeel Ni ɗa ne ga tsohuwa Tamira”! Duk da basa acikin hayyacin su sai da suka zazzaro idonsu akan fuskarshi. Cikin shessheƙar kuka Haris yace”ƴan..uwan mu suna a cikin ɗakin tsohuwa Tamira, Zafreen Ta kashe mana su, Muna jin sautin kukan su sai dai mun gaza ceton su saboda ta datse ƙofar.....” tun kan ya kai ƙarshen maganar, Salsabeel Ya wuce da wani irin sauri Ya sanya hannu Ya daki Jikin ƙofar Nan ta ke ƙofar Ta buɗe. A fujajen Ya faɗa Cikin Ɗakin Hankalin shi a matuƙar tashe Ya ke binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya, tun daga kan su azeeza dake kwance cikin Jini saman gadon Tamira har izuwa kan su Parveen da ke a sume ƙasa Babu kaya a jikinsu, Ga Uniform ɗin su yashe a kasa da ta Cire masu, Da ƙarfi Ya ambaci kalmar Inna lillahi wa’inna ilaihirraji”un runtse idon shi yai sosai tare da bugun iska da hannun shi daya dunƙule, Tsabar ƙunar da zuciyar shi ke yi mashi zafinta tamkar zai fasa ƙirjin shi, Zafafan hawaye ne su ka soma wanke fuskarshi Kamar ya haɗiyi zuciya ya mutu haka ya ke Ji. “Ya Allah ka ɗauki raina In huta Idan ba haka ba zan kashe kaina ne” Muryar Batul ce ta janyo hankalin shi ga Kallonta, wa’iya zubillah Wani mugun bugu Zuciyar shi ta yi ganin mahaifiyar shi kwance cikin Jini, Kunnuwanta Biyu babu su Ga kuma gawar tsohuwa Zafreen A can gefe ɗaya, tangal tangal yai kamar zai kife ƙasa Da sauri ya tsayar da kan shi Yana faman fitar da huci mai ɗumin gaske, Ba dan Zuciyar Imani ba wlh da ɗaya daga cikinsu baƙin ciki ba zai bari Ya rayu ba. Daga Salsabeel ɗin har su Haris Allah ne bai nufa zuciyar su zata buga ba, Amma tashin hankalin da su ka fuskanta a wannan baƙar ranar baya misaltuwa. Batul sam bata lura da shi ba, Ta zama mahaukaciyar ƙarfi da ya ji kamar ma ta zauce, Agaban gawar mahaifiyarshi ya zuƙunna cikin rauni na murya ya furta”ya za ki yi mini haka mommy na? Meyasa za ki mutu ba tare da mun cimma burin mu ba, why ki ka tafi ki ka barni ni kaɗai a cikin wannan Duniyar mai cike da ruɗani”? Daƙyar ya ke iya furta maganar, cikin rauni na murya yayin da hawaye ke cigaba da yin sintiri saman kuncin sa, tun da ya soma magana Batul ta ɗago da runannun idanuwanta waɗanda suka kaɗa jawur dasu ta ƙura su akan fuskarshi ba ta Iya gane wanene ba saboda batasan shi ba, A halin da ta ke a ciki bata Iya Fahimtar Kalaman shi. “Hada kai Aka kashe min Ƴan uwana ko! Kai ne ka kashe su wlh kaine”! ɗago wa yai tare da kallonta, Kafin yai yunƙurin furta magana, Batul ta daddage ta Haye saman jikinshi tare da dunƙule hannunta tadinga kai mashi bugu ta ko’ina tana faɗin Mugaye azzalumai wlh ba zamu ta6a yafe ma ku ba, Kun cutar da rayuwar mu, kun kashe mana ƴan uwa, wai laifin me muka aikata ma ku ne....? bata ƙarasa maganar ba kuka Yaci ƙarfinta, Rashin sani yafi dare duhu, sam bai ji komai da abunda ta yi mashi saboda hankalin shi ba akanta Ya ke ba, Yana akan gawar mahaifiyar shi, Bawan Allah Ya ji mutuwarta Fiye da tunanin mai tunani, Ya yi danasanin irin rayuwar da su ka ɗaukarwa kansu yanzu gashi ta mutu tana aikata sa6on Allah, Sai dai shi Allah gafurirrahim ne mai rahama mai Jin ƙai, Maganar su ta ƙarshe ya soma tariyo acikin kanshi. “Salsabeel ko bayan ba raina inason yaran nan su ku6uta daga KURKUKUN ƘADDARA! Ka yi min alƙawarin nan, ka taimaka masu ko dan su isar da saƙon mu zuwa ga mutanan duniya, Bana so acigaba da aikata zalunci agidan kurkukun nan Ina mai jin takaici da baƙin Cikin ganin yadda ake tauye wa ƙananun yara haƙƙinsu na rayuwa, basu ji ba basu gani ba, An hana su more rayuwar su ta duniya, Ana kashe masu rayuwa a lalatasu A ƙasƙantar dasu kamar dabbo bi, sannan a kashe su, kuma su mutu a wulaƙance! Ka faɗa min Laifin me suka aikata da su ka cancanci Yin irin wannan rayuwar? Idan har kana so In yi alfahari da kai a matsayin ka na Jini na to ka cika min burina, Bana so Ganin mutuwa ta yasa zuciyarka ta raunata nafi so a lokacin da ka yi tozali da gawata ka ƙara Jin ƙwarin gwiwar aiwatar da umarnin da na baka, idan mutuwa ta risƙe ni a gidan kurkukun nan bana so kabar gangar jikina a gidan kurkukun ƙaddara Ka yi nesa dani kafin ka binne ni.........” lokacin da tsohuwa Tamira ta yi mashi maganar sosai ya fashe mata da kuka yana faɗin zai yi duk abunda take so amma tadaina maganar zata mutu, ya ta ke so ya yi da rayuwar shi? Bashi da kowa a duniyar nan bayan ita, murmushi ta yi tare da ce mashi Kana da Allah sannan bayan shi ga ƴan uwanka nan suma basu da gatan daya wuce Allah da kuma kai, Don haka ka daina tunanin cewa sai da ni zaka Iya aiwatar da komai. Ni dai fatana Ku tarwatsa tarihin kurkukun ƙaddara, Azzaluman shuwagabannin da suka ƙirƙire shi ku tabbatar tun agidan duniya sun ɗanɗani kuɗarsu kafin su koma ga mahaliccin su bana so kubar hukuma ta hukunta su saboda duniyar nan acike take da marasa gaskiya idan kunga ba zasu baku goyan baya ba ku yi amfani da ƙarfin ikon da ku ke dashi wurin yi masu mummunan kisan da sai sun yi danasanin haihuwarsu da uwarsu tayi acikin duniyar nan, Kafin su mutu ku Azabtar dasu ta yadda zasu manta da duk wani jin daɗi da su ka yi a duniya, Idan har ku ka yi min hakan to zan jin daɗi, zan yi kuma alfahari da ku, Bayan ta yi mashi wannan maganar salsabeel yana kuka ya roƙe ta alfarma ɗaya kafin faruwar duk waɗannan abubuwan yace mata yana so ta kar6i musulunci akaro na biyu ta yi imani da Allah, Numfasawa tayi tare da ce mashi”Ba zai yiwu ba saboda Allah ba zai ta6a kar6ar tubanta ba ko da ta musulunci saboda ɗumbin zunubban da ta aikata sun yi muni sosai, Salsabeel ya yi ƙoƙarin fahimtar da ita ta hanyar Yi mata nasiha ya nuna mata cewa shi Allah gafurirrahim ne yana son bayinsa waɗanda su ka aikata zunubi suka gane kuskuran su kuma su ka tuba zuwa gare shi, daƙyar ya samu tsohuwa Tamira ta sake kar6ar shahada maganarsu ta ƙarshe data furta mashi”Zan je wurin Yaran can inaji araina wani abu yana faru a ɗakin su, Kafin na isa wurin su inaso ka yi gaggawar zuwa Ɗakin Madubin sihiri Ka canza ganin su ta yadda ba zasu fahimci abunda ke faruwa ba......wannan itace magana ta ƙarshe da tsohuwa tamira ta furta mashi kafin tabar wurin shi, akan hanyar shi ta zuwa ɗakin madubin sihiri Ya ga duk wani abu da ya faru da Angel kun ji yadda akai har yaje gare ta. Cakumar Batul ya yi da hannun shi tare da janyota ta dawo saman faffaɗan ƙirjin shi, Rungumeta yayi da hannayenshi tamkar zai mayar da ita cikinshi, Hakan da yayi mata ne yasa ta sassauta kukan nata...... Tsoro da fargaban abunda idanuwansu zasu nuna masu ya hana su shiga Cikin ɗakin, Bayin Allah suna atsaitsaye Bakin ƙofar suna sauraron gunjin kukan da Batul ta ke yi. Idan mu ka koma 6angaren Angel kuwa tun bayan tafiyar Salsabeel tana zaune cikin matsanancin tashin hankali, Da fargaban farfaɗowar Danish, Ba zato ba tsammani ta ga yatsun ƙafarshi na motsi, A gigice ta yunkura da niyar ta miƙe Sai dai kash ƙafarta ta ƙi bata haɗin kai, Wani irin tsami ta yi mata, a tsananin tsoroce take ja da baya tana kallon shi jikinta nata 6ari A hankali Ya ware kyawawan idanuwanshi Akan ceilling ɗin ɗakin na tsawon daƙiƙa talatin kafin Ya yunƙura ya miƙe zaune.... Ta wutsiyar idon shi ya ke hango kamar mutun na motsi, hakan yasa shi yin saurin kai idon shi gare ta, unexpected idanuwan shi su ka sauka acikin nata, da wani irin kallo ya ke bin ta da shi, gani ta ke yi kamar bai dawo hayyacin shi ba. Ya kasa tantance wacece ita? Saboda daskararren jinin da ke a jikinta, ta koma mashi kamar aljanna, ranta ne ya bata cewar ko dai ya dawo hayyacin shi? Wata’ƙil saboda munin da ta yi ne yasa bai gane ta ba, Cikin jin shakkar shi muryarta na kerma ta ambaci sunan shi”Da..nish..its me ur Angel” Ware fareren idanuwan shi yai sosai akan fuskarta, jin muryar da ya daɗe yana mararinta, ba zai ta6a mantawa da muryarta ba, A ruɗe ya motsa la66ansa tare da furta sunanta”Angel? Is that you”? Ita kanta batasan ya akai ta iya miƙewa ba, Tsabar farin Ciki da gudu ta nufe shi tana ƙarasawa gaban shi slowly ta zube saman gwiwowinta tare da faɗawa saman faffaɗan ƙirjinshi sosai ta rungume shi tana ku ka, Bai damu da ƙarnin jinin da ke a jikinta ba, sai dai zuciyar shi ta rikice ya shiga ruɗanin ganin canzawar da ta yi, Jikinta duk raunuka ta yi muni kamar ba Angel ɗinsa ba, Tunawa da Ƴan uwanta da kuma ƙurarren lokacin da ke gare su yasa tace mashi”Ka tashi mu tafi Danish ka kaini ɗaki, na bar su Azeeza suna jiran mu” shiru bai motsawa ba saboda ya rasa tunanin shi. Bugun bayan shi ta dinga yi da hannunta Cikin shessheƙar ku ka ta ke faɗa mashi Ya tashi ya ɗauke ta suje ɗaki ƴan uwan su na acikin haɗari, “ daƙyar ta samu Danish Ya miƙe ɗauke da ita saman faffaɗar kafaɗar shi, daga ina ya ke a tsaye Ya 6ace bai dura a ko’ina ba sai A cikin ɗakin su, Tunkan ya sauke ta ta riga zame jikinta, Su Haris da ke a tsaye bakin ƙofar ɗakin tsohuwa, a ruɗe su ke kallon shi Musamman Gabriel yasha ruwan mamakin ganin Danish da idon shi Garas. Muryar Angel na rawa ta soma ambaton sunayen su”Ha..ris..Mubeen..Naufal..Javed..”! akace labarin zuciya a tambayi fuska, Tun kan ma su yi mata bayanin abunda ya faru da gudu ta faɗa cikin ɗakin tsohuwa Tamira da ke a buɗe, Idanuwanta Azazzare take kallon Ƴan uwanta dake kwance ƙasa ba numfashi, Wata irin gigitacciyar ƙara ta saki ta fitar hayyaci wadda tayi silar faɗowar Danish dasu Haris cikin ɗakin sai lokacin su ka ga mummunan abunda tsohuwa zafreen ta aikata ma ƴan uwan su. Silar ƙarar da Angel ta fasa ne yasa Batul raba jikinta daga na salsabeel fuskarta jaga jaga da hawaye ta ɗago idanuwanta, tana yin tozali da Angel da gudu ta nufota tare da faɗawa saman ƙirjin ta suka ƙanƙame juna suna yin kukun zuci, Cikin shessheƙar kuka Batul ta labarta mata duk abunda ya faru bayan tafiyarta, Tasha kuka kamar ba gobe, ta yi fatan ace dukkan su ne suka mutu hada ita, gaba daya shirin su ya tarwatse taya zasu iya barin kurkuku Bayan ƴan uwansu duk sun mutu, Alƙawarin data ɗaukar masu bata samu cika shi ba, Ga danish ɗin ta ci nasarar dawo dashi sai da kash Ta faru ta ƙare, ƙaddara ta riga fata, Cikin raunatacciyar murya ta wanda ya gama sarewa da rayuwar duniya ta furta”Nashiga Uku na bani na lalace! Ya Allah zunubin me muka aikata mu ke fuskantar irin wannan mummunar jarabawar daga gare ka? Idan ba ka son mu, ka ɗauki ran mu mu huta, Mun gaji mun gaji Wayyo Allah na Na rasa Azeeza na rasa jemimah na rasa Deeja da sauran Ƴan uwana, To ni zaman uban me zanyi acikin duniyar nan wlh bazan rayu ba dole in kashe kaina......” Cikin fitar hayyaci ta furta kalaman, kamar mahaukaciya, ta juya da niyar ta je nemo makamin da zata halaka kanta dashi, Cikin zafin Nama Salsabeel Ya damƙi hannunta, tare da juyo da ita ta yadda zata fuskance shi”Meye ribar ki idan kin kashe kan ki? Dama ba sai da na faɗa maki Ba lallaine ku rayu ku dukan ku ba, Yanzu idan kika mutu Kinsan adadin rayukan da za’a cigaba da 6arin jinin su a gidan kurkukun nan? Idan har bamu lallashi zukatan mu ba mun kawo ƙarshen Azzaluman da suka cutar da ƴan uwan mu Duk wani ƙoƙarin mu ya tashi abanza kenan! Ya ku ke so inyi da raina ne? saboda ku na rasa mahaifiyata Ni kaina ashirye nake da in rasa raina in dai akan ku ne, Don haka kada wanda Ya ƙara Yi mana kuka Ya isa haka !! Mutuwa dole ce ko muna so ko bamu so, Kuma mutuwa sauƙi ce agare su saboda rayuwar duniyar bakomai bane acikinta face ruɗani, cike take da ƙalubale iri iri, ni banga amfanin yin kuka don wani ya mutu a cikinmu ba, Saboda Allahn daya halicce su wanda yafi mu sonsu shine ya kar6i abunshi, Sai sunfi jin daɗi fiye da na duniyar nan......’ sosai Salsabeel ya yi masu nasiha har saida yaga sun dawo hayyacin su tukunna Yace dasu babu isasshen lokaci su wuce su tafi, Danish Zai buɗe masu ƙofa, shi zai kula da gawawwakin Ƴan uwansu da suka mutu, Tun shigowar Danish ɗakin kusan suman tsaye yayi, saboda tsabar Kiɗima da ganin halin da ƴan uwan shi su ke aciki, Ya rasa bakin magana, Ya yi matuƙar girgiza da ganin yadda aka wulaƙanta rayuwar Ƴan uwan shi, Hankalin shi yai mugun tashi, Zuciyar shi tamkar zata faso ƙirjin shi ta 6allo saboda tsabar ƙunar da ta ke Yi mashi, Ya fusata Iya fusatuwa, ganin yadda yake huci ƙirjin shi na motsi ga wata narkakkiyar zufa dake wanke mashi fuskarshi, yasa Salsabeel yin saurin dakatar dashi ta hanyar yi mashi magana”Danish ka sassauta fushinka idan ba haka ba giant’s heart ɗin ka zata iya motsawa, pls ka ceci rayuwar su ku gudu daga kurkukun nan, duk wani abu da ya toshe maka kai, Unaisah zata yi maka bayani idan kun fita” daƙyar ya samu Danish ya iya sarrafa fushin sa. Muryar Angel adisashe tace dashi”Ni bazan Iya tafiya in bar gawar su Azeeza acikin wannan ƙazamin ginin ba, inaso na cika masu burin su duk da basa araye zan fitar da gawarsu waje in yaso sai mu binne su a akan hanya, dan Allah ku taimaka min” Tana magana hawaye Na wanke fuskarta. “Unaisah bamu da isasshen lokaci pls ku tafi kawai ku barni dasu zan san inda zan 6oye gawarsu” fashe mashi ta yi da kuka kamar zata haɗiyi zuciyarta, Hankalin Danish gaba ɗaya ya dawo kanta, tsananin tausayinsu duk ya kama shi. “Bazai yiwu ku iya tafi da su ba! Kubar su a wurina zan tsaga ƙasa In binne su” acewar Salsabeel Ataƙaice zan yi bayanin yadda su ka gudu daga KURKUKUN ƘADDARA, Angel ce ta goya Jemimah abayanta tare da sanya Mayafin kayan su da ta ɗauko acikin akwatin su, Gabriel ya goya gawar Azeeza abayanshi ya ɗaureta da mayafi, Naufal ya goya Parveen asaman bayanshi, Haris yaso ya goya Deeja abayanshi sai dai Salsabeel Ya hana shi gudun kada su ja ma kansu wata wahalar, Iya waɗannan kaɗai su ka ɗauka sauran Sun bar su awurin shi bayin Allah badan sun so ba, kusan mutun shida daga Ciki hada Deeja, Sarah, Eve, Yasmin, Rubina da Hibba, Danish ya yi ƙoƙarin yin amfani da sihirin shi wurin farfaɗo dasu, mutun ɗaya kaɗai ta samu damar tashi Hannah, a ƙarshe ya tabbatar masu da cewa Heart attack ne Yai silar mutuwar su, zuciyar su ce ta buga. Ƙululun baƙin Ciki kamar su Zauce, Kafin tafiyar su Mubeen ma ya yanke jiki ya faɗi, Don dole suka haƙura da shi, Lamarin ya yi matuƙar gigitar da su. Salsabeel ya yi masu alƙawarin Zai yi nesa da gawarwakin Ƴan uwan su, tare da ta mahaifiyarshi ba zai bari a wulaƙanta su ba, sun yi kukan rabuwa dashi, har magiya Angel ta dinga yi mashi akan ya zo su tafi atare da shi, amma yace masu ba zai iya bin su ba, su yi haƙuri su tafi idan Allah yasa yana da tsawaicin kwana zasu sake haɗuwa ne duk da yasan abune mai wuya ya rayuwa ko dan saboda 6arnar da suka aikata dole matsafan su azabtar da shi. Rabuwar su ta yi matuƙar ta6a zuciyar kowannan su, a gurguje su ka nufi sashen makewayin su, Tsabar tashin hankali yasa Gabriel mantawa da zancen Ƴar uwar shi Gabriella da ke a cikin kurkuku, tun da ya ga mutuwar ƴan uwan shi prisoners, yasa wa ranshi dangana. Suna shiga Cikin Toilet ɗin, Danish Ya datse ƙofar da sihirin shi, ya Janye tukunyar fulawar daga kan ƙofar, nan ta ke ta bayyana duk irin wahalar da suka sha ta ƙi buɗewa shi Bugu ɗaya yayi mata gaba ɗaya ta 6alle murfin ƙarfen ya dare biyu, Sun yi mamaki da al’ajabi yace da su”Ba zai bi su ba, zai tafi da Akwatin kayan su tare da back pack ɗin su, za su tarar dashi a bakin ƙofar da zasu 6ula idan sun ƙarasa” hankalin su bai kwanta da maganar shi ba, gani su ke yi kamar wani mummunan abun zai faru da su idan baya atare da su, ganin sun toge sunƙi tafiya yasa shi Kwantar masu da hankali, daƙyar ya samu su ka Zuƙunna ƙasa tare da kutsa kai ɗaya bayan ɗaya su ke shiga cikin ƙofar da rarrafe, Bayin Allah ga yunwa ga ƙishin ruwa, ga raɗaɗin da zuciyarsu ke yi masu, Ita kanta hanyar da suka biyo Wata uwar ƙura ga yanar girgizo da ƙwari sai hawan masu jiki su ke yi, Amma saboda rashin kwanciyar hankali yasa basu damu da su ba. Babu mai magana acikinsu saboda ƙunar da ran su ke yi masu, Angel ce tai ƙoƙarin tunasar dasu akan suci gaba da ambaton addu’o’in data koya masu ko sun samu sassaucin a wurin Allah, sun ɗau ki shawararta ahaka suka Dinga tafiya da rarrafe babu ƙaƙƙautawa, idan suka gaji su kan ɗan zauna su huta kafin su dasa da wata tafiyar, A ƙalla sun shafe tsawon awanni Takwas suna rarrafawa ba tare da sun kawo ƙarshen Ƙofar ba, a takure su ke Bayin Allah sun ga rayuwa gwiwowin ƙaffuwan su duk sun gurje sun sage, maƙoshinsu ya bushe ƙamas, tun suna ambaton ƙishir ruwa suke ji har sun gaji sun yi shiru.........”😭 💔Prisoners💔 Sun ci baƙar wahala saboda tsohuwar hanyace da ta yi shekaru aru aru a datse ba tare da an yi amfani da ita ba, Muggan ƙwarin da ke a ciki sai ɗallinsu su ke Yi, amma saboda azabar raɗaɗin da zuciyar su ke yi masu yaci uban raɗaɗin harbin da ƙwarin ke yi masu yasa ba su ji, A makance suke tafiya basu ji basa gani, ga wani azababben zafi daya addabe su, kowan nan su ya haɗa uban gumi burin su kawai su cimma ƙarshen ƙofar, wani ƙarin tashin hankalin fitilun da ke a hannun su Batul hasken su ya fara ƙoƙarin ɗaukewa abunda basu ta6a yi masu ba, sun fuskanci matsanancin tashin hankali har sai da suka fidda rai da fita saboda ganin tsawon awannin da suka shafe ba tare da sun kawo ƙarshen ta ba, tun da suna rarrafawa Hannah ke kuka tana faɗin ƙaiƙayi ta ke ji a jikin ta, duk da halin da su ke aciki hakan bai hana su rarrashin ta ba akan ta yi haƙuri, a lokacin da ba su yi tsammani ba kwatsam! hasken fitilun hannun su Ya ɗauke ɗuff Innalillahi wani irin duhu baƙiƙƙirin ya mamaye idanuwan su, ko fuskokin su basa Iya gani, duk sunbi sun firgice saboda hanyar ta 6ace masu, Sunan Danish su ke ta kira a bakunan su, sun manta cewa baya atare da su. “Danish ka taimaka mana, duhu bamu iya ganin komai, bamu san ya za mu yi ba,” abu biyu ya haɗe masu ga fargabar kar a rutsa su ga kuma Rashin haske gani su ke kamar Aljalinsu ne zai risƙe su awurin, Sautin koke koken su ne ya cika hanyar, sun kasa jurewa tsananin tsoro suke ji, Danish ka yi mana magana pls Ya zamuyi? Kada a rutsa damu, idan ba mafita ne ka faɗa mana.....” Cikin shessheƙar kuka Angel ta yi mashi maganar, kamar zasu yi hauka, sun rasa gane me ke shirin faruwa dasu ne? “Innalillahi wa’inna ilaihirra’un! ya Allah kawo mana ɗauki! Wai ina Danish ɗin ya ke bai jin mu ne ko baya atare damu”! Naufal ne yai maganar, tsabar matsewar da su ka yi yasa wani bai iya motsawa daga inda yake balle har su iya gano inda Danish ɗin ya ke, Yadda kasan kifin gwangwani haka suka cunkushe, Bawan Allah Haris gaba ɗaya baya acikin hayyacin shi, Damuwar shi Deejarshi da ya rasa, Yaji ƙuncin da har abada bazai ta6a goge mashi ba, zuciyarshi ta yi mashi nauyi ga dukkan alamu wani mummunan ciwon ne ke shirin kama shi. “Nifa ina jin tsoro ace Danish Ya canza ra’ayin shi na taimakon mu, zai iya komawa giant”! Gabriel ne yai maganar cikin rauni na murya “Ni da ma na fidda rai da rayuwa, bansawa raina zan bar kurkukun nan araye ba.” Javed ne yai maganar cikin rauni na murya. Suna Cikin Jimamin rashin Jin motsin Danish da fargabar me zai Biyo Baya. Ba zato ba tsammani suka soma hango haske Yana kurɗaɗowa ta Cikin wata ƙofa Yana gauraye inda su ke zazzaune, Tsabar ruɗani Ya sanya su ka Waro idanuwan su waje Kamar ƙwayar Zasu faɗo ƙasa Sun kasa gane hasken menene ke isowa gare su. Ba kowa ba ne abakin Ƙofar fa ce Garkuwar kurkuku shine ya buɗe ƙofar Kogon Bishiyar, Ashe ta inda zasu 6ullo Cikin kogon bishiya ne Mai girman gaske Wurin Ya wawake........ Saboda rashin wadataccen haske basu Iya ganin shi da kyau, Cikin sanyayyiyar murya ya furta masu “You ave reached the door. Today, you will finally leave the prison of destiny, am happy for the first time that you will live a happy life. am ready to be your shield, and I will not let you get hurt by the lows and difficulties of life.” Abun farin Ciki sai dai ba halin nuna shi saboda ba haka suka tsammaci zasu bar kurkukun ba, Ƴan uwan su duk sun mutu, duk irin burin da suka ɗaukarwa kansu na son Yin rayuwar Ƴanci gaba ɗaya ya tashi abanza, Cikin su goma sha takwas mutun goma suka tsira, ahakan ma basu da tabbacin zasu ƙarasa da ran su da lafiyar su ba tare da wani abun ya kuma faruwa da su ba, Kusan atare suka rushe da matsanancin kuka tamkar ana zare rayukansu, Kukan baƙin Ciki da ƙunci da raɗaɗi, Kuka mai matuƙar tsuma zuciya, Tsananin tsauyin su ne ya kama Danish A hankali ya ke ƙare masu kallo, Cikin sanyin murya yace da su Idan nace Ku yi haƙuri Na cuce ku, I can’t stop you from shedding your tears, except to encourage you to cry. It’s the only thing that can ease the pain in your heart.” Fuskar shi ɗauke da matsananciyar damuwa yai maganar, kamar ya ƙara tun zura su aiko suka ƙara sautin kukan nasu, Idanuwansu duk sun kumbura Fuskokinsu sun yi jawur. ganin basu da alamun motsawa yasa shi matsawa tare da ruƙo hannun Angel dake goye da gawar jemimah abayanta, ya turo ta waje a hankali, Tana fitowa ta runtse idanuwanta da ke tsastsafo da ƙwalla. ƙurmin Daji ne mai nau’ikan tsirrai da dabbobi iri-iri. Manya manyan bishiyoyi masu tsayi da faɗi suna da Dogayen rassa, Faɗaɗan Ganyayyakinsu Sun toshe hasken Farin watan da ke a sararin samaniya kaɗan ne ke samun damar haskowa ta tsakankanin Ganyayyakin, yau shekara Uku da watanni rabon da ta tsinci kanta A waje, Ina ga sauran ƴan uwanta Prisoners waɗanda tun da uwar su Ta haife su basu ta6a tozali da haske rana ba, Ɗaya bayan ɗaya Danish ya dinga janyo su kamar basu son fitowa, Kaf ɗin su Ya fiddo da su, kafin Ya maida ƙofar kogon tamkar ba’a ta6a ratsa cikinta ba. Sai faman zazzare idanuwansu suke yi suna bin Dajin da kallo duhu Ya hana su ga komai da kyau, Tsananin tsoro ne ya kamasu, Ga wani irin bala’intaccen san yi kamar Jaura ta gifta, Haƙoran su sai kakarwa su ke yi, muryoyinsu Na rawa suka soma ambaton sunan Danish Suna faɗin sanyi su ke Ji. Da sauri Ya buɗe akwatin kayan su dama shi ne ya ɗauko shi Tare da back pack ɗin Unaiza, Ya zaro masu bargunan su, A saman bayan su Ya lullu6a ma kowannansu bargo, Tunani ya shiga yi ya zaiyi dasu? Ga dukkan alamu sun gaji basu Iya motsawa gashi yana fargabar kada akawo masu hari yasan dole abiyo bayansu. Babu mai ƙoshin lafiya acikinsu kowa takan shi ya ke yi shiyasa ko farin cikin fitowar ba su yi ba duk da irin ɗaukin da suka dinga yi, su fa har yanzu basu yarda cewa sun fito daga kurkukun ƙaddara ba, gani su ke yi kamar har yanzu suna aciki, saboda duhun daya mamaye idanuwansu basu Iya gani dakyau hada ƙarin nauyin da idonsu yai masu sakamakon kukan da suka sha, wasu ma daga cikin su ciwon ido suke fama dashi, Danish ne kaɗai yake Iya ganin su da kyau. Yanke shawarar ya yi da zuciyarshi nan take ya haifar masu da jin matsanancin bacci, Asaman dogayen ciyayin da ke shimfiɗe masu cukowa, Kowan nan su Ya kwanta hada masu goyan cikin su, Ajiyar zuciya ya sauke tare da miƙewa, Ya ɗauki bargo ɗaya daga Cikin wanda Ya lullu6a masu Kamar walƙiya ya 6ace Bai dura a ko’ina ba Sai acikin kogon dutse mai girman gaske, da sihirin shi ya kawar da duk wani abun cutarwa Ya gyara wurin tsaf babu ko ƙura balle aje ga batun halittun da ke rayuwa a cikinshi, Bayan ya tabbatar da babu abun cutarwa Ya shimfiɗa bargon dake a hannun shi, Kafin Ya juya tare da 6acewa ya dawo wurin da yabarsu kakkwance suna bacci, Cikin mintuna Biyar Yai aikin da acikin awa biyu mutun zai iya yin shi, Bai da banbanci da Jinni, kamar walƙiya ya dinga ɗaukarsu ɗaya bayan ɗaya yana kaisu saman shimfidar da yayi masu a cikin kogon dutse bai bar kowa ba, Bayan ya kammala kwashe su ya ɗauke masu akwatin kayansu da jakar ya shigo dasu Cikin kogon ya ajiye shi. Komawa yai cikin dajin Ya haɗo itace dayawa ya shiga dasu ruƙe a hannun shi Cikin kogon dutsen, Ya jera su a ƙasa nesa da inda su Angel su ke akwance, Ya tsinto duwatsu guda Biyu ya gurzasu jikin juna nan take wuta takama Ya cinna ta a jikin itace sosai Wutar ta ruru, a ƙalla ya sauke ajiyar zuciya yafi sau a ƙirga, ya hada uban gumi shi kaɗai, jiki bai saba da wahala ba, fuskarshi sai naso ta ke yi kamar an watsa mashi ruwa, Ya jima zuƙunne abakin wutar Yayin da idanuwanshi ke akan ƴan uwanshi dake lullu6e cikin bargo suna bacci, wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarshi kamar an kora ruwan san yi, haƙika yayi danasanin duk wani abu da ya faru dasu, Ya ji ƙunci sosai A cikin ran shi, miƙewa ya yi a hankali ya ke tafiya yana tunkararsu a gaban shimfiɗar su Ya zuƙunna tare da miƙa yatsun hannayenshi Ya ruƙo bakin bargon dake lullu6e dasu Ya yaye shi, Hasken wutar da ke cini ne Ya haskaka mashi fuskokinsu, Idanuwanshi na akan Marasa ran cikin su, idan ka kalle su a yadda suke kwance baka ta6a cewa gawawwaki ne, Tuni idanuwanshi sun kaɗa jawur, Zuciyarshi ta ƙara karaya tsananin tausayin rayuwar ƴan uwanshi ne ya kama shi, Ya rasa ya akai duk waɗannan abubun su ka faru ba tare da sanin shi ba? Shin me ya faru da su bayan An ɗauke shi daga Cikin su? tambayoyi ya shiga jefa ma kanshi. Ataƙaice Daren Ranar Danish bai runtsa ba, Kwana yai a zaune yana gadin su. *MIDDLE STEP THE PRISONERS BOOK TWO🔥💫* *BIRNIN ABUJA🏙* *Boss Bature✍️ Mu haɗu Gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08103884440, Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*KURKUKUN ƘADDARA*_ _The Prisoners E5🔥💫_ *Daga alƙalamin Hafsat Bature* ~Middle step~ _A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._ *ANEELERH* Kwance ta ke asaman katafaren gadon ta da ke acikin haɗaɗɗen bedroom ɗinta da ke a sabon gidan su na Abuja mallakin Uncle ɗan Iya ɗaya daga Cikin ƙannan Abie ɗinta mazaunin garin Abuja, Attajirin mai kuɗi ne mai yiwa ƴan siyasa hidima, Tun bayan da Abie ya samu ƙarin matsayi a wurin aikin shi aka yi mashi transfer zuwa ministry of finance da ke anan Abuja, a ƙalla yau watan su bakwai da barin jihar jos, ba ƙaramin canjin rayuwa su ka samu ba a gidan ɗan Iya, mutunne mai son jama’a ga iya mu’amala da kyautatawa mutane, kusan halin shi ɗaya da matar shi Aishatu wadda ake da Aunty Ummi. “Aunty Aneelerh! Auntyna! Where are u? i’m back” can cikin bacci ta dinga jin ana ƙwala mata kira, Sautin muryar matashiyar budurwa. Nauyin bacci ya hana ta buɗe idanuwanta sai ma ƙara ƙudundune kanta da ta ke yi acikin lallausar bargonta, faɗowa cikin ɗakin ta yi Tabarakallahu Zankaɗeɗiyar budurwa jawur da ita, Jikinta na sanye da egyptian gown launin shuɗi, Ta yi rolling veil akanta, Light make up ne akan fuskarta daga ganinta ba ƙaramar wayayyi bace a jin farko, Takalman ƙafarta high hills ne launi ɗaya da Mayafinta white colour, hannunta na dama na asanya da Tsadadden agogo silver colour. Ƙamshin turaren Jikin ta mai matuƙar sanyaya zuciya, wayar da ke a ruƙe a hannunta ƙirar i phone 15 pro ce. Agogon bangon da ke a ɗakin ta kalla ƙarfe 9 Na safe, Da sauri ta wurga ƙwayar idanuwanta kan Aneelerh dake kwance saman gado, girgiza kai ta ɗanyi fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi tace”Auntyna kenan bakya gajiya da bacci, sam kin canza mini ba kamar yarda na sanki ba, Gaskiya zanyi magana da Daddy ya hanzarta sama maki aiki ki fara Ni bana son inga mutun yana zaman kashe buje” da zolaya ta yi maganar a yayin da take ƙarasa shigewa Cikin bedroom ɗin, Cikin sanɗa take tafiya tana tunkarar A.c remote da ke ajiye saman bedside drawer, ɗaukar shi ta yi saboda mugunta ta ƙure mata sanyin A.c, Jikin Aneelerh tuni ya fara kakarwa Sosai ta ke ƙara nannaɗe kanta Cikin bargo, Dariya sosai *FATIMA ZAHRA* ta sa ki a yayin da ta ke kallonta, Kasa jurewa Aneelerh saboda sanyin ya addabe ta, A gigice ta sanya hannu ta yaye bargon ta jefar dashi kafin ta yi yunƙurin buɗe ido da sauri Zahra ta rage sanyin a.c ta ajiye remove ɗin saman drawer, ta ruƙe qugu tana binta da kallo. Sleeping dress ne a jikinta Riga da wando Milk colour, Gashin kanta a hargitse, Tunkan ta buɗe ido ta soma surfa masifa tana faɗin”junaid bana hana ka ƙara min sanyin a.c ba? Saboda ka raina min wayau ko?wlh idan ka bari na damƙi hannun ka sai ka gane ba ka da wayau, Sullu6iyo kawai......” Bata ƙarasa maganar ba ta soma Jin sautin dariyar Zahra, hakan yasa ta yi saurin ware idanuwanta tare da wurga su kan fuskarta. Gwalo ta yi mata tare da ɗaga mata gira tace”Ba junaid bane yayar shi ce mai irin halin shi, “ Harara Aneelerh ta shiga watsa mata kamar ƙwayar idon zata faɗo kasa. Zahra tana dariya tace”Iya hararar ne kawai idan mutun ya isa ya sanya hannu ya dake ni, kai da ka zo baƙunta gidan mutane ka ishe su da baccin lalaci.....” bata samu damar ƙarasa maganarta ba, Aneelerh ta rarumi pillow a zafafe da duro daga saman gadonta, zaro ido zahra ta yi kafin ta juya da gudu ta nufi ƙofa cikin rashin sa’a ƙafarta ta jirkice ta fasa ƙara zata kife ƙasa da sauri Aneelerh ta janyota zuwa jikinta, sosai ta ƙanƙameta sai faman sauke ajiyar zuciya ta ke yi ta firgita sosai. “Rasa kunya 6eran tanka, Yanzu ga ki a hannuna, mai ƙwatarki yau sai Allah” Kokoyi su ka soma Yi kamar ƙananun yara, Zahra sai ƙwalawa Umminta kira ta ke yi tana faɗin tazo ta cece ta daga hannun Aunty aneelerh zata kashe mata ƴarta, Aneeleh na dariya tace”Nima ai ina da uwar sai in kirata tazo taga idon mara kunya” ta ambaci hakan tare da ƙwalawa Maminta kira. Sun shaƙe junansu sai nishi su ke yi gyalen Zahta tuni ya jima da zamewa saman tiles, gashin kanta baƙi wulik anyi mata kitson kalaba ya sauko har kafaɗarta. “Aunty Aneelerh Am sorry wlh na miƙa wuya, zan maki biyayya na tufa bazan ƙara ba” Azabar zafin da taji ne yasa ta furta mata hakan donta ƙyale ta. Sakinta Aneelerh ta yi don itama ta gaji da kokawar Sai haki ta ke yi, A nan ƙasa suka zauna saman floor suna kallon juna. “Ɗauko mun ruwa mai sanyi in sha” harara zahra ta ɗan jefa mata”Baki da hannu ne”? Zaro ido Aneelerh ta yi tare da cewa”bugun da nayi maki bai ishe ki ba” Jin haka yasa zahra yin saurin miƙewa hannunta ɗaya dafe da qugunta, Binta da kallo Aneelerh tayi fuskarta ɗauke da murmushi fucewa tayi daga Cikin ɗakin, after some minutes ta dawo hannunta ɗauke da glass ɗin ruwa me sanyi, ta miƙa ma Aneelerh hannu tasa ta kar6a tare da kafa ruwan abakinta Kur6a uku tayi mashi ya ƙare, Janye shi tayi daga bakinta tadan kalli zahra da ke tsaye tana gatsina mata hanci. “Ki gama yi mini rashin kunyar ina nan ina jiran ki, in dai ni ce za ki zo roƙona in faɗa maki ƙiyamil lailin da za ki yi don ki mallaki Zuciyar matashin saurayin nan da ki ka ƙwallafa rai akan shi, meye ma sunan shi? tai tambayar tana kallon Zahra, Dariya ta saki tare da kai hannu ta kar6i glass cup din hannun aneelerh, Cikin kwarkwasa ta Juya ta nufi ƙofar fita daga ɗakin tana faɗin”Heart beat of Obinna” Murmushi Aneelerh tasaki tare da cewa”Ehem shi nake nufi, zakiyi bayani ne” bayan fitar zahra miƙewa Aneelerh ta yi tare da juyawa har ta kusa shiga toilet Muryar zahra ta katse ta”Bafa tafiya nayi ba, taimakon nan dai da aka saba aunty Aneelerh, “ Juyawa aneelerh ta yi tare da kallonta, Fuskarta ɗauke da murmushi. Harara ta jefa mata”ƴar wahala wanka zan shiga idan na fito zamu tattauna” Zahra tace”idan ma shekara za ki yi zan zauna in jira ki” ta6e mata baki Aneelerh ta yi a yayin da ta ke shigewa cikin toilet taja ƙofa ta datse. Daga gefen gadonta Zahra ta zauna tana jiran fitowarta, almost 15 mins Aneelerh ta buɗe ƙofar toilet ta fito jikinta sanye da rigar wanka fara ƙyal, ganin yadda zahra ta tsare ta da ido yasa ta murguɗa mata baki “Tubarkallah” Dariya Zahra ta sa ki kafin ta tsagaita da yin dariyar tace”Masha Allah Iyayen mu sun Iya haihuwa” girgiza kai Aneelerh ta ɗanyi”Allah ya shiryeki Zahra, Yanzu dai ta shi ki fuce zan sanya sutura, Ki jira Ni a palour “ maƙe mata kafaɗa zarah tayi”Nifa ba ƙaramar yarinya bace da zaki kore ni, Menene aciki don kin sanya kaya agabana, sai kace wani gardin ƙato Nima fa macace kamar ke komai ki ke dashi ina da.....” Kafin ta ƙarasa maganar Aneelerh ta nufeta da gudu Zarah ta bar Cikin ɗakin tana dariya. Kaitsaye ta nufi Cikin Hadadden palourn gidan mai girman gaske. Tun kan ta ƙarasa ta hango mami da ummi zaune saman sofa suna fira, kowaccen su na sanye da atampha riga da zane ba ƙaramin kyau su ka yi ba. “Gani nan tafe” kamar daga sama suka ji miryarta. Atare suka ɗago suna kallonta, mami tace”yaushe kika dawo gidan”? “Ban jima da shigowa ba, Na shiga ɗakin Aunty Aneelerh ne, Na same ta kwance Tana bacci,” Tai maganar a yayin da ta ke zama saman sofa mai mazaunin mutun ɗaya. “Nasan kin kwaso gajiya, Tun asuba sai yanzu aka kammala aikin decoration ɗin, Kin ci abinci kuwa”? cikin Kulawa mami ta yi mata maganar, Fuskarta ɗauke da murmushi tace”mun aikatu Mami, Uban aiki kamar zamu shekara muna Yi, kinsan hidima idan akace maki ta Hamshaƙan attajiran masu kuɗine komai dagaske ake yin shi basu ƙaramar harka, Mami zanso Kije Gidan nan zaki sha mamaki wlh, Haɗaɗɗiyar Daular arziƙi ce....” tun kan Zahra ta rufe baki Ummi tace”Ae Obie estate Aljannar Duniya ce Mai zaman kanta, Idan fa ki ka shiga gidan Sai ki rasa gane Awace ƙasa kike, tsabar kayan alatun da ke a cikinsa, Yasin in mutun mai ƙaramin Imani na rayuwa acikin tuni zai daina Sallah.....” Dariya mami ta saki Yayin da take sauraron su, daga uwar har ɗiyar gwanaye ne wurin Iya bada Labari. “Aunty duk yadda zan kwatanta maki Haɗuwar Kayan alatun dake acikin Estate ɗinsu Ba zaki Fahimta ba, Gani da ido yafi abaka Labari, Obinna family duniyace mai zaman Kanta, Ranar dana ta6a zura ƙafa ta cikin gidan wlh Sai da gabana ya faɗi, nace Anya ko Mutane suna tunanin duniya? Yo abu kamar baza a mutu ba, wannan ae sai mutun ya manta cewa da tur6aya aka halicce shi” Dariya sosai Mami ta ke yi tana kallon Aunty Ummi da ke kora mata jawabi, Zahra ta ɗaura da cewa”Ni wlh Naso Daddy ya sama mun Ko aikatau ne agidan su, tun ranar da naji Salary din masu aikin gidan da dollar ake biyan su, Ci da sha da suturarsu duka A kyauta ake yi masu, ai duk wanda Ya haɗa alaƙa Da ɗan familyn Obinna kakar shi ta yanke saƙa, Shi da talauci sun raba Jaha....” in serious matter za’a ta ke magana, Ummi taci gaba da cewa”Shiyasa naso mahaifin ki ya kutsa ki cikin danginsu tun da dama ɗan bangar siyasa ne, Ni ko wannan Yaron ne *DR JAZZ* kisamu ki aure shi, ko mun samu muma mu dangawali arziƙi” ta ƙarasa maganar tana dariya, tur6une fuska zahra tayi Jin abunda Ummi tace”haba ummi, dr Jazz fa meye haka, Ni da na ke harin bugun zuciyar Family ɗin gaba ɗaya, Taya zaki haɗa ni da yaron da har yau ba’asan waye ubanshi ba acikin family ɗin” da mamaki akan fuskar Mami tace”kamar ya ba’asan Ubanshi ba”? Zahra tace”ɗaya daga Cikin ma’aikatan gidan su ce tazo dashi aikatau, Matar ma farar fata ce, ba ki ga yaron ba kyakkyawa ga son mutane, ni bazan Iya auran mara asali ba, Ta ya Ummi zatai min fatan auranshi? Ga gwarazan samari a family din kyawawan gaske masu kama da kakansu Obinna....” tana magana tana turo baki. Ummi tace”Saboda nasan baza ki Iya samun wanda kike so ba, Haukan banza ki ke yi a kan shi, ke kin sani Ruwa ba sa’an kwando bane, Babban Goro sai magogin ƙarfe, Wutsiyar raƙumi tayi nesa da ƙasa, In banda haɗama irin ta zahra taya zaki nace wa mutumin da yafi ƙarfin ki nesa ba kusa ba? Shiyasa nace ƙwara Dr Jazz ɗin shine dai dai da ke,” ɗaure fuska Zahra tayi jin abunda Umminta take faɗi, ta haɗe rai sosai, Muryarta a ƙule tace”Mami kinga ni ko? Ita fa mahaifiyata ce amma bata min fatan naci ka burina, Kullum sai dai tayi discouraging ɗina, meyasa ta ke yi min haka ne”? a bun ka ga me saurin kuka tuni idonta sun ciko tab da ƙwalla. Fuskar mami ɗauke da matashin murmushi ta soma magana a tsanake”kwantar da hankalin ki zahra, Ai duk kyan takalmi ƙafa ce ke taka shi, kuma idan Allah ya ƙaddara cewa shi Yaron wanda kikeso Mijin ki ne duk min muƙamin shi duk mun izzar shi da kyanshi wlh da kanshi zai nemo ki a duk inda ki ke, Ai shi so bashi a matsayin mutun, mai kuɗi ko talaka Zahra kuma ta haɗa komai da duk wani ɗa namiji zaiso zama da ita a matsayin matarshi,...” Tunda mamin Aneelerh ta soma magana zahra ta washe baki tana zabga uban murmushi kamar wadda akayiwa albishir da gidan Aljanna, Tsabar murna batasan sa’adda ta sauko daga saman sofa ɗin da ta ke zaune ba, ta dawo ƙasa saman carpet, Ta kafe mami ido tana kallonta kamar wadda ta samu Tashar Bolly wood, Hakan ba ƙaramin dariya yaso ba Ummi ba, Ganin yadda zarah ta ke sakin murmushi jin ana yabanta. “Mami ni ba ina kushe Zahra bane, Just bana so ta ƙwallafa rai akan abunda ita kanta tasan bazata ta6a mallakarshi ba, Yakamata ta runƙa tuna matsayinta, Mahaifinta fa ɗan bangar siyasa ne ba wani shege ba, Ta ya ya ta ke tunanin zata Mallakin Hamshaƙin mutun kamar *OWAIS SHARAFUDEEN OBINNA*!? Bazan iya lissafi ma matan da su ka yi hauka akanshi ba, Daga cikin hada Ɗiyar Chancellor na ƙasar Germany bayan ita akwai Ƴar sarkin saudi arab, Ga ɗiyar shugaban ƙasar America.....” Lamarin ya ɗaure wa mami kai, Baki asake ta ke kallon Ummi sai da ta kai ƙarshen maganar tukunna tace”Ni ko zanso In ga wanene wannan Namijin hurul ainin, Farin Jini sai kace ɗan gwal yo wannan koda lu’u lu’u aka ƙera fatar Jikin shi sai haka,” Dariya su ka saki gaba ɗayan su. “Saboda Farin Jinin da Allah ya yi mashi kakan shi Ya toshe duk wata ƙofa da za’a Iya ganin shi, Zaiyi wuya ki samu hoton shi a social media, shahararre ne sosai babu inda ba asan shi ba, Da zarar kin ambaci sunan shi awuri sai an girgiza” Ummi ce ta kora mata jawabi, Al’ajabi Ya kama Mami”Na ƙosa Inji tarihin Family ɗinsu, Najima Ina jin zancensu abakin mutune da kuma labaransu a gidan radio, Nasan fuskokin Ya’yanshi a tv sai dai bansan Komai dangane da su ba” Gyara zama Ummi ta yi”Jinin Nasara shi ne sunan da akeyiwa family ɗinsu laƙabi da shi saboda wadatar Arziƙin da Allah yayi masu, Suna ɗaya daga cikin Most richest family in the world, shahararru ne na bugawa A jarida, shi Obinna da ki ka ji ana faɗi Kakan su ne tsohon ɗan siyasa ne wanda yai gwagwarmaya ya ruƙe muƙamai da dama tun daga ƙasa Nigeria har zuwa ƙasashen waje, Allah ya yi su da farin Jini, matan shi biyu a yadda naji labari, amma dukansu basa araye yanzu, shi kaɗai ne ya rage, ƴa’ƴan shi bakwai kaf ɗinsu suna ruƙe da manyan muƙamai, su ke ruƙe da ƙasar nan, Manyan ƴa’ƴan shi ƴan Uku ne sune first born ɗin shi” numsafawa Ummi tayi kafin ta soma zayyana mata sunayen su kamar haka. “SENATE PRESIDENT LATEEF OBINNA, bayan shi akwai CHIEF OF ARMY STAFF SIR MUBARAK OBINNA, cikon Na ukun su shine HIS EXCELLENCY ABDUL RAZAK Obinna Gomnan Jihar Lagos, waɗannan sune yan ukun shi, bayan su akwai ƙannan su maza HIS EXCELLENCY DEEN OBINNA Gomnan Jihar kaduna state, mai bi mashi PRIME MINISTER HATEEM OBINNA Shugaban ƙasar Canada Shi ne ya ke auran Gimbiya mujeedat ƴar Sarkin Dubai.....” Tun da Ummi ta soma bata labarin Mami ta baza kunne tana sauraronta, ga dukkan alamu al’ajabi ya kamata duba da yadda ta saki baki tana kallonta “Bayan Hateem sai mai bi mashi SHARAFUDEEN OBINNA Current president na ƙasar Nigeria, Adalin shugaba hawan shi mulki da wata biyar kacal ba a ƙara jin ɗuriyar Ƴan ta’adda ba” Fuskarta ɗauke da murmushi ta yi maganar”Kada ki ji Ina yabon shi ya cancanta ne, matan shi biyu Uwar gidan shi ɗiyar Sarkin Yarbawan Jihar lagos ce, Ta biyun kuma ƴar gidan Alhaji wada ce, Ƙanwar former Gomna na Jiharku Jos” Murmusawa mami ta yi fuskarta da alamun mamaki tace”Wai Alhaji Ubaid ki ke nufi surukin tajudden? Dama ƙanwarshi ke auran Sharafuddeen”? Dariya ummi tayi”haba dai kada ki ce min ba ki da masaniya,” watsa hannu mami tayi”taya za’ae in sani? Ni da ba shisshige masu na ke yi ba, In banda ma abun ki ae bani da alaƙa dasu da ya wuce ƙawancen Benazir da Aneelerh, Makaranta ce ta haɗa kuma Yanzu sun rabu, amma duk da haka Na yi mamaki,” Ummi tace”Auran su shekara goma sha ɗaya kenan A lissafi na, kada ki yi tunanin ina sanya masu ido ne, Kinsan in mutun nada Arziƙi da ɗaukaka a kyauta ake bin diddigin shi....” ta ƙarasa maganar tana dariya Mamin ma dariyar ta ke yi. “Nasan zakiyi mamaki Idan na faɗa maki cewa Duk irin wadatar Arziƙin dake gare su da ɗaukakarsu Basu da yawa family ɗinsu, Jikokin Obinna Goma sha Biyar” A ɗan ruɗe mami tace”kai! Wai dagaske”? Jinjina kai mami tayi”ƙwarai kuwa, Saratu Obinna ce kaɗai ta ke da ƴa’ƴa Uku, twins zaid da zain sai autarsu Faryat Obinna, Na manta ma ban faɗa maki ita a jerin ƴa’ƴan shi ba, Saratu obinna Itace Autarsu, tana ruƙe da muƙamin Minister of health Mijinta Pravin Obinna ɗan ƙasar india ne silar zuwanta karatun likitanci india Allah ya haɗa ta dashi.....” Ummi bata ƙarasa maganar ba, Zahra tai saurin cewa”Cin Arziƙi ya kawo shi, tsabar son banza mami ya canza sunan ubanshi ya maidashi na Obinna, Sai ki rasa gane ɗa ne ko suruki a gidan” tun da suka fara magana sai Yanzu ta tsoma masu baki hannunta ruƙe da wayarta da alama chatting ta ke yi. “To ke ina ruwanki zahra? Na rasa meya tsone maki ido da mutumin nan, ya fa riga daya zama ɗan gida, yafi ƙarfin a kira shi da suruki sai da ɗa” Ta6e baki zahra tai”Haba Ummi haka ake surukuntaka, mutun ya tare a gidan surukai don kawai yana auran yar shi, nifa Pravin sam baya burgeni mutun kamar ɗan ta’adda” mami sai kallonta take yi, ta fahinci bata ƙaunar mutumin. Ummi na ƙoƙarin buɗe baki don ta yi magana Muryar Baby Junaid ta katse masu firar tasu. Mommy! I’m back! I really missed u, Na maki tsaraba” Gaba ɗaya suka ɗago suna kallon shi, shigowar shi kenan Cikin Falon Jikin shi sanye da suit Na yara Black colour, Madarar kyau, Ya ƙara girma ayanzu yana acikin shekara ta biyar a duniya. hannun shi na aruƙe da Farar leda ta shopping, ba shi kaɗai ya shigo palourn ba, Yana atare da Mahboob Ƙanin Zahra, Kamar su sak kamar tagwaye shi da ita, Crazy Jeans ne a jikin shi, daga sama Ya sanya farar t shirt, Sumar kanshi kwance luf tasha gyara, Miƙewa zahra tayi da gudu ta nufi baby junaid tana ware mashi hannu don yazo ta rungume shi, tunkan ta ƙaraso ya girgiza mata kai Yana faɗin”Na mommy ne wlh, Wayo kike so ki min dan In ɗan maki tsarabata” Dariya suka saki, Zahra tace”matsalata dakai kenan, Komai Mommy mommy, idan da kara nima ai uwarka ce, Zonan dallah” ta ambaci hakan tare da janyo shi zuwa jikinta. Ummi tana murmushi tace”Kada ka yarda Junaid, Aunty zahra wayau zata maka don ka ɗan mata tsarabarka, “ ɗaure fuska zahra tayi”Ummi kada kisa ya raina ni fa” Ummi tace”ƙarya nayi ne? Yaro yayiwa babarsa tsaraba ke kuma Uwar wayau kina son cinye mashi abu” gatsina mata hanci zahra tayi tare da Wuce Bedroom ɗin Aneeleh ɗauke da Junaid a hannunta, Ya ɗaure mata fuska duk don kada tace zata Ci mashi tsarabar shi. “Sannu da dawowa,” Mami ce tayi maganar tana kallon mahboob dake zaune saman Sofa, Fuskarshi ɗauke da murmushi Ya ce”Yawwa mami fatan na same ku lafiya,” Suka amsa mashi da lafiyalou “Har an kammala registration ɗin”? Ummi ce ta yi mashi maganar, ɗaga mata kai yai alamar eh Saura zuwa school Ya rage mashi On monday zai fara zuwa, Uniform ɗinshi suna acikin mota nabarsu, wlh nagaji Ummi yunwa nake ji kamar in ci ƴan hancin Cikina” yai maganar Yana yamutsa fuska, Ummi tace”nayi zaton Kun biya restaurant Cin abinci” ɗan zaro ido yai kafin yace”Tab, Ga abinci agidanmu sai in kwasa in tafi restaurant cin abinci saboda almubazzaranci, “ dariya mami ta saki, Mahboob Ya iya tattalin kuɗin shi, Ya tsani almuzarranci arayuwarshi. Yasan ciwon kuɗin shi. “Tsokanar ka na ke yi don nasan halinka, Da shegen maƙo, Fatana Allah yasa ba ka bar mana yaro da yunwa ba” ta6e la66ansa yai”Tun da muka baro school ɗin ya fara yi min kukan yunwa, don dole na tsaya a wata plaza na siya mashi snack, shine fa daya ci ya rage saura nace ya bani inci yace mommyn shi zai ma tsaraba, ni da na sayi abu da kuɗina amma ya hanani ci, Sauƙin ma wurin jatumarshi zanje ta biyani ƴan canji na,” tuntsirewa Mami tayi da dariya, ita kanta Ummin murmushi ne akan fuskarta, Lamarin mahboob sai addu’a, Babu mutunci indai akan kuɗine “Kai yanzu saboda rashin ta ido, Sai ka je wurin Aneelerh ka ce ta biya kuɗin daka siyama yaronta snacks? Ɗanka ne fa” Hura hanci yai tare da cewa”Kusan fa dubu ɗaya na kashe mashi, haba ummi, kinsan fa yadda nake wahalar neman kuɗi, Daddy fa ko sisi baya bani sai in yaga dama kema kuma haka” Baki asake Mami ke kallon shi Ummi tace”indai mahboob ne kaɗan kika gani, ae baida mutunci indai akan kuɗin shi ne, Mara Kunya tashi ka bamu wuri, kuɗinka kuma Ka zo da anjima ka kar6a ni zan biya ka,” har ya yunƙura zai miƙewa, Idon shi ya sauka akan Ana mai aikinsu Aneelerh, Fitowa tayi daga Kitchen hannunta ruƙe da tray an jera kayan breakfast ɗinsu, hankalinta kwance take tafiya jikinta na sanye da Skirt pensil baƙi yabi shape din Jikinta, Daga sama ta sanya Riga launin green, Ƙura mata ido yai yana kallonta, Idon su mami akanshi ganin yadda yake binta da ido. Tsawa Ummi ta daka mashi a firgice ya waiwayo yana kallonta, fuskarta a ɗaure tace”Uban me kake kallo”? Yamutsa fuska yai”Kayan abincin dake a hannunta nake kallo ba wani abu ba,” yai maganar tare da wuce ya nufi dining table ɗin, da Ana take jera masu kayan breakfast, Kujera yaja ya zauna Yana faɗin”Ya ki ke”? Murmushi ta sakar mashi”lafiyalou, na gan ka ɗazu da safe zaku fita da baby junaid” 6ata fuska yai”shine baki min magana ba mun gaisa”? Hankalinsu mami gaba ɗaya akanshi, Ummi tace”Oh Ni ƴar ubansu, Yaro ya zama mayen mata, In banda haɗama irinta Mahboob ina zai kai Ana”? Mami tace”tashen balaga ne kawai, nan da wani lokaci zai dawo hayyacin shi,” dariya suka saki, Kafin suka miƙe zuwa Dining ɗin domin suyi breakfast.. Lokacin da Zahra ta shigo ɗakin Aneelerh ɗauke da baby junaid, A zaune ta same ta gefen gado hannunta ruƙe da hoton su, wanda su ka yi aranar birthday ɗin Angel, tun da ta fito daga wanka, ta shirya kanta Cikin riga da skirt, kanta na ɗaure da mayafi, jin motsin shigowar Zahra yasa tayi saurin ɗaura hoton hannunta saman drawer, idanuwanta acike suke tab da ƙwalla. “Aunty Aneelerh Ga Baby Junaid ɗinmu Ya dawo” cikin sanyin murya zahra tayi maganar don ta fahimci yanayin da Aneelerh take aciki, taƙi ɗagowa su haɗa ido, saboda ba ta san zahra taga hawayenta. Sauke Junaid ta yi ƙasa, da gudu ya nufi Aneelerh ya haye saman Jikinta hannun shi ruƙe da ledar tsarabarta”Mommy ba ki yi missing ɗina ba”? a hankali ta ɗago ta kalle shi, wani irin farin ciki ya ratsa zuciyarta, duk halin da zata shiga idan tayi tozali da fuskarshi sai ta ji sanyi aranta, Ɗaukarshi tayi tare da ɗaura shi saman laps ɗinta sosai ta rungume abunta”Momy ga tsaraba ki ci” Zahra na atsaye tana kallon fuskar Aneelerh, tsananin tausayinta ta ke ji. “Thank U my baby Boy, Nayi kewarka kamar zan zauce, Ya school ɗin? Surutu ya soma yi mata yana zayyana mata kyawun makarantarsu, yana magana ya buɗe ledar tsabar ya curo guntun donut daya ajiye mata abaki Ya tura mata, taunar shi ta soma yi tana murmushi, daga gefen su Zahra ta zauna still idonta akan fuskar Aneelerh, Sai kakkauce mata take yi duk don kada su haɗa ido “Mommy uniform ɗina suna acikin motar bro, hada sandals ɗina, kuma ya ce in faɗa maki ba zai ƙara kaini school ba saboda fetur tsada yake yi, wai sai dai ke kina kai ni” dariya Aneelerh tasaki jin abunda yace”kwantar da hankalin ka, nima ai ina da mota, kuma zan fara zuwa aiki, Kamar yadda nake ɗawainiyar kai Angel makaranta lokacin da tana araye, inje in ɗauko ta kaima haka zan dinga yi maka....” zahra ce ta katse ta da cewa”nima ina da mota, kuma ashirye nake da in dinga ɗawainiyar kaishi,” sai da tayi wannan maganar Aneelerh ta ɗago tare da kallonta, Hawayen da take 6oye mata ne suke soma gangarowa saman kuncinta. “Haba Aunty Aneeleeh i know it’s hard to let go of the past, but worrying about it won’t change anything wlh bamu jin daɗi idan muna ganinki cikin damuwa” zahra na rufe baki Baby junaid yace”sai da na mata faɗa ta daina kuka, ta ƙi jin maganana, mommy bata jin magana zanje na faɗa wa mami kina kuka” yai maganar yana ƙoƙarin sauka daga saman jikinta da sauri ta ƙanƙame shi”na daina babyna, tun da baka so, ba sai ka faɗa ma mami ba kaji ko” amsa mata yai da toh amma idan ki ka ƙara saina faɗa mata” murmushi Aneelerh ta saki idonta akan zahra dake kallonta. “Idan ina kallon hotunansu ina tuna irin rayuwar farin cikin da mu ka yi, Shiyasa ni ke zubda hawaye na, Allah na gani bazan Iya mantawa dasu acikin rayuwata ba, waɗannan mutanan uku masu mahimmanci sun kafa tarihi acikin zuciyata, nayi imanin har in koma ga mahaliccina bazan ta6a samun wanda zai maye min gurbinsu ba, Nafi damuwa da Angel wlh ina son yarinyar nan naji takaicin rashinta naso ace sun rayu tare da ɗan uwanta junaid, Angel abun tausayice ta rayu ba tare da mahaifiyarta ba, Na rasa wata irin zuciya ce a ƙirjin benazir......” sosai Aneelerh ta fashe da kuka, Jikin zahra duk yai sanyi, zagayo da hannunta tayi saman bayan Aneelerh ta kwanto da kanta saman kafaɗarta”I feel ur pain Aunty Aneelerh, da inada halin da zan iya yaye maki damuwarki da nayi sai dai babu, abu ɗayane nayi maki alƙawari zan tayaki addu’a, ni a tunanina bai kamata ace anyi shiru da maganar nan ba, idan har ba a yaɗa labarinsu taya za’asan in suna araye? Yakamata atada zancen labarin 6acewarsu a social media, inaso labarin ya zama sabo tamkar a yau ya faru in dai har mu ka yi hakan in sha Allah indai suna araye zasu bayyana ne.......” tunda zahra ta soma magana Aneelerh ta natsu tana sauraronta, ga dukkan alamu ta gamsu da zancenta Da sauri ta ɗago da kanta daga saman kafaɗar zahra muryarta adisashe tace”Zahra kina ganin idan muka yi hakan za’a dace” fuskar zahra ɗauke da murmushi tace ƙwarai kuwa in sha Allah zamuyi nasara, Kibar komai a hannuna Idan Daddy ya dawo zamu yi magana dashi, tunda kinga shi mutunne na jama’a zai tsara mana yadda za’a watsa labarin 6acewarsu, so nake duniya ta ɗauka,” lumshe ido Aneelerh tayi har cikin ranta take jin ƙwarin gwiwa. “Samu Ƴar uwa kamarki zaiyi wuya Zahra, shiyasa nakeson ki ina matuƙar ƙaunarki, ke ta dabance kina da kaifin basira, Ni ban ta6a tunanin tada zancen 6acewarsu tajuddeen ba sai da ki ka bani shawara, Allah ya Biya maki buƙatunki na alkhairi” “Ameen auntyna, ko dan saboda farin Cikin ki zanyi ƙoƙari inga an watsa labaransu tare da hotunansu, “farin ciki ya cika Aneelerh, sosai ta rungume zahra, Baby Junaid yayi lamo saman ƙirjinta, sai faman lumshe ido ya ke yi bacci ne ke shirin ɗaukarshi “Excuse ma’am” muryar Ana ce ta katse su, atare suka ɗago suna kallonta, tana daga tsaye bakin ƙofar ɗakin, a mutunce suka gaisa kafin ta sanar dasu cewa Breakfast yana jiransu a dining’ amsa mata su ka yi da toh, kusan atare suka miƙe, Aneeleh na ɗauke da babyn junaid” *Boss Bature✍️ Mu haɗu Gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08103884440, Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*KURKUKUN ƘADDARA*_ _The Prisoners E6🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* ~Middle step~ _A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._ *JUSTICE DEMOCRATIC PARTY* (JDP HQ) Manyan mutanene dattawa da matasa zazzaune a babban ɗakin taro na jam’iyyar Justice democratic party ɗaya daga cikin jam’iyun da su ka shara a ƙasar Nigeria, zungureran table ne wanda ke kewaye da kujeru, daga saman teburin akwai microphones na kowani member da zai yi magana, An tanadi kayan sha jere saman table, ɗakin taron yai tsit babu mai magana a cikin su, fitinannan ƙamshin turaren jikinsu ya gauraya da sanyin A.c na comference room ɗin da su ke a ciki. Tsabar 6acin rai ne da fusata akan fuskokin su ga dukkan alamu suna fuskantar tashin hankali a jam’iyarsu, musamman party leader ɗin su Alhaji bukar mai guduma fuskarshi a murtuke ta ke babu annuri, baƙin shi ya nunku har shining ya ke yi, Ya dunƙule tafin hannayensa da ya ɗaura su saman table din, Kowannan su ya ɗauki wankar tsadaddiya shadda daga gani naira ta zauna masu, kuma gogaggun ƴan siyasa ne waɗanda su ka jima a harkar suna gwagwarmaya, tsawon mintuna goma shabiyar, kafin shugaban jam’iyar mai guduma ya sassauta fusatar fuskarshi idanuwanshi jawur ya ɗago yana kallon mambobin su, tun daga jerin waɗanda ke a 6angaren damansa, Alhaji ubaid wadata Alhaji musa wadata former president, Alhaji badamasi da sauran ƴa’ƴan jam’iya, A hankali ya ɗauke idanuwan shi daga ta 6angaren dama ya mayar dasu kan mambobin dake zaune 6angaren hagunsa, Jinjina kansa ya ɗanyi yayin da ya ke fitar da huci ya soma magana tamkar mayunwacin zaki”Me ke shirin faruwane da jam’iyar mu? Zamu zauna ne mu zuba ido kamar mazurai muna kallon su? Mun ɗaura shugaban ƙasa dudu 4 yrs ya faɗi aza6e, mun kuma tsayar da sabon ɗan takararmu ubaid wadata an kayar dashi aza6e, Ga dukkan alamu durƙushewar jam’iyarmu ce tazo, tayaya jam’iyar da bata fi shekara biyar da kafuwa ba zata nemi ruguza tarihin tamu party din? A zafafe ya kai ƙarshen maganar yana kallon kowan nan su, babu wanda yai yunƙurin tanka mashi saboda sunsan halin shi idan ranshi ya 6aci, wani irin bauɗaɗɗan mutunne, Jinjina kan shi yai yayin da ya ke fitar da huci duk irin sanyin A.c da ke shawagi a ɗakin hakan bai hanashi fitar da gumi ba. “Babu irin tarihin da jam’iyar mu bata kafa fa, Ina ce shi kanshi dattijon arziƙin rainon jamiyar jdp ce, daga baya ne ya sauya ra’ayin shi akan wata manufa tashi ta daban wadda ba mu da masaniya akanta ya kafa tashi jam’iyar mai taken Progressive action party (PAP) Yan zu ga shi cikin ƙanƙanin lokaci sun ƙwace ƙarfin ikon da mu ke da shi a ƙasar nan, tsabar haɗama gaba ɗaya ƴa’ƴan shi ke juya ƙasar nan idan har bamu ta6uka wani abu ba zamu tashi a tutar babu ne”! Ya ƙarasa maganar tare da kai hannu Ya daki table din gaban shi, kowa yasha jinin jikin shi, damuwace ƙarara akan fuskokin su. Gyaran murya Alhaji Ubaid wadata yai kafin atsanake ya soma magana cikin dattako “Allah ya huci zuciyar mai girma jagoran mu, Ni anawa ganin yakamata mu fito da dabarun da za mu bi don ganin mun dawo da ƙarfin ikon da mu ke da shi ada, idan ma ta kama mu bi tsarin da su ka ɗauko wanda yasa jama’a suke rububin tasu jam’iyar, Idan har muna so mu farfaɗo da tamu jam’iyar” bayan Alhaji ubaid yai magana sauran Ƴan jam’iyar kowa Yana tofa albarkacin bakinsa, Idan ka cire mutun ɗaya wanda tun da ya zauna meeting ɗin idanuwanshi su ke a lumshe daga gani yana da jiji da kai da izza, ɗakin taron ya rikice da zafafan zantuttukan su kowa yana faɗin ta cikinsa, rai amatuƙar amace Ya sanya hannu ya daki table ɗin gabanshi wanda silar hakan ya janyo hankulansu ga dubanshi, Ƙaraminsu babbansu slowly ya buɗe idanuwanshi akan faces ɗin su, sun kasa kunne suna jiran jin me zaice hatta shugaban jam’iyar tasu ya natsu yana jiran jin bayani daga gare shi. Cikin harshen turanshi Ya soma magana da kakkausar murya”Let’s take a step back and focus on what we need to do right now. We need to come up with a strategy for the next election, We need to come up with a plan to fight back. We need to show the people that we are the party that can make a difference in their lives. We need to show them that we are the party that cares about their needs. We need to show them that we are the party that will fight for them, And We need to let them know that we are the party that is on their side.” tun da Alhaji musa wadata ya soma magana ƴa’ƴan jam’iyar su ke jinjina kansu ga dukkan alamu ya ɗauko magana mai ma’ana a ƙarshe ya daki table din gabanshi ya furta”Sharafudden obinna ba zai haura 4 years a mulki ba! Alƙawarine na ɗaukar wa kaina, duk yadda za’ae sai mun kayar dashi a za6e na gaba, dole jam’iyar mu ce asama babu wani mahaluƙi da ya isa ya durƙusar da jam’iyar mu, abokan hammaya ba za su ta6a cin galaba akan mu ba,” yana kai ƙarshen maganar azafafe ya yunƙura ya miƙe yana gyara malunmalun ɗin jikin shi, Ko sallama baiyi masu ba, Ya haura ƙafa yabar cikin ɗakin taron, yayin da su ke bin bayanshi da ido, har saida ya 6ace ma ganinsu tukunna suka dawo da dubansu kan maiguduma. tattaunarwar tasu ta ɗauki tsawon awa ɗaya kafin suka rufe taron da addu’a da kuma fatan nasara ga jam’iyarsu, Ɗaya bayan ɗaya suke fitowa harabar headquater inda jerin danƙara danƙaran motocinsu suke a killace. Bayan sun ƙara gaisawa da juna kowa Ya nufi motarshi, Musa wadata Yana kishingiɗe a back seat na danƙareriyar motarshi tsadaddar gaske, Ya lumshe idanuwanshi sanyin A.c ta ko’ina, gefen shi P.A dinsa ne, security ɗin da ke jigilar tuƙa su yana zaune a driver seat yana jiran jin umarninsa. Ƙwanƙwasa glass ɗin motar da akayi ne yasa shi ware manyan idanuwanshi, muryar Alhaji ubaid ce ta ratsa kunnuwanshi”Ina son magana da kai” Iya abunda ya furta mashi kenan, Muryarshi da izza ya amsa mashi da toh, daga haka yaba drivern nashi iznin ya tada motar su nufi gida” A jere motocin su su ka nufi gate ɗin fita daga cikin headquater ɗin su... *JOS CITY* Zaune ya ke saman darduma cikin shigar larabawa farare ƙal, kyakkyawan balarabe daga ganin fuskarshi ba ƙaramin mutun bane ya ɗan fara manyanta, Arab turban ɗin da ke nannaɗe akanshi, ya ƙara mashi kyau ga wani kwantaccen saje baƙi wulik mai matuƙar jan hankali, lallausar sumar kanshi ta sauko har saman wuyanshi dark black. Daddaɗan ƙamshin turararen jikin shi mai matuƙar sanyaya zuciyar mai shaƙar shi, idanuwan shi suna a lumshe yayin da ya ke yin qira’ar Alqur’ani mai girma, Yatsun hannunshi na dama na a asargafe da cazbaha, Qur’anin da ya ke karantawa yana agabanshi saman wooden qur’anic stand dogayen eye lashes ɗinsa a jiƙe su ke sharkaf da hawaye ga dukkan alamu ayar da ya ke karantawa ce ta sanya shi tsuma. Sam bai ji takun tafiyar mutun acikin ɗakin shi ba, tafi ƙarfin mintuna talatin da shigowa, idanuwanta akanshi ganin bai da niyar tsagaita karatun ƙur’anin nashi ne yasa ta ambaci sunan shi *”DR SHUREIM*”Nasan kana jin takun tafiyata don haka idan ka kai ƙarshen Aya ina son magana da kai”! tamkar ta yi magana da bango ko kallo bata ishe shi ba, sai ma ƙara sautin muryashi da ya yi” dogon tsoki taja tare da zuwa gaban dardumar ta shi ta kai hannu ta rufe qur’anin da ya ke karantawa, a tsiyace ta ƙwace cazbagar dake nannaɗe a hannun shi ta ɗaura ta saman qur’anin, don ta fahinci da gayya ya ke yin karatun duk don kada ya saurari maganarta. Tana huci ta ɗago tana kallon shi still bai buɗe idanuwanshi ba, kuma bai dakata da yin karatun ƙur’anin ba domin kuwa haddace akanshi “Ka da ka bari raina ya 6aci wlh zan yi maka abunda baka tsammani, na rasa uban me na yi ma ka daka ɗaura mun karan tsana sai ka ce ba uwarka ba! Ko kana da wadda tafi ni ne a duniyar nan”? Ta jefa mashi tambayar, Shiru bai ce uffan ba, gyaɗa kai tayi”ilmin addinin na ka ya tashi abanza tunda ba ka san ka girmama iyayen ka ba, tsawon shekara da shekaru kana nuna wariya tsakanina da mahaifinka laifin me namaka Shureim”? Cikin jin ƙunar rai ta yi maganar, A hankali ya buɗe idanuwanshi farare ƙyal da su ya ɗaura su akan fuskar Mahaifiyar tashi, ba kowa ba ce fa ce Layla mahaifiyar Benazir, Doctor shureim shine babban ɗansu, Ya ya ne awurin Benazir mahaifiyar Angel. Daddaɗar muryar shi ce ta ratsa kunnuwanta”ba ki min laifin komai ba, har yanzu kina nan a matsayinki na mahaifiyata, kawai bana buƙatar kusancin ki da ni” Zagayawa ta yi zuwa gefen gadon shi ta zauna suna fuskantar Juna”Nasan dalilin dayasa ka ke yin fushi dani, haba shureim tsawon shekaru nawa why za ka ruƙe abu aranka yai ta damun ka? Yakamata mu manta da abunda ya wuce, kuskure ne an riga da an ta6ka, kuma in sha Allahu hakan bazata ƙara faru wa ba” fuskarshi a ɗaure ta ke babu walwala” tayi tsammanin zai tanka mata sai ji ta yi ya yi shiru bai ƙara magana ba. Ƙululun baƙin ciki ne ya tokare mata maƙoshinta, zuciyarta na ƙuna tace”na lura sam faɗuwar mahaifinka bata dame ka ba, An ya kuwa shureim kana ƙaunar mu a matsayin mu na iyayenka? Cos na fahimci baka son cigaban mu” murmushin takaici dr shureim ya saki, da ido tabi shi da kallo ganin yana dariya har fararen haƙoran sa su ka bayyana masu kyau da tsari. “Mahaukaciya ka mai da ni? ina magana kana dariya” fuskarta a ɗaure tayi maganar, Yunƙurawa yai tare da mikewa Ya fuskance ta kafin ya soma magana”Saboda ku ba iyaye bane daya kamata a nuna damuwa akan ku! Daga ke har shi bakusan ciwon kan ku ba, Gaba ɗaya hankalin ku na akan son abun duniya damuwar ku akan cigaban ku ne ba akan mu ba! Ta ya ya zan damu don mahaifina ya faɗi a za6e? Aini abun farin cikine agare ni, don na fahimci siyasarshi tafi komai mahimmanci awurinku! Saboda rashin sanin ciwon ƴa’ƴa Yau tsawon shekara goma sha shidda Benazir bata a tare da ku, hankalin ku a kwance ba ku iya ta6u ka komai ba, duniya kawai kuka sa agaba, Wlh na jima ina danasanin kasancewar ku Iyayen mu! Na yi fatan ace mutun yana iya canza iyaye da tuni na yi hakan, Nifa ba ku da amfani acikin rayuwata! Kun riga da kun yi min abunda har abada zuciyata bazata ta6a mantawa da shi ba, kune silar duk wata masifa dana tsinci kaina aciki.......” daƙyar ya ƙarasa maganar cikin jin ƙunar rai, a bun ka ga farin mutun tuni fuskarshi ta canza launi zuwa ja, numfashi yaja muryarshi adisashe yace”kun manta cewa ƴa ƴa amana ne agare ku? Ranar gobe ƙiyama Allah zai tambaye ku game da amanar da ya ba ku, Rashin nasara yanzu ku ka fara gani, in sha Allah ba zaku ta6a samun abunda ku ke so ba, har tsayuwar dare zanyi maku akan kada Allah ya cika maku burinku na mallakar kujerar.....” bai ƙarasa maganar ba sakamakon zazzafan marin da Layla ta sakar mashi, da sauri ya dafe kuncinsa da tafin hannun shi na dama, Idanuwanshi sun rune zuwa ja. Tana hu ci ta nuna shi da yatsa”don uban ka ka tattara kayan ka kabar gidan nan tunkafin ranka ya 6aci, shashasha kawai wanda baisan ciwon kanshi ba,” Cikin sanyin murya yace”zan tafi koda ace baki kore ni ba Mommy, dama ita gaskiya ɗaci gare ta, kuma in sha Allah zanje na nemo ƴar uwata benazir aduk inda take, idan ku bakusan ciwon kanta ba ni na sani....” tunkan ya kai ƙarshen maganar layla ta nufi ƙofar fita ɗaki kamar zata tashi sama tsabar 6acin rai. Zuƙunnawa yai saman gwiwowinsa idanuwansa jawur hawaye na cigaba da gangarowa saman kuncinsa, haƙiƙa mahaifiyarshi ta fama mashi mikin dake acikin zuciyarshi, matsawa yai gaban gadon shi ya miƙa hannu ya ɗauki wayarshi yana duban hoton da ke a kan wallpaper na wayarshi, lumshe idanuwanshi ya ɗanyi kafin ya ware su sosai akan hoton da yake kallo, baya gajiya da kallon fuskarta A hankali ya furta _ke ce silar tarwatsewar farin cikina kuma kece silar shiriyata! Ki yafe min nayi kuskuren da bazan ta6a gyara shi ba, ina son ki sosai ina jin ki har cikin raina, nasan haƙƙin ki ne ya ke bibiyar rayuwata_ kifa kansa yai saman mattress sosai ya fashe da matsanancin kuka kamar ƙaramin yaro. Bayan fitar Layla kaitsaye ta nufi falon gidan, ranta ya 6aci sosai, kalaman Dr shureim sun sosa mata zuciyarta, yau kusan shekara uku da dawowarsu Nigeria tun bayan barin su Dubai, Layla taji takaicin faɗuwar Alhaji ubaid saboda tafi kowa ƙwallafa rai akan hawan shi mulkin shugaban ƙasa don ta ji daɗin yin sharholiyarta a matsayin first lady, sai dai Allah bai basu nasara ba, bugu ɗaya aka ƙundumo shi ƙasa, tun farko sai da ya ji fargabar tsayawa takarar jin wanda za su kara da shi, don kuwa yasan muddin Sharafudden Ya nemi takarar shugaban ƙasa zaiyi wuya ya iya kada shi, sanin farin jinin da Allah ya yi mashi, Mutun ne na jama’a mai kyautatawa al’umma. “Hajiya..”muryar mai aikin gidan su ce a dabarbarce ta ambaci sunanta ganin yadda ta bi ta da matsiyacin kallo”lafiya”? Cikin harshen larabci ta ce “Mun yi baƙi ko da ya ke sun wuce baƙi” “Saboda ƙannan uwata ne”? Ta jefa mata tambayar, Sunnar da kai ƙasa zainab ta ɗan yi”Hajiya Aisha ce matar governor tare da....” bata kai ga ƙarasa maganar ba, layla ta dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannu”ni ban gayyaci uban kowa ba a gidana, Matsiyatan banza gulmace ta kawo su wato an zo aga yadda na ƙare to ta Allah ba ta su ba ƴan kutmar uba, jajen ne har yanzu bai ƙara ba abu an kusa rabin shekara da faruwarshi saboda baƙin hali sunƙi su manta..” tun da ta fara sambatu zainab ta yi kasaƙe tana kallon fuskarta ba ki asake, ta fahimci zallar baƙin ciki ne Azuciyar uwar gidan ta ta, rashin nasarar su ya tsaya mata a zuciya nema ta ke ta zauce, dama ya lafiyar gwiwa mutun mai ƙarancin imani. Tsawa layla ta daka mata, firgigit! zainab ta ɗan zabura”Ki je ki sanar da su cewa bana nan” muryarta na ɗan rawa tace”Ae an riga an faɗa masu cewa kina a cikin gidan, yanzu haka anyi masu iso suna acikin main palour...” daƙyar zainab ta ƙarasa maganar tana mai haɗiyar yawu ganin irin kallon da layla ta ke jefa mata tamkar ƙwayar idonta zata faɗo ƙasa, guntun tsoki taja”masu aikin gidana sun fara raina ni saboda rashin nasarar mu dole na yi wani abu akai, su kuma waɗancan taron magulmatan zanje gare su, bari na fara zuwa ɗaki in zuba gwalagwalai na don kar su raina ni” acikin zuciyarta ta yi maganar tare da juyawa ta nufi sashen da ɗakinta Ya ke. Binta da ido zainab ta yi haɗi da ɗan girgiza kanta”Allah ya shirye ki layla” har zata Juya idon ta ya sauka akan Dr shureim da ke shirin fitowa daga ɗakin shi hannun shi ruƙe da key ɗin motarshi, tsananin tausayin shi ne ya kamata ganin yadda ya canza, ta lura da damuwar da ke akan fuskarshi, a hankali yake tafiya yana tunkaro inda take ga dukkan alamu bai lura da ita ba har sai da ɗan yi mashi gyaran murya, tukunna ya ɗaura fararen idanuwanshi akanta, Sam babu walwala akan fuskarshi, darajar da ta ke da shi a idon shi yasa shi nufarta, ya ɗauki zainab taimkar auntynsa, Babbar macace mai hankali da natsuwa. Yana ƙarasa gabanta ya duƙar da idon shi ƙasa ba tare da ya gaishe da ita ba “Ko ba ka faɗamin ba dr shureim naga damuwa akan fuskarka, na ɗauke ka tamkar ɗan ciki na, dan Allah shureim ka da ka bari damuwa ta canza ka, inaso ka sani komai ya faru muƙaddari ne daga Allah, rubutacciyar ƙaddara ce wadda ba wanda ya isa ya canza ta” cikin kwantar da murya ta ke lallashinsa, sai faman karkaɗa car key ɗin hannunsa yake yi, tun da ta fara yi mashi nasiha bai tanka mata ba sai da ta kai aya tukunna ya soma magana a tsanake “Aunty zainab na aikata babban zunubin da har abada ni nasan Allah ba zai ta6a yafe min ba, Ni kaina nayi danasin mara amfani....” duk yadda yaso ya jure ya kasa kamar ƙaramin yaro cikin muryar kuka yaci gaba da cewa”Ina sonta aunty zainab sune silar komai, bazan ta6a yafe masu ba na tsane su, Mu kuma tamu jarabtar ta iyaye ce, basu damu da mu ba, buƙatar su itace agabansu, Yan zu haka da nake maki magana Mommy ce ta kore ni saboda na faɗa mata gaskiya, ki yi haƙuri Aunty zainab kada ki ce za ki dakatar dani ƙwara na tafi, zama atare dasu bai da amfani, zanje na nemo ƴar uwata Benazir In ruƙe ta a hannuna waɗannan mutanan ina zargin sune silar tarwatsewar rayuwarta kamar yadda su ka yi silar tarwatsewar tawa rayuwar......” yana magana hawaye na cigaba da wanke fuskarsa, ita kanta zainab ɗin tuni idanuwanta sun cicciko tab da ƙwalla, ruƙo hannunshi tai a cikin nata, da sauri ya ɗaura kanshi saman kafaɗarta”Shureim Allah ba azzalumin bawansa bane, duk wanda ya cuci wani Allah zai saka mashi, ko a tsakanin ƴa’ƴa da iyayen su akwai hisabi, Na yi maka alƙawarin zan taimaka maka akan komai, ashirye ni ke dana zama uwa agareka, Ae ɗa na kowa ne idan su basu so to ni inaso, dama ban ta6a haihuwa ba” jin abinda tace ne yasa shi ɗago da fuskarshi yana kallon ta, murmushi ya ƙaƙaro akan fuskarshi, haƙiƙa kalamanta sun sanyaya masa zuciyar shi. “Aunty zaina are u serious zaki taimaka min”? Jinjina mashi kai tayi alamar eh, farin cikine ya bayyana akan fuskarshi’Aunty zainab akwai wani aiki da nake so mu yi atare bana so kowa Ya sani....” bai kai ƙarshen maganar ba, Takun tafiyar Mahaifiyarshi Ya dakatar dashi, muryar zainab na rawa tace mashi “Ka tafi kawai zan kira ka awaya anjima sai mu yi magana” amsa mata yai da toh, Da sauri Ya fuce ita kuma ta nufi hanyar kitchen. Cikin takun izza ta ke tafiya, har ta canza kayan jikinta zuwa tsadadden leshi wuyanta da hannyenta Zinari ne, ta buga uban ɗaurin kallabin nan ture kaga tsiya, Takalman ƙafarta high hills ne, ta wanke jikinta da turare, tana tafiya tana hura hanci Tana dab da zata shiga palourn gidan muryoyin manyan matan da suka kawo mata ziyara ta karaɗe kunnuwanta, da sauri ta la6e tana sauraron abunda su ke tattaunawa “Ae ban ta6a ganin mutum mai haɗamar tsiya irin Alhaji ubaid ba, nifa tun lokacin da ya sauka mulki yana fama da ciwon ƙafa raina ya bani cewar wani munafuncin suka ƙulla ashe kujerar shugaban ƙasa yake so, yanzu gashi ba wan ba ƙanin duka sun rasa” 6a66akewa su ka yi da dariya “Ni dama tun da naji Sharafudeen Ya tsaya takarar shugaban ƙasa raina ya bani cewar shi zaiyi nasara, sai gashi ta tabbata, wa zai Iya ja dasu? Ganganci ne ya kai Alhaji ubaid, Ko da ya ke matar shi ce mai haɗamar a yadda na fahimta” hajiyar da ta yi maganar ta ƙarasa tana dariya, wata ta ɗaura da cewa”ai ko sharafudeen bai tsaya takara ba kinsan Allah ba wanda zai za6i ubaid, Mutanan da basu son darajar ƴa’ƴan su ba taya zasu Iya ruƙe ƙasa irin nigeria mai cike da taron Talakawa? Ƴar ta fa benazir tana ƙasar ture, ayadda naji labari karuwanci take yi kuma ana zargin uwarce ta turata, Allah na tuba zato zunubi, duk da ni dai daga majiya mai ƙarfi naji ...”Hankalin layla idan yai duba toh ya tashi, tseguminta da suke yi yayi matuƙar gigitata, bata ta6a tunanin mutane zasu sanya masu ido game da rayuwarsu ba, haƙiƙa ranta ya 6aci, Ta yi niyar ta shiga tayi masu korar kare amma saita lallashi zuciyarta, Ta daidaita natsuwarta tare da yi masu sallama ta kutsa kai cikin katafaren palourn jin motsin shigowar ta ne yasa su ka yi saurin dakatawa da yin firar, ɗaya bayan ɗaya ta ke binsu da kallo, mata kenan abin a Jininsu ya ke....... *UNCLE ABDALLAH* A ƙalla yau wata ɗaya da dawowarsu Nigeria, sun fara sauka a adamawa state wurin dangin hajiya adama kafin dawowarsu gidansu da ke anan Jihar jos, zaune ta ke saman sofa mai mazaunin mutun uku, Jikinta na sanye da riga bubu ta material ta yafa mayafi akanta, Yayin da idonta ke asanye da farin glass, hutu yazauna mata ta ƙara ƙiba abunta. Ta natsu tana kallon portrait artist ɗin dake zuƙunne agaban Drawing board Yana gudanar da aikinsa, daga ƙasa gefenshi Kayan zananshi ne, Hada hoton Angel da hajiya adama ta miƙa mashi don Ya zana mata Ita, tana son ganin yadda zata koma a shekarunta na yanzu don su samu sauƙin gane ta “Ranki shi daɗe, Yarinyar zata kai shekara nawa Ayanzu”? Me zanan ne yai mata tambayar. “I think 15 to 16 years,” amsa mata yai da okey, Kafin yaci gaba da aikin zanan shi, “Mijina ya faɗa min cewa kai ƙwararre ne a 6angaren zana mutane, so please don’t disappoint me” murmushi mutumin ya saki ba tare daya juyo ya kalle ta ba ya furta mata”In sha Allah” “Assalamu Alaikum”! Muryar Uncle abdallace ta janyo hankulansu ga dubanshi, Shigowarshi kenan Jikinshi na a sanye da shadda launin maroon, idan ka kalli fuskarshi Sak Uzair hatta duhun fatarsu iri ɗayane. Cikin girmama mai zanan ya gaishe da uncle abdallah, Bayan ya amsa mashi da fara’a ya ɗago ya kalli Hajiya adama”mu shiga ciki ina son magana da ke” amsa mashi tai da toh, Yai gaba ta miƙe tabi bayanshi, A cikin bedroom ɗinsu su ka tsaya suna fuskantar Juna “Tun ɗazu nake jiran shigowarka, Inataso muyi maganar zuwan mu abuja, almost one month da dawowarmu Nigeria banje naga jikana ba duk irin yadda na ƙwallafa raina akan son ganinshi, “ “Duk yadda kika kaiga ƙagara da son ganinshi ba ki kaini ba,” “Ni banga alamun hakan ba, pls idan munje mu tafo dashi, tunda ka ga bamu da wani ɗa da zamu dinga kallo muna jin daɗi” fuskarta amarairaice tayi mashi maganar, girgiza mata kai Uncle Abdallah yai”idan mukayi hakan bamuyiwa Mahaifiyarshi adalci ba, ta rasa mijinta yanzu kuma sai mu tada zancen zamu kar6i yaro daga gurinta”? Ɗaure fuska Hajiya adama tayi, ranta ya 6aci”Abdallah baka son farin cikina, Ni zan koma palour wurin mai zanan can” Ta ambaci hakan tare da juyawa a fusace zata tafi, Har takusa kaiwa bakin ƙofa muryarshi ta katse mata hanzarinta”ba zan ta6a manta irin wahalar da nasha kafin na mallake ki a matsayin matata, ta ya ya kike tunanin bana son farin cikin ki”? shiru bata Juyo ta kalle shi ba, idonshi na akan bayanta “A yanzu haka da ni ke yi ma ki magana, na yi mana cuku cukun komawa can da zama, na samu aiki a babban companyn sharafudeen saboda ba zan Iya raba uwa da ɗanta ba, haka zalika bazan Iya raba kaka da jikanta ba, shiyasa na yanke shawarar komawarmu can, Nasan hankalin ki zaifi kwanciya idan kina ganin shi akai akai” idanuwanta ne suka cuko tab da ƙwallar farin ciki. Fasa fita ta yi daga Cikin ɗakin, Jiki asanyaye ta nufe shi tare kwantar da kanta saman ƙirjinshi, Hannun shi Ya ɗaura saman bayanta yana cigaba da gayamata daɗaɗan kalamai masu kwantar mata da hankali, tsawon mintuna biyar kafin ta ɗago dakai Tana kallon shi “Inaso zanyiwa Aneelerh kyautar zanan fuskar Angel da akayi min a south korea, Nasan za ta yi farin ciki saboda tana matuƙar ƙaunarta, kuma zatayi mamakin ganinta a shekarunta na yanzu don inada tabbacin idan har Allah yasa ta bayyana zamu iya ganinta da suffar da mai zanan ya zanata, kasan sun ƙware a iya zane” tana magana Hannunta ruƙe da gaban rigarshi kamar tana gyara mashi ma6allinta “Idan ki ka bata zanan ke fa? Almost dala dubu ɗari akayi maki shi fa” murmushi ta ɗan saki”saboda haka yasa nace ka kiramin wani mai zanan ni sai na ɗauke shi,” yace”mai zai hana ki bata sabon zanan da za’ayi ke sai ki ruƙe na koriyan? Girgiza kai ta yi alamar “a’a, Nafison nayi kyauta da abunda yafi kyau da tsada, Farin cikinta kawai nakeso,” yanayin fuskarshi ya nuna tamkar bayason taba Aneelerh zanan fuskar Angel da akayi mata aƙasar korea, ba ta kawo komai aranta ba saboda ta fahinci Son zanan ya ke yi ba don saboda tsadarshi ba. “Hajiya an kammala” daga Cikin palour su ka jiyo sautin muryar me zanan, da sauri Hajiya adama ta nufi falon uncle abdallah yabi bayanta, tunkan su ƙarasa shiga Ciki idanuwansu suka soma hango masu Kyakkyawar fuskar Angel jikin allon zanan nashi, Tsabar mamakin yadda suffarta ya fito ne yasa su sakin baki, Kamanninta sak dana tajudden Hasken fatarne kaɗai na mahaifiyarta da kuma sumar kanta. “Wow! Zanan sak kalar na south korewa nayi mamaki! Banbancin kawai tsadar kayan aikin da akayi amfani wurin yin wancan zanan amma wlh yayi kyau over” hajiya adamace take ta sambatun ganin zanan, Shi kanshi uncle abdallah Ya yi mamakin ganin zanan, Suffar Angel sak sai dai an ƙara mata girmanta, takai dai dai age ɗinta na yanzu 15 to 16 years, Mai zanan yana atsaye yana kallonsu, sai sakin murmushi yake yi jin yadda suke yabon aikinsa “Ina fata Angel ta bayyana kamar yadda muka ganta a zananta, in har hakan ta faru nayi maka alƙawarin zan ninka maka kuɗinka” fuskarta ɗauke da murmushi tayi maganar tana kallon mai zanan, washe baki yai yana faɗin”In sha Allah ranki ya daɗe ƴar ki zata bayyana kamar yadda na zana ta a hoton nan, kuma ina roƙon Allah yasa zanene ya zama silar ganinta” atare suka amsa mashi da ameen, Kafin tafiyar mai zanan saida suka haɗa mashi sha tara na arziƙi. *EVIL FOREST* *the Prisoners💔* Kamar matattu haka su ka sha baccin su cikin kogon dutse, Allah kaɗai yasan awanni da su ka kwashe suna sharar bacci, Bawan Allah Danish A zaune ya ke bacci, Wutar da ya kunna masu tuni ta jima da mutuwa, Hasken rana ya kwalo daga sararin samaniya duhun dajin ya ɗan washe, A hankali ta soma mutsun mutsun buɗe idanuwanta a yayin da ta ke ambaton Sunan Allah, tsabar kumburan da idon nata yai daƙyar ta ke iya buɗe shi, ga uwar kwamtsa cunkushe da idon, kaɗan ta ke iya buɗe shi tana kallon Saman kogon dutsen, cikin rashin fahimtar ina ne? sam ta manta cewa sunbar kurkukun ƙaddara, wani irin tsorone ya kamata muryarta sam babu wadataccen sauti ahaka take ƙoƙarin ƙwalawa ƴan uwanta kira ɗaya bayan ɗaya, duk tabi ta furgice. “Batool! Gabriel! Haris kuna ina ne? Duhu bana iya gani da kyau, Naufal wai Ba mai ji na ne”? Shiru taji babu motsin mutun a kusa da ita, Jikinta yai mata tsami, ko yatsanta ta gaza motsawa, ga dukkan alamu dannau ne ya danneta, kware muryar tayi da ƙarfi ta furta Sunan Danish! Har cikin dodon kunnan shi ya ji sautin muryarta, slowly ya ɗan ware kyawawan idanuwanshi akan fuskarta, bargon da ya lullu6a mata a iya ƙirjinta ya tsaya hakan ya bashi damar kallon ta da kyau, duk da jinin da matsafa su ka yi mata wanka dashi ya koma mata tamkar fenti tayi muni sosai, cikin sanyin murya ya furta sunanta”My Angel” jin muryarshi yasa ta dakatawa da yin sambatun nata, ƙoƙari take wurin ganin ta motsa jikinta don ta samu damar zuwa gare shi, fahimtar hakan yasa shi matsawa dab da ita, kwanto da fuskarsa yai saitin fuskarta yai mata rumfa da faffaɗan ƙirjinsa, numfashinsu har yana kokawa dana juna, kaɗan ta ke iya ganin fuskarshi, wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarta, muryarta na ɗan rawa ta furta sunanshi”Da..Nish” fatanta Allah yasa ba mafarki bane. Dogayen yatsun hannun shi ya ɗaura a gefen fuskarta ya shafa a hankali da sauri ta ɗaura nata hannun saman nashi dake akan face ɗinta, Sai yanzu ta samu damar motsa jikinta, zafafan hawaye ne su ka soma wanke mata fuskarta, Ɗago da ita yai zuwa saman ƙirjinshi Ya kwantar da ita, duka yatsun hannayen shi na acikin sumar kanta, sosai ya ƙanƙameta, yanayin yadda su ka rungume junansu zai tabbatar maka da irin kewar juna da su ka yi, ba ka jin komai sai sautin nunfashinsu, da bugun zuciyarsu dake harbawa da sauri da sauri, “I can’t explain how much I miss you. I’m sorry for what happened, it’s all my fault. I’m sorry, Angel.” Cikin rauni na murya yai maganar, Cikin shessheƙar kuka ta soma yi mashi magana”ba laifinka bane Danish, ka daina faɗin hakan, ni abunda yafi damuna rashin ƴan uwan mu da suka rasu, na yi takaici Danish, ban cika masu alƙawarin da na ɗaukar masu ba, Jemimah da Azeeza sunci burin fita daga kurkuku don suje gidan daddyna, haka parveen burinta ta ci abincin gidan daddyna, baiwar Allah deejah ga sauran ƴan uwan mu da mu ka rasa” daƙyar ta ƙarasa maganar, zafin jikin su duk ya ɗumamasu, Yanayin weather ɗin dajin San yi sosai, daga inda suke suna iya jiyo sautin kukan Namun dawa. Ɗaura tsinin hancinsa yai saman sumar kanta, shi kaɗai yasan raɗaɗin da ya ke ji acikin zuciyarshi, Jin shiru bai tanka mata ba, yasa ta ɗago da kanta daga saman ƙirjinshi ta ɗaura eye balls ɗinta akan fuskarshi, bacci ne bai ishe shi ba, sai faman lumshe idanuwanshi yake yi, a tsanake su ke ƙarewa juna kallo tsawon mintuna goma sha biyar, ‘ “Bana so su Gabriel su farka su taras da gawawwakin su azeeza, abun zai ƙara ta6a zuciyarsu, ka taimaka min Danish mu binne su kafin farkawarsu,” shiru bai tanka mata ba sai kallon ta ya ke yi kamar yau ya fara ganinta “Danish! Am talking to u, bana jin daɗin jikina, maganar ma daƙyar nake iya furtata” Still bai motsa la66ansa ba’ ta rasa meyasa ya ke kallonta yana lumshe ido Ya ƙi tanka mata,” Gyaɗa kai tai”shikenan tun da bazaka taimaka min ba, Ni zan je na rufe su” tana ƙoƙarin miƙewa sexy voice ɗin shi ta ratsa kunnuwanta”Kin ta6a ganin an binne mutun da ranshi”!! ras taji gabanta ya faɗi a matuƙar ruɗe ta zazzaro idanuwanta waje tana kallon shi........ *Boss Bature✍️ Mu haɗu Monday Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08103884440, Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*KURKUKUN ƘADDARA*_ _The Prisoners E7🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* ~Middle step~ _A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._ “ka na nufin ba su mutu ba suna a raye”? A ƙagare ta jefa mashi tambayar, jinjina mata kai yai ba tare da ya furta mata kalma ba, bugun zuciyarta ne ya qaru a sukwane ta juya baya don ta samu damar ƙare masu kallo, bargunan da ya lullu6e su da shi ya hana ta gan su da kyau, jikinta na 6ari ta ƙara sa gaban su ta zuƙunna tare da kai hannu ta ɗage saman bargon, duk wani motsin ta akan idon Danish. Wani irin farin ciki ne Ya lullu6eta haƙiƙa ta yi al’ajabin wannan iko na Allah, kamar zautacciya haka ta dinga ɗaura kanta saman ƙirjinsu haɗi da jogana kunnanta saitin zuciyar su don ta ji idan tana bugawa, daga kan Jamimah ta fara tana ɗosa kunnanta bugun zuciyar jemimah ya daki dodon kunnan, nan ta ke ta fahimci cewa bacci su ke yi, Tambayoyi ta shiga jefawa kanta, Ta ya ya akai haka ta faru? Dama wanda ya mutu yana tashi? don ita dai a iya saninta idan an mutun ba adawowa, ɗaura kunnanta ta yi saman ƙirjin Azeeza lumshe idanuwanta ta yi wani irin sanyi ne ya ratsa zuciyarta, jin bugun zuciyar azeeza na har6awa, matsawa ta yi gaban Parveen tunkan ta ɗaura kanta saman ƙirjinta idanuwanta su ka sauka akan ƙaramin bakinta ganin yana motsi yasa ta fahimci tana araye, Lamarin yai matuƙar ɗaure mata kai, ta ya akai su ka rayu! Kuma Danish da kanshi ya tabbatar masu cewa Heart attack ne yai silar mutuwarsu, duk da bata da ƙoshin lafiya hakan bai hana smart brain ɗinta aiki ba, Zurfin tunani ta shiga idan har su Jemaimah su ka iya jure abunda ya faru dasu ya kenan ta 6angaren Sauran ƴan uwansu da su ka baro? Waro idanuwanta waje ta yi yayin da zuciyarta ka harbawa da sauri da sauri, a fujajen ta zabura ta miƙe kamar an zungure ta, ta juya ta nufi Danish dake a zaune Ya ɗan lumshe idanuwanshi, ƙoƙari ya ke ya hana kanshi yin bacci gudun kada yaja masu matsala, zuƙunnawa tai agabanshi “Danish taya akai su Jamima su ka rayu? Bayan kai da kanka ne ka faɗa mana cewa zuciyarsu ce ta buga” ware idanuwanshi yai akan fuskarta, tsananin tausayinta ne ya kama shi, damuwarta akan ƴan uwanta, bata damu da kanta ba, ƙarantar shekarunta yafi komai ɗaure mashi kai, yadda harta iya jure waɗannan wahalhalun rayuwar wanda yayi imanin ko wani babban ba zai Iya jurarsu ba. “Danish bana so ina magana kana share ni, ka faɗa min ta ya ya akai su ka rayu? A iya sanina idan mutun ya mutu baya tashi, Sai gashi su Azeeza sun tashi, ko dai ka yi amfani da sihirinka ne wurin dawo masu da rayuwarsu...”? A ruɗe tai maganar babu kwanciyar hankali atattare da ita, a hankali ya ɗan motsa la66ansa. “My Angel, u should stop talking about them, ba ki da lafiya u need a rest,” damƙar wuyar best ɗin jikin tai sosai ta fashe mashi da kuka tana faɗin”Danish ka faɗa min dama kasan suna araye shi ne ba ka bari mun goyo su Deeja mun taho da su ba? Me yasa ka yi mana ƙaryar cewa zuciyarsu ce ta buga”? Tana magana tana ku ka, raunin gefen bakin ta tuni ya fara tsastsafo da jini. Ranta yai mugun 6aci zuciyarta ta harzuƙa, A haukace ta miƙe tana faɗin”Zan koma na taho da su Deeeja, ban damu da in rasa raina ba,” a hanzarce ya miƙe jin abunda tace, ido cikin ido su ke kallon juna”Am sorry Angel i don’t mean to hurt u, kinsan bana ƙarya, sannan bani da amsar da zan baki that’s why nayi shiru, hatta su Azeeza ban san suna araye ba, a daren jiya na yi ƙoƙarin binne su cos bana son ku farka ku taras da gawawwakinsu, hakan zai fama ma ku ciwon da ke a cikin zuciyarku, nayi amfani da sihirina wurin tsaga ƙasa har na fara sanyasu a ciki idona ya sauka akan yatsun ƙafafuwansu dake motsi, i was shocked cos ban yi expecting din zasu rayu ba, kin ji yadda akai nasan suna a raye” kamar ta so ta fahimce shi sai dai wani sashe na zuciyarta yaƙi aminta dashi, girgiza mashi kai tai”Ni dai zan koma kurkuku in ɗauko su Deeja, Saboda ina ji araina cewa Suna araye” Ya fahimci damuwace ke ƙoƙarin zautar da ita, Zaiyi wuya ta fahince shi, yasan halin kayansa da rigima ga kafiya da taurin kai, juyawa ta yi tare da nufar ƙofar fita daga kogon dutsen, da sauri Ya bi bayanta tare da ruƙo arm ɗinta ya janyota zuwa jikinshi, sosai ya matseta. “Angel daji ne fa, ba mu a kusa da kurkukun ƙaddara, ta zarar awanni ce, A daren Jiya bayan mun fita ni ne na ɗauko ku na dawo da ku nan duk don na sauƙaƙa maku wahala” daƙyar ya ke magana, damuwace ƙarara akan fuskarsa, ƙoƙarin raba Jikinta tayi daga nashi. Zuciyarta ce ke azalzalarta sam bata fahimtar kalamansa, idanuwanta sun makance “Ka sake ni Danish, nasan ko nace kaje ka ɗauko min su Deeja ba za ka je ba, don haka ni zanje, saboda ina ji araina ƴan uwana suna araye basu mutu ba gashi mun baro su a hannun Azzaluman mutanancan.....” cikin shessheƙar kuka ta ƙarasa maganar, duk yadda yaso ya hanata tafiya taƙiya, har kwatanta mata haɗarin da dajin gare shi amma ta kafe akan sai taje, sakinta yai idon shi akan bayanta, sam babu kuzari a jikinta ahaka ta fuce daga cikin kogon dutsen, Hasken ranane ya galle mata idonta da sauri ta lumshe su na ɗan sakanni kafin ta ware su tana ƙarewa ƙurmin Dajin kallo, Daddaɗar iskar dajin ce ta ratsa sassan jikinta ni’imtacciyar gaske, hatta sumar kanta sai kaɗawa take yi saboda ƙarfin iskar, saboda taurin kai irin na Angel da kasada, Ahaka ta soma tafiya tana nufar cikin dajin ita ala dole saita gano inda kurkukun ƙaddara ya ke, tun kan aje ko’ina ta fara tsorata da ganin ƙananun halittun da ke yawo Saman bishiyoyi, duk da haka bata sare ba taci gaba da tafiya hada ɗan saurinta da gudunta, ko takalma babu a ƙafarta. Tun bayan fitarta Danish Ya fito daga cikin kogon dutsen, ya goya hannayenshi saman faffaɗan ƙirjinshi Yana kallon bayanta, Ta yi matuƙar bashi mamaki, duk da ya fahimci babu hankali atattare da ita, in ba haka ba ta ya ya wanda ya tsira yake ƙoƙarin komawa ga halaka. Yarinta ce ke damunta da kuma son ƴan uwanta. Tana cikin yin tafiyar nan, kukan namun dawa Ya dakatar da ita cak ta tsaya tana ƙarewa wurin da take atsaye kallo, ba zato ba tsammani idanuwanta suka sauka akan Snake ɗin dake bin jikin bishiya yana ƙoƙarin saukowa ƙasa, zaro ido waje tai a gigice ta fasa ƙara tare da juyawa da gudun gaske tamkar zata tashi sama, majicin na ƙarasa saukowa yabi bayanta, tashin hankali duk ta bi ta rikice don ta fahimci ita yake bi, tun da uwarta ta haife ta bata ta6a yin tozali da maciji ido da ido ba sai yau da Allah ya haɗosu, Tarasa gane ta wace hanya zata bi ta koma cikin kogon dutsen. Danish ta dinga ƙwalawa kira kamar maƙoshinta zai 6allo, sai da ta gama galabaita cikin rashin sa’a tai tuntu6e da dutse gaba ɗaya ta tafi zata kife ƙasa, ƙiris ya rage ta kife ƙasa a lokacin da ba ta yi tsammani ba taji Ya damƙo ta tare da kwantar da ita saman chest ɗinsa. ƙanƙameshi tayi sosai ta fashe mashi da kuka tana zazzaga mashi masifa akan me zai barta ita kaɗai acikin daji? Idan ma don saboda ta yi mashi kafiya ne, bai ga ita yarinya bace, tun da fara mashi faɗa bai tanka mata ba, hannayen shi biyu suna tallabe da ita, sai da ta yi mai isarta, tukunna ta buɗe kumburarrun idanuwanta akan fuskarshi, tun daga kan tausasan red lips ɗinsa ta soma bi da kallo har izuwa ga dogon hancin sa kafin ta ɗauke idon nata ta ɗaura su kan sexy eyes ɗinshi masu matuƙar jan hankali. ƙoƙarin shagala su ke yi da kallon Juna, tunawa da ƴan uwansu da su ka baro a kogon dutse ne yasa tayi saurin katse masu kallon ƙurullan da suke bin juna dashi”Danish mu koma kada wani abu ya same su” girgiza mata kai yai in a smoky voice ya furta mata”ba abunda zai same su, ina sane dasu, na rufe kogon dutsen babu wani abun cutarwa da zai Iya tunkarar su”Sam hankalin bai kwanta da kalaman shi ba “Danish ni dai mu koma,” ashagwa6e tayi mashi maganar, ita kanta batasan ta sanya shagwa6a ba’ “Zamu koma, but before that, Inaso ki raka ni cikin Dajin in nemo mana abunda zamu ci, ko kina so su farka suna Jin yunwa ne”? Girgiza mashi kai tayi”a’a amma ni ba zan bi ka ba, Ka maida ni cikin kogon dutsen in ya so kai sai ka je nema mana abunda zamuci” kafe ta da ido yai, hakan yasa ta jefa mashi harara haɗi da murguɗa mashi baki, munin fuskarta bai hana shi ganin kyanta ba, musamman da ta yi mashi abunda ke jan hankalin shi gareta, Harara da murguɗe abun A jinin ta ya ke. “Idan ba za ki bi ni ba, Ga hanya nan ki koma kogon dutsen ni kin ga tafiyana” yai maganar tare da nufar Cikin dajin, da ido tabi bayanshi da kallo, ranta a 6ace yasan ba zata iya kai kanta ba shiyasa yace ta koma, Tunawa da macijin da ya biyota ne yasa ta zabura da gudu tabi bayanshi, Yana cikin tafiya yaji ta zura hannunta cikin nashi, ƙayataccen murmushine ya bayyana akan fuskarshi. Ta yi tsammanin Iya abincin da zasu ci ne zasu nemo, ba ta san plan Ya shirya mata ba, Yanayin Iskar dajin ba ƙaramin ni’ima ta saukar masu ba, Suna tafiya suna kallon Juna, wani irin Sanyi ne ke ratsa zukatan su, dakatawa tai dayin tafiyar ta ɗan kalli fuskarshi”Na gaji Danish ƙafata ciwo ta ke yi min” ba tare da ya amsa mata ba, ya juya mata bayan shi, ta gane me yake nufi, da sauri ta haye Saman bayan Ya miƙe ɗauke da ita, ba ƙaramin daɗi taji ba, shin me yafi ranta gata ga garkuwar kurkuku, ta ƙanƙameshi sosai, lumshe idanuwanta tayi sai faman shaƙar mashi fatar wuyan shi take yi, bai sauke ta a ko’ina ba sai abakin wani tabkeken ruwa mai gudana, Ta jikin dutse ruwan ya ke gangarowa tsaftatacce fari ƙal dashi. “Mun ƙaraso,” Jin abunda yace ne yasa ta ɗago da kanta, tana ƙarewa wurin kallo, nan ta ke ta ji tana sha’awar shan ruwan, Zuƙunnawa yai ta sauko daga saman bayan nashi, a jere suka tsaya suna bin ruwan da kallo, ga dukkan alamu ya burgesu . “Danish ƙishi na ke ji, nasan kaima kana ji, mu sha sai mu ɗebi wani mu kai ma su Parveen ko”? Ba tare da ya juyo ya kalli fuskarta ba ya soma magana”Wanka nake so nayi maki, saboda kinyi muni, jikin ki yayi datti” Har saida gabanta ya faɗi jin abunda yace, juyowa yai da fuskarshi ya kalleta tare da kashe mata ido ɗaya “za ki iya cire kayan ko in taimaka maki ne”? gabanta ne ya dinga faɗuwa sai ta ga kamar ya canza mata, babu alamun wasa akan fuskar shi yai maganar. Ganin yana matsowa kusa da ita, yasa ta juya da niyar ta gudu, ko ta ku ɗaya bata kai ga yi ba taji Ya damƙi ƙugunta, ƙarfi ba ɗaya ba, Duk yadda taso ta kubce mashi ta kasa, matseta yai a ƙirjin shi, A hankali Yai amfani da hannun shi ɗaya wurin zame rigar Jikin shi, tare da wandon kakinsa na Giant, ya rage daga shi sai short fari, saman gungurumeman dutsen dake agefen ruwan, ya jefar da uniform ɗinshi. kamar jinjira haka ya ɗauke ta, kaitsaye Ya nufi Cikin ruwan da ke gangarowa, ba yadda ta iya dashi, Tana kuka tana fadin bataso ya ƙyale ya rabu da ita, ahaka yayi mata wanka tass ya wanketa Kamar yayi amfani da sabulu ita kanta tayi mamikin yadda Jinin jikinta ke fita, Farar fatarta sol ta dawo har wani salƙi takeyi da ɗaukar ido, hatta uniform ɗin da ke ajikinta sun wanku sosai sun manne ma fatarta, kwantar da kanta yai saman broad chest ɗinshi, Ya cusa yatsun hannunshi cikin sumar kanta yana cuccuɗata da ruwa, Jinin da ya danƙare mata a cikin kan ya dinga fita, gashin kanta ya dawo ainihin launin shi dark brown mai kyan gaske, ba ƙaramin taimakonta yai ba da yayi mata wanka, Ita kanta tasan bazata iya wanke najasar dake a jikinta ba, ƙanƙame jikinshi tayi sosai la66anta na kerma take faɗin”sanyi Danish san yi ni ke ji, tamkar ana ƙara gudun ruwan sun jiƙe sharkaf acikinsa, sai da ya kammala tsaftace mata jikinta tukunna ya ɗaukota saman kafaɗarshi ya dawo da ita Gefen dutsen da ya ɗaura uniform ɗinshi. Tun da ya sauke ta ta faɗa ma faffaɗan ƙirjinshi, ta zagayo da hannayenta saman bayanshi, sai faman sauke ajiyar zuciya take yi, idanuwanta a lumshe, ita kaɗai tasan daɗin da ta ke ji, da farko taji haushi da ya yi mata wanka, amma yanzu ta fahimci Dalilin dayasa ya tursasa mata yin wanka, jikinta yayi mata daɗi wata irin ni’ima ke sauka, tamkar an yaye mata damuwar dake acikin zuciyarta, sun natsu suna sauraron bugun zuciyar junansu, irin yanayin da yafi son kasancewa tare da ita, yana son Angel dinsa fiye da yadda yake son kanshi, a shirye yake daya sadaukar da ranshi indai akanta ne” Fatar wuyanta ya ƙurawa ido fara sol sai ƴan tabannin da ba arasa ba, na gurjewar da tayi, ɗaura tafin hannayensa yai asaman bayan nata, “My Angel!” a kasalance ya furta sunanta shiru bata amsa mashi ba “Are you feeling sleepy?” kamar yayi magana da bango shiru taƙi buɗe ba ki ta yi magana, ƙoƙarin rabata yayi daga ƙirjinsa, sai dai taƙi bari ya ɗago da ita, ta yi tighting ɗin shi tamkar zata koma cikin shi, baiwar Allah, Dama abuƙace take da ta samu inda zata sassauta raɗaɗin da ke acikin zuciyarta, abubuwan da suka faruwa a rayuwarta ta soma tariyowa tun daga lokacin da ta mallaki hankalin ta, har zuwa rayuwarta a hannun fulanin Daji da kuma faɗowarta gidan kurkukun ƙaddara, Zafafan hawayene suka wanke fuskarta, jin shessheƙar kukanta ne yasa shi rikicewa ya shiga ambaton sunanta adabarbarce, daƙyar ya iya 6an6arota daga ƙirjinshi, eyes dinshi akan fuskarta ta runtse idonta “My Angel I don’t want you to dwell on what happened before, I know it hurts you, but please forget about the past. I don’t like to see you cry. tun da ya soma lallashinta bata buɗe idanuwanta ba, tsawon mintuna kafin a hankali ta ɗago da kanta tare da jingina bayanta jikin dutse. Matsawa yayi jikin ƙaton dutsen ya miƙa hannu ya ruƙo uniform ɗin shi, A tsanake Ya sanyasu a jikin shi “Zaki Iya jirana anan”? girgiza mashi kai tayi”tsoro nake ji, ka maida ni cikin ƴan uwana” yaso ta amince ko dan ya samu ya shiga cikin Dajin Ya nemo masu abunda zasu ci, kwantar mata da hankalinta yai”Yanzu zan dawo, bana so ƴan uwanmu su tashi da yunwa pls ki jirani anan, ba abunda zai same ki, kada kije ko’ina” bai jira amsarta ba, ya 6ace ma ganinta. Tunawa da cewa ita fa yanzu mai ƴanci ce yasa ta ɗan saki murmushi, har ta fara tunanin irin mugun kisan da za ta yi ma waɗanda su ka sadaukar da su, badajimawa ba ta soma Jin motsin tafiyar mutun a firgice ta buɗe idanuwanta lokaci ɗaya ta sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya ganin Danish ne ya dawo hannun shi a ruƙe da Zomayen Daji da ya yo masu farautarsu, ya ruƙe ƙafafuwansu da hannu ɗaya, yayin da ɗayan hannun ke aruƙe da gorar ruwan, mamaki ne ya kamata ganin zomaye, miƙa mata gorar ruwan yai da sauri tasa hannu ta kar6a, Acike take da ruwa, jera kafaɗa su ka yi suna tafiya suna satar kallon juna, abunda ya ɗaure mata kai yadda Danish yasan komai dangane da Daji mutumin da bai ta6a fita daga cikin kurkuku ba, Yanzu tadaina yi mashi kallon solo6iyo, A Namijinsa ta ke kallon shi. Lokacin da su ka ƙaraso Gaban Kogon dutsen, Atare su ka shiga Ciki, Ya ajiye zomayen saman korayen ciyayin da ke shimfiɗe ƙasa, ya ɗago da ido ya kalle ta, zanje na haɗo itace yanzu zan dawo, Ta amsa mashi da toh,’ Bayan tafiyarshi ta ajiye gorar ruwan ƙasa, kafin ta nufi shimfiɗar su, ba ta yi mamakin ganin ba su farka ba saboda ta riga ta gane aikin Danishi, gaban akwatin kayansu ta zuƙunna ta buɗe ta curo tsoffin uniform ɗinta, Cikin ƙanƙanin lokaci ta canza na jikinta da suka jiƙe ta shanya su daga wajen dutsen, dawowa tayi cikin kogon Agaban shimfiɗar ta zuƙunna tana ƙare masu kallo, idanuwanta akan Jemimah da Azeeza, daɗi kamar zai kasheta, a ƙagare ta ke da su farka su ga wurin da Allah ya kawosu tasan zasu sha mamaki da al’ajabi kuma zasu ji daɗin cika masu alƙawarin da ta yi. Sam ba ta ji motsin shigowarshi ba, har sai da yai mata gyaran murya tukunna ta waiwayo su ka haɗa ido da shi In zo in tayaka”? girgiza mata kai yai” a’a bana so ki wahala” miƙewa tayi tare da zuwa gabanshi ta zuƙunna tana ƙare mashi kallo, hankalin shi ya koma akan itacen da ya ke jerawa bayan ya kammala ya ɗauki duwatsun jiya da yai amfani wurin rura wuta, duk wani motsin shi akan idonta har ce mata yai “kije ki huta mana, ba kince kina jin sanyi ba? Ki ɗauko bargo” maƙe mashi kafaɗa tai alamar ba za ta je ba. Bawan Allah shiya zauna zaman gasa masu naman, sai maiƙo yake yi kamar an soya shi da mai, Kitsan jikin zomayen ne ke narkewa, bayan ya kammala ya ɗaura gasasshen naman da ya tsira Jikin icce saman faffaɗan ganyan da ya shimfiɗa a ƙasa. “Danish” ɗagowa yai tare da kallonta, bakomai ya gani acikin idanuwanta ba face Tsantsar tausayin shi “Kada ki damu kanki am ok, idan zan shekara inayi maku bauta ba zan gaji ba” kalamanshi sun ƙara sanya mata ƙaunarshi acikin zuciyarta. “A ina ka samu wannan gorar ruwa”? Tai maganar tana nuna ta da yatsa “A cikin Daji ba abunda ba zaki Iya samu ba, Hada kan mutun” murmushin gefen fuska ta saki, ga dukkan alamu zasu fara kafa nasu tarihin soyayyar tun acikin Daji. Ɗagowa yai da lumsassun idanuwanshi ya ɗaura su kan fuskarta “Can you eat by yourself? Or do I need to feed you?” Girgiza mashi kai tai” ka wahala sosai, ni ya kamata in baka da hannuna” ya ji daɗin maganarta har ya buɗe baki da niyar mayar mata da martanin maganarta, kwatsam! muryar Jemimah ta katsesu da wani irin sautin mai amo take kwaɗawa Angel kira amatuƙar gigice take fadin”Genie wayyo Allah Genie Zafi Jikina ƙaiƙayi nake ji” Ahanzarce Danish da Angel suka miƙe da sauri suka nufi shimfiɗarsu atare suka zuƙunna agabansu, Hannu biyu Angel ta sanya ta ɗauko ta zuwa saman jikinta, ta ƙanƙameta, Duk tabi ta furgice sai kuka takeyi masu tana harba ƙafafuwanta, Sautin kukanta ne ya farfaɗo da sauran ƴan uwan nasu, Batul ce ta fara miƙewa kamar fatalwa idanuwanta luhu luhu sun kaɗa jawur, baiwar Allah har faɗawa tayi sai uban haske, gashin kanta kuwa a hargitse yake, Buɗe idonta keda wuya ta sauke su akan na Danish dake kallonta, Muryarshi na ɗan rawa ya furta sunanta”Ba..tul” ɗauke idonta tayi daga kan fuskarshi ta mayar dasu Kan kogon dutsen da suke aciki saƙo da lungu tabi da kallo, kukan farin cikine ya kubce mata, Da sauri Danish ya ruƙo hannunta acikin nashi ya kwanto da kanta saman ƙirjinshi, sosai ta ƙanƙameshi tana cigaba da yin kukan. Farkawa Gabriel yai zumbur ya miƙe yana ambaton sunan Azeeza, da ita ya kwanta acikin ranshi, sai tsuma yake yi yana fitar da huci, Cikin shessheƙar Kuka Angel tace dashi”She’s still alive! Azeezar mu bata mutu ba, suna araye,” Karaf maganarta ta sauka akan kunnan sauran ƴan uwan su da suka farka, a zazzaune suka miƙe Tun daga kan Javed, Naufal da Hannah mutun uku ne basu motsa ba, parveen Azeeza da Haris, ga dukkan alamu sun farka daga bacci sai dai sun kasa motsawa, Jikinsu ba ƙoshin lafiya, ko yatsan su sun gaza ɗagawa. Hankulansu gaba ɗaya ya koma kan su, kowan nan su fuskarshi akumbure take suntum, babu walwala ko annuri, dagaske Azeezana bata mutu ba? Gabriel ne yai tambayar yayin da idonshi ke fitar da hawaye, Danish ne ya bashi amsar tambayarshi, Tsabar farin Cikine ya bayyana akan fuskarshi, Rumfa yai ma azeeza da ƙirjinshi motsa la66anta da take yi ne ya tabbatar mashi da cewa tana araye sungumarta yai tare da ɗaurata saman laps ɗinshi, Danish Ya miƙa mashi gorar ruwa don ya bata tasha, Yatsun hannun shi na kerma ya kar6a ya kafa mata abaki, ruwan yana wucewa ta maƙoshinta sai dai ta gaza buɗe idonta, Farin Ciki duk ya cikasu, Naufal ne ya ɗauki Parveen Baiwar Allah anji jiki, miƙa mashi gorar ruwan Gabriel yai ya kar6a yabawa parveen kamar zata haɗa da gorar duka ta shanye, Sai lokacin Danish Ya raba jikin shi daga na Batul Ya rarrafa zuwa gaban Haris dake kwance kamar matacce ya ɗaura hannayenshi biyu wurin ɗago dashi ya kwantar da kansa saman kafaɗarshi, Cikin sanyin murya ya ke ambaton sunanshi”Haris! Haris!” shiru bai amsa mashi ba, jikin shi yai zafi sosai babu alamun lafiya atattare dashi, ɗaura tafin hannun shi yai saman ƙirjinshi bugun zuciyar haris a hargitse yake fita, hakan ba ƙaramin tada mashi hankali yai ba, Yana fargabar wani abu ya same shi. “Ɗan uwana Rabin raina nasan kana jin muryata pls kada ka bari damuwa tayi maka illa, ina atare da kai” jin muryar Danish acikin kunnanshi yasa shi ƙoƙarin motsa la66ansa sam sautin yaƙi fita, Fahimtar hakan yasa danish matsar da kunnanshi saitin bakin Haris “Deeja ta mutu! Na rasa Deeja Danish! Bazan iya rayuwa ba tare da ita ba, zuciyata nauyi take yi min, ka taimaka ma rayuwata” a hargitse yake magana, tsananin tausayin shi ne ya kama Danish, dama sai da ranshi ya bashi cewar akan Deeja ne ya shiga mawuyacin halin nan. “Haris ka kwantar da hankalin ka, ba mu da tabbacin suna araye ko sun mutu, tun da har su Azeeza suka farka bayan munyi tunanin sun mutu ina saran suma za’a iya samun masu rai acikin su” cikin jin ƙunar rai Haris ya furta”Danish idan har hakane deejana tana araye azzuluman mutanancan zasu Iya kashe min ita, mun barsu fa a kurkuku, Danish ka koma ka ɗauko min ita, idan baso kake na mutu ba’ sosai ya sanya mashi kuka, Rarrashin shi ya dinga yi yana lalla6a shi duk don ya samu ciwon nashi ya lafa. Waɗanda suka fi jin jiki a cikinsu Jemimah ce da Azeeza sai Haris, Ita parveen tunda taji ta ajikin Naufal ta wartsake, har tana iya ambaton yunwa take ji, Jemimah kuwa taƙi daina yi masu kuka, Sautin kukanta ya karaɗe kogon dutsen kamar ana zare ranta, Hankalin Angel duk yabi ya tashi, Ta rasa ya zatayi da ita, Cikin muryar kuka take yiwa Danish magana akan yazo yataimaka mata, Har ƙwara Azeeza tun da ta ƙanƙame Gabriel bata ƙara motsawa ba, ta lafe mashi idanuwanta arufe suke gam. Sun rasa ya za su yi dasu, kukan jamima ba ƙaramin tsuma zuciyarsu yake yi ba, taji jiki baiwar Allah, Sunga ƙoƙarinta da har ta iya yin kukan, azabar raɗaɗin gabanta ne ya addabeta, ta rasa ina zata tsoma ranta taji daɗi, fuskarta jaga jaga da hawaye, yarinyar da bata wuci shekara goma da watanni ba, ta rasa budurcinta, su kansu sunyi mamakin da ta iya rayuwa, lokacin mutuwarta ne baiyi ba, Tana kuka suna kuka, Babu wanda bai zubar mata da ƙwalla ba in ka cire Danish, kwantar da Haris yai saman shimfiɗar, jikinshi na tsuma ya nufi Angel Ya sanya hannu biyu ya kar6i jemimah daga hannunta, fucewa yai da ita daga Cikin kogon dutsen basu san Inda ya nufa da ita ba. Tsawon mintuna sai gashi ya dawo rungume da ita a ƙirjinshi, ajiyar zuciya suka sauke Jin tayi shiru tadaina kukan, Akwatin kayansu ya buɗe ya ɗauko mata rigar sanyi, cikin waɗanɗa tsohuwa ta yi masu kyautarsu, Ya sanya mata a jikinta, ga dukkan alamu wanka ya yi mata, bayan ya kammala sanya mata rigar, ya curo mata hula ya zura mata akanta, ya kuma ɗauko Mayafin kayansu, Sai kallon shi suke yi, Danish ya basu mamaki, Asaman bayanta ya yafa mata mayafin ya miƙe tsaye yana lallashinta kamar yadda akeyi wa jarirai, jemimah ta natsu sai faman lumshe idanuwanta takeyi, Jikinta ya lafa sosai ta daina jin raɗaɗi ciwo nata, juyowa yai tare da nufar Angel ya miƙa mata jemimah, “Zan tafi da Azeeza ki basu naman su fara ci” amsa mashi tayi da toh, ta kar6i jemimah tare da rungume ta a ƙirjinta, bayan Ya ɗauki Azeeza Ya fuce da ita, janyo masu naman tayi zuwa gabansu, duk da halin da suke aciki hakan bai hanasu Cin naman ba, Saboda matsiyaciyar yunwar da suke ji, Mutun ɗayane ya kasa cin naman, ko da Javed Ya tallabo shi ya zaunar dashi Yana tura mashi abaki, Amayar dashi ya dinga Yi, ruwa kaɗai ya iya sha, sun damu da rashin lafiyar Haris Ya galabaita sosai, Jemimah dai ta ɗanci naman Angel ce take bata abaki, har yanzu bata buɗe idanuwanta ba, balle ta san a ina suke. Shigowa cikin Kogon Danish yai Hannunshi ɗauke da Azeeza, Ya wanke ta tass jikinta sai kakarwa yakeyi, tunkafin ya ƙaraso Gabriel Ya buɗe akwatin kayansu ya ɗauko mata rigar sanyi tare da mayafi, Bayan Danish Ya miƙa mashi ita, Ya sanya mata rigar asaman uniform ɗinta, Ya ɗaura mata mayafi saman kanta, kafin ya kwantar da ita saman ƙirjin shi, Abaki ya dinga gutsuro namanta yana tura mata abaki daƙyar take iya taune shi, Hakan ba ƙaramin daɗi yayi masu ba, duk fa wannan budurin da sukeyi Azeeza da Jamimah da Parveen basu san cewa sun bar kurkukun ƙaddara ba, Saboda basa acikin hayyacin su. Danish bai samu damar cin nashi naman ba, Jira yai sai da suka kammala ɗaya bayan ɗaya ya raka su zuwa bakin ruwan nan suna yin wanka, da taimakon shi Haris ya samu yayi wanka jikin shi ya ɗanyi mashi daɗi, bayan sun kammala Ya ƙara haɗo wasu itacen Ya kunna masu wuta Kogon dutsen ya ɗumama sosai Sanyin da su ke ji ya washe, sun cinye namansu duka, Kaɗan Danish ya samu yaci, kamar masu zaman makoki haka su ka zauna kewaye da wutar da ke ci, Suna kallon junan su kowa da abunda ya ke saƙawa aran shi, jemimah tuni bacci ya ɗauketa kamar jinjira haka Angel ta matseta a ƙirjinta, haka azeezama bacci ne ya ɗauke ta, tana kwance saman jikin gabriel, Haris ya langwa6a kanshi saman kafaɗar Danish, Batul ta ɗaura kanta saman kafadar Angel, Parveen tana a kwance saman ƙirjin naufal, da hannu biyu ya tallabeta, haka zalika Hannah tana arungume jikin Javed, sun natsu suna sauraron kukan namun dawan dake hargowa acikin Dajin, ba zaka ta6a fahimtar yanayin da su ke a ciki ba, kowa da abunda yake saƙawa aranshi. *OBIE STATE* In Abuja🏙 *Boss Bature✍️ Mu haɗu gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*KURKUKUN ƘADDARA*_ _The Prisoners E8🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* ~Middle step~ _A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._ *Obie Estate*Haɗaɗɗiyar Daular arziƙi, Aljannar duniya da babu tamkarta a faɗin nahiyar Africa, Hamshaƙin Estate Ne Da ya haɗa tanƙama tanƙaman luxury Villas, da duk wani Ababen more rayuwa, Kayan alatun da ke a cikinsa kaɗai abun kallo ne, dollar ta yi kuka awurin ƙera ginin, yana da 6angarori da dama, kama daga katafaren Gate ɗin shiga Estate ɗin wanda Jami’ae ne ke tsaron shi Sojoji da ƴan sanda Ko sauro bai isa Ya ƙetara ƙofar shiga gidan ba saboda tsaron da ke gare shi, ba iya mutane ba hada na’urorin da ke sanya ido ga duk wani mai shige da fuce, kowace kusurwa ta villas ɗin tana maƙale da na’urorin cctv camera, daga bakin faffaɗan gate ɗin Santalelen titi ne zai isar da kai ga Interior ɗin daular, akwai Harabar ajiye motocinsu, Gardens da swimming pools area, Ga zoo wurin da ake kiwata dabbobin gidan. Kowani Villa na estate ɗin Yana da nashi kayan alatun na more rayuwa, parts ɗin da ke a cikin kowani gida ya haɗa da Haɗaɗɗun falullukansu waɗanda suka ji jigunannun furniture, Bedrooms, Dining rooms, Kitchens, Bathrooms, Laundry rooms, da sauransu, akwai Ƙayatattun dogayen benaye zubin twin stairs da U-shaped stairs, Idan ma mutun baida ra’ayin Hawa Benan Kowane Villa yana ɗauke da residential elevator wadda aka fi sani da lifter, tun daga Hawa na farko zata ɗauki mutun har izuwa hawa na Uku, dai dai da cokalin amfani na gidan babu wanda aka ƙera a ƙasa Nigeria, kaf kayansu daga ƙasar waje ake shigo dasu, mai karfin imani ne Kaɗai zai iya rayuwa acikin estate dinsu ba tare daya shagala daga yin ibadarshi ba, sai dai ta inda masu rayuwa cikin gidajen zasu burge ka Allah ya hore masu baiwar Ilmin duka na addini dana zamani, wayayyun mutanene masu daraja da ƙima a idon duniya, Sun Iya takun su ba zaka ta6a Iya aibatasu ba, saboda kyawawan ɗabi’unsu da halayansu, komai nasu is Extraordinary. Tun da garin Allah ya waye masu aikin gidan su ke ta kai komo, kowaccensu ta yi dressing cikin chef’s uniform launin farare, ƙwararru ne a 6angaren girke girke da gyaran gida, basu wasa da aikin su, Suna ba lokacin mahimmancin sa, kuma suna takatsantsan wurin kula da buƙatun mutanan gidan. A tsastsaye su ke a Cikin Katafaren Kitchen ɗin gidan mai girman gaske, A shaƙe ya ke da kayan Amfani, ko’ina a tsaftacensa ya ke tamkar ba amfani su ke yi da shi ba, aiki su ke yi tuƙuri babu kama hannun yaro, Matasan Ƴan mata da manyan su, wasu suna aikin wanke nama wasu suna yanke yanken kayan lambu agaban cutting board, yayin da wasu su ke agaban manyan gass cooker suna kula da girkin da suka ɗaura, akwai waɗanda ke a tsaye in front of kitchen microwave suna aiki. Ƙamshin girkinsu ya karaɗe ko’ina tun daga cikin kitchen ɗin har izuwa Babban falon gidan. Babbar macace ta shigo kitchen ɗin domin duba masu aikin don ganin yadda komai ke gudana, A ƙalla za ta kai shekara 40 a duniya, Ta kasance ɗaya daga cikin Masu yi masu hidima a gidan, ita ce head maids shugaban ma’aikatan Cikin gidan, Macace mai yawan fara’a ga son mutane, ma’abociya son Shigar fararen Kaya, A yanzu haka pakistan ne a jikinta riga da wando farare ƙal anyi masu adon duwatsu launi daban daban, ƙafarta na sanye cikin flat shoes, bakowa bace wannan face *DIVYA* ba’indiyace amma sunfi kiranta da *HAJJATY* tun da ta shigo kitchen ɗin masu aikin suka fahimci itace tazo dubasu nan fa suka ƙara dage damtse suna aiki duk don su ku6uta daga faɗanta. A hankali ta ke zagaye Kitchen ɗin, Hannayenta a goye saman ƙirjinta, ɗaya bayan ɗaya take binsu da kallo, na ɗan wani lokaci kafin tayi masu gyaran murya, kusan atare su ka ɗago suna kallonta, Hannu ta tafa masu “Aikin ku yana kyau, You ladies Are doing a fantastic job, everything smells delious, i’m sure ɗanɗanon girkin zaiyi daɗi kamar yadda ƙamshinsa ya ke da daɗin shaƙa, Ina ƙara jinjina ma ku,” ta ƙarasa yi masu maganar tare da ɗaga masu babban yatsan hannunta na dama alamar Jinjina. Murmushi ne Ya bayyana akan fuskokin su, ba ƙaramin daɗi suke ji ba, Idan hajjati ta yabe su, suna matuƙar sonta kuma suna girmamata saboda kyawun halayanta da ɗabi’unta. “Dame dame aka kammala ne”? ta yi tambayar tana kallon faces ɗinsu, Abla ce ta soma Yi mata jawabi “Kebab with chips, Beef shawarma, burger and pancakes,...” kusan abu goma ta lissafa mata, Jinjina kai Hajjaty ta ɗanyi kafin ta ɗaura da cewa”Kada na katse maku aikin ku, lokaci Yana ƙurewa, Ku hanzata ku kammala, “ “An aikawa Hajiya saratu Breakfast ɗinta!”? da sauri Safa tace”yanzu nake shirin zuwa in kai mata, Nice nike duty part ɗinta” Gyaɗa kai Hajjaty ta yi. “Okey, shirya min fresh fruit ki haɗa min da kakkauran tea,” Wadda aka kira da Sarah ta amsa mata da toh, ba tare da 6ara lokaci ba ta shirya mata kayan marmari a cikin ƙayataccen wooden tray, tare da cup of tea, ta miƙa mata hannu biyu tasa ta kar6i tray din tare da juyawa ta fuce. Bayan fitarta, Fira ta 6arke a tsakaninsu “Safa ashe ke ce kike duty a part ɗin Aunty jarabatu zaki sha Masifa, “ Abla ce tai mata maganar, murmushi suka saki, sophia tace”Ai hajiya saratu ba daga baya ba, In dai wurin Iya masifane, Last time fa da naje kai mata abinci cewa ta yi wai na gutsiri ƙafar kaza, hada cewa ita bata yarda damu ba, wama ya sani ko mun saka mata guba acikin abinci donta ci ta mutu,” dariya suka saka “Tana da wuyar sha’ani bata yarda da kowa ba, In ba wannan Mijin nata ba, Uban son banza suruki da zaman gidan surukai Ko kunya babu” sophia ce tai maganar, Safa tace”Ai koni na samu wurin zama agidan nan abunda zanyi kenan, waman taraka bati siddan, shiyasa a kullum nake roƙon Allah ya bani bugun zuciyar family ɗin, Wlh idan na Aure shi nadaina sakin baki ina bacci, nafilfili zanta yi akan Allah ya dawwamar da auran mu don nasan maƙiya da mahassada ba zasu bar mu mu zauna lafiya ba, Musamman Mahaifiyarshi uwar Ji da izza, kinga matar nan bata ɗaukar raini batason Mu’amala da bare....” tun da ta fara zuba suke binta da kallon rainin wayau saida takai aya tukunna Abla tace”you don’t ave sense, Dama najima da zargin kwakwalwarki ba dai dai take aiki ba, Ko Jazz da muka raina wlh yafi ƙarfinki, Ni kaina ba zance bana son Owais ba, amma ance abunda yafi ƙarfinka ka haɗa shi da baka so” kwa6e fuska Safa tai”kiyi min fatan alkhairi kawai, Nima a hausa novels ni ke jin irin hakan na faruwa, mafi yawanci zaki ga ƴar aiki ta auri ɗan masu gida, wani sa’in ma mai gidan ta ke aurewa....” sautin dariyarsu ne Ya hana ta ƙarasa maganar, suna fira suna aiki, “Safa kina atare da wahala, in dai ko zaki cigaba da tunanin zaki samu abunda ki ke so kamar yarda ki ke karantawa ahausa novels, Ni Bance baya faruwa ba amma Allah a zamanin da mu ke ciki zaiyi wuya, mai kuɗi sai ƴar mai kuɗi, talaka sai ɗan talaka, Ina jiye maki tsoron heart attack ya kama ki silar son wanda bai son Kina yi ba, a ƙarshe ki ƙare a emergency room” Dariya suka saki gaba ɗayan su, kwata kwata firar da suke yi bata ɗauke masu hankali daga yin aikin su ba, manyan cikin su ne kadai basa magana sai dai idan sun faɗi abunda ya basu dariya su ɗan murmusa. “Ni takaici na magadan gidan nan basu da yawa, duk irin tarin dukiyar nan ace Iya mutun goma sha biyar ne ke da gadonsu” Abla ce tai maganar. Abla tace”Nikaina abun na damu na, Yana yi mun ciwo a zuciya, na rasa gane meyasa basa son haihuwa, daga mai ƴa’ƴa biyu sai mai ƴa’ƴa uku, Allah ya hore masu wadatar arziƙi sai ƴa’ƴa ne zasu gagare su? Abun na ƙona mun rai, komai nasu na rayuwar turai, Mu da zasu taimaka su Aure mu, duk bayan ƴan watanni zamu dinga sakar masu ƴa’ƴa tuni zamu cika famiy ɗin” Maganar Abla ba ƙaramin dariya ta basu ba, Sofiya tace”Sannu kaza suma ai suna son ƴa’ƴan, sannan bada son ransu bane ba su haihuwa, Ƙaddarar su ce ta zo masu ahaka, naji labari a bakin Hajjaty saboda tafi mu daɗewa a gidan, Suna haihuwa amma ƴa’ƴan basu zuwa da rai, A mace ake haihuwarsu yawanci da zarar sun yi haihuwar fari da ta biyu zaiyi wuya kiga sauran sun rayu a matattu su ke haihuwarsu, Allah ni tausayi suke bani, Musamman prime minister Hateem shifa Bai ta6a haihuwar ɗa Namiji ba, shi da matarshi Gimbiya mujeedat, ƴa’ƴa biyu duka mata, rashin haihuwarsu ba ƙaramin gi6i yai masu ba arayuwarsu, Ki duba fa hateem shine yafi kowa arziƙi a family ɗinsu daga shi sai sharafudeen,” mamakine akan fuskar Wasu daga cikinsu waɗanda basu daɗe da fara aiki ba “Abun da ɗaure kai, Kuma an duba lafiyarsu? Ko dai wata lalurar ce da suka gada tun kaka da kakanni”? “Ko ɗaya, Tun daga ƙasa Nigeria har zuwa ƙasashen waje an bincika lafiyar kowan nan su, Ba su da wata matsala da ta shafi ƙwayoyin haihuwarsu, lafiyar su ƙalau, har manyan malaman addini saida kakansu ya sanya don su bincika mashi meke faruwa a zuri’arshi, Sakamakon ɗaya ne dana asibiti, basu da wata lalura,” Jikin su duk yai sanyi, Basu ta6a sanin zancen haihuwar da matansu keyi yara suna zuwa ba rai ba sai yau da sophia ta sanar da su. “Allah mun tuba ka yafe mana, shiyasa akace zato zunibi koda ya kasance gaskiya, Gulma ba ta yi rana ba, Mune kullum tsegumin mu akan suna yin irin rayuwar turai ba su son haihuwa ashe ba laifin su bane, jarabtace daga Allah” murya asanyaye Safa Tayi maganar. Abla tace “Na tausaya masu, kuma In sha Allah zamu ta ya su da addu’a, akan Allah ya yaye masu lalurar da ke damun su” shiru suka ɗanyi Na wani lokaci, daga bisani Safa ta shirya Kayan breakfast ɗin Hajiya saratu A Babban tray ta jera mata su, Bayan fitarta daga Cikin kitchen ɗin su ka ɗaura da wata firar, sam basa gajiya da firar Familyn Obinna. “Muna fa da gagarumin bikin ranar zagayowar Haihuwar Obie, Nasan za’ae shagali na kece raini, za’a yi 6arin Dollar da pounds, Aranar zamu ga Zaratan ƴa’ƴan Obinna da Jikokinshi waɗanda basa a ƙasar, Ina da tabbacin Owais ma zai halarta” Fuskar Sophia ɗauke da farin Ciki tayi maganar, Abla tace”Anya ko Owais zai zo? Kinsan fa halinshi, samun lokacin shi abune mai wuya” “ai ko baiyi niya ba sai obinna Ya matsa mashi akan ya zo, Kinsan fa kaf cikin jikokinsa yafi ƙaunar Owais, kowa yasan da wannan zancen, Kinga ko ba zai so ayi shagalin nan ba tare da Owais Ya halatta ba,” acewar Abla Murmushi Sopy tayi “Can’t wait to see Allah Ya nuna mana Lokacin, Dole naje ayi min wankin ido, don na samu damar ƙare Mashi kallo” “Da rabon kisha mari, Owais baya son Kallo Idan Yana magana mutun bai isa Ya ɗaga ido ya kalle shi ba, Sannan ba’a katse shi, Sauƙin shi ɗaya Idan har kika karanci halayanshi da ɗabi’unsa tsaf zaku zauna lafiya, mutunne mai sauƙin kai baida girman kai, Yana da tausayi ga taimakon na ƙasa dashi.....” tun da ta fara jera masu Kyawawan halayanshi bata tsagaita ba har saida Landline ɗin dake a bakin ƙofar fita kitchen ɗin ta yi ringing tukunna ta dakata da yin magana, da sauri Sophia ta fuce ta je ta ɗauki landline ɗin Ta ɗaga kiran daya shigo, Cikin girmamawa tayi sallama, Jikinta sai 6ari yake yi. “Cofee....” Iya abunda Taji an furta mata acikin wayar, jin yayi rejecting yasa ta zame ta daga saman kunnanta ta ajiyeta saman table, Dawowa Cikin kitchren ɗin Tayi Hankalinsu gaba ɗaya ya dawo kanta. Har suna haɗa baki wurin tambayar ta “Wanene Ya kira” kwa6e fuska tayi tare da cewa”Nakasa gane muryar wanene acikinsu, Zaid ne ko Zayn, Coffee su ke buƙata, wa zai kai masu”? Ta yi tambayar tana kallon sauran. Shiru babu wanda yace zai kai, saboda Mugun tsoron shiga part ɗinsu suke Yi, saboda masifarsu,” “Kinga tun da ke kika ɗaga Kiran nan Ki lalla6a ki je kawai ki kai masu awuce wajen” Acewar Abla, Yamutsa fuska marwa ta yi, Ba yadda ta Iya don dole ta haɗa masu coffee acikin mugs guda biyu ta ɗaura saman Plate ta fuce daga cikin kitchen ɗin. Tun lokacin da Able ta fita hannunta ɗauke da tray Na breakfast ɗin Hajiya Saratu, Kai tsaye ta nufi Part ɗinsu, Tun kan ta ƙara sa gaban ƙofar ɗakin ta daddaɗan ƙamshin turarenta Ya daki hancinta, macace mai son ƙamshi ga iya ɗaukar Wanka, A bakin door ɗin Ta tsaya tare da Yi mata sallama, daga cikin ɗakin tajiyo muryar Hajiya saratu “U can come in” A hankali ta tura ƙofar ta shiga, Hajiya saratu tana azaune tsakiyar Katafaren gadonta, jikinta na asanye da jallabiya, Kanta babu Kallabi Kitson zanene all back Wutsiyar gashin ta sauko har saman kafaɗarta, fararen idanuwanta suna a manne da farin glass medicated, tana da duhun fata mai kyan gaske, Hutu ya zauna mata, Hankalinta gaba ɗaya yana akan tsadaddar Apple Laptop ɗin da ta ke yin operating, ga dukkan alamu aiki ta ke yi. “Once you’re done looking at me, please put the food on the table and leave my room.” Muryarta ce ta fargar da Safa daga kallon ƙurullan da ta ke bin ta da shi, Adabarbace ta gaishe da ita”Ina kwana Hajiya,” Guntun tsoki taja ba tare da ta amsa mata ba, ko kallo ba ta ishe ta ba, asaman front table din bakin gadon, Safa ta ɗaura mata tray din “ko akwai wani abu da ki ke buƙata “? cikin Jin shakkarta Safa ta yi mata tambayar don tasan halinta, in har bata ba mutun iznin tafiya ba, yai yunƙurin Juyawa zai tafi atsawace zata ce mashi da Iznin wa! Safa har ta gaji da tsayuwa shiru bata tanka mata ba, tamkar bata san da mutun awurin ba, Halinta ne share mutane, sai da ta mula ta sha iska tukunna ta ba ta zinin tafiya, bayan fitar Safa daga ɗakin, Ta dakata da yin aikin laptop ɗin, Yunƙurawa tayi tare da kai hannu ta damƙo Burger Ta soma turata abakinta tana ci, Bata wasa da Cikinta, Cikin ƙanƙanin lokaci ta handameta, ta kuma janyo Chicken wings tana ci, baya tagama ta ɗauki bowl ɗin dake shaƙe da plaintain chips hannu baka hannu ƙurya kamar mai fama da cutar yunwa, Saida ta lamushe komai, a ƙarshe ta kora da ruwan lemu mai sanyi. “Daɗina dake bakya wasa da Cikin ki,” Jin muryar Mijin nata yasa ta ɗago da eye balls ɗinta akan fuskar shi, Daga cikin toilet ya fito waist ɗinshi ɗaure da towel, Ƙirarshi tamkar ɗan wrestling, Kakkarfan mutunne Jibgegen ƙato, Kyakkyawan ba’indiye Sumar kanshi akwance luf saman kanshi, Ga wani kwantaccen saje gefe da gefen doguwar fuskarshi, ‘ ta6e mashi baki Tayi”meye haka? Bana hanaka yawo da towel a qugunka ba? Yanzu da ace mai aikin nan tana acikin ɗaki ka fito fa? Fuskarta aɗaure tayi mashi maganar, Matsawa yai kusa da ita yaɗan ranƙwafa saitin fuskarta”yaushe zaki daina kishina? Murga mashi baki tayi”Bansani ba, Ni dai na faɗa maka, Karka kuskura ka ƙara fitowa ɗaure da guntun abu a qugunka bana son ta6ara” Ido cikin ido suke kallon Juna. “Ƴa’ƴan mu Uku, kowan nan su Ya mallaki hankalin shi, Na yi tsammanin zaki rage kishi na da kike Yi” harara ta watsa mashi”pls Ka wuce ka je ka sanya suturarka, bana son ganin ka ahaka” Hannu ya kai yana ƙoƙarin warware towel ɗin gabanshi da sauri ta damƙi hannayenshi aɗan fadace tace”Pravin meye haka? Yarinta ce fa wannan”? Kashe mata ido ɗaya yayi fuskarshi ɗauke da murmushi yace”indai ina atare dake bazan ta6a girma ba, saboda tsantsar ƙaunar da kike nuna min” ta6e baki Saratu Tayi”naji yanzu kaje ka sanya suturarka, Sannan me kake son Ci insa akawo maka” Murmushin fuskarshi bai washe ba yace”abunda kika ci shi nake sonci abar ƙaunata, naga ma har kin kammala naki breakfast ɗin why ba ki bari na fito munci atare ba?” Ɗaure mashi fuska tayi “Pravin mu fa ba ƙananun yara bane da zaka tsaya kana gayamin kalaman Soyayya, ko da ya ke nafa tuna kufa indiyawan nan bautawa soyayya kuke yi har ku tsufa kuna abu ɗaya” cikin Zolaya ta ƙarasa maganar, gyaɗa kanshi yai”komi zaki ce bazanji haushin kalamanki ba, Amaryata kuma uwargidana, sannan uwar ƴa’ƴana abun alfaharina,” lumshe ido ta ɗanyi idan zata biyewa pravin ba zai barta taci gaba da yin aikinta ba, gwanine a fagen Iya soyayya da daɗin baki, Ya ƙware wurin Iya jan hankalin mace. “Romeo, now your Juliet is at work, I’m almost done, zansa a kawo maka breakfast ɗin ka, Ni da kaina ma zan baka abincin abaki” Amsa mata yai da Okey, Daƙyar ta lalla6a shi Ya miƙe ya nufi Cikin ɗakin Yana tafiya tana satar kallon Bayanshi, a gaban closet ɗin kayanshi Ya tsaya tare da kai hannu ya buɗe “My Juliet ba ki faɗa min kayan da ki ke so In sanya ma”! Murmushi ta saki”Yau babu aiki, ka samu hutu don haka Nafi sha’awar ganinka Cikin shigarku ta al’ada, Ya gane me take nufi, riga da wando Ya curo kalar na mazan Indiya ya sanya su ajikinshi, sun bi shape din jikinshi yadda kasan matashin saurayi saboda haɗuwarshi. Bayan ya kammala Shirya kanshi, Hajiya saratu tasa aka kawo mashi breakfast, Da kanta take bashi abaki Yana ci, mugun son shi ta ke yi, ta mutu akan pravin, kamar yadda shima yake ƙaunarta, Allah Ya hada jininsu. Babu mai cin moriyarta irin Mijinta, komai nata mallakin shi ne. Lokacin Da Sophia ta ƙarasa Bedroom ɗin twins dake acan Upstairs Second floor, Jikinta na kakarwa ta yi knocking ƙofar, almost 3 times kafin tajiyo muryar ɗaya daga Cikinsu “you can come in” Numfashi taja kafin ta tura ƙofar Haɗaɗɗen bedroom ɗinsu, Sanyin A.c da ƙamshin Turarensu ne Ya daki hancinta har sai da ta lumshe idanuwanta saboda tsabar yadda ƙamshin Ya kurɗaɗa ta ƙofofin Hancinta, tunkan ta shiga ciki Ta hango Ɗaya daga Cikinsu A tsaye Gaban tanƙameman dressing mirror Daga shi Sai short a jikinsa launin ja, Yayin da twin brother ɗin shi yake a kwance saman gado rabin jikin shi lullu6e da duvet. Kyawun surarsu sak irin na mahaifinsu Pravin, tamkar yayi kakinsu. Muryarta na ɗan rawa tace”Barka da safiya yalla6ai, Ga coffee ɗin Ina zan aje’ ba tare da ya juya ya kalle ta ba yace “On my head” tuni tasha jinin jikinta, Batasan Ya zatayi ba, Zaid dake a kwance saman gadon Ya ɗaura ƙafarshi ɗaya saman front table ɗin gaban gadon. “Is that how your parent taught you to enter a room without saying ‘Assalamu Alaikum ? Ɗakin kafurai kika shigo”? Muryarshi tamkar ta mashayin giya “Afwan yalla6ai, kafin in shigo saida na fara yin sallama, wata’ƙil baka jini ba ne” A sukwane Ya juya yana binta ɗan iskan kallo “Am I deaf?” girgiza mashi kai tayi muryarta na kakarwa tace “That’s not what I meant, sir...” bai bari takai ƙar ƙarshen maganarta ba, ya nuna mata ƙofar fita Aɗan tsawace ya furta “Oya Go back ki sake yin wata sallamar” fuskarshi a murtuke yayi maganar, Idanuwan sophia tuni sun ciko tab da ƙwalla, Jiki asanyaye ta juya ta koma waje. Kware Murya tayi”Assalamu alaikum” shiru bai amsa mata ba, shiga ciki tayi”Sir nayi sallamar in shigo? Coffee ɗin Yana hucewa” Kafin Ya bata amsa Zayn dake kwance saman gado ya furta “I didn’t hear it. Go back and make another greeting” Tayi mamakin Jin muryarshi duk a tunaninta bacci yake yi, ashe idonshi biyu, “ Maƙoshinta tamkar zai 6allo ta ƙara kware murya wurin Yi masu Sallama, Tun tana yi da marmari har ta fara gajiya, idanuwanta sunyi luhu luhu, A ƙalla tayi masu sallama kusan sau Goma sha biyar ba tare da sun bata iznin shiga ɗakin ba, Har saida Coffeen hannunta Ya salafce, sai da suka tabbatar Ta jigata sosai tukunna Zaid yace da ita ta shigo ciki, hawaye nabin kuncinta ta shigo. Kishingiɗe ta samu zayn ya ɗaura kanshi saman pillow, Ko kallon arziƙi bata ishe shi ba, jiki na 6ari ta nufi Table zata ɗaura plate ɗin, Kakkausar Murayar zayn ce ta dakatar da ita “Don’t you dare put that on the table! Ki koma ki canza wani coffee ɗin, wa zai sha abu ya salafce” juyawa marwa tayi tana kuka ta fuce daga Cikin ɗakin, ko a jikinsu, sun Iya rashin mutunci da mugunta idan suka so, duk rana ta Allah sai sun sanya ɗaya daga cikin masu aikin gidansu zubar da hawaye. “Bro, when are we going back to America?” Zaid ne yai maganar while sitting on the dressing table chair. Yatsina fuska Zayn yai “we have no way out, Zaid, seriously, naji takaicin tursasa mana dawowa Nigeria da obie yai, Ya hana rayuwarmu sakat, mu kaɗai mu ka tsone mashi ido, ga Owais can kamar tsuntsu Yana shawagi a ƙasashen waje sai mu da muka tsone mashi ido, nifa na gaji da halin dattijon nan, na rasa zaman me yake yi acikin duniyar nan, duk shekara sai na sayi sabon likafi da miski na mutuwarshi but yaƙi tafiya” Ranshi a6ace yake magana Zaid dake kallon ɗan uwan nashi yana murmushi yace” I know what you’re mad about” Yatsina fuska yai”Kai ma ɗin itace damuwarka, Ummin america ce silar komai, “ Yana magana a harzuƙe ga dukkan alamu an fama mashi raunin dake acikin zuciyarshi. “Everything about her is different. From the first day I saw her, I knew she was a classy woman with a magnetic personality that could captivate any man.” lumshe ido zayn yayi, bakomai yake tariyowa ba face farkon haɗuwarsu da ita. “Naso ace ta amince min, ba abunda zai hana in aureta, zan tattara dukiyata gaba ɗaya data mahaifiyata, da ta Dattijon can duka In bada a matsayin sadakinta, sai dai kash ta nuna bata buƙatar aure arayuwarta, Zaid ya zanyi da raina? Ta sanya min jarabar da bazan Iya gogeta ba” cikin jin shauƙi yake magana. Harara zaid ya watsa mashi”nifa ban gane ba, Taya zaka dinga yi min magana akan macen da nake son in mallaka? Kasan dai haramun ne muyi sharing mace ɗaya a gidan aure ko?, awaje ne muke da ikon yin hakan duk da shima yin hakan haramun ɗinne” ta6e la66ansa yai”Zaid ni ba zan yi jayayya dakai ba, just Kada kamanta ni ne gidan kuɗi, na gaban goshin mommy, mata kuma saida kuɗi” Dariyar shaƙiyanci zaid ya sakin kafin yace “Nima ina da daddy, kada ka manta komai na mommy mallakinsa ne” Sakin baki Zayn yai saida Zaid ya karasa maganar tukunna yace”Daddy ai ɗan koren mommy ne, mutumin da ke zaune agidan surukansa? Mommy ce fa silar arziƙinsa, tayaya zaka hada kan ka da Ni? baya kasan Mune ke da dukiyar Ku kuma Bayin mu ne, Sai mun ɗan watsa maku hatsi tukunna kuke samun wanda zaku tsastsaga.....” Kallon al’ajabi Zaid yake bin ɗan uwansa dashi, yadda yake magana Yana kushe mahaifinsu yai matuƙar ɗaure mashi kai, da ace wani bare ne yai wannan maganar, hada shi za’a haɗu wurin cin ubansa, don sun tsani gorin da akeyiwa mahafinsu akan yana zaune gidan surukansu. “Assalamu Alaikum” Muryar Sophia ce ta katse masu firar tasu, daga wajen bakin ƙofar ta tsaya”Yalla6ai ga coffee din na canza wani” har suna haɗa baki wurin furta”we don’t need it!” ranta ya 6aci, duk wahala da tasha a ƙarshe sunce basu sha, gyaɗa kai ta yi tare da juyawa ta bar part ɗin nasu. “Zayn ba ka da mutunci, daddyn namu ka ke yi wa gori? Yunƙurawa yai tare da mikewa zaune A harzuƙe yace”ƙarya nayi ne?ni ban ta6a ganin Mutun mai matattar zuciya irinta daddy ɗinmu ba, har yau in na tuna gorin da akeyi mana raina 6aci yake yi, Allah ya hore mana komai na rayuwa amma daddynmu yaja mana abun magana” Jinjina kai Zaid yai”Nima fa abun na ƙona min rai yana yi min ciwo a zuciya, amma ya zamuyi dole mu rungumi ƙaddararmu” saukowa Zayn yai daga saman gado Ya nufi toilet ya shige, ya rage saura Zaid a ɗakin ya tasa mirror gaba yana kallon fuskar shi, bakomai yake tunanowa ba face fuskar *UMMIN AMERICA*. *MIDDLE STEP💋* Daga alkalamin Boss✍️ Kishingiɗe yake saman lallausar Darduma, a Cikin Haɗaɗɗen Garden ɗin gidansa, jikinsa na asanye da Voile sky blue riga da wando, Kayan sun zauna mashi, Fari ne Ba irin sosai ɗinnan ba, dukkan wasu alamun tsufa sun bayyana akan fuskarshi da jikinshi, A ƙalla zai kai shakara tamanin a duniya, daga ganin fatarshi hutu ya zauna mashi, kan shi babu hula, tsufanshi bai 6oye mashi Kyawun fuskarshi ba, tsabar kyan Da Allah yayi mashi zaiyi wuya mutun yai mashi kallo ɗaya ya kauda kai, saboda haɗuwarshi da iya ɗaukar wankanshi, sumar kanshi akwance take tasha gyara hurhura duk ta lullu6e ainin launin gashin nasa, daga gaban goshin sa akwai siraran hurhura, da akayi gayu da ita, ba ƙaramin kyau ta yi mashi ba,Yana da tsayin fuska, da Manyan idanuwa, Launin gray mutunne shi ma’abocin son ƙamshi, tamkar Da ruwan turare ya ke yin wanka saboda tsabar yadda jikin shi ke fitar da daddaɗan fragrance mai kwantar da tarzoma, Dogon gemun shi fari fat ya sauko har saman ƙirjin shi, Yana da yalwatacciyar suma. Dattijon Arziƙi kuma gwarzon Namiji mai ɗauke da suffofin Jagoranci, waɗanda su ke da Jan hankalin Jama’a, mutunne shi mai daraja, Wadatar Arziƙi, kaifin basira da bajinta, Jajircewa, Mai cikar kamala, ga iya mu’amala Da mutane, kaifi ɗaya ne kuma bai Sa6a alƙawari,Ta ko’ina Allah Ya hore mashi, Kuma duk mun tarin dukiyar da ya mallaka Hakan bai gusar dashi daga Yin ibadarshi ba, Hakokin Ubangiji kama daga fidda zakka, sadaka, Da kyautatawa al’umma, mutun ne mai jin ƙan talaka, Shi nashi arziƙin bai ɗaura mashi Girman kai da maƙo ba, Da kuma ƙyamar Talaka, kowa Nashi ne wannan kenan. daga bayan shimfiɗar shi Sandar shi ce jingine da bishiya wadda aka ƙerata da zallar Gold kuɗin ta kaɗai sun ishi bawa yai maganin talaucinsa, Yayin da iskar Garden ɗin take ratsa sassan Jikin shi, A hankali ya ke ɗan lumshe idanuwanshi yana buɗesu haɗi da ƙarewa ƙayatattun kayan alatun da ke a garden ɗin kallo, a duk lokacin da kewar jikanshi ta addabe shi yakan ke6ance kanshi daga Cikin Jama’a, ba tare da sanin kowa ba, ya ke shigowa garden shan iska, yasan muddin masu kula da lafiyarshi suka gan shi shi kadai agarden sai sun kira ya’yanshi sun faɗa masu daga nan su kuma zasu rasa kwanciyar hankalinsu, har sai sunzo sun duba shi, sun tabbatar da lafiyarshi tukunna hankalinsu zai kwanta, shi kuma bayason ya katse masu aiyukansu, saboda suna ƙoƙari wurin zuwa ganinshi akai akai, Suna matuƙar ƙaunarshi, Babbar damuwarshi a yanzu Jikanshi daya mutu akan ƙaunarshi yayi nesa dashi, ya kwallafa rai akan son shi, ko ƴa’ƴanshi da ya haifa baya yi masu irin son da ya ke yi mashi, gaba ɗaya hankalin shi na akan, kyawawan furannin cikin garden ɗin, Da Halittun dake yawo acikinsa irinsu ɗawisu da filfilo Yana matuƙar son ganin su. Shu’umin ƙamshin Humran Jikinta ne ya daki Hancinsa, tun kan ta ƙaraso Ya ɗago da idanuwanshi Ya kalle ta kafin Ya kawar da idon shi gefe ɗaya sam babu walwala akan fuskarshi Ƙarasowa tayi daga gabanshi Ta ɗan russina ta gaishe shi cikin girmamawa, shiru bai tanka mata ba, hakan da yai mata yasa ta fahimci babu lafiya, ba ta ta6a ganin damuwa akan fuskar dattijon ba sai yau, cikin sanyin murya tace”Yalla6ai na duba acikin gida baka nan shiyasa nazo duba ka a garden, fresh fruit ne na kawo maka” tai maganar tare da ɗukawa ta ajiye mashi kayan marmarin. Da buɗar bakinsa sai cewa yai”Owais Ya dawo gidan nan”! murmushin gefen fuska Hajjaty tasaki”yalla6ai owais Ai baya a ƙasar Ko kamanta ne” yamutsa fuskarshi yai” Oh toh na manta, “har zata miƙe ta kuma cewa”Ko kana buƙatar wani abun ne”? Girgiza mata kai yai”bana son kowa yasan ina a garden”! amsa mashi tayi da toh kafin ta kama hanyar fucewa Kaitsaye ta nufi Entry hall na shiga gidan, Zuciyarta a cunkushe take da tunanin meke damun dattijon? Ta ya ya zata Iya sani? Duk ta damu kanta akanshi saboda Kyautatawar da yake yi masu bazata so ta gan shi a irin wannan yanayin ba. Adai dai Ƙofar shiga Falon suka ci karo da matashin dake ƙoƙarin fitowa, Dogo siriri bai da ƙiba ko misƙala zarratin, Fari sol dashi daga ganin shi farar fata ne bai haɗa komai da jinsin baƙaƙe ba, Jikinshi na sanye da Kayan likitoci farin wando, Farar shirt daga sama ya ɗaura Lapcoat, Fararen idanuwashi na manne da farin glass, Masha Allah Kyakkyawan gaske, Sumar kanshi har saman wuyanshi, “Jazz! “ yanayin yadda ta ambaci sunanshi ne yasa shi cin burki, Yana kallonta, fuskar shi a ɗaure yace “Me kike buƙata? Allura ko tiyata”? Dariya ta ɗan saki har fararen haƙoranta suka bayyana. “Kinga sauri nakeyi Yanzu aka kirani awaya, Ina da patient” yai maganar yana ƙokarin bi ta gefenta Zai je wuce, ruƙo Hannun shi da tayi ne yasa shi yamutsa fuska Hada bubbuga ƙafarshi atakure Yake kallonta Cikin sanyin murya ta soma magana”Jazz kana araye obinna ya ke6ence kanshi a garden? Hankalina ya tashi ganin damuwa akan fuskarshi....” Tunkan ta ƙarasa maganar Jazz Ya zame glass ɗin idon shi, Yanayin fuskarshi Ya canza sosai, ba tare daya ce mata uffan Ba ya nufi garden ɗin gidan, bin bayanshi tai da kallo fuskarta ɗauke da murmushi don tasan muddin Jazz yaje garden, damuwar obinna ta ƙare, Saboda kaifin basirar dake gare shi Tsab zaiyi mashi solving matsalar shi. Kamar yadda Hajjaty Tabar Obinna haka Jazz ya same shi a kishingiɗe saman darduma, ya ɗan lumshe idanuwanshi, bai ta6a kayan marmarin da ta kawo mashi ba. Sautin muryar Jazz ce ta daki kunnanshi”ina gwanin wani ga nawa!Kai ni fa bani da tamkar dattijon nan aduniya, Akanshi zan iya faɗa da kowa, duk mutumin da bai daraja gemunshi ba babu mutunci tsakanina dashi....” Cikin ɗaga murya ya ke yin maganar. Hakan ba ƙaramin faranta zuciyar obinna yai ba, a tsanake yake kallon shi, Kashe mashi ido ɗaya Jazza yai”ku fa tsaffin nan sai ana lallashinku ana tarairayarku, da zarar mutun ya haura shekara 70 a duniya sai kaga ya fara ɗabi’u irin na Yara, haba Uban mu maganin kukan mu, Idan Yunwa kake ji ba sai kai magana abaka abinci ba? Shine don rigima zaka ke6e kanka cikin garden salon ka jamana bala’e ace bamu baka kulawa yadda ya dace”? fuskarshi a ɗaure yai maganar, still murmushine akan fuskar obinna, A faɗace Jazz Ya nuna mashi hanya da yatsan hannun shi”maza tashi ka koma gida idan ba so ka ke Kaji ɗanyar geza a jikin ka ba, “ Wannan maganar da yayi tayi matuƙar bashi dariya sosai Obinna ya tuntsire da dariya yana kallon shi, jinjina kai Jazz yai hada ruƙe qugu yace”Na fahimci rashin mabugi ne ke damun ka, “ yai maganar tare da juyawa yana neman bulalar da zai buge shi, Dariya hada dafe ciki obie yake yi, Yayin da yake kallon shi, “Mutun bai rasa ci da sha ba, Sutura Allah ya hore mashi, wadatar arziƙi da ta ƴa’ƴa mai yafi wannan aduniyar nan”? A faɗace yai maganar, kamar wanda aka 6ata ma rai, alhalin nan duk cikin zolayane, ganin yayi nasarar sanya shi farin ciki yasa shi matsawa kusa dashi. Hannayenshi ya ruƙe acikin nashi”haba sanyin idaniyata, Dan Allah kafaɗin menene damuwarka? Ashirye nake dana sanyaka farin ciki,” fuskarshi amarairaice yai mashi maganar, Lumshe ido obie ya ɗanyi kafin a hankali ya waresu kan fuskar Jazz “Shi ne damuwata, Kafi kowa sanin hakan, bansan ya zanyi ba, inason ganin shi, ban ta6a tunanin zai ɗauki tsawon lokacin nan batare da yazo kawo min ziyara ba,” farin ruwane kwance acikin idanuwanshi, Hankalin Jazz ba ƙaramin tashi yai ba. “Kamar yadda ka damu dashi, shima haka ya damu dakai! Ayyuka ne suka yi mashi yawa, pls ka yi mashi uziri....” “Jazz Inaso Owais Ya halacci shagalin da za’ayi na murnar zagayowar ranar haihuwata, Amma nasan abune mai wuya ya iya zuwa” shiru Jazz ya ɗanyi yana kallon fuskarshi. “Idan zaka Iya bani dama zan sa shi yazo, Nayi maka alƙawarin hakan,” Yai maganar tare da kai hannu ya ɗauki 6arin kanka Cikin kayan marmarin da hajjaty ta kawo ma Obinna, Abaki Ya tura yana sha. “Na bar maka komai a hannunka, Indai zaka Iya cikamin burina na ganin Owais Ya halacci taron nan,” “Kada ka damu dattijo, ko babu mota ba abun hawa sai owais yazo kasar nan, “ yai maganar tare dakai hannu zai ƙara ɗaukar Ayaba, Obie Ya ka6e mashi hannu “Jazz ka raina girman gemuna, Kowa yana jin shakkar tunkarata amma kai Ko kaɗan ba ka Jin kunyar kallona ido cikin ido, “ dariya yasaki tare da cewa’Suma don basu son ainihin wanene kakana ba, shiyasa suke jin shakkarka, “ “Ba aiki zaka je bane”? zaro ido waje yai sai lokacin ya tuna da mara lafiyan da zaije dubawa, da sauri ya mike yana faɗin”Rigimamman tsoho ni nayi nan Allah ya ƙara lafiya da nisan kwana, ‘ har ya miƙi hanyar zai bar garden ɗin ya kuma dawowa ya zuƙunna a gaban farantin kayan marmarin ya ɗibi mai uban Yawa Kafin ya mike yana faɗin”Allah yaja da ran dattijon arziƙi tsoho mai ran ƙarfe, An buga dakai an barka, Namijin zaki uban dawa” Murmushi ne ɗauke akan fuskar shi, idanuwanshi akan bayan Dr jazz har saida ya 6ace ma ganin shi tukunna ya ɗauke idon shi. *Boss Bature✍️ Mu haɗu gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*KURKUKUN ƘADDARA*_ _The Prisoners E9🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* ~Middle step~ _A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._ Wuraren ƙarfe biyar da rabi na marece, Aneelerh ta fito daga cikin toilet bayanta a goye da baby junaid tayi mashi wanka ta ɗaura mashi towel, A saman Gado ta kawantar da shi fuskar shi ɗauke da murmushi, ɗan zaro mashi ido tayi”Why are u smilling at me”? “Mommy daɗi nake ji, Angel zata dawo” aɗan ruɗe ta bi shi da kallo”Junaid! Waya faɗa maka Angel zata dawo”? Da yatsan hannun shi ya nuna mata saitin zuciyarshi, murmushi ta saki haɗi da ɗan girgiza kanta”my baby boy nima ina ji araina ƴar uwarka ta kusa bayyana in sha Allahu nan bada jimawa ba, in dai tana numfashi a doron duniyar nan....”tunkan ta rufe baki yace”Mommy Angel tana sona? ɗaga mashi kai ta yi alamar eh”Angel tana sonka junaid tun kafin zuwanka duniya ta ƙwalla fa rai akan son ganin ka,” Ta yi maganar tare da juyawa ta nufi gaban mirror ta ɗauko Mayukan shafawarshi, a saman mattress ɗin ta ɗaura su, ta soma shafa mashi ajikinshi. “Aunty Aneelerh,!” muryar zahra ce daga waje take kwaɗa mata kira, A hanzar ce Junaid ya buge hannun Aneelerh data ruƙe shi, ya damƙi towel ɗinshi dake yashe saman katifar, Lamarin yai matuƙar ɗaurewa Aneelerh kai, ganin yadda yake kiciniyar ɗaure qugunshi, duk don saboda zahra kada ta gan shi babu kaya, Kafin zahra ta faɗo ɗakin tuni ya kammala maida towel ɗinshi sai faman haki yake yi, ƙasa ƙasa da murya tace”junaid ban kammala shafa maka man ba”, turo mata baki yai”Ni ae bana sho Aunty zahra ta gane min abuna, idan ta tafi sai ki ƙarasa shafa man....”kumshe dariya Aneelerh tayi abakinta. “Aunty Aneelerh Abie da daddy suna son Yin magana dake, Na riga na faɗa masu komai game da tada zancen 6acewar su tajuddeen, sun amince da yin hakan” Farin Ciki ne ya bayyana akan fuskar Aneelerh”Zahra, zanje yanzu mu yi magana da su, Ga junaid nan ki cigaba da shafa mashi...” kasa ƙarasa maganar ta yi sakamakon toshe mata baki da Junaid yai da tafin hannun shi, Kallon fuskarshi tayi, 6acin rai ta gani akanta. Ta6e baki zahra tayi idonta akan fuskar Baby junaid,”Kin ga Aunty Aneelerh Ki tashi ki je suna a palour, bana so damar nan ta wuce mu, Ki barni dashi zan ƙarasa gyara mashi jikin” amsa mata ta yi da toh, kafin ta sakko daga saman gadon ta nufi closet ta buɗe ta curo mayafinta bayan fitarta ɗakin, Junaid ya takure kanshi jikin headboard na gadon, lallashinshi ta soma yi”haba habibina meye na 6ata fuska nifa ma mommyn ka ce, zo nan in gyaran maka jikin ka, Maƙe mata kafa ɗa yai”so ki ke ki kalle mun abuna, ni banso, Zan jira mommy ta dawo” ɗaure fuska tayi ganin zai 6ata mata lokaci yasa ta haye gadon ta cafko shi, ya dinga kuka yana shure shuren ƙafa, daƙyar ta samu ta shafe mashi jikin tana fadin”ɗan jakar uba, Jiki duk madara, da ace baka da kyau ko kallo baka ishe ni ba” tur6une mata fuska yai hada jifarta da harara, Miƙewa tai daga saman gadon ta sauko ta nufi closet din kayan su ta ɗauko mashi riga da wando, ta dawo ta zauna gefen shi, a tsanake ta zura mashi a jikinsa, tunkan ta kammala Wayar Aneelerh ta soma ringing “Wayar mommy tana ringing” junaid ne ya sanar da ita “Ni bana ɗaga wayar mutun idan bashi ya bani izni ba” gatsina mata hanci yai”Angel ce ke kira aunty zahra dan Allah ki ɗaga, kada ta katse” kwantar da kanshi tai saman ƙirjinta, faɗi yake ni ki sake ni, inje in ɗaga kiran Angel” taƙi barin shi ya motsa, suman kanshi take shafawa da hannunta, shiyasa ya ke gudun zahra ta ɗauke shi, kamar ta samu lallausan bready haka take daƙuna shi. Bayan fitar Aneelerh A palour ta taras da Uncle ɗan Iya tare da abie hada Mommy da Ummi zaune saman Sofa, cikin girmamawa ta ƙarasa tare da zuƙunnawa ta gaishe su, A mutunce suka amsa mata, daga ƙasan sofa ɗin da mami da ummi ke azaune ta jingina bayanta, tare da sunnar da kanta tana jiran jin me zasu ce. Gyaran Murya uncle ɗan Iya ya yi, hakan yasa ta ɗago da ido ta kalle shi, ya ƙwama farin Glass a fuskarshi Ya ɗan sauko har saman karan hancinsa, a halitta baƙi ne wulik, kamar ba jinin Abie ba, yana da Manyan idanuwa hancin shi a wargaje yake, Haka bakin shi manyan la66a ne dashi, wandon shadda ne a jikin shi Daga sama Malun malun ce babi Ƴar Ciki, Ya ƙwama Hula Akanshi Ga uban sanƙo, a saman Kujera mai mazaunin mutun uku suke zaune su Biyu, gyaran murya yai kafin ya soma magana”Zahra ta faɗa min komai, a gaskiya kun kawo shawara mai kyau, Kunyi tunani na hankali” yana magana yana watsa hannayenshi Ɗabi’arsa ce Yin hakan. “bai kamata don abu ya haura shekaru da faruwa muja baki muyi shiru, tun da har yanzu bamu da tabbacin suna araye ko sun mutu! Idan ko suna araye ba ƙaramin ganganci mu kayi ba, Na watsar da zancen 6acewarsu, wata’ƙil Silar tada zancen Allah Ya bayyanar mana dasu.....” tun da ya soma magana suka natsu suna sauraronshi, Aneelerh ta duƙar Da kanta ƙasa Farin Ciki duk ya cikata, gani take kamar ma har an riga an ganso su. “In sha Allah zanyi magana da ziyad babban ɗan jarida ne muddin labarin nan ya je gare shi ina mai tabbatar baki da cewa cikin ƙanƙanin Lokaci Duniya zata ɗauka tamkar bai jima da faruwa ba, a manyan Kafafan sada zumunta za’a yaɗa labarinsu, irin su BBc, CNN, and ONt, muma kuma zamu bada gudummuwar mu, wurin Yaɗa hotunansu a social media” Bayan Uncle ɗan Iya ya takaita da zancen nashi Abie ya ɗaura da cewa”kafin Gobe ki tabbatar kin tattara duk wasu hotunansu Tajudden kin tura mashi, Sannan Adage da addu’a duk danasan kina ƙoƙari wurin yi masu, Mamie ta fadamin kullum sai kin tashi yin nafilfili dare, naji daɗin jin hakan sosai, Allah yayi maki albarka” amsa mashi ta yi da ameen, Mamie tace”Ubangiji Allah ya bayyanar mana dasu, Allah yasa silar tada zancen 6acewarsu da za’ayi su bayyana, mungode sosai” godiya suka hau yiwa Uncle ɗan Iya, kafin daga Bisani Aneelerh ta miƙe tare da yi masu sallama ta Nufi bedroom ɗinta tsabar zumuɗi kamar zata tashi sama, lokacin da ta shiga ɗakin, A kwance ta samu zahra tana fuskantar ceilling hannunta a ruƙe da wayarta, ga dukkan alamu Chatting take Yi, Baby junaid tuni ya jima dayin bacci yana kwance saman ƙirjinta. Jin motsin shigowar Aneelerh Yasa ta ɗan kawar da kanta daga kallon wayar ta take Yi ta kalli Aneelerh tunkan ta ƙarasa shigowa ciki Ta lura da tsantsar farin Cikin dake akan fuskarta “Yah aunty Aneelerh Ina fatan komai lafiya”tana murmushi tace”abie yace in tura ma Uncle hotunansu tajuddeen wlh bakiji daɗin da naji ba,”Zahra na murmushi tace”Allah yasa Adace sister, nima zan tayaku sharing a instagram page ɗin mu,” Godiya Aneelerh ta yi mata, ringing ɗin wayarta ne Yaja hankalinta ga duban saman pillow, Da sauri ta nufi wayar takai hannu ta dauke ta “Bansan wanene ke kiranki ba, Tun ɗazu bayan kin fita wayar ke ta ringing ban daga ba” “Why ba ki ɗaga ba zahra, Surukata ce fa” ta6e baki zahra tayi”matar da ke son ƙwace mana baby junaid ɗinmu ai ƙwara daban ɗaga ba” picking call ɗin Aneelerh tai tare da kanga wayar a kunnanta. Cikin girmamawa tayi mata sallama”Assalamu akaikum” on the other hand Hajiya adama ta amsa mata da”Wa’alaikum salam daughter In law, ina kika shiga inata kira ba aɗagawa”? aneelerh tamkar tana agabanta tace”Bana akusa da wayar ne bansan kun kira ba” gaisawa sukayi kafin hajiya adama tace”guest what”? ɗan zaro ido Aneelerh ta ɗanyi tana wurwurga eye balls ɗin ta can tace”kun dawo ƙasar”? Sautin dariyar hajiyar adama ne yasa ta saki murmushin farin ciki. “Mun dawo, in sha Allah end of this month zamu shigo Abuja, two days kin daina kiran layina Why? Ko dan saboda kada na ƙwace maki Yaro”? Cikin Jin kunyar maganarta Aneelerh tace”ba haka bane mommy, wlh ina ta zucci zuccin in kira ki Allah ne bai nufa ba” Tai maganar a yayin da take kokarin zama saman stool, Ta gaji da tsayuwar, Zahra ta kasa kunne tana sauraron Firarsu. “Idan ma don saboda dashi ne to ki kwantar da hankalin ki, babu wanda zai raba ki da ɗanki, Munyi magana da abdallah Ya fahimtar dani game da cutuwar da zakiyi idan muka ce zamu raba ki da shi, Ni kaina bazanso Inyi silar sanya ki baƙin ciki ba....” buɗe ido Aneelerh Tayi Wani irin farin cikine tsantsa akan fuskarta, Zahra da ta tsareta da ido tana kallonta, sai faman yi mata mimi da baki takeyi donta fada mata me Hajiya adama ke fada mata wanda yasa ta farin ciki “Zan kira mamin naki mu yi magana, Sannan akwai wata gagarumar kyauta dana shirya maki idan mun zo zaki gani” Hawayen farin Ciki ne su ka wanke fuskar Aneelerh, kasa jurewa tayi batasan lokacin da kuka ya kubce mata ba. Muryar Hajiya adama a ɗan ruɗe take fadin Aneelerh why? Kuka kuma? Meya faru? cikin shessheƙar kuka tace mata kukan farin Cikine, taji daɗin ƙaunar da take nuna mata, tana alfahari da su, samun surukai irinsu abune mai wuya, Hajiya adama taji daɗin daɗaɗan kalaman da Aneelerh take faɗa mata, tsawon lokaci suna waya Kafin daga bisani Tayi mata sallama, Idanuwanta acike tab da ƙwalla ta wurga su kan fuskar zahra tambayarta ta shiga me suka tattauna da Hajiya adama? Nan Aneelerh ta sanar da ita komai, Fasa ihu zahra Tayi tare da jefar da wayarta gefenta, ta sauke junaid daga saman jikinta a hankali ta kwantar dashi, kafin ta sauko daga saman gadon ta nufi Aneelerh ta rungumeta kamar zata maidata ciki, Farin Ciki duk Ya cikasu, Miƙewa Aneelerh tayi bayan ta ajiye wayar gaban mirrror, Rawa suka soma takawa ita da zahra, hada ɗebo shoki suna kifawa saman goshinsu, Yayin da suke sakin Dariyar murna. *EVIL FOREST* A ƙalla yau satin su ɗaya acikin kogon dutsen ba tare da sun motsa ba, saboda marasa lafiyan cikinsu, jikinsu yai tsauri, duk da haka suna ƙoƙarin basu kulawa ta musamman, Danish Ya haɗa masu garin maganin da su ke sha suna samun warakar raɗaɗin ciwonsu, A cikin gorar ruwansu ya ke jiƙa masu maganin, Bayan haka duk in za su yi tsarki da ruwan zafi su ke yin shi, danish ne yai masu dabarar yin hakan, Alhamdulillam Jikinsu Azeeza yayi kyau sauƙi ya samu, ba su rasa ci da sha ba, kullum ne sai sun ci abinci sau uku, Danish ne ke ƙoƙarin yi masu farautar abunda zasu ci wani sa’in zoman daji yake kaso masu ko tsuntsaye hada kayan marmari ya ke samo masu, saboda su ya ke hana idonshi bacci, A zaune yake kwana shi da Angel dinsa, tana ɗebe mashi kewa, shaƙuwace mai ƙarfi a tsakaninsu. Burinsu marasa lafiyar cikinsu su ƙarasa wartsakewa ko sun samu su cigaba da tafiya. Yau tun da sanyin safiya ta soma Jin hayaniya acikin kunnuwanta, ƙasa ƙasa take iya jin maganganunsu, Tsantsar mamaki ne ya kamata Jin muryoyin su Batul, tamkar a mafarki, a harzarce ta buɗe idanuwanta tare da miƙewa zaune tana ƙarewa Kogon dutsen kallo, Haris ne kaɗai ya rage a kwance yana bacci, Ya ƙudundune kanshi cikin bargo, ƙoƙarin tariyo abunda ya faru jiya ta soma yi, da wata irin kasala ta miƙe tsaye tare da yin hamma, abu biyu ya ɗaure mata kai da farko tayi tsammanin zata ga su Azeeza sai dai bata kowa ba. Hankalinta A matuƙar tashe ta fito tana ƙarewa Dajin kallo, Kamar daga sama tajiyo muryar Jemimah tana ambaton Sunan da take kiranta dashi”Genie!’ ras taji gabanta Ya faɗi, A ruɗe ta wurga ƙwayar idonta kansu, Gaba ɗayansu ne banda Haris, Yau wata rana sun fito daga kogon dutse jiki yayi kyau, Sai wasa suke Yi suna tsalle tsalle, Farin Ciki duk ya cikasu, Bakunansu awashe kamar gonar auduga, ba ta san lokacin da hawaye suka soma wanke fuskarta ba, Nan ta ke ta zube saman gwiwowinta tare da kifa kanta ƙasa ta yi sujjada tana godewa Allah da ya nuna mata wannan ranar, Haƙiƙa tayi farin ciki mara misaltuwa, kafin ta ɗago daga sujjadar Jemimah ta watso da gudu ta faɗo saman bayanta, sai tiƙar dariya ta ke yi tana fadin”Genie Daɗi kamar zai kashe mu, Wlh daɗi muke ji, wannan wurin mai kyau bamu ta6a ganin irin shi ba, Genie Yau zamuje gidan daddynki ko”? Kasa ɗagowa Angel tai, wani irin yanayi take jin kanta. Ƙarasowa Azeeza tayi Hannunta ruƙe cikin na Gabriel, Sauran Ƴan uwansu na abiye da bayansu, agaban inda tayi sujjadar suka tsaitsaya suna kallon ta “Angel muna son yin magana dake”muryar parveen ce ta ratsa kunnanta, daƙyar ta iya haɗiye kukan da ke shirin kubce mata ta ɗago da kanta, tare da zagayo da hanneyenta biyu ta ruƙe Jemimah gudun kada ta faɗo daga bayanta Ɗaya bayan ɗaya take binsu da kallo, tun daga kan fuskar Azeeza dake ta sakin murmushi, fatar jikinta tayi haske sosai dama ita can launin skin ɗinta na farar fata ne, da launin gashinta, ta rame sosai ta ƙara komawa ƙarama. ɗauke idon ta tayi daga fuskar Azeeza ta mayar dasu kan fuskar parveen, itama ta faɗa duk sunyi haske kamar fatalwu, Murmushi ta ɗan saki tare da kallon Batul dake a tsaye tana sakar mata murmushin ƙauna. “Rabin rai kin tashi lafiya, Nasan kinyi mamakin ganin mu awaje muna shan iskar duniya, Danish ne ya fito da mu waje kuma yace da zarar ya sama mana abinci mun ci zamu kama hanya” lumshe ido Angel ta ɗanyi tare da ware su kan fuskar Hannah. Muryar Gabriel ce ta janyo hankalinta ga kallon shi”Muna so muyi maki godiyane akan irin ƙoƙarin da kikayi mana, Angel kin cancanci ayaba maki, babu wasu kalmomi da zamu Iya yin amfani da su wurin yi maki godiya ke da Danish, Allah ne kaɗai zai Iya biyanku” Cikin sanyin murya tace”Allah shine abun godiya Gabriel, Alhamdulillah ala kullu halin, ina taya ku murnar Samun ƴanci arayuwarku, Kuma inayi mana fatan Allah ya bamu sa’a adukkannin abunda muka sa agaba, Ubangiji Allah yasa ƙarshen wahalar mu ce tazo....” addu’o’i ta dinga jera masu suna amsa mata da ameen, Sai da ta kai ƙarshen maganarta, muryar jemimah ta katse ta”Genie ba zamu ƙara komawa kurkuku ba ko?” Batul tace”har abada mu da kurkukun ƙaddara, Daga nan sai Gidan daddyn Genie, ko kina son komawa ne”? Zaro ido tai tare da girgiza kanta”banso, Allah ya tsinema su da tsohuwa zafreen, muguwa idan mu ka yi ƙarfi sai mun kashe su, damu da daddyn Genie, zamu rugurguza kurkukun kowa ya huta, Kuma zamu ƙwato ƴan uwanmu da ke a wurinsu” ranta a6ace ta ke yin magana, kumatunta sunyi jawur da su. Angel tace”In sha Allah Jemimah mune zamu kawo ƙarshensu, Allah sai ya saka mata cin zalunmu da su ka yi, haƙƙin mu ba zai ta6a barinsu ba, tun agidan duniya zasu fara gir6an abunda suka shuka” tana magana hawaye nabin fuskarta. “Angel Ba ki faɗa mana ina ne nan ba? Munga wasu abubuwa da su ka ɗaure mana kai waɗanda bamu ta6a ganinsu ba ko a mafarki,” Javed ne yai mata maganar fuskarshi da alamun ruɗu. “Angel munga kalar ganyan da ake kawo mana muna ci a kurkuku,” still fuskarta da murmushi ta yunƙura ta miƙe hannunta ruƙe da Jemimah, Gabriel ta kalla”meyasa baka yi masu bayani ba”? Ta6e la66ansa yai”sun fi so suji daga bakin ki,” Ajiyar zuciya ta sauke tare da cewa”Okey, Ku jira Danish Ya dawo, idan muka kammala cin abinci, muka kama hanya zanyi maku bayanin komai” amsa mata su ka yi da toh. Kafin wani ya ƙara cewa wani abu, Motsin tafiyar Danish ta janyo hankulansu ga dubanshi. A tsanake ya ke yin tafiya yana tunkaro su, hannun shi ɗaya a ruƙe da kwandon da ya haɗa masu saboda ajiyar kayan abincin su, tunkan ya ƙaraso Jemimah ta sauko daga bayan Angel, da gudu suka nufe shi ita da Azeeza da parveen, atare suka faɗa mashi tare da ƙanƙame shi suna sakin dariyar farin ciki. Ganin shi suke yi tamkar mahaifinsu, saboda kyautatawar da ya ke yi masu wurin yin jinyarsu, nufo wurin su Angel tayi tana faɗin”Sannu da dawowa My Man, Na farka ban gan ka, meyasa baka tada ni mun tafi atare ba” ta yi maganar tare da kai hannu ta ruƙo hannun Kwandon da ya ruƙo, sakar mata yai ta kar6a tana leƙa cikinsa Kayan marmari ne ashaƙe cikin kwandon. Da sauri ta ɗago suka haɗa ido da juna, murmushi ta sakar mashi”sannu da ƙoƙari, duk namu ne wannan,” ɗaga mata gira yai alamar eh, “mun gode Danish, Allah ne kaɗai zai Iya biyanka,” lumshe mata ido yai kafin ahankali ya ware su akan fuskarta. Su Parveen sun ƙi sakin jikin shi tun da su ka rungume shi ba su ɗago ba, faffaɗan tafin hannun shi ya ɗaura asaman kawunan su a hankali ya ke shafa sumarsu kan su, sai ƙara ƙanƙame shi suke Yi, a hankali ya furta masu”Ya Jikin naku”? Jemimah da Azeeza suka haɗa baki”Ai mun warke, Gidan daddyn Genie zamu je yau” Ganin sunƙi sakin shi yasa Angel yi masu magana”ku sake shi mana, Ko mun samu muyi sauri muci mu tafi, idan har ba barin Dajin nan mukayi ba Hankalina ba zai kwanta ba” Jin maganarta yasa suka sake shi, Ya ruƙo hannun Azeeza dana Jemimah suka jera atare suna tafiya, Cikin Kogon dutsen su ka koma gaba ɗayansu, suna shiga suka tarar da Haris zaune shi kaɗai, bai jima da farkawa daga bacci ba, A ƙasa kowanansu ya zauna, Angel ta curo kayan marmarin ta rarrabamasu, A tsanake suke sha suna kallon Juna, bayan sun kammala sha, Suka fara shirin tafiya, Ba tare da 6ata lokaci ba, Angel Ta goya jemimah abayanta da mayafi ta ɗaureta, Gabriel Ya goya Azeeza abayanshi, sai daɗi suke ji an goyasu har gwalo suke Yima Parveen, Batul kuma ta Goya Back pack ɗin Unaiza abayanta, Javed Ya ruƙe masu akwatin kayansu, basu bar komai acikin kogon ba, Hatta Gorar ruwansu acikin kwandon kayan marmarinsu su ka sanyata, Parveen ce ta ruƙe kwandon a hannun ta. Matafiya sun shirya tsaf saura tafiya ta rage masu, kafin fitarsu daga kogon dutsen saida Angel ta yi masu addu’o’i tabi kowan nan su ta tofe shi tun daga ƙasa har sama ko da ta zo kan Danish sai ce wa yai me take yi haka? ta daina watsa mashi yawu baiso, dariya tayi batare da tace mashi komai ba, Danish ne ke ruƙe da Haris saboda rashin ƙwarin Jikin shi. Suna tafiya suna fira a dokar dajin, Su parveen sunga abubuwan da suka ɗaure masu kai, Komai suka gani sai sun tambayi Angel menene shi? Lokacin da rana ta ƙwalo Kowannansu Ya zazzare idanuwanshi suna kallon Sararin samaniya inda rana ta hudo, Angel sai ƙoƙarin hanasu takeyi akan su daina kallonta, gudun kada hasken ranar ya kashe masu idanuwan su. Bakomai yasa su yin hakan ba face tsantsar mamaki da al’ajabi, su fa duk ɗaukarsu Fitila ce aka ajiye sama, kamar dai yadda ceiling ɗin ɗakin su na kurkuku Yake, Parveen sarki kwa6a magana da ta gaza jurewa tace da Angel ta faɗa mata tayaya akai har aka ɗaura fitilar sama? Ita bata ta6a ganin fitila mai hasken ta ba,” Dariya Angel tasaki tare da cewa”Kai parveen Nafa ta6a faɗa maku saboda gudun haka, Rana ce wannan da kuke Gani, Babu wanda ya ɗaurata Yana daga cikin halittar ubangijin mu Allah, bayan ita akwai Wata da taurari suma duk Allah ne ya halicce su, Idan Dare yayi zan nuna maku su, taci wahala wurin wayar masu da kai daƙyar ta samu suka fahimce ta, kusan saida ta maimaita masu karatun data koya masu tukunna suka Iya tunawa, A ƙalla sun shafe awanni suna kutsawa cikin Dajin babu alamun zasu shigo cikin Garin, Wani irin kurman Dajine ta ko’ina acunkushe yake da tsirrai. Gaba ɗaya sun gaji da tafiya, Dama jikinsu bai saba da wahala ba, Ga6o6in jikinsu duk sun raunata, Mutun Biyune basu jikata ba, Jemimah da Azeezah, hankalinsu kwance Har bacci ya ɗauke su a goye sai daga bisani suka farka, “Wlh mun gaji Angel, Wai haka zamu dinga tafiya ba tsayawa? Ƙafafuwana duk sun rurruƙe, Ga yunwa inaji” Parveen ce tayi maganar, “Ya ki ke so muyi parveen dole muyi tafiya da da halima hada gudu, in ba haka ba zamu ƙare acikin Dajin nan ne,” fuskar Angel ayamutse ta yi maganar, Danish duk yana sauraronsu, hankalin shi na akan Haris daya ruƙe. Parveen ta hanasu sakat, don dole Naufal Ya goyata abayanshi, Jemimah hada tsokanarta”ƙatuwa dake dole sai an maki goya irin namu” Harara parveen ta watsa mata. Ba tare da tace komai ba. Zogin da ƙafafuwansu suka fara yi masu ne yasa suka yada zango agaban wata ƙatuwar bishiya suka zazzauna suna faman yin haki, Gorar ruwa parveen ta curo masu, Bayan tasha ta miƙa ma Naufal yasha ya miƙa ma Hannah, sai dakowa yasha ruwan, Sun natsu suna faman lumshe idanuwansu, “karfa kuyi mana bacci anan, bamu gama tafiya ba, naga kuna rufe ido,” Angel ce tayi masu magana, Fuskar Parveen atur6une tace”kaɗan zamuyi, “ batul Ta natsu tana kallon Bishiyoyin dake a kewaye dasu, “Angel Su waɗannan basu gajiya da tsayuwa ne”!? Fuskar ta aɗaure tayi maganar babu alamun wasa “Su wa kike nufi” Angel ta tambaya tana kallon fuskar Batul, Da hannu ta nuna mata Bishiyoyin dake fuskantarsu, Ɗan zaro ido Angel tayi tare da kallon Danish dake kallon fuskarta, kiris ya rage ya saki murmushi jin wautar Batul. hankalinta a kwance taci gaba da cewa”tun da muka taho suke ta tsayuwa babu motsawa, Itama rana sai binmu takeyi da gudu duk inda mukayi sai na ganta, to wai su basu gajiya ne”? Kalamanta sun rufe ma Angel baki ta kasa bata amsa, daƙyar ta iya cewa”Haka Allah ya Halicce su Batul” Gabriel da ya ƙumshe dariya abakin shi yace da ita”ke yanzu idan waɗannan bishiyoyin suka motsa zaki tsaya? Har kina da bakin cewa Basu gajiya da tsayuwa”? Sai lokacin ta ɗan saki murmushi ba tare data kalle shi, shiru su ka ɗanyi na wani lokaci, Har bacci ya fara ƙoƙarin ɗaukar su Jemimah ta fara ambaton fitsari take ji, Ɗaukarta Angel tayi tare da miƙewa ta kalli Danish”Zanje nakaita tayi fitsari,”lumshe mata ido yai tare da cewa”No, basai kunje nesa ba, Zata iya yi ko abayan bishiya ne” Amsa mashi tayi da toh, kafin ta nufi bayan bishiyar da ita, bayan sun dawone tace dasu su tashi suci gaba da tafiya kada dare yayi masu anan, Miƙewa su kayi jiki duk ba ƙwari, Ta maida goyan Jemimah gabriel ma ya goya azeezarshi suka dasa da tafiya. Allah ya tsare su tunda suke tafiya babu wata muguwar dabbar da suka ci karo da ita, Sai dai sautin koke kokensu da suke ji acan wani sashe na Dajin, Sunyi nisa da tafiya kwatsam Ba zato ba tsammani Akuya ta faɗo wurinsu kamar an jehota, a matuƙar figirce suka watsa da gudu cikin dajin duk su ka tarwatse saboda tsabar firgitar da su ka yi. Hankalinsu Danish ba ƙaramin tashi yai ba, babban abunda suke jima tsoro kada wata dabbar ta handamesu, Mutun biyar ne suka watse waɗanda suka rage Danish ne sai haris shima saboda Ya ruƙe shi ne ya kasa guduwa, Gabriel dake goye da azeeza sai Jemimah da Angel, Basu ta6a ganin akuya ba sai yau, shiyasa Suka watse, mun shigo uku Danish! Ya zamuyi? Angel ce ta ambaci hakan, Bai amsa mata ba ya kwantar da Haris jikin bishiya da gudun gaske ya faɗa Cikin Dajin don Ya tattarosu. Jemimah ta ƙanƙame angel sai satar kallon akuyar take Yi, ta yi tsaye tana Lasar baki, Ciyawar dake awurin take Ci, Ran Angel ya 6aci, Duwatsu ta tsinta a kasa ta dinga jifar akuyar, Da gudu Ta watsa tana kuka, Sautin dariyar Jemimah ne ya karaɗe kunnuwansu “Genie ashe ma matsorayaci ce, wai wannan abun su Batul suke ma gudu, ni sun bani dariya, Ko kunya ma bata ji tana yawo zindir babu kaya a jikinta, ƴan nonuwanta azube kamar na tsohuwa, Genie itama mutunce kamar mu ko”? shiru Angel bata tanka mata, Damuwace ƙarara akan fuskarta, Hankalinta ba zai ta6a kwanciya ba idan har ba adawo dasu Batul ba. Azeeza tana a la6e saman bayan Gabriel, Muguwar matsoraciya tun da akuyar nan ta faɗo wurinsu Ko yatsanta tagaza motsawa, Numfashinta ma a dabarbarce yake fita, Jikinta sai kakarwa yake yi, ba dan Allah yasa tana a goye a bayan Gabriel ba kuma ya ɗaureta da mayafi da kuwa Silar 6acewar azeeza kenan acikin Daji, Allah kaɗai yasan inda zata kutsa kanta saboda tsoro. “Shiru basu dawo ba Angel, Ni inaga zan bi bayan Danish ne” Gabriel yai maganar, da sauri tace”A’a, Kada kaje ko’ina, Inaji araina zasu dawo atare, nasan duk inda suka shiga Danish zai nemo su” Haris dai Yana a langwa6e jikin bishiya, suna cikin jimamin rashin ƴan uwansu, suka soma Jin takun tafiyarsu da sauri suka Juya baya suna kallon su, a jere su ke tafiya suna tunkaro su, abun da zai baka mamaki Hada naufal da javed su da suke maza, Batul na aruƙe da hannun Hannah, dana Parveen Sai haki sukeyi sun hada uban gumi, Danish na abiye da bayansu, Tunkan su ƙaraso Angel ta fashe da dariya hada dafe cikinta, Hatta Gabriel dariyar yake yi masu, hakan ba ƙaramin ƙona ransu yai ba. Ko da su ka ƙaraso zazzaga masu masifa Naufal ya shiga yi yana fadin meyasa basuyi masu bayanin cewe akuyace ba, ae su basu son suffarta ba, iya namanta da suke ci ne suka sani,’ Sai da yayi mai isarshi parveen ma ta ɗaura da nata faɗan akan dariyar da suke yi masu, sauran dai basu ce komai ba, Ruƙo haris danish yai tare da taimaka mashi ya miƙe tsaye. Zuciyarsu Naufal a jagule suka ci gaba da tafiya, Rayuwarsu ta daji gwanin ban sha’awa, Ga cin dariyar kwa6ar su batul komai basu sani ba sai Angel tayi masu bayani, idan dare ya tsala gefen bishiya Danish Yake yi masu shimfiɗa, bayan sun kwanta Yabi su da barguna Ya lullu6e su, sannan ya shiga daji Ya samo itace ya haɗa masu wuta saboda sanyin Dajin, Tun da suka fara tafiyar nan Danish bai runtsa ba, Su kaɗai suke Yin baccinsu, Baya gajiya dayi masu hidima, basu da matsalar komai Abinci har sai sun ture, Nama iri iri suke Ci na dabbobin da yake yi masu farautarsu, Ga kayan marmari availabe cikin Dajin, wasa wasa kusan Watansu ɗaya suna tafiya babu alamun zasu taddo cikin gari, Lamarin Ya ɗaga hankulansu, A haka ma Danish yana taimakon su ba tare da sun sani ba, Duk idan dare ya nutsa bacci ya ɗauke su ɗaya bayan ɗaya ya ke ɗaukar su Ya nutsa dasu Cikin dajin ya yi tazarar tafiyar awanni dasu, basu ta6a lura da hakan ba, duk don ya sauƙaƙa masu wahalar tafiyar, shiyasa ya ke yi masu hakan, don kuma su yi gaggawar barin Dajin, Don ya fara Jin alamun wani baƙon Yanayin a jikin shi, fargabarshi kada Giant’s heart ɗinshi ta motsa batare daya Nisantu daga dajin ba. *PRISONERS💔* Dare Ya nutsa sosai suna akwakkwance suna bacci, Hasken Wutar Dake Ci Ya haskaka zagayen wurin da suke, yana a Zaune gaban wutar idanuwanshi akan shimfiɗarsu, Sai faman lumshe idanuwanshi Yake yi, ga dukkan alamu baccine yake ƙoƙarin fuskarshi. Angel da ke a kudundune cikin bargo taƙi runtsawa duk don saboda shi, ta kasa samun natsuwa, Yaye bargon tayi tare da fitowa daga Ciki Ta miƙe tana miƙa ta nufi inda yake zaune, Tunkan ta ƙarasa taga yana gyangyaɗi Ƙiris Ya rage ya kifa kanshi Cikin wutar dake agabanshi da gudun gaske Ta ƙarasa tare da zubewa gefen shi saman gwiwowinta, da hannyenta biyu ta tallabo fuskarshi tana bin shi da kallo, Sam ya gaza buɗe idanuwanshi sunyi mashi nauyi, rungume kanshi tayi saman kirjinta, idanuwanta suka ciko tab da ƙwalla, tsananin tausayinshi take ji. “Danish muje mu kwanta,” muryarshi ƙasa ƙasa ya furta mata”bazan iya bacci ba Angel idan har ba barin Dajin nan mukayi ba, Ina jin fargabar wani abu ya same ku ta silar rauni na” ƙara ƙanƙame shi tayi a jikinta”In sha Allah ba abunda zai same mu Danish, Allah Yana atare damu, Kuma Inayi mana addu’a, Kada kaji komai kazo mu kwanta, rashin yin baccin zai Iya ja maka wata matsalar da bana fata” A hankali ya zagayo da hannayenshi saman waist ɗinta, kafin ya lumshe idanuwanshi. Jin shiru bai ƙara motsi ba yasa tayi tunanin ko baccin ya ɗauke shi ne, Kiran sunanshi tayi”Danish” amsa mata yai”Na’am” cikin kulawa tace dashi”nayi tsammanin ka fara baccin ne, pls kayi bacci Danish, inaso ka huta, bana so kana wahala” daɗin murya yake ji acikin kunnuwanshi, har baison intana magana tadaina, Yafi son taita yi mashi surutu. “Danish naji ka yi shiru baka ce komai ba”? Har saida ta fidda rai da zaiyi mata magana tukunna taji yace”Angel ni wannan ba damuwata bace, i ave told u duk wahalar da zanyi indai akan ku ne bana gajiya, ke ce ƙwarin gwiwar da nike da shi Angel “ murmushi tasaki idanuwanta akan Kitson zanan dake akanshi, “Faɗamin me ka ke ji akaina? sannan Meyasa kake ƙaunata? Ta yi maganar tare da Ɗaura yatsun hannunta saman kanshi, tuntuni ta ke son ta kwance mashi kitson da akayi mashi a prison don bata son ganin shi da kitso kamar mace tafi son ta ganshi a Namijin shi. “Nikaina bansani ba” amsar daya bata kenan, Ɗagowa yai da kanshi tsinin hancinsu Ya haɗe jikin na juna, Hasken wutar dake cine ya haskaka fuskokinsu Hakanan Taji gabanta na faɗuwa, ganin launin idonshi na canza mata, duk tabi tasha jinin jikinta, ƙwarjini yayi mata da sauri ta kawar da idonta gefe ɗaya “Abu ɗaya nake fargaba a duniyar nan! Shi ne ace za’a raba ni da ke!” Dawo da dubanta tayi akan fuskarshi, jaddada mata maganar shi yai”Zan iya komai a wannan lokacin,” “Maganar raba ni da kai ma bata taso ba Danish, dani da kai tamkar anta da jini ne, mutuwace kaɗai zata Iya raba ƙaunar dake a tsakanina dakai, Amma agidan duniya bani da madadinka” kalamanta sun ɗan sanyaya zuciyarshi, “Ina tsoron ranar da zaki Canza min, duk da bana kawo hakan araina, Angel wani zai Iya ƙwace min ke, kinga ni bani da komai da zan iya faranta maki da ya wuce kaina” Muryarshi araunace yai maganar. Ɗaure mashi fuska ta yi “Danish zaka Iya bari wani ya ƙwace maka ni”? Girgiza mata kai yai alamar a’a, ya ƙara da cewa”Sai inda ƙarfi na Ya ƙare, “ Lumshe ido ta ɗan yi calmly ta furta “Yadda muka sha wahala atare Danish, Haka nake so Mu ji daɗi atare, Bani da abokin rayuwar daya wuce kai a faɗin duniyar nan, Kaine mallakina, masoyi na har abada, ta ya ya kake tunanin zan iya canza ma ka? Ai kaine nake tsoron Ka canza min idan mun shiga Cikin gari, saboda nasan mutane da yawa zasu dinga rububinka saboda kyawun Da Allah yayi maka, Sannan bansan su wanene Iyayenka ba, amma inaji araina ba ƙananun mutane bane yadda kake da kyan nan da izza ɗabi’unka sak Irin na ƴa’ƴan Hamshaƙan masu kuɗi ne, Ni ko ka ga ba ƴar kowa bace, Mahaifina ɗan Jarida ne kuma ya rasu ma, “ Idanuwanta acike tab da ƙwalla tayi maganar, ƙwallar na gangarowa saman kuncinta yai saurin sanya tongue dinshi Ya lasheta, nan ta ke ta ji yanayin jikinta ya fara canzawa. “Ni bani da iyaye Angel, Ki daina yi min maganarsu bana son ji, ke ce uwata kuma kece ubana, Kece gatan da nake dashi, Idan ina dake bani buƙatar kowa,” muryarshi a kausashe yake yi mata magana, Ta fahimci bayason zancen Iyayen shi da take yi mashi. “Meyasa bakason Inayi maka maganar iyayenka? Danish Salsabeel ya faɗamin tun kana jariri aka sadaukar dakai, Naji raɗaɗi jin hakan acikin zuciyata, sai dai Ni bazan Iya yankewa iyayenka hukunci ba, Kada ka manta sadaukarwar kurkukun ƙaddara ba dole sai iyayenka ba, zai iya yiwuwa ba sune suka sadaukar dakai ba, wata’ƙil ma basu da masaniyar kana araye....” bai bari ta taƙarasa maganar ba yai saurin toshe mata bakinta da tafin hannun shi”Is ok, Kije ki kwanta dare Yana ƙara yi,” maƙe mashi kafaɗa tayi”Idan Kaga na kwanta toh muna atare da juna ne,”kafiya ta sanya mashi ya rasa ya zaiyi da ita, A ƙarshe dole Ya haƙura Ya ƙyaleta, kwantar dakanshi yai saman ƙirjinta, Taci gaba da kwance mashi kitson kanshi, Kafin bacci Ya ɗauke su saida ta warware kitson duka, A manne da juna suke ta sharar baccin su, Karo na farko da ya fara runtsawa Acikin Dajin❗❗❗ *Boss Bature✍️ Mu haɗu gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*KURKUKUN ƘADDARA*_ _The Prisoners E10🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* ~Middle step~ _A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._ A Kwance ya ke saman shimfiɗeɗan gadonsa, Kamar kullum cikin shigar larabawa, hannun shi a ruƙe da wayarshi, Ya ƙurawa Hoton wallpaper ɗin shi ido, ko ƙyaftawa bai yi sam baya gajiya da kallon hotonta, Yanayin fuskarshi Ya nuna tsantsar damuwa, a hankali ya ɗaura yatsun shi saman hoton kan wayar yana shafa fuskarta, lumshe idanuwanshi Ya ɗanyi kafin a hankali ya ware su kan hoton, waƙar larabci ya soma rairawa da daddaɗar muryarsa duk akan hoton wadda ya ke kallo, ya dage yana yi mata waƙa mai nuni da ƙaunarta da yake yi, Tunawa da bata a raye yasa shi dakatawa da raira waƙar, Ya jefar da wayarshi gefe ɗaya saman mattress ɗin, haɗi da kifa kanshi saman pillow, kamar ƙaramin yaro ya fashe da kuka mai tsuma zuciya, abun ne yana damunshi ya hana rayuwarshi sakat. “Shureim, Ka yi haƙuri Ka daina sanya damuwa aranka, I know it hurts you, but worrying won’t make anything better, it’ll only make things worse kuma ka tuna Allah yanasan bayinsa masu tuba, Kana fa da ilmin ka ba sai na tunasar da kai ba,” bai tsammaci jin muryarta ba, A hankali Ya ɗago da idanuwanshi Waɗanda su ka kaɗa jawur da su, ya ɗaura su kan fuskar Zainab. Tana a tsaye cikin shiga ta riga da skirt, kanta sanye da hula, ga dukkan alamu daga kitchen ta fito. “Babu wanda yasan nashigo shureim, Satar hanya nayi don nasan idan hajiya layla ta sani ba za ta bar ni in zo wurin ka ba.......” numfasawa ta ɗanyi kafin ta ɗaura da cewa”Tuntuni na so mu samu lokaci muyi magana sai dai ban samu damar yin hakan ba saboda baka nan, till today” har cikin zuciyarshi ba ƙaramin sanyi yaji ba, yunƙurawa yai tare da miƙewa ya zauna ya jingina bayansa jikin headboard din gadon Yana kallonta, Still hawaye basu daina wanke fuskarshi ba, Zainab ta damu dashi sosai, har mamaki ta ke yi yadda wasu iyayen Allah ya basu damar haihuwar ƴa’ƴa nagartattu amma suke watsi da su, basu damu da damuwar su ba, yayin da wasu neman ƴa’ƴan su ke yi ruwa Ajallo, tana matuƙar jin takaicin haka. “Aunt Zainab, Kin tabbata ba wanda yasan kin shigo? Ina mommy da daddy ne” “Layla tana a palour, mahaifin ka kuma Yana a garden shi da kawunka Musa” Jin hakan Yasa shi saukowa daga saman gadon shi Ya nufe ta, tsayawa yai suna fuskantar Juna. “Ka faɗa min wani taimako ka ke so In yi maka? in sha Allahu babu abunda zai gagara, a shirye nake da in share maka hawayen ka” Hannayen ta biyu ya ruƙo a cikin nashi gabanta sai faɗuwa ya ke yi, tsoronta kada wani daga cikin Iyayenshi ya faɗo ɗakin, muddin hakan ya faru zata ɗanɗani kuɗarta ne. “Aunt Zainab I feel in my heart that she’s still alive! Tun bayan da abun ya faru I’ve never dreamed of her as dead, I’ve always seen her alive in my dreams.” tun kafin ya ƙarasa maganar ta katse shi “How could that be possible, Shureim? Mutumin da ya mutu ai baya dawowa and the dreams you’re having aren’t real Don’t believe what you see in your dreams.” Fuskarshi a yamutse ya ke dubanta “Amma ni inaji araina bata mutu ba!” kafe mata yai akan zancen shi Ta fahimci ya fara zaucewa, Zaifi ta lalla6a shi don ta kwantar mashi da hankalin shi”shureim, idan ma tana araye da buƙatar mu shirya plan don mu tabbatar da abunda muke zargi,” Jinjina mata kai yai alamar yana fahimtarta. “Dole Ka bi duk a bun da zan faɗa maka,” amsa mata yai da in sha Allah, mu zauna sai muyi magana” girgiza mashi kai tayi”a’a ina tsoron Mahaifiyarka ta faɗo dakin nan, Just A tsaitsaye zan faɗa maka matakin da zaka ɗauka domin mu ci nasara akan binciken da zamu yi” zame hannunta tayi daga cikin nashi da sauri ta nufi ƙofar ɗakin ta leƙa tana duban ko’ina don kada wani ya faɗo masu, ganin bakowa yasa ta gyara labulan ɗakin nashi, ta juyo da sauri ta nufe shi Yayin da take cigaba da yin maganarta”mataki na farko shine Dole ka tanƙwashi zuciyarka, ka danne raɗaɗin da ka ke ji ka daina sanya damuwa aranka” “Mataki na Biyu Ka daina gudun Iyayen ka, Ina nufin Ka koma masu tamkar yadda ku ke da su Ada, Biyayya sau da ƙafa, ka nemi yafiyarsu akan 6ata masu rai da ka ke Yi.....” tun kan ta kai ƙarshen maganar ta lura da canzawar da yai, a marairaice yace da ita”Aunty zainab taya zan iya yin hakan? Ni bana jin zan Iya sakar masu fuska mu koma kamar yadda muke ada” murmushi ta ɗan saki kafin tace”Shureim kenan, Nafi so ina magana kana fahimtata, ta wannan hanyarce kaɗai zamu Iya gano meke wakana a tsakanin Iyayenka” jinjina mata kai yai alamar ya fahimta. Har ya buɗe baki zai yi Magana ya ji ta yi saurin katse shi da cewa “Me ka ke buƙata in kawo maka? nasan kana jin Yunwa” A ruɗe ya ke kallonta da mamaki Akan fuskarshi, Me ya kawo zancen yunwa acikin maganar su. “Ko dai kana buƙatar chips in haɗo maka da shi”? Ta wutsiyar idon shi Ya hango Layla A tsaye bakin ƙofar, Ta kifa ɗaurin ɗan kwalin atampa akanta, Riga da skirt ne sun bi shape ɗin jikinta, duk da alamun manyantaka atattare da ita, hakan bai 6oye kyawun surarta ba. Wahalallan Yawu ya haɗiya haɗi da sauke nauyayyar ajiyar zuciya, aranshi ya ayyana ko yaushe tazo bakin ƙofar! Sai yanzu ya fahinci dalilin canza maganar zainab, ita tun kafin layla ta shigo tajiyo takun takalmanta saboda bata sanya takalmi idan ba mai tsini ba, Ba don Allah yasa taji motsinta ba da ko ta yabawa aya zaƙin ta “Aunty zainab wai meyasa ki ke son takurani akan dole sai naci abinci, nace maki bana jin yunwa ki tafi kawai, Ni bana buƙatar ganin kowa akusa da ni, ana dole ne” Ranshi a matuƙar 6ace yai maganar, tare da Juya mata baya, Ya ruƙe qugu da hannu ɗaya, Zainab dake kallon bayanshi tace”Shureim zama da yunwa zai Iya haifa maka wata matsalar, abunda bama fata, Ni bari naje na faɗawa mahaifiyar taka kaƙi cin abinci wataƙil idan ita tayi maka magana ka ci” Har zata Juyawa shureim Ya juyo a sukwane Ya daka mata tsawa”Karki Kuskura ki ce zaki haɗani da ita, Ko kin faɗa mata abanza, matar da bata damu da ci na ko sha na ba.....” Sai da yai wannan maganar, Layla ta kai hannu ta ɗan kwankwashi Jikin Ƙofar ɗakin nashi Don hankalinsu ya dawo kanta, tamkar basu san da zamanta ba suka ɗago suna kallonta, Fuskarta tasha uban make up, gashinta baki wulik har mid back ɗinta, Cikin takun izza da nuna isa Ta nufo su tana magana”Zainab Nagode da kulawarki akan ɗana, ki ƙyale shi, shureim ya daina jin maganar kowa a yanzu bansan laifin me mu ka yi mashi ba da yake gudun mu,’ tun da ta fara magana Zainab take sauke ajiyar zuciya, jin bata gano me suke tattaunawa ba, shureim ko sai ƙara ɗaure fuskarshi ya ke yi kamar zata fashe saboda tsabar nuna fusatarshi. Idanuwan mahaifiyarshi akan fuskarshi, Cikin girmamawa zainab tace”Shureim har yanzu yaro ne, tun da yana a ƙarƙashin kulawarku, sai ana haƙuri dashi ana kuma lallashin shi da jan shi a jiki ta hakanne zamu iya sanin meke damun shi” jikinta na ɗan kerma tayi maganar, gyaɗa kai Layla tayi”is Okey, ba sai kin koyamin yadda zan Kula da ɗana ba, Ni da na haife shi ni nasan kayana, Zaki Iya tafiya ki bamu wuri” ta yi maganar tare da nuna mata ƙofa da hannu. layla kenan Ita ba’a mata gwaninta, Jiki asanyaye zainab ta kama hanyar fita ɗakin tana tafiya tana waiwayon shureim da ido take Yi mashi alamar Ya sake mata, kada ya manta da shirinsu, Lumshe mata idon da yai ne yasa ta fahimci ya gane me take nufi, Bayan fitar zainab, Layla ta tsare shi da idanuwanta “me zan yi maka wanda zaisa Ka daina guduna? Haba Shureim saboda na kore ka cikin fushi shine ka kama Hanya ka tafi egypt wurin Ammi, Kasa ta kirani awaya tana ta zazzaga min masifa, ‘ ranta a6ace take yin maganar, har ya harzuƙa zai mayar mata da martani kalaman zainab suka faɗo mashi arai da sauri ya danne fushinsa, abunda ta tsana dashi tana magana Yana shareta, Wuyan farar jallabiyar jikinshi ta damƙa da hannayenta waɗanda ke a sanye da awarwaro da zabba na zallar zinari, Jijjiga shi tai”Shureim so kake baƙin cikin ka ya kashe ni? Na rasa benazir kaima kuma kana neman ɗaura min hawan jini, so ka ke zuciyata ta buga in mutu shureim”? hankalin shi ba ƙaramin tashi yai ba, ganin hawaye sun ciko idonta. Duk da yasan ta yi hakanne don ta samu kanshi, sassauta muryarta tayi tare da sakin Kwalar rigarshi”Kai kaɗai nake gani naji daɗi, Meyasa ba za ka manta da abunda yawuce ba, ina magana kana share ni, kasan bana son hakan, Yana ƙona min rai” baisan sa’adda hawaye suka cigaba da wanke fuskarshi ba, muryarshi na ɗan rawa ya furta”?mommy saboda ni za ki zubar da hawayen ki”? Muryarta a kausashe tace”Shureim, how many times have I cried for you? I understand that you’re trying to drive me crazy,” Shureim ka daina ƙaunata” Tai maganar tana watsa hannayenta’ shiru Ya ɗanyi yana kallon fuskarta, tabbas ya ga 6acin rai acikinta. “Astagfurillah” jin ya ambaci haka Yasa ta zaro idonta akan fuskarshi “Mommy, I didn’t know you cared about me that much, I thought you’d stopped loving me, amma yanzu mommy akaina kike zubar da hawayenki”? Mamakin kalaman shi ne yasa ta kafe shi da ido ba ƙyaftawa, Hadisi Ya soma janyo mata da ayoyin al’kur’ani mai girma waɗanda ke magana akan wanda Ya ƙuntatawa iyayen shi. “Shureim ka sani kuma kake take sani? Shine Ka rufe ido Kana ƙuntata min? Meyasa”? Marairaice mata fuska yai”ya zanyi! Sharrin zuciyane da kuma sharrin shaiɗan, sune suke azalzalar zuciyata akan abunda Ya faru, sunƙi bari na manta komai,” Dafa kafaɗar shi tai da hannunta ɗaya”Ka yafe min shureim, nayi maka alƙawarin zan tarairaye ka na baka kulawa kamar yadda muke ada, Sannan inaso kamanta da abunda ya wuce, Ba laifin mu bane, mu ne sila, amma kaine ka aikata komai ba tare da ka yi shawara damu ba, kai kasan ba yadda za’ai da hankalin mu da tunanin mu mu goyi bayanka akan aikata hakan, a lokacin da ace ka yi shawara damu wlh shureim ba zamu goyi bayan abunda ka aikata ba” har cikin zuciyarta ta ke magana, Shi kanshi Yaji jikinshi yai sanyi, zuciyar shi ta karaya, tabbas maganar da ta faɗi gaskiya ne. “ Mommy, ni ne ya kamata na nemi yafiyarki, akan gudun ku da nake Yi ke da Daddy, Dan Allah ku yafe min, na gane kuskurena” yai maganar yana ƙoƙarin zubewa saman gwiwowinsa da sauri ta ɗago da shi ta rungume shi tana ɗan bubbuga bayanshi da yatsun hannayenta, Farin ciki duk Ya cikata, ta manta when last ta ji ɗumin shureim a jikinta, saboda rashin jituwar dake a tsakanin su. Muryar shi da alamun karaya ya furta mata”Mommy, ana ‘uhibuk kathiran” Hawayen da suka taru acikin idanuwanta ne suka soma gangarowa saman kuncin ta, still ba su raba jikinsu daga na juna ba, martanin maganarshi ta mayar mashi”i love u too My son, ba zan Iya misalta farin cikin da nake a ciki ba, Shureim ka faranta min rai,” ta yi maganar tare da raba jikinsu daga na juna, fuskokin su ɗauke da murmushin ƙauna “Idan har dagaske mun shirya inaso daga yau ka goge duk wasu hotunanta dake a cikin wayarka, kallonsu baida amfani shureim, saboda suke fama maka raunin dake a cikin zuciyar ka” Shiru yai yana kallon fuskarta, har sai da ta kai ƙarshen maganar, Har ga Allah bai jin zai Iya goge hotonta a wayarshi, don ba ƙaramin sanyaya mashi zuciya suke yi ba aduk lokacin da ya kalle su, Allah ya jarabce shi da ƙaunarta, Yafi sonta akan kowa na duniyar nan, duk da bata araye. Gudun kada ta zarge shi, yasa shi yin saurin cewa”saboda farin Cikin ki mommy zan yi deleting ɗinsu, ni kaina bana son abunda zai ƙara shiga tsakanina da ke,” Gyaɗa kai ta yi “Shureim ka ɗauko wayar ka goge su agabana In gani” tuni yasha jinin jikin shi, ba don yaso ba ya amsa mata da toh, slowly ya juya ya nufi gadon shi ya ɗauko wayar, Kafin Ya kai mata, wayar ta hau ruri, hakan ba ƙaramin daɗi yai mashi ba, Waiwayowa yai still tana a tsaye tana kallon shi”who’s calling u”? Ta jefa mashi tambayar, Nuna mata screen ɗin wayar ya yi sunan Daddy ne Ya bayyana akai” Umarni Ta bashi ya ɗaga kiran Ya kara wayar a kunanshi, Muryar Alhaji Ubaid ce ta ratsa kunnuwanshi”Shureim Uncle ɗin ka na son ganin ka, gamu nan zamu shigo cikin gidan” muryarshi A sanyaye ya amshi mashi da toh, takaicin shi ɗaya layla taƙi tafiya, ta tsare shi da ido, adan dole sai ya goge hotunanta awayarshi. A hankali ya zame wayar daga kunnan shi, matsawa yai kusa da ita, Bayan ya cire password Na wayar Ya miƙa mata adai dai kan Gallery ɗinshi, Ta kar6i wayar tana duba hotunan, Ta yi mamakin ganinsu kamar hauka, hada wanda ya ke a rungume da ita saman ƙirjinshi, ta6e baki layla tayi, hankalin shureim ba ƙaramin tashi yai ba ganin zata danna delete all, jikin shi har tsume ya ke yi. “Assalamu alaikum”! Muryar zainab ce ta katse mata hanzarin ta, a sukwane ta juya tana binta da kallo, a bakin ƙofa ta tsaya”Alhaji ne ya shigo tare da kawun shureim, Shine yace nayi maki magana...” yatsina fuska layla tayi”Naji, ga ni nan zuwa” Miƙa wa shureim wayar tayi”ka tabbatar ga goge su, sannan ka fito ku gaisa da kawunka,” Amsa mata yai da toh, Bayan ya kar6i wayar, fitar ta keda wuya Ya cire memory ɗin wayar, Ya 6oye shi a cikin rigar pillow, Ajiyar zuciya ya sauke Ba ƙaramin daɗi yaji ba, don ji ya ke kamar za’a raba shi da ranshi idan akace ya goge hotunanta. Toilet ya shiga ya wanko fuskarshi, Ya futo Ya nufi dressing mirror, cikin jerin turarurrukansa ya ɗauki ɗaya ya feshe shi a jikin shi, bayan ya ajiye ya fito daga ɗakin Ya nufi babban palourn. *GIDAN ƊAN IYA* Tun da ta fito daga cikin toilet ta ke a tsaye bakin wardrobe, daga ita sai Towel ɗaure a ƙirjinta, Ya sauko har saitin gwiwarta, a ƙalla Tafi ƙarfin mintuna goma, ba tare da ta motsa ba, idanuwanta na akan Jerin suturarta da ke a ninke sun sha guga, ba komai ne ya tsaida ta ba fa ce neman kayan da zasu dace da tarban Manyan baƙin su da zasu Yau, Ruwan ido take yi, duk kayan da ta ɗauko sai taga kamar ba zasu dace da ita ba, Wayarta dake a jiye saman drawer ce ta soma ringing, nan ta ke taji gabanta ya faɗi fatanta Allah yasa basu bane suka ƙaraso, Da ɗan saurinta ta nufi wayar tare da kai hannu ta ɗauketa, ko da ta duba screen ɗin wayar, babu sunan wanda ya kira, Baƙuwar number ce, kokwanto ta shiga yi akan ta ɗaga ko karta ɗaga? Don ita a tsarinta bata ɗaga baƙuwar number in dai ba wadda ta yi saving akan wayarta ba ce, kusan sau uku kiran nashigowa Yana yin rejecting ba tare da ta ɗaga shi ba, tayi kasaƙe kamar an dasa mata Aya, Shigowa Cikin ɗakin Zahra ta yi, bakinta ɗauke da sallama, turkish gown ce a jikinta launin pink ba ƙaramin kyau tayi mata ba, tayi rolling veil saman kanta. Ganin Aneelerh a tsaye yasa tace”lafiya? Ya akai naga baki shirya ba? Ko kin manta cewa suna a hanya? Sun fa kusa isowa, Na rasa meke damunki, Ko har yanzu kewar baby junaid ɗin ce bata sake ki ba”? Harara Aneelerh ta ɗan jefa mata, Ba tare da tace koma ba, ta ɗaura wayarta saman mattress, kafin ta juya ta nufi wardrobe din Kayan da ta bari a buɗe. “Zahra zo Ki tayani zabar kayan da zan sanya, Ruwan ido Ya hana ni ɗauka tun ɗazu” murmushi zahra ta saki yayin da take tunkarar wardrobe ɗin”Aunty aneelerh, shiga za ki yi ta mutunci, ta kece raini, Lace ko shadda su zasu fi dacewa, “ Ta yi maganar tare da Kai hannu cikin wardrobe ɗin kayan ta janyo mata wani haɗaɗɗan lace launin golden colour, ta miƙa ma Aneelerh, Fuskarta ɗauke da murmushi ta kar6i Kayan da zahra ta miƙa mata”na yadda ke ƙwararriyace a6angaren iya zabar kayan da zasu dace da mutun, nafi karfin 15 mins ina neman wanda zasu dace dani na kasa, sai da ki ka zo” Zahra tace”kada ki manta aikina ne, burina kiyi kyau auntyna, surukanki su ganki a mutuncenki, bari naje na ɗauko maki sarƙar da zata dace da kayan, ‘ amsa mata Aneelerh tayi da toh, Wuce wa zahra tayi agaban drawer chest Ta zuƙunna ta dauko mata jewelry box dinta, Ta buɗe ta lalubo mata necklace da earrings launin Lace ɗinta, maida box dinta tayi kafin ta miƙe ta daura mata su gaban mirror. “Aunty aneelerh, Ga su nan saman mirror, Pls Ki shirya da wuri, Ni zan je na taya su mami shirya masu abincin” Amsa mata ta yi da toh ta ƙara da yi mata godiya, Bayan fitar zahra, Aneelerh ta shirya tsaf cikin Lace ɗinta, riga da skirt, sun yi bala’in yi mata kyau, sun ɗan kama jikinta, shape ɗinta ya fito sosai, Kamar a jikinta aka ɗinka kayan, a gaban mirror ta zauna tana yin make up, lip gloss ta shafa ma la66anta, Ta ɗan shafa hoda, ta ɗauki brush tana gyara jagirarta, ‘ Sumar kanta Ta sauko har saman bayanta, ƙarar Shigowar text a wayarta ne yasa ta ɗan kalli 6angaren da wayar take ajiye saman gado, sai lokacin ta tuna da baƙuwar number da ake ta kiranta ɗazu, sai da ta fara Ɗaura dan kwalin leshin Kafin ta miƙe ta nufi wayar ta ɗauke ta, Da yatsan hannunta ta janyo sakon A hankali ya buɗe, Ta yi mamakin ganin Sunanta da aka rubuta da manyan haruffa, menene ma’anar sakon? Just Aneelerh? Wanene wannan? Kiran number ta soma ƙoƙarin Yi sai dai taƙi shiga, A ƙarshe ta hakura ta daurata saman pillow, Gaban Mirror ta koma ta ɗauki jerin turarurruka tana feshe jikin ta da su, tunawa da baby junaid ɗinta yasa ta ɗan saki murmushi, tayi missing ɗinshi sosai, yau tun da safe Mahboob Yaje kai shi school, Bayan ta haɗa da shi da kuɗin fetur, kusan sati biyu da fara zuwanshi makarantar, kullum da fara’a yake tafiya, yana zumuɗi, da zarar an kaishi Ya ke saka masu rigima sai sun dawo dashi gida, Har atashi daga school ɗin Yana yin kuka, Fuskarshi jawur ake dawo mata da shi. Malaman makarantar har sun canza mashi suna daga Junaid zuwa babyn mommy, saboda sunanta da yake yawan kira masu. Daga waje tajiyo muryar Zahra tana kwaɗa mata kira”Aunty Aneelerh! “ girgiza kai tayi aranta tace”Ko yaushe ne zahra zata daina Yi min irin wannan kiran talaucin kamar zata ƙararmin da sunana” Zahra na shigowa ɗakin ta Waro ido waje tana fadin”Wow!!! Tabarakallahu Ahsanul khaliqin Aunty aneelern kinga yadda ki kai kyau? Kamar wadda zata shiga gasar miss world,” harara Aneelerh ta jefa mata fuskarta asake tace”Naji na gode Da yabo, ni dai yanzu faɗa min Kiran menene kike yi min”? Watsa hannu Zahra Tayi”dama ummi ne ta aiko ni zaki ci abinci yanzu ko sai anjima idan sunzo”? “Yunwa nake Ji zahra, ba zan Iya jira sai sun zo ba, ki samu plate ki zuba min dambun shinkafa, Ki haɗo min da lemu mai sanyi, “ “Toh, Amma kafin nan mu ɗanyi selfy mana” ta yi maganar tare da Kunna camera din iphone nata, ta ɗaga Wayar Tare da ɗaura kanta saman kafaɗar Aneelerh, gaba ɗaya suka saki murmushi, ‘ kusan hotuna Biyar tayi masu atsaye kafin Ta nufi hanyar fita ɗakin tana faɗin”Idan surukan naki sunzo zamu ƙara yin wasu hotunan tare, Hakan Yana ƙara danƙon zumunci,” fuskar Aneelerh ɗauke da murmushi ta ke bin Bayan Zahra da kallo, gefen gadon ta zauna tana Jiran dawowarta. *EVIL FOREST* Tun da garin Allah Ya waye Masu a cikin ƙurmin dajin, Kowan nan su Ya farka, Da wata irin matsiyaciyar yunwa, suna zazzaune abakin bishiya sun jingina bayan su, Sai hamma suke Yi, Jiya basu ci abinci da yawa ba kafin Kwanta, sauran Kayan marmarin da suka rage ne su ka sha, dan ma suna da jumurin yunwa, Hankalin su ba akwance Yake ba, Danish Yaƙi farkawa daga bacci, tsawon awanni tun daren Jiya da Angel ta sanya shi yin bacci yake ta yi, Ko motsi Ba ya yi numfashinsa ne kaɗai ke fita, tun suna sa ran zai farka har sun fara tunanin Anya kuwa Lafiya? Baccin ya wuce na hankali, domin kuwa tuni safiya ta jima da wuce wa sun shiga tsakar rana. Sun tsare shi da ido suna kallon shi, A saman shimfiɗar da Angel ta yi mashi, ya ke a kwance sun ƙudundune shi da bargo, tuntuni su ka so su tada shi daga bacci amma Angel ta hana su, ita aganinta bai kamata su takura mashi ba, tsawon wata ɗaya baya runtsawa kullum shine yin gadinsu, Na yau kawai Ya samu ya runtsa ai bai kamata su katse mashi hutun shi ba. “Angel Yunwa mu ke Ji” Parveen ce Ta yi maganar, Fuskarta A kumbure ga miyan bacci a gefe da gefen bakinta, sumar kanta A haukace take babu gyara kamar Ƴar mahaukaciya, Angel da ke Fuskantar su tana zaune daga gefen shimfiɗar Danish, fuskarta sam babu walwala, abun ya fara damunta ganin yaƙi farkawa fatanta Allah yasa baccin lafiya ne ya ke yi. “Genie we are feeling hungry, pls cikina kukan Yunwa yake mini” Jemimah ce tayi maganar, tamkar zata fashe da kuka, idon Angel akan fuskokinsu, Batul sai hamma take Yi, tana faman yamutsa fuskarta. “Ki jaraba Tada shi mana, wata’ƙil Ya farka, Tun da kinga mu bamu san kan dajin nan ba, balle mu ce zamu shiga ciki mu nemo abinci” Naufal ne yai maganar muryarshi da kasala. “Ni zan Iya zuwa na nemo mana abincin sai mu ci” Gabriel Ne yai maganar, hannunshi ɗaya asaman sumar kan Azeeza da ke kwance saman ƙirjin shi. Girgiza kai Angel ta yi”A’a Gabriel, ba sai ka je ba, Danish ne kaɗai zai Iya shiga dajin nan Ya dawo ba tare da wani abu ya same shi ba,” bubbuga ƙafa jemimah tayi cikin shessheƙar kuka tace”wai genie Ya ki ke so Mu yi ne mu fa yunwa muke ji, Ki tada shi ki tada shi Kin ƙiya so kike mu mutu ko”? Gaba ɗaya hankalinsu Ya koma akan jemimah dake Yiwa angel faɗa, ita kanta Angel kallon nata take yi, ganin yadda ta 6ata fuska, Kumatuntu sun yi jawur da su tsabar fusata. “Angel ku tada shi mana” Da sauri suka kalli Haris Da yai magana, Tun da su ka baro kurkuku, baya magana daga Eh sai a’a, su kaɗai ne abunda Yake iya furtawa, amma yau sai gashi yayi masu magana, sun ɗanyi mamaki kuma sunji daɗi ga dukkan alamu sauƙi ya samu Saboda maganar Haris yasa ta kai hannu ta bubbugi kafadar Danish, Muryar ta ƙasa ƙasa take furta sunanshi”Danish wake up! Ka tashi suna jin yunwa,” shiru bai motsa ba, Kusan sau biyar tana yi mashi magana har acikin kunnanshi takai bakinta Nan fa gabanta ya fara faɗuwa, Parveen tace”ki buge shi mana wata’ƙil ya farka” Ba tare da ta kalli parveen ba tace”bazan Iya ba” ta ambaci hakan tare da cigaba da kwala mashi kira. “Angel nauyin bacci ne da shi, Ba haka yakamata Ki tayar dashi ba, let me help u, “ Gabriel ne ya ambaci Hakan, Sai da ya fara janye azeeza daga jikinshi, tukunna Ya matsa gaban shimfiɗar Danish, bubbuga kafadarshi ya yi Da ƙarfi haɗi da ambaton Sunanshi”Danish! Danish!” yadda yake kware murya hatta su kansu sautin Ya cikasu, amma wani iko na Allah Danish ko girgiza Bai yi ba, Zuciyar Angel a jagule ta ɗaura Kunnanta saitin ƙirjinshi Bayan ta yaye mashi bargon, jin heart beat ɗinsa yasa ta ɗan sauke ajiyar zuciya sai dai ta yi mamakin dalilin rashin farkawarshi, Hankalin sauran ƴan uwan Yaƙi kwanciya, Gaba ɗaya suka dawo kewaye da shimfidarshi Kowa Ya zuƙunna Su Azeeza har sun fara shessheƙar kuka suna faɗin Wayyo Allah Danish ɗinmu meke damunka, dan Allah ka farka ka yi mana magana ko hankalin mu ya kwanta, Mu mun haƙura ma da abinci kai kawai muke so ka tashi. “Ko dai suma ya yi ne? Ku duba cikin gorar ruwan mu idan akwai sauran ruwa ku ɗauko Mu yayyafa mashi” Gabriel ne yai maganar cikin rashin kwanciyar hankali, Angel tace”a’a kada ku watsa mashi ruwa, Zuciyarshi fa tana bugawa, bacci ya ke yi, kunsan Danish da nauyin bacci, Balle kuma da ya ɗauki tsawon kwanaki bai runtsa ba,’ ɗaya bayan ɗaya suke jogana kunnansu saman kirjinshi don su ji idan zuciyarshi na bugawa, Hankalinsu Ya ɗan kwanta da jin sautin heart beat din nashi. “Nasan nan bada jimawa ba zai farka, Mu ɗan ƙara haƙuri” Miƙewa Jemimah tayi tare da bubbuga ƙafarta, abunka ga yaro ba haƙuri, Yunwa ce ta addabeta, Juyawa tayi gaba ɗaya suka bi bayanta da kallo, agaban korayen ciyayen dake shimfiɗe a wurin ta tsugunna, ta soma tsigowa tana turawa abaki tana ci, hakan da tayi ne ya tuna masu da Ganyen da ake basu a prison, aiko da sauri batul da Parveen da azeeza suka mimmiƙe agaban jamimah su ka zuƙunna kamar akuyoyi haka suke cizgar ciyawa suna ci, tsawa Angel da daka masu”Meye haka dan Allah? Kunsan wani irin ganye ne ku ke ci? Ku daina” a tsawace ta ƙarasa maganar, ta mike ta bi su ɗaya bayan ɗaya tana kwace ciyawar da suka damƙa a hannun su, Fashe mata da kuka Parveen da jemimah su ka yi Nan take taji zuciyarta ta karya, cikin shessheƙar kuka suke faɗin ba za su iya jurewa ba, yunwa ce ta addabe su, ta taimaka tabar su su ci ganyen, suna jin daɗin shi ahaka. Idanuwanta acike tab da ƙwalla tace”Is ok, Bari na shiga cikin dajin in nemo mana abincin da zamu ci,” miƙewa Gabriel yai”Zan bi ki Angel” girgiza mashi kai tai”A’a gabriel, Ka zauna ka kula da su Azeeza, Yanzu zan dawo” ba don yaso ba ya amsa mata da toh, Kallon sauran Ƴan uwan nasu tayi”Javed Naufal, Ku kula da su Azeeza, Yanzu zanje na dawo,” Naufal yace”meyasa zaki tafi ke kaɗai, bayan kin faɗa mana mu yi takatsantsan da dajin nan akwai mugayen halittun da zasu Iya cutar damu, why angel? Gaskiya ni ban goyi bayan ki tafi ke kaɗai ba, sai dai mu tafi mu duka,” Yai maganar tare da miƙewa, Javed ma Ya miƙe, haris ne kaɗai Ya rage a zaune yana sauraronsu. Ita kanta gabanta faɗuwa yake yi gani ta ke yi kamar wani mugun abun zai iya faruwa da ita Murmushi ta ƙaƙalo akan fuskarta duk don ta kwantar masu da hankulan su yasa tace”Bawani abu fa, da zarar nayi addu’a Allah zai tsare ni har inje in dawo lafiya, ku kwantar da hankalinku” girgiza kai Gabriel yai”bazai yiwu ba Angel, bana so wani abu ya same ki ta silar mu, idan har ba zaki bari mu bi ki ba, To ki bari Danish Ya farka Ya je da kanshi ya samo mana abincin....” tunkan ya ƙarasa maganar Angel tai saurin katse shi da cewa”su Azeeza yunwa su ke Ji, Na yadda Gabriel Ka raka ni mu tafi, ku kuma ku zauna yanzu zamu dawo” Hankalinsu ya ɗan kwanta, Atare da Gabriel Suka nufi Cikin dajin, Hannunta ruƙe da ƙaramin kwandon su, komawa su azeeza su ka yi abakin bishiya suna zaman jiran dawowarsu. Cikin dajin suka kutsa suna tafiya suna dan tattauna fira a tsakaninsu, ta ko’ina bishiyoyine masu tsayi Da faɗi, Rassansu sun lullu6e wurin da inuwar su. “Hankalinka ya kwanta ka biyo ni, ni ban san ma ina zamu dosa ba, Ka ta6a shiga daji”? Ta jefa mashi tambaya, girgiza mata kai yai alamar a’a”bazan Iya tunawa ba Angel, na manta da komai na rayuwata, amma inaji araina koda ace ban ta6a shigowa daji ba, zai iya yiwuwa na ta6a kallon shi a waya, Ni yanzu burina mu fita daga Cikin Dajin nan, Ko mun samu mu tona asirin zaluncin da ake yi a cikin kurkukun ƙaddara, Angel na damu da rashin ƴar uwata, ina tsoron kafin mu yi nasara su kashe min ita” yayin da yake yin maganar yanayin fuskarshi ne Ya canza, abun ba ƙaramin ta6a zuciyarshi yake yi ba duk in ya tuna da ƴar uwarshi Gabriellah. Cikin nuna jin tausayin shi angel tace”ka kwantar da hankalin ka, Idan Allah yasa mai tsawaicin kwanace zamu ganta, in kuma ta riga mu gidan gaskiya, Allah Ya jiƙanta, yana daga cikin ƙaddarar bawa, ba dole ya rayu da abunda ya ke so ba, wata rana ma kowa zai mutu ba wanda za’a bari gadin duniyar.......” fira ta yi daɗi sai nutsawa suke Yi, cikin Dajin ba tare da sunsan inda zasu dosa ba, Ga wata iska mai daɗi da ta ke kaɗawa, wasa wasa Ƙarfin iskar sai ƙaruwa ya ke Yi, ta cika masu idanuwansu daƙyar suke buɗe su. Yayin da su Angel suka tafi nemo masu abinci, Sun yi zazzaune zaman jiran tsammani, Har sun fara lumshe idanuwan su saboda iskar dake kaɗa masu ba ƙaramin kasala take haifar masu ba, kwatsam! Ba zato ba tsammani kunnuwansu suka soma Jiyo masu wani irin sautin gurnani mai matuƙar rikitarwa da razanarwa, A firgice suka ware idanuwansu, Yayin da zuciyarsu ke buguwa da ƙarfi da ƙarfi tamkar zata 6allo ƙirjin su, tsananin tsorone Ya kamasu sai faman wurwurga ƙwayar idanuwansu suke Yi, a ƙoƙarinsu na su gano ta inda sautin gurnani ke fitowa, sai dai sun kasa sani kuma sun kasa ta6uka komai, Azeeza tuni ta shige ma Batul kamar zata koma Cikinta, Jikin su sai faman yin kakarwa yake yi saboda gurnanin ya cika kunnuwansu, Haris dake azaune gaban shimfiɗar Danish muryar shi adabarbarce ya ke ambaton sunanshi”da..da..nish ka tashi, pls ka tashi danish, Wani abu yana tunkaro mu’ Da rarrafe su batul suka ƙarasa gaban shimfiɗar Danish, Cikin fitar hayyaci suke bugun Jikinshi don ya farka ya ceci rayuwarsu, duk sun bi sun ruɗe tsigar Jikinsu ta tashi haiƙam, Har suna haɗa baki wurin ambaton sunanshi”Danish mun shiga uku, dan Allah ka farka, Wannan wani irin sauti ne haka babu daɗin ji, ga Angel bata nan sun tafi tare da Gabriel, Ni dama nasan zai yi wuya mu bar dajin nan da ran mu’ cikin shessheƙar ku ka suke magana hawaye na bin fuskokinsu, Jemimah da azeeza tuni sun rushe da kuka mai sautin gaske, tunkafin ma suga menene ke tunkarosu, sautin kukansu Jemimah shiya ƙara Janyo hankalin Abunda ke nufo su, basu san sune suke Janyo shi ba, babu wanda yai hankalin Ya tsawatar da su akan su daina Yin kukan suyi shiru, ba su yi tunanin yin hakan ba, lokacin da sautin gurnani ya ƙarfafa hatta ganyayyakin dake a wurin Girgixa suke yi, nan take idanuwansu suka tsaya cak akan wurin da suke zargin zai 6ullo, Kamar An Jeho suka faɗo ƙasan wurin, wasu irin Mugayen Halittun namun dawa, masu gashi gashi a jikinsu babu kyan gani gwanin ban ƙyama, Suffarsu tamkar ta majici sai dai sun gurmi maciji a halitta tsaf zasu Iya haɗiye mutun su nannade shi a cikin bakunansu, Tashin hankalin da ba’a sama shi Date, Wata irin gigitacciyar ƙara suka fasa, Ganin Yadda halittun suke Kurɗaɗowa saƙo da lungu masu Yawan gaske gasu manya manya, Gadan gadan suke tunkarosu Harwani nannaɗe Jikinsu suke yi suna harɗewa, tsabar firgi da tsoro ne yasa suka Watsa da gudun gaske kamar zasu Tashi sama, Gudu su ke yi na fitar hayyaci, gudun ceton rai, su kan su basu son Inda zasu dosa ba, wani ƙarin tashin hankalin Halittun da gudu suke binsu, Ga sauri da Allah yai masu, sun fuskanci matsanancin tashin hankali mara misaltuwa, musamman ƙananun cikinsu Azeeza da jemimah duk sun tarwatse kowa Da inda nufa, dan bala’i, Halittun suna lura da kowace kusurwa suka faɗa, Yadda suka raba kawunansu haka suma halittun su ka karkasa kawunansu wurin binsu, Haris da ba ƙoshin lafiya gare shi ba, tuni Numfashin shi ya soma sarƙewa, bakinshi ya soma fitar da jini, Gashi kowa Ya watse sun barshi, Yana ji yana gani halittar nan Ta ta taɗiye ƙafarshi gaba ɗaya ya kife ƙasa, tana gurnani ta wage bakinta masu haƙora a jere babu kyan gani, ta Zurma ƙafafuwanshi.....Innalillah A 6angaren Azeeza da ke ruƙe da jemimah suna tiƙar gudu, hada tuntu6e sun rasa ina zasu dosa, Jemimah sai kuka take yi tana ambaton sunan Genie, Cikin rashin sanya Wasu muggan ƙayoyi suka Sargaho ƙafafuwansu kusan atare suka rubza ƙasa kansu ya daku. A 6angaren Batul da parveen da Hannah da suka nufi Hanya ɗaya, Halittun nan sai binsu suke yi, sun rasa ina zasu dosa, suna gudu Sumar kansu Na rufe Masu idanuwansu, ba zato ba tsammani ƙafafuwansu suka zurma a cikin wani rami da ca6ali ya cika shi, gaba ɗaya su ka nutse cikin shi, Ko numfashi basu Iya fitarwa. Idan muka Koma 6angaren Angel da Gabriel, lokacin da suka ƙaraso bakin wata bishiyar Mangaro sun tsaya suna tunanin hawa saman bishiyar don su tsigo su, atare suka haye suna aikin tsinkar magaro, sai da suka gama ɗibarshi a cikin kwando, Gabriel na yunƙurin zura ƙafarshi Ya sauko ƙasa kwatsam idanuwanshi suka sauka akan kurar dake ƙasan bishiyar tana cin wani namun dawa data kamo, wahalallan yawu ya haɗiya tare da kallon Angel, ita sam bata lura da abunda ya hango ba, “Gabriel mu sauko mana, Suna jiran mu” Muryarshi Na kakarwa yace”Angel mun shiga uku, wlh kura ce a ƙasa take cin nama,” Sai lokacin ta wurga Idanuwanta ƙasan bishiyar, Gabanta yai mugun bugu, muryarta da tashin hankali ta furta Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un! Kafin Gabriel ya furta wani abu daga can cikin Dajin ihun muryar Naufal Ta karaɗe kunnuwan su, Kallon Juna su ka yi nan ta ke su ka fahimci babu lafiya a wurin Ƴan uwan su, zufa tuni ta wanke fuskarsu, ganin tana yunƙurin sauka yasa gabriel damƙo hannunta, muryarshi a hargitse yace”Kada ki sauka angel kashe ki za ta yi” Girgiza mashi kai tayi idanuwanta sun rikiɗa jawur dasu tace”ƙwara ta cinye ni, wlh sai naje wurin ƴan uwana, Baka ji ihun naufal ba, Allah kaɗai yasan meke faruwa dasu” kokawa suka soma yi da Gabriel a saman bishiyar, ya hana ta saukowa sai kiciniyar kwace kanta ta ke yi, aiko Suna cikin Yin kokawar nan Gaba ɗayansu suka ƙundumo ƙasa agaban kurar nan, Bakin ta ca6a ca6a da jini, Kafin ta ɗago da ido ta kallesu, Da iya ƙarfinsu na ƙarshe suka yunƙura suka miƙe a guje suka watsa, da gudu itama kurar tabisu tana gurnani, babu wanda bai fita hayyacin shi ba, lokacin da suka faɗo wurin da suka bar su azeeza hankalinsu ba ƙaramin tashi yai ba, gabin babu kowa ga kuma Danish a kwance yana ta sharar baccin shi. Kafin Angel tayi yunƙurin zuwa wuri shi kurar nan ta dako uban tsalle ta faɗo masu, Da ƙarfi gabriel Ya fusgi hannunta tana kuka tana ambaton sunan danish Tana miƙa hannu yaja ta da gudu, wani iko na Allah kurar ta tsalle Danish tabisu da gudu, su kawai ta ke hari, kurɗaɗawa suka yi cikin dajin suna gudun famfalaki Kura ta zamar masu masifa ta hanasu sakat.........” *Boss Bature✍️* Tun bayan da dr shureim ya fito daga bedroom ɗinshi ya nufi Palour, A zazzaune ya samu Alhaji ubaid tare da Uncle musa zaune saman Sofa mai mazaunin mutun uku, Layla tana a zaune saman sofa mai mazaunin mutun biyu, Idon shi na akan Uncle ɗin nashi, Ya ɗauki wankan tsadaddiyar shadda mai ɗaukar ido, ƙamshin turaren shi Ya cika palourn, idanuwanshi suna a lumshe, hannun shi na dama haɗaɗɗiyar agogon diamond ce wadda a ƙalla price ɗinta ya kai 300m, mutunne mai ji da naira, hutu ya zauna mashi ko Alhaji ubaid ba zai nuna mashi tarin dukiya ba, ko a muƙami bai kai shi matsayi ba, Alhaji musa ƙanine ga Alhaji ubaid uwa ɗaya uba ɗaya, kuma shine former president, akwai tazarar shekaru a tsakaninsu, A kyawun halitta Musa ya zarce Alhaji ubaid, Yana da hasken fata yayin da Alhaji ubaid yake da duhun fata, Sannan yana da Yalwatacciyar sumar kai tasha gyara ga sajen gefe da gefen fuskarshi baƙi wulik, Kamar matashin saurayi. Ya iya ɗaukar wanka ga aji ga kuma ji da kai. Daga ƙasan carpet dr Shureim ya zauna cikin girmamawa ya gaishe dasu, Alhaji ubaid ne kaɗai ya amsa mashi, kawun nashi kuwa ko arziƙin kallo bai samu ba, har sai da hajiya layla tace mashi”baka ji shureim yana gashe ka ba”? Ba tare daya buɗe idon shi ba yace”Naji,” sanin halin shi yasa Shureim bai damu ba, Layla dai ce ranta ya 6aci dama ita bata iya 6oye fushin ta, Alhaji ubaid ko murmushi ne akan fuskarshi, Har yau mamakin Halin Ƙanin nashi Yake yi. “Shureim, kasan shi fa mutumin turaine ba haka yake son ka gaishe shi ba, Ka matsa kusa dashi yaji ɗumin ɗanshi a jikin shi” acewar Alhaji ubaid, Yatsina fuska layla tayi, aranta kuma ji take kamar ta shaƙe wuyan Alhaji musa, jin kanshi na matuƙar ƙona mata rai, miƙewa shureim yai tare da nufar sofa ɗin da musa ya ke a hakimce, ya zauna daga ƙasa, “Uncle sannu da zuwa, Ya gajiyar tafiya” sai lokacin ya ɗan ware idanuwanshi tare da kallon shureim na tsawon mintuna, sai da ya mula ya sha iska tukunna ya soma magana “Babu gajiya atare da ni, kai zanyiwa sannu, ni banzo da niyar in ganka ba, banma yi tunanin kana a ƙasar ba, sai da Ya ya ya ke faɗamin, shureim kafi ƙarfin ka tako kazo gidana ne? Laifin hada ni ya shafa kenan”? Tun da ya soma magana, hajiya layla take jifar shi da harara a fakaice batare da ta bari Alhaji ubaid ya gani ba, ita sam baya burgeta, haushin nuna isar da yake yi take ji, “Ay min afwa Uncle, bani da kwanciyar hankali ne shiyasa bana samun damar zuwa, amma kuna araina,” Ta6e baki Alhaji musa yai ba tare da ya furta kalma ba Hajiya layla tace”To ai kaima ɗin baka damu dashi ba, Ba ka neman shi taya zai yi tunanin kana buƙatar ganin shi a gidan ka......” bata ƙarasa maganar ba, da sauri ta dakata ganin irin kallon da Alhaji ubaid ya ke jefa mata, sam baya son tana shiga tsakanin shureim da ƙanin shi, saboda mugun son shi ya ke yi baya son 6acin ranshi. “Kare shi za ki yi”? Alhaji musa ne yai maganar sautin muryar shi a kausashe, Shiru tayi bata tanka mashi ba, “Kada ki shiga tsakanin Uba da ɗansa, Kija baki kiyi shiru” Alhaji ubaid ne yai maganar, Ta6e baki tayi tana faman hura hanci. “Ae da kabarta yaya ta ƙarasa maganarta,” yai maganar fuskarshi ɗauke da murmushi. Kafin ya kawar da idonshi daga kallonta. “Shureim, Idan na tashi tafiya abuja atare da kai zamu tafi, bazan barka a gidan nan ba, don Na fahimci akwai masu takura maka, Shiyasa duk ka rame kayi duhu,” Cikin kulawa yake yi mashi maganar, hannun shi ɗaya asaman kafaɗar dr shureim ɗin, Layla ta yi mamakin jin abunda yace, mutumin da ko ƴa’ƴan shi bai sakar masu fuska shine ya ke zancen zai tafi da shureim, kwa6e fuska ta yi don ta fahimci so ya ke ya ƙuntata mata. Alhaji ubaid yana murmushi yace”naji dadin jin hakan, wata’ƙil idan kuka je can yafi sakewa, don na fahimci shureim baya son zama gida...” kafin ya ƙarasa maganar, layla ta katse shi da cewa ‘’ae sai ku tsaya kuji ra’ayin shi ko? Idan ya ce yana son zuwa can ɗin,” Tana rufe baki Alhaji musa yace”ai ba shawara nake nema dashi ba, Umarni ne” Cikin isa Ya furta hakan, Kafin ya kalli dr shureim, ka shirya komai naka idan muka tashi tafiya atare zamu tafi” Lamarin ya ɗaure mata kai, shi dai Dr shureim yai shiru bai tanka masu ba, Girgiza kai Hajiya layla tayi’bazai yiwuwa ba, haba dan Allah duka yaushe muka samu shureim ɗin ya dawo wurin mu, Sannan kuma yanzu kace zaka tafi dashi? Aɗan bari ya huta mana, Shi kaɗai fa nake gani inji daɗi,” rai a6ace take magana, Sun natsu suna sauraronta, sai da takai ƙarshen Aya tukunna Alhaji ubaid yace da ita”meye na tada jijiyoyin wuya? Guduwa zai yi dashi ne? Bafa raba ki zaiyi dashi ba, Yana so ya zauna gidan shi na ɗan wani lokaci,” fuskar Alhaji musa aɗaure yace”idan na ga dama zaici gaba da zama awurina ne kuma ke baki isa ki hana shi ba” murmushin fuskar Alhaji ubaid bai washe ba yace”ba girmanku bane ku tsaya kuna sa’insa akan Shureim sai kace wani ƙaramin yaro, ko da ya ke laifin ka ne shureim tuntuni nake baka shawarar kayi aure ka ƙi yi, da ace kana da Iyali babu wanda ya isa yai iko da kai” da zolaya yayi maganar, Shureim dai ya natsu yana jinsu, Ya jima yana jin takaici yadda rayuwa ta canza mashi, Ya koma tamkar ƙaramin yaro a idon kowa, saboda raunin zuciyarshi. daƙyar Alhaji ubaid ya samu Ya maida sa’in sar tasu Wasa, dama can basu jituwa tsakanin Layla da ƙanin shi tunfil azal. “Yakamata mu tashi muje muci abinci, zainab ta shirya mana a dining” layla ce tayi maganar, Ɗaya bayan ɗaya suka miƙe tare da nufar Dining room. *Kaɗan daga Cikin Na sati mai zuwa idan Allah ya kaimu da rai da lafiya* *Evil forest* Sautin Ƙarar Danƙararen Helicopter mai saukar angulu Ƙirar UH-60 Black Hawk mallakin Sojin Ƙasar america ne Ya karaɗe ko’ina Na Cikin Dajin Evil forest Hatta rassan bishiyoyin da ke a cikin dajin girgiza suke yi saboda ƙarfin iskar fankar Jirgin, Shawagi jirgin yake yi a saman Iska Yana kewaye ko’ina na tsawon mintuna talatin, Yayin da Hot soldiers din dake a tsaye saman jirgin cikin shigarsu Ta ka ki sun ɗaura ɗamarar Yaki, Sai dai ga dukkan alamu Sun kammala gudanar da abunda Ya kawo su Cikin Dajin, Ɗaya daga Cikin sojojin dake a tsaye bakin ƙofar helicopter ɗin Hannun shi ruƙe da tactic phone Wayar da sojoji suke yin amfani da ita wurin yin sadarwa ga Manyansu dake acan Headquater, Cikin Harshen turancin Yake Yin magana muryarshi na fita da amon murya saboda ƙarfin iskar Dajin “We successfully apprehended the criminal. We are now on our way back to the U.S. with the eleven children we found in the forest.” Da wani irin speed jirgin ya karya kwana ya miƙi hanyar komawa ƙasar da ya fito......, Nima kuma na ajiye alƙalamina. *Boss Bature✍️ Mu haɗu gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*KURKUKUN ƘADDARA*_ _The Prisoners E11🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* ~Middle step~ _A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._ Gaba ɗaya Haris ya fidda rai da rayuwa, tun da halittar nan ta zura ƙafafuwansa cikin wawakeken bakinta, tsabar tsoro da firgici sun hana shi motsawa jini duk ya wanke bakinsa har saman rigar sa, jikinsa yai wani irin mahaukacin zafi na fitar hayyaci, Bawan Allah sai sambatu ya ke yi yana ambaton Sunan Danish dana sauran ƴan uwan su don su kawo mashi agaji. Ba zato ba tsammani ya ji Sautin dirar wani abu daram! tamkar zai fasa kunnansa, tsabar firgitar da yai ne yasa nan take ya sume saman koraren ciyayin. Wani Gabjejen Bature ne A tsaye cika shigar Kaya na tatattun Ƴan ta’adda babu ɗigon Imani akan fuskarsa, Hannunsa ɗaya ya ruƙe da Bindigar da yai amfani da ita wurin harbin Halittar da ta nannaɗe Jikin Haris, yayin da ɗayan hannun ya ke ruƙe da cigarette. Hankalin shi a kwance ya ke zuƙar Tabar Cikin ƙwarewa Har ta hanci Hayaƙin Ya ke fita, kwarkwararrun idanuwanshi na akan Haris dake kwance Ya sume, Tuntsirewa Baturen Ya yi da dariya hada ɗan girgiza kanshi, da ƙarƙarfan muryar sa ta Mashaya giya cikin harshen turanci ya ke faɗin “wani irin ganganci ne ya kawo ka ƙurmin daji da ƙananun shekarun ka, ba ka da hankali ne? Matashi da kai kake son ƙare rayuwarka abanza? Ina iyayen ka su ke”? kamar zautacce Shi kaɗai ya ke yin maganar shi, sam bai fahimci Yaron Ya sume ba, Sai da Ya gama Magana kafin ya matsa inda Haris yake a kwance, Ya zuƙunna Bayan Ya soke pistol ɗin a qugunsa, Ya sanya hannayensa Biyu Da ƙarfi Yake jan jikin halittar, Har sai da yai nasarar zaro ƙafafuwan Haris daga bakinta, Allah yaso ba ta kai ga Gatsa haƙoranta akan legs ɗinsa ba, da ko ta yi mashi babbar illa, Bayan Ya zame jikin Halittar da karfi Ya jefar da ita gefe ɗaya, yunƙurawa yai ya miƙe tsaye yana kakka6e tafin Hannayensa, Zuƙar Tabar sa Ya ƙara Yi”Bani da zuciyar Imanin da zan Iya taimakon ka, ka gode wa Allah da na raba ka da dabbar nan, da ko yau Ka rasa ƙafar zuwa gidan Iyayen ka” Yana magana yana sakin dariya idanuwansa akan fuskar Haris. Sautin kururuwar neman a gajin da ya Ji ce Tasa shi Kan ga kunnansa ga iska Don Ya ji da kyau, Muryar Naufal ce Ya ke faman Fasa Ihu, Da gudu Baturen Ya kutsa Cikin Dajin Yana Tunkarar inda sautin Ƙarar ke fitowa, ta wutsiyar idon shi ya hango gifcin mutune sanye da Jajayen kaya, Ta tsakantsakin jibga jibgan Bishiyoyin dake a kewaye da wurin da yake, Cikin Zafin Nama Ya daka uban tsalle ta tsakiyar wasu bishiyoyi, Kamar an jeho shi Ya faɗo Tsakar wurin da Su Naufal su ke, Gaba ɗaya sun fita hayyacin su, Halittun sun kewaye su sai gurnani su ke yi, Naufal da javed sun ƙanƙame Juna, Kuka hada majina fuskokin su jaga jaga da hawaye, wandunansu a jiƙe sharkaf da ruwan fitsarin da suka saki, Ɗan iskan murmushi dangerous terrorist Ya saki kafin Ya zaro bingidar da ke soke a qugunshi, Ya saita Jikin Halittun ɗaya bayan ɗaya yake sakar masu alburushi, duk wadda ya harba nan take Tsakiyar Cikinta yake tarwatsewa Ƴan hanji su fito waje, Sautin harbin bindigar da basu ta6a ji bane Yasa su rikicewa Kusan atare suke yanke jiki saman koraren Ciyayin suka faɗa a sume, Tuntsirewa Baturen yai da dariyar shaƙiyanci Yana faɗin “Yaran nan kuna da ban dariya, Sai ka ce ba maza ba? Kun iya shiga daji amma ba ku Iya faɗa ba? Zaman gida da sanya buje zaifi da cewa da ku, In yaso kun cigaba da taya iyayen ku shiga kitchen yin girki” acikin harshen turanci ya ke yin maganar. Gabanshi Ne yai mugun faɗuwa Jin ƙarar Jirgi A cikin kunnuwansa, Da sauri Ya kai idanuwansa saitin rassan bishiyoyin da suka lullu6e sararin samaniya, nan ta ke yanayin fuskar shi Ya canza daga annuri zuwa tsantsar baƙin ciki, fargaba da tashin hankali, Juyawa yai da gudun gaske tamkar zai tashi sama Haka ya dinga buga uban tsalle Yana gudun Ceton, ga dukkan alamu bai da gaskiya shiyasa ya ƙe ƙoƙarin gujewa waɗanda suka kawo mashi Hari, tuni Ya jima da jefar da tabar hannun sa, kwata kwata Baya a cikin Hayyacinsa, shi kansa baisan in da ya ke wurga ƙafafuwanshi ba, saboda tabar firgicin da ya shiga, ko ma su wanene su ka biyo shi sun shammace shi bai yi tsammanin za’a gano inda ya 6uya ba. Sautin Ƙarar danƙareran Helicopter mai saukar angulu Ƙirar UH-60 Black Hawk mallakin Sojin Ƙasar amurka ne Ya karaɗe ko’ina Na Cikin Dajin Evil forest Hatta rassan bishiyoyin da ke a cikin dajin girgiza su ke yi saboda ƙarfin iskar fankar Jirgin, har wani jijjiga ya ke yi tamkar zai fasa dodon kunnan mutun, Shawagi ya ke yi a saman Iska Yana kewaye ko’ina. Hot soldiers din da ke a tsaye baƙin ƙofar jirgin zafafan gaske fusatattun sojoji masu ji da ƙarfi, cikin shigarsu Ta ka ki sun ɗaura ɗamarar Ya ki, Ɗaya daga cikin su Hannayen sa biyu Na ruƙe da Telescope abun hangen nesa, Ya kanga shi saitin idanuwansa, Sojan da ke a gefen shi Yana Ruƙe da Tactical phone wayar da sojoji ke Yin amfani da ita wurin yin sadarwa da Manyansu dake acan headquater, Cikin Harshen turanci Ya ke Sanar da su cewa Sun ƙaraso Dajin ayanzu hake suna kewaye shi domin gano Location ɗin da ɗan Ta’addan Ya 6uya a dajin. Me ruƙe da abun Hangen nesan ne Ya soma magana Yana ɗaga murya ya ke faɗin A samu wuri a sauke Jirgin Yana zargin me laifin Yana a yankin da su ke, Jin maganar Shi Yasa sojojin dake sarrafa Jirgin su ka Soma ƙoƙarin Samun wurin Da zasu Sauka, A hankali helicopter ɗin Ya ke yin ƙasa tunkafin ya ƙarasa direwa, Sojojin suka soma diddirowa ƙasa Sautin Army boots ɗin dake a kafarsu Yana bugun ƙasa kamar zasu dare ta, Hannayensu ruƙe da Jibga jibgan bindigu, Haka zalika qugunansu na soke da pistols ƙananun bindugu, Sun rufe kawunansu da helmet (hular kwano) Hatta faces ɗin su ba ka Iya gani, Iya idanuwansu ne kaɗai a bayyane, Kusan su shidda ne su ka sauko daga jirgin, Da hannu Commender ɗin su ya rarraba su zuwa gida Uku, kafin ya basu Umarnin shiga Dajin, Da gudun gaske Su ka faɗa cikin zafin nama su ke kurɗaɗawa Cikin ƙurmin Dajin, Babu tsoro ko fargaba suna da ƙwarin gwiwa akan aikin su da ƙwarewar su, kuma suna da tabbacin za su yi nasarar Yin aikin da aka turo su, saboda duhun dajin Da fitilu masu haske su ke yin amfani wurin haska gabansu. Gaba ɗaya sun Yi matuƙar galabaita, tun suna tiƙar gudu Hancin Angel Ya soma bleeding zufa duk ta wanke fuskokinsu da jikinsu, Maƙoshinsu ya bushe ƙamas sai azabar raɗaɗi da ƙaiƙayin da ya ke yi masu ƙafafuwan su Zogin azaba su ke yi masu, Sun rasa ina zasu tsoma ransu su ji daɗi, Suna a tsaka mai wuya tsakanin mutuwa da rayuwa, Kurar dake a biye dasu Tana gab da zata cimmasu, Wani irin uban tsalla ta daka tana Gurnani Ta takaiwa Ƙafar Angel Cafka da haƙoranta, wata irin gigitacciyar ƙara ta fasa ita da Gabriel a matuƙar razane. Kurar na ƙoƙarin Gutsire ƙafar Ba zato ba tsammani, Sautin dirar bullet Ya ratsa kunnuwan su, Basu san daga Ina aka harbo bullet ɗin ba, Gaba ɗaya ya tarwatse Kan kurar, Nan take ta saki ƙafar Angel Ta faɗi ƙasa tana birgima, wata irin nauyayyar ajiyar zuciya Gabriel Ya sauke Yayin da zufa ke cigaba da wanke fuskarshi, angel kuwa Tsabar firgice ne Yasa ta yanke Jiki Ta faɗi ƙasa a sume tamkar matatta. Hankalin Gabriel Ba ƙaramin tashi yai ba, Ganin yadda Angel ta zube, Cikin shessheƙar kuka ta wanda ya gama galabaita muryarsa na kakarwa ya furta sunan ta da ƙarfin”Angel! no!No! Don’t die Angel, Na shiga Uku, Pls Angel ki tashi Ina zansa rai na!” Fuskarsa sharkaf da hawaye yake yin maganar, Zuciyar shi a karye Ya zube saman gwiwowinsa agaban Angel, Ya dinga kuka yana jijjiga jikinta Da hannayenshi, Sam baya acikin hayyacin sa, shiyasa ma bai yi tunanin Su wanene suka kashe Kurar ba, duk a tunanin shi Angel ta mutu ne, duk yabi ya zauce ya rasa madafa. Jin Takun Tafiyar Mutanan da ke tunkaro shi ne yasa shi saurin wurga eye balls ɗinsa da suka kaɗa jawur Yana duban su, Sojoji ne Su biyu Hannayen su Ruƙe da Bindugu, duk da baya acikin hayyacinsa saida Ya zabura yana neman guduwa a zaton shi Gianta ne na gidan kurkukun ƙaddara. Kakkausar Muryar Sojan ce ta ratsa kunnuwanshi”Don’t Move or else i will shoot ur head wit My gun” Wannan maganar da ya yi ce tasa Gabriel dakatawa da yin tafiyar ba tare da ya juyo ya kalle su ba, ya soma magana cikin rawar murya “Just kill me so that I can finally rest, Na rasa ƴan uwana, bani da burin cigaba da yin rayuwa a duniyar nan, ku kashe ni kawai idan ba haka ba ni zan kashe kai na” Yana magana zufa na tsastsafowa ta jikin fatar shi. Muryar Sojan ce ta kara ratsa kunnanshi cikin harshen turanci yace “ba zamu kashe ka ba, rayuwarka tana da mahimmanci a wurin mu, Aikin mu shi ne mu shiga tsakanin ku da mugun da ya yi garkuwa da ku Ya kawo ku cikin Dajin nan, Idan ka bamu haɗin kai zamu mai da ku ƙasar ku” tun da Sojan Ya soma Yi mashi magana Cikin kwantar da murya, sai ya ji natsuwarshi ta fara daidaita, kuma ya fahimci ba jami’an kurkukun ƙaddara ba ne. Da sauri Gabriel Ya waiwayo baya yana dubansu, a jere suke tsaye su biyu, Yawu ya haɗiya Muryarshi still adabarbarce ya furta”idan har dagaske kuna son taimakona, akwai ƴan uwana da suke a cikin dajin, muna acikin mayuwacin hali, wasu mugayen halittune suka biyo mu, ina tsoron su kashe min su” Jin wannan Maganar Yasa ɗaya daga cikin sojojin ya tasa ƙeyar gabriel Gaba, Zuwa Cikin dajin. Yayin da ɗayan Sojan da su ka bari a tsaye gaban Angel ya soma magana ta hanyar yin amfani da tactical phone ɗin hannun shi, Ya sanar da commender game da yaran da suka tsinta a dajin, suna zargin ɗan ta’addan ƙasarsu ne ya gudo dasu cikin dajin yai garkuwa da su don ya kare kanshi daga farmakin da zasu kawo mashi. Commender ɗin ya ba da Umarnin A tattaro yaran dukansu, a lokacin har sunyi nasarar Cafke ɗan ta’ addan da su ka zo kamawa, Mugun ɗauri suka yi mashi duka jikinshi suka nannaɗe da igiya suka ɗaure shi tamau bayan sun yi mashi allurar kashe ƙwarin Jiki gudun kada ya kubce masu saboda sanin shi da su ka yi, mugun ɗan ta’adda ne mai hatsarin gaske, A cikin jirgin suka wurga shi. A saman Kafaɗa Sojan Ya ɗaura Angel Ya nufi wurin da suka sauke helicopter ɗinsu, A ciki ya shigar da ita ya kwantar, Bada jimawa ba, sai ga wasu sojojin su biyu ɗauke da Nufal da Javed saman kafaɗin su. bayan sun shigar dasu Cikin jirgin sai ga kira daga Ɗayan Sojan daya tafi da Gabriel gaba ɗaya suna jin muryarshi ta cikin wayarsu, sanar da su yai akwai sauran yaran da zasu nemo acikin Dajin, Yana buƙatar a turo Wasu sojojin da zasu ɗauke su, Umarni commender yaba sauran sojojin da suka dawo akan su je su zaƙulo sauran yaran, Da gudu suka kutsa cikin Dajin. Gabriel da sojan da ya taso ƙeyar sa suna cikin Tafiya sai faman wurwuga ido gabriel yake yi a ƙoƙarin shi na ya gano inda su Batul su ke, Gabanshi sai faɗuwa ya ke yi tsoron sa kada ace halittar nan ta hanɗame su, Har zasu gifta kwatsam ta wutsiyar ido Soja Ya hango launin jajayen kaya ƙuɗundune cikin koraren ciyayi da sauri ya furta”wait” hakan yasa Gabriel dakatawa da yin tafiyar, Reverse sojan yai tare da juyar da kanshi Ya wurga ƙwayar idanuwanshi saitin wurin da ya hango jan uniform ɗin, Gabriel na yin tozali da su da ƙarfi ya furta sunan Azeeza, da gudu ya nufi wurin da suke maƙale da juna babu numfashi, Sojan na ganin Ya tunkari wurin shima yabi bayanshi, agabansu Gabriel ya zube saman gwiwonsa Yana Ambaton sunayen su cikin karyayyiyar murya ta wanda ya Sare, kafin sojan Ya motsa Sai ga sauran Sojojin da commender ya turo sun kutsa ta wurin da suke. suna ƙarasowa ba tare da 6ata lokaci ba suka ciccire ƙayoyin da suka sargafe ƙafafuwan Azeeza da jemimah, Kafin su ka ɗauke su saman kafaɗunsu, da hanzari suka juya dasu zuwa cikin jirgin. Bayan tafiyar su Sojan Ya ce da Gabriel Za su Iya tafiya yanzu? Da sauri ya girzgiza kai, cikin disasshiyar murya ya faɗa mashi”Akwai sauran mutun uku da babu acikin su” Sojan Yace ya tashi su shiga neman su, Ba su buƙatar 6ata lokaci, Akwai Iya adadin da aka basu, Idan har ya cika zasu tafi ne” jin haka yasa Gabriel Miƙewa shi kansa ba ƙoshin lafiya ne dashi ba, ƙarfin haline kawai. A ƙalla sun shafe tsawin mintuna goma shabiyar suna neman Su Batul, Sai kurɗaɗawa suke Yi cikin dajin babu su babu alamarsu, ganin zasu 6ata lokaci yasa sojan ce mashi”Su tafi kawai, Zai iya yiwuwa sun rasa rayukansu ne” kamar ƙaramin yaro haka Gabriel ya fashe mashi da kuka tare da zubewa saman gwiwowinsa Ya ruƙe ƙafafuwan Sojan Ya dinga kuka Yana roƙonshi akan kada su tafi su bar ƴan uwan shi a dajin, Shi yana ji aranshi suna araye wata’ƙil sun faɗa wani wurin ne sakamakon muggan halittun da suka tsoratar dasu,’ Tsawa Sojan Ya daka mashi a harzuƙe Ya hambare Gabriel da ya ruƙe mashi ƙafa. Muryarshi a kausashe yace “Get up and let’s go. Otherwise, we’ll leave you here in the forest.” Hawaye na bin kuncin Gabriel, Ya girgiza mashi kai yana faɗin”bazan Iya tafiya nabar su ba, Atare muka sha wahala, bai kamata mu tsira mu ƙyale su ba, ni banga gawarwakinsu ba, Tayaya zan yadda sun mutu,” numfashi yaja kafin ya ɗaura da cewa”Zaku iya tafiya da waɗanda kuka ɗauka, Ni ku barni anan zanje na nemo ƴan uwana ko da ace zan rasa raina ne” Juyawa Sojan Yai a fusace Ya soma tafiya, Sai da yai nisa zuciyarshi ta soma tariyo masa kalaman Gabriel, Dakatawa ya ɗanyi yana wani tunani, ga dukkan alamu kalaman sun ta6a zuciyarshi, A hankali ya ɗan waigo Baya yana dubanshi, Bawan Allah Ya kifa kansa saman ciyayi, Sai kuka yake yi kamar ranshi zai fita, takaicine ya ishe shi ga samu ga rashi, Yasan muddin sojojin suka tafi shida barin dajin har bada, a ƙarshe ma ya rasa ranshi, sai dai baya jin zai Iya binsu alhalin sauran ƴan uwanshi da suka sha wahala suna acikin dajin! ya zasuji idan suka dawo hayyacinsu suka taras babu su? Me zai biyo baya? A lokacin da Gabriel baiyi tsammani ba, muryar Sojan Ta ratsa kunnanshi “Yaro ka ci albarkacin sarƙar cross ɗin da ke a wuyan ka, A karo na biyu zan Taimake ka, mu gano sauran Ƴan uwan naka” wani irin farin Cikine ya lullu6e Gabriel Jiki na rawa ya yunƙura Ya miƙe, kafin su fara tafiya sai ga sauran Sojojin da su ka je kai su Azeeza hada ƙarin wasu kusan su shidda suka nufi Dajin neman sauran Yaran, Marece ya nutsa abun da sojojin suke gudu dare ya yi masu a dajin saboda Sanin hatsarin dake gare shi, Daƙyar Gabriel Ya samu Ya gano masu hanyar wurin da suka yi shimfiɗarsu, da gudu Ya nufi Danish da ke a kwance yana sharar baccin shi. Tun kafin sojojin su ƙarasa Gabansu yai wani irin faɗuwa saboda razanar da su ka yi da ganin shi, Wani abu ya ɗaure masu kai, har saida su ka kalli junansu da alamun ruɗu akan fuskokin su, Ba Iya kyawun Fuskar Danish bane Ya girgiza su, Zazzafar surar Jikinshi Ta yi matuƙar rikitar dasu, Kaf a cikinsu babu mai kalar ƙirar ƙarfin shi, Hakan ba ƙaramin kokwanto Ya saka masu ba acikin zuciyoyin su, har sun fara kokwanton Anya kuwa ɗan ta’addan da suka Biyo ne yai garkuwa da yaran? Ta ya ya za’ai ɗan ta’addan Ya iya sato wannan jibgegen ƙaton mai ƙirar sadaukan Yaƙi, a ganin su ko shi ɗan ta’addan bai kama ƙafar Matashin yaron ba wurin zubin halittarshi. Muryar Gabriel da sassarfa yake Ambaton sunan danish Hannayenshi duka biyu akan jikinsa sai jijjigashi yake yi yana faɗin”Danish ka tashi, mun samu taimako za’a fidda mu daga cikin daji, Har ma an tafi dasu Angel, pls ka tashi, Bana so mu tafi mu bar ka” Ko motsi Danish bai yi ba, ganin haka yasa shi juyawa yana kallon Sojojin, Sun ƙame a tsaye suna kallon Abun al’ajabi kusan suman tsaye sukayi yayin da suke kallon Danish “Dan Allah ku taimake ni, ɗan uwanmu ne, haka Allah ya halicce idan Yana yin bacci yakan ɗauki tsawon awanni bai farka ba,” a ruɗe yake kora masu bayani, duk don ya samu su tafi da Danish kada suce zasu barshi anan, don ya fahinci tashin shi ba yanzu ba Daƙyar ɗaya daga cikin sojojin ya iya shanye mamakin shi ya sarrafa kanshi wurin furta” bai da lafiya ne? Ko ya suma ne”? “A’a, bacci ya ke yi, kuma ba zai Iya farkawa yanzu ba, ....”tun kan ya ƙarasa maganar ɗaya daga cikin soldiers ɗin Ya zaro penlight ya zuƙunna agaban shimfidarsa, da yatsun hannayensa yai amfani wurin gwale idanuwan Danish ya haskasu ya tabbatar da yana araye ga numfahi na fita a tsanake, Kallon sauran sojoji yai”he’s alive” jin haka yasa suka gasgata maganar Gabriel, mutun Biyu suka ranƙwafa tare da ɗaura hannayensu da nufin su cuccu6i Danish sai dai wani abun ɗaure kai ko motsi baiyi ba, saboda tsabar nauyin sa duk irin ƙarfin da Allah ya yi ma sojojin na halitta da kuma na horon aikin da suka samu baisa sun Iya cuccu6ar Danish ba, A ƙarshe suka Yanke shawarar zuwa ɗauko stretcher domin ɗaukar shi, zaifi Yi masu sauƙi, abun ɗaukar Majinyatane da ake amfani dashi, Yana da maruƙi a jikin sa, saman shi faɗine dashi kamar allo, bayan sun ɗauko stretcher ɗin Saida suka haɗa ƙarfi su huɗu tukunna su ka iya cuccu6ar Danish tare da ɗaura shi saman abun ɗaukar, su ka ɗaga shi har zuwa Bakin helicopter din kafin suka samu damar shigar dashi ciki, Bayan sun tafi da danish Ɗaya daga Cikin Sojoji biyu da suka rage Ya ɗauki Back pack ɗinsu da ya gani a jikin bishiya, don suna buƙatar duk wasu shaidu da za su zamar masu hujja. da hannu ɗaya ya ruƙo jakar ɗayan hannun kuma ya ruƙe hannun akwatin kayansu Yaja shi zuwa Bakin jirgin. A can Cikin Dajin Gabriel ne Ya rage tare da Sojan nan, Suka kuma kutsawa cikin dajin Don ya sanar mashi akwai sauran Ƴan uwanshi, Abun dai ya ɗaurewa Sojan kai, Su fa duk a tsammaninsu ɗan ta’addanne ya yi garkuwa da su daga ƙasar su america Ya shigo da su Dajin, Saboda Yaran sunyi kama da mutanan ƙasarsu, Hasken fatarsu da Doguwar sumar kawunansu, a hasashensu kenan, sai dai duk da haka sun ɗanyi mamakin wasu abubuwa da suka sanyasu yin al’ajabi, tayaya har ɗan ta’addan ya iya guduwa dasu bayan ƙasarsu tana da mugun tsaron da babu wani shege da ya isa Ya ƙetare ta cikin Salama, Abu na biyu Ta ya ya Ɗan ta’addan Ya iya ɗaukar mutun mai mugun Nauyi irin matashin saurayin da suka gaza ɗagawa? Abu na uku da ya ɗaure masu kai Uniform ɗin Jikin yaran masu ɗauke da numbobi sunyi mamakin hakan. Suna Cikin yin tafiya, Zuciyar Gabriel na dakan uku uku tamkar zata faso kirjinshi ga kishirwa da ya ke ji, babban tashin hankalin shi Ina Su Batul suka kutsane a cikin Dajin? Ga dare yana shirin yi masu adajin, fargabansa kada sojojin su ce zasu tafi. “Kana tunanin ƴan uwanka zamu same su? Lokaci Yana ƙure mana” Sojan ne yai mashi maganar, gabriel bai samu damar amsa mashi ba saboda tashin hankalin da ya ke aciki, Sai faman wurwurga ƙwayar idanuwansa ya ke yi akan bishiyoyin dake a kewaye dasu, Suna Cikin yin tafiya suka ƙaraso gaban wannan ramin mai ɗauke da ta6o, har zasu gifta shi Kwatsam Sojan Yaji ya taka wani abu, Da sauri Ya ɗage ƙafarshi yana kallon Warin Slipper ɗin dake asaman ciyayin, Gabriel na ganin takalmin Ya zuƙunna tare da kai hannu ya ɗauke shi, Gabansa ne ya faɗi A gigice ya kalli sojan tare da furta”Takalman Ƴar uwata ne!” Ya gane slippers ɗinsu ne Da tsohuwa Tamira tai masu kyautarsu, dama tunda suka shigo Dajin da takalmansu suke yawo a ƙafafuwansu, shiyasa ko ƙaya ba ta ta6a shigarsu ba. “Dan Allah ka taimaka mun, wlh takalmansu Batul ne ƴan uwana” Muryarshi na rawa yake maganar, cikin ƙagara. Waige-waige Sojan ya ke yi yana bin ko’ina Na dajin da kallo, Kafin ya sauke idonshi akan Ramin ta6on, kasancewar Sojoji suna da ƙwarewa wurin sanin takan Daji, Nan take ranshi ya bashi cewar Ta6on da ke a wurin Ramine, mutun zai Iya rubzawa cikinsa, musamman wanda ke gudu cikin fitar hayyaci. Matsawa yai gaban ramin, Bayan ya soke bingidar hannun shi a ƙugun shi, Ya ɗan zuƙunna saman ƙafarshi, a tsanake Ya tura hannun shi Cikin ramin ta6o, Cikin sa’a Ya damƙo gashin ɗaya daga Cikin su, matsar da hannun shi yai ya ruƙo Hannunta, Ya ɗago da ita gaba ɗaya jikinta ya 6aci kaca kaca da ta6on baka Iya ganin komai na fuskarta, hatta Gabriel bai gane wacece a cikin su ba, A ƙasa sojan ya kwantar da ita tare da ƙara zura hannun shi Ya ƙara cafko hannun wata ya curo ta, bayan ya kammala zaraso duka ukun Gabriel Yace mashi suke nan babu saura, Jin haka yasa Sojan Zaro wayarshi Ya sanar ma sojojin dake a bakin helicopter din cewa sun ƙara samu Yara Uku azo da stretcher a ɗauke su, Cikin ƙanƙanin Lokaci sai ga sojoji sunzo da abun ɗaukar, duka ukun suka ɗaurasu saman shi kamar tsummokarai haka suka nannaɗe. Sojoji biyu ne suka tafi dasu zuwa Inda jirgin ya ke, Hankalin Gabriel Ya ɗan kwanta sam ya manta da Haris saida suka kamo Hanya zasu Nufi jirgin ba zato ba tsammani su ka ci karo da haris a sume, Ba tare da 6ata lokaci ba, Sojan da suke atare Ya sa6e shi saman kafaɗa, suka nufi Jirgin Bayan sun Shiga su dukansu. Matuƙar jirgin suka Tada shi, Da wata irin jijjiga tayoyin jirgin su ka soma motsawa suna yin tafiya sannu a hankali, Gabriel da ya kasance shi kaɗai idon shi biyu, farin Ciki duk ya cika shi, sam baiyi tunanin wace ƙasa za’a kaisu ba, hankalin shi bai kai nan ba, fatan shi su bar dajin Cikin ƙoshin lafiya. Bayan tashin jirgin sama Ɗaya daga Cikin sojojin dake a tsaye bakin ƙofar helicopter ɗin ne Ya kanga Tactical phone ɗin hannunsa jikin kunnansa Yana magana Cikin Harshen turancin muryarshi na fita da amon murya saboda ƙarfin iskar Dajin “We successfully apprehended the criminal. We are now on our way back to the U.S. with the eleven children we found in the forest.” (Munyi nasarar cafke mai laifin, yanzu muna akan hanyar mu ta dawowa U.s, tare da yara goma sha ɗaya da mu ka samu a dajin) Da wani irin speed jirgin ya karya kwana ya miƙi hanyar komawa ƙasar da ya fito. *Alhamdulillah Finally Ex-prisoners sun Bar Evil forest Fatan Nasara* _~*BossLadiesWriters*~_ _*KURKUKUN ƘADDARA*_ _The Prisoners E12🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* ~Middle step~ _A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._ *GIDAN ƊAN IYA* Gaba ɗayan su sun Hallara a bakin Entry hall na shiga palourn gidan, Mommy da Mami sun yi matuƙar yin kyau cikin shigar Lace, Zahra da Aneelerh sai Abie da Uncle ɗan Iya sun yi shiga ta alfarma, Bakomai ne yasa su fitowa ba fa ce tarbar Su Hajiya adama, A ƙagare su ke da ganin baƙin nasu, badajimawa ba su ka kira Aneelerh awaya su ka sanar da ita cewa sun shigo garin abuja, har ta tura masu da addrress ɗin gidan. Ƙarar Horn ɗin motarsu ne Yasa kowan nan su Sakin fuskarshi, da sauri mai gadi Ya fito daga ɗan ɗakin sa, Ya je ya buɗe masu gate. A hankali Danƙareriyar Motar uncle abdallah ƙirar Kia optima ta kunna kai cikin gidan kai tsaye ya nufi wurin Ajiye motocin su, bayan yai parking ɗin motar, Ya fito daga ciki fuskar nan ɗauke da annuri, ya ɗauki wankan shadda gezna, ƙafafuwanshi na asanye da patent leather shoes launin Shaddar shi, ƙamshi ta ko’ina. Zagayawa yai ta other side ɗin motar ya buɗe ma Hajiya adama ƙofa, ƙafar ta ta fara zurowa nan take Zahra ta ɗan zaro ido tare da kallon Aneelerh, murmushi gefen fuska Aneelerh ta sakar mata don ta fahimci abunda ya sa zahra mamaki, wato tsadar High hills ɗin dake ƙafar Hajiya adama. Zahra ta ƙware wurin sanin farashin Kaya, A kunne ta yi ma Aneelerh whispering “Surukar ki Ta ji naira yasin, Takalman ƙafarta kalar na saratu obinna ne” girgiza kai Aneelerh ta yi ba tare data tanka mata ba. Lokacin da Hajiya Adama ta ƙara sa fitowa daga Cikin Motar ba ƙaramin tafiya ta yi da imaninsu ba, saboda tsabar wankan kece rainin da ta ɗauka na tsadadaddan Swiss cord lace launin brown mixed wit yellow, Riga da zani ne ta daura, kanta yasha ɗaurin ɗan kwali, sarƙar wuyanta da awarwaron hannun ta, da zabbanta duk na zinari ne, ta yarfa mayafin kayan saman kafaɗarta, babu make up a saman fuskarta zallar kyan da Allah ya yi mata ne, Hajiya adama akwai kyau ga diri. Kallon abdallah ta yi fuskarta ɗauke da murmushi, da hannu yai mata nuni da surukansu da ke a tsaye suna fuskantar su “mu je ko?” Sai lokacin ta lura da su, tafiya suka soma Yi a jere tunkan su ƙaraso Zahra take ta faman ingiza kafaɗar aneelerh “ki je ki tarbo su,” kunya ta hana Aneelerh zuwa, har saida suka ƙaraso, Abie Yana dariya Ya ruƙe hannun Abdalla suka fara yin gaisuwarsu ta manya”Marhaban marhaban lale surukai na gari, Sassannun ku, kun sha hanya, ku ƙaraso ciki” Ya ja hannun abdallah, Mamie da hajiya adama suka rungume juna fuskar kowan nan su ɗauke da murmushi, bayan sun raba jikinsu, Ummi ta miƙe mata hannu suka gaisa a mutunce”Sannu da zuwa Hajiya, mu shiga daga Ciki” ta yi maganar, tare da jan hannun hajiya adama wadda idonta ke akan Aneelerh, sai faman noƙe kai ta ke yi, “Kunya kamar bafullatana, Ni kaina da nake bafullatana Bani da kalar kunyarki,” da zolaya hajiya adama ta yi maganar, Yayin da su ke shiga cikin babban falourn gidan, daddaɗan ƙamshin turarensu ya gauraya da sanyin A.c. A saman soma mai mazaunin mutum uku Mami da ummi da hajiya adama su ka zauna, Abie da Uncle ɗan iya su ka zazzauna saman 2 sita, Aneelerh tana zaune saman one sita, Yayin da zahra ta ɗan zauna saman hannun sofa ɗin da Aneelerh ke zaune, sai faman sakarwa juna murmushi suke Yi, Gaisuwa ta musamman suka ƙara yiwa junan su cikin girmama juna da mutuntaka. Uncle ɗan Iya Yana faman washe baki Yace”Abdallah Kai ne ka koma haka?gaskiya mun daɗe bamu haɗu ba, tun lokacin da ka fito daga cikin mota, idanuwana su ka yi tozali da kai sai da gabana ya faɗi araina nace ina muka samu baƙin Bature, Abdallah hutu ya zauna maka daga kai har Hajiyar taka kun yada zumunci ko in ce mun yada zumunci Allah dai ya shiryemu” dariya suka saki gaba ɗayan su. Ummi tace”Ya gajiyar tafiya? Nasan Kun jigata sosai, tafiya daga jos zuwa abuja ba abune mai sauƙi ba, kun ma yi ƙoƙari dana ganku da kuzarin ku” mami ta ɗaura da cewa”Alhamdulillah mun gode ma Allah da ya kare mana ku ya tsare mana ku har ku ka ƙaraso Lafiya, wannan abun farin ciki ne agare mu, gamu ga surukanmu, mutane masu ƙima da daraja, muna ƙara yi maku barka da zuwa” Maganar Mami ta yi matuƙar faranta zuciyoyinsu. Musamman Hajiya adama har saida ta ɗan saki murmushin da ya bayyana jerarrun fararen haƙoranta. A tsanake tace “A gaskiya ba zamu Iya misalta farin Cikin da muke aciki ba, ni dama tun da muka fito daga cikin mota raina Ya bani munzo gidan mutunci da karamci musamman da naji gidan Uncle ɗan Iya ne Masha Allah, Fatan mun same ku lafiya” atare suka haɗa baki”Lafiya lou Alhamdulillah” Uncle abdallah ne ya soma yin magana cikin dattako da halin girma “Mun jin daɗin samun ku cikin ƙoshin Lafiya, Abun farin cikine wannan kuma muna godiya da irin tarbar da muka samu, Ina yi mana fatan kamar yadda muka haɗu anan, Ubangiji Allah Ya haɗamu A gidan aljanna alfarmar Annabi muhammad SAW, kusan atare suka haɗu wurin furta kalmar SAW “Yakamata mu fara yiwa annabi Salati” Abie ne yai maganar, tare suka ɗaga hannuwansu bayan sunyi salati ya ci gaba da jero masu addu’o’i Suna amsawa da ameen ameen Bayan ya kammala, Uncle ɗan Iya ya wurga idon shi kan Aneelerh da ke ta faman sakin murmushi tana noƙe kai Jin Muryarshi tasa ta ɗago da ido tana kallon shi Daƙuwa ya sakar mata”Ungo nan, jira ki ke sai mun ce ki je ki gaishe da surukan naki? yarinya sai ka ce jinin fulani” Tsuntsirewa su ka yi da dariya gaba ɗayansu, Yadda yai magana yai matuƙar basu dariya hada Aneelerh, Da sauri ta miƙe daga saman sofa ta nufi Hajiya adama daga ƙasa saman carpet ta zauna gefen ƙafar Hajiya adama, muryarta ƙasa ƙasa ta furta”Sannunku da zuwa, Ya gajiyar tafiya, ya kuma aka baro mutanan can” ɗaura hannu hajiya adama tayi saman kafaɗar Aneelerh “Lafiyalou daughter in-law Fatan na same ki Lafiya” Aneelerh ta amsa da lafiyalou, kafin ta matsa gefen uncle abdallah Ta gaishe da shi, da fara’a ya amsa mata Bayan sun gama gaisawa da aneelerh, Zahra ta gaishe dasu, suka amsa mata Kafin daga bisani, Mami tace”bismilla mu shiga ciki, Ku huta kada mu Cika ku da surutu, “ ta faɗi hakan ne don tasan yanayi na matafiya yafi buƙatar hutu, Miƙewa su ka yi Mami da Abie na agaba Hajiya adama da uncle abdallah suna abiye dasu, wuce abie yai da uncle abdallah zuwa ɗakinsa, Itama mami ta wuce nata ɗakin tare da hajiya adama bayan tafiyar su. Fira ta 6arke tsakanin Zahra da Ummi, a lokacin Uncle ɗan Iya ya fita waje domin amsa kiran da akayi mashi a waya “Wlh ummi takalman ƙafarta kalar na saratu obinna ne, kinsan ko kuɗinsu yakai dubu talatin” Ɗan zaro ido Ummi ta yi” Tab Aneelerh ashe surukan ki Attajiran masu kuɗi ne, ai naga sarƙar wuyanta da awarwaron hannunta duk na zanari ne, gaskiya kin taki sa’a, Yarinya mai ƙashin arziƙi,” kwa6a fuska Zahra ta yi”ni kuma mai ƙashin tsiya ko”? ummi na dariya tace”Ni dai bance ba, kema ina maki fatan miji na gari da surukai na gari” yatsina fuska ta yi ƙasa ƙasa da murya ta furta”Suruki na gari kamar Owais, surukai na gari hamshaƙan masu kuɗi irin hajiya sarauta” Aneelerh dake zaune saman carpet ta miƙe ta koma saman sofa ta zauna Ummi ta kalleta”nasan zasu buƙaci ganin jikansu, gashi ya tafi school till 6 na marece za’a tado su saboda lesson na Islamiya da ake Yi masu, “ zahra tace”Zan kira mahboob A waya ya je ya ɗauko shi, Ni fa dama can banso aka sanya shi hada islamiyyar ba, ace kullum sai ƙarfe shidda zai dawo gida, in banda weekend,” Harara ummi ta ɗan watsa mata”Sannu Uwarsa, islamiyarce ke ba ki so ya yi kenan sai dai na bokon” Girgiza kai zahra tayi”Ba haka nake nufi ba ummi, Yaron ya yi ƙaranta brain ɗinsa ma ƙarama ce ta ya ya ki ke tunanin zai Iya ɗauke duk abunda aka koya masa” Tun da suka fara magana aneelerh ta yi shiru tana kallonsu, acan ƙasan zuciyarta kewar baby junaid ce ta addabeta, maganar zahra tasa duk ta ji ba daɗi ita kanta ba ta son Yana kaiwa har ƙarfe shidda sai dai ba yadda za ta yi ita kanta tana so yaronta ya saba da karatun boko dana addini. Tsawon lokaci suna fira a tsakanin su jefi jefi har aka fara kiran sallah, Abie da Uncle abdallah suka fito da haramar zuwa masallaci, a harabar gidan suka yi arba da uncle ɗan Iya zaune saman Kujera Yana danna waya, Abie ya ce da shi Ya tashi su je masallaci, A nan suka jira shi ya shiga gidan ya ɗauro alwala kafin ya dawo suka ɗunguma zuwa masallacin dake a kusa da gidansu Acan Cikin Gidan kowa ya koma ɗaki domin yin sallar magrib, hankalin Aneelerh Yaƙi kwanciya, Jin shiru mahboob bai dawo mata da yaronta ba, Gashi har an kira sallah. A zaune ta ke saman darduma hannayenta Biyu sama tana jera addu’o’i tasha dogon hijabinta. Ba zato ba tsammani ta ji saukar mutun saman Bayanta, Ya ƙanƙameta Yana tiƙar dariya”babyn mommy is back” Gabanta harya faɗi sai da taji muryarshi tukunna ta sauke ajiyar zuciya, haɗi da ɗan sakin murmushi jin ya kirata da sunan da malamansu suke kiranshi wato babyn mommy, bayan ta shafa addu’ar, ta zagayo da hannunta ta ruƙo damtsen shi ta zagayo da shi tare da zaunar da shi saman laps ɗinta, Kamar kullum fuskarshi duk jirwayen hawaye, uniform ɗin jikin shi riga ce fara sai wando red colour, daga saman rigar akwai ƴar coat launin Ja, kafin ya ta fi school saida ta gyara mashi sumar kanshi amma yanzu da ta kalli sumar kan nashi A hargitse ta ke. Idanuwanshi luhu luhu ya furta”Mommy, kin ga banyi kuka ba yau ko? Ai kince in daina” smiling softly tace”jirwayen menene akan fuskarka” tai maganar tana nuna hawayen da indext finger dinta, kwa6e mata fuska yai”mommy ai ni bake nayi ma kuka ba, uncle mahboob ne da safe da zamu school, Ya cinye min chocolate ɗina da kika saka min a basket” idanuwanshi cike tab da ƙwalla yai mata maganar, ranshi ya 6aci. Ɗaure fuska aneelerh tayi”Na rasa gane me ke damun mahboob, shi bai siya maka ba sai dai ya cinye maka? Tir wlh andai ji kunya” “Mommy don’t worry, Ni ma ai na rama” “Dame ka rama” da mamaki ta yi mashi tambayar, hannu taga ya zura cikin aljihun wandonsa, ya zaro ɗan ƙaramin box mai kyan gaske Ya nuna mata “Menene wannan”? Shu’umin murmushi babyn mommy ya saki”pls mommy kada ki yi min faɗa, inaso yadda ya sani zubar da hawayena shima ya yi kuka, A motar shi na samu wannan, buɗe ki gani abun da ke a ciki” yai maganar yana miƙa mata box din, bayan ta kar6a ta buɗe akwatin, haɗaɗɗen zoben azurfa ne, na mata mai kyan gaske stone ɗin jikin shi har ƙyalƙyali Ya ke yi, Jinjina kai aneelerh tayi”Lallai Mahboob Ya iya kashe na ƴan mata kuɗi amma bai Iya kashe ma ƴan uwan shi ba, dama irinsu babu mai cin moriyarsu sai mata, kowace mai sa’ar ce wannan Ya siyama zobe kuma daga gani mai tsada ne” “Mommy daga ni sai ke, kada ki faɗa mashi ni na ɗauka, Mubar shi yai ta wahalar nema shima Ya ji idan akwai daɗi” Cikin 6acin rai ya ke yin maganar. “Babyn mommy, ai ni farin cikinka shine nawa, don haka kar6i box ɗin nan ka 6oye mana shi cikin rigar pillow,” kar6ar zoben junaid yai da gudu ya nufi gado ya haye tare da ruƙo pillow ya zuge zip ɗinshi Ya tura box ɗin, abun mugunta ya samu sai faman sakin murmushi yake yi kamar gonar auduga Miƙewa ta yi daga saman sallayar, bayan ta cire hijab din jikinta ta tura a wardrobe, Baby junaid ta ɗauka ta nufi toilet dashi, Wanka tayi mashi bayan sun fito ta ɗauko mashi riga da wando na shadda, ta zura mashi kayan ajikin shi, ta feshe ko’ina na jikin shi da turare bayan ta kammala gyara mashi sumar kansa ta ɗauke sa suka nufi Palour, kafin su ƙarasa sai da ta yi mashi huɗuba akan ya natsu ya gaishe da kakanninsa kada ya bata kunya, ya amsa mata da toh, Lokacin da suka ƙarasa palourn babu kowa duk suna a dining area sun hallara domin Cin abincin da aka shirya masu, dukkansu Ne a zazzaune saman dining chairs, zahra da Ana ke yin aikin zuba masu abinci. Farin Ciki a wurin Hajiya adama baya misaltuwa, shima Uncle abdallah sai murmushi yake saki ganin jikan nashi, Yayi matuƙar tafiya da hankulansu, tun daga kan yadda ya zuƙunna kamar wani babban mutun ya gaishe da su, Hajiya adama ta ɗauke shi Tana shafa sumar kanshi tace”Masha Allah, Yaro kamar rainon turai, Jawur dashi” atare suka ci abinci, tana ci tana bashi abaki, Junaid an samu jikin Granny, Ya ƙanƙameta yana zuba mata shagwa6a shi ala dole ga jikallen Hajiya adama da uncle abdallah. Bayan sun kammala Cin abincin, aka fara kirayen kirayen sallar isha’i, Mazan suka tashi domin zuwa masallaci. Shigowa cikin kitchen Mahboob yai fuskarshi a ɗaure babu annuri, Ana dake a tsaye bakin sink tana wanke kwanukan da aka 6ata, Jin motsin mutun yasa ta waiwayo don ganin wanene, ganin mahboob ne atsaye sai ta saki fuska tana faɗin”mahboob sannu da dawowa ashe kaine banji motsin shigowarka ba” Yamutsa fuska yai muryarsa agajiye ya furta”kin ban mamaki Ana, Yanzu hada ke aka haɗa baki wurin yin almubazzaranci? Sai ka ce gidan Obinna abinci har kala Biyar? Ina laifin ko shinkafa da wake ne adafa masu In yaso sai a yayyanka masu kayan lambu asama” ranshi a matuƙar 6ace yake yin maganar, Fuskar Ana da alamun ruɗu take kallon shi “Mahboob me kake nufi”? Hura mata hanci yai”magana nake akan almubazzarancin girka abinci da ku ka yi saboda surukan Aneelerh” dafe kai tai da hannu ɗaya “Pls mahboob ka daina magana kada wani daga Cikin su Ya faɗo kitchen ɗin ba tare da sanin mu ba, bansan meke damunka ba, menene damuwarka idan an girka masu abinci kala Biyar? Ko sisin ka babu acikin kuɗin girkin” harara ya wurga mata tamkar ƙwayar idon zata faɗo kasa, rai a6ace ya ce”Abar zancen, Zuba min abinci yunwa nake ji” girgiza kai Ana ta yi kafin ta nufi dish rack ta ɗauko plate ta zubo mashi dambun shimkafa, Ta miƙa mashi, Matsiyacan kallo yabita da shi “Shi kaɗai aka girka? da mamaki akan fuskarta tace”yanzu ka gama zazzaga min masifar almubazzaranci na girka abinci Kala Biyar, yanzu kuma ka ke tambayata shi kaɗai aka girka? Dalla ni kar6i plate if not shima zaka rasa ne” fuskarta a ɗaure ta yi mashi maganar, hakan ba ƙaramin kayar mashi da gaba yayi ba, sassauta muryarshi yai”nifa wasa nake yi maki, dan Allah ki zuba min komai da aka girka yunwa nake ji, idan na gama cin abincin akwai wata kyauta da zanyi maki” magiya ya dinga yi mata daƙyar ya samu Ana ta zuba mashi abinci kala Biyar ta ɗaura masa saman dinner table na kitchen Yana ci yana santi, Musamman da ya zo kan Farfesun ganda, duk ya bi ya susuce hada siɗar hannu kamar ɗan maroƙi. Bayan kammala sallar isha’i tun akan hanyar dawowa daga masallaci Uncle abdallah yace da abie Yana so zasu wuce idan sun koma, abie yace ba zai yiwu ba, dama ba kwana zasuyi ba? uncle ɗan Iya da ke atare da su Yace”Yaya ka ƙyale shi, sai mu ga ta ƙofar da zai fita, Dama Hajiyar shi na cikin gidan dole shima Ya shiga, Haba Abdallah yanzu ku kwaso uwargajiya sannan ka ce zaku tafi? A wani masauki zaku sauka ne da yafi namu? Uncle abdallah yace”A hotel ne zamu sauka” ya 6oye masu cewa sunyi gida a abuja, Uncle ɗan Iya na jin haka yace”ai da kuɗin hotel ɗin da zaka bayar ƙwara ka dunƙule su ka bani sai ku kwana a gidanmu dan na fahimci kuɗin ne su ka yi maka yawa” dariya suka saki gaba ɗayansu suna tafiya suna Yin fira gwanin ban sha’awa, Bayan komawarsu gidan uncle adallah da abie suka nufi ɗaki atare. Hajiya adama na akwance saman gadonta, Har ta canza kayan jikinta daga Lace zuwa Rigar bacci, da har ta yi shirin tafiya tana jiran uncle abdallah ya dawo su tafi, sai ga mami ta shigo ɗakin, ganin tana shirye shiryen tafiya yasa ta ce da ita ina zuwa tace ae zasu sauka a hotel ne, girgiza kai mami ta yi ki ma daina faɗin hakan don ba zai yiwu ba, ga gida kuma sai ku ce zaku kwana a hotel? Hajiya adama tace”bamu son mu ɗaura maku nauyi ne, mami tace”babu wani nauyi wlh, idan ma kina tunanin ko dan saboda gidan ƙaninsa ne, to ki kwantar da hankalin ki, gidansu ne su biyu, kusan ma rabi da kwata na abunda aka kashe a ginin da kuɗin abie ne, Allah ne bai nufa zamu dawo nan ɗin ba, sai daga Baya da ya samu ƙarin matsayi awurin aiki kin ji yadda akai muke zaune agidan, na faɗa maki ne don ki kwantar da hankalin ki, idan da kara ae gidan surukai gidan ƴan uwana ne tun da anzama ɗaya, Ga ɗan jikanmu junaid ya ƙara mana danƙon zumunci” maganar Mami ce tasa hajiya adama fasa shirin tafiyar, mami bata jima da fita daga ɗakin ba Kiran uncle abdallah Ya shigo wayarta, ko da ta ɗaga kiran sanar da ita yai game da fasa tafiyar su sai zuwa gobe, hankalin ta ya ƙara kwanciya, ba tare da 6ata lokaci ba ta canza kayan jikinta zuwa na bacci, tana shirin kwanciya, muryar Aneelerh daga waje ta katse ta, sallama tayi mata, hajiya adama ta amsa mata da wa’alaikum salam, Suruka ta gari shigo ciki mana’ cikin Jin kunya Aneelerh ta turo ƙofar ɗakin hannunta ɗauke da baby junaid, saukowa yai daga jikinta da gudu ya nufi hajiya adama tana dariya ta ɗauke shi kafin ta zauna gefen gadon tana shafa sumar kanshi, ganin Aneelerh na ƙoƙarin zama daga ƙasa yasa ta katse ta da cewa”ki Zaune gefe na, Muyi fira” komawa gefen gadon aneelerh tayi “Mommy barka da dare, Ya gajiyar tafiya”? Hajiya adama tace”ai Gajiya tabi jiki tun da na ga jikana” shiru suka ɗanyi kafin Hajiya adama ta ce”Ya haƙurin rashin da mu ka yi”? Duƙar da kai Aneelerh ta ɗanyi, a duk lokacin da aka yi mata maganar 6acewar su tajudden tamkar an fama mata mikin dake acikin zuciyarta ne, nan take hawaye suka cika idonta, Muryarta na ɗan uwa ta furta”Haƙuri an gode Allah, muna ta binsu da addu’a,” “Ko akwai wani abu da ku ke shiryawa ne game da 6acewarsu”? Jinjina kai Aneelerh tayi”Eh mommy, dama na jira ne sai kun huta mu yi magana.....” gaba ɗaya Aneelerh ta kwashe komai dangane da tada zancen 6acewar su Uzair ta labarta mata, annurin da ta gani akan fuskar Hajiya adama ne Ya tabbatar mata da zata samu goyon bayanta, “Kunyi tunani mai kyau surukata, Naji daɗin shawarar da zahra ta baki, Yarinyar tana da hankali, duk cikinmu babu wanda yai tunanin tada zancen, idan har akaci nasara silar shawarar da ta bada, Na yi mata alƙawarin kyauta ta musamman” Ba ƙaramin daɗi Aneelerh ta ji ba, Mommy adama ta ɗaura da cewa”In sha Allah zamuyi magana dashi abdallahn dangane da tada zancen, sannan zamu bada tamu gudummuwar, fatana Allah ya dafa mana, Ya dube mu da idon Rahma, Ya bayyanar mana da su idan suna a raye, ko da basa a raye da buƙatar muji meya faru da su”! Cikin girmamawa aneeleeh tace”In sha Allah zamuyi nasara mommy, saboda bana son in rasa surukai na gari irin ku” Sam batasan Ta furta hakan ba, Dariya Hajiya adama ta yi”Nima ai bana so na rasa suruka ta gari irin ki Aneelerh, domin kuwa zai yi wuya asamu tamkar ki,” cikin jin kunya aneelerh ta miƙe tana faɗin”Bari na kawo maki abun sha” bata jira amsarta ba, ta yi saurin Juyawa ta fuce daga ɗakin, Bayan fitarta Hajiya adama ta dubi Baby junaid dake kwance saman ƙirjinta, Ya tsareta da ido, tun da suka fara magana bai tanka masu ba, ya kasa kunne yana sauraronsu, sai yanzu ya samu damar yi mata magana “Granny kinsan Angel” jinjina mashi kai tayi”nasanta mana, Inason Angel sosai” marairaice mata fuska yai tamkar zaiyi kuka”baiwar Allah Angela ɗina, Mommy ta faɗa min da ita da daddynta da daddyna sun 6ace, ni tsorona ma kada ace 6era ne ya cinye su ba....” Zaro ido Hajiya adama tayi can kuma sai ta tuntsire da dariya “Granny, mommyna kusan kullum sai ta yi kuka saboda su angel, ƴar baiwar Allah, mami ta hanata Yin kuka amma bata Jin maganarta, sai da nayi mata faɗa, na nuna mata raina ya 6aci tukunna ta daina” sosai hajiya adama ke yin dariya, Sambatu iri iri junaid ke yi mata ba ƙaramin nishaɗi ya ke sanyata ba, “Gobe akwai school junaid, mu kwanta mu yi bacci” maƙe mata kafaɗa yai”Ina tsaraba na”? “Nayi maka amma sai gobe zan baka, nafi so ka huta yanzu muyi bacci” amsa mata yai da toh mu jira mommy ta kawo mana abun sha ko? in mun sha sai mu kwanta, Turo ƙofar ɗakin Aneelerh tayi hannunta ɗauke da cup of coffee asaman table ta ajiye mata shi, Godiya hajiya adama tayi mata, daga nan su ka yi sallama da junansu Aneelerh ta fuce, Atare da junaid suka sha coffee ɗin Bayan sun kammala, Hajiya adama Ta kwantar dashi ta tottofe shi da addu’a, sauka tai daga saman gadon ta nufi switch ta kashe hasken ɗakin, kafin ta dawo ta hau gadon ta rungume jikallanta aƙirji, ahaka bacci ya ɗauke su ****JOS CITY MUN WAYI GARI LAFIYA AGIDAN ALHAJI UBAID******* zazzaune suke a saman dining suna Yin breakfast A tsanake shiru baka jin sautin komai saina cokulansu, kwas kwakwas kamar zasu fasa plates ɗin, sun natsu suna tura abinci a cukunnansu, Alhaji ubaid na sanye da Jallabiya Hajiya Laila dake agefensa arab gown ce a jikinta launin royal blue ansha uban make up, Alhaji musa ya ɗauki wankan tsadaddun suit sun zauna mashi, mutumin fa akwai kyau kamar shi ya tsara kanshi ya iya ɗaukar wanka ga aji, daga gefen shi Dr shureim ne cikin shigarshi ta gado wato Kayan larabawa, daddaɗan ƙamshin turarensu mai daɗin shaƙa, musamman turaren Alhaji musa fragrance ɗinsa na dabanne. A hankali ya ɗan ɗago yana duban shureim ya lura ba abincin ya ke ci ba, tun da suka zauna yake ta faman jujjuya spoon ɗin hannun shi acikin plate ɗin gabanshi, gyaran muryar da Alhaji musa yai mashi ce tasa shi ɗagowa ya kalle shi Cikin kulawa ya ke yi mashi magana”meyasa bakasan cin abinci shureim? Na lura tun shekaran Jiya da nazo gidan nan baka ci wani abun kirki ba” Hajiya Laila ta ɗan dakata da cin abincin fuskarta a yamutse take kallon alhaji musa aranta tace”ji wani ikon Allah ko’ina ruwanshi da cin shi da shan shi? Ni narasa gane shisshigin nan da yake yiwa shureim, mutumin da bai damu da shi ba, sai yanzu ne yasan da zaman shi’ Cikin sanyin murya shureim ya kalli uncle ɗin nashi”ina ci mana, kawai ni nafi sha’awar abincin hausawa ne wannan baya min daɗi abaki” Alhajin ubaid yace”Meyasa tuntuni baka yiwa zainab magana ta girka maka ba? Kamar ba ka da bakin magana, komai naka ya zama na shiririta shureim so ka ke ka koma yaro”? shiru shureim yai shi kanshi haushin rashin ƙwarin gwiwarshi yake ji, ya koma kamar wani sakarai komai sai yadda akayi da shi. “Kada ka damu Yayana, da zarar mun koma abuja zai dawo asalin Dr shureim ɗin da ka sani ne, Kasan matata ta iya bada tarbiya zata gyara maka ɗanka ya zama namijin gaske” Wannan maganar ta Alhaji musa tayi matuƙar ƙona ran Hajiya layla, har dai tagaza jurewa “Me kake nufi? Ni ban iya bada tarbiya ba kome”? Ko kallo bata ishe shi ba saima Ya ɗauki glass ɗin lemu mai sanyi yakai baki Yana kur6a. “Haba layla, meyasa bakya iya 6oye fushin ki ne? Laifine don ya yabi matarshi? Harara ta wurgawa Alhaji ubaid tamkar ƙwayar idon zata faɗo kasa “bansan meyasa kake goya mashi baya ba, idonka ya rufe kwata kwata baka ganin laifin shi, wannan ba adalci bane” rai a6ace ta ƙarasa maganar tare da buga table din, A fusace ta miƙe tabar dining ɗin Miƙewa shureim yai da niyar yabi bayanta da sauri Alhaji ubaid ya dakatar dashi”dawo ka zauna” komawa yai ya zauna “daddy bana jin daɗin hakan, kasan halina tunfil azal bana so inga ran wani daga cikin ku ya 6aci” Shureim ne yai maganar “ka kwantar da hankalinka, In sha Allah zan sasanta tsakaninsu, Yanzu zan shiga wurinta in lallasheta” Yai maganar tare da miƙewa yabar dining din bayan tafiyar Ubaid Alhaji musa ya ɗago ya kalli shureim “You should start preparing, Ƙarfe shabiyu zamu bar jos, already nayi magana da pilot ɗina, bana buƙatar ka tafi da komai naka, Duk wani abu da za ka buƙata za’ayi maka acan” murmushin yaƙe dr shureim ya ɗan saki “in sha Allah Uncle yanzu zan shiga ciki In ƙara shiryawa” amsa mashi Yai da toh, Kafin miƙewar Dr shurem P.a Ɗin Alhaji musa yai sallama daga wajen palourn, Hakan yasa shi saurin miƙewa cikin takun izza ya nufi ƙofar fita daga palourn Ajiyar zuciya dr shureim ya sauke, shi kanshi shakkar Alhaji musa yake ji, mutumin babu wasa a harkarshi. *Boss Bature✍️ Mu haɗu gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*KURKUKUN ƘADDARA*_ _The Prisoners E13🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* ~Middle step~ _A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._ Juyawa yai da sauri ya nufi kitchen maimakon ɗakin shi, Yana shiga ya ci karo da zainab tana goge tiles da floor wiper sam bata lura dashi ba, har saida yai mata sallama tukunna ta ɗago suka haɗa ido Fara’a ta sakar mashi”shuraim tun jiya na ke son yin magana da kai, fargaban Iyayenka ta hanani tunkarar ka” ƙarasa shiga kitchem ɗin yai “Aunty zainab Ya zamuyi? Uncle musa ya matsa min akan saina bishi abuja, ƙarfe sha biyu zamu bar jos, “ dafe kai ta yi da hannu ɗaya “Naji takaicin jin haka shureim, Duk plan ɗin da muka shirya ya tashi abanza kenan” Girgiza mata kai yai”in sha Allah komai zai tafi dai dai aunty zainab, ko da ace bana nan that will not change anything” Damuwa ce cunkushe akan fuskarta “How ka ke tunanin komai zai tafi dai dai bayan bamu a wuri ɗaya”? murmushin gefen fuska ya sakar mata har dimples ɗinsa suka lotsa. “Kin manta da waya? Ina da ita kina da ita, zamu dinga yin communicating da junanmu, hakan ma zai fi ba tare da wani ya zarge mu ba” ƙayataccen murmushi zainab ta saki “Allah ya yi maka albarka shureim ni sam na manta da waya, amma fa zan yi missing ɗinka sosai mutumina Murmushin fuskarshi bai washe ba yace”Ni kaina zanyi missing ɗin auntyna mai share min hawayena, amma in sha Allah zamu dinga yin waya akai akai, Inaso komai da ke faruwa a gidan nan kidinga sanya min ido, da zarar an samu update ki kirani awaya ki sanar dani, amma fa sai kinyi takatsantsan kinsan Iyayen nawa ba ƙananun mutane bane” jinjina kai Zainab ta yi don ta gamsu da bayanin shi “In sha Allah zan kiyaye shureim, kaima ka kula min da kanka, “ idanuwansu duk sun ciko da ƙwalla, don ba ƙaramin ƙaunar juna su ke yi ba, tana jinshi tamkar Ɗanta, shima Yana jinta tamkar mahaifiyarsa, sun jima a kitchen ɗin sunayin magana kafin daga bisani yai mata sallah. Ba tare da 6ata lokaci ba, Dr shureim Ya fara shirye shiryen tafiya abuja, bai canza komai na suturar jikinsa ba, Iya turarurrukansa kaɗai ya feshe jikinsa, sannan ya warware Ɗaurin larabawan dake akanshi, Ya sharce lallausar sumar kanshi Ya gyarata tsaf yabi da mayukansa ya shafe ta, Kafin barinsa ɗakin saida yai Nafila Ya roƙi Allah da ya tsare shi ya kare shi daga sharrin mutun sharrin zuciya da duk wani abun cutarwa, ya kuma roƙi Allah da ya sa silar komawarshi gidan uncle din shi abuja rayuwar shi ta canza ya dawo kamar yadda yake ada, addu’o’i sosai shureim yayiwa kanshi, Bayan ya kammala ya zaro memory ɗinshi da ya 6oye a cikin rigar pillow ya zaura shi awayarsa, Hankalin sa Ya ɗan kwanta zai samu natsuwar cigaba da kallon hotunan Abar ƙaunarsa awayarsa. A gefen gadon shi ya zauna yana daddana wayar shi, Lokaci ya ke jira ya cika. **DAULAR OBIE ESTATE** A Hankali Jigunannun Motocinsu su ke kunno kai saman shantalelen titin obie estete, gaba da baya Sojoji ne ke tafiya akan ƙafafuwansu, Hannayensu ruƙe da bindigu, Motar farko mallakin Sir mubarak ce, motar dake a biye da ita zungureriya ƙirar Navigator limousine wadda cikinta tamkar bedroom ya ke saboda tsabar haɗuwarta, Dattijon arziƙi ne hakimce acikin motar tare da Jikokinsu tagawaye zain da zaid sai Dr Jazz shalelensa, Motar da ke abiye da tasu Danƙareriyar gaske mai numfashi mallakin Senate president Lateef Obinna ce, Yayin da motar ƙarshe Ta pravin Obinna ce, gayu mutanan Allah su kansu motocin da dattaku ake yin driving ɗinsu a tsanake cikin ƙwarewa, sautin karatun kur’ani mai girma ne ya karaɗe ko’ina, Ƙirar Ahmad suleiman mai matuƙar ratsa sassan jiki, daga motar dattijon arziƙi ƙirar ke fitowa, ƙa’ida ne a lokacin da suka fito zasu tafi masallaci sai yasa an kunna masa ƙirar Ahmed suleima haka zalika idan zasu dawo daga masallaci sai an kunna masu karatun wani sa’in Idan ƙirar takai mashi karo har bi yake yi yana lumshe ido, A yanzu haka dawowarsu kenan daga masallacin Juma’a. Sannu A hankali su ke tunkarar Moto park ɗinsu, kusan atare motocin suka Yi parking at same time, Da azama sojoji su ke bubbuɗe masu mota, A hankali Obie Ya sauko ƙafarshi dake sanye cikin takalma kalar na sarakuna, Jikinsa Jallabiya ce daga sama Ya ɗaura alkebba haɗaɗɗar gaske sai ƙyalli ta ke Yi, ɗaya bayan ɗaya su ke fito daga Cikin motocin, gaba ɗayansu haɗaɗɗun Jallabiyoyi ne a jikin su daga Iyayen Har ƴa’ƴan. “Mu shiga ciki ko”? Obie ne Yai masu maganar, Zaid da zayn Sai faman sunnar dakai ƙasa suke yi kamar marasa gaskiya, mamakin hakan yasa Mahaifinsu pravin tanka masu “Lafiya”? Kafin su yi yunƙurin bashi amsa Sir Mubarak ya tari numfashin su “Zaku ci ƙaniyarku ne, ƙananun Ƴan iska masu kwana da wando, har ni zaku dinga kakkaucema wa? Kun raina ni ko”? Fuskar shi a ɗaure ya ke yi masu magana, sir mubarak mutunne mai fusatacciyar zuciya abu kaɗan ke hasala shi sai da ta wani 6angaren yana da sauƙin kai. Dr jazz Yana ruƙe da hannun Obie dariya ce ƙumshe abakinsa, ya ƙi bari ta kubce masa gudun kada Ya ji saukar mari daga Sir mubarak, Twins kuwa Duk sun sha jinin jikinsu sai faman noƙe kai suke yi haɗi da sosa ƙeyarsu. A fusace Ya daka masu tsawa har saida suka ɗan razana atare su ka ɗago da fararen idanuwansu akan fuskarshi” Ina magana kuna kallona? Saboda tsabar fitsara”? Da sauri suka sunnar da kawunansu ƙasa, Alkunyace ta hana Pravin sanya baki, Gyaran murya senate Lateef Ya yi ma ɗan uwan nashi, Ya juya yana duban shi, cikin muryan Manyantaka Ya soma magana “Aymasu afwa, Yarane su har yanzu, basu mallaki hankalin su ba, Sai ana haƙuri da su” girgiza kai Sir mubarak yai”Pls ka daina wannan maganar, Yara sun balaga kana faɗin basu mallaki hankalinsu ba”? Juyawa yai tare da kallon su twins muryarshi a kausashe yace”Dagaske baku mallaki hankulan ku ba”? Har suna haɗa baki wurin furta”wlh mun mallaki hankalinmu, pls Ka yi haƙuri Uncle mun gane kuskurenmu zamu gyara in sha Allah, Dan Allah daddy ka bashi haƙuri wlh ba zamu ƙara ba” A marairaice suke kallon Mahaifin nasu pravin, Shi dai Obie bai tanka masu ba, murmushi ne ɗauke akan fuskarshi. “Za ku Yi bayanine, muddin Owais ya dawo ƙasar nan zan sanya shi Ya ba ku horon isod, Ni dama can ban Goyi bayan aikin Company da ku ke zuwa yi ba, saboda ba ku iya komai ba” Zaro ido waje su ka yi jin abunda yace Hankalinsu ya tashi matuƙa, saboda suna mugun tsoron training ɗin Isod har ƙwara abasu horon aikin Soja, tuni sun raina kansu, Muryoyinsu tamkar zasu fashe da kuka su ke kallon Kakansu obinna don ya sa baki akan maganar Pravin na murmushi yace”dama kun daina wahalar da kan ku, kunsan wanene Kawun na ku mubarak, Idan ya yanke hukunci babu wanda Ya isa ya dakatar dashi, Ni ma kuma na goyi bayan hukuncin da ya yanke” Ransu ya 6aci jin abunda daddyn su Yace, juyawa su ka yi afusace suka nufi gidan. Girgiza Kai Sir mubarak yai”kun ga irinta ko? Ana magana sun juya sun tafi saboda rashin ganin girman nagaba da su, duk izzar Owais ba ka ta6a yi mashi magana Ya juya maka ƙeya duk mun rashin daɗinta, natsuwa ya ke yi ya saurareta, Ai duk laifinka ne Pravin da kai da Saratun Kun sangartasu duk cikin Ƴa’ƴanmu babu sangartattu irin twins, Zanyi maganinsu ne” Maganar Sir mubarak ta ta6a zuciyar Pravin, yana ɗaya daga Cikin abunda ya tsana, ya ji an kushe ƴa’ƴan shi an yabi na wasu, Musamman owais, gani yake kamar don saboda Shi ba Jinin family ɗin bane Shiyasa suke nuna ma ƴa’ƴan shi wariya. Tuni yanayin fuskarsa ya canza sam babu annuri, Ba tare da ya kalli fuskokinsu ba Ya furta”Ni zan Shiga ciki Sai kun ƙaraso” Yana faɗin hakan Ya zura hannayenshi cikin aljihun jallabiyar shi ya nufi gidan. Gaba ɗaya sun fahimci canzawar da yai, Senate Lateef ya girgiza kai Yana bin bayan pravin da kallo “Narasa gane kan mutumin can, ƙaranci Hankali nadamun shi, meye aciki don Anyi maganar ƴa’ƴan shi sangartattune? Ƙarya aka yi ne”? ran sir mubarak Yafi na kowa 6aci”Ka barni dashi, zan koya mashi hankaline, Maganar horon Isod da za’a ba ƴa’ƴan shi ba fashi ko da zuciyarshi zata buga ne ɗan rainin wayau” gyaran murya Obie Yai masu hakan Ya janyo hankulansu ga kallon shi, ya ɗan jingina bayan shi jikin motarshi su kaɗai suka rage a harabar ajiye motocin, tun bayan isowar su gidan sojojin da ke take masu baya suka watse zuwa 6angaren da suke kula da shi na gidan. “Sai kuna Yi mashi uziri, Pravin yana da raunin zuciya, ga shi dai a ido kamar Namiji sai dai a zuciya baida mararraba da mace, shima auta ne kamar saratun, mijin auta ai auta ne shima inda kara” ƙumshe dariya Dr jazz yai jin sharrin da Obinna ke yiwa Pravin Fuskar senate Lateef ɗauke da murmushi yace”A’a, baba ai ko saratun dakakkiyar zuciyace da ita, kaima ka sani gaba ɗayanmu Jinin ka muka Biyo, babu ragwantaka atare damu, shi dai ne macen Mijin tace, ita kanta saratun Juya shi take yi son ranta, Ina ji ran nan mun shigo gidan tana yi mashi masifa akan Ya zari kuɗi a account ɗinta ba tare da ya nemi iznin ta ba, sai lalla6ata ya ke yi kamar zai yi mata sujjada” Gaba ɗaya suka tuntsire da dariya, daga obinna har shi Sir mubarak ɗin. Dr Jazz ya saki baki yana tiƙar dariya kamar wani babba ya shige cikinsu, sai da suka kammala Yin dariyar, Sir mubarak Ya lura dashi, sam ya manta da dr Jazz a cikinsu, Ɗaure fuska Yai”kai! Me ka ke wa dariya? Akwai tsaranka ne acikin mu”? Da sauri Dr jazz Ya shanye dariyarshi, Hada la6ewa bayan Obinna. Senate lateef yace”Ni zan wuce gida Baba, In sha Allah zan samu lokaci in shigo ciki mu ƙara gaisawa” obie yace”kada ka ta kura kanka, Ai kuna ƙoƙari ma, Ko awaya ne munyi magana, Idan ka shiga gidan ka gaishe min da hajiyar taka, Ina nan ina jiranta ta zo ta same ni agida mu gaisa” Amsa mashi yai da toh, kafin Ya kalli ɗan uwan nashi”Ni zan wuce Mubarak agaishe min da Turai,” amsa mashi yai da toh”Nima a isar min da saƙon gaisuwa zuwa ga madam ɗin taka” A mutunce sukayiwa junansu sallama, “Baba nima zan shiga ciki, amma kafin nan zan raba ka da wannan mata mazan” yai maganar yana ƙoƙarin damƙo hannun Dr jazz, Ƙanƙame obie yai, Sir mubarak yace” So ka ke ka karyamana Uban namu, Fito nan, Ni ba wani abu zanyi maka ba, Inaso ne mu shiga ciki, ka gaida mahaifiyar taka, nasan saboda ni ya sa ka daina leƙowa wurinta, tsakaninka da sai kira awaya sai kuma idan ta shigo gaida baba” Jin abunda yace ne yasa shi sauke ajiyar zuciya, don ba ƙaramin jin shakkar Uncle mubarak ya ke yi ba, ruƙo hannun shi mubarak Yai “Zaka rabani da sanyin idaniyata” acewar dattijon arziƙi. Dr jazz yace”kada ka damu kakana, Ba zan jima ba, zan shigo gidan, pls Ka kwanta ka huta,” lumshe ido obie yai idonshi akansu har saida suka 6ace ma ganinshi, tukunna Ya ruƙe sandarshi Ya nufi cikin gidan. Hajiya saratu ce zaune gefen gadonta cikin shiga ta bubu gown anyi mata kaftan style, kanta babu mayafi, Ta natsu tana kallon screen ɗin laptop ɗinta dake ajiye a gabanta saman round table, fuskarta ɗauke da murmushi, Video call ta ke Yi da ƴar autarta Faryat dake zaune gidan Yayanta Hateem na ƙasar canada Matashiyar budurwace launin fatarta kalar na mahafiyarta ne, tana a zaune saman wasu haɗaɗɗun kujeru dake a kewaye da table, agaban tafkeken swimming pool, gefen laptop ɗinta Cup ɗin coffee ne ajiye, ta ɗauki wankan short gown ajikinta launin pink tabi shape ɗin jikinta. “Yaushe zaki dawo gida ne? Na yi missing ɗin ki daughter” Fuskar Faryat ta cika screen ɗin laptop ɗinta, faɗaɗa murmushin fuskar ta tayi da zazzaƙar muryarta ta furta “I’ll come home as soon as we have a school break because I can’t wait to see you, my first love.” “Canada ta kar6e ki daughter, kinyi haske kinyi kyau abunki, faɗamin dame dame ki ke yi a lokacin da ba ki yin komai”? Farfari Faryat tayi mata da ido kafin ta soma jera mata “Going to the movies, beach, club, playing games... “ tunkan ta ƙarasa maganar Hajiya saratu ta dakatar da ita, Fuskarta a ɗaure tace”Faryat! Kina zuwa club? Da beach..? waro ido Faryat tayi batasan tayi su6ul da baka ba, da sauri ta toshe bakinta da tafin hannuwanta “Mom, I was just joking. You know Uncle Hateem would never let me go to those places. Also Yazrin and Nazli keep an eye on me, even when there’s no school, they keep me company. I’m too busy to waste time.” Hankalin saratu har ya ɗan kwanta “Dama nasan ƙarya kike yi min, Na yadda da yayana Hateem nasan duk wani shige da fucen ki Yana a tafin hannun shi, duk da yana busy hakan bazai hana shi sanya jami’an da zasu dinga kula da motsinki ba, shiyasa tun farko na tura ki can don su gyaramin natsuwarki, kuma Alhamdulillah naga canji” Dariya Faryat ta saki jin abunda mommyn nata tace, Tsawon mintuna talatin sunayin wayar kafin daga bisani sukayi sallama da juna. Layin Landline na kitchen Hajiya sarah ta kira Safa ce ta ɗaga kiran. “Assalamu alaikum” Sarah ce tai sallama, Hajiya sarah bata tsaya amsa sallamarma ta ce”Jira ake sai nace akawo min abinci? Ko so ake in taƙo da ƙafafuwana in zo kitchen ɗin in ɗiba”? Muryar safa adabarbace ta furta”Ba haka bane Hajiya, duk laifin abla ne, itace take da aiki apart dinki, amma in sha Allah yanzu zata ƙaraso” yatsina fuska Hajiya saratu tayi fuskar ta babu annuri ko misƙala zarratin “Okey, ina buƙatar dambun nama, A haɗo mun da fresh fruit, kada amanta da farfesu...” a ƙalla ta lissafa kusan abu takwas da za’a kawota don tayi breakfast....tunkafin Ta yi rejecting kiran muryar Pravin ta ratsa kunnata Ranshi a6ace ya shigo yana zazzaga masifa”wannan wani irin wulakanci da cin fusk ne, Nifa nagaji da aibata ƴa’ƴana da ake Yi” yana huci ya ƙarasa maganar tare da goya hannayensa saman ƙirjinsa, idon saratu akanshi bayan ta katse kiran ta ɗaura wayar saman nightstand A tsanake ta soma yin magana”wanene ya ta6a min romeo ɗin nawa”? ko sallama babu ka shigo kana ta zazzaga masifa? Tell me meya faru”? Aƙagare tayi maganar, tare da yunƙurawa ta miƙe tana fuskantar shi Zuciyarshi A harzuƙe ya furta”Yayyanki mana, Akan me zasu dinga kushe ƴa’ƴana suna yabon nasu? sai yaushe ne zasu daina nuna min wariyar launin fata? Saboda kawai ni bani da alaƙa daku shine zasu dinga kushe min ƴa’ƴana”? Idan da kara ƴa’ƴana ai nasu ne’ Tsabar fusata yana magana facial muscles ɗinsa na kerma. Matsawa tayi kusa dashi, fuskarta a ɗaure ta furta”what? Wanenen acikinsu yai maganar”? Da alama ranta ya 6aci hakan ba ƙaramin daɗi yayi mashi ba “Lateef ne da Mubarak, Agaban obie da sangartaccen Yaron nan dr jazz suke kushe Twins, har faɗi sukeyi wai sangartattune basu Iya komai ba irin na maza, zaifi kyau su ajiye aikin da sukeyi na company su koma ɗaura zani” Baki asake saratu ke kallon shi hada ruƙe qugu, muryarta akausashe tace”Pravin dagaske sune suka furta hakan? Kuma agaban Baba shine bai tsawatar masu ba”? Kwa6e fuska pravin yai”ae abunda zai baki haushi, baisanya baki amaganar ba, saima murmushi da yake saki, hada wannan munafukin Yaron, Shi da ba ɗan kowa ba agidan face ɗan mai aikin, wama ya sani ko shege ne, dani da uwarshi duk ɗaya muke ai, yadda bani da alaƙa da ku, itama haka har ƙwarani mun samu ƙaruwa ta ƴa’ƴa har uku” Ran Hajiya saratu ya 6aci matuƙa, sai faman jinjina kai take yi tana fadin”bari naje wurin baban, yanzu har takai ga ƴa’ƴana aka kushewa agaban sakaran yaron nan jazz? suma waɗanda suka yi maganar zasu fuskanci 6acin raina wlh, zasu san dani suke magana” takai ƙarshen maganar tare da juyawa tana neman mayafin da zata yafa, Pravin hada saurin rigata ƙarasawa gaban closet ɗin kayansu Ya buɗe ya ɗauko mata mayafi da kanshi ya ɗaura mata shi asaman kanta, A fujajen ta fuce daga cikin ɗakin, fitarta keda wuya pravin ya soma sakin shu’umin murmushi, ba tun yau ba ya saba haɗata faɗa da ƴan uwanta, mugun munafuki ne na bugawa a jarida, A zubin halitta idan ka kalle shi tamkar Namiji. Bayan fitar Hajiya saratu da ƴan mintuna, ya sauke ajiyar zuciya yana ƙoƙarin zame jallabiyar jikin shi da niyar canza kaya, Sallamar Abla ta ratsa kunnuwanshi, Jimm ya ɗanyi kamar bazai amsa mata ba, daƙyar Ya iya buɗe baki Ya furta”shigo daga Ciki” a hankali ta turo ƙofar, Hannunta biyu ruƙe da faffaɗan tray na Kayan breakfast ɗin Hajiya saratu. Ganin Pravin shi kaɗai a ɗakin Yasa ta ɗanji faɗuwar gaba, miryarta na rawa ta furta”umm..amm dama Kayan breakfast ne na kawoma Aunty saratu” lumshe idon shi Ya ɗanyi, tare da tunkarota Ya ruƙe tray din hannuta”bari na ƙarasa shigar maki da shi ciki,” kar6a yai tare da juyawa ya ɗaura tray ɗin saman table, kafin Ya juya ta yi saurin kai hannu zata tura ƙofar ɗakin saboda sanin halin shi, sai dai kafin ta kaiga ƙarasawa ga ƙofar yai saurin damƙota ya janyota zuwa jikinshi, Hankalin abla Ba ƙaramin tashi yai ba tsananin tsorone da fargaba duk ya cikata, ƙamshin turarensa ya addabi hancinsa, cikin shessheƙar murya take faɗin”pls ka sake ni dan Allah, na roƙe ka kada kaja min bala’e,” kwantar da kanshi yai saman kafaɗarta dogon hancin shi na gogar fatar wuyanta, yayin da hannayensa ke asaman ƙirjinta ahankali yake matsasu, kamar zatayi hauka ƙoƙarin kwace kanta take yi saida ya hanata yin haka saboda ƙarfine dashi kamar doki, fashewa tayi da matsanancin kuka tana yakushin hannunshi da akaifun hannunta kamar zatayi hauka. “Nashiga uku, Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un, Ya Allah ka kawo min ɗauki,” hankalin shi kwance yake cigaba da ƙoƙarin tura hannayenshi cikin rigarta “Daddy!” muryar Zayn ce tasa shi saurin sakin Abla, ɗaure mata fuska yai “Don’t you dare tell anyone what happened. Wipe ur tears off your face right now.” Jinjina mashi kai tayi da sauri ta sanya ƙasan rigarta ta share hawayenta, shu’umin murmushi pravin ya saki’Good zaki Iya tafiya sai mun haɗu wani lokacin” wani irin ɗaci taji acikin zuciyarta, Tana buɗe ƙofar ɗakin taci karo da twins, ko kallonsu batayi ba da sauri tabi ta gefensu ta wuce, awata ƴar corner ta la6e ita kaɗai ta zuƙunna tana cigaba da yin kuka haƙika pravin ba ƙaramin cin zarafinsu yake yi ba, shiyasa suke gudun zuwa su tarar da shi a ɗakin Hajiya saratu musamman idan bata nan, Romancing ɗinsu yake yi tamkar zai kashesu, halinshi ne bunsuranci, har ƙwara Ƴa’ƴan shi twins duk iskancinsu babu ruwansu da masu aikin gidan, amma shi uban nasu baya iya kauda idonshi akansu, Ya maidasu kayan biyan buƙatar shi, Kuma ba su isa su ce zasu hana shi ba, saboda barazanar da yake yi masu, hakan yasa suke mugun jin shakkar fallasa shi awurin masu gidan, kuma hada ƙarin basu son yayi masu silar barinsu aiki gidan, ba don kudin da ake biyansu da dollar ba, sai don sabon da sukayi da mutanan gidan sannan da yawansu Iyayensu masu ƙaramin hali ne, wasu ma babu Iyayen neman na kansu suke yi don su rufawa kansu asiri. Ex-prisoners Meya hwaru Bayan jirginsu Ya ɗaga daga Cikin Dajin Evil forest shin sun sauka lafiya ko kuwa akasin hakan”? *SAN ANTONIO-TEXAS🏙* *UNITED STATES OF AMERICA* San antonio texas babban birni ne da ke a cikin jihar Texas ta america Yana ɗaya daga cikin jigunannun manyan biranan America Masu matuƙar ƙayatarwa Manya manyan gine gine na tarihi dana zamani, abubuwan more rayuwa masu ban sha’awa na musamman da kuma wadatar arziki, Hadaddiyar daula ce a U.s tsayawa suffanta kyawun birnin 6ata baki ne, balle ni da nake da abunyi. *San Antonio International Airport🛫* Katafaren Airport ne na tashi da safkar jirage dake a cikin birnin san antonio, ƙayataccen gaske, sanarwa ce ta soma fitowa daga muryar na’urar computer (PA announcement) Kunnuwan Ma’aitakan Airport ɗin da fasinjojin dake zirga zirga a cikinsa gaba daya sun natsu suna sauraron sanarwar kwamfutar “Attention, passengers. A UH-60 Black Hawk helicopter is scheduled to land at San Antonio International Airport in approximately 10 minutes. We appreciate your patience and understanding.” (“Amaida hankali, fasinjoji. Jirgin sama mai saukar ungulu na UH-60 Black Hawk yana shirin sauka a filin jirgin saman San Antonio a cikin kusan mintuna 10. Muna godiya da haƙuri da fahimtar ku.”) Tunkafin ƙarasowar Helicopter ɗin nasu tuni Daga can headquater na sojoji an kira Emmergency Number ta Asibitin University Hospital Domin zuwa ɗaukar Marasa lafiyan da Jami’an su suka ɗauko, Da wata irin jiniya Jibga jibgan Ambulances din suke zuba uban gudu saman titin da dai sadaka da airpot din, jiniyarsu ta karaɗe ko’ina duk inda suka bi darewa akeyi abasu Hanya tunkafin su ƙaraso saboda sanin aikinsu na agaji, kowace ambulance tana ɗauke da tambarin sunan asibitin UHS which means (University Health System) daga gefen rubutun Zanan white cross ne backround dinsa launin Ja,Kusan su uku ne Motocin suka jera, a Airport helipad ambulances ɗin suka Yi parking, helipad yanki ne na musamman da aka tanada domin safka da tashin helicopter. Mintuna goma na cika cuf cuf A gogon birnin San antonio ya buga ƙarfe 5 na safe, adai dai Wannan lokacin sautin Danƙareran Jirgin Da ke shawagi Saman iska Ya karaɗe kunnuwan kowa dake a yankin airport ɗin ga dukkan alamu Matafiya sun ƙaraso 🛫. Sannu Ahankali Helicoptern Ya sauke tayoyin shi yayin da ya ke yin ƙasa ƙasa, Slowly yake tafiya har yakai ga inda zai dakata a filin helipad, Sojoji ne Kewaye da Jirgin waɗanɗa suka zo tarbarsu daga headquater, Motocinsu na ajere dana ɗaukar marasa lafiyan. Buɗe Bayan Ambulances ɗin akayi at same time, Ma’aikan Jinyane waɗanda ake kira EMTs (emergency medical technicians) suka soma diddirowa daga bayan motar, mata da maza turawa cikin shigar fararen kaya masu ɗauke da tambarin Lafiya Hannayensu da ƙafafuwansu duk safunane haka zalika Sun toshe rabin fuskokinsu da face mask. Saukowa Sojojin helicopter ɗin suka soma Yi daga cikin shi, Biyu daga cikinsu ruƙe da ɗan ta’addan da su ka damƙo a evil forest, Kaitsaye suka nufi motar ƴan uwansu sojoji da suka zo daga headquater, Abayan Kanta suka wurga shi tare da datse ƙofar, Dawowa su ka yi wurin ƴan uwansu, nan fa aka fara rungume juna, ƴan uwan nasu nayi masu jinjina ta ban girma, akan Nasarar cafke ɗan ta’addan da su ka yi. Ba tare da 6ata lokaci ba, Emts suka Curo stretcher daga motarsu kusan guda Takwas, agaban Helicopter ɗin suka ƙarasa da shi ɗauke a hannunsu, Da taimakon sojoji suka dinga Jigilar ɗaukar su Angel suna miƙa su cikin motar, da aka zo kan Danish Sai dai sojojin suka kar6i stretcher ɗin suka shigar dashi ambulance ɗin, Bayan sun kammala kwasarsu, Motar sojoji gaba da baya a yayin da motocin Ambulances ɗin ke a tsakiya, da wata irin Jiniya suka haura saman titi da gudun gaske, sauran sojojin dake acikin motar da ɗan ta’addar yake tuni sun raba hanya sun nufi headquater ɗinsu da shi. *Boss Bature✍️ Mu haɗu gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*KURKUKUN ƘADDARA*_ _The Prisoners E14🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* ~Middle step~ _A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._ *Universal Hospital* Ba sai na tsaya misalta kyawun asibitin ba, tun da akace america zance Ya ƙare just imagining ɗinsa zakuyi, lokacin da motocin suka ƙaraso entry way na shiga asibitin ɗuff suka ɗaukar jiniyar bayan shigarsu A parking space motocin suka dakata da yin tafiyar, Cikin ƙanƙanin lokaci Emts Suka kammala jigilar shigar dasu cikin asibitin duk wani motsinsu akan idon sojojin Bayan kammala Shigar da su asibitin, Likitoci da nurses suka duƙufa domin duba lafiyar jikinsu, tuni sun canza masu kayan jikinsu daga Uniform ɗinsu Jajaye zuwa Patient’s uniform launin Light blue, hatta waɗanda suka 6aci da ta6o sun wanke su tass tamkar basu ta6a faɗawa cikin ca6ali ba. gaba ɗayan su a Amenity ward aka kwantar dasu, sashe na musamman da ake kwantar da sarakuna da hamshakan masu kuɗi, duk mutun ɗaya ɗaki ɗaya, tsabar haɗuwar ɗakunan tamkar bana jinya ba, anzuba ababen more rayuwa, kama daga haɗaɗɗen gado, ga A’c hada tv da frigde komai na jin daɗi, tuntuni sun farfarɗo daga suman sai dai gaba ɗayansu they were in a state of unconsciousness sakamakon firgici da tsoron da ya rikitar da su, razana suke yi haɗi da yin sambatu hakan yasa likitoci su ka yi masu allurar kashe ƙwarin jiki don su samu damar duba lafiyar jikin su, the first thing da doctors su ka fara yi masu is general checkup wanda ya haɗa da sauraran bugun zuciyar su duba hunhunsu, fatarsu da idanuwansu daga bisani suka fara yi masu gwaje-gwaje da su ka shafi blood test, chest X-ray, da sauran gwaje gwajen hotunan wasu 6angarori na ga6o6in su, domin duba raunukan da suka ji da cututtukan da ke damunsu, Cikin ƙwarewa likitocin su ke gudanar da binciken nasu, ɗaya daga cikin abunda suka gano wanda ya ɗaure masu kai, duka yaran akwai depression atattare da su (ciwon baƙin ciki da damuwa) Mutun ɗaya ne ke fama da Ciwon Zuciya (stress-induced cardiomyopathy, agaggauce su ka fara bashi taimakon gaggawa, Ga ƙarancin Jini da ya ke fama da shi, tuni sun fara yi mashi Blood transfusion. A ƙalla likitoci sun shafe tsawon awanni akansu, wani abu da yai mugun ɗaurewa Likitocin kai Ƙoshin Lafiyar Danish da kyawun surar shi! Tun da Allah ya halicce su basu ta6a ganin mutun mai rai da lafiya irin shi ba, gashi yaƙi farfaɗowa sun rasa gane wani kalar bacci ne ya ke yi, kuma sam babu wata lalura da ke gare shi, bacci ne kawai yake ta shara abin shi, Duk sun ƙagara da su ji bayani daga Gare su, Amma sun bari sai Yaran sun ji sauƙi tukunna su ji daga bakinsu menene ya haddasa masu depression? Da ƙananun shekarun su, mutun ɗaya da Sojojin su ke tsammanin Jin bayanai daga gare shi, Tun acikin jirgi da suka yi mashi allurar bacci bai ƙara farfaɗowa ba, Yanzu haka Yana akwance saman gado sai sharar baccinsa Ya ke yi. Till Wuraren ƙarfe 12 Na rana, Gabriel ya soma mutsun mutsun farkawa daga bacci, Dama jiran shi suke Yi ya tashi, Kasancewar akwai na’urorin cctv a kowace kusurwa na medical rooms ɗin ta hanyar su likitocin su ka san da tashin sa. Slowly ya buɗe idanuwanshi Akan ceilling ɗin ɗakin, Tamkar a mafarki Ya ke kallon shi, tsantsar mamaki ne da al’ajabi akan fuskarshi, Tambayar kanshi ya soma yi cikin ruɗanin zuciya, Ina ne nan? Wanene ya kawo ni? Anya ba mafarki nake Yi ba”? da wata irin kasala Gabriel ya miƙe zaune Yana faman wurwurga ƙwayar idanuwansa akan haɗaɗɗen room ɗin da ya ke a ciki, Lamarin ya ɗaure mashi kai, Daddafe kanshi yai da hannayenshi biyu tamkar zai fasa ƙara, abunda ya ƙara rikitar da shi Uniform ɗin da aka canza mashi, daga jajaye zuwa light blue Riga da wando, Ƙasa ƙasa da murya yake ambaton sunayen ƴan uwan shi “Azeeza! Angel! Danish! Batul! Naufal! Javed! Par.....” bai ƙarasa maganar ba sakamakon Jin motsin buɗe ƙofa, A firgice ya zazzare idanuwanshi akan masu shigowa. Uku daga Cikinsu asanye suke da scrub suit, Kayan Likitoci, biyun da ke biye da su cikin kakin Sojoji masu ruƙe da muƙaman Major da Captain wakilai ne da aka turo daga can headquater, likitocin uku dake atare dasu Turawa sun haɗa da md (medical director) Dr. mark Johnson, bayan shi sai Hospital Ceo Dr. laura Davis babbar macace fara jawur, na ƙarshen su health records technician ne Dr. Danial Brown hannun shi ruƙe da Apple ipad. A gaban gadon shi su ka tsaya suna dubanshi Cikin harshen turanci suke Yin magana “Fatan ka farka Lafiya? Ya jikin naka”? Dr Brown ne yai mashi maganar, cikin kulawa,.Muryarshi adabarbarce ya furta”Ina ƴan uwana suke”? Tambayar farko da ya fara jefa masu. “Did you forget that we found you in the forest? (Kamanta a daji muka tsince ku”?) Major ne Yai mashi maganar, Gabriel was silent as he tried to remember what had happened. They could see that he was confused and would need time to sort out his memories. Nuna mashi screen ɗin Ipad dr bown yai, hotunansu Angel ne a jere da suka ɗauka yayi saving ɗinsu akan wayar, ƙura ido gabriel yai akan screen ɗin, a tsanake ya ke ƙare masu kallo, nan take ya zaro ido wani irin farin Cikine Ya lullu6e shi, hada murmushin sa. “Do you remember everything now”? Major ne yai maganar, Jinjina mashi kai yai alamar eh, janye wayar dr.bown yai tare da kallon abokan aikin nasa da sojojin “He needs some food and a cold drink” Jinjina kai su ka Yi, A waya Md Ya kira nurse Ya isar da saƙon abunda za’a kawo masu, cikin ƙanƙanin Lokaci Nurse ta shigo hannunta biyu ruƙe da round tray saman shi plate ne shaƙe da abinci sai bottles biyu na ruwa dana lemu mai sanyi, A saman table ɗin gaban gadon gabriel ta sauke tray ɗin kafin ta juya ta fuce, Zama suka yi saman sofa ɗin dake a ɗakin suna jiran shi Ya kammala ci. Kafin ya fara cin abinci sai da ya fara ɗagowa ya kalle su”Ni zan ci”? murmushi suka sakar mashi Jin tambayar da yai masu Md yace”’It’s all yours. Eat until you are satisfied. We need to talk to you when you’re done.” A kan idonsu Gabriel Ke cin abincin sai da ya ci ya ƙoshi Ya kora da ruwan sanyi, tukunna ya dawo da duban shi gare su. “Zamu iya farawa yanzu” ɗaga masu kai yai alamar eh Major ne Ya fara yi mashi magana “Zaka Iya fadamin alaƙar dake a tsakaninka da sauran yaran? Jinjina kai Gabriel yai”Eh, Ƴan uwana ne” “Menene sunayenku da shekarunku”? Duk wata kalma da Gabriel ya furta a rubuce dr. Brown ya ke shigar da bayanan cikin ipad ɗin hannunsa. “Muna zargin Ɗan ta’addan da muka je kamawa A dajine yai garkuwa da ku don gujewa farmakin da zamu kai mashi Shin dagaske ne”? Ras Gaban Gabriel Ya faɗi, tuni yanayin fuskarshi ya canza baisan amsar da zai basu ba, jin shiru yasa Major ambaton sunanshi”Gabriel amsar ka mu ke jira, muna so mu tabbatar da hasashen mu ne” idanuwanshi sunyi wuƙi wuƙi akan fuskokinsu, duk sun ƙagara da son jin amsar da zai basu, abunda yasa ya shiga ruɗani kokwantone yake yi Akan ya faɗa masu gaskiya ko kuwa ya 6oyeta gudun kada su ƙara jefa rayuwarsu cikin hatsari, Yana tsoron abunda harshenshi zai furta, Tunawa da Angel yasa shi saurin cewa “I have forgotten everything, but my sister Angel knows everything.” ya faɗi hakanne don su ƙyale shi, don kuma su tuntu6eta don yasan tafi shi wayau ita kaɗai tasan yadda za ta yi ta fidda su. Numfasawa Kowan nan su yai, sun fahimci har yanzu babu kwanciyar hankali atattare da shi “Gabriel, please calm down and explain to us what happened. We’re medical professionals, and we have the right to examine your health and help you get better. And those soldiers you see are the ones who saved your life in the forest. If you cooperate with us, we’ll help you and reunite you with your family.” cikin kwantar da murya dr laura ta yi mashi magana. wahalalln Yawu gabriel ya haɗiya muryarshi na rawa ya furta”Angel tasan komai, duk wani bayani da kuke son ji daga bakina ita zata faɗa maku,” “Can you identify your sister from these photos? Wacece Angel a cikinsu”? Dr.brown ne yai maganar tare da nuna mashi hotunansu ta cikin ipad’s gallery din hannunsa Ƙura ido gabriel yai akan fuskarta ya ɗaura yatsan shi”Itace” Dr. mark ne ya soma yin magana “muna son jin bayani dangane da abunda ke damunku”? Ya yi mashi tambayar ne saboda abun da ya ɗaure masu kai, na farko Depression dake damunsu da ƙananun shekarun su, na biyu dangane da matashin saurayin nan da ya tsone masu ido wato Danish da ya ƙi farkawa daga bacci. “Babu” amsar daya basu kenan Captaim yace”ka natsu kayi mana bayani, ba cutar dakai zamuyi ba, idan har baka bamu amsa ba zamu maida ku inda muka ɗauko ku ne” jin haka yasa Gabriel zazzare mashi ido, da sauri ya girgiza kai yana faɗin”Ni ai bansan komai ba Angel ce ta sani,” kansu ya ɗaure jin yanata ambaton sunan Angel “We should wait until your sister wakes up and see if she can provide any information that might help us.” acewar dr. brown Gaba ɗaya sunyi amanna da hakan, Miƙewa Sojojin sukayi tare da likitocin Bayan sunce mashi ya koma ya kwanta suka fuce daga ɗakin, A bakin ƙofar ɗakin suka tsaya suna tattaunawa a tsakaninsu, Hankalinsu yaƙi kwanciya da yaran, sun fara kokwanton Anya kuwa Jinsin su ne? Ko dai sun yi kuskure wurin ɗauko su a matsayin ɗan’ta’addan ƙasar su ne yai garkuwa da su, Kyawun yaran yafi komai tafiya da hankalin su, sun rasa da wani jinsi zasu danganta su, Saboda Kyawun prisoners Ya banbanta dana sauran mutane su ɗin na dabanne. Bayan kammala tattaunawar su, Sojojin sun bar asibitin da niyar idan sauran Yaran suka farfaɗo daga bacci Ayi hanzarin kiransu da gaggawa don suna buƙatar ganawa da su. Nauyayyar ajiyar zuciya Gabriel ya sauke tun bayan fitarsu yake ta sakin murmushi baƙin shi yaƙi rufuwa, tuni hawayen farin ciki sun wanke fuskarshi bakomai yake tunawa ba fa ce twin sister ɗinsa da sauran ƴan uwansu da suka rasa rayukan su a kurkuku, Ya ji raɗaɗin Rasa su da su ka yi da yanzu duk atare zasu ji daɗin rayuwarsu, don yana ji aranshi ƙarshen wahalar su ce tazo, babban burin shi a yanzu sauran ƴan uwansu su farfaɗo, Yasan zasuyi farin ciki Mara misaltuwa, fatan shi Allah yasa Idan Angel ta farfaɗo Ta yi ƙoƙari wurin yin magana da sojojin cikin hikma yadda zata yi masu hanyar komawa gidan daddynta ko dan saboda azeezarshi da ta ƙwallafa rai da son zuwa can. Yayin da ya ke yin tunanin, hawaye basu daina yin sintiri akan fuskarsa ba, a saman pillow ya ɗaura kansa, ga sanyin A.c dake ratsa jikinsa. Motsin buɗe ƙofa ya ji da sauri ya ɗan yunƙura ya miƙe zaune yana kallon mai shigowa ciki, Matashiyar Nurse ɗin da ta kawo masa abinci ce ɗazu, Fuskarta ɗauke da murmushi agaban gadon ta tsaya tare da goya hannayenta saman ƙirjinta Fuskarta da murmushi ta soma magana “Hello, I’m Sister Rebecca, May I know your name?” Daƙyar ya iya buɗe baki ya furta suna shi “Gabriel” jinjina kai nurse rebecca tayi a wayance tace “It’s wonderful to meet you, Gabriel. How is your body? I hope you’re feeling better now,” Rashin sabo ya hana ya saki jiki da ita, cikin rashin natsuwa yake amsa mata. Ganin yadda take sakar masa fuska yasa shima sakin tashi fuskar “Is there any part of your body that’s hurting?” cikin kulawa ta yi mashi tambayar. Girgiza mata kai yai”A’a lafiyata ƙalau” “Okay, is there anything you need?” again ta ƙara tambayar shi. Ƙasa ƙasa da murya ya furta “No, thank you.” “Okey, ko akwai wani abu da kake buƙata”? Shiru ya ɗanyi yana faman wurwurga eye balls dinsa ɗakin Ya ke bi da kallo Ganin kamar tv yake kallo yasa tace” “Would you like to watch some TV?” Numfasawa yai tare da mayar da idon shi akanta “I wanna see my brothers, I want to know how they’re doing.” “Please, don’t worry, Your relatives are in good health and we expect them to wake up soon.” da sauri ya tari numfashin ta “Can you help me go to their room to see them?” A ƙagare yai mata maganar “Don’t worry I’ll take you to see them but first you need to rest. You’ve traveled for hours, and you must be tired. I’ll turn on the TV so you can relax, and if you need anything, you can use the phone to call me.” ta yi maganar tana nuna mashi wayar dake ajiye saman table na gefen gadonshi “Ga kuma ƙofar shiga toilet idan kana buƙata” duk abunda ta yi mashi bayani saita nuna mashi da hannu Bayan ta kammala, Taje gaban plasma tv dake manne jikin bango ta kunna mashi tashar da ake wasan ƙwallon, don tasan mafi akasin maza sunfi sha’awar kallon wasan ƙwallo, A ƙirji ya rungume pillow yana kallon tv ɗin, fuskar nan ɗauke da annuri banza ta samu an samu ƴanci, Yadda nurse ɗin ke tarairayarshi kamar wani ƙaramin yaro da bai wuci shekara goma ba. Kafin barinta ɗakin saida ta ɗauki Kayan abincin da ta kawo mashi ta fuce da su robar lemun da bai sha ba kaɗai ta bar mashi, Hannu ya miƙa ya ɗauke ta, Yana sha Yana kallo Hankalin shi kwance gwanin ban sha’awa *The prisoners Middle step❤* Wuraren ƙarfe ɗaya na rana agogon birnin san antonio ta buga, adai dai wannan lokacin sambatun muryar Angel ya cika ɗakin da aka kwantar da ita, tana akwance saman haɗaɗɗen gadon, patient’s gown ce a jikinta launin ligh blue, drip ɗin da aka sanya mata tuni ya jima da ƙarewa, zazza6in jikinta ya sauka temperature ɗinta ya dai dai ta. Muryarta na kakarwa take ambaton sunan danish, Shi ya tsaya mata arai shiyasa take sambatun ambaton sunansa, duk da sanyin A.c na ɗakin hakan bai hana zufa tsastsafo mata ba, zucyarta na harbawa da ƙarfi da ƙarfi “Danish ɗina kura ta cinye min shi, wayyo Allah Danish ɗina na shigo uku munbar Danish Gabriel kura Zata kashe min shi.....” tuntana sambtun a hankali har takaiga ƙware murya da wata irin firgita Ta ware Gray eyes dinta ta zazzare su akan haɗaɗɗen ceilling ɗin ɗakin, Sam bata acikin Hayyacinta, bakomai take gani acikin idanuwanta ba face Fuskar Kurar da ta biyo su A daji tana gurnani, gizo take yi mata, A gigice ta zabura har batasan ta fisge iv line ɗin dake hannunta ba, durowa daga saman gadon tayi Hannayenta bibbiyu daddafe da kanta, Tsantsar tashin hankali ne akan fuskarta, duk tabi ta furgice, doguwar sumar kanta har saitin gwiwarta gaba ɗaya ta hautsine gashin kan tamkar na mahaukaciya, Sam bata acikin hayyacinta batasan A ina take ba? Daji kawai take gani a idonta Sosai ta fashe da kuka tamkar ranta zai fita, idanuwanta sun makance,, Da gudun gaske Likitoci suka faɗo ɗakin da take a ciki, Dama jiran farkawarta suke yi, wasu daga cikin Ƴan uwanta sun farka acan inda aka kwantar dasu, Sun rasa gane kan Yaran tsabar tsoro da firgici Jikin su sai kerma ya ke yi sunga mutanan da basu saba gani ba, duk wanda yai yunƙurin tunkararsu ƙara suke fasawa tamkar ana zare ran su, Kalma ɗaya su ke iya ambato abakunansu Sunan Angel wannan yasa Likitocin su ka ƙara da ta farka, don sun fahimci ita kaɗaice zata Iya sarrafa su. Sam bata ji motsin shigowarsu ba, Sai dai ta ji muryoyinsu akanta, Nan fa hankalin Ta ya ƙara tashi, A firgice ta waiwayo tana binsu da kallo tun daga ƙasa har sama, Waro idanuwanta waje tayi tamkar ƙwayar zata faɗo kasa, jijiyoyin wuyanta sun fito ruɗu ruɗu, tsantsar tashin hankaline akan fuskarta da ruɗani, sai lokacin ta soma tunanin wai ma A ina take ne? Ya akai ta tsinci kanta a wurin nan? Wanene Ya kawota? ina ƴan uwanta suke? Su wanene waɗannan masu fararen Kayan kamar likitoci ne”? Wahalallan Yawu ta haɗiya, zufa duk ta wanke fuskarta da jikinta, yadda kasan wadda ta yi tozali da aljanu, ganin komai take yi tamkar a mafarki Cikin kwantar da murya su ke yi mata magana don sun fahimci arikice take babu natsuwa atattare da ita “Ki kwantar da hankalin ki, Dukanmu nan da kike gani likitoci ne, mune masu kula da lafiyarki, Sannan anan inda kike Asibitine.....” Ras taji gabanta ya faɗi Cikin sarƙewar murya ta soma motsa small lips ɗinta “Ban...ban..gane ba wanene ya kawo ni nan? Su wanene ku kuma Ina ƴan uwana su ke”? Kallon tuhuma take binsu da shi gani take yi kamar mugaye ne. “Ƴan uwanki suna nan Cikin ƙoshin Lafiya, idan kika natsu zamu Nuna maki su, wata’ƙil hankalinki ya kwanta” maƙe mashi kafaɗa tayi”wlh bazan yarda daku ba, so kuke ku cutar dani, Ni ku faɗamun Ina danish ɗina yake da sauran ƴan uwana.....” cikin disasshiyar murya tayi maganar hawayen nabin fuskarta, ganin suna matsowa kusa da ita aiko da sauri ta dinga ja da baya tana girgiza masu kai, haɗi da zazzare masu ido don karsu ta6ata Hakan yasa suka dakata da yin tafiyar, turo ƙofar da akayi ne yasa gaba ɗayansu suka juya don ganin wanene Nurse rebecca ce Ta shigo ɗakin hannunta ruƙe dana Gabriel, Wani irin farin Cikine Ya lullu6e shi ganin Angel, Ita ko ta runtse ido, Masifa kawai take Ji, da ƙarfi Ya ambaci sunanta”ANGEL!!” Kaitsaye kiran ya daki dodon kunnanta, Kamar an tsunkuleta Ta buɗe ido Tana faman zazzaresu Akan fuskokinsu, da gudu gabriel Ya ƙarasa gabanta, Gaba ɗaya ya rungumeta Yana dariya, A ƙalla ta sauke ajiyar zuciya yafi a ƙirgita, ƙanƙame shi tayi tamkar zasu koma mutun ɗaya. Likitocin dake a tsaitsaye cirko cirkon suna kallonsu, murmushine ya bayyana akan fuskokinsu, tamkar sun samu tv. Raba Jikinta Tayi daga na Gabriel Muryarta na rawa take faɗin”Gabriel wanene ya kawo mu nan? Pls ka faɗamin Aruɗe nake bangane komai ba, Ina danish dina da sauran Ƴan uwana? Ruƙo Hannayenta yai acikin nashi”Angel mun tsira! Mun ku6uta daga kurkukun ƙaddara da Evil forest.......” a tsanake Gabriel Ya kwashe komai Ya sanar da ita, Cikin harshen hausa, hakan yasa Doctors din basuji me yake faɗa mata ba. Maimakon tayi dariya Sai gani suka yi ta rushe da matsanancin kuka, abunda da ya ɗaure masu kai, tana kuka tana dariya a lokaci ɗaya, slowly ta zube saman gwiwowinta, tare da ɗaura goshinta saman tiles, Sujjada tayi domin nuna godiyarta ga Allah daya nuna mata wannan ranar da suka daɗe suna Jiranta! *Boss Bature✍️ Mu haɗu gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*KURKUKUN ƘADDARA*_ _The Prisoners E15🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* ~Middle step~ Lokacin da ta ɗago daga sujjadar fuskarta jaga jaga da hawayen, Tafin Hannayenta ta ɗaga sama ta soma ambaton sunan Allah tana Yi mashi kirari, Hakan Ba ƙaramin ruɗar da likitocin yai ba, shi dai Gabriel sai murmushi yake saki yana dubanta, Bayin Allah su kaɗai suka san Wahalar rayuwar da suka fuskanta Dole suji daɗin wannan Ranar, Ta jima tana addu’a, Sam takasa miƙewa daga zaunan da take, Hawayen fuskarta tamkar zasu ƙare Sai sintiri suke yi saman kuncinta “Angel pls stop shedding ur tears” Gabriel ne Yai mata maganar, Cikin shessheƙar kuka ta ɗago ta Kalle shi da rinannun idanuwanta waɗanda suka kada jawur da su “Gabriel dole in yi kukan farin Ciki, kai ka sani irin wahalar da muka sha, munyi rayuwar kulle tamkar dabbobi har ƙwara ni akan sauran ƴan uwana tun suna jarirai, wannan ne karo na farko da zasu ɗanɗani rayuwar ƴanci acikin ƴan uwansu mutane, Iya cuta an cuci rayuwarsu mun tsira amma raunin dake acikin zukatanmu na har abada ne, saboda akwai abubuwan da muka rasa wanda nayi imanin baza su ta6a gogewa a tarihin rayuwarmu ba” Hankalin likitocin ba ƙaramin tashi yai ba ganin yadda take kuka tana surutu gashi ba su fahimtar abunda take cewa, sai dai sun gane akwai abunda ke damun su wanda yai silar haifar masu da ciwon damuwa da baƙin ciki Gabriel da ke a tsaye tuni shima ya fara zubar da hawaye. Gabanta ne Ya ɗan faɗi Jin kukan Jemimah, Nan take shessheƙar kukan da ta ke yi ya dakata, Dr. Laura ce ta shigo Ɗakin hannunta ɗauke da Jemimah Tsabar jaraba ta runtse idanuwanta sun yi suntum saboda kuka, Sunan Genie kaɗai Take furtawa, jikin Angel na rawa Ta yunkura ta miƙe da sauri ta nufi dr. laura Hannu biyu tasa ta kar6eta sosai ta rungumeta a ƙirjinta, hannunta hada cannula da aka sanya mata. “Angel” Muryar Batul ce ta ratsa kunnuwanta, da sauri ta ɗago tana kallonsu, A jere su ke shigo ɗakin kowan nan su Yasha kuka Idanuwa sunyi luhu luhu, doguwar suman kawu nan su A hargitse kamar waɗanda aka koro daga gidan mahaukata. Kowan nan su Na sanye da light blue uniform da aka sanya masu, hannayensu sanye da cannula na drip da aka sanya masu. Batul ce ta farko, Bayanta Parveen ce da hannah, Sai mazan Javed da Naufal, da gudum gaske suka ƙarasa shiga ɗakin gaba ɗaya suka ƙanƙame Angel kamar zasu kada ita ƙasa. Al’ajabi Ya hana Likitocin cewa komai, Sun saki baki galala suna kallon Ikon Allah, Aransu suna Mamakin ƙaunar da suke yi ma ƙaramar Yarinyar da su ke kira da Suna Angel. Farin Ciki kamar zai kasheta, Daɗi take ji tarasa ina zata tsoma ranta, Sun lullu6eta suna yi mata kuka, ko numfashi daƙyar take Iya fitarwa “Angel ina ne nan? Wanene Ya kawo mu? Wlh tsoro muke ji, munga wasu mutane da bamu saba gani ba, kada su cutar damu Angel, sai kallon mu suke yi kamar zasu lashe mu” Su parveen ne ke kora mata jawabi “Ko dai mafarki muke Yi ne? Mu dake acikin Daji Ya akai muka tsinci kanmu a wannan wurin tare da wasu mutane masu fararen Kaya, Angel ko dai Aljannace da kike bamu labari? Idan mun mutu zamu shiga” Maganar Batul tayi matuƙar bata dariya, Daƙyar ta samu suka saketa, Ga jemimah ta ƙanƙameta Jikinta sai kerma Yake yi. Azeeza tana maƙale da Gabriel Sarkin tsoro, Ta kasa ɗauke idanuwanta daga kan faces ɗin Likitocin dake a tsaitsaye cirko cirko suna kallonsu. “Angel mun shiga ku, Sai kallon mu suke yi,” Hanna ce ta yi maganar Muryar dr. Laura ce ta katse masu Hanzarinsu cikin harshen turanci ta ke yin maganar “Ku kwantar da hankalinku, babu wanda zai cutar daku, Anan inda kuke Asibiti ne, mu kuma da kuke gani likitoci ne da nurses haƙƙinmu ne kula da Lafiyarku, Za mu taimaka maku don ganin kun warware daga lalurar dake damunku, Muna so ku ɗauke mu tamkar Ƴan uwanku, idan ku ka yi hakan munyi maku alƙawarin zamu share maku hawayenku, Zamu gatanta ku mu baku kyakkyawan kulawa har izuwa lokacin da zamu miƙa ku ga Iyayen ku. Tun da tafara Yi masu magana kowannansu Ya natsu yana sauraronta, da alama sun fara fahimtarta Matsowa Kusa Dr Brown Yai daga gefenta Ya tsaya”duk wani abu da kuke buƙata zamu yi maku shi, ku ɗauka tamkar kuna a gidan Iyayenku ne, burin mu shine ku bamu haɗin kai, Ku daina Jin tsoron mu” Muryar Dr Jack Ce Ta janyo hankulansu ga dubanshi “Mun haɗa ku wuri ɗaya ne saboda mun fahimci ba za ku ta6a sakewa damu ba, idan har ba Kuna atare da Ƴar uwarku Angel ba, Muna fata Yanzu hankalinku zai kwanta, ga ku ga Mamanku Angel” Da zolaya yayi masu maganar, murmushi Angel ta saki tana kallonsu, daga gani suna da mutunci. “Masoyiya Angel faɗa min me ki ke yi wa Yaran nan naki ne? Don na lura ba ƙaramin ƙaunar ki su ke Yi ba” Dr Brown ne yai magana haɗi da ɗaga mata gira ɗaya, Sunnar da kanta ƙasa Tayi dariya takeso tayi sai da takasa. “Yaushe kika haife su ne? Sannan Ina Mijin naki”? Kunyace ta rufe Angel da sauri ta ɗaura Kanta saman sumar kan Jemimah dake ruƙe a hannunta. Dariya Dr. laura ta saki”Wow Kunya take ji, To ko dai Matashin saurayin nan mai bacci ne mijinki? Wannan kyakkyawan don naji kamar kina ambaton sunanshi” gaba ɗaya sun sanyata jin Kunya ji take kamar ta nutse ga farin Ciki da ya lullu6eta. Da biyu likitocin suke zolayarta, Yana daga cikin aikinsu kwantar da hankalin Mara lafiya musamman su da suke son su saki jiki da su, Ta hakanne zasu samu bayanan da suke so daga gareta. “Mun fahimci Masoyiya Angel bakinta ya mutu, saboda An sosa mata inda ke yi mata ƙaiƙayi, Yanzu faɗa min me kikeson Ci ke da Ƴan uwan naki mu kawo maku” Cikin kulawa Dr. laura ke yi mata magana. Kallon sauran Ƴan uwan nata tayi “Ko ba ku jin yunwa ne”? Shiru suka yi ba wanda Ya bata amsa, idonsu akan Angel, Dariya doctors ɗin suka saki “Oh Baku Iya magana sai da izninta, to ke masoyiya Angel Faɗa mana me kikeso akawo maki keda Ƴa’ƴan naki don bama son barinku da Yunwa” Cikin Jin kunyarsu Angel ta furta”komai muka samu zamu ci” Jinjina kai Dr Laura Tayi kafin ta juya ta kalli Sister rebecca”A shirya masu lafiyayyan abinci da Kayan sha” amsa mata Tayi da toh da sauri ta juya ta fuce. Dawo da dubanta tayi akan fuskokinsu “Yanzu zamu tafi mu baku wuri Pls Idan an kawo maku abincin Ku tabbatar Kun cinye min shi duka kaf, zanji daɗin hakan,’ dr Laura davis Na rufe Maki Dr Mark Yace”Zamu dawo Da Anjima, Kyawawan ƴan mata, dole in za6i ɗaya daga cikin ku, irin wannan Kyau haka” Dr Bown Yace”ai ba kai kaɗai ba mutumina, Ni ruwan ido ma ya hanani zabar ɗaya, ta ko’ina Kyau nake gani musamman Masoyiya Angel ta tafi da ni” Dariya ce ta kubcewa Angel da Gabriel Harara Dr Laura davis Ta watsa mashi”bazaiyiwu ba, Duk na riga ku, Nima nayiwa ƴa’ƴana kamun matan aure a Cikin su’ Nishaɗi sosai suka sanya su. “Zamu tafi Masoyiya Angel, Amma kafin nan Ki kula mana da ƴa’ƴanki, Ki lallashesu su daina mana kuka dake kanki bama so kuna zubda tsadaddun hawayenku” Cikin sanyin murya Angel ta amsa mata da toh, Sallama suka Yi masu atare suka fuce daga ɗakin suna masu santin Kyawun Yaran acikin ransu. Fitarsu keda Wuya Ange Ta fada saman Gadon rungume da jamimah tana tiƙar dariyar Farin Ciki tana faɗin”ALHAMDULILLAHI ALA KULLI HALIN” “Kuyi Farin Ciki mana, Ina Tayamu murna Mun ku6uta daga Kurkukun ƙaddara, Mun zama masu ƴanci” Su Batul sunƙi sakin jiki har yanzu basu fahimci Ta ya ya akai suka tsinci kansu a wannan wurin ba. Gabriel ne yai ƙoƙarin fahimtar da su abunda Ya faru zuwan Sojoji Dajin. Wayyo Allah daɗi Wani irin annurin farin cikine Ya bayyana akan fuskokinsu, Bakunansu sun kasa rufuwa Fararen haƙoransu tamkar Gonar auduga “Gabriel kana nufin Yanzu mun bar kurkuku da daji? Muna acikin Mutanan duniya” Fuskar Gabriel da murmushi Ya amsa masu”ƙwarai kuwa, Babu ku babu zubar da hawaye baƙin ciki da kunci sun ƙare” Tsabar Farin Ciki Suna kuka suna dariya, gaba ɗaya suka Haye saman Gadon Angel, suka kwanta a jere da ita sai daɗi suke ji saman ceilling ɗin ɗakin suka ƙurawa ido kowa Yana tariyo abubuwan da suka faru a rayuwarshi jin shessheƙar kukansu ta cika ɗakinne Yasa ta soma yi masu magana cikin lallashi “Dan Allah ku daina, Yanzu lokacin farin ciki ne, Godiya yakamata Muyiwa Allah, a koda yaushe shi mahaƙurci mawadaci ne, yau gashi dai mun shaida hakan Allah ya kar6i kokenmu yaji ƙanmu ya raba mu da ƙangin rayuwar da muke aciki, A yau mu masu ƴan ci ne zamu shaƙi Iskar duniya son ranmu batare da wani yayi mana Iyaka da ita ba” Murmushine Ya bayyana akan fuskokinsu Cikin shessheƙar Kuka Azeeza ta soma magana tana fadin”Ni ƴan uwanmu nake tunanawo waɗanda muka rasa acikinmu, tare da Salsabeel da ya taimaki rayuwar mu, nasan dole su kashe shi idan suka kama shi Yana acan kurkuku Suna azabtar dashi” Naufal ya ɗaura da cewa”babu Deeja! Babu Mubeen Akan idonmu ya yanke jiki Ya faɗi, a lokacin muna aga6ar barin kurkuku.....” Kasa ƙarasa maganar Yayi saboda kukan da ya ciyo shi. Javed ya dasa daga Inda ya tsaya”Mun rasa tsohuwa tamira! Mun rasa Eve da Yasmin sannan mun rasa Hibba da Rubina, da Sarah! “ tunkan Ya rufe Baki Angel ta ɗaura da cewa”Allah Sarki Unaiza Ƴar gidan daddy, da Majnoon Bayin Allah ban ta6a tunanin zamu tsira ba tare dasu, Muna ƙaunar ƴan uwanmu sosai, Sai dai mutuwa tayi mana Yankan ƙauna, Ta raba mu da su, In sha Allah zamu haɗu da su agidan Aljanna inda babu kurkukun ƙaddara babu duk wani mugu, Allah sarki tsohuwa tamira da Salsabeel waɗannan bayin Allahn Har duniya ta naɗe bazamu ta6a mantawa dasu ba, saboda Sun kafa tarihi acikin zukatanmu In sha Allah a koda yaushe zamu dinga binsu da addu’a, sannan zamu Cika masu burin su na ruguza tarihin KURUKUKUN ƘADDARA. Abubuwa da dama suke tariyowa na rayuwarsu na baƙin Ciki da farin Ciki “Angel Danish fa har yanzu bai farfaɗo ba, Haris kuma Bashi da ƙoshin lafiya nurse ta faɗa min abunda ke damun shi ni nasan silar deeja ne, Amma tace Ciwon nashi bazai jima ba, Zaiji sauki” Jin wannan maganar yasa gabanta faɗuwa, A hanzarce ta miƙe zaune saman mattress ɗin, su Batul ma suka mimmiƙe suna kallonta, sun sha kuka fuskokinsu sunyi jawur dasu abunka ga farare, Ita dai Jemimah tunda ta lafe ma angel hankalinta kwance bata da sauran damuwa. Ƙasa ƙasa da murya ta ambaci kalmar Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un! Gabriel Akwai matsala! Wai ni wace ƙasa ce wannan”? A matuƙar ruɗe ta jefa mashi Tambayar, duk budurin da akeyi bata lura da fararen fata bane sai da yayi mata zancen Danish. “Ni kaina Angel bansani ba” Dafe kai tayi da hannu ɗaya, Yayin da take bin ko’ina na room ɗin da kallo, karaf idonta ya sauka akan wani hoto dake manne jikin bango, a jikin shi an rubuta SAN ANTONIO TEXAS United states of America zazzare idanuwanta waje tayi wuƙi wuƙi Muryarta Na kakarwa ta soma maimaita Sunan America, tun da take arayuwarta bata ta6a taka kafadarta a ƙasar waje ba, Iya Nigeria ne, Yau ƙaddara Ta jefo su America a maimakon Nigeria! Hankalinta idan yai dubu toh ya tashi, ta ya ya zasu Koma Nigeria har su samu damar ɗauko ruwan zamzam da zasu ba Danish? Don tana Ji aranta Baccin da yake yi bana lafiya bane zaiyi wuya ya farka batare da giant’s heart ɗinsa ta motsa ba, Muryoyinsu Aruɗe su ke ambaci sunanta”Angel menene? Bamu tsira ba ko? Wani abu zai faru damu”? Girgiza masu kai tayi muryarta tamkar zata fashe da kuka tace”Wlh ba Nigeria bace wannan ba ƙasa ta bace, America ce ƙasar turawa, taya akai haka ta faru!? Nauyayyar ajiyar zuciya suka sauke, don su basu san abunda take gujemawa ba, Lamarin ya girgizata har tafara tunanin dama kurkukun ƙaddarar ba A nigeria ya ke ba? Akwai gagarumar matsala dole su nemi mafita. “Angel ae zamu Iya zuwa can ko”? Da sauri Gabriel ya amsa masu da cewa”Eh mana ba wani abu, kada ku damu kanku, Sojoji sunce idan muka basu haɗin kai zasu damƙa mu wurin Iyayenmu, Idan suka tambayemu sai mu faɗa masu cewa Mu ƴan nigeria ne” Kafin wani Ya ƙara magana acikinsu, Nurse rebecca Ta turo ƙofar ɗakin Hannunta ruƙe da faffaɗan tray na kayan abinci da aka jera masu, A saman table ta ɗaura masu, kafin ta ɗago tana dubansu fuskarta ɗauke da murmushi tace”Idan kuna buƙatar wani abu zaku Iya kira awaya ku sanar dani” Ta yi maganar tana nuna masu wayar dake ajiye saman table, al’ajabi ne ya kama su wai yau sune ake tarairaya? har tambayarsu ake yi in suna buƙatar wani abu? Wannan wani irin abun farin ciki ne! Har ta juya zata fuce, Muryar Angel ta dakatar da ita “Sister, which country are we in?” ? ta tambaye ta ne don ta ƙara tabbatarwa Juyowa Nurse rebecce tayi fuskarta da fara’a ta furta”San antonio texas” idanuwan angel luhu luhu ta ce”Thank u” Hankalin Angel Yaƙi kwanciya, sam bata lura Sun fara Cin abincin ba, gaba ɗayansu sun dawo bakin gadon, Su parveen banza ta samu, soyayyar kaza mai maiƙo ta damƙa tana turawa abaki atsiyace take cizgar Naman kazar, Jemimah ta sungumi tsiran nama ita da azeeza, Batul kuwa Soyayyan ƙwai ta ɗauka tana Ci har wani nannaɗe shi take yi kafin ta tura abaki, Hannah ko warmer ta ɗauka shaƙe da Chips tana ci, Ba baka sai kunne, Su naufal an dahi Chicken shawarma, Javed ko Kayan marmari ya damƙa yana sha, kamar kwancen Yunwa Sun zaƙe suna ci suna Korawa da lemu me sanyi kala kala aka kawo masu, basu san akwai cctv ba a ɗakin, Duk wani motsinsu ana kallonsu😂 Ita kanta Angel data dubesu saida gabanta ya faɗi, Ganin yadda suke cunkusa abinci abakunansu Kamar kuraye, Muryarta na rawa take faɗin’pls ku bi a hankali kada ku shaƙe” tamkar kurame babu wanda ya dubeta bama su san akan me take magana ba, a dole ta ƙyalesu ta zura hannu ta ɗauki burger tana ci........... *BARI MU LEƘA GIDA NIGERIA* *A DAULAR OBIE ESTATE* A Zaune take dirshan acikin Katafaren Bedroom ɗin Obinna, wa’iya zubilla kai kace ɗakin matashin saurayine saboda tsabar haɗuwarshi, An kashe dukiya a furniture ɗin ɗakin komai na cikinsa launin Red and golden ne, Ko sarki Albarka, Tanƙamemen gadonsa Royal state bed irin gadon da ko mutun baijin bacci ya hau sai Ya runtsa, Ga wasu matassan kai launin red da golden jere a gaban headboard ɗin, Dogayen labulaye ne a kewaye da ɗakin, ga wasu bedside drawers masu ɗauke da lamp, daga saman ceilling ɗin ɗakin Haɗaɗɗen Chandeliar ne dake bada hasken ɗakin ga wata zungureriyar Sofa Bayan ita akwai arm chairs masu ɗan banzan kyau, Ga wani ƙayataccen table dake ɗauke da Kayan Ado na ɗaki. Daga jikin bangon ɗakin haɗaɗɗiyar wallpaper ce mai zanan flowers masu matuƙar ƙayatarwa da jan hakalin me kallonsu, floor ɗin ɗakin tamkar mirrored tiles ne Kana Iya ganin fuskarka a cikinsa tamkar madubi, ga wani Jigunannan Dressing mirror Tafkekan gaske Jerin tsadaddun turarurrukane ne asaman shi da sauran kayan gyaran jiki, idan nace zan cigaba da zayyana haɗuwar Ɗakin dattijon arziki tabbas zamu ƙare takun tsakiya wurin fasalta Kyawunshi. Yana daga kishingiɗe saman lallausar mattress ɗin gadon, Apple laptop ce agaban shi, Da alama Video call Ya ke yi da wani, ɗabi’arsa ce yana magana yana shafa gemun shi wani sa’in har Jan shi ya ke yi. Hajiya saratu tayi zaman cin tuwo saman lallausan carpet ɗin gaban gadon shi, tana jiran Ya kammala Yin wayar, ta tsare shi da ido babu annuri akan fuskarta, Hankalin shi gaba ɗaya yana akan fuskarta, Nazarin yanayinta ya ke yi, kamar daga sama ta tsinkayi muryar shi akanta “Saratu kin wuni lafiya”? Ƙara tamke fuskarta tayi”lafiyalou baba, fatan na same ku lafiya” murmushin gefen fuska ya sakar mata”Alhamdulillah, in ce ko lafiya? Naga yanayin fuskarki da 6acin rai, Waye ya ta6amin autata ne yanzu in ɗaura ɗamarar yin yaƙi da shi” murmushin Yaƙe ta ƙaƙalo, har ta buɗe baki zatayi magana yai saurin tarar numfashinta”nasan kinzo gaishe da baban nakine kamar yadda kika saba, Naji daɗi sosai mamana, Bari na kira hajjaty A waya ta kawo mana dinner mu ci atare ni da autana” tur6une fuska Hajiya saratu tayi”ba yunwa nake ji ba, Zuwa nayi mu yi magana, kafin barina ɗaki sai da nayi magana da masu aiki nasan sun kai min a ɗakina” “Ai nasan ba yunwa kike ji ba, Ni nake ra’ayin cin abinci tare da ke, idan mun kammala sai mu yi magana” aruɗe take kallonshi, ƙiri ƙiri Ya hana tayi magana. Ba tare da ya jira amsarta ba, Ya ɗauki waya dake saman bedside drawer, Ya kira landline na kitchen, bugu uku aka ɗaga kiran, muryar sophia ce ta ratsa kunnansa cikin girmamawa ta gaishe da shi. “Ina buƙatar Dinner ɗina a shigo min da shi ɗaki yanzu” amsa mashi tayi da toh kafin yai rejecting call ɗin, idanuwanshi akan saratu da ta haɗe rai, kasa jurewa tayi don baƙaramin takura tayi ba hakan yasa ta soma magana ba tare da ta jiran umarninsa ba. “Baba ni gaskiya ba a kyautamin agidan nan, akan me za’a dinga kushe min ƴa’ƴana ana yabon na wasu, abun yana ƙona min rai bana jin daɗi, haba dan Allah wannan ba adalci bane, kuma ba girman Yaya Lateef bane da yaya mubarak su zauna suna faɗan maganganun marasa daɗi akan ƴa’ƴana, ni kaɗai ke ba’ason ya’ya na a family din nan ko dan saboda ban auri jinsin mu bane” Rai a6ace take yin maganar, tun da ta fara magana bai dakatar da ita ba, ya natsu yana sauraronta idonshi akan fuskarta, dama tun kafin ta fara yin maganar yasan meya kawo ta, Yana mamakin Halin saratu, ko irin alkunyar nan babu, idonta ya rufe akan ƴa’ƴa da miji, abu ɗayane take jin nauyin yi wato idan tana zazzaga masifa bata bari su haɗa ido dashi, murmushine akan tausasan la66ansa “Kin gama maganar ko akwai saura” bata ɗago ta kalle shi ba idonta na akan carpet ɗin da take a zaune dirshan “Hateem Faɗa min menene sunan macan da take ɗaukar zigar miji”? ras taji gabanta yai mugun faɗuwa, A ruɗe ta ɗago da ido tana kallon fuskar obinna, ƙayataccen murmushine akan fuskarshi, Ji take tamkar ta yunƙura ta miƙe ta zuba da gudu don ta fahimci Video call yake yi da Yayanta hateem na ƙasar Canada, Hakan na nufin duk wata magana da ta ke faɗama babansu akan kunnanshi, Hankalinta ya tashi don ba ƙaramin jin shakkar shi ta ke Yi ba, duk acikin yayunta tafi fargabar sharafudden da hateem. A hankali Obie Ya juya mata Lapton ɗin gabanshi don suyi magana da Yayanta, sunnar dakai ƙasa tayi sam ta kasa ɗagowa ta kalli screen ɗin laptop nasa Daddaɗar muryar prime minister Hateem ce ta ratsa kunnuwanta “Ji ra kike in gaishe ki”? Girgiza kai tayi tamkar tana agabanshi, cikin girmamawa ta soma gaishe da shi “Ina wuni Yayana, Ya aiki Ya iyali” “Ki ɗago da ido ki kalle ni Saratu”! Da kakkausar Murya ya furta hakan, Yawu ta haɗiya kafin A hankali kamar maijin tsoro ta saci kallon screen ɗin. Tabarakallahu ahsanun khalikin!! Ni kaina da nake rubutawa sai da alƙalamina ya girgiza da ganin Kyakkyawar surar nan mai cikar kamala, gwarzon namiji jajirtacce, kallon ɗaya zaka Yiwa fuskarshi ka shaida Jinin Obinna ne, Yana ɗaya daga Cikin waɗanda su ke kama da babansu, basu baro komai nashi ba, Kyanshi, ɗabi’unsa da halayansa, Fatarshi kaɗai abun kallo ce, yadda kasan da ruwan madara ake mulketa saboda tsabar kyau, skin colour ɗinshi launin na mahafinshi ne, A zaune yake Cikin Katafaren Office ɗinsa dake a Presidential residence Na ƙasar Canada, tsayawa zayyana kyawun Office ɗin da dukiyar da aka kashe masa wurin zuba kayan cikinsa abune da hankali ba zai ɗauka ba, wata’ƙil zamu ƙare Takun tsakiyane wurin zayyana shi, wasu hadaddun tailored suit ne a jikinsa sunbi shape ɗin jikinsa, mutumin akwai ƙira. “Bai kamata kiji kunyar haɗa ido dani ba Saratu, tunda har kika iya tako ƙafafuwanki kika zo ɗakin baba don kiyi mashi masifa, Ke ko kunya bakya ji? Ki zauna Miji Yana ziga ki Kan ƴan uwanki? Sara Ba haka nasanki ba, Ni ba haka ƙanwata take ba, jarumar macace mai hankali da tunani, why kike son bani Kunya”? Maganar Hateem tayi matuƙar sanyata jin kunya, duk sai ta ji haushin kanta ya kamata, tayi danasanin zuwa ɗakin obinna, saboda tana matuƙar jin nauyin Hateem, da ace tasan da shi suke yin video call da batayi gigin zuwa kawo ƙorafi ba. “Kiyiwa kanki faɗa saratu, Ba girmanki bane, Ƴa’ƴanki ai namu ne, babu wani banbanci, nasan abunda Yaya mubarak da Yaya lafeef zasu faɗi bazai wuci akan Cigaban Ƴa’ƴanki bane, maisonka shike faɗa maka gaskiya duk min ɗacin ta, Maƙiyinka kuwa sai dai Ya 6oye maka yakamata Kiyi tunani ƙanwata” Cikin kwantar da murya yake yi mata nasiha, shi kanshi Obinna har lumshe ido yake yi saboda jin daɗin nasihar da Hateem Yake yiwa ƙanwarshi, kuma ga dukkan alamu jikinta yayi sanyi sosai Muryarta tamkar zata fashe da kuka ta soma magana”In sha Allah yaya zan kiyaye, bazan ƙara biye mashi ba, zuciya ce ta ɗibe ni, Ni kaina nasani kuna son ƴa’ƴana shiyasa kuke yi masu faɗa don su gyara, duk wanda ya rasa faɗi a duniya yai asara, ina jin daɗin ƙoƙarinku akaina da ƴa’ƴana, Allah ne kaɗai zai Iya biyanku” idanuwanta har sun cicciko da ƙwalla “Kada ki bari hawayen nan su zuba, Kinsan banaso ko”? Ɗaga mashi kai tayi alamar eh”Okey yi min murmushin nan naki in gani” Dariyace ta kubce mata, da sauri ta ɗaura kanta saman manyan laps ɗinta “Ya aikin naki? Fatan komai na tafiya lafiya” amsa mashi tayi da”lafiyalou” Jinjina kai Hateem yai”Allah ya taimaka” sallama sukayi da ita Obie Ya juya laptop ɗin, idon shi akan Hateem “Shiyasa nake Ƙaunarku, Saboda ku ɗin na dabanne, ƴa’ƴana abun alfaharina, Allah Yabar munku, ubangiji Allah ya tsare mun ku Ya kare munku daga sharrin maƙiya da mahassada......”addu’o’i obinna yadinga jero mashi, Yana masa mashi da ameen ameen hada saratu wurin amsawa daga bisani Suka yi sallama dashi Rufe laptop ɗin yai tare da miƙe ma saratu, Yunƙurawa tayi tare da matsawa gaban gadon ta kar6i laptop ɗin ta nufi saman desk ɗinta ta ɗaurata. “Assalamu akaikum” muryar Hajjaty ce ta ratsa kunnuwan su, atare suka amsa mata da wa’alaikum salam shigo daga Ciki, Tura ƙofar tayi kamar kullum fararen Kayane a jikinta, Tasha uban ado kamar amarya, sam bata gaji da ca6a ado, Hannayenta sun sha ƙunshi na jan lalle. Hajiya saratu dake a tsaye tana kallonta, Haushin Matar take ji, ta tsani taga ƴar aiki tana ɗaukar wanka kamar yar masu gida, zuciya da saƙe saƙe, sai ta dinga ganin kamar obinna bin jikinta yake yi da kallo, fargabanta kada wata rana dattijonsu ya ƙyasa, Ƙarasawa Hajjaty tayi cikin ɗakin Asaman Carpet ta ɗaura tray ɗin, sai faman sakar mashi murmushi take yi shima ɗin mayar mata da martanin murmushin yake yi, Hankalin Hajiya saratu yaƙi kwanciya Tana a tsaye ta ruke qugunta “Yalla6ai fatan ka wuni lafiya, tun ɗazu nake jiran shigowarka gidan bansan kun dawo daga masallaci ba, ae da tuni na jima da kawo maka abinci” Yanayin yadda take magana muryarta tamkar ana busa sarewa, ƙamshin turarenta Ya addabi hancin hajiya saratu Lumshe ido yai kafin ya amsa mata da”lafiyalou Alhamdulillah, nagode da kulawarki agareni, Kina ji da dattijon nan naki sosai nima na yaba da hakan” Fuskar Hajiya saratu a ɗaure ta furta”ke! Tashi kibar ɗakin nan tunda kin kawo mashi abincin,ya gode sai anjima” miƙewa Hajjaty tayi tare da jiyawa ta kalleta”Ina wuni hajiya” “Da ban wuni ba kin ganni, Ƴar rainin wayau sai yanzu kikasan dani aɗakin, dallah ni zo ki fuce waje” jikin Hajjaty yai sanyi duk sai ta ji ba daɗi “Inaso zan zuba mashi abincin....” tunkan ta ƙarasa Hajiya saratu ta daka mata tsawa”Nace ki fita ko”? Matsawa tayi tare da fusgo hannun Hajjaty taja ta waje, Obinna dake a kishingiɗe saman gadon ƙayataccen murmushine akan fuskarshi, lamarin saratu sai addu’a ya fahimci kishin mahaifin nata takeyi. Bayan fitarsu daga ɗakin, a bakin ƙofar suka tsaya da tafiya, Hajiya saratu na faman ciccije le6e ta furta”Ni ban yadda dake ba, akan me zaki dinga zuwa ɗakin Ubanmu, balallaga dake Ina laifin Ki turo matasan ƴan matan masu aikin su dinga yi mashi hidima”? Idanuwan hajjaty tuni sun cicciko tab da ƙwalla, ta tsani faɗan hajiya saratu, a shekaru kusan tsaran junane amma ta tasata gaba tanayi mata faɗa kamar wata ƙanwarta “Ai shine ya za6eni bani nake kawo kaina ba, Yafi so ina yi mashi hidima, kuma ki tambaye shi zai fada maki hakan” Harara Hajiya saratu ta watsa mata”ae dole ya za6e ki, tun da kin riga kin asirce shi da wannan munafukin turaren naki, mace sai kace karuwa, Kin bi jiki duk kin feshe da turare Bakisan haramin bane mace ta fesa turare mai ƙarfi ba? Ina laifin wanda zaki ɗan matsa a hammata!” yawu hajjaty ta haɗiya batare da tace mata komai ba “Idiot, daga yau karki kuskura In ƙara ganin Kin a ɗaki babanmu, tun fil azal ni baki kwanta min araina ba, Ina raga maki ne saboda mijina ba dan haka ba wlh da tuni na jima da korarki can ƙauyanku na can india, A tsawace takai ƙarshen maganar tare da ingiza hajjaty, tai taga taga zata faɗi daƙyar ta samu ta dafe bango, dogon tsoki Hajiya saratu ta buga kafin Ta juya ta koma ɗakin obinna. Jiki asanyaye hajjaty ke tafiya yayin da hawaye ke bin fuskarta, Da mayafin hannunta take share ƙwallar dake sintiri saman kuncinta, Kalaman Hajiya saratu sun ƙona mata rai. Tun fitar Hajiya saratu daga ɗakinta, Pravin Yana zaune gefen gadon shi, Shi da Tagwayensa zayn da zayn, suna zaune saman sofa, ransu ya 6aci matuƙa babu annuri akan fuskokinsu “Yanzu me kuke so ayi”! ya jefa masu tambaya yana mai kallon fuskokinsu “Ka sama mana hanyar da zamu bar ƙasar nan, saboda mun gaji da zaman gidan nan, a takure muke kowa baya son mu kusan kullum ne sai anyi mana Gori” murmushin gefen fuska Pravin ya ɗan saki Yana duban ya’yan nashi cikin so da ƙauna “Kun bani Kunya wlh, Why maganar mutane zata dame ku? Har wani ya isa yasa kubar Danginku? Kenan wata rana zaku Iya kashe kanku saboda wani ya 6ata maku rai eye”! ɗaure mashi fuska suka yi don sun fahimci uban nasu babu zuciya a ƙirjinsa, shiyasa bai ganin illar abunda ake yi masu, yafi so su zama masu matattar zuciya irin shi “Daddy pls, ka fahimce mu, bama jin daɗin zama gidan nan, america muke son komawa da zama” girgiza kai pravin yai”bazaiyiwu ba, ai baku keda kanku ba, Nima ina buƙatar ku atare dani, Ku faɗi wani abun na daban da kuke so zan iya yi maku shi” magiya suka dinga yi mashi akan ya amince masu su koma america, “Daddy bafa da kuɗinka xaka ɗauki ɗawainiyarmu ba, munsan komai kakeso mommy zata yi maka taimakonmu kawai zakayi mu samu ta amince mana” Ɗaure fuskarshi yai”saboda ni bani da arziƙin da zan Iya ɗaukar nauyinku”? Girgiza kai sukayi atare Ta6e la66ansa yai”bansan me kuka ɗauke ni ba, Ita kanta mahaifiyar taku A yanzu bata kama ƙafata wurin arziƙi ba,” kallon Juna su ka yi da mamaki akan fuskokinsu Miƙewa yai daga gefen gadon Ya nufi gaban drawer chest, Ya buɗe ya zaro atm card, dawowa yai ya zauna yana fuskantarsu “Banyi maku Iyaka da kuɗin dake acikin acct bank ɗina ba, don nasan har abada bazaku Iya ƙarar da su ba, a duk lokacin da kukeso zaku Iya cirar kuɗi ku biya buƙatunku, sannan kuje ƙasar da kuke so, Farin Cikinku shine nawa” Kallon da suke yi mashi kamar basu yarda da maganarshi ba, saboda sun raina arziƙinsa, Still murmushine akan fuskarshi yace”baku yadda da mahaifinku ba ko”? Shiru basu tanka mashi ba, Aransu suna ayyana may be babu ko sisi a atm ɗin, idan ma akwai kudi to Na mommynsu ne tunda ita ke da kuɗi. Miƙa hannu pravin yai tare da ruƙo wayarshi dake a gefenshi, kamar sakarkaru haka suka tsare shi da ido suna kallon shi, Daddana wayar yayi kafin Ya miƙa masu da sauri Zayn ya kar6i wayar Suka haɗa ido suna kallon screen ɗin wayar, Total balance ne na kudin dake a acct bank dinsa, tsabar firgita har saida suka ɗan zabura ganin millions of dollars, wanda a kuɗin nigeria Billions ne. Aruɗe suka haɗa baki wurin furta”Daddy Numbobi ne waɗannan ko kuwa kuɗin ne dagaske” dariya ya sakar masu “Abunda idanuwanku suka nuna maku, Just ku ɗauki atm ɗin zan tura maku pin ɗinsa ta text message,” lamarin yai mugun ɗaure masu kai, Girgiza kai Zayn yai”a’a daddy kuɗin sunyi mana yawa, ni tsorona ma kada ace Na mommy ne” Miƙa mashi wayar yai “Idan har kuka bari na kar6i atm ɗin nan kada ku ta6a tsammanin zan taimaka maku!” Kallon Juna sukayi zuciya na azalzalarsu akan su kar6i atm din suyi sharholiyarsu “Zayn mu kar6a ko”? Girgiza kai zayn yai”A’a zaid kuɗin mommyne fa, idan muka ta6a zata gane ni dai ban goyi bayan hakan ba” “Pls zayn tun da daddy ne ya bamu just mu kar6a kawai” “No zaid, kuɗin sunyi yawa zasu sa mu shagala mu daina yin sallah ne” Pravin dake kallonsu ba ƙaramin dariya suka bashi ba. “Har yanzu akwai ƙuruciya atattare daku, kuɗin kuke gudu? Ai nayi tunanin idan na baku jiki na rawa zaku kar6a, ban ta6a tunanin kuna da zuciyar Imani akan kuɗi ba, Sam baku da haɗama, Ga dama ta samu amma kuna ƙoƙarin yin watsi da ita”! Muryar zayn na rawa ya furta”Daddy zamuyi shawara tsakaninmu, ka ajiye mana atm ɗin zamu kar6a” jiki na rawa ya ruƙo hannun Zaid suka fuce daga ɗakin. Ajiyar zuciya ya sauke tare da miƙewa Ya maida atm ɗin inda ya ɗaukosa, komawa yai gefen gadon ya zauna yana cin abincin Da abla ta kawoma Hajiya saratu *Dr.Jazz* Tun zuwa shi gidan Mommynsa ta ke ta faman tarairayarsa tamkar ƙaramin yaro, Yana daga kishingiɗine saman doguwar sofa ya ɗaura kanshi saman laps ɗinsa, Sai zuba mata shagwa6a yake yi, yatsun Hannayenta na acikin sumar kanshi Tana yi mashi susa Mahaifiyar Dr.Jazz Baturiyar ƙasar England ce, sunanta na asali Harriet, Silar zuwanta aikatau gidan ta musulunta suka canza mata suna zuwa khadija amma sunfi kiranta da Turai, Farace jawur tana da jiki bata da tsayi launin idonta green ne, sumar kanta launin blonde, A yanzu ba matsayin mai aiki take ba, Matace awurin Sir mubarak, Ya daɗe da auranta tun Bayan rasuwar matarshi Hajiya naja’at, Ƴa’ƴan shi biyu da uwar gidansa gaba ɗayansu ba mazauna Nigeria bane, Suna a ƙasar canada suna kula da Babban companynsu tare da sauran ƴan uwansu dake zaune agidan Hateem. Turkish dress ne a jikinta, Riga da wando launin red colour, Ta ɗaura satin scarve asaman wuyanta, ta zubo da gashin kanta har gadon baya, Allah yayita da ruwan kyau. “Jazz sai nake ganin kamar baka yi kewata ba, Meyasa bakasan zuwa ganina? kullum Sai in ni na shiga gida nake samun damar ganinka idan naci sa’a baka tafi aiki ba. Fararen idanuwanshi ya daura akan fuskarta, “Mommy ba haka bane, Ni just banason haɗuwa da daddyne, ya cika faɗa, kuma sharri yake yi min yana cewa wai ni mata maza ne, Fisabilillah” “Ya faɗi hakanne donka Gyara rayuwarka, ni kaina ina mamakin shagwa6arka sai kace wani yaron goye, komai naka irin na mata” Ɗaure mata fuska yai”mommy kina goyan bayansa kenan, yaci gaba da kira na mata maza”? Girgiza mashi kai tai”A’a, Ai nafi kowa jin haushin inji ya kiraka da hakan, Yana ta6a min zuciyana, donni nasan namiji na haifa ba maca ba” murmushi Jazz Ya saki”to kice mashi ya daina” “Zan buga mashi warning, kada ka damuwa” maƙe mata kafadai yai”Allah mommy ni nasani wasa kikeyi, saboda ke kanki shakkarshi kike ji ba zaki Iya buɗe baki ki yi mashi magana akan ya daina ba” Jan kumatunshi tayi da hannunta In jiwa ya faɗa maka! Ni bana jin tsoronshi awaja ne mutane ke jin shakkarshi, da zarar ya shigo nake juya shi son raina, Har girki yana yi min” Baki asake Jazz ke kallonta “Uncle mubarak ɗin”! Jinjina masa kai ta yi”ƙwarai kuwa, ae dukkan Namiji bawan matane, Har ya buɗe baki zai ƙara magana, Wayar Aljihun wandonshi ta soma ruri, miƙewa yai da sauri ya curo wayar, bayan ya duba sunan mai kiran nashi ya ɗago tare da kallon mommynsa, Wanene ya kira”? Bai amsa mata ba sai dai ya sakar mata murmushi, da sauri Ya fito daga falon gidan, Kamar wani munafuki duk faɗin gidan bai isheshi ba sai da ya shiga garden tukunna ya dakata da yin tafiyar, Yai picking call ɗin jiki na rawa ya kara ta akan kunnansa, Kirari ya soma yiwa wanda ya kira shi wayar tamkar maroƙi, “Yalla6ai Kajin nan suna nan cikin ƙoshin Lafiya, Suna samun kyakkyawar kulawa yadda ya dace,” dakatawa ya ɗanyi da yin maganar, yana sauraron muryar mai magana, “Ana basu hatsi yalla6ai mai rai da lafiya, Yanzu haka idan nagama magana da mama zan tafi gidan gona domin duba lafiyarsu,” sai faman sakin murmushi yake yi, aladabce yake yin maganar ‘kasan kajin turawa saida hatsi mai kyau, Gaskiya basu da matsala yalla6ai, biyu daga cikinsu ne kaɗai suke neman gazawa, shi zakaran ciwon nashi Ya lafa, sauran Kajin muna nan muna basu kyakkyawar kulawa, in sha Allah zasu samu lafiya harma asamu nayin farfesun sallah” Tuntsirewa dr Jazz yai da dariya hada dafe ciki. duk wannan surutun da ya ke yi acikin waya baisan Sir Mubarak na tsaye abayanshi ba, daga shi sai gajeran wando, Da singlet fara, hannunshi ɗaya ruƙe da Cup na coffee Mamaki ne ƙarara akan fuskarshi Jin dr jazz na Zancan kajin turawa awaya “Okey toh, Zuwa anjima idan nashiga gidan Gonar zan Kiraka Awaya” Daga haka sukayi sallama, Juyawar da zaiyi karaf suka haɗa ido da sir mubarak, tuni yasha jinin jikinsa, Duƙar da kai ƙasa yai ido ya raina fata “Jazz! Dawa kake magana a waya? Kajin menene naji ana magana akai? Ni dai A iya sanina likitan mutane ne kai bana dabbobi ba” sosa ƙeya jazz yai, mirya dabarbarce yake faɗin”am...umm..dama “ Ya rasa ta ina zai taro zancen, Kallon tuhuma Sir mubarak ke jafa mashi hakan yasashi yin saurin fauzewa “daddy, Ni da abokina ne dr fawan muka buɗe gidan gona, kajin turawa ne muke kiwo, wasu ne babu lafiya shine ya kira muna tattaunawa game da yadda zamu shawo kan matsalar” Ajiyar zuciya Sir Mubarak Ya sauke”Okey, mu shiga gidan” yai maganar tare da miƙa mashi Cup din hannunsa, da sauri jazz Ya kar6a Yana sha atare suka nufi gidan sai faman sauke ajiyar zuciya yake yi. *GIDAN ƊAN IYA* Mahboob ne ke ta faman zuba sauri Yana tunkarar harabar ajiye motocin su, ya ɗauki wankan shadda, tunkan Ya ƙarasa idonshi ya sauka akan motar Uncle abdallah, ƙura ido yai yana kallon bayan motar sunanta Ya karanta, Aranshi Ya ayyana lallai mutanan nan ba ƙananun shaggu bane wannan mota haka mai tsada! saboda almubazzaranci da rashin sanin ciwon kuɗi, Ina laifin ko ƴar ƙaramar honda mutun ya saya ya wadatar, mutane sun ɗaurewa ƙaryar arziƙi wurin zama, Allah dai ya shirya mu, ae ni wlh ko nayi arziƙi ban Iya fidda kuɗina in sayi mota, na ƙwammace duk inda zanje in taka da ƙafata, idan ma da nisa ne ƙwara in biya kuɗi In hau motar Haya, Ita ma wannan motar da nake amfani da ita ba don babansu abokina ne ya bani kyautarta ba kuma ina ganin mutuncin shi saboda ya ji tausayina ya siyamin ganin ina hawa motar haya yasin da tuni na jima da siyar da ita’ Shi kaɗai ya ke yin sambatunsa, Har ya ƙarasa gaban motarshi Ya buɗe front seat Ya shiga Ciki Yana ƴan dube dube, da alama wani abu yake nema, saƙo da lungu na motar yake ta bincikawa, har ƙarkashin seat, tuni ya haɗa uban gumi. “Ina na ajiye zoben nan Jiya? Ko dai ban shigo da shi mota bane? fuskarshi a hautsine Ya jefawa kanshi tambayar, zurfin tunani ya shiga yi still bai tunano inda ya ajiye shi ba, A ƙarshe Ya soma tunanin kodai Ya shigar da shi ɗaki ne, Fitowa yai daga cikin motar Ya datse murfin, Jiki na 6ari ya nufi cikin gidan. Abie da Uncle ɗan Iya ne zaune a saman sofas na palourn tare da Uncle abdallah, Sun nutsa suna tattaunawa dangane da 6acewarsu tajuddeen, Mahboob Ya faɗo falon Ko kallo basu ishe shi ba hankalin shi na akan zoben shi da bai gani ba. “Wancan ba mahboob bane? Kamar naso na wayi fuskarshi” Uncle abdalla ne yai maganar, Girgiza kai uncle ɗan Iya yayi Yayin da yake bin bayan mahboob dake ƙoƙarin karya kwana zai nufi sashen ɗakinsa “Shine, halan bai gaishe ka ba”? Murmushi ɗauke akan fuskar Uncle Abdalla yace”Tun da muka zo ban yi tozali da shi ba, sai dai naji labarin shi awurin junaid” Cikin nuna 6acin rai Ɗan Iya yace”baida wayau ne ai ni bansan baizo ya gaishe ka ba, bari ya fito daga ɗakin ɗan rainin wayau, Zahra tafi shi hankali” Abie yace”Ƙuruciyace ke damunshi, Zahra kuma ae tafi shi shekaru baza a haɗata da shi ba” Ɗan Iya yace”babu wata ƙuruciya atare da shi, Sarai yasan me yake yi sai girman jiki ba wayau” da alama Ranshi ya 6aci da rashin gaishe da uncle abdallah da baiyi ba. Kafin wani daga cikinsu ya ƙara yin magana Hajiya adama ta fito daga ɗaki hannunta ɗauke da baby junaid, tun da ya dawo daga school a wurinta ya wuni ya hanata sakat duk inda za ta je ƙafarta kafarshi toilet ne kaɗai yake bari ta shiga, Ta canza Kayan jikinta zuwa atampa riga da skirt, Ta yafa mayafi akanta, kafin ta ƙarasa shiga palourn Mamie ta fito daga ɗakin Ummi su biyu ganinta yasa suka nufi wurinta fuskokin kowannansu da fara’a suka soma gaisawa da junansu Atare suka ƙarasa shiga palourn, Kowa ya samu wuri ya zauna, Kafin suka fara gaishe da Mazajensu, miƙa ma junaid hannu uncle abdallah yai”zonan kyakkyawan Jikana mu gaisa,” da sauri Junaid ya sauko daga saman laps din Hajiya adama ya nufi sofa ɗin da uncle abdalla yake azaune Ya haye saman jikinshi yana faman sakar mashi murmushi, shafa fuskarshi yai da tafin hannunshi”Masha Allah mutumina, Ka tashi lafiya? Fadamin meyasa baka je school ba yau? Sannan baka bi mu zuwa masallacin Juma’a ba” Zaro ido Junaid yai haɗi da ɗan girgiza kanshi muryarshi da shagwa6e yace”nafa je, ae yau da wuri ake tada mu duk ranar juma’a, kuma ni ai ban isa zuwa masallaci ba inji mommy” maganarshi ba ƙaramin ƙayatar da su take yi ba, musamman In ya haɗa da shagwa6a, “Junaid kaji tsoron Allah, Aneelerh ce ta faɗa maka haka? Faɗamin gaskiya ka dai san me ƙarya ɗan wuta ne” jin haka yasa shi saurin sanya tafukan hannayenshi biyu ya toshe fuskarshi Yana tiƙar dariya” muryarshi ƙasa ƙasa ya furta”ba ita bane, ae malaminmu ne yace mu ƙananu ne bamu isa ɗaukar zunubi ba” gaba ɗaya suka saki dariya, bayan sun tsagaita da yin dariyar ne, Uncle ɗan Iya yai masu gyaran murya hakan yasa suka dawo da dubansu gare shi. “Dama yanzu nake shirin aikawa a kira mun ku, don mu haɗu duka muyi magana, Kafin mu shiga cikin zancen Ina ƙara yiwa baƙinmu barka da zuwa fatan kun wayi gari lafiya” da fara’a Hajiya adama ta amsa mashi a mutunce Mami tace”tun ɗazu da safe take son yin magana mun fara sai nace ta bari idan kuka dawo daga masallacin juma’a zaifi mu haɗu mu duka mu tattauna tunda abune daya shafi kowannanmu da buƙatar aji shawara daga bakin kowa” Jinjina kai Abie yai”hakane, Yanzu Ina aneelerhn take”? “Tana a ɗakin zahra, Bari na shiga na kirata” kafin ta mike muryar junaid ta katse mata hanzarinta. “Ni zan Kirata” Bai jira amsarta ba, Ya sauko da gudu Ya nufi Ɗakinsu, uncle abdallah ne ya ɗan ɗaga murya yana yi mashi faɗan ya daina gudu kada ya faɗi yaji ciwo, Jin haka yasa shi dakatawa da yin gudun ya soma yin tafiya a tsanake A lokacin Aneelerh da Zahra suna zaune saman gado kowa ya dafi waya suna fira suna chatting, sun ɗauki wankan dogayen riguna “Ba zaki leƙa wurin surukar taki ba? Kin barta a ɗaki ita kaɗai” acewar zahra “Ɗazu da safe na shiga na gaishe ta, har ma na tarar da mami zaune suna tattaunawa shiyasa ban tsaya ba,” “Gaskiya aneelerh ki godewa Allah, surukarki tana da mutunci ta iya magana ga faran faran da jama’a, Ni wlh ba ƙaramin burgeni take yi ba, Inasonta sosai, da ace tana da wani ɗan Bayan Yaya uzair Allah dana aure shi” har cikin zuciyarta take yin maganar, Aneelerh na murmushi tace”Chief Owais din fa? Ko kin fasa”! farfari Zahra Tayi mata da ido “shi wannan na dabanne, idan ana maganar ƙarauƙarau ba a maganar Zinari, My dream man inaji araina ma ya kusa dawowa ƙasar jiya har mafarkinsa nayi” Murmushin gefen fuska Aneelerh ta saki “Allah Ya cika maki burinki zahra, Ni na ƙosa inga fuskar Owais ɗin nan, har tambayarki nayi hotonsa kinƙi ki nuna min, bansani ba ko rowa kike yi min” dariya Zahra tayi”Ina jin fargabar zuciyarki ta buga silar ganin kyakkyawar fuskarshi, kuma kinga ke matar aure ce bana son ki kalli haramun” Sakin baki aneelerh tayi yayin da take kallonta, tama rasa bakin magana “Fuskarshi tsadane da ita, idan har zaki Iya biyan farashi sai muyi ciniki in nuna maki” fashewa da dariya aneeleeh tayi jin wani zancen abakin zahra. Faɗowa Ɗakin Junaid yai tun abakin ƙofa yake faman ƙwala mata kira”Mommy!mommy!” a hanzarce ta kai idonta ga ƙofar “Babyn mommy lafiya kake ta ƙwalamun kira” tai maganar tare da sakowa daga saman gadon ta nufe shi, hannu biyi tasa ta ɗauke shi tana kallon fuskarshi “Mommy ana kiranki, ki zo inji su abie” “Sune sukace ka kira ni”? Ɗaga mta kai yai alamar eh ya ƙara da cewa”ke kaɗai banda Zahra” Harara zahra Ta wurga mashi”aiko sai naje ɗan baƙin ciki, so kake kayi mun buƙulu wata’ƙil ƙudi ne za’a raba mana, Saukowa tai daga saman gadon ta ɗauko masu mayafi a closet ita da Aneelerh ta yafa mata akanta, atare suka fuce daga ɗakin zuwa palour Hankalin Mahboob Ba ƙaramin tashi yai ba, ganin babu zoben a ɗaki, duk yabi ya birkice ɗakin, ya tarwatsa komai, Hatta zanin gadon shi da fululluka duka yayi wurgar dasu saman tiles, ya zazzago da jerin ninkakkun kayansa na cikin wardrobe kaf dinsu Ya bazasu saman gadonshi, zufa ta ko’ina, Bawan Allah shine har ƙarkashin gado neman zobe, Cikin drawer chest, da laundry basket, kanshi harya fara yi mashi ciwo, ya tsani asara a rayuwarshi, a haukace ya tura ƙofar toilet dinsa ya shiga ciki Yana neman zoben, gaba ɗaya ya fara zaucewa, ganin babu zoben a toilet ɗin ya dawo ɗakin, yana haki zufa sai tsastsafo mashi take Yi, Idanuwanshi sunyi jawur dasu luhu luhu yakai maƙura tamkar zai rushe da kuka, jiri ne ya fara ɗibarshi a hanzarce ya koma gefen gadon shi ya zauna tare da sanya hannayenshi biyu ya tarbe kanshi Takaicin duniya ya ishe shi, bakomai yake tunawa ba face kuɗin da Aka sayi zoben, har zazza6i yai daya miƙa su dubu goma sha biyar. Ahakama kuɗin bada guminsa ya same su ba, Abokin shi ne ya siya mashi zoben saboda ya nuna yana so kuma baida kuɗi. *Boss Bature✍️ Mu haɗu monday Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*KURKUKUN ƘADDARA*_ ~Middle step~ _The Prisoners E16🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* Kusan a tare Aneelerh da zahra su ka shigo palourn, a saman carpet kowan nan su yai zaman cin tuwo Junaid na azaune gefenta, tun da su ka zauna idanuwan su Mami da Abie na akan su, at same time suka haɗa baki wurin gaishe dasu cikin girmamawa, fuskokinsu Uncle abdallah da fara’a suka amsa masu. Bayan kowan nan su Ya natsu, Hajiya adama ta soma magana cikin nutsastsiyar murya “Dama jiyane Aneelerh ta ke faɗamin dangane da tada zancen 6acewarsu tajuddeen da za’ayi, a gaskiya naji daɗin jin hakan sosai, Kuma na yabama zahra da ta kawo wannan shawarar ta yi tunani mai kyau” Tun da ta fara magana sun natsu suna sauraronta, Zahra sai faman washe baki take yi jin anyabi shawararta, tana matuƙar son taga An yabeta. Bayan Hajiya adama ta ƙare magana Uncle abdallah Ya ɗaura da cewa”yanzu haka abun da mu ke tattaunawa akai kenan, Ni kaina Naji daɗin tunanin nan da akayi abune mai kyau da buƙatar atada zancen 6acewar su ya dawo sabo, wata’ƙil ta silar hakan Allah ya agaza mana Muji ɗuriyarsu duk da bamu da tabbacin ko suna araye don ni har yau bana ji araina cewa babu su a doron duniyar nan!” Numfasawa Abie Yai Kafin ya ɗaura da nashi jawabin”In sha Allahu muna sa ran wannan Karan zamuci nasara, dama dalilin taruwar mu anan don kowa Ya bada tashi shawarar” Bayan Kammala Maganar abie, Uncle ɗan Iya Ya soma magana “Na riga nayi magana da Ziyad babban ɗan jarida ne, Tun ranar da muka Yi magana da Aneelerh, ta turo min hotunansu already na tura mashi su, da duk wasu bayanai da za’a buƙata, Ya ce min in sha Allah cikin weekend da zamu shiga komai za’a fara yaɗa labarinsu” Murmushine Ya bayyana akan fuskokinsu da alama sun ji daɗin Jin hakan Uncle abdalla yace”Wai kana Nufin Ziyad ɗan Gidan senate Lateef”? Jinjina kai Uncle ɗan Iya yayi”ƙwarai kuwa, Ziyad yanzu ae shi ke jan Ragamar Companynsu Na jarida mai suna Obinna News Network (ONT) Yaron Akwai hazaƙa Kullum ne saina bibiyi Labaransu a shafinsu, ƙwararrune a 6angaren Aikin Jarida, duk wani labari da zaiyi trending a social media Sune na farko da zasu fara buga shi a shafinsu” Uncle abdalla Yace”Allah sarki, Uzair Da tajuddeen Sunci burin yin Aiki a companynsu, suna son Yin aiki tare da Ziyad Allah bai nufa ba” cikin karyayyiyar Murya Uncle abdallah ya ƙarasa maganar, jikin kowan nan su Yai sanyi “Nima a bakin uzair na ta6a jin labarin Ziyad ɗin nan shahararran ɗan Jarida, “ Acewar Hajiya adama Uncle ɗan Iya na murmushi yace”Allah sarki, ae muna mutunci da Iyayensu, lokacin da ace nasan suna da burin yin aiki da shi ai dana haɗasu, Yadda Taj da uzair suke da hazaƙa a 6angaren Jarida tabbas da suna atare ba ƙaramin Cigaba za’a samu a ƙasar nan ba, don shima Ziyad ɗin Akwai ƙwalwa Bashi da tsoro gaskiya tsirararta yake faɗin ta” murmushi kowannan su Ya saki. “Yakamata ka gayyato mana shi agidan nan, tunda kowa nasan ganin shi, Ko da ya ke nasan zaiyi wuya ya iya samun lokacin zuwa sai dai mu muje inda Yake” Abie ne yai maganar “In dai ziyad ne baku da matsala, mutunne mai sauƙin kai, zan Gayyace zuwa gidan nan” Tun da suka fara magana sai Yanzu ummi tasa baki”kaga daga nan Idan Yazo sai mu bashi auran zahra....” tunkan ta ƙarasa magana zahra dake chatting da wayarta A sukwane ta ɗago Girarta a haɗe tana kallon fuskar mami. Hakan da ta yi ba ƙaramin dariya ya basu ba, Uncle ɗan Iya yace”kin kawo shawara mai kyau, Ni kaina nayi tunanin hakan don yaron akwai farin Jinin ƴan mata ita kanta zahra nasan zata ƙyasa” Kifa kai zahra tayi saman cinyoyinta, takaicin Duniya ya isheta, ita da ta ke da burin mallakar Uban gayyar family ɗin su kuma suna yi mata zancen Ziyad. “Akwai Kyauta ta musamman da zan ba Aneelerh, nasan Itama zata taimaka mana sosai” Hajiya adama ce ta yi maganar idonta Akan uncle abdallah. “Na baro ta a mota, jiya na manta ban shigo da ita gidan ba, Bari naje na ɗauko” yai maganar yana yunƙurin miƙewa Sai ga Mahboob Kamar an wurgoshi Rai a6ace yake Tafiya Fuskar shi a haɗe babu mutunci. “Ka koma ka zauna Ga mahboob nan, ka bashi key ɗin motar ya ɗauko maka” Karaf acikin kunnanshi Maganar ta sauka, Har ƙara sauri yake yi don yabar falon Ɗaga murya Uncle ɗan Iya yai”Kai Mahboob zonan” Cak Ya tsaya da yin tafiyar fuskarshi A murtuke ya Juyo Ya nufi inda suke zazzaune saman sofa. Zuƙunnawa Yai ƙasa Ya ɗago da fuska Yana kallon Abie ɗin nasu Rai a6ace yace dashi”Mahboob ba ka ga munyi baƙi bane a gidan namu”? Hannu yasa ya ɗan sosa ƙeyarshi Muryarshi ƙasa ƙasa Ya furta “Bana Jin ɗaɗi jiya shiyasa ban samu damar zuwa ganin su ba,” Wani kallo Da Ummi ke wurga mashi daga inda take zaune saman Sofa kamar zata kifa masa mari, Hakan yasa shi yin sauri kallon Uncle Abdallah Ya furta”sannunku da zuwa, ya gajiyar tafiya, ya kuma aka baro mutanan can” fuskar uncle abdalla asake ya amsa mashi”lafiyalou Mahboob, ya school ko an kammala” fuskar shi ba yabo ba fallasa ya ce”diploma ce na kammala” Ganin yanayin fuskarshi babu walwala Uncle abdalla yace “Ko dai har yanzu ba lafiyane? Naga kamar baka acikin natsuwarka” Sai lokacin Ya ɗan sakin murmushin yaƙe “Bakomai, ai naji sauƙi” Iya abunda ya furta kenan, Baby Junaid ya tsareshi da ido, Dariya ce ƙumshe a cikin bakinshi don ya fahimci damuwar rashin zoban shi ce ta sanya shi shiga wannan halin, Cikin kunne yai ma Aneelerh raɗa”Mommy zoben yake nema, kalli idonshi ki gani sunyi jawur, Allah bani bashi mommy sai ya zubar da hawayensa” Ƙiris ya rage Aneelerh ta saki dariya yayin da take sauraron muryar junaid, ita kanta ta lura da 6acin ran da ke akan fuskar Mahboob. “zai baka Key ɗin mota, saƙo zaka ɗauko mashi” Fuska a ɗaure uncle ɗan Iya yai mashi maganar, tare da kallon uncle Abdalla “Bashi key ɗin motar,” acewar ɗan Iya, ciro key ɗin uncle abdallah yayi kafin ya miƙa ma Mahboob, Ya sanya hannu biyu ya kar6a. Yunƙurawa yai ya miƙe ya fuce daga ɗakin yana ƙunƙuni. Kafin dawowar Mahboob Junaid Ya miƙe da sauri Ya nufi ɗakin Mommyn shi don Ya duba zoben da su ka 6oye. Yana shiga ɗakin Ringing wayar Aneelerh Ya daki dodon kunnan shi, Da sauri ya nufi wayar dake Ajiye saman pillow Ya haye gadon ya janyo ta. Jikinshi har kerma yake yi wurin yin Picking call ɗin ya kara wayar a kunnanshi. Da ƙarfi Ya furta”Wanene”? Shiru ba”a tanka masa ba. Hakan baisa ya fasa yin maganar shi ba “Mommy bata nan tana a palour suna magana da su Abie, I’m the only one in the room.” still ba’a tanka mashi ba, Surutu Yaci gaba da Yi “Angel ce ke kira”? Shiru ba amsa”Sister Angel, say something! It’s your brother, Baby Junaid. I miss you so much” Da shagwa6a ya yi maganar, Sai lokacin Muryar mutumin da ya kira a wayar ta bayyana da sauti mai matuƙar Ratsa zuciya. “Where is the owner of the phone?” ta6e baki Junaid yai”ai na faɗa maka tana a palour” “Okey ina son yin magana da ita, ko zaka Iya kai mata wayar” Tuntsirewa Junaid Yai da dariya yana faɗin”a’a Sai dai ka yi magana dani, sai in faɗa mata” “Pls ka kai mata wayar, “ maƙe kafaɗa Junaid Yai kamar yana agabanshi”ni dai a’a, Ka faɗamin sai in faɗa mata saƙon” “Shekarunka nawa”? Ga dukkan alamu wanda ya kira wayar ya fahimci ƙaramin yaron ne ya ɗaga tun daga kan voice ɗinsa. “Huɗu Biyar shidda” Sautin dariyar mutumince ta ratsa kunnan junaid. “No wonder ashe babban mutun ne kai, zamu iya zama abokai” maƙe kafaɗa junaid yai”to aini yarone kai kuma babba”. “Okey yanzu faɗamin Ina yayarka Angel”? Kwa6e fuska junaid yai cikin muryar shagwa6a yace”ta 6ace 6era ya cinyeta ita da daddynta da daddyna sun mutu nima mommyna ta faɗa min” sosai mutumin Ya fashe da dariya, jin wautar Junaid “Ka hana Ni Yin magana da mommynka, gashi kanata cinye min kati” “Ae nace ka faɗamin saƙon sai In gaya mata” mutumin yace”Okey, ka faɗa mata DADDYN UNAISAH NE ya Kira”! “To zan faɗa mata Sai anjima” Yana kai ƙarshen magana Yai rejecting call ɗin tunkafin mutumin yai mashi sallama, Pillow Ya janyo ya zuge zip ɗin Ya curo ring box ɗin Yana Kallon zoben “Na Angel ne wannan, Bazan bashi ba Allah tun da ya cinye min chocolate ɗina” Yana magana yana ta6e la66ansa. Shigowa Mahboob Yai cikin palourn Hannun shi ruƙe da Kyautar wani abu Mai faɗi an rufe shi da wrap sheet mai Ƙyalƙyali, Karasowa Yai agaban sofas din da Uncle Abdallah Yake zaune Ya sauke gift ɗin kafin ya miƙa mashi key ɗin motar, Kar6a Uncle Abdalla yai”nagode sannu da ƙoƙari” muryarshi ƙasa ƙasa Ya amsa da”yawwa” Juyawa yai da sauri Ya nufi Sashen kitchen ganin Ana na zarya kai abinci a dining. Tunkafin a buɗe Kyautar kowa Ya ƙagara da son ganinta, musamman zahra ta ƙura idanuwanta kamar na mazuru. Ummi na murmushi tace”masha Allah wannan kyauta tunkafin abuɗe mun fara zumuɗin ganinta” Mami tace”ni kaina a ƙagare nake Allah” A hankali Uncle Abdallah Yake warware wrapping sheet ɗin, slowly Kyawawan idanuwanta dara dara suka Fara Bayyana, da mamaki su ke Kallon juna cikin rashin fahimtar wacece wannan Kyakkyawar Matashiyar. Lokacin da ya warwaro wrapping sheet ɗin dai dai Saitin hancinta ya ƙarasa 6an6are ledar gaba ɗayanta, adai dai time ɗin Mahboob da Ana sun fito daga kitchen Hannun shi ruƙe da glass Na lemu Karaf Idanuwanshi suka sauka akan Hoton zanan fuskar Angel, Nan take ya saki glass ɗin hannunshi gaba ɗaya ya tarwatse ruwan lemun dake acikinsa ya tsiyaye saman tiles. Tsabar Al’ajabi da mamakine Yasa Aneelerh da mami Yunƙurawa a sukwane suka miƙe tsaye Suna ƙare ma Zanan Kallo Yasha fenti kamar horonta aka ɗauka. Gaba ɗaya sun Rasa bakin magana, zanan yayi bala’en Yin kyau, fuskar Angel ta fito raɗau Kyakkyawar matashiyar balarabiya bugu da ƙari buzuwa a 6angaren Mahaifinta” Zahra Ko sai faman Yarfa hannu take yi tana ambaton Wow wow Tabarakallahu ahsanul khalikin! Gaskiya koma wanene portrait artist ɗin da ya zana hoton nan ba ƙaramin ƙwararre bane ya baje basira” Ummi tace”Masha Allah, Yarinyar ba ƙaramar kyakkyawa bace, kamar tajuddeen Ya yi kakinta, Kamanninta sak Kalar nashi, Hasken fatarne ta ɗauko Na mahaifiyarta benazir” Lamarin ya ɗaurewa Ana kai Ganin yadda Mahboob Ya fasa glass cup ko ajikin shi, Hankalin sam baya atare dashi, Zanan Fuskar Angel Ya tafi da Imaninsa, dama can tun fil azal Mahboob Mayen mata ne. “Mahboob Meke damunka ne? Baka ga 6arnar da ka yi ba ne’? Ba tare da ya kalli fuskar Ana ba Ya furta”dama akwai matan Hurul aini A duniya”? Girgiza kai Ana ta yi Fuskarta ɗauke da murmushi ta nufi dinning, don ta jera kayan tray din hannunta. Farin Ciki Ya hana Aneeleeh furta kalma, agaban zanan da ke a jingine jikin hannun sofa, ta zuƙunna saman gwiwowinta, yatsun hannayenta na kerma ta ɗaura su saman fuskar Angel, Lokaci ɗaya ta fashe da matsanancin kuka ta kifa kanta saman zanan “Haba Aneelerh menene abun kuka? Ke da za ki yi farin Ciki”? Mami ce tayi maganar Hajiya adama ta miƙe ta nufi Aneelerh ta ɗan ranƙwafa ta ɗaura hannunta saman kafaɗarta. “Share hawayen ki Aneelerh, banaso pls, Ni ban Kawo maki zanan nan don ki yi kuka ba, saboda farin Cikin ki yasa Nasa aka yi min shi, nasan zaki ji daɗi sosai” Abie yace”in dai ko bazaki daina kukan nan ba, zansa su koma da zanan” sai lokacin ta ɗago da rinannun idanuwanta da suka kaɗa jawur ta kalli fuskokinsu cikin shessheƙar kuka tace”Nadaina, wlh kukan farin cikine Ya kubce min, Inason Angel sosai, na kasa jurewa ne, da na ga zanan nan sai naji na ƙara ƙagara da son ganinta a shekarunta Na yanzu” Mayar da idanuwanta ta yi a kan hoton “Allah sarki my Angel, ɗiyata ƙanwata kuma ƙawata abokiyar firana, Na yi missing ɗinki sosai bazan ta6a mantawa dake ba har abada” Kifa kanta tayi saman hoton Hawaye suka cigaba da wanke fuskarta, ta yi matuƙar karya masu zuciya. *Middle step A gidan Alhaji ubaid* Tun lokacin da Dr. shureim Ya kammala kimtsawa ya zauna gefen gadon shi ya natsu yana kallon hotunan abar ƙaunarsa, Ƙarfe Goma sha Biyu Na bugawa, Kiran Alhaji musa Ya shigo wayarsa. Da sauri Yai picking call ɗin Ya kara a kunnanshi “Shureim Ina Jiran ka a palour!” Abun da Ya furta mashi kenan, Ajiyar zuciya ya sauke Tare da miƙewa Ya fito daga Bedroom ɗinsa, Yana mai jin kewar ɗakin nashi, tafiya yake yi tamkar bayason Taka ƙasa, Ji yake kamar In yabar gidan zai ƙara nisanta kanshi da ita ne, duk irin yadda yake zumuɗin barin gidan hakan bai hana wani sashe na zuciyarshi ƙin amince masa ba, Saboda acikin gidan ne, abar ƙaunarsa ta kafa tarihi acikin zuciyarshi. Lokacin da ya ƙaraso palourn, A zaune ya samu Alhaji musa da Uncle ubaid, Sai Mahaifiyarshi laila Da Mai aikin gidansu zainab, Hannunta ruƙe da shopping bag. Yanayin fuskokin su Ya nuna alamun rashin jin daɗin tafiyar shi, musamman mai aikin gidansu zainab da kuma Mahaifiyarshi Layla, tana a tsaye ta ruƙe qugu fuskarta babu annuri ko misƙala zarratin zallar 6acin raine. Shi ko Alhaji ubaid sai faman sakin fara’a ya ke yi babu alamun zaiyi kewar ɗan nashi idan ya tafi. Idanuwan dr. Shureim akan na mahaifiyarsa, da sauri ya nufi inda take atsaye, hannu biyu ta sanya ta rungumo shi a ƙirjinta, hakan da tayi mashine yasa shi jin hawaye sun cicciko idanuwanshi. Bubbuga bayanshi take yi a hankali tana faɗin”Shureim ɗina, zanyi missing ɗinka sosai, naji takaicin tafiyar nan duk da ba wani wuri zakaje me nisa ba, sai dai sam hankalina bai kwanta da tafiyarka ba, Naci burin In gatantaka In baka kulawa ta musamman tuntuni, sai dai rashin zamanka agida da kuma gudunmu da ka ke yi, shi yasa ban samu damar yin hakan ba, Yanzu kuma na samu na shawo kanka, an nuna anfini iko da kai za’a rabani da kai,’ tun da ta fara magana Alhaji musa Ya haɗe rai fuskarshi a tamke ba annuri, don yasan dashi take magana. “Mommy ki samin albarka ita nake buƙata daga gare ki, Sannan ki kwantar da hankalinki, Ni musulmine kuma nayi imani da Allah dashi na dogara, aduk inda zan kasance Allah yana atare dani, ballanta kuma agidan Uncle ɗina ne ba nisa zanyi ba, nasan za ku dinga zuwa akai akai kuna ganina, Nima kuma zan dinga zuwa gida” Maganar Dr. shureim ta yi matuƙar karya mata zuciya, Allah na gani tana son ɗanta sosai, Muryar Alhaji musa ce ta katse su”shureim bamu da isashen lokaci, ka wuce mu tafi” Ɗagowa Yai daga jikin mahaifiyarshi ido cikin ido suke kallon Juna, Canza harshe ta yi zuwa larabci kafin taci gaba da magana “Shurem hankalina bai kwanta da kawunka ba, Ni ban yarda dashi ba, Bai ta6a nuna damuwa akanka ba, tun lokacin da ƙaddarar nan ta risƙe ka har ka fara shaye shaye a ƙarshe ma kabar ƙasar gaba ɗaya, musa bai ta6a bibiyar rayuwarka ba, babu ruwanshi dakai Ƴa’ƴanshi kaɗai Ya sani, Ta ya ya hankalina zai kwanta da zuwan ka gidan shi? Allah kaɗai yasan mugun nufin shi akan ka” Tana magana tana shafa sumar kanshi da ta sauko saman wuyanshi, babu wanda Yasan me ta ke cewa, dama da biyu ta yi mashi maganar da larabci don saboda tasan basa Jin Yaren, mai aikinsu kaɗaice ta ke ji saboda itama balarabiyace, jikin zainab duk yai sanyi da jin maganar Hajiya layla, baiwar Allah duk ta damu da Shureim gani ta ke yi kamar idan ya tafi wani abu zai faru dashi. Muryarshi araunace Ya soma magana da harshen larabci”Mommy kidaina wannan tunanin dan Allah bana so, ki kwantar da hankalin ki, Uncle musa bazai Ta6a cutar dani ba, duk da bai damu dani ba a lokacin baya, yanzu ya nuna yana ƙaunata zai Iya yiwuwa ko dan saboda tausayin halin da nake aciki ne, Nafi so ki yi mashi kyakkyawan zato mommy” Gyaɗa kai ta yi “Shikenan shureim zan cigaba da yi maka addu’a akan Allah ya kare mun kai ya tsaremun kai daga sharrin duk wani abun cutarwa” Cikin harshen labaraci ta dinga jero addu’o’i tana tottafa masa Yana amsawa da ameen. Bayan ta kammala ya ɗago da ido Ya kalli zainab, idanuwanta sun cicciko tab da kwalla. Matsawa ya yi kusa da ita, fuskarshi ɗauke da murmushi yace”auntyna zan tafi asanyamin albarka” yai maganar tare da duƙar da kanshi, Hakan ba ƙaramin daɗi yayi mata ba, Ƴan hawayen da ta ke matsewa tuni sun soma shararowa saman kuncinta. Tafin hannunta ta ɗaura saman arab turban ɗin dake naɗe akanshi, a tsanake take jero addu’o’i tana tottofa masa a ƙarshe ta ƙara da cewa”Allah yasa Silar komawarka can ka samu farin Ciki na har abada” Ya amsa mata da ameen ameen”Allah ya saukeku lafiya shureim” ya ƙara amsa mata da ameen Daga Haka Ya juya ya nufi Mahaifinshi Alhaji Ubaid. Fuskarshi ɗauke da murmushi yake duban shureim”daddyna, asanya min albarka” Da buɗar bakin Alhaji ubaid sai cewa yai “Shureim sai ka ce zaka Bar ƙasar, irin wannan bankwana haka! Na lura Jikinka duk Yai sanyi, Ko kamanta Abuja ne zaka je gidan ƙanina”? Harara Hajiya layla ta jefa ma Alhaji ubaid a fakaice. “Lokacin da ka ke ƴan guje gujenka ba tare da sanin kowa ba, Ka ke barin ƙasar nan sai yau don zaka tafi gidan uncle ɗinka kake Neman albarkarmu”? Da mamaki akan fuskar Dr Shureim ya ke kallon Alhaji ubaid, Ran Hajiya layla ya 6aci A harzuƙe tace”Dan Allah Ya isa haka! Me yakawo wannan maganar? Saboda kawai yace ka sanya mashi albarka? Idan baza ka sanya mashi ba sai ka ƙyale shi Ya tafi, dama albarkar uwa aka fi buƙata, bata uba ba” Runtse ido shureim Yai, Maganar daddynsa ta ta6a mashi zuciyarshi tuni ƙwalla sun Ciko idonshi, Hatta zainab ta ji ɗacin maganar Alhaji ubaid ji take kamar ta kikkifa mashi maruka a kuncinsa. Still da murmushi akan fuskar Alhaji ubaid ya ke dubanta, kafin ya maida dubanshi ga shureim. “Ka ji abunda Mommynka tace, babu buƙatar albarka ta, Don haka zaka Iya tafiya” cikin jin ƙunar rai Yace”daddy na roƙe ka, Ka sanya min albarka ina buƙatar taka”! hawaye tuni sun wanke fuskarshi, Jinjina kai Alhaji Ubaid Yai, Kafin Ya janyo Dr shureim Ya rungume shi, Yana tofa mashi albarka, Hankalin shi ba ƙaramin kwanciya ya yi ba. Miƙewa Alhaji musa yai daga saman sofa ɗin da ya ke azaune, ko kallo basu ishe shi ba, Cikin takun nan nashi na izza, ya juya ya fuce daga falon don shi arayuwarshi Ya tsani 6ata lokaci. Tsoki Hajiya layla taja aranta tace”abanza, Uban Ji da kai, ai ni da za ka burgeni, ka kama Hanya ka yi tafiyarka, kabarmin ɗana” Ruƙo Hannun dr shureim Alhaji ubaid Yai, Yaja shi suka nufi Hanyar fita falon, Da sauri Zainab Tabi su Hajiya layla kam zama tayi dirshan saman sofa tana faman cije le6e. Abakin Engry hall na gidan, Zungureriyar motar da zata ɗauki Alhaji musa zuwa airport tayi parking, Hamshaƙiyar gaske Ƴar ubansu mota mai numfashi. Yana daga kishingiɗe a ɗaya daga cikin back seat na motar, tamkar yana acikin bedroon ɗinsa saboda tsabar haɗuwarta, slowly murfin motar ke zugewa Dr shureim na ƙoƙarin shiga ciki, Muryar Zainab ta katse masa hanzarinsa. “Namanta da wannan, kai na haɗamawa” juyowa yai tare da kallonta, Ledar hannunta ta miƙa masa, fuskar shi ɗauke da murmushi ya kar6a Yana yi mata godiya, kafin daga bisani yayi masu sallama, yasa kai cikin motar, daddaɗan Sanyin a.c ya ra6i sassan jikinsa shi kanshi Ya yi al’ajabin haɗuwar motar. Mutun Biyune agaban motar, Driver ɗinsa da kuma p.a ɗinsa wani gabjejen mutun mai ƙirar Ƙarfi daga gani yana gym saboda ko’ina na jikinsa a murɗe Yake, wankan suit ne a jikinsa Baƙi wulik baida fara’a a fuska. Kaitsaye Airport Suka nufa, already An shirya mashi privet jet dinsa, Bayan shigarsu cikin jirgin wanda Tsayawa zayyana Haɗuwarshi 6ata lokaci ne, abune da hankali bazai ɗauka ba, saboda an kashe dukiya kamar ba asan zafin nemanta ba, Kai kace saman bishiya ake tsinko kuɗin ana amfani da su. (😂) Dr. shureim Yaga aljannar duniya, Bayan tashin jirgin Cikin mintuna da basu wuci arba’in ba Suka ƙaraso Airport ɗin Abuja, Tun kafin jet ɗinsa ya ƙaraso airport ɗin tuni Escords ɗinsa sun hallara abakin motocin su cikin shiga ta baƙaƙen suits domin tarbarsu da kuma basu tsaro. *EX-PRISONERS❤* Tun Bayan da suka kammala Cin abinci kowan nan su yai kulu wash rabu hani’an, Nurse ta shigo ɗakin ta kwashe kayan abincin da suka ci ta fuce da su waje. Gaba ɗayansu suna A saman gadon zazzaune Sai Yanzu su ka samu damar ƙarewa ɗakin kallo. “Angel menene wancan”? Parveen ce ta yi maganar tana nuna mata plasma tv dake manne a jikin bango. “Tv ce da ita ake yin kallo” “To ki kunna mana mu gani mu ma” girgiza kai Angel ta yi”a’a Parveen ku bari sai munje gidan daddyna tukunna” ta faɗi hakanne don tasan muddin ta kunna masu kallo zasu birkice mata ne, a ƙarshe ay abun kunya, tun da basu ta6a gani ba. Tambayoyi suka dinga jera mata kamar ƴan jarida, komai na ɗakin sai sun tambayeta menene shi ya akeyin amfani da shi, ita kanta ba komai ta sani ba saboda ba kalar ɗakinsu na gida bane, Iya abunda ta sani take amsa masu. “Zan shigo toilet” Batul ce ta yi maganar, saukowa ta yi daga saman gadon ta nufi ƙofar da take tunanin ta toilet ce ta tura da hannu ta shiga, tun da ta shiga take bin ko’ina da kallo sauƙin ma toilet ɗin su na prison na zamani ne, da ko anga ƙauyanci sai dai da banbanci sosai, don wannan akwai sink da bathtub hada shower ga mirror da sauran Kayan amfani. Agaban madubi Batul ta tsaya tana kallon fuskarta, bata ta6a ganin Kyanta irin na yau ba yatsun hannunta ta tura cikin Curly hair ɗinta tana cakuɗa shi. Acan bedroom ɗin Bayan shigarta toilet, zuciya da saƙe saƙe Angel sai ta dinga ayyanawa aranta ga Batul can ta kunna Ruwan zafi amaimakon na sanyi” Jiki Na rawa ta sauko daga saman gadon ta nufi toilet ɗin, ko neman excuse babu ta shigo toilet din kamar an jeho ta. Jin motsin shigowar mutun yasa Batul Juyowa a firgice don ganin wanene. Kusan atare suka sauke Ajiyar zuciya “Dama ba wani abu za ki yi a toilet ɗin ba”? Murmushi Batul ta sakar mata”Inaso ne in ƙare ma ko’ina kallo,” “In dai wannan ne kada ki damu zan yi maku bayanin komai, amma Yanzu ki fito mu koma ɗaki” Amsa mata ta yi da toh ta juya ta nufi Angel ta ruƙo hannunta suka fito, shugowarsu ɗakin ke da Wuya Aka buɗe ƙofar, Dr Daniel brown ne tare da Nurse rebecca. Fuskokinsu ɗauke da murmushi, cikin harshen turanci ya soma yi mata magana. ‘Masoyiya Angel da ƴa’ƴanta, fatan na same ku Lafiya” Amsa mashi sukayi da lafiyalou “Ya jikin naku? Ko akwai inda ke yi maku ciwo “? Atare suka girgiza mashi kai “Okey, Starting tomorrow, you’ll be receiving injections for three days, and you’ll also be taking regular medication to improve your health.” cikin kulawa dr brown ke yi masu magana idonshi akan fuskar Angel. Murmushi ta sakar mashi”mun gode sosai da kulawarku agare mu, Allah ne kaɗai zai Iya biyanku” “Kada ki damu, aikin mu ne, Ko akwai wani abu da kuke buƙata”? Cikin raɗa Batul ta yi ma Angel magana a kunne”muna son ganin Haris da Danish” “Doctor, can we see our brothers?” kamar mai jin shakkar shi ta yi maganar. Jinjina mata kai Yai alamar eh, Kafin ya ɗaura idonsa akan Nurse rebecca” Ki kai su ɗakin Ƴan uwansu” “Okey sir” Mayar da idonshi yai kan Angel” pls muna so ki samu natsuwa sosai, ki kwantar da hankalinki dana ƴan uwanki, akwai magana da zamuyi dake tare da sojojin da suke ceci Rayuwarku, sunce da zarar kin farka a sanar da su, Ni kuma na bari sai zuwa gobe idan kin ƙara wartsake wa duk da naga jikin naki da ƙwari” shiru Angel ta yi tana faman zazzare mashi gray eyes ɗinta aranta ta ayyana komai suke son sani? fatanta Allah ya bata ikon amsa masu tambayoyin da zasu Yi mata “Haɗin kanki mu ke buƙata Masoyiya Angel” murmushin yaƙe ta sakar mashi wanda bai kai zuci ba. Bayan fitar shi daga ɗakin, Nurse ta kalli faces ɗinsu”zamu Iya tafiya” A hanzarce suka sassauko daga saman gadon suka bi bayanta, tun da suka fito daga ɗakin gabansu ke faɗuwa ganin haɗaɗɗen wurin da suka tsinci kansu a cikinsa, Asibitin Har ya gaji da haɗuwa, babu tazara a tsakanin ɗakunansu da inda aka kwantar da su Haris duk acikin amenity ward ne. Abakin ƙofar ɗakin da aka kwantar da Haris suka tsaya, sai da nurse ɗin ta fara tura ƙofar ta shiga tukunna Ɗaya bayan ɗaya su ka soma shiga cikin ɗakin cike da zumuɗin son ganin ɗan uwansu, tun kan su ƙarasa suka hango Haris kwance magashiyan saman medical bed an sanya mashi robar oxygen a hancin sa. Da sauri suka ƙarasa gaban gadonshi, gida biyu suka raba kansu, gefen dama Gabriel ne da Javed sai Naufal da Parveen ta 6angaren hagu Angel ce da Batul, Jamimah da azeeza sai Hannah, tsananin tausayin Haris ne Ya kamasu, tuni idanuwansu sun cicciko tab da ƙwalla. Cikin shessheƙar kuka Angel ta ambaci sunansa”Haris!” har cikin dodon kunnanshi Kiran Ya isar mashi, sambatu ya soma yi masu Yana ambaton sunan Deeja yana faɗin”mu koma ku ɗauko ta, Deeja na tana araye suna can suna azabtar min da ita, dan Allah ku taimakamin ku cece rayuwata ku ɗauko min deeja na” tuni Hawaye sun wanke fuskokinsu, Hatta nurse rebecce Dake atsaye jikinta yai sanyi ganin hawayen su, Duk da bata iya jin abunda ɗan uwan nasu ke cewa “Haris”! Muryar Angel ce ta ƙara ratsa kunnan su, A hankali Ya soma ƙoƙarin buɗe idanuwansa da suka kumbura jawur ya ɗaura su akan fuskarta, Ware su yai sosai, Ganin Yana ƙoƙarin miƙewa yasa Nurse ɗin Yin saurin matsawa bakin gadon ta rankwafa ta zame mashi roban oxygen din daga hancinsa, ta taimaka mashi Ya miƙe zaune Bayan ta sanya mashi pillow a tsakankanin bayan shi da headboard na gadon. Sun natsu suna kallon shi, azabar ciwo tasa shi canza kamanni, fatarshi ta yi haske Ya rame sosai, hakan ba ƙaramin Kyau ya fiddo mashi ba, sumar kan shi a cukurkuɗe kamar mahaukaci sabon kamu, ɗaya bayan ɗaya ya ke binsu da kallo Yana ambaton sunansu da raunatacciyar muryarsa “Angel, Batul, Azeeza, Jamimah, Hannah, Javed, Naufal, Gabriel..” Numfashi Yaja Kafin ya furta sunan Deeja”Ya akai banganta ba? Ina aka kaimin deejana? Baku zo da ita ba”? Idanuwanshi acike tab da hawaye yai masu maganar Cikin sanyin murya Angel tace”Haris pls ka daina sanya damuwa aranka, dubi kaga yadda ka rame, tamkar ba Haris ɗin mu ba, duk kabi ka zauce, Why pls? Bama Jin daɗin canzawar da ka yi, gashi baka da ƙoshin lafiya” daƙyar sautin muryarshi ke fita”Bazan Iya jurewa bane Angel, inason deejana ina jin tsoron ace narasa ta, donni inaji araina tana araye tun da har su azeeza basu mutu ba, Itama sumane tayi” “Haris idan har baka kwantar da hankalin ba, Ta ya ya zamu Iya samun ƙwarin gwiwar fallasa asirin masu kurkukun ƙaddarar har muci nasarar ɗauko sauran ƴan uwanmu da suke acan idan basu mutu ba? Dole fa sai ka bamu haɗin kai ka danne damuwar dake aranka tukunna zamu Iya Cin galaba akan su”! Angel ce ke yi mashi magana cikin kwantar da murya Gabriel ya ɗaura da cewa”Kin faɗi gaskiya Angel, Haris pls ka taimaka ma kanka muma kuma ka taimake mu sannan ka taimaki rayuwar su Deeja Rashin lafiyarka shi zai tarwatsa mana shirin mu, Nurse ta faɗamin abunda ke damun ka, Ciwon zuciyane Haris kuma nasan bakomai ne ya jawo hakan ba face Deeja!! kaga yanzu mun ku6uta daga Daji muna acikin mutanan duniya, Nan inda muke asibiti ne Inda ake duba marasa Lafiya sune suka bincika lafiyarka kuma suka tabbatar mana da cewa damuwace ta silar wani abu daka ƙwallafa rai akan son shi, pls Haris Ka taimaka mana! Idan har ba ka ji sauƙi ba Likitocin nan bazasu ta6a bari mu koma Nigeria ba gidan daddyn Angel” tunda Gabriel Ya fara magana Haris Yake bin ɗakin da suke da kallo, sai lokacin Ya gane ba adaji suke ba, shifa gaba ɗaya baya acikin hayyacinsa baisan ma a ina yake ba, idanuwanshi sun makance. Azeeza sarkin tausayi tun da ta tsareshi da ido, Hawaye ke bin fuskarta. Cikin shessheƙar kuka tace”Dan Allah haris ka yi haƙuri, In sha Allah deejan mu bata mutu ba da sauran ƴan uwanmu Zamuje mu ɗauko su” Batul tace”kwanciyar hankalinka kawai muke buƙata Haris, idan ba haka ba kaga zaka mutune kafin muyi nasarar dawo da su deeja, me kake tsammani idan Ka mutu muka gano deeja araye ya za ta ji? Ka mutu saboda ita? Kaima ka sani yadda take ƙaunarka itama mutuwa zatayi tabi ka” lumshe idanuwanshi yai, ƴan uwanshi ba ƙaramin sanyaya mashi zuciya suke yi ba, sai kwantar mashi da hankali suke yi duk don su samu ya wartsake “Ina ɗan uwana”? yai tambayar yana kallom faces dinsu “Danish bai farka ba Haris Har yanzu, bacci yake yi, “ Angel ce ta bashi amsa, damuwace ƙarara akan fuskarshi “Angel wani irin bacci ne wannan Har yanzu bai farka ba? Ina jin tsoro wani abu yasame shi” girgiza kai Angel tayi”a’a Hairs ba abunda zai same shi, Ni inaji araina Lafiyar danish qalou, Bacci ne kawai ya ke yi kasan ya ɗauki tsawon lokaci bai runtsa ba shiyasa bai farka ba” Gyaɗa kai yai”Allah yasa hakane,” . “Haris ka ci abinci ko kana jin yunwa”? Kallon parveen yai”bana Jin yunwa parveen, Naji daɗin kulawarku agare ni, sannan Ina tayamu murnar barin kurkukun ƙaddara” murmushi kowan nan su Ya saki, shima ya ƙalalo murmushi akan fuskarshi Muryar Jemimah da shagwa6a tace”Idan ka ji sauƙi, zamu ga deeja ma har kuci abinci atare da ita, kana bata abaki itama tana baka abaki, agidan daddyn genie ɗita” gaba ɗayansu suka sanya dariya, Nurse rebecca dake tsaye tuni ta zauna saman chair tana dubansu sam bata gajiya da kallon Yaran burgeta suke Yi kamar ta sace su take ji. Haris Ya ji daɗin maganar Jemimah har saida yaɗan murmusa “Sannan Haris zai dinga wanke ma deeja gashin kanta yana sharce mata shi,” Batul ce tayi maganar, tsabar daɗin maganarta har saida fararen haƙoransa suka bayyana. “Bayan haka zai dinga goyata a saman bayanshi Suna yawo” acewar Hannah sosai Haris ya fashe da dariya yayin da hawaye ke cigaba da yin sintiri akan fuskarsa, Lamarin ya ɗaurewa rebecca kai, mamakinta yadda yaran suke matuƙar ƙaunar junansu, wani abu da ya ƙara burgeta yadda suke ta sanya shi dariya tabbas su ka ɗai suke Iya sarrafa junansu. “In sha Allah Haris our dream will come true” lumshe idanuwanshi yai tare da buɗe su akan fuskokinsu sai ya dinga ganin tamkar Deejar sa ce zaune a tsakiyar gadon tana sakar mashi murmushi, hakan yasashi sakin murmushi kamar wani zautacce “Haris ka kwanta ka huta, kada mu cika ka da surutu, zamuje ɗakin Danish mu duba shi” “Nima inaso naganshi Angel, muje atare” Kallon Nurse ɗin tayi”pls sister zamu Iya tafiya da shi ɗakin ɗan uwanmu”? Smilling gently, nurse rebecca tace”badamuwa, zamu Iya tafiya da shi” ta yi maganar tare da miƙewa Ta nufi gaban gadon, da taimakonta Haris ya sauko daga saman gadon tace mashi ya dafa shoulder ɗinta don ya samu damar yin tafiya, Rurruƙeta yai da hannayenshi a haka suke Yin tafiyar, Su Angel suna abayansu har suka ƙaraso ɗakin da aka kwantar da garkuwa, Jikin Angel har 6ari yake yi saboda tsabar zumuɗi, tun kafin su ƙarasa shiga ɗakin suka hango Danish Baje saman gadon, kamar matacce, lallausar sumar kanshi ta tarwatse saman mattress ɗin gadon, da sauri Angel ta nufi gadon Ta haye daga gefe Idonta akan Kyakkyawar fuskarshi, Har kullum kamar ana ƙara ninka mashi kyawunshi, fatarshi tayi smooth fara sol Ko tabo babu, Sun canza mashi uniform ɗinshi wanda ke a jikin sa Yanzu kalar nasu ne Riga da wando light blue, rigar tayi tighting ɗinsa, gajeran hannu ne da ita Hakan ya bayyana ƙaƙƙarfan Damtsen hannun shi, Likitoci sun sha wahala wurin canza mashi kayan Jikinshi saida suka haɗa ƙarfi tukunna su ka samu damar raba shi da su. A hankali take bin Shi da kallon so da ƙauna tun daga saman sumar kanshi har i zuwa kan Long eye lashes ɗinsa, dogon hancin nan nashi yayi sam6al babu lanƙwasa, full lips ɗinsa sun ciza launinsu, slowly ta sauke idonta akan Zanan tattoo dake a gefen dogon wuyanshi Yayi bala’in yi mashi kyau A gefe da gefen gadonshi kowannansu Ya samu wuri ya zauna hada haris da nurse ta zaunar dashi, natsuwa su ka yi a yayin da su ke kallon ɗan uwansu, daɗi kamar zai kashe su Angel ta shagala da kallonsa ji ta ke kamar ta faɗa saman chest ɗinsa ta ƙanƙame shi ko ta samu sassaucin kewarsa da ta ke yi, Muryar Haris ce ta fargar da ita. “Angel zuciyarshi tana bugawa”? A hanzarce ta kwantar da kunnanta saman chest ɗinsa saitin heart ɗinsa nan take taji bugun zuciyarshi na harbawa a tsanake Ɗagowa tayi fuskarta ɗauke da murmushi tace dasu”zuciyarshi tana bugawa, bacci ne yake yi” Jin haka yasa Kowan nan su Ya matsa kusa da shi, ɗaya bayan ɗaya suke ɗaura kunnuwansu saitin zuciyarshi, nurse rebecca dake a tsaye murmushine ɗauke akan fuskarta hankalinsu ba ƙaramin kwanciya yai ba, jin zuciyarshi na bugawa “Sai yaushe zai farka? Baccin yayi yawa” Javed ne yai maganar, Naufal yace”may be saiya ɗauki adadin kwanakin da yayi bai runtsa ba tukunna zai farka” zaro ido Angel tayi haɗi da girgiza kanta”in sha Allah ba zai kai wannan lokacin ba zai farka. Ta ƙare maganar tare da ruƙo zira ziran yatsun hannun Danish na dama acikin nata, sosai ta runtse su (nima kuma na runtse alƙalamina) *Boss Bature✍️ Mu haɗu gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*KURKUKUN ƘADDARA*_ ~Middle step~ _The Prisoners E17🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* A ƙalla sun shafe kusan 30 minutes a ɗakin Danish, Ji suke kamar abarsu su kwanta a ɗaki ɗaya saboda haka su ka saba kwana a kurkuku, daga bisani Nurse tace dasu zasu tafi zuwa gobe zasu Iya zuwa su ƙara duba shi’ jiki asanyaye suka miƙe suna tafiya suna waiwayon shi musamman Angel ji ta ke yi kamar ta koma ta rungume shi. Bayan fitar su daga ɗakin, Nurse Ta raka kowan nan su room da aka kwantar da shi, ba su so aka raba su ba, har yanzu tsoron mutanan su ke ji, ba dan Angel ta lalla6a su ba da ko babu inda zasu je, a ɗakinta zasu kwana, musamman Azeeza da jemimah ɗaƙyar Angel ta lallashesu ta lalla6asu don ta fahimci dokar asibitin ce haka ba’a haɗa mutun fiye da ɗaya a ɗaki, wata’ƙil sai idan ya kama dole, sauƙin ma kowan nan su akwai nurse ɗaya da ke kula da ɗakin shi, duk wani abu da zasu buƙata zasu yi masu, hatta toilet suna raka mutun In ya buƙaci hakan musamman gasu da basu san yadda zasuyi amfani da wasu abubuwan ba. A daren ranar sun yi kwanan farin ciki basu da wata damuwa. *Daular Alhaji Musa wadata* idan nace zan tsaya zayyana maku zunzurutun Kayan alatun da ke a gidan Alhaji musa daga ni har ku zamu koma Yin Mafarkinsa ne, wato Haɗaɗɗiyar Daular arziƙi ce, Katafaren Villa ne Wanda Idan ka zura ƙafarka acikinsa tamkar ka Bar Nigeria ka shiga Dubai ne, Aljannar duniyace ƴar ubansu, A ƙalla security din dake tsaron Kafcecen Gate ɗin shiga gidan sunkai su goma shabiyar, Wasu gabza gabzan Garada Masu Ƙirar sadaukan Yaƙi, Babu wasa akan fuskokin su, Bana tunanin ko aljani zai Iya gifta gate din gidan salin alin ba tare da sun cafke shi ba, Shantalelen titi ne zai sadaka da Cikin gidan kai tsaye daga bakin babban gate ɗin, yadda kasan da zallar goal aka ƙera ginin saboda ɗaukar idon gilassan Ƙofofin da Windows, ko gidan shugaban ƙasa albarka, Babu ce kaɗai ke babu agidan Alhaji musa, komai na gidanshi babu made in Nigeria, an zabga almubazzarancin dollar wurin ƙera ginin, don hatta sample dinsa da ƙwararrun da suka ginasa kaf aikin turawa ne. Mamaki da al’ajabin dukiyar Uncle din nasa Ya hana shi Kwantar da hankalinsa, Tun Bayan da escords suka ɗauko su daga airport, Motocin suka shigo gidan gabanshi ke ta faɗuwa, saboda sabon gini ne baya a ƙasar Uncle ɗin nasa Ya mallake shi, shiyasa komai yake ɗaure masa kai, Kafin shigarsu gidan Saida shureim Ya dinga jero addu’o’i acikin zuciyarshi Yana neman tsari akan Allah ya kare shi daga shagalar duniya, Idan har zaman shi gidan ba alkhairi bane, Ya roƙi Allah da ya yi mashi silar barin shi cikin sauƙi ba tare daya sha Wahala ba. Tun da suka shiga gidan Kamar wani baƙauye Haka ya dinga bin ko’ina da kallo, wasu matsiyatan Chandeliers saman ceilling Masu ƙyalƙyali tamkar zasu rubzowa mutun saman kanshi, Ga wasu Haɗaɗɗun twins stairs, masu ɗauke da Glass Elevator a gefensu. Idan ka shiga cikinta Kana iya hangen mutanan dake zarya a palourn Yayin da take Yin sama dakai ko take dawowa dakai ƙasa. A katafaren Palourn gidan kuwa Wasu Jigunannun Royal Sofas set ne Ƴan ubansu masu numfashi Ga Arm chairs kalar Na sarakuna, A gefe da gefen kujerun Sofa table ne, Tiles din palourn baida banbanci da Mirrored tiles Kana kallon Fuskarka acikinsa Idan kana Tafiya, zallar haɗuwa, An zuba komai na more rayuwa, Idan nace zan tsaya zayyana haɗuwar Komai dake acikin Gidan Tabbas zamu ƙare middle step da last step acikin gidan Alhaji musa (🤣) Babu wanda Yasan da zuwansu, Hatta Iyalinsa Ba su san da dawowar shi a yau ba, yana ɗaya daga Cikin Halayan Alhaji musa, Idan zai yi tafiya babu wanda ke sani Matar shi ko ƴa’ƴanshi, Haka zalika Idan Zai dawo sai dai su ganshi, saboda zuwan ba zata Ya ke yi masu. A Kwance take saman Prayer mat, Tasha Dogon Hijabi a jikinta duk ta ƙudundune kanta acikinsa, daga gaban dardumar Qur’anic Stand ne, ga dukkan alamu Bacci ne Yai awon gaba da ita a yayin da take Yin karatun al’ƙur ani mai girma. “Zeenat! Kiran Sunanta da akayi ne Yasa ta firgita a Hazarce Ta farka daga baccin ta ɗago da kanta tana faman zazzare dara daran Kyawawan idanuwanta farare ƙal launin Ocean Blue, Masha Allah Kyakkyawar matashiyar budurwa Kamanninta sak Alhaji musa tamkar yayi kakinta, sai dai Daga gani Farar fatace Haskenta ya ɗare na mahaifinta, Fara ce sol Jawur da ita, tana da yalwatacciyar sumar kai Launin blonde har saman fore head ɗinta kwantaccen gashi ne, ga doguwar fuska, dogon hanci da ƙaramin baki launin pink, Ba ta da ƙiba ko misƙala zarratin siririya ce, abu ɗayane ke da girma a jikinta, dukiyar fulaninta acike suke kamar an jera balon balon. “Zeenat! Bacci ki ke Yi”? Muryar Mahaifiyartace ta rasa kunnuwanta, da sauri ta zabura ta miƙe tare da wurga ƙwayar idanuwanta kan Mai shigowa ɗakin, babbar macace mai cikar kamala, Ta ɗauki wankan Shadda ajikinta launin Ja, Tasha uban ado akan fuskarta, baturiyace Siririya bata da ƙiba, daga ganin surarta a wurinta matashiyar budurwar ta gado hasken fata da launin ido, da kuma doguwar sumar kai, Hajiya Sarah Uwar gida kuma amarya awurin Alhaji musa, ta ɗaure kanta da kallabi, hakan bai 6oye doguwar sumar kanta da ta sauko har gadon bayanta, Necklace ɗin wuyanta da earrings ɗinta na zallar diamond ne sai ƙyalƙyali suke Yi da ɗaukar ido. Muryarta Adisashe ta amsa mata”mommy karatun ƙur’ani nike Yi bacci ya ɗauke ni bansani ba” ta yi maganar tana Yin miƙa haɗi da yin hamma “Ba ki ji dirar motoci ba ne”? Ras Taji gabanta Ya faɗi, Muryarta na rawa ta furta”dad... daddy is he back “? Ta6e baki Hajiya Sarah tayi”ya dawo tun ɗazu, yanzu haka yana a ɗakinsa, yace baya son takura, kinsan halinsa” Hankalin Zeenat Ba ƙaramin tashi yai ba, ta rasa gane farin Ciki za ta yi ko baƙin Ciki, Tana son mahaifinta sosai, sai dai tana mugun jin shakkarshi saboda rashin sakar masu fuska da baya yi, duk da wani lokacin idan yaso yana nuna masu so da ƙauna. Jin ta yi shiru zugudum tana faman zazzare ido Yasa Hajiya Sarah cewa”ya naga kamar baki farin Ciki da dawowarshi”? A hanzare ta girgiza kai” “I’m so happy he’s back, na yi murna ai shi ɗinne baya son takura” Murmushi tasakar mata”Albishirinki”! Da mamaki ta tsayar da eye balls ɗinta kan face din momyn nata “Goro”! “Fari ko ja” “Fari” Matsawa Mommyn ta yi kusa da ita Cikin raɗa ta furta mata”Ba shi kaɗai ya dawo ba, Hada Yayanki Dr shureim yanzu haka Yana kwance a bedroom ɗin da aka ware masa” Tun kafin Hajiya sarah ta ƙarasa Maganar, Zeenat ta zube saman gwiwowinta tare da ɗaura goshinta saman tiles ta yi Sujjada tsabar farin cikin jin anzo mata da sahibinta “Ah lallai ashe Har yanzu Kina son Yayan naki, Hada Yin sujjada” ɗagowa Zeenat Tayi, tare da miƙewa tsaye Hijab ɗin jikinta sai Ja da ƙasa Yake yi. “Mommy bazan Iya jurewa ba, Zanje wurin Yayana inyi mashi barka da zuwa” tsantsar farin cikine akan fuskarta “No kada ki je Yanzu ki bari masu aiki su kammala Girka mashi abinci, In yaso sai ki je ki kai mashi a ɗakinsa, Daddynki ne Ya bada Umarnin A girka mashi abinci hausawa” Zeenat da takasa rufe bakinta don Murna duk tabi ta ƙagara don a kwaɗaice take da son ganinsa “Na faɗa maki zuwanshi ne Don ki kimtsa, Ki gyara kanki, Nasan Halinki da sanya dogon Hijabi salon kije mashi ahaka, Ki samu Ko ɗan gyalene ki yafa a kafaɗa,” turo baki zeenat tayi da ƴar shagwa6a tace”Mommy ae shima Yaya shureim ɗin yafi son mace mai sanya dogon hijabi” “To ai bance bayaso ba, tun da acikin gidane ki samu gyale ki yafa” ta ƙare maganar da zolaya ta furta”Muslimatun matar limam” Dariya Zeenat ta sanya tana kallon mommyn nata. “Zan koma kitchen, Ki tabbatar kin shirya da wuri” Amasa mata tayi da toh Bayan fitarta, da sauri Zeenat ta cire hijab ɗin jikinta, ta nufi toilet ta shige, cikin Ƴan mintuna ta fito Sanye da bathrobe (rigar wanka) fara Ƙyal a jikinta, hannunta ruƙe da short towel tana tsane sumar kanta, Bayan ta kammala tsane gashin, a gaban tafkeken dressing mirror ta zauna saman chair tana Gyara Jikinta, Hair dryer ta kunna Ta busar da sumar kanta, Bayan ta gama ta soma shafa tsadaddun Mayukan shafawarta dake a jere gaban madubin. Zeenatu muguwar sangartacciyace ta saba tun tana ƴar ƙarama duk In za ta yi make up ko zata sanya sutura masu aikin gidansu ne ke taimaka mata, saboda ba ta Iya komai na aikin wahala ba, hatta sanya ɗan kunne bata Iyaba wahala take sha, Yau saboda zumuɗin zuwan ya ya shureim bata bari wani ya taimaka mata wurin sanya sutura ba, tun tana agaban mirror mai aiki ta ƙwanƙwasa ƙofar ɗakinta ta nemi zinin shigowa, ta tambayeta Ko tana Buƙatar wani abu, tace mata a’a taje kawai za ta yi komai da kanta, ashe da rabon tasha wahala. Gaba ɗaya saida ta faffasa kayan kwalliyar gaban mirror, bata da natsuwa ko misƙila zarratin tana da rawar kai da zumuɗi, tun daga kan Hoda da ta ɗauko zata shafa, Ta sil6e daga hannunta gaba ɗaya ta tarwatse a saman tiles, garin hodar ya zube, Ta kuma janyo janbaki a tsiyace take murza ma la66anta nan take ya gutsire guntulan Ya faɗi ƙasa ta jefar da shi, duk kwalbar turaren data ɗauka sai ya sil6e ƙasa Ya daki tiles kwalbar ta fashe ruwan Ciki Ya tsiyaye, hakan bai dame ta ba, don ta yi asararsu. Bayan Ta kammala ƴan shafe shafenta, bata bi takan kayan da ta faffasa ba, tsallake su ta yi ta nufi tafkekiyar glass wardrobe ɗinta, daga wajen glass ɗin kana Iya ganin jerin suturar sanyawarta ashaƙe tamkar a company, Abayas, shadda atampa leshi, material, english wears, Pakistans, ga jerin Kayan baccinta, komai fa anzuba mata su, shalelen daddy musa Da hannu ta zuge glass wardrobe ɗin, Ta ƙura ido tana tunanin suturar da zata sanya don ta burge Yayanta shureim, idanuwanta ne su ka sauka akan haɗaɗɗiyar atampa, yatsun hannunta na kerma ta cafko ta, tana kiciniyar ciro atamfar ai ko gaba ɗayan jerin Kayan da ke a gidan tsakiya suka zazzago saman tiles, ko ajikinta, saida ta 6arar da kayan wardrobe ɗin wurin neman sutura ɗaya kacal da zata sanya a jikinta, Ga abu a fili ta ɗauka tasa shine bazata Iya ba, tafi so saita haukata komai na ɗakin tukunna a ƙarshe tabar masu aiki da wahalar gyara mata su. Tamkar zata fashe da kuka, ruwan ido Ya hanata ɗaukar Kayan da zata sanya don ta burge Yayanta. “Assalamu alaikum” Muryar ɗaya daga Cikin masu aikin gidan ce babbar mace wadda suke Kira da Tani. Da sauri Zeenat ta juyo tana kallonta, “Yawwa Tani, shigo ciki ki taimaka min narasa wasu Kaya zasu dace dani, Inaso ne na burge yaya shureim” Baki asake Tani take bin ɗakin da kallo, Sam ba ta yi mamakin ganin yadda Zeenatu ta faffasa Kayan Kwalliyarta da turarurrukanta ba, Halinta ne yin 6arna kamar 6era. “Haba zeenat, Dubi yadda kika zazzago da ninkakkun Kayan Cikin wardrobe ɗinki ƙasa, sannan kinbi kayan kwalliyarki da kwalaban turare duk kin faffasa su why pls? Harfa larai na turo donta taimaka maki ki shirya a tsanake amma sai ki ka ce mata ta tafi za ki yi da kanki, yanzu kin kyauta abun da ki ka yi”? Cikin kwantar da murya take Yi mata magana. Zumbura mata Baki Zeenat tayi”Nifa bana son faɗa, Idan ma na faffasa su ai daddy zai canza min wasu, kuma ai bada gangan nayi ba ko” Girgiza kai Lami tayi haɗi da sakin murmushin takaici “Oh, Saboda kinsan daddynki zai siya maki wasu shiyasa kika faffasa su? Ke Baki damu da asarar dukiyar da za’ayi ba kenan”? Bubbuga ƙafafuwa Zeenatu tayi fuskarta a tur6une tace”Ni ki daina Yi min faɗa, Nace maki ba laifina bane kuma in sha Allah zan gyara, pls ki taimaka min In gyara komai kada mommy tazo taga ban shirya ba” Gyaɗa kai Tani tayi”ai dole kam in tayaki gyarawa, idan ba haka ba hada ni zata shafa” Ƙarasa shiga ɗakin Tani tayi, cikin ƙanƙanin Lokaci ta ɗauko Parker ta tattara Kayan kwalliyar da zeenatu ta faffasa ta zubar a trash can na ɗakin, Ta koma bakin wadrobe din ta soma ninke mata kayan da ta zubar a kasa ta jera mata su a cikin wardrobe, duk tana a tsaye ta ruƙe qugu tana kallon tani. Wani haɗaɗɗan Cord lace ta ɗauko mata Red colour anyi mashi adon flower yellow. “Zeenat wannan zaiyi maki kyau sosai, Red and yellow, kalar farare ce sannan kuma kyawawa irinki” Washe fararen Haƙoranta tayi Jiki na rawa ta sanya hannu ta kar6i kayan da Tani ta miƙo mata, Sai da Tani ta taimaka mata wurin ɗaura zani da ɗaura ɗan kwali don ba ta iya ba, masha Allah Lace ɗin Yayi bala’en Yi mata kyau. “Bari na ɗauko maki Takalman da zaki sanya” Tani ta yi maganar tare da nufar Shoe rack din ɗakin, Inda jerin takalman Zeenatu suke na gayu masu tsini da flat, ta ɗauko mata yellow kalar head ɗinta. Ta dawo ta ajiye mata su agabanta, ta koma ta ɗauko Jewelry box dinta, ta ɗauko mata sarƙar diamond da earrings, Bayan ta kammala sanya mata su, sai da ta gyara mata make up ɗin fuskarta. Ita kanta Tani Kyawun Zeenatu ya tafi da imaninta, Inaga wanda Akayi adon domin shi. “Kinyi kyau sosai shalelen daddy musa, Muje kitchen ɗin in shirya maki dinner dinsa ki kai mashi” Ta amsa mata da “Toh” Daƙyar take yin tafiya da high hills din ƙafarta, Bawai don bata saba sanya takalmi mai tsini ba, sai don rashin natsuwarta. Bedroom ɗinta a second floor Yake, Ƙa’ida ne idan zata sauko down stairs sai dai Ta hau elevator saboda a wurinta wahala ne taka bene. Atare da Tani suka Hau elevator ɗin ta sauko dasu down, da kwarkwasa take yin tafiya tana taka tiles sautin na bada kwas kwas kwakwas. Kaitsaye kitchen suka nufa, tun daga Cikin Katafaren palourn gidan kana Iya hangen Masu aikin dake safa da marwa acikin kitchen, a tsakiyar falon ta dakata da yin tafiya. Tani tace “Bari na ɗauko maki Kayan abincin” ta ƙarasa maganar tare da juyawa ta nufi kitchen, badajimawa ta fito hannun ta ruƙe da wooden tray faffaɗan gaske, daga saman shi wasu haɗaɗɗun Warmers ne da flatware da sauran kayan abinci” “Anya kuwa zeenatu zaki Iya ruƙe tray din nan? Naji da nauyi, ko dai In raka ƙi ɗakin nashi”? Girgiza mata Kai tayi”a’a Zan Iya ki bani kawai” miƙa mata tray din tani tayi, Ta rurruƙe shi da hannu Biyu, tana tafiya tana rangwaɗa, Tani dake a tsaye ta ƙurawa bayanta ido, ita tasan daƙyar zata Iya kai shi ɗakin ba tare da ta 6arar dashi ba. Ɗakin da aka warema Dr shureim a gidan baida banbanci dana sarki saboda luxury furniture dake a cikinsa, sam ta manta ba ta tambayi Tani a wani room ya sauka ba, sai faman wurwurga eye balls ɗinta take yi a ƙoƙarinta nata gano masaukinsa, Cikin sa’a ta hango ɗaya daga cikin ɗakunan dake a rufe ƙofar shi ta buɗe hakan na nufin anan aka saukar da shi. A lokacin Yana a kwance saman katafaren gadon ɗakin, Ya cire Jallabiyar jikinsa, Iya short ne fari, ya zame arab turban din kansa, Kwantacciyar sumar kanshi baƙa wulik, ya sanya singlet tabi shape ɗin ƙirjinsa. Bacci ne ya ɗauke shi gefen shi wayarshi ce ajiye yana cikin kallon hotunan abar ƙaunarsa bacci yai awon gaba da shi. “Yaya shureim ɗina” Muryar Zeenatu ce ke ƙwala mashi kira, tun kafin ta ƙarasa bedroom ɗin. “Ya ya shureim am coming” kasancewar tana da zaƙin murya mai tsiwa har cikin kunnanshi yake jin muryarta. “Yaya shureim” firgigit! ya farka daga baccin haɗi da miƙewa zaune la66ansa na ambaton sunan Allah, idanuwanshi har sun canza launi saboda bacci. ɗakin Yabi da kallo a ƙoƙarin shi na ya gano ta inda zata 6ullo, sautin takun tafiyarta ne Yaja hankalin shi ga kallon ƙofar ɗakin. Daƙyar ta ke tafiya, sai faman zabga murmushi take yi akan fuskarta, tun da ta shigo ɗaki ta tsayar da blue eyes ɗinta akan fuskarshi, da ƙarfi ta furta hubby na” kamar a mafarki shureim ke kallon zeenatu, kamar yau ya fara ganinta sam ya kasa motsawa daga zaunan da yake saman gadon. Ganin yadda take yin tafiya babu natsuwa yasa shi yin saurin furta”bari nazo na taimaka maki” maimakon ta dakata da yin tafiyar tun da yace zai taimaka mata, sai ma ta ƙara saurin tafiyar da take yi, a hanzarce dr shureim ya haura ƙafafuwanshi ya sauko daga saman gadon sai dai kafin yai saurin zuwa gareta, Cikin rashin sa’a takalmin ƙafarta ya karkace ai ko Gaba ɗaya Ta saki tray ɗin hannunta Ya kife saman tiles kayan abincin ciki duk suka tarwatse, Nan take zanin da aka ɗaura mata Ya warware Ya zame ƙasa, Daga Ita sai ɗan pant ɗinta. Runtse ido dr shureim yai, ba arziƙi ya dakata da yin tafiyar. Jikinta sai kerma yake yi, Kunya duk ta isheta muryarta na rawa ta soma magana”wayyo Allah na, Am sorry yaya shureim wlh duk zumuɗin ganinka ne bansan ya akai zanin ya warware ba, gashi na zubda maka kayan abincin” ta yi maganar tana faman yarfa hannayenta, Kunyar duniya ta ishe shi “Yaya shureim bari na koma Tani ta gyara min ɗaurin zanin, yanzu zan dawo maka da wani abincin tun da wannan Ya 6are” saboda tsabar ruɗu Anan tabar mashi zanin da kallabinta da ya warware, da takalmanta, da gudu ta juya ta fuce daga ɗakin A hankali dr shurem ya buɗe idanuwanshi Yana kallon 6arnar da Zeenatu tayi mashi, rashin natsuwar yarinyar ba ƙaramin burge shi yake yi ba, Saboda yana samun nishaɗi sosai, tsabar shiririta ita da tace za taje a gyara mata zani ta tafi tabar zanan a ƙasa. Yaushe rabon da ya yi dariya irinta yau harya manta, Hada dafe cikinsa tun da zeenatu tabar ɗakin bata ƙara dawowa ba saboda Kunya gare ta, kamar ba jinsin turai ba, Tani ce tazo ɗakin ta bashi hakuri game da 6arnar da zeenatu tayi mashi yace mata bakomai ai yarinyace yana yi mata uziri, Bayan tani ta kwashe kayan da ta 6arar mashi, Ta koma kitchen ta canzo mashi wani abincin ta dawo ta kawo mashi, kafin Tani tabar ɗakin sai da ta tattara kayan zeenatu da ta bar masa zaninta da ɗan kwalinta da takalman duka ta kwashe ta fuce da su, dr shureim yaso ta dawo suyi fira sai dai yasan abune mai wuya ta bari su ƙara haɗuwa yau sai dai zuwa gobe idan kunyar ta sake ta. *PRISONERS MIDDLE STEP💋❤* Ƙarfe 7 na safe agogan San antonio ta buga, adai dai lokacin Sojojin sun zo duba marasa lafiyansu daga headquater, mutun uku ne Commender, Major, tare da Captain sun zo cikin shigarsu ta kaki, A office ɗin dr. Laura davis suka fara zama domin tattaunawa. A6angare Angel tana ƙudundune cikin bargo tasha baccinta, sai mutsu mutsu take yi duk ta yamutsa bedsheet ɗin ga dukkan alamu mafarki take Yi, A firgice tafarka Haɗi da yakice bargon ta wurgar da shi gefe ɗaya, hannayenta biyu saman fuskarta, cikin shaƙaƙƙar murya take ambaton sunan Danish, Mummuna mafarki tayi akanshi Ya farka Ya rikiɗa ya zama dodo Yana shan Jinin mutane, Hankalinta duk yabi ya tashi haiƙam gani take kamar mafarkinta zai iya zama gaskiya. Ta yi zurfi acikin tunaninta muryar Nurse ta Fargar da ita “Barka da safiya Masoyiya Angel, fatan kin wuni Lafiya” da sauri ta ɗaura idonta kan fuskar nurse ɗin In a cool voice ta amsa mata Lafiyalou “How are you feeling today? Are you experiencing any pain?” girgiza kai Angel tayi”A’a” “Okey, nasan zaki buƙaci shiga toilet, ki gyara fuskarki, akwai sojoji da suka zo suna son ganawa dake, Amma kafin nan Zan kawo maki breakfast ɗinki ko kina da za6i na abunda kike son ci”? Girgiza kai Angel tayi”a’a” Okey daga haka Nurse ɗin ta juya ta fuce, Saukowa tayi daga saman gadon abakin ƙofar shiga toilet ta zura slippers dake ajiye saman carpet, kafin ta tura door din ta shige ciki. A hankali take tafiya tana bin ko’ina na toilet ɗin da kallo A tsaftace yake fari ƙyal Kamar ba’a ta6a amfani da kayan Cikinsa ba. Agaban mirror Ta tsaya tana kallon Kyakkyawar fuskarta, batasan lokacin da murmushi Ya kubce mata ba, nan take dimples ɗinta biyu suka lotsa, yatsun Hannayenta, ta tura cikin sumar kanta, a hankali ta soma barbaza gashin, aranta ta ayyana inama akai su saloon Agyara masu gashin kansu ba ƙaramin kyau za su yi ba, fanfo ta kunna Ruwa Ya soma kwararowa cikin sink, ta shigo da niyar ta wanke fuskarta sai kuma ta tsinci kanta da sha’awar son Yin alwala, nan take ta canza ra’ayinta, Tsarki ta fara yi kafin ta soma Yin ta a tsanake, bata manta komai na daga yadda akeyin alwala ba, bayan ta kammala Yi, ta fito daga Cikin toilet ɗin tana Tunanin tayaya zata Iya yin sallah bayan babu Hijabi? Buɗe ƙofar da akayine yasa ta ɗago tana kallon mai shigowa nurse ce ta shigo hannunta ruƙe da tray na kayan breakfast ɗin Angel asaman table ta ɗaura mata shi. Ɗagowa tayi suka hada ido da juna”Is there anything you need?” Da sauri tace”Hijabi da abun sallah inaso zanyi” Da murmushi akan fuskar nurse ɗin tace”are u muslim”? Ɗaga mata kai Angel ta yi alamar eh, nurse ɗin tace”Okey, ki jira ni yanzu zan dawo” Fuce wa tayi daga ɗakin, Angel ta sauke ajiyar zuciya, tana ƙare ma ɗakin kallo, shigowa nurse ɗin tayi hannunta ruƙe da hijab da Prayer mat ta miƙa mata, Farin Ciki a wurin Allah bakinta yaƙi rufuwa. “Thank u so much” nurse ɗin na murmushi tace da ita”never mind” ita kanta batasan Ina ne alƙibla ba, sai da ta tambayi nurse ɗin tayi amfani da wayar hannunta wurin yi mata bincike ta gano mata Alƙiblar da zata fuskanta tukunna ta shimfiɗa carpet ɗin, a tsanake ta kabbara sallah, saman chair nurse din ta zauna tana jiranta, Raka’a Biyu Angel tayi kafin ta sallame sallar, wani irin daɗi take ji yau tayi sallah, bakinta yaƙi rufuwa, tafin hannayenta biyu ta ɗaga sama tana karanto addu’o’ kirari tafara yi ma Allah kafin tayi ma ƴan uwanta da suka rasu addu’a, da su kansu a ƙarshe ta roƙi Allah akan Ya haɗa ta da ƴan uwanta ba tare da ta sha wahala ba, Allah yasa daddynta Yana araye, da auntynta Aneelerh. bayan ta kammala Yin addu’ar, Ta shafa a fuska, ta yunƙura ta mike, ta nannaɗe prayer mat ɗin da hijabin ta dubi nurse ɗin “Kin gama” ɗaga mata kai Angel tayi alamar eh, Miƙewa tayi tare da zuwa gaban angel ta kar6i carpet din da hijabin juyawa tayi ta nufi closet ɗin ɗakin ta buɗe ta sanyasu aciki. “Aduk lokacin da kika buƙaci yin ibadarki zaki iya ɗauka ki yi” godiya Angel tayi mata, daga bisani ta zauna zaman Cin breakfast, lafiyayyan kalaci aka haɗa mata, tana ci tana tunane tunane sam tamanta da sojojin dake jiranta. Sai da ta kamalla cin abincin ta ƙoshi, Nurse ɗin ta tattara komai ta fuce dashi, Zama tayi gefen gadon idonta akan ceilling ta ƙurawa haɗaɗɗen kwan ɗakin ido, Yayin da zuciyarta ke tariyo mata abubuwan da suka faru. Ba zato ba tsammani ta tsinkayi muryoyinsu a yayin da suke shigowa ɗakin, A hanzarce ta miƙe tana faman zazzare gray eyes ɗinta akansu, sojojinne tare da likitocin, saman doguwar sofa ɗin ɗakin suka zauna a jere suna fuskarta, Dr Laura davis ta zauna gefenta, Kamar wata mara gaskiya duk ta kama kanta, Hankalinta ba ƙaramin tashi yai ba. “Masoyiya Allah fatan Kin wayi gari lafiya? Ya jikin naki” muryarta adabarbarce tace”da sauƙi sosai” cikin kulawa suke Yi mata magana da harshen turanci Dr Mark jackson ne ya fara yi mata magana”mun nemi jin bayani daga bakin ɗan uwanki Gabriel sai dai bai bamu haɗin kai ba, Yace duk abunda muke son sani ke ce zaki amsa mana. Jin wannan maganar yasa hankalinta ƙara ɗugunzuma. Fahimtar yanayin ta ne yasa dr mark cewa” Ki kwantar da hankalin ki, Bamu zo da niyar mu takura maki ba, Ƴan tambayoyi ne zamuyi maki da zarar kin amsa mana zamu tafi, munfiso ki natsu kiyi nazari kafin ki amsa mana” “Kin shirya”? Ɗaga mashi kai tayi alamar eh, duk tabi tasha jinin jikinta. “Da farko zamu so ki fada mana Ya akai kuka tsinci kanku A daji? Waye ya kai ku can? Sojojin kasar mu suna hasashen ɗan Ta’addan daya gudu zuwa canne Yai garkuwa daku don ya kare kanshi daga farmaki da suka kai mashi, shin dagaske ne ko kuwa? Ƙura masu ido ta yi ɗaya bayan ɗaya take kallon fuskokinsu, tsabar fargaba ƴan hanjin cikinta sai kaɗawa suke Yi, Tarasa Tayaya zata fara basu amsar tambayarsu? sam ba ta jin zata Iya faɗa masu ainihin Abunda Ya faru da rayuwarsu, ita aganinta kamar idan suka ji zasu guje su ne, musamman idan Danish Ya farka a matsayin giant ba ƙaramar masifa zaija masu ba, Zaiyi wuya su yarda da abunda zata faɗa masu, saboda Labarin baƙar izayar da suka sha a prison ba kowane zai gasgata kalamanta ba, zama su Iya tunanin ƙarya take yi masu, bayan haka tana tsoron ta fada masu, su kuma su tara Ƴan jarida su sanar dasu a ɗauki hotunansu ayi share da labarin prison tabbas yin hakan zai jaza masu babbar matsalar da zata Iya ja su rasa rayukansu don tasan dole Shuwagabannin kurkukun ƙaddara su bibiyi rayuwarsu ko dan saboda abu biyun nan na farko Garkuwar kurkukun da su ka gudu da shi, Na biyu don kada su tona masu asiri. duk da sanyin A.c dake ratsa fatar jikinta hakan bai hanata zubar da zufa ba, ta ko’ina take tsastsafo mata, Hakan ba ƙaramin ɗaure masu kai yai ba, farat ɗaya suka fahimci akwai wani gagarumin al’amari atattare da yarinyar sai dai zaiyi wuya ta iya sanar da su gaskitar zance. Gyaran murya Commender yai mata, A hargitse ta wurga eye balls ɗinta akan fuskarshi “Kin yi shiru baki ce komai ba meyasa”? Dafa kafaɗarta dr laura tayi da hannu ɗaya”Ki kwantar da hankalin ki my daughter, Ki natsu ki bamu amsa, a shirye mu ke da mu taimaki yaruwarku, haɗin kanki kaɗai muke buƙata, kuma muna tabbacin zaki Amsa mana tambayoyin mu” gaba ɗaya ta ruɗe saboda saƙe saƙen da zuciyarta ke yi mata, wani sashe Yana jan kunnanta akan karta kuskura koda gigin wasa tace zata faɗa masu abunda ya faru a rayuwarsu, Yayin da wani sashe na zuciyarta ke Jan hankalinta akan ta faɗa masu wata’ƙil su taimaka masu wurin kawo ƙarshen Azzaluman kurkukun ƙaddara, Yanzu idan ta 6oye masu taƙi faɗa masu gaskiya kwatsam wani abin da ba’a fata ya zo ya same su har su rasa rayukansu shikenan tarihin kurkukun ƙaddara zai cigaba da wanzuwa ne. Sun tasata gaba kamar sun sami tv, duk sun ƙagara da su ji amsarta, gashi taƙi buɗe baki tayi magana. “Idan har baki bamu amsar tambayoyinmu ba, zamu maida ku Dajin da muka ɗauko ku”! Acewar Major Ras Taji gabanta ya faɗi, Lokaci ɗaya ta fashe masu da matsanancin kuka mai ratsa zuciya Cikin shessheƙar kuka take faɗin”Ni bansan komai ba, Bazan Iya tunawa ba, Namanta komai, ɗan uwana danish shi ya sani” Ta ƙara rikita masu lissafi, Captain yace”kun haɗa baki ne? Mun tambayi ɗan uwanki Gabriel ya faɗa mana cewa ke kaɗaice kika san komai, Yanzu kuma mun tambayeki kince kema bakisan komai ba A tambayi Danish! Why kuke son Yi mana yawo da hankali....? Da alama Ya Hasala ne dan muryarshi a kausashe yake mata magana. Da sauri dr laura ta katse shi”Sir, bata da ƙoshin Lafiya, Ni a ganina bai kamata mu tsareta da tambayoyi ba a yanzu, ƙaramar yarinya ce sai ana lalla6ata” Sassauta fushin fuskarshi Yai, Cikin kwantar da murya yaci gaba da cewa”Okey, Share hawayenki, ki daina yi mana kuka bama so” Muryarta Na rawa ta amsa mashi da toh. Miƙewa Dr laura ta yi ta nufi fridge ta buɗe ta ɗauko mata fanta me sanyi, ta haɗo mata da tissue, Ta dawo gefen gadon ta zauna tare da miƙe mata tissue ɗin, Hannayenta na kerma ta kar6a ta soma goge ƙwallarta da hancinta, Bayan ta gama share hawayen dr laura ta miƙa mata lemun kar6a tayi tare da yi mata godiya. kamar tasan Mayyar fanta ce, Buɗe wa tayi agaban su ta kur6i ruwan lemun kusan sau uku tana sha, Sun tsareta da ido suna kallonta, hakan ba ƙaramin rikitar da ita yake yi ba. “Pls Masoyiya Angel, Ki taimake mu ki taimaki rayuwarki da ta sauran ƴan uwanki, Ki faɗa mana gaskiyar abunda Ya faru a rayuwarku wanda yai silar haifar maku da ciwon damuwa, Idan har baso kikeyi mu maida ku daji ba” acewar Captain. “Abunda mukeson sani shine Ya akai kuka tsinci kanku a ƙurmin dajin Evil forest? saboda ɗan ta’addan ƙasarmu da muke hasashen shine Ya kai ku can mun titsaye shi akan ya faɗa mana menene alaƙar shi da ku, Ya faɗa mana cewa Baisan komai dangane da ku ba, Ya taimaki wasu daga Cikin ƴan uwanku ne, Munyi dogon nazari akanku, da farko munyi tunani ƴan ƙasarmu ne ku, sai kuma muka ji kuna magana da wani harshe wanda bana nahiyarmu ba! Mun rasa gane daga wani Jinsi ku ke? sannan menene maƙasudin haddasa maku ciwon damuwa da baƙin ciki? lamarin ya ɗaure mana kai da ƙananun shekarunku? hada me fama da ciwon zuciya! Wani abun al’ajabin ɗaya daga cikin Ƴan uwanku yaƙi farkawa daga bacci mun rasa gane meke damun shi......” tun da major ya soma yi mata magana a tsanake ta tsare shi da ido tana kallon la66ansa har ya ƙare maganarsa, tukunna ta fara magana “Gaskiya ne abunda ɗan ta’addan ya faɗi, bashi ne yakaimu daji ba, Mun jima Acan kusan zance tun kafin mu mallaki Hankalin mu, bazan Iya tuna abunda Ya faru arayuwar mu ba, kome yakai mu Dajin, abunda na sani shine Munci baƙar wahalar rayuwa dani da ƴan uwana, wanda silar hakan yajaza mana depression....” Kallon Juna su ka yi, still sun fahimci bazata faɗa masu abunda suke son ji ba, sam bata son su sani babu alamun zata yarda da su. Murmushin gefen fuska Major ya sakar mata”Ni dama tunda naga idanuwanki da ƙaramin bakin nan Naki raina ya bani kina da wayau sosai,” duƙar da idonta ƙasa Ta yi zuciyarta na bugun uku uku. Dr. Laura sam ba ta so suka matsa mata da tambayoyi ba, tuntuni ta basu shawarar su bari Yaran su saba da su tukunna amma da yake Sojoji ne Yana ɗaya daga cikin Halayansu, Idan suna son jin bayani daga bakin mutun ba wani uziri da suke Yi mashi dolenshi ya amsa masu. “Yaren da ku ke yin magana da shi na wace ƙasa ne”? Captain ne Ya jefa mata tambayar. Muryarta na ɗan rawa ta furta”Ni.. geria” Tsabar mamaki ne yasa su kallon Juna. “Kina nufin daga Nigeria ku ke? Tayaya hakan zai yiwu? Dama Nigeria suna da farar fata ne acikin su? a iya sanina baƙar fatane mutanan Nigeria, Sannan matansu kuma basu da dogon gashi, kuma Launin idonki Kalar na mutanan ƙasarmu ne” Dr. Mark jockson ne Yai maganar da alamun mamaki akan face ɗinsa Dr. Laura na murmushi ta dube sa”kada ka bani kunya mana, ko mu a ƙasarmu ai akwai black americans, zai Iya yiwuwa suma suna da alaƙa da fararen fata ne ina nufin half cast” “Dagaske Ku ɗin Ƴan Nigeria ne? Jinjina masa kai tayi”Eh, ai yaren da muke yin magana dashi hausa ne na nigeria, zaku Iya bincikawa” Ba ƙaramin mamaki suka yi ba, Hatta turancin da yaran suke magana da shi sak Na america ne bana Nigeria ba. “Yanzu dai bazaki faɗa mana gaskiyar abunda ya faru da ku ba ko! To Shi ɗan uwan naki da kika ce yasan komai tayaya zamu Iya farkar da shi daga bacci”! Anzo dai dai wurin da tafi so, marairaice masu fuska ta yi”maganinshi Yana a nigeria, dan Allah ku taimaka ku maida mu ƙasarmu, idan ba haka ba ɗan uwanmu zai Iya mutuwa” hada ƙwallarta “Meke damun shi ne” Dr Brown ne yai mata tambayar, batare da ta yanke shawara da zuciyarta ba tace”nima bansani ba, Idan yafara bacci yana ɗaukar tsawon lokaci bai farka ba, to akwai maganin shi kuma yana acan ƙasar” Murmushi kowannansu ya saki, hakan yasa tasha jinin jikinta, Commender yace”Kin Iya acting, da farko kince bazaki Iya tuna komai daya faru a rayuwarku ba, amma ayanzu kin faɗi inda za’a samu maganin ɗan uwanki hakan na nufin tunaninki yana nan baki manta komai ba ko”? ɗaure mata fuska yai “Zaki faɗa mana gaskiya ne? Ko kuwa kunfi so mu je dake can headquater Ki amsa mana tambayoyinmu ta tsiya” tashin hankalin da ba’a sanya mashi date Maganar commender tayi matuƙar tsoratar da ita Jikinta Ya hau yin kakarwa duk tabi ta rikice, A ƙarshe data ga dagaske zasu titsayeta saita amsa masu tambayoyi ko su tafi da ita headquater, aiko da ƙarfi tasa wata irin gigitacciyar ƙara data firgitar dasu, Hannayenta Biyu ta sanya ta daddafe kanta tana faɗin”Nace maku ni bansan komai ba! Dan Allah ku maidamu ƙasarmu Nigeria, ɗan uwana zai Iya rasa ranshi, Na roƙe ku idan har dagaske zaku taimaki rayuwarmu to ku maidamu Nigeria wurin danginmu,” kamar mahaukaciya haka tadinga nanata masu akan su maidasu Nigeria. Hankalinsu Ba ƙaramin tashi yai ba, ganin yadda Ƙwayar idanuwanta suka burkice Launin Ciki Ya 6ace sai zallar farin idon, Jijiyoyin wuyanta dana Gaban goshinta shatunsu ya fito ruɗu ruɗu, Jefar da robar fanta hannunta ƙasa ta yi, a zafafe Ta miƙe saman gadon kamar ƴar daba, ta dunƙule hannayenta, taci gaba da ambaton Ku rabu dani ku ƙyaleni, Ku maida mu ƙasar mu Nigeria nace ku kaimu ƙasar mu, can muke son zuwa” Har suna haɗa baki wurin lallashinta”sorry ki kwantar da hankalin ki, zamu tafi yanzu, Ki daina kuka ki kwantar da hankali, Ki koma ki kwanta, babu wanda zai Ƙara tambayarki wani abu” sun firgita da ganin haukan Angel. Dr laura duk tabi ta ruɗe Sun rasa gane kanta. Kallon Sojojin ta yi”Pls, Ku ƙyale yarinyar nan, Muje office muyi magana, idan ba haka ba za’a Iya samun matsala” gyɗa kai sukayi ba don sunso ba suka Juya tare da fucewa daga ɗakin tare da Likitocin, Ya rage da ita sai Dr laura. “Pls My daughter kukan Ya isa haka, Ki koma ki zauna muyi magana kinji”? Lallashinta tashiga yi, Daƙyar Angel ke iya kallonta sumar kanta duk ta rufe mata fuska, dagangan ta ƙirƙirarma kanta Ciwon hauka. Marairaice mata fuska Angel tayi”dan Allah ki taimaka mana, su maida mu ƙasarmu, banaso mu rasa ɗan uwanmu zai Iya mutuwa, maganinsa yana can, Nayi maki alƙawarin idan ya farfaɗo zan fada maku duk wani abu da ku ke son ji dangane da mu” saukowa Angel tayi daga saman gadon, A sukwane ta zube saman gwiwowinta agaban Dr laura, Idanuwanta sun cicciko tab da hawaye take faɗin”Na roƙe ki Ki taimaka mana, kamar yarda Allah Ya taimake ki, Kice ma sojojin can sumaida mu Nigeria, Idan ba haka ba Ɗan uwana danish zai mutune, ba zaku Iya sarrafa shi ba, maganinsa yana acan, Ni na yarda ku sanya jami’an ku, su bimu can kasar don su shaida abunda na faɗa masu su sanya mana ido’ Muryarta ashaƙe ta ƙarasa maganar. Tsananin tausayintane Ya kama dr. Laura har cikin ranta ta aminta da yarinyar, Miƙa mata hannu tayi”miƙe tsaye” da sauri Angel ta ɗaura hannayenta asaman na dr laura, ta yunƙura ta miƙe, ba zato ba tsammani taji ta rungumeta a kirjinta, ƙamshin turarenta Ya daki hancin Angel sosai ta ƙankameta tana faman sauke ajiyar zuciya. Shafa sumar kanta dr laura tayi a hankali take yi mata magana “Ni tun farko banso suka tsareki da tambayoyinsu ba, sunyi gaggawar yin hakan, But Inaso ki kwantar da hankalin ki, Zanyi iyakar bakin ƙoƙarina wurin ganin sun maida ku ƙasar ku, idan har kikayi min alƙawarin zaku faɗa mana abunda ya faru da ku bayan ɗan uwan naki ya farfaɗo kamar yadda kika ce” Cikin sanyin murya Angel tace”Nayi maki alƙawari shiyasa ma nace su sanya jami’an da zasu bibiyi rayuwarmu” ta ƙare maganar tare da raba Jikinta daga na Dr laura Shafa fuskarta tayi”is ok, Zanje muyi magana da su yanzu ki koma ki kwanta ki huta” Amsa mata Angel tayi da toh, Bayan fitar dr laura, Daɗi kamar zai kasheta, don tana ji aranta zasu amince masu su koma Nigeria, juyawa tayi tana neman robar fantar data jefar a ƙasan tiles can ta hangota gefen nightstand zuwa tai ta ɗauko lemun ta koma gefen gadon Hankali kwance taci gaba da shan lemun fatanta Allah yasa su amince masu. Gaba ɗayansu sun Hallara a katafaren ofishin dr laura, Kowan nan su Ya samu wuri ya zauna saman haɗaɗɗun kujeru, table ne Ya ratsa tsakaninta da su,. “Shawarar da zan bada shine bai kamata mu takura masu da tambayoyi ba, duba da Yanayin yaran akwai ciwon damuwa atattare da su, tursasa masu zai Iya haddasa masu wata matsalar da bama fata” Dr laura ce ta kora jawabin idonta akan faces din sojojin Commender yace”Ya zamuyi kenan? Menene Mafita don muna buƙatar son Jin ainihin abunda ya faru da su a dajin nan” Numfasawa dr laura tayi”Munyi magana da yarinyar, tabbas bata manta komai ba, tasan abunda ya faru da rayuwarsu sai dai rashin yarda da tsoron fargabar abunda zai biyu baya idan ta faɗa mana sun Hana ta sanar damu, abun duba anan shine Babu yarda za’ae su saki jiki damu don ta yanzu, saboda basu sanmu ba bugu da ƙari kuma ba ƴan kasar mu bane, donni na yarda da maganarta, Idan har munaso muci nasara akansu dole sai mun yi masu abunda su ke so, ta hakanne zasu saki jiki damu har su faɗa mana gaskiyar abunda mu ke son ji daga gare su, sannan suna buƙatar wadda zata Kula da rayuwarsu tamkar mahaifiyarsu, Ta hakanne zasu saki jiki da ita har su Iya faɗa mata damuwarsu, abu na biyu shine Muyi masu abunda suke so! Musamman ita Angel din ta roke ni akan mu maida su ƙasarsu, Akan idonku kunga haukan da tayi mana tabbas akwai ƙamshin gaskiya a maganarta, tace maganin ɗan uwansu yana acan, kuma tace zamu Iya sanya jami’ae su bi su har can kasar sannan tayi alƙawarin idan harya farfaɗo zata faɗa mana duk abunda muke son ji. Shiru suka ɗanyi na wani lokaci kowan nan su Yana nazarin maganar dr laura. Numfasawa Major yai kafin ya soma magana”Me zai hana mu damƙa Case ɗinsu ya koma hannun Hukumar Isod? (Intelligence Special Operations Division) Tun da shugabansu Ɗan ƙasar Nigeria, su kaɗaine zasu Iya bincikar Ainihin abunda Ke faruwa da yaran, saboda suna da ƙwarewa a 6angaren. Jinjina kai Commender yai da alama ya gamsu da jawabin Major “Hakane ka kawo shawara mai kyau, case ɗin yafi dacewa dasu, Tunda Aikinsu ne Yin binciken sirri Harma da fafatawa idan ta kama kuma duk muna atare dasu banbancin kaɗan ne mu ba jami’an sirri bane su kuma duka sun Haɗa sunayin aiki a matsayin sojoji sannan kuma jami’an sirri” Captain Yace”Nima na goyi bayan hakan, amma fa zaiyi wuya mu iya samun chief ɗin nasu a waya, So the best way to contact him is through email, We need to start making our request for the case through their email, If they show interest in the case, we will turn everything over to them.” Commender yace”shugaban nasu ai Yana a Washington (babban birnin america) kuma naji raɗe raɗen kamar cikin weekend da zamu shiga zai bar ƙasar ya koma Nigeria, duk da bani da tabbaci kunsan aikin nasu na sirri ne babu mai sanin shiga da fucen su, Idan har muka samu ya nuna interest akan case ɗinsu komai zai zo mana da sauƙi, In yaso sai mu damƙa mashi Yaran ya tafi da su can, mu kuma zamu dinga bibiyarsu don jin ya ake ciki” Murmushi Dr laura tasaki, Har cikin ranta ba ƙaramin daɗi taji ba, Fatanta Allah yasa Chief ɗin Isod Ya amince da case ɗin Yaran, ko dan saboda Yarinyar da ta roƙe ta akan amaida su ƙasarsu” “Doctor, how long do you think it will take for the children to be discharged”? captain ne yai mata tambayar, Dr. Laura ta bashi amsa da cewa “After the three-day injection course is completed, we will be able to discharge them, Shima Ɗayan Yaron mai fama da ciwon zuciya Zamu Iya sallamar shi idan har aka Kiyaye sharuɗɗan da zamu rubuta na bashi kulawa ta musamman, “ ta ƙara da cewa”zasu Iya zama a asibitin namu har zuwa lokacin da shi chief ɗin zai Amsa mana buƙatar mu” Commender yace”dole ne mu sama masu wadda zata Iya kula da su tamkar ƴa’ƴanta kamar yarda kika bada shawara, wadda zata Iya tarairayarsu ta basu kulawar da zasu Saki Jiki sosai,” Yai maganar yana kallon fuskar dr laura Major yace”why not bazamu damƙa amanar kula da yaran a hannun UMMIN AMERICA ba? Tun da itama Ƴar Asalin ƙasar Nigeria ce, hatta yaren da naji Yaran suna magana da shi itama tana jin shi sosai” Jin Major Ya ambaci sunan Ummin america yasa Dr Mark da dr brown Kallon Juna ga dukkan alamu sun girgiza da jin an ambaci sunanta, Dr laura ta zaro ido tana faɗin” The Baddest mistress? There’s no way we can leave the children in her care, She’s a dangerous woman. How could she possibly know how to take care of them?” hankalinta bai kwanta da zancen miƙa yaran ga Ummin america ba saboda sanin wacece Ita. Bayan ta ƙare magana Major yace”Ai ba yau tafara Yi mana aiki ba, tana taimaka mana sosai akan irin case ɗin nan, Ina da tabbacin zata Iya! Fiye da yadda baki tsammani”Kwa6e fuska Dr laura Tayi don ita har aranta Fargabar Ummin americe take ji, Kowa yasanta sananna ce a 6angare Iya karuwanci tantiriyar ƴar bariki ce, tayi ƙaurin suna america shiyasa su ke yi mata laƙabi da Ummin america, tsabar Iya shaiɗancinta har award ake bata akan Iya Karuwanci. “Mu zatayi ma aiki, bai shafi sana’arta ba, Kawai munaso Yaran su kace a hannunta amatsayin guardian ɗinsu, Kafin Mu damƙa mata su zamu yi yarjejeniya da ita idan har ta amince to lafiyalou ba zamu samu matsala da ita ba” ta6e baki dr Laura tayi”amma dai ba’a asibitin mu za’a gayyato mana ita ba, Don ina jin fargabar ta rikitar mana da ma’aikatan mu da surar jikinta” Gaba ɗaya suka sanya dariya jin abunda tace, ta faɗi hakanne don tasan Ummin America kamar maganaɗisu take awurin Iya jan hankalin mutun da surar Jikinta, Dirine da ita na bala’e’ Sunjima suna tattaunawa a tsakaninsu kafin daga bisani Commender yace “Dr mun gode sosai da shawarar ki, Zamu koma bakin aiki Yanzu, Idan har Chief din isod Ya amince da buƙatar mu zamu tuntube ku” Daga haka Sojojin sukayi Ma Dr laura sallama, Har bakin parking space na asibitin ta rakosu, Bayan tafiyar sojojin suka dawo Cikin asibitin. *Boss Bature✍️ Mu haɗu gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*KURKUKUN ƘADDARA*_ ~Middle step~ _The Prisoners E18🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* *DAULAR OBIE ESTATE* A katafaren ɗakin Hajjaty head maids ta gidan obinna, tsabar haɗuwarsa tamakar bana ƴar aiki ba. fitowar kenan daga bathroom, ga dukkan alamu wanka tayi, ta ɗaure ƙirjinta da towel fari, iya gwiwar ƙafafuwanta ya tsaya mata, fatarta da lemar ruwan wankan da ta yo, a gaban mirror ta tsaya tana kallon kyakkyawan fuskarta har yanzu akwai sauran make-up ɗin jiya da ta yi jan bakin bai goge ba, don ita bata rabo da kwalliya a fuskarta. Har ta miƙa hannu zata ɗauki man shafawarta cikin jerin mayukanta, ba zato ba tsammani muryarshi ta ratsa kunnanta”My heart beat” ras taji gabanta ya faɗi, sam bata ji shigowarshi ba, A hargitse ta yi saurin wurga idonta kan fuskarshi Yana daga kishingiɗe saman gadonta, farar singlet ce a jikinsa da short. Hankalinta ba ƙaramin tashi yai ba, muryata na rawa ta furta sunan shi”PRAVIN”! Dafe kai tayi da hannu ɗaya, tsananin fargaba ne ya kamata. “Nashiga uku, why Pravin meyasa zaka yi min haka! Kana so ne kaja min bala’e? Yanzu idan wani ya faɗo ɗakin nan me kake tunanin zai biyo baya”? A ruɗe ta ke yi mashi magana tana faman zazzare dara daran idanuwanta, “Haba pravin baka min adalci ka riga da kasan ko’ina na kusurwar gidan nan cctv ne za’a iya ganin duk motsin ka” Tun da ta fara magana, Pravin ya tsareta da manyan idanuwanshi, har sai da takai Aya, tukunna Ya sauko daga saman gadon ya nufe ta kamar wani zaki, dab da ita Ya tsaya ƙamshin turaren jikinsa ba ƙaramin Illa Ya ke yi mata ba tuni ta fara shiga yanayi. “My honey, ni ban zo donna 6ata maki rai ba, haƙƙina nake so, Nakasa jurewa ina buƙatarki, kinsan bani da haƙuri in dai akan buƙatar kaina ce, sannan ki kwantar da hankalin ki, babu wanda yasan na shigo ɗakin ki, daga ni sai ke” Ya ƙare maganar yana faman sakar mata shu’umin murmushin nan nashi, Idanuwanshi akan ƙirjinta da suka tsone mashi ido. Jikinta sai kerma yake yi kamar wadda sanyi ya kama, tana matuƙar jin tsoron wani ya faɗo masu a ɗakin, ita kanta a buƙace ta ke da shi tana son kasancewa da shi sai dai tana tsoron wani ya gansu. Still sautin muryarta adabarbarce take furta”Pravin ni ina fargaban wani ya gan....” bata kai ga ƙarasa maganar ba, yai saurin zura harshen shi acikin ƙaramin bakinta, hannayenshi biyu ya ɗaura saman manyan mazannanta ya ci gaba da murzasu, nan take numfashinsu ya fara hauhawa yana fita da sauri sauri alamun sun fara hawa kan network, ko’ina na jikinta ya ke bi yana matsawa da hannunsa, Sosai yake kissing ɗin ta tamkar zai cire mata la66anta, Zame tongue ɗinsa yai daga bakinta, tun daga kan wuyanta ya fara manna mata hot kiss har izuwa ƙirjinta, ya warware towel ɗin da tayi ɗaurin gaba dashi gefe ɗaya ya jefar da shi, gaba ɗaya ya ɗauketa ya jefar saman gado, doguwar sumar kanta tuni ta tarwatse saman mattress, Ya sanya hannu ya zame Singlet ɗin jikin shi Ya haye saman gadon Yaja bargo Ya ƙudundune su, To jama’a nidai bansan me sukeyi a cikin bargon ba, na dai ji sautin gurnaninsu tamkar namun nawa na fafatawa. Bargon da suka lullu6a dashi sai yamutsewa yake yi yana motsi kamar ana dambe a cikinsa, ba yau bane karo na farko da ya fara biyan buƙatarshi da ita ba, sam basa gajiya da juna pravin da divya wato hajjaty, Babu wanda yasan suna harƙalla atsakaninsu. (To fa, akwai gwarama yasin Ana wani abu agidan Obinna, Ko ina hajiya saratu taje? Ana nan za’a 6ata mata tarbiyar Miji🤣) A hankali danƙareriyar Motar Hajiya saratu ta kunna kai Cikin Villa dinsu adai dai parking space security ɗin da ke driving nata yai parking na motar, Da sauri Ya fito daga driver seat Ya zagaya Ya buɗe mata ƙofa, ta zura ƙafarta dake sanye cikin High hills, dawowarta kenan daga meeting da suka yi a ministry of Health tare da manyan ministocin Kiwon lafiya da suka kawo masu ziyara daga Who (world health organization) don inganta Lafiya. Tsadadden leshi ne fari a jikinta, riga da zani daga sama ta ɗaura lap coat, fararen idanuwanta na amanne da glass fari matar fa akwai Iya ɗaukar wanka, ta ko’ina Jikinta ƙamshi yake fitarwa. Saukowa ta yi daga Cikin motar, da sauri ta nufi cikin gidan hannunta ruƙe da hand bag ɗinta, duk inda ta gifta masu aiki ne ke safa da marwa, cikin girmamawa su ke gaishe da ita, idan ta gama dama ta amsa idan bata ga dama ba sharesu take yi. A katafaren Main palour na gidan ta shigo, Tafkeken gaske A ƙalla Yana ɗauke da Royal sofas two set saboda faɗinsa. “Sannu da dawowa Hajiya” muryar Safa ce ta dakatar da ita daga Yin tafiyar, Fuskarta babu annuri a ɗaure take tamau kamar wadda aka 6ata ma rai”Pravin Ya dawo ne”? Tambayar da ta jefa mata kenan. “Bani da masaniya, da ya ke mu na yin aiki a kitchen ne bansan ko ya dawo ba” Gyaɗa kai Hajiya saratu ta yi”Okey, zan shiga ɗakin baba, kafin in dawo ki tabbatar kin kai min lunch ɗina a ɗaki, bana son 6ata lokaci” amsa mata tayi da toh hajiya. Da sauri safa ta nufi kitchen don ta shirya mata abincin. Kaitsaye hajiya saratu ta nufi sashen obinna. Tana gab da zata shiga ɗakin Dr jazz ya fito Yana sanye da suit black colour. Ko da suka haɗa ido da ita gabansa ba ƙaramin faɗuwa yai ba. Muryarshi asanyaye ya furta”ina wuni mommy” harara ta wurga mashi “Kai bana ce kar na kuskura na ƙara ganinka acikin gidan nan ba? wannan wata irin mayuntaka ce? Meye haɗinka da babanmu”? Tafa Hannu ta yi haɗi da ruƙe ha6a. Muryarshi adabarbarce ya furta”ai ba anan nake zaune ba tun lokacin da ki ka ce bakison ganina, na koma gidan daddy da zama...” daƙyar ya ida maganar ganin irin ƙasƙantaccen kallon da take wurga mashi. “Uban waye daddyn naka? In banda yaudarar kai yaushe Yaya mubarak ya zama uban ka? Kai fa ba ɗan kowa bane a family ɗin nan, ka daina ɗaukar kanka wani shege, ai tun ranar da aka faɗamin cewa hada kai ake tsegumin ƴa’ƴana, naji na ƙara tsanar ka matsiyacin banza, in banda zaƙewa da shisshigi da kutsu da samun wuri irin na ɗan talaka ina kai ina haɗa kafaɗa da masu asali a dangi eyeh? A faɗace take yi mashi magana tamkar zata rufe shi da bugu, Bawan Allah dr jazz tuni hawaye sun cicciko idon shi. Ta6e baki tayi”dallah jibarka, sai uban tsawo kamar fal waya ba ƙiba, duk irin arziƙin da ku ke ci a ƙarƙashin inuwar mu har yau baka ƙara komai ba, Sai Iya gulma da munafunci shashasha kawai, dallah ni bani wuri in wuce kar na ham6are ka” jiki na rawa ya matsa mata hanya, ta shiga ɗakin obinna. Idanuwanshi sun kaɗa jawur, babu mai yi mashi gori irin hajiya saratu ƙiri ƙiri take nuna ta tsane shi, sam ya kasa motsawa saboda jirin da ke shirin ɗibarshi, a hanzarce ya dafe bango da hannu ɗaya, Ƴar ƙwallar da yake 6oyewa tuni ta gangaro saman kuncinsa, a hankali yake cizon pink lips ɗinsa haɗi da lumshe idanuwanshi. “JAZZ”! Ras Ya ji gabanshi ya faɗi sam bai ji takun tafiyarsu ba, a fakaice Ya zaro hanky daga trouser pocket ɗinsa Ya share ƙwallarsa, Kafin ya ɗago yana kallonsu. Turai ce mahaifiyarshi tare da Sir mubarak sun shigo gaida baba, jallabiya ce a jikinta ta yafa mayafi akanta, Sir mubarak yana sanye shima da jallabiya ta maza. Hankalinta ba ƙaramin tashi yai ba ganin damuwa akan fuskarshi “Jazz lafiya naga kamar idonka ya canza launi”? Girgiza mata kai yai”bakomai mommy am ok, idona ne ke yi min ciwo, yanzu nike shirin zuwa gida.....” Sir mubarak ne ya katse mashi hanzarinshi. “Jazz meke damunka ne? Sai kace wani ƙaramin yaro? Idan ba ka da lafiya baka san Hanyar zuwa asibiti bane? Ba za ka je aduba maka idon naka ba”? Cikin sanyin murya yace”zanje in sha Allah, nagode da kulawar ka daddyna. Hankalin turai bai kwanta da abunda ɗan nata ya faɗa mata ba, Matsawa tayi kusa dashi, ta ruƙo hannunshi acikin nata “My Son, ka je gida ka kwanta ka huta, idan muka dawo zamuyi magana” cikin kulawa take yi mashi magana Amsa mata yai da toh mommy, bayan yayi masu sallama ya kama hanyar fita daga gidan. Hajiya saratu na zaune saman carpet, sir mubarak yai sallama hannun shi ruƙe dana matarshi, daƙyar ta amsa masu sallamar, A saman doguwar sofa ɗin ɗakin suka zauna, hakan ba ƙaramin ƙona mata rai ya yi ba, ganin ita ta zauna saman carpet su kuma sun Haye saman sofa. “Yaya mubarak Ina wuni, Ya iyali” “Lafiyalou saratu, Ya naki aikin ya kuma Iyali”Alhamdulillah” ta amsa mashi Sir mubarak yace”baba baya nan”? Yai maganar yana bin ɗakin da kallo Hajiya saratu tace”ya shiga toilet ne, shine yace min Injira shi” sir mubarak Ya furta Okey, ina mijin naki na shigo gidan ban gan shi ba, Ko ya tafi office ne” yai tambayar ne don yasan aikin nasu na Companynsu har Saturday suna zuwa banda sunday and Friday. “Tun da safe muka rabu da shi, yana shirin tafiya office, bai dawo ba ne” Ran turai ba ƙaramin 6aci rai ba, ganin hajiya saratu da tayi a ɗakin obinna ya tabbatar mata da cewa Itace silar halin da Jazz ya shiga, batun yau ba tasa ba yi mashi gori. “Saratu Baki gaishe da Auntyn taki ba” kamar yayi magana da bango, Ta haɗe fuska ba annuri Da ɗan tsawa Sir mubarak Yace”Saratu baki Ji ina magana bane” sai da ta mula tasha iska tukunna tace”yaya ai bani ya dace in fara gaishe da ita ba, saboda ni ce agaba da ita,” Ran Sir mubarak ya 6aci, zuciyarshi ta motsa, Tsawa ya daka mata har sai da turai ta zabura saboda firgitar da tayi. “Kada ki kuskura ki bari in sake nanata maki! Nace ki gaishe da ita tunkafin na 6ata maki rai” sanin halinshi yasa ta wurga ma turai harara kafin tace”Ina wuni matar yaya” Cikin sanyin murya ta amsa mata Lafiyalou. Fitowa Dattijon arziƙi yai daga toilet, jikinsa sanye da jallabiya, dogon gemunsa kamar ana ƙara mashi tsawo fari fat, fuskarshi ɗauke da murmushi yake binsu da kallo “Gayu mutanan Allah, wa nake gani kamar turai? Rufe fuska turai tayi da mayafin jikinta, Sir mubarak na murmushi yace”yau surukar taka tazo gaidaka, tun ɗazu da safe tasa naci akan saita shigo, nace tabari mu zo atare” “Amma nayi farin ciki, ni nasan ɗiyata tana son zuwa duba babanta, kaine dai ka hanata zuwa mubarak, Allah ya kamaka, dama Ana kawo min tseguminka, akan ƙuntata mata da ka ke yi kana yi mata kulle agida” Ƴar dariya Sir mubarak yai yana faɗin”gaskiya kowaye ya faɗa maka haka baba to ka bincike shi, Ni nasan ma baya wuce Jazz ne, Aiko inda shine yau a headquater zai kwana” Dariya suka sanya banda hajiya saratu data ɗaure fuska, muryarta aƙula ta soma magana “Baba dama na shigo ne don in gaishe ka, inaso zan wuce” Ganin tana yunƙurin miƙewa sir mubarak yai saurin dakatar da ita ta hanyar yi mata magana”Koma ki zauna sarkin fushi, indai saboda mune kike ta 6ata fuska yanzu zamu koma gidanmu,” ya ƙarasa maganar tare da kallon Baban nasu, hankalin shi na akan fuskar saratu “Zamu wuce baba” “Ban gaji da ganinku ba, ku zauna muyi fira mana” acewar Obinna “Auta Ya meeting ɗin naku? Yamutsa fuska tayi”lafiyalou, baƙin har sun tafi, shiyasa na dawo gida” “Masha Allah,” ya ambaci hakan tare da shafa gemunshi “Ya shirye shiryen tarbar baƙinmu na gida da zasu zo? Ko kun manta da shagalin da zamuyi ne”? Sai lokacin Saratu ta sassauta fushin fuskarta jin anzo inda tafi so”A’a baba taya zamu manta da rana mafi mahimmanci agaremu ranar da mahaifinmu abun al’faharinmu yazo duniya,” Kalaman saratu sun faranta mashi ranshi. Sir mubarak yace”Ai nafi kowa zumuɗin ranar tazo baba, naso ace ni aka ba damar ɗaukar ɗawainiyar duk wani abu da za’ayi a ranar, sai dai kash Hateem yai min kutse, gaskiya ban ji daɗi ba, Haka last time Sharafuddeen ne ya ɗauki nauyin gudanar da shagalin” Da murmushi akan fuskar obinna yace”ai ba wani abu, dakai da su din duk abu ɗayane awurina, ina matuƙar alfahari da ku, kuma Inajin daɗin yadda kuke nuna mini ƙauna” Ya ƙare maganar tare da kallo Turai, da zolaya yace”Surukar wannan karon wani kalar wanka zaki ɗauka”? Duƙar da kai ƙasa tayi fuskarta ɗauke da murmushi. Hajiya saratu tace”anko ne zamu fidda ae, zanyi magana da zahra ɗaya daga cikin matasan Yaran da suka yi mana decoration lokacin birthday din twins, ta ƙware wurin iya tsara anko in yaso ma sai su yi mana decoration ɗin” Jinjina kai Obie yai’naji daɗin jin haka, nima na yaba da aikinsu, yarinyar da kike magana akanta ai na ganeta ƴar gidan ɗan Iya ce, suna da mutunci mutanan kuma mahaifinta yana yi mana hidima sosai, Yakamata ayi masu magana da wuri, tun da mun shiga watan” “Insha Allah idan na koma ɗaki zan Kira zahran awaya in sanar da ita, amma baba kowa da kowa zai hallara ko? Dan banason inga babu wani adanginmu” Sir mubarak yace”dolensu ma su zo ai, ƙwan su da kwarkwatarsu, babu wanda zamu yi ma uziri acikinsu, da na gida nigeria da na ƙasar wajen kowa zai zo, Inyaso mutun zai Iya komawa aranar da yazo don wlh bamu raga ma kowa, just rana ɗaya kacal zamu taya mahaifinmu birthday, banga dalilin da zai hana mutun zuwa ba” a tsanake obinna ke kallonshi, yana matuƙar jin daɗin girmama shi da su ke Yi. “Ku kwantar da hankalinku, in sha Allah kowan nan su zai zo, munyi waya da lateef da abdul razak duk sun tabbatarmin da zuwansu, dama ni banida matsala dasu, Mutun ukun nanne suka fi shiga busy, sharafuddeen da Hateem inayi masu uziri sosai saboda yanayin aikinsu, to su dinma dai Alhamdulillah sun tabbatarmin da zasu samu damar halatta, hada sauran jikokina owais dai ne bani da tabbacin zai zo ko kuwa, har yau dai bansamu wayarshi ba,” muryarshi da rauni ya ƙarasa maganar. ta6e la66a hajiya saratu ta yi aranta tace”sai kace wani ɗan gwal duk yabi ya dami kanshi akan owais, kamar shi kaɗai ne jikanshi” Muryar sir mubarak ce ta fargar da ita daga yin zancen zucin”indai owais ne yana sane da wannan ranar mai muhimmanci, duk mun busy din da zai shiga bazai manta da ranar nan ba, saboda ƙaunar da yake yi maka, don haka ka kwantar da halinka baba, In sha Allah Jikanka zaizo. Nauyayyar ajiyar zuciya obinna ya sauke, zallar farin ciki ne kwance akan fuskarshi har ya ƙosa ranar ta ƙaraso ko dan yaga Jikanshi daya daɗe yana mamarinsa. “Baba Ni zan wuce ciki” hajiya saratu ce tayi maganar a yayin da take miƙewa tsaye tana gyara mayafinta. “Har mun gama magana”? Ya jefa mata tambayar, murmushin yaƙe ta ɗan saki”inaso ne in shiga ciki, namanta na sanya mai aiki ta kaimin abinci, idan naci na huta zan Kira zahran awaya duk yadda muka tattauna da ita zanzo na sanar maka” Gyaɗa kai obie yai”nima nafi so ki huta autana, ki ci abinci ki ƙoshi idan takama ki kwanta kiyi bacci” dariya ta dan saki tana kallon baban nasu, maganar shi ta tuna mata ƙuruciyarta, shi dai burinshi saratu taci abinci ta kwanta ta huta idan ta dawo daga makaranta, bayason tana aikin wahala. “Nagode da kulawarka akaina baba, Allah yabar mana kai abun alfaharin mu” Amasa mata yai da amin, Juyawa tayi ta kalli Sir mubarak da turai “Ni zan wuce yayana, a huta lafiya” bata jira amsarsu ba, da sauri ta fuce daga ɗakin. Bayan fitarta, tattaunawa suka cigaba da yi game da yadda za’a tsara komai na shagalin da za su yi. Tun da ta shigo ɗakin, komai na ciki agyare ta same shi, Safa ta kawo mata lunch ɗinta yana asaman table ta ɗaura mata shi. Cire lapcoat din jikinta tayi a saman Hanger ta sagala ta, shaf shaf ta canza kayan jikinta zuwa, rigar shan iska, daga bisani ta koma gefen gadon ta, ta zauna domin cin abinci, farawa da bismilla ta kai hannu ta damƙi haɗaɗɗan cup na cofee ta kur6e shi, bayan ta gama ta soma shan farfesun naman kaza da zafi zafinshi, cikin ƙanƙanin lokaci ta shanye shi ta kuma damƙar Chips ta cinye ta cakumi cheese burger ta tura abaki hankalinta kwance take cin abincinta. Ringing ɗin wayarta ne ya janyo hankalinta ga duban hand bag dinta dake ajiye saman pillow. Ba ta yi niyar ɗaga kiran ba, don ita a ƙa’ida bata picking call idan tana cin abinci saita kammala, hakanan dai tayi ra’ayin duba me kiranta, tissue ta yaga ta goge bakinta, kafin ta yunkura ta ruko handbag din, duba sunan me kiran nata tayi sunan ya fito 6aro 6aro asaman screen ɗin iphone ɗinta *Princess Mujeedat* murmushi hajiya saratu ta saki da zumuɗi ta ɗaga kiran cikin harshen turanci ta soma yi mata kirari “Uwargidan shugaban ƙasar Kanada, Gimbiya mai jiran gado ta Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa! Sarauniya ɗaya tilo da ke mulkin zuciyar Yaya Hateem, Wuu hu huu! ina gwanar wata ga tawa, Uwar gida sarautar mata daga ke babu ƙari mun kulle ƙofa” sautin ƙayataccen murmushin gimbiya mujeedat ne ya karaɗe kunnuwan saratu, da alama taji daɗin yabon da saratu ke yi mata. bayan ta gama yi mata kirarin ta ɗaura da cewa”Habawa auntyna nayi fushi Allah, sai yau aka tuna dani, ai amana batace haka ba fisabilillah, daga ke har Yaya hateem ɗin baku tunawa da mutane sai wanda ya taka yaje inda ku ke” (idan kaga hajiya saratu na magana da mutun fuskarta asake to koma wanene ba ƙaramin mutun bane, babban gorone magogin ƙarfe dai dai da ita koma fiye da ita, zaranne yai dai dai da kalar yadin🤣) Ni kaina da naji muryar mai magana saida naji shock, kai daga jin voice ɗinta zaka shaida jinin sarauta ce, gaba da baya, Jinin arziƙi waɗanda suka gaji abun, da izza da dattako ta ke yin magana tamkar bata son furtata. “Ba abun da ki ke tunani bane ƙanwata, ban manta dake ba kina araina shiyasa ma na kira don mu gaisa” itama da turancin ta mayar mata da amsa don ba ta jin hausa. “Duk da haka ban sauko daga fushin ba, gaskiya idan kinason mu shirya ki biyo yaya hateem kuzo Nigeria taya murnar birthday din baba, nasan halinki bakison taka ƙasarmu” fuskar hajiya saratu awashe take yi mata magana. “Naji daɗin kirarin da ki ka yi mini, shiyasa a kullum nike ƙara godewa Allah daya bani surukai nagari irinku, wannan abun alfaharine, haƙika ban ta6a danasanin auran hateem da nayi ba, saboda tunda muka kasance a ƙarƙashin inuwa ɗaya har Allah ya azurtamu da samun zuri’a ban ta6a samun matsala da shi ko dangin shi ba, Kuna nuna min ƙauna sosai nima Ina sonku” Hajiya saratu baki yaƙi rufuwa, sauran burger din dake abakinta tuni ta ƙarasa haɗiye ta, dadi take ji yau gimbiya mujeedat ta kirata awaya. “Me kike ci ne? Naji bakinki acunkushe da wani abu, wato har yanzu ƙanwata baki daina ciye ciye ba ko”? Tuntsirewa hajiya saratu tayi da dariya annurin fuskarta sai ƙara nunkuwa yake yi. Mamaki takeyi yarda Gimbiya mujeedat keyi mata magana matar da saboda izzarta idan ka kirata awaya bata picking sai ka fara tura mata text message ka nemin iznin yin magana da ita, idan taga dama zata baka reply akan ka kirata a lokaci kaza, amma muddin mutun ya kira layin mujeedat batare da ya fara neman izni ba to bata ɗaga kiran nashi. *A GIDAN ƊAN IYA* Idan muka koma 6angaren su Aneeleeh tun ajiya Hajiya adama da Uncle abdallah suka sanar da su game da zancan komawarsu gida, Abie yace bazai yiwuwa ba su ɗan ƙara kwanaki mana, Anan uncle abdallah Yake sanar dasu cewa Ai sun samu gidan da zasu zauna a abuja ya 6oye ne bai sanar dasu, harma ya samu aiki a companyn sharufuddeen, ba ƙaramin farin Ciki su ka yi ba sun tayashi murna sosai, musamman da suka ji cewa bazasu raba Aneelerh da junaid ba ko da yakai shekarun da zasu Iya kar6ar shi ne, Zasu haƙura ne har Allah ya bayyanar masu da su Uzair, dama rashin ɗan nasu ne yaja har suke son kar6ar shi, Aneelerh hada kukan farin Ciki, Ta ƙara jin son surukan nata, ba ita kaɗai ba hatta su mami sun ji dadin ziyarar da suka kawo masu sun kuma jinjina ma ƙoƙarinsu na barma Aneelerh ɗanta, su kansu sun fahimci ba ƙarami so suke yima yaron ba tun da gashi ta dalilinsa sun dawo abuja da zama, ba su kai ga barin gidan ba, abie ne ya dakatar da su yace su ɗan jira akwai malaman da zai sanya su yi masu safkar alƙur’ani a sabon gidan su, hakan ba ƙaramin daɗi yai masu ba, don su basuyi tunanin yin hakan ba. Hankalin Mahboob yaƙi kwanciya tun da yayi tozali da hoton Angel, a daren ranar daƙyar Ya iya runtsawa, saboda fuskarta da ke yi mashi gizo, ya kwana da mamakin baiwar Kyan da Allah Yayi ma yarinyar, bai ta6a ganinta ido da ido ba sai dai ahoto yasanta tun tana ƴar ƙaramarta, Aneelerh take ɗaukar ta hoto da video tana sanyawa a status dinta to anan yasanta, a ƙarshe daya gaza haƙara bayan sun dawo daga sallar asubahi, ya lalla6a yaje ɗakin aneelerh, tsabar Iya fadanci hada Kiranta da aunty, bai ta6a kiranta hakan ba sai yau da Allah ya jarabe shi da son sanin komai dangane da Angel. Tambayoyi ya tsare Aneelerh da su akan ta fada mashi dagaske yarinyar mutunce bata haɗa jinsi da aljanu ba? Don shi gaskiya bai yarda da kyanta ba, Ya zarce na jinsin mutane, tun da yake kallon indian film, da korean drama bai ta6a ganin jarumar da ta kama ƙafar Yarinyar a kyau ba. Aneelerh taci dariyar wautar Mahboob, har tambayar shi ta yi ko dai sonta ka ke yi ne? Naji kanata zuzuta kyawunta, “ da sauri ya dafe ƙirjinshi da hannu Yana faɗin”Sai kace dai bani da hankali aunty Aneelerh? Ae rijiya ba wurin gaɗar makaho bane, Nasan ciwon kaina ban shirya yin jinya a gadon asibiti ba, ni kawai kyanta ne ya ruɗe ni ba wani abu ba, tsakani da Allah yarinyar ba matar yaku bayi bace, ko makaho ya shafa fuskarta zai shaida hakan tafi dacewa da Manyan ƴa’ƴan masu kuɗi waɗanda suka jiƙe da naira, ni yanzu idan nace zanso ta, ko zan aureta, Aunty Aneelerh ina zan samu kuɗin ɗaukar ɗawainiyarta? Kuɗin man shafawarta dana zuwa saloon kaɗai sun isa su takaita jarin mutun balle ni da ba kuɗi gare ni ba” tsabar dariya Aneelerh hada hawaye, shiko fuskarshi a daure yayi mata maganar bada wasa ba, ya ƙara da cewa”ƙwara na auri ƴar talaka wadda ba ta da tsayin gashi, sai yafi min sauki, in manna mata ƴar naira ɗari biyar taje gidan kitso ayi mata, man shafawa a jiki kuma Ko vaseline na siya mata ya wadatar, Iya kuɗin ka iya shagalin ka, Amma wannan Ifritun yarinyar wlh aunty Aneelerh duk talakan da ya aureta ya cuci rayuwarta, yasin ni har kotu zan Iya kai ƙarar shi, ita kanta idan ta auri talaka batayiwa kanta adalci ba fisabilillahi. Lamarin mahboob sai addu’a, Haka ya dinga santin kyan Angel, Har faɗi yake shi ya kosa A gano su, in sha Allah zai tayasu da addu’a akan Allah ya bayyanar dasu, burinshi idan Allah yasa ta dawo gidansu da zama zai zama na hannun damanta saboda idan ta auri basarake ko wani mai ji da naira, ya dinga samun ƴan canjin kashewa. Saboda Angel Ya manta da zancen neman zoben shi, gaba ɗaya ya ɗaura burin duniya akan Angel, harya fara ƙiyasta kuɗin da zai tatsa wurin Mijin da zata aura. Daƙyar Aneeleerh ta samu mahboob Ya fita daga ɗakinta, ya addabeta da zancan kyawun Angel. Alhamdulillah, a yau labarin 6acewarsu Angel ya dawo tamkar sabo a shafukan sada zumunta, ta ko’ina buga labaransu Akeyi tare da hotunansu, tun da Ont suka fara yaɗa labarin nan take sauran gidajen jaridu suka bubbuga labaran da gidan radio. Ta ko’ina zancen su akeyi kamar yau abun ya faru, labari ya dawo sabo, Yanzu shine Top story dake trending a social media, mafi yawan mutane Kyawun Angel ke ruɗarsu har su kaiga ɗaukar labarin su karanta sannan suyi share ɗinshi don ataimaka a gano su. Fuskar Aneelerh tun safe da annuri akanta, Mutane sai kiranta sukeyi awaya sunayi mata jaje haɗi da tambayarta wasu bayanai da suka danganci Angel, a ƙarshe sunayi mata fatan Alkhairi, Numbobinsu ne akan labaran da akayi share nasu shiyasa mutane ke ta kiransu suna yi masu jaje. Ta natsu saman mirror chair, turkish gown ce a jikinta launin maroon tayi bala’en yi mata kyau, babu mayafi akanta zallar sumar kantace Hannunta na aruke da wayarta, tun ɗazu take maimaita karanta labarin su Angel da akayi posting ɗinsa a shafin Ont na insta “Mommy” muryar junaid ce ta janyo hankalinta ga kallonshi, ta cikin mirror, Hajiya adama tayi mashi gayu don yau ma a ɗakinta Ya wuni, ita tayi mashi wanka, tasa Aneelerh ta kawo mata kayan shi ta santa mashi jeans da shirt fara, sumar kanshi tasha gyara. Ƙarasawa yai gaban kujerar da take a zaune, ya daura kanshi saman laps ɗinta, ƙamshin turaren jikinsa na Hajiya adama ne da ta shafa masa ‘Wow my baby boy, kayi min kyau sosai, lallai granny ɗin nan taka tana matuƙar sonka irin wannan gayu haka da tayi maka” Ɗaura wayar tayi gaban mirror, ta sanya hannu biyu ta ɗago da junaid ta ɗaura shi saman laps ɗinta, langwa6ar da kanshi yai saman kirjinta “Mommy namanta ban faɗa maki ba, jiya wani mutun ya kira awaya har yace wai in faɗa maki....” katse shi tayi”yaushe aka kirani? Bana son ƙarya fa” Muryarshi da shagwa6a ya ce “mai ƙarya fa ɗan wuta mommy, ni dai Allah ba ƙarya nake maki ba” miƙa hannu Aneelerh tayi ta ɗauki wayar, tana shiga call logs tayi arba da New number da aka kira kuma an ɗaga kiran. “Junaid bana hanaka ɗaga min kira ba”? Zumbura mata maki yai’to ai nayi tunanin Angel ce ke kira, kuma baki a ɗakin shine na ɗaga, kuma yace in kai maki wayar ku yi magana ni kuma naƙiya nace sai dai ya faɗamin in gaya maki” tun da ya fara magana ta ƙura mashi ido tana kallon shi, komai nashi burgeta yake yi, musamman in yasanya shagwa6a a maganar shi. “Meyasa baka kawomin wayar ba”? Ƙura mata ido yai ba tare daya furta kalma ba Sam hankalinta bai kwanta da baƙuwar number da ake yawan kiranta da ita, tuntuni take ganin missed calls daga Number taƙi yarda ta ɗaga kiran don har yanzu bata daina fargabar mutanan nan da suka ɗauketa da sunan jami’an sirri. “Junaid, daga yau karka kuskura ka ƙara ɗaga min kira kaji ko”? Ɗaga mata kai Yai alamar eh, tace”yanzu zan sanya number ɗin a black list, hankalina zaifi kwanciya’ ta yi maganar a yayin da take cigaba da daddana wayar hannunta, blocking number din tayi saida ta kammala baby junaid yace “Mommy namanta ban gaya maki ba yace wai in faɗa maki daddyn um am....” natsuwa ta yi tana kallon shi, “What”? Shine yace min wai ince maki daddyn ummm...” sam ya kasa tuna sunan duk ta ƙagara da sonjin ƙarashen sunan “Kai nake sauraro ka fadamin mana” “Wai ma daddyn.....” girgiza kai ya ɗanyi”mommy kaina ya cunkushe na manta, idan na tuna zan gaya maki” Murmushine shimfiɗe saman la66anta, Idanuwanta akan face dinsa “Shikenan My baby boy, yanzu faɗa mun Ina ka 6oye zoben Mahboob? Na duba cikin rigar pillow ban ganshi ba, yakamata mu maida mashi abunsa kada ayi mana kallon 6arayi” Gatsina mata hanci junaid yai haɗi da murmura idanuwanshi yace”tab ae Allah bani bashi, Na angel ne na 6oye shi wani wuri inda ba wanda ya sani, Allah Angel zan baimawa shi, kuma kada ki fada ma kowa in baki so mu 6ata dake,” Dariyace ƙumshe abakinta”kai junaid babu kyau fa, da guminsa ya sayi zoben taya zaka ce ba za ka bashi ba? Kana so Angel ɗinka ta sanya abun sata? Kayan haram da ba mallakin ka ba? Girgiza mata kai yai”a’a mommy, to ai bani da kuɗin da zan siya mata wani” Shafa sumar kanshi tayi”mommynka tana da kuɗi, zan siya maka wani but pls ka maida ma mahboob zoben shi kaji my boy” Ɗaga mata kai yai”Toh zan maida mashi badan halinshi ba, kuma Allah idan ya ƙara cinye min chocolate ɗina saina sanya shi kuka” fashewa Aneelerh tayi da dariya, ba ƙaramin nishaɗi yake sanyata ba. *DAULAR ALHAJI MUSA* Ya kasa fita ko da ƙofar ɗakinsa ne, tun jiya da ya zo gidan baƙunta yake yi masu, fitowa yai daga Cikin bathroom jikinshi sanye da bathrobe fara ƙyal, ya ɗaure igiyarta a tsakiyar cikinsa daga can ciki akwai short da ya sanya, sumar kansa ta manne ma fatarsa saboda lemar ruwan wankan daya jiƙata, Dr shureim ba dai kyau ba, ta ko’ina sanyin A.c ne ke ratsa fatar jikinsa, ya ji daɗin dawowarshi gidan uncle ɗinsa baida wata damuwa, musamman tarbar da ya samu awurin Hajiya sarah, ta nuna farin cikin ganinshi kamar ɗan cikinta haka take tarairayarsa. Walking slowly ya nufi dressing mirror Don Ya kimtsa kanshi Gyaran muryar da aka yi mashi ne yasa shi yin saurin juyo wa baya don ganin wanene Lokaci ɗaya ya sauke ajiyar zuciya yana kallon uncle ɗin nasa Yana daga tsaye bakin ƙofa, kayan gym ne a jikinsa, short da riga sun ɗame jikinsa, mutumin akwai ƙira kamar ɗan wrestling. Da fara’a akan fuskar shureim ya furta”My Uncle” yai maganar yayin da yake tunkarar shi, gabanshi sai faɗuwa yake yi ya rasa gane dalilin dayasa a duk lokacin da ya yi tozali da uncle din nashi sai yaji faduwar gaba. Kyakkyawar fuskar Alhaji musa, mai ɗauke da ƙayataccen saje, ba murmushi sai dai yaɗan sakar mashi fuska. “Fushi nakeyi da kai shureim baka iya takowa kazo ɗakina ka gaishe ni, ko dama jira kake inzo room ɗinka”? Cike da izza da nuna isa yake yin maganarsa. Yawu shureim ya haɗiya”ba haka bane uncle, yanzu nake ƙoƙarin zuwa part ɗin naka” Yamutsa fuska Yai”okey, nima na fadi ne kawai ba don wani abu ba, ko akwai abun da ka ke buƙata”? Girgiza kai shureim yai”a’a aini ka gama min komai kawuna, nagode sosai da kulawarka agareni, Allah yabarmun kai” matsawa Alhaji musa yai dab dashi, Ya janyoshi a jikinshi yai hugging nashi tightly, in a whisper ya furta”idan akwai abun da kake buƙata ka sanar dani, idan ma baka Iya fadamin ka tura min ta text message, sannan akwai saƙo da za’a kawo maka zuwa anjima, ya ƙarasa maganar tare da raba jikinsu daga na juna. Still face din Uncle musa ba fara’a, haka Allah ya halicce shi baida sakin fuska. “Nagode sosai uncle, tun jiya da nazo gidan nan akayi min kyakkyawar tarba naji daɗin Hakan sosai” “Shureim ba’ayi min godiya, next time kada ka ƙara” fuskarsa a ɗaure yai maganar Cikin jin shakkar shi shureim ya furta”in sha Allah” ya ƙara da cewa”burina ka canza rayuwarka shureim, banason ganinka acikin damuwa, kaman ta duk wani abun da ya faru a rayuwarka, shiyasa na dawo dakai gidana saboda nasan zaka fi samun kwanciyar hankali, sannan Inaso naji ra’ayinka, bance ka bani amsa yanzu ba, nafi so sai ka natsu kayi nazari tukunna. Jinjina kai shureim yai, idanuwanshi na kallon ƙasa, saboda ƙwarjinin alhaji musa bai iya jurar kallon fuskarsa. “Bazan hana Ka Yin duk wani abu da za ka yi don jin daɗin rayuwarka ba, sai dai ban goyi bayan zamanka a cikin gida ba aiki ba, abu na biyu kuma Aure, kasan shi sunnah ce ta manzon Allah SAW, Aure yana ɗaga darajar mutun yazamto mai cikar kamala da natsuwa, rayuwarka zata canza idan ka yi aure, Na gaji da ganinka a matsayin tazuru” Yai maganar yana ɗaga mashi gira, da zolaya akan fuskarshi, kunyace ta hana shureim furta komai, ji yake kamar ƙasa ta tsage ya shige, Yana jin nauyin uncle din nasa. “Da ace kayi aure da wuri da yanzu mun samu ƙaruwar babies” da sauri shureim Ya juya mashi ƙeya ya rasa ina zai tsoma ranshi, hakan da yai ba ƙaramin nishaɗi yaba kawun nashi ba “Zeenatu ta shigo kun gaisa”? Muryarshi ƙasa ƙasa ya amsa mashi da”eh jiya tazo” “Okey, pls, shureim inaso kana taimaka mata, Kuna fita yawo atare, still ƙanwar taka bata canza ba, sam bata da natsuwa, ni ban ta6a ganin mahaddaciyar ƙur’ani mara natsuwa irinta ba, zaka ga duk min rashin natsuwar mutun indai yana yawan karanta al’ƙur’ani natsuwa na shigarshi amma ita kullum abun nata ƙara gaba yake yi” A hankali shureim Ya juyo ya kalle sa, mamakine ƙarara akan fuskar Shureim wai yau shine kawu musa keyi ma magana har haka? Mutumin da bai Iya surutu ba. “In sha Allah uncle, zanyi ƙoƙari wurin ganin na taimaka mata, “ gyaɗa kai yai”haka nakeson Ji, Ni zan shiga Ciki, idan ka yanke shawara game da abunda na faɗa maka, ka same ni a ɗaki ka sanar dani ko kuma ka kirani awaya” Amsa mashi yai da toh, sallama Uncle musa yai mashi kafin ya fuce daga dakin Ajiyar zuciya shureim ya sauke, hannun shi ɗaya dafe da ƙirjin sa. Lokaci ɗaya zuciyarshi ta fara tariyo mashi haukan zeenatu na Jiya, murmushin gefe fuska ya saki, aranshi ya ayyana ko ta na ina yanzu, yasan zai yi wuya ta jure rashin ganinshi. Ai tun Jiya data bar ɗakinshi Cikin sanɗa ta nufi ɗaki akan hanya suka ci karo da Tani, Abunka game saurin kuka nan take ta ƙware mata baki tana kuka ta faɗa mata abunda ya faru Lallashinta tani tayi tana fadin to menene aciki, Ki kwantar da hankalinki dr shureim dai ɗan uwanki ne ba wani bare ba, yanzu bari na baki mayafi na ki ɗaura a qugunki, ni kuma zanje ɗakin nashi in ɗauko maki zanin, Ai mantawa nayi ban baki undy kin sanya ba jiya, ke kuma baki tuna min ba,” Cikin shessheƙar kuka take faɗin Na tsani kaina Tani, bani da hankali, sai yaushe ne zan daina hauka, sam bani da natsuwa, meyasa na kasance haka”? Cikin kwantar da murya tani tace”karna kuskura na ƙara ji kince haka, in banda abunki ma, meye na damuwa?, Haka Allah ke son ganinki, don haka ki share hawayenki, ai ni wlh ba ƙaramin burgeni kikeyi ba saboda kina da hankali, dayawa wasu ƴa’ƴan masu kuɗin basa girmama ƴan aikinsu amma ke kin ɗauke mun tamkar iyayenki, shiyasa nake ƙara ƙaunarki” “Tani ba zaki gane ba, ni duk ba wannan ba, Yaya shureim bazai ta6a ɗauka na a matsayin mace ba, idan har ban daina wannan haukan ba” tsabar kukan da takeyi make up din fuskarta ya ca6e mata, jan bakin har saman kumatuntu. Ɗaura mata Mayafi Tani tayi asaman waist dinta, tace”ki koma ɗaki, zan shigo muyi magana” ta amsa mata da toh, ta juya da sauri ta nufi ɗakinta. A daren ranar daƙyar Tani ta lallasheta, ta kwantar mata da hankalinta akan tadaina cewa ta tsani kanta saboda yarda Allah ya halicce, kowa da irin tashi ƙaddarar, bawa bai ta6a zama 100% batare da an samu naƙasu atare da shi ba. Sannan Idan saboda yayanta shureim ne takeyin kuka waya fada mata rashin natsuwarta zai hana shi sonta? Wata’ƙil ma haukan nata ne zai ƙara mashi ƙaunarta, don shi so babu ruwan shi da yanayin mutun abu ƙalilan ke haifar dashi indai mutun ya kasance ƙaddararka. Kafin Tani tabar ɗakin sai da ta tabbatar ta kwantar mata da hankali tukunna ta fuce, tsakar dare Zeenatu ta farka, ta shige toilet ta ɗauro alwala kamar yarda ta sama tashi yin nafilfilin dare, yawanci addu’arta duk akan Allah ya bata natsuwa take yinta, abun yana damunta. (Abunda Ya faru a daren Jiya kenan bayan zeenatu ta baro ɗakin Dr shureim) Tun safe baiwar Allah taƙi fitowa daga ɗaki, tarasa ya zatayi, kunyar duniya ta ishe ta, aƙarshe ta janyo al’ƙur’ani ta cigaba da karantawa, har rana ta fito tukunna Ta ajiye shi ta shiga bathroom tayo wanka, ta fito ta sanya doguwar riga ta zura hijabi maroon har kasa, ko make batayi ba, cikin sanɗa ta fito daga ɗaki tana tafiya tana waige waige kamar wata munafuka, a haka ta ƙaraso part din daddynta. A lokacin bai jima da fitowa daga wanka ba, tun bayan da ya baro room din shureim, Ya dawo nasa ɗakin, Jallabiyace a jikinsa launin milk mai kyan gaske, Yana daga kishingiɗe saman doguwar sofa ta cikin katafaren ɗakisa, tsayawa zayyana kyawunsa 6ata baki ne hankali ma bazai ɗauka ba. Ya ɗaura kansa saman pillow, Yayin da apple laptop ɗinsa ke a saman flat tommy ɗinsa. Idanuwanshi suna a lumshe ya natsu yana kallon wani abu a laptop din nasa, ga dukkan alamu video call ya ke yi, sautin muryarshi baya fita yayi low sosai, yana magana eyes dinshi suna lumshewa. Kusan sau Uku zeenatu tana ƙwala mashi sallama baiji ba, saboda hankalin shi baya atare da shi. Tasan baison ashigar mashi room batare da an nemi izininsa ba. Jin shiru bai amsa mata ba, Yasa ta haura ƙafa ta shiga ɗakin tana tafiya babu natsuwa sai faman zumbula sauri take yi burinta kawai ta ƙasa gare shi, duk da fargabar shi da take ji. Cikin rashin sa’a, garin sauri hijab ɗin ta da ke ja da ƙasa Ta harɗe ƙafarta ɗaya, wani irin sul6i ne ya kwashe ta, gaba daya ta rubza saman Sofa table din gabanshi, wanda ke ɗauke da Cup na coffee mai zafi da aka ajiye mashi, gaba ɗaya Cup din Yai tsalle Ya fada mashi ruwan ya wanke Laptop dinsa da gaban jallabiyarshi, zeenatu kuwa tunda ta kife saman sofa table din bata ɗago ba, jikinta sai kakarwa yake yi hankalinta idan yai dubu to ya tashi, zufa ta ko’ina take tsastsafo mata, duk da sanyin A.c ɗin ɗakin. ko gizau baiyi ba idonshi akan keyboad ɗin laptop nashi da ruwan coffee ya jiƙa, Tashin hankalin da ba’a sama shi data🤣 *Boss Bature✍️ Mu haɗu gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*KURKUKUN ƘADDARA*_ ~Middle step~ _The Prisoners E19🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* In a smoky voice ya furta”I’ll call you later.” da mutumin da su ke yin video call ɗin da shi ya ke magana. Tun kafin ta ɗago da kanta cikin shessheƙar kuka ta ke faɗin”Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un Am sorry daddy, nayi kuskure bani da hankali, dan Allah ka yi haƙuri wlh bazan ƙara ba” lumshe idonshi ya ɗan yi kafin gently ya sauko da ƙafafuwanshi ƙasa, Hannun shi tallabe da laptop ɗinsa, ko kaɗan bai ji zafin ruwan da ya hau saman jikinsa ba. Zeenatu ba ta dai na yi mashi magiya akan ya yi hakuri ba, hankalin ta duk yabi ya tashi saboda mugun tsoran daddyn nata ta ke ji. “Daddy na tuba bazan ƙara ba, Ka yafe min nagane kuskure na” tsoro Ya hana ta ɗago su haɗa ido. Miƙewa yai daga saman sofa ɗin ya juya ya nufi cikin Katafaren room ɗin nasa, After some minutes sai gashi Ya dawo babu laptop din a hannunsa, Ya canza jallabiyar jikinsa, ɗaura idanuwansa yai akan bayan zeenatu, dogayen yatsun hannunta sai kerma suke Yi. Agaban Sofa table ɗin Ya dakata da yin tafiya, da kakkausar murya yace”Ke! Miƙe tsaye tun kafin ran ki ya 6aci” Jikinta na kerma ta ɗago da kanta hawaye sun wanke fuskarta sharkaf, abunka ga farar fata face ɗin ta yi jawur, Blue eye balls dinta sun ciza launin su idon nata ya rune, small pink lips ɗinta tsabar ƙarantarsu tamkar na jariri. Cikin rashin natsuwa ta zube saman gwiwowinta, Idanuwanta na kallon tiles ɗin ɗakin “Dad...am sorry bazan ƙara ba, nasan bana jin magana bani da natsuwa amma ka yafe min, kada ka hukun......” Gigitacciyar tsawar da ya daka mata ce tasa ta yin saurin toshe kunnuwanta da tafin hands dinta A razane take faɗin “Na shiga uku daddy, nace maka bazan ƙara ba, Nagane kuskure na” Muryarshi a kausashe Ya furta sunanta”Zeenatu? Sau nawa ina gargaɗin ki akan ki daina faɗo min ɗaki ba tare kin nemi izni na ba? Waya baki iznin shigowa ciki”? Wahalallan yawu ta haɗiya, idanuwanta sunyi luhu luhu sai faman wurwurga eye balls ta ke Yi kamar ƙwayar zata faɗo ƙasa. “Am sorry dad...” katse ta ya yi”Kin Iya tsallan kwaɗi?” tun da ya fara magana bata bari ta ɗago sun haɗa ido ba sai Yanzu da ta ji yace Tsallan kwaɗi A hargitse ta zare mashi manyan idanuwanta A matukar ruɗe take girgiza mashi kai”daddy bazan Iya ba, Ni bansan yarda akeyi ba, ai nace ka yi haƙuri bazan ƙara ba” Gyaɗa kai Yai”Tashi ki fuce ki bani wuri shashasha, daga yau karki kuskura ki ƙara faɗo min ɗaki” Zuciyarta ba ƙaramin karaya tayi ba, duk sai ta ji ba daɗi, ba ƙaramin kewar daddyn nata tayi ba, maimakon Ya nuna farin Cikin ganinta saima korar ta da yayi. Ganin yarda ta tsare shi da ido taƙi motsawa ne Yasa shi daka mata tsawa”nace ki tashi ki fuce min daga ɗaki tun kafin In yi ball dake” fuskarshi a haɗe Yai maganar ba annuri. A gurguje Zeenatu ta miƙe ta juya tana tafiya Jikinta na kakarwa har Ta kai bakin ƙofar fita ɗakin, ta ji ba za ta iya jure fushin daddynta ba, tasan duk akan kuskuren da ta yi mashi ne. Yana atsaye ya goya hannayenshi saman faffaɗan kirjinshi Ya natsu Yana kallon Bayanta, Har ta kusa fucewa daga ɗakin A lokacin Ya juya zai shige ciki ba zato ba tsammani ya ji an rungumeshi ta baya, ƙanƙameshi ta yi tana faɗin”wlh daddy ba in da zan je, ai na faɗa maka kuskure ne bada sani na na 6arar maka da coffee, yakamata ka yi haƙuri ka yafe min, Ni banason kana fushi dani saboda kai mahaifina ne, kuma inason ka sosai bazan Iya jurar fushin ka ba” Har cikin zuciyar shi ba ƙaramin sanyi ya ji ba, kalaman zeenatu sunyi matuƙar kashe mashi jiki, Ba tun yau ba duk idan ta 6ata mashi rai ko ya kore ta daga ɗakinsa ba ta tafiya shiyasa yai mata hakan don ta ga ne kuskuren ta yasan dole ta dawo ta bashi haƙuri. Da hannu ɗaya ya ruƙo hijabin jikinta Ya janyota zuwa gabanshi, Ya kwantar da kanta saman chest ɗinshi, A hankali ya ke ɗan bubbuga bayanta da hannayenshi cikin sigar lallashi, hakan da yai mata ba ƙaramin kwantar mata da hankali yai ba, harta fara samun natsuwa. Tsawon mintuna kafin ya raba Jikinshi daga nata, fuskarta jawur idanuwanta har sun ɗan kumbura. “Kin 6ata min riga da hawaye” tana faman zazzare ido ta furta”am sorry” “Is okey, kinsan banason ganin hawayenki, meyasa kike min kuka”? “Daddy ai kai ne ka sani yin kuka, Ina baka haƙuri kaƙi ka saurareni” “Zeenatu ɗago ki kalli Cikin idona” daƙar ta Iya ɗagowa ta sanya idonta cikin nashi gabanta Ba ƙaramin faɗuwa yai ba saboda ƙwarjinin da yai mata. “Bansan meyasa ki ke jin tsorona ba, Nifa daddynki ne, saboda kawai kin 6arar min da coffee shine duk kika ɗaga hankalin ki? Ni shine abunda Ya 6ata min” fuskarshi a ɗaure tamau yai mata maganar. Muryarta na ɗan rawa ta furta”dad..dy ai kai ne baka dariya ko murmushi ba ka yi min kullum fuskarka a ɗaure, kuma baka son ina zuwa kusa da kai, nasan saboda rashin natsuwata ne amma in sha Allah daddy zan daina, ina yin addu’a ma har tsakar dare Akan Allah ya yaye min...” Yatsan Hannun shi ya daura saman lips ɗinta “Ya isa haka, Karki kuskura na ƙara ji kin ce bana son kina zuwa kusa dani, kinji ko? Ɗaga mashi kai tayi alamar eh Mayar da ita Yai saman chest ɗinsa, Yaci gaba da shafa bayanta Yana ƙara lallashinta. A haka Hajiya sarah ta riskesu, a bakin ƙofar shiga room ɗin nashi taci burki, farar mace alkebbar mata doguwar riga ce a jikinta fitted gown ta lace, Kusan rabin ƙirjinta awaje Yake, Tubarkallah na shanunta atsaitsaye su ke, tamkar bata ta6a haihuwa ba, light make up ne akan fuskarta, Ƙafafuwanta na sanye cikin High hills, sun ƙara mata tsayinta. Babu mayafi akanta zallar sumar kantace tasha ado tsabar haɗuwarta tamkar budurwa. “May I come in”? Muryarta har cikin kunnuwansu, Alhaji musa ne ya bata Iznin shigowa ciki, ɗagowa zeenatu ta yi daga kan chest ɗinsa, Muryarta na ɗan rawa ta furta”daddy zan tafi” “Da iznin wa”? Ya jefa mata tambaya, shiru ta yi tana ƴan kame kame, Sam ba ta son mommynta ta shigo ɗakin daddynta idan tana aciki. Ƙarasowa Ciki Hajiya saratu tayi, kaitsaye ta nufi Alhaji musa, fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi take duban su shi da zeenatu. “Masha Allah, Uba da ƴarsa kunyi kyau fatan ban takura maku ba” Zeenatu ce tai saurin cewa”Mommy, na shigo gaida daddy ne dama, yanzu zan tafi” kallon da Alhaji musa Yai mata ne yasa ta yin saurin canza magana”A’a ba yanzu zan tafi ba, sai daddy ya bani iznin tafiya” Ta yi maganar tare da samun wuri saman sofa ta zauna, Jikinta nata yin kerma acan cikin zuciyarta addu’o’i take karantowa. Matsawa Hajiya sarah Ta yi dab da shi, duk da shakkarshi da ta ke ji hakan bai hanata nunawa mijin nata soyayya, tarairayarshi ta ke yi kamar sabon jinjiri ta haka ta ke iya samun damar Iya sarrafa shi. Hannayenta ta ɗaura saman waist dinsa, Daddaɗan ƙamshin turarenta tuni ya fara Kashe mashi jiki. “Baby, jiya ka hana kowa yazo kusa da kai, kuma ina buƙatar ka, Na kwana da son kasancewa atare da kai” cikin harshen turanci ta ke yi mashi magana, gogan naka babu fara’a akan face ɗinsa ya ƙame a tsaye kamar soja. “Zeenatu, ta shi ki je ɗakin Yayanki shureim, Tani ta faɗa mini tun safe ba ki ci abinci ba, nayi mata magana ta shirya mashi abincin aɗakinsa, Za ki Iya zuwa can kuci atare da shi” Kamar Jira ta ke yi mommyn ta yi mata magana, da sauri ta miƙe ta nufi hanyar fita daga ɗakin Har Allah Allah take aranta, saboda bata son ganin Iyayen ta suna yin romancing din junansu agabanta Kunya take ji kuma hakan Yana jefata wani hali. Baya fitar Zeenatu ta dawo da dubanta akan fuskar shi. Muryarshi a kausashe Ya furta “Baki da kunya? Baki ga me kika ruƙe min ba ne” Kashe mashi ido ɗaya tayi muryarta da kwarkwasa ta furta”kaine ka koyamin rashin Kunyar,” hakan da tayi mashi ba ƙaramin jefa shi yanayi tayi ba, dama Shi mutunne da baya wasa da duk wani abu da jikinshi ke buƙata. “Yanzu ina da aikin da zanyi, Da anjima zan neme ki” marairaice mashi fuska tayi”A’a baby, yanzu nake buƙatarka ni, kusan 3 days baka atare dani, bazan iya jurewa ba.” Yamutsa fuskarshi Yai, Kafin Yai yunƙurin ƙara furta wata kalma, tayi saurin zame wuyan rigar jikinta, Ba ƙaramin shammatarshi tayi ba, gaba ɗaya ya rasa sukuni, Baisan ya akai ba ya tsinci kanshi asaman gado sun tsunduma suna Korar shaiɗanu, Suturar jikinsu A saman floor na tsince su bansan ina zan kaisu ba, Laundry ko toilet? (🤣 wato duk izzar namiji sai in bai haɗu da mace ba) Tuni Dr shureim Ya kammala shiryawa, Ya canza suturar jikinshi, still Arab dress ne, kayanshi na gado, Yana daga zaune gefen gadon shi, Hannun shi ruƙe da Wayarshi Yana kallon hoton abar ƙaunarsa da ya buɗo a gallery. Ba zato ba tsammani Yaji Muryar matashin saurayi Yana Kwaɗa sallama daga bakin ƙofar ɗakinsa, slowly ya ɗago da ido yaɗan Juya yana kallon Saurayin dake sanye cikin black suit, dogo kuma faffaɗa, Hannun shi ruƙe da Ƙatuwar shopping back mai ɗauke da sunan *Obinna tech* A sukwane Dr shureim ya ɗaura wayarsa saman mattress Ya yunƙura ya miƙe Still idonshi akan mutumin. “Dr shureim Barka da warhaka” Muryarshi babu natsuwa ya furta”yawwa barka dai” duk yasha jinin jikinshi saboda mutumin babu fara’a akan fuskarshi kamar wanda aka ɗaurawa aure da mutuwa. “Saƙo ne daga Uncle ɗinka” nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke tunawa da saƙon da uncle musa Yace za’a kawo mashi. A hanzarce ya ƙarasa bakin ƙofar ɗakin, Ya miƙa hannu biyu ya kar6i kayan daga hannun mutumin haɗi da yi mashi godiya. Fuskar shurem ɗauke da murmushi ya nufo cikin ɗakin, A saman gado Ya ɗaura shopping back ɗin, Bayan yayi bismilla, Ya buɗe ta tare da zura hannu Ya zaro kayan dake aciki, har saida gabanshi Ya ɗan faɗi. Apple laptop ce, tare da Apple watch, abu na ƙarshe da ya gani Unexpected Danƙareran Key ɗin Mota, Zubewa yai saman gwiwowinsa agaban Kayan Yana duban su, A tsanake Ya ke ƙare masu kallo, haƙiƙa Yayi farin Cikin Kyautar nan da uncle musa yai mashi ya ji daɗi sosai, ɗaga Hannayenshi sama Yai, Ya soma jera addu’o’i Yana yiwa kawunsa bisa irin farin cikin daya Sanya shi ayau, Ya faranta mashi sosai. Bai gama shan mamakin Kayan ba, Muryar mutumin da ya kawo Kayan ta katse mashi addu’o’in da ya ke yi. “Dr shureim Zan iya shigowa Ci ki? Da sauri Ya miƙe tsaye Yana kallon shi. Manyan Akwatuna ne guda Biyu a hannun shi ya ruƙe handle ɗinsu Yana Jansu irin masu tayoyin nan. “Bismillah” yai mashi nuni daya shigo Ciki, Bayan ya shiga Cikin ɗakin agaban tafkekiyar Glass wardrobe ɗin ɗakin mai faɗi Ta mamaye bangon da take a jikinsa, Anan mutumin Ya dakata da yin tafiya ya buɗe akwatunan, Farin Ciki Ya hana dr. shureim Rufe bakinsa. Arab dress ne kala kala Na maza, Kalar waɗanda Yafi so, A ƙalla sunkai kala Hamsin sababbi fitigil dasu shaƙe cikin akwatin, Hada Arab turban ɗin da Yake naɗawa akanshi. Atare da mutumin suka soma jera kayan acikin wardrobe ɗinsa, Bayan sun kammala jera kayan, Man ɗin Ya buɗe ɗayan akwatin Wa’iya zubilla Uncle musa Ya gwangwaje ɗan nasa da Haɗaɗɗun leather shoes da tsadaddun turarurruka Na Larabawa, Da suran Kayayyakin amfani na gyaran Jiki, a gaban mirror suka jera Kayan, Bayan mutumin Ya kammala, Dr. shureim yai mashi godiya suka Yi sallama da shi. Yana atsaye idonshi akan sabbin Kayanshi sai binsu ya ke yi da kallo, daɗi kamar wanda akayiwa albishir da gidan Aljanna. Muryar Tani ce Ta janyo hankalin shi ga dubanta. A yayin da ta ke shigowa ɗakin nashi “Dr shureim barka da rana, Fatan Ka wuni Lafiya? Ya kwanan gidan uncle ɗin naka” Hannunta biyu ruƙe da Faffaɗan wooden tray, daga saman shi jerin lunch ɗinsa ne. Da fara’a akan face dinsa Ya soma Amsa mata gaisuwar”Alhamdulillah, Fatan kema Kina Lafiya ya aiki”? “Lafiyalou, ai Munji daɗin zuwanka gidan nan, Ko ba komai zaka ɗebe ma Zeenatu kewa, Baiwar Allah jiya tayi murnar zuwanka, Tana matuƙar son yayanta” Fuskarta awashe Ta yi maganar, adai dai takai gaban table ta ɗaura mashi tray ɗin. Murmushin gefen fuska Yasaki tare da faɗin”Allah sarki, Tun Jiya bata ƙara dawowa ɗakina ba, Idan ba damuwa ki kira min ita idan kin fita, nasan saboda Kunyar abunda Ya faru Jiya ne Yasa ta kasa zuwa gaishe ni da safe” “Wlh kamar ka sani, abunda ya hanata zuwa kenan, ai zeenatu akwai kunya, Yarinyar kuma tana da mutunci ga kamun kai, Ga ilmi, ita dai taji daɗin rayuwarta, Gaskiya ba ƙaramin mai sa’a bane zai mallaki Zeenatu” tun da Tani ta fara Yi mashi sambatun Kyawawan halayar zeenatu Ya natsu Yana sauraranta haɗi da kallonta, Ya fahimci so ta ke Yi, Ta yi mata gyaran hanya awurin shi. Dama tun Jiya da yazo matar take ta yi mashi sambatu akan zeenatu. “Idan badamuwa, inason Ganinta” washe baki Tani ta yi”Toh, yanzun nan zaka ganta,” Da sauri Ta juya ta fuce daga ɗakin. Tattara Kayan saman gadonshi yai, acikin Shopping bag ɗin Ya tura su. Ajiyar zuciya ya sauke Ya koma gefen gadon shi ya zauna yana jiran ƙarasowar Zeenatu. Akan Hanya Tani taci karo da zeenatu tana tafiya kamar munafuka, sam babu natsuwa atattare da ita, sai ƴan waige waige take Yi, har sai da suka bangaji juna da Tani tukunna ta zabura ta kalleta suka haɗa ido “Ina kika shiga ne?” “Ɗakin daddy” ta bata amsa “Hawayen menene akan fuskarki! Waya ta6amin ke” zumbura mata Baki Ta yi ba tare da ta bata amsa ba. Ruƙo hannunta Tani tayi”Muje ɗaki ki gyara fuskarki, dr shureim ne yace in kira mashi ke” waro ido waje tayi jin ance Yaya shureim ke kiranta. Jiki na rawa Tabi Tani suka nufi falo abakin stairs suka hau elevator takai su Second floor, Bayan sun fito da sauri suka nufi ɗakin zeenatu, sai da Tani ta jira tayo wanka tukunna ta taimaka mata wurin canza Kayan jikinta, Pakistan ta sanya riga launin blush pink har gwiwa, Tare da burgujejan wando Fari anyi mashi adon stones, Tani ta ɗaura mata Mayafi akanta, Babu makeup Iya kyawun fuskarta ne. Flat shoes Ta zura a ƙafarta, Atare da Tani suka baro ɗakin Bayan sun sauko down, sai da Tani taja mata kunne akan ta natsu kada Tayi mashi hauka, ta amsa mata da toh. A hankali take Yin tafiya tana nufar sashen room ɗinsa, a bakin ƙofar ɗakinshi ta la6e tana leƙensa Yana zaune idonshi akan screen ɗin wayarshi, Ya natsu Yana kallo ko motsi bai yi, Kunyace ta kama ta, muryarta Ƙasa ƙasa take ambaton sunanshi”yayana rabin raina” shiru dr a Shureim bai amsa mata ba “Hubbyna” still shiru, da alama bai ji sautin muryarta ba. Tunani ta soma yi ko menene ya ke kallon acikin wayarshi wanda yai silar ɗauke hankalinshi! Ras taji gabanta Ya faɗi sakamakon amsar da zuciyarta ta bata na cewa wata’ƙil hoton girl friend dinshi yake kallo. Cikin sanɗa ta ke yin tafiya cikin ɗakin nashi duk don ta gano abunda Yake kallo, daga 6angare hannun dama na gadonshi ta zagaya tana yi mashi dogon wuya, ƙamshin turarenta ne Ya tona mata asiri, lumshe idonshi yai yana tunanin a ina aka samu fragrance me daɗin shaƙa a ɗakinsa, ɗagowar da zai yi keda wuya idonshi ya sauka akan zeenatu dake leƙan wayarshi, da sauri ya danna power button hasken phone ɗin ya ɗauke screen yai duhu. Duƙar da kanta ƙasa ta yi, yanayin fuskarta ya canza”yaya shureim ɗina, ka wuni lafiya? Am sorry Jiya ban dawo mun gaisa ba” A hankali Ya miƙe ya zagayo ta Inda take atsaye dab da ita ya tsaya yana ƙare mata kallo. Baisan ya akai ya tsinci kanshi da kallon wankan pakistan ɗin da ta ɗauka ajikin ta, ta yi bala’en yi mashi kyau, Yarinyar kamar Fure haka take da ɗaukar ido. Tabbas Idan yaci gaba da kallonta zai shagala ne Acikin zuciyarsa Ya ambaci “A’uzubillahi minasshaiɗanirrajim” A fili kuma Yace”Zeenatu, kada ki damu bakomai, ay nayi maki uziri kece kika takura kanki” Muryarta da shagwa6a tace “Mommy ne tace inzo muci abinci atare, tun Jiya dana bar ɗakinka banci komai ba” Ya rasa gane wani irin yanayi yake ji atare dashi, tana yin magana blue eye balls ɗinta na jujjuyawa, Yatsun hannunta sai kerma sukeyi saboda rashi natsuwarta. Abu mafi jan hankali a jikinta ƙirjinta kamar zasu tsonewa mutun ido “Ki jirani awaje”! Abunda Ya furta mata kenan “Yaya shureim ba abinci zamuci atare ba”? “Eh, amma ba’a cikin ɗakina ba, kinsan babu kyau mace da namiji su ke6e a ɗaki ko”? Ɗaga mashi kai tayi alamar eh “Bari na ɗauko mana kayan abincin sai mu koma dining room” tuna abunda ya faru Jiyane yasa shi yin saurin cewa”No! Ni zan ɗauka,” amsa mashi tayi toh” Ya zagaya other side ya ɗauko tray din Kayan abincin da hannu biyu ya ruƙo shi, yana agaba tana bayanshi, a Haka suka ƙarasa cikin Haɗaɗɗen ɗakin Cin abincin gidan, Dining tables har kala Uku, Kowanne a kewaye da chairs, a saman table Ya ɗaura masu tray ɗin, suka zaune suna fuskantar juna, Hankalin shi ba ƙaramin kwanciya yai ba, A inda suke Masu aiki Na iya hangensu daga main palour. Sai faman sakar mashi murmushi take Yi “Yaya shureim, zamu dinga fita yawo atare ko? Kaga kullum ina agida daddy baya barina zuwa yawo, tun da na kammala secondry school kullum Ina agida” ta ƙarasa maganar tare dakai hannu ta ɗauki serving spoon ta buɗe warmer ta Fried rice ta zuba masu a plate Biyu, ta sanya masu spoons aciki. Suna ci suna Yin fira ga lemunsu me sanyi a glass. “Kada Ki damu, Munyi magana da daddynki, Yace yanason ina taimaka maki da wasu abubuwan” Washe baki Tayi”yaya shureim zamu fara fita shan ice cream da zuwa cinema? And shopping ko”? Ɗaga mata gira yai alamar eh, cizon pink lips dinta tayi”Yaya shureim Amma ka ta6a yin soyayya”? Ƙiris ya rage ya shake saboda surutun zeenatu, girgiza mata kai yai”ban ta6a ba ke fa”? “Maza dayawa suna haukan sona, Ni kuma nafison auran miskilin namiji, mai ilmin addini dana zamani kuma Yana amfani da su, sannan me Koyi da sunnar Annabi Muhammad SAW” Tunda ta fara lissafa kalar namijin da takeso, dr shureim ya dakata da cin abincinsa, Ya natsu yana kallon pink lips ɗinta, taƙi tsayar da idonta wuri ɗaya Sai faman ƙeƙƙeftasu takeyi kamar babie. “Yaya shureim kai fa watakalar mata ka ke son Aure” baisan sa’adda Ya furta”ra’yinmu ɗaya” zare mashi ido tayi “What”? Girgiza mashi kai tayi”amma yaya shurem idan ra’ayinmu ɗaya kenan bakason mace me surutu? Mara natsuwa mai rawar kai haka”? Murmushi ya sakar mata har dimples dinsa suka lotsa. “Nidai nace Ra’ayinmu ɗaya” ya sake nanata mata maganarsa, murmushin gefen fuska tasakar masa”indai dagaske Ra’ayinmu ɗaya da kai, Toni inason Namiji mai surutu mara natsuwa mai rawar kai, kaga kenan Kaima kana son mace irin haka” dariya ce ta kubce mashi, Harya shaƙe da abinci Da sauri ta miƙa mashi lemu Ya kar6a Yana kur6a, Gwanin ban sha’awa haka suka cigaba da cin abinci tana Janshi da surutu. *DAULAR OBIE ESTATE* A ɗakin Hajjaty, Kwance suke asaman gadon sun mannewa juna, Babu sutura a jikinsu zufa duk ta wanke jikinsu tamkar A.cn ɗakin Bata aiki, tsawon awanni da suka gama sharholiyarsu baccine Ya ɗauke su, Faɗaɗan tafukan hannayenshi ya cikasu da boobs ɗinta, ƙafarshi ɗaya tana a tsakankanin cinyoyinta sosai Ya shigeta, Ahaka bacci yai awon gaban dasu. Sautin ringing ɗin wayarshi ne Yai silar farkawarshi, Idanuwanshi sunyi jawur dasu, kasala duk Ta baibaye shi, daƙyar Ya Iya zame jikinsa daga nata, wani irin mayataccen kallo yake binta dashi, ji yake kamar ya ƙara second round don Baya gajiya da ita, matsawa yai saitin face dinta, ya kama lips dinta yai sucking dinsu, kafin A hankali Ya zame tongue ɗin ya mayar saman nipples dinta sosai yai sucking dinsu kamar zai karar dasu. wayarshi sai ringing ta ke Yi yaƙi mayar da hankali kanta. Jin Zafin abun da Yake yi mata ne Yai silar farkawarta, idanuwanta sunYi mata nauyi muryarta a disashe ta furta sunansa”Pravin pls ya isa haka, Yakamata Ka tafi, marece har Yayi, Nasan Hajiya saratu zata neme ka,” ɗagowa yai da idonshi Ya kalli face dinta “Kin gaji dani ne”? Girgiza mashi kai tayi”kaima ka sani bani gajiya da kai pravin, da ace zan gaji da kai da tuni na rabu da kai” daƙyar take yin magana idanuwanta na lumshewa har yanzu mayen shi ta ke Yi. “Pls ka tafi pravin na roƙe ka” Da kasalalliyar muryarshi yake yi mata magana”zanyi kewarki nasan idan Owais ya dawo gidan nan ba ƙaramin takura zan yi ba, amma duk da hakan zanyi ƙoƙari ina satar hanya ba tare da kowa ya sani ba zan dinga zuwa ɗakin ki kina rage min zafi’ harara hajjaty ta ɗan jefa masa”matarka fa? har mamaki nakeyi irin yarda kake liƙe min bayan matarka tafi ni komai” Ta6e lips dinsa yai’kada ki ce haka, arziƙi kawai zata nuna maki bayan haka bana tunanin akwai wani abu da zata Iya finki dashi, sai dai ma ki fita. “Amma kafi sonta akaina? Saboda Ta haifa maka ƴa’ƴa” “Waya faɗa maki? Kema ai na samu ƙaruwa dake, sai dai Allah bai nufa zai yi tsawaicin kwana ba, Ya rasu amma zamu sake haifar wasu idan kina so” Tamkar ya fama mata raunin dake acikin zuciyarta, kifa kanta tayi saman pillow, Hannu ɗaya ya ɗaura saman sumar kanta yaci gaba da shafa lallausan gashin kanta. “Its ok, kada Ki yi min kuka kinsan banaso My honey, “ Cikin shessheƙar Kuka take faɗin”Pravin na gaji da irin rayuwar nan, bana jin daɗin kasancewata a matsayin ƴar aiki agidan nan saboda matarka saratu, ta tsane ni bata sona, har Gori ta ke Yi min tana kirana da sunan karuwa, wai ina shisshigema babansu wai ni pravin...’ sautin kukanta ba ƙaramin ta6a mashi zuciya yai ba Lallashinta ya soma Yi”am sorry nasan ba daɗi but ki yi haƙuri, in sha Allah zan nema maki mafita, idan bakya son zama gidan zan siya maki wani ki koma ki zauna can Hakan Yayi maki”? Ya yi tambayar yana leƙen fuskarta Ba tare da ta ɗago da kanta daga saman pillow ba tace”A’a, ai ni bana son inyi nesa da kai, Idan ka siya min gida na koma zaka Yi min wuyar gani, amma idan anan ne zan dinga ganinka akai akai, koda ba za mu yi magana ba idan ka gifta ina jin sanyi araina. Lumshe ido yai, muryarta na ƙara jefa shi cikin Yanayi na jin shauƙinta. “Shiyasa nake ƙara sonki My heart beat, kin fiye min kowace mace a duniya divya, kinyi haƙuri dani da daɗi da ba daɗi kin zauna dani, Inason ki sosai, kema kin sani, saratu bata fiye min ke ba, zan Iya rabuwa da ita amma ke bazan Iya rabuwa dake ba saboda ke Jinina Ce kuma amanace ke agare ni. Kalaman pravin sun sanyaya mata zuciyarta sosai, bata ta6a kokwanto akan abunda yake faɗa mata ba. Idanuwanta jawur take duban fuskarshi “I love u so much, My life partner,” murmushi ya sakar mata. “Idan akwai abunda kike buƙata Ki sanar dani zanyi maki shi” Girgiza mashi kai tayi”a’a ai ni ka gama min komai pravin, ka haɗani da mutanen kirki waɗanda har yau ina alfaharin kasancewa ta acikin su, sun ɗauki nauyin komai na rayuwata ci na shana da suturar sanyawata, kaine sila pravin, bayan Albashi da nake samu awurinsu kaima kana turamin kuɗi duk ƙarshen wata masu yawan gaske, bansan ina zan kaisu ba, Tun da bani da buƙatarsu da ace Yaronmu yana araye kaga sai mu dinga siya mashi abubuwan wasan Yara, da sutura masu kyau .....”da rawar murya takai ƙarshen maganar, sosai ta sanya mashi kuka. Cikin shessheƙar Kuka tace”Pravin bazan 6oye maka ba, Inason na haihu ko dan na samu madadin shi” “Ki kwantar da hankalinki, Zanyi shawara akan hakan” jinjina mashi kai Tayi Yunƙurawa yai tare da miƙewa Ya sanya hannu Biyu ya cuccu6eta duk girman jikinta baya jin nauyin ɗaukarta, Saukowa yai daga saman gadon Ya nufi toilet da ita, wayarshi da ya bari acikin aljihun short dinsa dake yashe ƙasa sai ringing take Yi, da zarar kiran ya katse wani ke shigowa. ****************❤ A ƙalla ta shafe sama da mintuna 30 tana zarya A cikin ɗakinta, Hannunta ruƙe da I phone dinta, Yayin da idanuwanta ke kallon Haɗaɗɗiyar agogan bangon ɗakinta Ƙarfe 6 na marece, Lamarin Ya ɗaure mata kai, damuwa ce ƙarara akan fuskarta, Tun ɗazu da ta kammala Yin waya da Gimbiya mujeedat, Hankalinta ya dawo kan Mijinta, Ganin time ɗin dawowarshi daga aiki har Ya zarce babu shi babu alamar shi, saboda damuwar rashinsa ta manta da zancen Kiran Zahra, Hatta P.A dinsa Ta kira awaya ta tambaye shi ina pravin? Yace mata ai shi tun wuraren ƙarfe sha Biyu na safe rabon shi da pravin, Hankalinta ba ƙaramin tashi yai ba, hakan na nufin ko aiki baiyi a office ba, to ina Ya shiga? Tun ɗazu take kiran layin shi ba’a picking, abun duniya ya isheta, saboda ta damu da pravin tayi kewarshi sosai, bata tunanin ko abincin zata Iya ci idan bai dawo ba. Guntun tsoki taja A fili ta furta”ya Salam, Ya Allah ga bawanka nan, Ka tsare min shi a duk Inda Yake, “ ta ambaci hakan tare da jefa wayarta saman Gado, da sauri ta nufi tafkeken closet na kayansu ta buɗe ta ɗauki Mayafi ta Yafa a kafaɗa, tsabar sauri takalman da ta zura a ƙafarta daban daban, adai dai baƙin ƙofar fita daga ɗakin Suka yi kicibus da Twins Bakunansu ɗauke da sallama, Wankan suit ne a jikinsu, sun bi shape ɗinsu, Masha Allah, wrist watch dinsu mai Kyan gaske, Wani irin daddaɗan ƙamshi ke fita daga Jikinsu. Hankalinsu ba ƙaramin tashi yai ba ganin mommyn nasu fuskarta babu walwala. Har suna haɗa baki wurin furta”Mom Lafiya? Meke damunki ne” girgiza kai Tayi”inafa lafiya, daddynku tun ƙarfe shabiyu yabar office, har yanzu bai dawo ba, Na kira Layin shi wayar tana ringing ba’a ɗayawa. Atare suka kalli juna, babu alamun damuwa akan fuskokinsu. Kwantar mata da hankali suka soma Yi”mommy ki kwantar da hankalinki, daddy fa ba wani ƙaramin yaro bane da zaki tashi hankali akanshi, Yasan inda Yaje kuma zai dawo ne in sha Allah” Fuskarta babu walwala take dubansu”pls ku bani Hanya in wuce inaso Naje na faɗa ma baba” har suna haɗa baki wurin furta sunan baba “Haba Mommy, Akan wani dalili zaki je ki faɗa mashi? So kike ki tashi hankalin shi, Gaskiya a’a ki koma ki zauna, zamuje mu nemo daddy duk In da ya shiga” Ruƙo Hannunta Zayn yai, Suka koma Cikin ɗakin, Gefen gado ya zaunar da ita, “Zayn pls, Ku duba daddynku, Ni damuwata kada ace wani abunne ya same shi dama jiya ya faɗamin baya jin daɗin jikinshi” muryarta tamkar zata fashe da kuka ta yi masu maganar. Zaid Yace”in sha Allah ba abunda ya same shi mommy, yanzu zamuje mu nemo shi” ya ambaci hakan Tare da ruƙo hannun ɗan uwansa suka fuce daga ɗakin. Ransu ya 6aci matuƙa, daga gaban ƙofar ɗakin suka tsaya suna kallon juna “Mutumin nan ɗan rainin wayau ne, wlh Zaid zan tona mashi asiri awurin mommy, Ta ya ya zai bar mahaifiyarmu cikin damuwa, Yana can Yana sharholiyar shi, dama zuba mashi ido nakeyi ina tara shi....” duk yadda zaid yaso ya dakatar da Zayn Akan Yai shiru yaƙi rufe baki saida Yakai ƙarshen Aya “Ka daina ɗaga murya bro, Ni bawai ina goyan bayan abunda yake yi ba ne, just ka yi tunani mana, muddin ka tona ma daddy asiri wlh mu zaka ja ma bala’e, Kana ganin irin gorin da ake yi mana a family, akan mahaifinmu yana zama gidan surukansu Yanzu idan ka faɗama Mommy cewa daddy Yana bin matan banza me kake tunanin zai Biyo baya”? Sassauta fushin fuskarshi Yai”Hakane Zaid amma abun Yana ƙona min rai, why ya ke son ja mana baƙin jini? Dame mommy ta rage shi da har yagaza kama mutuncin kansa, wai shi so yake dole saiya 6ata mana suna” tuni idanuwanshi sun cicciko tab da ƙwalla Ya ci gaba da cewa”Shine silar komai dake faruwa arayuwarmu, Zaid Ina kishin mahaifiyata sosai, Ina jin takaici da ƙululun baƙin Cikin mutumin nan, wlh duk ranar da mommy taji labarin abunda Yake aikatawa tabbas zuciyarta zata Iya bugawa saboda tana da kishi kuma Tana son daddy, ni har kokwanto nakeyi anya daddy yana son mommy kuwa? Ko dai Abunda mutane suke hasashe akanshi gaskiya ne? ya aureta saboda dukiyar family dinmu’ yana magana hawaye naci gaba da taruwa acikin idanuwanshi. Dafa kafaɗarshi Zaid Yai”duk abunda ka ke ji zayn nima inajin shi, Amma Ya zamuyi? Mu tamu ƙaddarar ahaka tazo mana, Muyi haƙuri wata rana sai labari Sannan Yakamata muna tayashi da addu’a akan Allah ya shirye shi, saboda shi mahaifinmu ne duk inda za’aje adawo mu jininsa ne kuma ba zamu so mutuncinsa ya zube a idon jama’a ba. Lallashin junansu su ka yi, Hannunsu ruƙe cikin na juna suka Nufi Babban falon gidan, masu aikine keta kai komo. Suna dab da zasu fuce daga falon, Kwatsam Pravin Ya faɗo Sai faman zumbula sauri Yake Yi, Jikinshi sanye da Suit dinsa light brown, ƙiris Ya rage su ban gaji juna da shi, duk da faɗin ƙofar kasancewar Kowan nan su Hankalinshi ba a kwance yake ba Har zasu gifta shi, suka ci wani uban burki agabanshi, Tun daga Kan Yarda suke jefa mashi kallo yasa shi kame kanshi. “Har kun dawo daga aikin”? Tambayar daya jefa masu kenan. Zayn tamkar ya shaƙe baban nasu haka Yake ji, takaici Ya hana su yi magana. “Lafiya? Baku ji ina magana ba”? Saida suka taushi zuciyoyinsu tukunna suka Iya yi mashi magana, Zaid yace”Sannu da dawowa daddy, Ya office din? Naga yau ka yi marece ko duk Aikin ne ya ruƙe ka”? Basarwa Yai tare da cewa”Eh, “ daga haka bai ƙara tanka masu ba, Sai bi da yai ta gefen su Ya wuce, kamar sakarkaru haka suka Bi bayanshi da kallo, Sam baisan cewa sun san abunda yake aikatawa ba. Kusan atare suka girgiza kawunan su. “Zayn tunda Ya dawo mu koma ɗaki, dama Ni agajiye nake wlh, inaso na ɗan kwanta In huta” Juyawa sukayi Atare suka nufi part dinsu. Hajiya saratu na zaune gefe gadonta, baiwar Allah damuwar duniya ta isheta Hannu biyu ta zabga uban tagumi, gabanta sai faɗuwa yake yi gani take yi kamar wani abunne Ya faru da mijinta, Kasa samun natsuwa tayi zumbur ta miƙe kamar an zungureta da sanda, safa da marwa taci gaba da yi acikin ɗakin tana ƙarewa agogon bango kallo. Ba zato ba tsammani muryar Pravin ta ratsa kunnuwanta”Assalamu alaikum” tunkafin Ta juyo ta kalleshi ta soma sauke nauyayyar ajiyar zuciya, tsabar farin ciki da sauri ta nufeshi, hannu biyu ya rungumeta a ƙirjinsa. Sai faman sauke ajiyar zuciya take Yi, yayin da take ƙara shaƙar ƙamashin turaren jikinsa. “Am sorry My wife, nasan ban kyauta maki ba....”tunkan Ya ƙarasa maganar, Hajiya saratu ta dago da fuskarta, babu annuri ko misƙala zarratin tuni yasha jinin jikinshi. Da kakkausar Murya ta furta”PRAVIN DAGA INA KAKE”!? Rass Yaji gabanshi Ya faɗi “Na kira p.A dinka Awaya ya sanar dani cewa tun ƙarfe 12 kabar office, Inason Jin ya akai kabar office ina kuma kaje”? Rai a6ace take Yi mashi magana, Hannunta ruƙe da qugunta. Ya tsareta da Ido batare daya furta kalma ba, hakan ba ƙaramin Ƙona mata rai ba, Tsawa ta daka mashi kamar mahaukaciya Ta cakumi Gaban rigarshi. “Nace ka faɗamin Ina kaje pravin? Saboda ka maidani shashasha ban da amfani awurinka shine zaka kama Hanya kabar office tun ƙarfe sha Biyu baka kirani awaya ka sanar dani ba, Kasa duk nabi na tashin hankalina akanka, ni na ɗaukama wani abunne ya same ka sai gashi ka dawomun lafiyarka qalou” Ƴan hanjin cikinsa tuni sun soma kaɗawa, Abunka ga shu’umin namijin wanda yasan takan mace, runtse idonshi yai tare da kai hannu ya dafe gefen cikinsa. Nan take Hankalinta yai matuƙar tashi la66anta na rawa take faɗin”pr...pravin? Lafiya? Meke damunka” Da wata irin kasalalliyar murya ya furta”My stomach, bana jin daɗi ai tun Jiya na faɗa maki,” ya ƙarasa maganar yana faman cizon la66ansa, lokaci ɗaya fushin fuskarta ya sassauto, tsananin tausayin shine Ya kamata, ganin yana tangal tangal kamar zai faɗi yasa tayi saurin talla6e waist ɗinsa, da taimakon ta suka ƙarasa gaban Gado Ya hau Ya kanta Yana fuskantar ceilling, daga gefen gadon ta zauna daga gefenshi tana kallon shi “Pravin am sorry nayi maka faɗa bansan baka da lafiya ba, kaine kaƙi Yi min magana, why pravin kasan baka da lafiya meyasa baka kira awaya ka sanar dani ba? Cikin kulawa take yi mashi magana, har ta manta da zancen tambayarshi Ina yaje. Wahalallan Yawu ya haɗiya, Cikin mawuyacin Hali Ya furta”wayar bata a hannuna ne a mota nabarta, Ina Cikin Yin draving zan dawo gida, Ciwon ciki Ya takura min, draving dinma na gagara Yi, shine na wuce gidan abokina dake anan kusa, to acan bacci ya kwashe ni, “Pravin why baka je asibitin Gida ba? ai da komai yazo maka da sauki, yanzu ka tashi ka shirya In kaika asibiti da kaina inyaso sai in dubaka acan” Tana Ƙoƙarin miƙewa yai saurin fusgo hannunta, gaba ɗaya ta faɗa saman jikinsa, Ƙanƙame ta yai da hannayenshi biyu Yana faman cizon le6e ya furta”rashin lafiyata bata asibiti bace, My wife kece kike damuna saboda rashin bani haƙƙina da bakya yi akai akai, shiyasa nake fama da ciwon cikin nan, ko da yaushe Aikinki ne agabanki, idan dare yai nayi maki magana kina danna laptop sai kice min In jira ki kammala daga nan har bacci ya ɗauke ni baki gama ba......” Pravin Ya kashe mata Jiki da kalamansa, ta yarda da abunda ya faɗa mata saboda tasan bata kyauta mashi ta 6angaren nan mafi yawan time idan Ya matsa mata tana Yin aiki bata kula shi saita kammala. “Am sorry dear, indai nice zan gyara, kayi haƙuri nayi kuskure but bazan ƙara Ba, tun da abun Yana affecting dinka”. Lumshe ido Yai, har cikin zuciyarshi ba ƙaramin daɗi Yaji ba, ganin yai nasara akanta. “Yanzu ka faɗamin me kakeso? Za ka yi wanka in taimaka? Ko zaka fara Cin abinci ne” Yana faman sakin nishi Ya furta”nafi buƙatar wankan, amma idan kin amince muyi atare” Murmushi tasakar mashi”is Okey, shine kaɗai abunda kakeso”? Ɗaga mata Gira yai alamar eh, A hankali ta ɗaura yatsun hannayenta saman coat din jikinsa Ta cire mashi ita, kafin ta zame mashi belt din wandonsa, yunƙura yai tare da miƙewa ya sauko daga saman gadon Ya ƙarasa zame wandon ya rage daga shi sai short da singlet dinsa, Yaja hannunta suka nufi toilet, da gudu nabi bayansu sai dai kafin in ƙarasa Pravin Ya kulle ƙofa. *EX-PRISONERS❤* Idan muka koma 6angaren Prisoners, sai dai muce Alhamdulillah, tun bayan da Dr laura davis ta tattauna da Sojoji bata ƙara Ji daga gare su ba, An dai samu damar Kammala Yi masu injections ɗinsu kuma kullum sai sunsha magani na safe daban na rana daban na dare daban, injection ɗin duk mutun ɗaya uku suke Yi mashi arana, Likitoci sun ci kwakwa Wurin ma Matan allura, Musamman Azeeza da Jamimah, mugun tsoron Allura su ke ji, idan za’ayi masu sai an kira Angel ta ruƙesu, tukunna ake samun sauƙin yi masu allurar, Mazan dai da sauki basu tsoron Allura tamkar basu son ana tsira masu ita a jikinsu ba, cikin kwanaki huɗu da su ka Yi a Texas Rayuwarsu ta fara canzawa, saboda kyakkyawar kulawar da suke samu tarairayarsu ake Yi kamar new born babies, abinci sau uku ake basu, Breakfast, lunch and dinner, Lafiyayyan abinci mai gina jiki, sau ɗaya ake sanyasu yin wanka, su canza Kayan Jikin su, Su Angel an dage da yin sallah da addu’a, har tsakar dare tana tashi yin night prayers, yawanci addu’o’inta akan Danish ne, ta roƙi Allah da ya kare mata shi, idan farkawarshi Alkhairi ce Allah Yasa ya tashi cikin amince, idan kuma farkawarshi ba Alkhairi bace Allah yasa yaita sharar baccina har zuwa su koma Nigeria zaifi masu sauƙin su Yi control dinshi, duk da yanzu ta fara fargaban kada su zo Nigeria A nemi Ruwan zam zam arasa tabbas ba ƙaramar matsala za’a samu ba, damuwarta yanzu akan Sojojin ce shiru basu dawo ba, Kuma bata Ji daga bakin dr laura Ya ake ciki ba, Shin za’a maidasu ƙasarsu ne ko kuwa a’a, Ta dai zubawa sarautar Allah Ido 👀 Sam ta kasa runtsawa, tun wuraren ƙarfe tara na dare ta farka, saboda mugun bugun da ƙirjinta ke yi mata, tabbas tana ji aranta wani abun ne ke shirin faruwa. Miƙewa Tayi zaune saman gadonta, ta jingina Bayanta Jikin pillow, idanuwanta suna a lumshe, sanyin A.c sai ratsa fatar jikinta Yake yi wata irin kasala take Ji da matsanancin faɗuwae gaba. “Masoyiya Angel, Lafiya kika farka daga bacci? Na lura kamar wani abu ke damunki” Muryar Nurse Jessica ce ta fargar da ita, har saida ta ɗan zabura don bata yi tsammanin jin Muryar mutun a kusa da ita ba. Slowly ta wurga eye balls ɗinta akan fuskar nurse ɗin, tana daga zaune saman chair ta kusa da gadonta, hannunta ruƙe da wayarta, fara ce sol, uniform ɗin jikinta light blue ne kalar nasu, ta ɗaure jar sumar kanta da ribbom. Nauyayyar ajiyar zuciya Angel ta sauke tare da cewa”sister, nagode da kulawarki agareni, nakasa runtsawane saboda inason ganin yan uwana ko zaki Iya taimaka min”? Smiling gently nurse jessica tace”Na lura kina son ƴan uwan nan naki, cos tun ranar dana fara kula da ke, sau uku kike zuwa room ɗinsu Kina duba su, faɗamin ko dai akwai damuwane? Ko tsoro kike ji kada mu sace maki su”? Da zolaya nurce jessica tayi mata maganar Cikin jin kunya Angel takama ƴan kame kame tana faɗin”am.... Ba haka bane just inason su sosai, mun shaƙu da juna, shiyasa bana samun natsuwa idan ban gansu akai akai ba” Nurse jessice tace”Kuna burgeni sosai, inaso Inga ƴan uwan masu son junansu, masu haɗin kai, ta hakanne ake cin ribar zaman duniya, idan har kana da ɗan uwa mai share maka hawayenka, mai nuna maka ƙauna wanda baya gajiya dakai tabbas ka gode ma Allah, zai yi wuya ka rasa madafa a duniyar nan, babu wanda zai yi gigin cutar dakai muddin kuna da haɗin kai a tsakaninku, amma idan Ya kasance kuna ƴan uwa baku da haɗin kai, danasani zai biyo baya cos dayawa rashin kulawa keja har damuwa tayi ma ɗan uwanka Illa, ya akaita abunda zakuyi danasani gaba dayanku” Angel ta natsu Tana sauraron Kalaman Nurse Jessica, Haƙika kalamanta sun ta6a mata zuciya, sai taji ta ƙara ƙaunar ƴan uwanta, ta ɗanyi mamakin yarda nurse ɗin take sakar mata fuska suke Yin fira, saboda ta ta6a Jin ana faɗin turawa sun tsani baƙar fata suna nuna masu wariyar launin fata, sai dai tayi tunanin ba duka aka taru aka zama ɗaya ba, sannan kuma su basu da banbanci dasu, hasken fata, launin ido da kuma sumar kai, shiyasa suka zama ɗaya. “Ki tashi muje in raka Ki ɗakunan ƴan uwan naki, Nima Inason ganin su, musamman twins ɗin nan” murmushine Ya bayyana akan fuskar Angel jin abunda nurse ɗin tace, tuntuni ta faɗa mata, ba twins bane Jamimah da azeeza ɗaya ta girma ɗaya amma taƙi yarda, ba ita kaɗai ba hatta sauran nurses ɗin da likitocin kallon twins suke Yi masu acewarsu Basu da banbanci, Komai nasu kala ɗaya. da zumuɗi Angel ta sauko daga saman gadon, light blue uniform ɗinta ne a jikinta, sai da ta fara zuwa gaban closet ɗin ɗakin ta buɗe ta ɗauko Hijabin da aka bata Nayin sallah ta zura a jikinta. Hannunsu ruƙe cikin na juna ita da nurse ɗin suka fito daga ɗakin, hasken electric bulbs Ya haskaka Asibitin tamar da rana, a tsanake suke Yin tafiya suna tattaunawa a tsakaninsu, ɗakin Gabriel suka Fara shiga, tayi mamakin ganinshi idon shi biyu Shida nurse rebecca, ta kunna masu kallo sun natsu abunsu. Jin motsin shigowar Mutun yasa suka kai eyes dinsu ga ƙofar, murmushi ne ya bayyana akan faces dinsu Mayar masu da martanin murmushin nasu Angel tayi”ɗan uwana, Baka Yi bacci ba? Fadamin meya hana ka Yin bacci”! Kafin Ya bata amsa nurse rebecca tace”Ni na hana shi, Ko bakisan mun fara soyayya bane, Gabriel baka faɗa mata ba”? Gaba daya suka sanya dariya, jessica tace”har kinyi kamu kenan” ɗaga mata gira tayi”yap, taya zan bari damar nan ta wuce ni”? Firarsu ba ƙaramin nishaɗi take sanyasu ba, Angel tuni ta haye saman gadon gabriel, Ruƙo hannunshi tayi acikin nata, “My sister, meya hana Ki yin bacci”? Ƙasa ƙasa da murya ta furta”Danish, Hankalina Yaƙi kwanciya da rashin farkawarshi, Yaufa kusan One week kenan a lissafina, Gabriel bansan ya zanyi ba, Ni nafi so Mu koma nigeria....”katse mata maganar yai da cewa”ai kin faɗamin dr laura tace zata taimaka mana mu koma can ko? Ɗaga mashi kai Tayi”eh, amma har yau shiru, banji daga gareta ba, Kuma kaga sojojin basu ƙara dawowa ba” Ganin kamar duk ta damu yasa shi kwantar mata da hankali”Wani jinkirin alkhairi ne Angel, wata’ƙil ki ga gobe anzo mana da kyakkyawan labari, don haka Mu ƙara haƙuri kada mu damu kanmu komai zai tafi dai dai My lovely sister” Yai magabar Tare da jan kumatunta da hannunshi, Hakan ba ƙaramin dariya Ya bata ba. “Masoyiya Angel, zamu Iya tafiya “? Muryar nurse Jessica ce ta katse masu tattaunawar tasu. Peck tayi mashi saman cheek dinsa”ka kwanta ka huta,” ta ambaci hakan tare da saukowa daga saman gadonshi ta nufi nurse jessice taja hannunta suke fuce bayan sunyi masu sallama. Room ɗin Batul suka shiga, A kwance suka same ta saman gado, ta ƙudundune da bargo, da alama tayi zurfi abaccinta, Basu shiga ɗakin ba suka wuce ɗakin Jemimah, Itama baccin take Yi, ta wawware ƙafafuwanta ta saki baki da hanci, nurse din dake kula da ita, Tana acikin ɗakin har gaisawa sukayi da ita kafin suka nufi ɗakin Azeeza, Kamar yarda suka samu jemimah haka suka sameta a kwance bacci yai daɗi, murmushi Angel tasaki kafin suka ƙara gaba zuwa ɗakin Parveen, Hallau dai mai hali Baya ta6a canzawa, bata Yi mamakin ganinta a zaune gefen gado ta tasa abinci saici take Yi, An kunna mata tv tana kallon mbc channel Suna Yin cartoon tom and jerry, Sai tiƙar dariya take Yi kamar zata kifa kanta saman table din gaban gadon, babu alamun bacci a idonta, sam bata ji motsin shigowarsu ba, plate ɗaya ne agabanta shaƙe da chicken wings, gefen plate ɗin kuma Apple juice ne, Duniya Ta yi mata daɗi, Gyaran muryar da Angel Tayi mata ne yai silar Jawo Hankalinta ga dubansu, bakinta cunkushe da nama ta furta “Angel” Nurse ɗin da suka zo atare da ita sai murmushi take saki, Da alama parveen ta burgeta, ba tun Yau ba, duk in tazo dubata sai ta sameta tana Cin abinci, da wuya ka same ta bakinta babu abun taunawa. Farin Cikine Ya bayyana akan fuskarta, Da sauri ta ƙarasa suka rungume juna ita da Angel. Shafa sumar kanta Tayi”Parveen kowa Yai bacci banda ke, kina nan kinata cin abinci Ko gajiya bakya yi, so kike ki karya masu jari ko”? Da zolaya tayi maganar, bayan ta raba jikinta daga na Angel, Just 4days Har kumatu ta ƙara. “Ai nurse ɗinne Yace min duk in ina buƙatar wani abu Inyi mashi magana...” zaro ido Angel Tayi hada ruƙe ha6a tace”Eyehh! Wato saboda yace maki haka shine kuma ko da wani lokaci sai kince mashi zaki ci abinci, Angaya maki nan Restaurant ne? You’re a patient bai kamata aga kina cunkushe cunkushen abinci, kamar me fama da cutar Yunwa” sam Sun manta da nurse din da ke abayansu, Da turancin Angel Keyin maganar, hakan Yasa ta fahimtaci abunda suke tattaunawa, sai faman sakin murmushi take Yi tana binsu da kallo. “Angel ai su ba ruwansu, komai mutun yake so suna yi mashi, baki ga yarda nurse din Ya ke ji dani ba, Shine ma Ya kunna mun abun nan ba ƙaramin Daɗi naji ba” ta yi magana tana nuna mata plasma tv Watsa Hannu Angel Tayi”Okey, Koma Ki cigaba da cin abincinki, pls Ki samu ki kwanta ki huta, ki kula mun da kanki” murmushi parveen ta sakar mata “Thank u sis, Allah yabar mana Angel ɗinmu” Nurse jessica ta tsaresu da ido, gwanin ban sha’awa take kallon su Sallama sukayi Ma parveen bayan sun fito daga ɗakin suka nufi ɗakin Hannah, Yarinya ƴar madara, hankalinta kwance take sharar baccinta, Rabin jikinta duvet ne. Bayan sun ƙara gaba ɗakin Naufal su ka shiga da ɗakin Javed, Kowan nan su bacci Yake Yi, daga ɗakin Javed suka nufi ɗakin Haris, Bawan Allah ba laifi Jiki Yai kyau, yana samun kulawa fiye da sauran ƴan uwanshi saboda lalurar shi. Sunyi tunanin bacci yake yi ganin shi kwance ya rufe idanuwanshi, Har sun Juya zasu fuce muryar shi ta katse masu hanzarinsu “Angel!” Atare suka Juyo suna kallonshi, Ya buɗe idanuwanshi da suke a lumshe, farin Cikine Ya lullu6e Angel, da sauri ta nufi gadon shi daga gefe ta haye, taimaka mashi tayi ya mike zaune, ta rungume shi a chest ɗinta, hannunta asaman bayanshi tana shafashi “Haris ɗina Ya jiki naka da sauƙi ko”? Muryar shi, ƙasa ƙasa Ya masa mata”da sauƙi Angel, bana jin ciwo a jikina sai dai har yanzu ina yin mafarki akan Deejana, ina ganinta a prison suna azabtarmin da ita, tana kuka tana roƙona akan in taimaki rayuwarta’ cikin rauni na murya yai maganar “Ka kwantar da hankalinka haris, Mafarki ba gaskiya bane, sau dayawa mafarki Shaidanne yake assasa shi, wani daga Allah ne wani mafarkin kuma ya danganta daga Yarda ka ƙwallafa abu aranka, shiyasa nace ka dage da yin addu’a, in sha Allah haris in dai Deeja tana araye zaku haɗu ne,” Nurse ɗin ta zuba masu ido tana kallon su, bata san me suke tattaunawa ba a tsakaninsu, saboda sunyi amfani da harshen hausa. Still Haris bai ɗago kanshi daga saman chest ɗinta ba ji yake kamar deejanshi ce “Wlh Angel inason deejana, Kuma inayi mata addu’a, Ko yanzu da kika sameni na rufe idanuwana, addu’a nakeyi mata, Ni bazan ta6a gajiya dayima deeja addu’a ba, Har nunfashina na ƙarshe” Tuni idanuwan Angel sun cicciko tab da ƙwalla, (Ƙaunar dake a tsakanin haris da Deeja, daga Allah ne, irin son da ake kira true love, Inason ka kana so na badan wani abu ba❤ Allah Ya bamu masu sonmu tsakani da Allah🙏) Shafa sumar kanshi Angel Ta yi da hannunta, Jin shessheƙar kukan shi Ba ƙaramin Karya mata zuciya yai ba “Haris pls don’t cry, kasan bana son jin kukan ka, ko ba danni ba, nurse da ke kula dakai bazata Ji daɗi ba, Suna iyakar bakin ƙoƙarinsu wurin ganin sun sanyaka farin ciki duk don ka rabu da ciwon zuciyar dake damunka” a hankali ya ɗago da kanshi Idanuwanshi sun ɗan kumbura. “Angel, nadaina bazan ƙara ba” tafin hannunta ta ɗaura saman fuskarshi tana share mashi hawayenshi “Zan tafi Yanzu nurse tana Jirana, Amma kafin nan kayi min murmushi mana” daƙyar ya ƙaƙaro murmushi kan fuskarshi, Hakanan taji gabanta Ya faɗi ƙura ido tayi akan face dinshi kamar tana son gano wani abu sai dai ta kasa gane menene shi. Ganin yadda take kallonshi yasa yace mata Lafiya Angel’? Girgiza mashi kai Tayi bakomai, ka kula mun dakanka, Sai Allah Yakaimu” daga haka ta sauko daga sama gadon, suka fice daga ɗakin shi ita da nurse jessica. Last room da suka Nufa ɗakin Garkuwa, tunkafin su ƙarasa take Jin faɗuwar gabanta na ƙaruwa, ji take yi kamar idan ta shiga ɗakin wani abu zai faru, Da bismillah abakinta ta kutsa kai dakin nurse jessica tabi Bayanta, kamar matacce haka suka same shi kamar kullum Sai sharar baccin shi Ya ke yi, Lamarin Danish ba ƙaramin ɗaurewa likitoci kai Yai ba, tsawon kwanaki mutun Yana yin bacci yaƙi tashi? Tun abun na damunsu har sun haƙura sun zubawa sarautar Allah ido. Saman chair nurse ta zauna idonta akan face din Danish A hankali Angel ta zauna gefenshi Tana ƙare mashi kallo, Ji take yi tamkar ta fasa ihu acikin kunnuwanshi wata’ƙil idan Yaji zai farka, sai da tasan ko Tayi abanza, Allah shine shaidarta, ta matsu a ƙagare take da son farkawarshi kamar ta yi hauka Sam ta manta da nurse dake a ɗakin, ta natsu tana kallon shi kamar zata Haɗiye shi, A hankali Ta ɗaura small pink lips ɗinta farar fatar cheek dinsa ta manna ma kiss. Murmushin gefen fuska nurse jessy ta dan saki, abun ba ƙaramin ƙayatar da ita yai ba, kamar ta samu tv haka take kallonsu. A hankali Angel ta kwantar da kanta saman faffaɗan chest dinshi ta kasa kunne tana sauraran heart beat dinsa Muryarta cikin raɗa take Yin magana”My man pls wake up, nayi kewarka kamar zan zauce, dan Allah ka taimaki rayuwana ka farka danish, a matse nake duk na takura da rashinka, pls idan kana Jina Ka amsa min” hauka ta soma yi mashi asaman jikinsa tabi duk ta hayeshi, shessheƙar kuka tadinga yi mashi duk don ya farka sam babu hawaye akan face dinta, ɗagowa tayi da kanta, gray eyes dinta akan fine face nasa, eyes lashes dinsa ta ƙurawa ido masu kyau da tsari. Bakomai take tunawa ba face Farkon haɗuwarsu a prison, a karo na farko da Ta yi tozali dashi saida gabanta Ya faɗi saboda zazzafan Kyanshi, Murmushi tasaki tunawa da maganar farko data fara haɗasu lokacin da tana zazzaga masu masifa akan afaɗa mata ubanwa ya kawota prison Muryarshi ta ratsa kunnanta, tamkar ana busa sarewa “Bansan wacece ke ba, amma na lura kamar kina son wuce gona da iri, yakamata ki kiyaye harshen ki, wannan tsohuwar da ki ke gani tamkar uwa take agare mu, tun da mu ke da ita bata ta6a cutar damu ba, muna samun kyakkyawar kulawa daga gare ta, don haka bazamu bari zuwan ki ya zama silar tarwatsewar farin cikin mu ba hope u understand me!” a lokacin takai maƙura A zafafe Ta juyo ta kalle shi tsabar mamaki tamkar ba daga bakinshi maganar ta fito ba, duk da bugun da zuciyarta tayi mata na ganin kyanshi hakan bai hanata zazzaga mashi masifa ba. “Sannu isasshen me walkin sa! Kai kuma a suwa ɗan wake a hotel? am talking you are talking? duk wanda ke son zaman lafiya acikin ku, kada ya kuskura ya shiga gona ta, domin ni ba irin ku bace! Wlh uban mutun zanci kuma a zauna lafiya!” Batasan lokacin da dariya ta kubce mata ba, Rayuwa kenan, Idan mutun ya kasance ƙaddararka baka isa ka canza shi ba, bata ta6a tunanin zasu sasanta tsakaninsu ba, saboda rashin jituwarsu sai gashi a yanzu sun shaƙu da junansu ita da sauran ƴan uwanta prisoners. Nurse Jessica Har tafara Gajiya da zama bacci na shirin kwasarta a saman kujera, sam batason ta katse Angel donta fahimci ba ƙaramin so take Yiwa ɗan uwan nata ba, duba da yadda ta haye saman jikinshi tana sambatu hada murmushi da dariya. Soft lips ɗinsa ta ƙurawa ido tamkar anyi mixing din launinsu da pink “Masoyiya Angel Yakamata mu koma ɗaki ko”? Muryar Nurse jessica ce ta fargar da ita, Amsa mata Tayi da toh Kafin ta miƙe ta ɗan dukar da kanta saitin fuskarshi sumar kanta ta yi mashi rumfa, A hankali ta ɗaura small mouth ɗinta saman Forehead dinsa Da Niyar ta manna mashi peck ba zato ba tsammani taji ya damƙi waist dinsa ruƙo bana wasa ba, Agigice Take kallon face dinsa wani abun mamaki bai farka daga baccin ba, tashin hankalin da ba’a sama shi data, Nan take Jikinta Ya hau Yin kakarwa ido Ya raina fata, wata irin zuface ta soma tsastsafo mata ta cikin hudar gashin jikinta....... *Boss Bature✍️ Mu haɗu Monday Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*_ ~Middle step~ _The Prisoners E20🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* Hankalinta a matuƙar tashe take kallon fuskarshi, Numfashinta na hauhawa zuciyarta na bugawa da sauti mai ƙarfin gaske tamkar zata tsaga ƙirjinta, tsabar tsoratar da ta yi, Nurse Jessica da ke a zaune ta rasa gane meke faruwa ne? taga dai tun da Angel ta yi mashi rumfa taƙi motsawa, kamar an daskarar da ita, idanuwanta ba su hango mata hannun Danish da ya damƙi Qugun Angel da shi, sakamakon Sumar Kanta da Hijabin jikinta sun lullu6e shi. “masoyiya Angel, Ke nake Jira, kusan ƙarfe goma na dare, Yakamata Muje ki kwanta ki kwanta ki huta” Cikin Kulawa ta yi mata maganar Tana leƙen fuskarta sai dai bata samu damar ganinta ba, saboda wuyan Hijabinta Ya zame tuntuni sumar kanta ta zazzago gefe da gefen fuskarta, ta rufe su. Yunƙurin kubcewa tayi daga ruƙon nashi sai dai ko gizau wannan bai yi ba, kuma bai motsa ba, Ya matseta A jikinshi, tamkar an ɗaureta da igiyoyi, duk da sanyin A.c na room din hakan bai hana ta zubda gumi ba, zufar dake wanko fuskarta kaitsaye take sauka saman fatar face nasa, idanuwanta azazzare, yayin da acan cikin zuciyarta ta ke ta ambaton”INNA LILLAHI WA’INNA ILAIHIRRAJI’UN”! Ba ƙaƙƙautawa. Muyar Nurse Jessica ce ta ƙara fargar da ita”Lafiya kuwa Angel? Ya akai naji Kinyi shiru? Ko kinyi bacci ne a jikin shi” ta ƙare maganar tare da yunƙurawa ta miƙe daga saman chair ɗin ta nufi gaban gadon ta tsaya tana ci gaba da yi mata magana, tsabar yadda la66anta ke yin kerma ta kasa buɗe baki ta faɗa mata Halin da take a ciki. Miƙa Hannu nurse jessica ta yi da niyar ta ɗago da Angel, saboda ta yi tsammanin bacci ne Yai awon gaba da ita, Sai dai Kafin ta ruƙo ta, Angel Ta yi ƙoƙarin Yin magana Muryarta A hargitsa ba natsuwa ta furta”ɗan Uwana Ya farka! Shine Ya ruƙe Ni” Mamaki Ne Yasa Nurse jessica Zaro Ido haɗi da buɗe Baki, Ta Furta” Are u serious Ya farka? “Ya farka, but he didn’t open his eyes. He held me so tightly that I couldn’t separate myself from him” cikin shessheƙar Kuka Angel ta furta maganar. Jin haka Yasa Nurse jessica faɗin”Bari Na taimaka maki ki miƙe” Hannu Biyu ta sanya ta ruƙe Angel ta soma kiciniyar 6an6arota daga Jikin Danish da Iya ƙarfin ta na ƙarshe sai dai takasa ta6uka komai, Mugun ruƙo Yai mata, Hatta dogayen nails ɗinsa sun yi mata shatu saman bayanta, Lamarin ya ɗaurewa Nurse Jessica kai, ganin ta sanya Iya ƙarfinta na ƙarshe Amma abanza, hakan ba ƙaramin ruɗar da ita yai ba, Muryarta na rawa ta furta”Bari naje na kira doctor” Da sauri ta fuce daga Cikin ɗakin hada ɗan gudunta A lokacin da bata Yi tsammani ba, Sexy voice ɗinsa ta ratsa kunnuwanta muryar da ta daɗe tana mararin Jinta “My Angel” Iya abunda ya furta mata kenan. nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke, jin ya ambaci sunanta, hakan na nufin Yana acikin Hayyacinsa, ƙura ma fuskarshi ido tayi ganin yana mutsu mutsun buɗe idanuwanshi, sannu A hankali yake ƙoƙarin ware su, sunyi mashi nauyi saboda baccin da yai na tsawon kwanaki, Ta yi matuƙar ƙagara da son Yin tozali da kyawawan Reddish-brown eyes ɗinsa, kaɗan Ya buɗe su bai ƙarasa ware su ba, sun ciza launinsu, hakan ba ƙaramin kyau suka ƙara ma shi ba, Tsabar farin ciki batasan sa’adda ta fashe mashi da kuka mai tsuma zuciya, tana haɗawa da dariyar farin Ciki, ya natsu yana kallonta da wata irin kasala a jikinshi, sam bai san a ina suke ba Iya fuskarta Yake Iya gani. Cikin shessheƙar kuka haɗi da shagwa6a take faɗin”Nayi missing ɗinka My man, sai yau zaka farka? Kabarmu da kewarka da fargabar a wani hali zaka tashi, sannan kuma ka tsoratar dani sosai....” lumshe idanuwanshi ya ɗanyi tare da ware su saman fuskarta, Hawayenta sai jiƙa masa face dinshi suke Yi, har cikin bakinsa, hakan bai dame shi ba, tamkar ya samu ruwan sha, haka ya ke yin swallowing dinsu. Kallon da ya ke yi mata kallo ne dake nuni da tsantsar ƙaunarta da kewarta da yayi, hucin numfashinsu sai gaurayewa yake yi dana juna, hakan bai sha masu kai ba. Idanuwanta sharkaf da hawaye sun rune jawur taci gaba da cewa”dan Allah ka faɗamin ba abunda ke damunka? Naga kanata kallona kaƙi kula ni” ta ƙare maganar still da shagwa6a, yamutsa fuskarshi yaɗanyi haɗi da motsa tausasan la66ansa calmly ya furta “ke ce damuwata, kinsan bana son zubar hawayenki, ki daina yi min ku ka or else I’ll go back to sleep yai maganar yana ƙoƙarin lumshe idanuwanshi da zolaya yai mata hakan aiko da sauri ta shanye kukanta, tana faɗin”na daina My man, kaine ka ƙi kwantar min da hankali na” ba zato ba tsammani taji ya manna mata peck saman fore head dinta, farin ciki duk ya cikata. Muyarta har shaƙewa ta ke yi saboda kukan da tasha”ka sake ni, Ka matse ni” tayi maganar tana ƙoƙarin kubcewa daga ruƙon da yai mata, so ta ke yi ta nuna mashi sabon wurin da suke acikin shi, ƙanƙameta Ya ƙara yi yana faɗin “Ki jira, zan sake ki, ina samun natsuwa atare da ke” ƙayataccen murmushi ta saki, ta ɗan dakata suna kallon cikin idon junansu, lokaci ɗaya taga Ya haɗe face dinsa. “Lafiya”? Tai tambayar tana cigaba da kallon shi “Namanta, ban sama maku abincin da zaku ci ba, Na bar ku da Yunwa” Murmushin gefen fuska ta sakar mashi”Ka kwantar da hankalin ka, Muna cin Lafiyayyan abinci har sai mun ture, shiyasa nace ka sake ni inason nuna maka wani abu” slowly ya zame hannunsa daga ruƙon Da yai Mata, Light bulb ɗin ɗakin Ya haske mashi ido, saukowa tayi daga saman gadon ta fuskanci gabas Ta duƙa tayi sujjada tana godewa Allah daya farkar mata dashi cikin ƙoshin Lafiya ba tare da wani abu ya same shi ba. Alhamdulillahi Ala kulli Halin. Ya yi matuƙar Yin mamakin ganin room ɗin da ya ke aciki, a kasalance ya yunƙura Ya miƙe zaune yana ƙarewa ko’ina Kallo, tunani ya shiga yi Ina ne nan? Waye ya kawo su? Fuskarshi da alamun ruɗani ya Tura yatsun hannunshi cikin yalwatacciyar sumar kanshi yaci gaba da cakuɗata tamkar yana sosata, saukowa ya yi da ga saman gadon. Jikinshi yayi mashi nauyi daƙyar yake taka ƙafarshi, yayin da yake ƙarewa ɗakin Kallo, Angel tana a duƙe tun da tayi sujjada bata ɗago ba, addu’o’i take tayi masu. Yana ƙoƙarin buɗe baki da niyar ya yi mata magana, Sai ga doctors da nurses sun shigo ɗakin da saurin su, Kusan atare su ka ci uban burki suna kallon kallon a tsakanin su da shi, Mutumin da suka daɗe suna mararin ganin Ya farka, sai yau Allah ya nufa zai tashi, Sun yi matuƙar girgiza da ganin Shi a tsaye kan ƙafafun shi, kyan fasalin shi Ya yi masu ƙwarjini. Da hannu Yai masu Alamar su wanene su? Sai Ƴan kame kame suke Yi An rasa me Iya buɗe Baki Yayi mashi magana. Juyawa yai da sauri Yaje gaban Angel da ta yi sujjada, Da hannu ɗaya ya ruƙo damtsen ta, Ya ɗago da ita tsaye kamar wata ƴar baby, nuna mata likitocin Ya yi da hannun shi “Who are they, and where are we?” daƙyar ta samu natsuwar Fayyace mashi komai tun daga kan Yadda aka tsunto su a daji aka zo da su asibitin kamar yadda Gabriel Ya sanar da ita. Bayan ta gama kora mashi jawabi ta kalli fuskokin likitocin tace “ku ta ya ni murna ɗan uwan mu Danish Ya farka” murmushi kowan nan su Ya saki Nurses din dake a cikinsu kamar sun samu tv haka suke Binshi da mayataccen kallo, ba mazan ba ba matan ba. “Muna ta ya ki Murna masoyiya Angel, munga brother ɗinki Ya farka cikin koshin Lafiya” nurse jessica ce Tayi maganar Daƙyar wani dr ya iya buɗe baki yace”Danish Fatan Ka tashi Lafiya, tsawon lokaci muna jiran ranar da zaka buɗe idanuwanka, Sai yau muka samu damar ganin ka, Mun ji daɗi sosai” yai maganar tare da miƙa mashi hannu don su gaisa, Man ɗin fa bai yarda da su ba, dama yana da wuyar sha’ani ga ƙiwuya kamar ƙaramin Yaro. “Danish Ka miƙa mashi hannu ku gaisa” Angel ce tayi mashi magana, goya hannayenshi yai saman broad chest dinsa, Alamar ba zai miƙa mashi hannun ba” murmusi yaƙe ta ɗan saki”ku yi haƙuri, Danish baisan ku ba, Har yanzu baccin bai sake shi ba, nasan kafin zuwa gobe zai Warware’ Nurse rebecca tace “badamuwa, Dama mu fatan mu Ya farka da ranshi da lafiyarshi, Hakan ma ya wadatar” Dr. Anthony Yace”Calm down, Danish. No one will bother you. We are doctors, and we have the right to check your health until you feel better.” still bai tanka masu ba. Dr harry yace”ni dama tun kafin Ya farfaɗo raina Ya bani zai yi wuyar sha’ani, sai gashi maganata ta tabbata, mutane masu irin Kyanshi bakowa suke kulawa ba” da zolaya yai maganar, Ya ƙara da cewa “mu dai yakamata asaki jiki damu tunda malaman lafiya ne, muna so ka bamu dama mu ƙara bincika Lafiyarka” tun da suka fara Magana bai tanka masu ba sai kallo da yake binsu dashi kamar yaga wasu halittu daba na mutane ba. “Ko akwai Inda ke yi maka ciwo yanzu”? Dr anthony ne yai mashi maganar, Angel sai ƙoƙarin ingiza hannunshi take Yi don yayi masu magana amma Yaƙiya, Nurse jessica tace”ga dukkam alamu rowar muryarsa yake yi mana, Ni inaga Mu ƙyale shi zuwa gobe nasan zai warware kuma zai saki jiki da mu” Kamar za su yi hauka wurin yi mashi magiya don yayi masu magana yayi shiru abunshi, har so sukayi su bincika lafiyarshi amma Ya hana, duk wanda yai gigin matsowa kusa dashi, zazzare masu ido yake yi alamar zaiyi fighting dinsu, lamarin ya ɗaure masu kai, ganin sun sanya naci akan sai sun duba shi, Angel ta roƙe su akan su ƙyale shi zuwa gobe, fargabanta kada su hayaƙa shi azo asamu matsala, tunda harya fara zare masu ido yana ɗaure masu fuska. Ba don sun so ba, su ka yi masu sallama da niyar gobe zasu dawo, kusan atare suka fuce waje, aransu suna Ayyana irin kyawun fuskarshi da surarshi, sai santin shi suke Yi musamman nurses din cikin su. Su Uku Suka rage a ɗakin, Nurse Jessica ta dubi Angel”na lura brother ɗin nan naki, ke kaɗai yake jin maganarki, Inaso ki tambayar min shi ko akwai abunda yake buƙatar ci”? Kallon shi Angel Tayi, idonshi na akan plasma tv ta ɗakin, sai ƴan kalle kalle yake yi. “My man kana jin Yunwa”? Da budar bakinsa sai cewa yai”Ina haris da su Batul? Inason ganinsu” Kallon Nurse din Tayi”yace yana son ganin ƴan uwanmu” gyaɗa kai tayi”badamuwa Zamu Iya zuwa” Ruƙo Hannunshi tayi acikin nata”muje in nuna maka su” nurse jessica tana agaba suna abayanta, tun da suka fito daga ɗakin Yake ƙarewa ko’ina kallo, agogo kaɗai mutun zai kalla ya gane cewa dare ne amma donta hasken light bulbs na asibitin ba za ka ta6a gane dare bane. Nurses ɗin dake yin zarya da doctors sai satar kallon shi suke yi, hada masu yin tuntu6e. Ɗakin Haris suka Shiga, tun bayan fitar Angel bacci ya ɗauke shi. Rabin jikinshi lullu6e da bargo, da sauri Danish ya ƙarasa daga gefen gadonshi Ya zauna Yana kallon shi, nurse da Angel suna a tsaye suna dubanshi. “Bacci ya ke yi Danish, ko zamu bari sai gobe idan Ya farka mu dawo” ɗaga mata kai Yai alamar eh, dama burinshi ya gansu hankalinshi sai yafi kwanciya, ɗaura hannunshi yai saman sumar kan Haris ya shafata a hankali, tsantsar farin Cikine akan face dinsa’ mintuna Biyar kafin Ya miƙe, suka nufi ɗakin Batul, ko da suka shiga, basu sameta a saman gadonta ba, nan fa hankalin Angel Ya tashi, “ina batul taje” nurse jessica harta buɗe baki zata bata amsa, suka ji motsin fitowarta daga toilet, Kamar a mafarki take kallonsu kafin ta tsayar da idonta kan Danish, da ƙarfi ta ambaci sunanshi, da gudun gaske fa ƙarasa ta faɗa saman faffaɗan ƙirjinshi, ɗaura Hannayenshi yai saman bayanta sosai ya yi tighting ɗinta, daɗi kamar zai kasheta, annurin fuskarshi sai ƙara nunkuwa yake yi, da alama yaji daɗin canjin rayuwar da suka samu. Ɗagowa tayi da kanta daga saman chest dinsa, ido cikin ido suke kallon juna, tuni hawaye sun cika idonta muryarta na rawa ta soma yin magana “Ɗan uwana rabin raina, kaga canjin rayuwar da muka samu ko? Nasan Angel ta faɗa maka komai, Danish ba zamu Iya misalta kewarka da mu ka yi ba, wlh naji daɗin farkawarka nayi farin cikin ganinka” a tsanake ya furta mata”nima nayi farin ciki Batul, Ina taya mu murna, ina yi mana fatan wannan ya kasance ƙarshen wahalarmu” Angel da nurse jessica sai murmushi suke saki yayin da suke kallonsu. “Danish nasan za ka ji wani iri, nan ba kamar prison ba, inda aka ƙuntata rayuwarmu, tun muna Yara wannan ne karo na farko da muka fara tsintar kanmu awajen prison cikin mutanan duniya, Iskar da muke shaƙa a yanzu ta ƴanci ce bata kurkukun ƙaddara ba” kalamai masu daɗi take faɗa mashi “Muna samun kyakkyawar kulawa awurin mutanan nan” tayi maganar tana nuna mashi nurse jessica”sun bincika Lafiyarmu, kuma sun taimaka mana wurin samun sauƙi, sannan muna samun Cin abinci har sau uku arana, komai muke so sunayi mana, Ina fata kaima zaka saki jikinka da su sannan ka ba su haɗin kai donsu duba lafiyarka, idan akwai wani abu dake damunka zasu taimaka maka wurin samun sauƙi in sha Allah, sannan idan kana Jin yunwa ka yi masu magana zasu baka abinci, ba sai kasha wahalar neman abunda zaka Ci ba...” muryarta na rawa ta ƙarasa maganar, hawaye tuni sun cigaba da wanke face dinta Ɗaura tafin hannunsa yai saman face nata, share mata hawayen fuskarta ya soma Yi Calmly ya furta”its ok, stop shedding ur tears, ngde da shawararki, zan basu haɗin kai,” “Danish babu wasu kalmomi da zan Iya yin amfani da su wurin yi maku godiya kai da Angel, Allah ne kaɗai zai Iya biyan ku, haƙiƙa kun taimaki Rayuwarmu kun gatanta mu, kun yi mana silar barin mu kurkukun ƙaddara, duk wani cigaba da zamu samu a duniyar nan kune sila, ba zamu ta6a mantawa da halaccin ku agare mu ba, kun fiye mana iyayenmu sau dubu, matsayin da suka rasa awurinmu kune kuke ruƙe da shi....” sosai ta fashe masu da kuka, Janyota yai zuwa saman chest dinsa ya ƙara yin hugging dinta yana lallashinta. Daƙyar ya samu Batul ta dakata da yin kukan, bayan ya raba ta da jikinsa, ta rungume Angel sosai suka ƙanƙame juna, tsawon mintuna kafin suka raba jikinsu. “Allah yabar Mana ke, Our Super star, Allah ya cika maki burikanki dake da Danishi ɗinmu” murmushi kowan nan su ya saki, sun ɗan jima a ɗakin Batul kafin suka Yi mata sallama, Sauran ɗaku nan su Azeeza suka shiga kowan nan su bacci ya ke yi, Ya haƙura sai zuwa gobe zai gaisa da su. Komawa ɗakinshi su ka Yi, nurse jessica tace da Angel, zata kawo mashi Abinci, kafin ta dawo ta taimaka mashi Ya shiga toilet ya gyara jikin shi, amsa mata tayi da toh, Bayan fitar nurse ɗin, Taja hannun Danish suka shiga toilet, tun da suka shiga yake bin ko’ina da kallo, Karaf Ya ɗaura Idonshi Kan madubin toilet din A firgice taga Ya Juya mashi Baya. “Danish meya faru”? Hankali atashe tayi mashi Tambayar “Bana son ganin shi,” ba ta yi mamakin jin abunda yace mata ba, tunawa da ranar da tsohuwa tamira ta basu kyautar madubi, kowa ya duba fuskarshi, amma shi Yaƙi Yarda ya kalle shi. Dubara tayi wurin Cire Hijabin jikinta, taje gaban mirror ɗin ta lullu6e shi. “Nayi maganin matsalar Juyo ka gani” a hankali Ya juya yana kallon mirror din nan take ya sauke ajiyar zuciya, ganin ta rufe madubin. “My Man, Ka fara Yin wankan, almost one week jikin ka bai ga ruwa ba, I’ll wait for you outside.” Akan idon shi ta fuce, a bakin ƙofar toilet din ta jingina Bayanta tana jiran fitowarshi, ta kasa kunne tana sauraron motsinshi, daɗi take ji kamar wadda akayiwa albishiri da gidan Aljanna, a ƙalla ta sauke ajiyar zuciya yafi a ƙirga fatanta Allah yasa subar america batare da sun samu wata matsala ba. Gaba ɗaya hankalinta baya atare da ita, gangar jikin ce kaɗai, ruhin Yana atare da Danish dake acikin toilet, har Nurse jessica ta shigo ɗakin hannunta ruƙe da food trolley, ta gunguro shi zuwa gaban table, murmushi tasaki tana kallon Angel dake maƙale jikin toilet door, aranta ta ayyana ko dai soyayya ce a tsakaninsu, don wannan shaƙuwar tasu tafi ƙarfin a kirata da abokantaka. Bayan ta ƙaraso gaban table din, ta soma jera kayan abincin saman shi, har ta gama jera su, ta juya da food trolley din duk Angel bata lura da ita ba, Har ta fuce daga ɗakin. Jin motsin buɗe ƙofarshi, Yasa tayi saurin komawa gefen gado ta zauna tana faman sakin murmushi kamar wata zautacciya. Zuro ƙafarshi yai saman carpet dake gaban ƙofar shiga toilet ɗin, Kafin ya ƙarasa fitowa, jikinsa da danshin ruwan wanka da yai, Ya maida uniform dinsa da aka sanya mashi. Tun ya fito idonshi na akanta, ya lura da tsantsar farin cikin dake akan fuskarta, Hakan ba ƙaramin daɗi yayi masa ba. Gefenta Ya zauna yana ƙare mata kallo “Na fito” sai da ya ambaci hakan tukunna ta ɗago suka haɗa ido wani irin asirtaccen kallo suke jefa ma junansu kamar zasu haɗiye kawunansu tsabar ƙauna. Lokaci ɗaya ta samu kanta da jin kunyar shi, Muryarta adabarbarce ta furta”am..um.. Ga abincinka da nurse ta kawo nasan kana jin yunwa” ta yi maganar haɗi da nuna mashi table din, ɗaura idonshi yai akan kayan abincin kafin ya dawo da dubanshi gareta”baki jin bacci? Naga sauran ƴan uwanmu suna yin bacci, ta hakan na fahimci dare ya nutsa” Maƙe mashi kafaɗa tayi”bana jin bacci, inaso na zauna a kusa dakai, don na taimaka maka da wasu abubuwan, tun da yau ka farka ba ka san komai dangane da wurin nan ba, bana so in tafi in barka kai kaɗai a room” natsuwa yai yana kallonta, har ta ƙare maganar tukunna ya furta mata”nagode da kulawarki agareni, kuma nagode da nuna damurki akaina” still murmushin fuskarta bai washe ba “Zamu ci abincin atare? Ko kin ci naki”? Yai tambayar yana duban fuskarta, Yafi son tana kallon Cikin idonshi idan suna magana. “Bana jin yunwa, amma Zan Iya taimaka maka ka ci naka” amsa mata yai da”okey, “ miƙa hannu tayi tana buɗe plates din, lafiyayyan abinci aka haɗa mashi Grilled chicken with roasted vegetables, and black bean burger with sweet potatoes fries, hada Green tea a mug. “My Man, komi da ka gani a saman table ɗin nan duka sai ka cinye shi, yadda kasha baccin nan na tsawon kwanaki nasan cikin ka babu komai ko ruwa ma babu, yanzu faɗamin me ka ke son fara ci? Cikin kulawa take yi mashi magana. “Ki za6a min” murmushi ta sakar mashi, Mug din ta miƙa mashi, Yasa hannu biyu ya kar6a, a tsanake yake kur6anshi da zafi zafinshi, idonshi na akan face dinta, ta ƙurawa adam’s apple dinsa ido. Batasan Ya janye cup din ba sai dai taji muryarshi acikin kunnanta”me kike kallo”? Yamutsa fuska ta ɗanyi”bakomai, tun da ka gama shan tea din, zaka Sha ruwa? Ko lemu”? Girgiza mata kai yai”a’a, tea din ya ishe ni, sai dai wani abun” Kamar wani ƙaramin yaro haka take tarairayarshi, da hannu ta dinga bashi grilled chicken din yana ci, Idan ka kallesu a yadda suke zaune sai ka sha mamaki saboda girman da yai ma Angel, Bata wuci Ya lullu6eta da faffaɗan kirjinshi ba, amma saboda sabo da juna, da kuma shaƙuwa da ƙaunar dake a tsakaninsu bata ganin girman shi. Ɗaya daga cikin abunda ke burgeta, idan ta tura mashi abincin abaki yadda yake motsa tattausan full lips nasa da kuma motsin Adam’s apple dinsa, komai nashi ƙayatar da ita yake yi kamar yarda itama ta ke burge shi, a ƙarshe sai suka koma suna feeding din junansu tana bashi abaki, Shima yana bata abaki. Abunda basu sani ba, Har safiya tayi gari ya ware babu wanda Ya lura a cikinsu, tuni sun kammala cin abincin, sun shagala suna kallon juna. *ABUJA NIGERIA A GIDAN ƊAN IYA* A round ƙarfe 10 na safe agogon Nigeria, tun bayan kammala sallar Asubahi da ta koma bacci bata farkaba ba saboda Jiya sun sha fira da Aneelerh sun kusa raba dare kamar ƴa’ƴan Aljanu, shiyasa yau take ta sharar baccinta kamar matatta, ta wawware ƙafafuwanta saman mattress, ta saki baki da hanci, sai jan minshari ta ke yi kamar ragon sallah, daɗin bacci hada yawu a gefen bakinta, Gajeran wandone a jikinta sai ƴar farar half vest data zura, sumar kanta babu kitso zallar gashinta a hargitse ba gyara. Tayi zurfi acikin baccinta, Wayarta dake ajiye saman side drawer ta buga uban ringing, Babu alamun zata farka har kiran ya katse, wani ya kuma shigowa, sautin ya cika ko’ina banda kunnan zahra dake yin bacci. Shigowa cikin ɗakin Aneelerh Tayi, jikinta asanye da doguwar riga, ta yi rolling mayafi akanta, kaitsaye ta nufi drawer din ta miƙa hannu ta ɗauki wayar tana faɗin”Allah ya shirya zahra, wannan bacci haka kamar matatta, ana ta kiran mutun awaya wama ya sani ko arziƙi ne ke kiranta...” Waro ido waje aneeleeh tayi ganin sunan mutumin dake kiran Aneelerh, Ya fito 6aro 6aro saman screen din, bakowa bace face Hajiya Saratu Obinna, Jiki na rawa ta haye saman gadon takai hannu tana bubbuga ƙafar zahra”banza, ki tashi arziƙine ke kiran ki, zahra ki tashi kada muyi asara” yamutsa fuska zahra tayi muryarta kamar ta mashayin giya ta furta”dallah wanene ke takuramin, ni a ƙyaleni inyi bacci na, ba dama mutun ya ɗan kwanta ya runtsa sai an samu wani uban anacin ya tada shi’ cikin magagin bacci take yin sambatun. kiran har yayi rejecting, zuƙunnawa Aneeleeh tayi saitin kunnan ta da karfi ta furta”Shashasha Hajiya saratu obinna ce ke Kira” A haukace Zahra ta zabura Ta miƙe tana faman mutsustsuke ido, A fujajen take fadin”Wai dagaske? Ina wayar? Gaba ɗaya tabi ta ruɗe jin an ambaci sunan Hajiya saratu obinna, sai faman zazzare ido take yi. Miƙa mata wayar Aneelerh ta yi “yo har yayi rejecting, Tun ɗazu nake ta ƙoƙarin tada ki, Kinƙi ki farka gashi yanzu kin ja mana asara....” bubbuga katifa zahra tayi da hannu tsabar takaici hada hawaye akan fuskarta”Aunty aneelerh, kin karyamin jari, meyasa da kika tada ni naƙi tashi baki shiga toilet kin ciko bokiti da ruwa kin watsa mun ba”? Babu wasa akan face dinta ta yi maganar, Sakin Baki aneeleeh tayi tana kallonta Zahra ta ci gaba da yin kuka tana faɗin “Nashiga uku, wayyo Allahna, ni wlh bakiyi min adalci ba, wama ya sani ko kujerar Hajji za’a raba mana,” sosai ta fashe ma Aneelerh da kuka. Lamarin ya ɗaure mata kai, ta rasa ina zahra da mahboob suka gado shegen son kuɗi, sai dai tafi tunanin ta 6angaren mahaifinsu ne. Lallashinta ta soma yi”Kiyi hakuri sister kukan Ya isa haka, wata’kil ta ƙara Kiran ki,” cikin shessheƙar kuka tace”taya za’ae ta sake kira na, bakisan halin masu kuɗin nan ba, basu ɗaukar raini, za ta yi tsammanin dagangan naƙi ɗaga kiranta, Wayyo Allahna aunty Aneelerh, nayi wa arziki ƙulli, har ƙiyamil laili nayi akan Allah ya bude mun kofofin samu, da kuma miji nagari a sabuwar shekarar da zamu shiga...” dariyace kumshe abakin Aneelerh. Dafa kafaɗarta tayi”Sorry My lovely sis, Yanzu abunda za’ae, Ki kira Layinta mu gani ko zata ɗaga” kar6ar wayar tayi daga hannun Aneelerh, Yatsun hannunta har kerma sukeyi sam babu natsuwa, kiran layin ta soma Yi, tamkar zata fashe da kuka ta kalli Aneelerh”line busy, dama ni nasani, wlh basa ɗaga kira, idan ba su suka kira mutun ba” Aneelerh tace”mu ɗan ƙara haƙuri, zuwa anjima sai mu ƙara jaraba kiran layinta, yanzu ki tashi ki shiga toilet ki ki gyara jikin ki, zan Jiraki anan,” cikin shessheƙar kuka ta amsa da toh, kafin ta sauko daga saman gadon ta nufi toilet ta shige. Bayan shigarta da mintuna biyar Aneeleeh tana zaune tsakiyar gadon tana jiran fitowarta, zuciyarta acunkushe take da tunanin baby junaid ɗinta tayi kewarshi, tun shekaran Jiya Uncle abdallah da hajiya adama suka koma gidansu, anyi rabuwar mutunci sun nemi alfarma Junaid ya zauna wurinsu na tsawon 2 weeks, zai dawo gida, sannan duk weekend za’a dinga kai masu shi, yanzu haka yana acan gidan nasu, tsawon kwana uku da yayi acan kullum ne sai ya matsa masu akan su kira mashi Mommyn nasa, wani lokacin tun kafin ta farka daga bacci kiran su ke shigowa wayarta saboda jarabar junaid. Tayi zurfi cikin tunaninta, Wayar Zahra ta soma yin ringing, Kafin ta wurga idonta kan inda zahra ta ajiye wayar saman drawer, da ƙarfi taji sautin buɗe ƙofar toilet, Ras taji gabanta Ya fadi ganin zahra ta watso aguje, jikinta duk kumfa daga ita sai gajeran towel tayi ɗaurin gaba da shi, hatta fuskarta kumfar sabulu ce, miƙa hannu tayi ta rurumi wayar, tsabar zumuɗin ganin wanene ke kiranta, fatanta Allah yasa hajiya saratu obinna ce, cikin sa’a idonta yai mata nuni da sunanta akan screen, sai ƙoƙarin ɗaga kiran takeyi kumfar hannunta ta hana touching din yin aiki, kamar zata fashe da kuka, sai da aneelerh ta taimaka mata wurin answer mata call din tukunna ta samu natsuwa, a Hands free ta sanya kiran don suji me zata je Cikin girmamawa zahra tayi mata sallama”Assalamu alaikum” kamar tana agabanta. On the other hand sautin muryar hajiya saratu ya karaɗe kunnuwansu “Wa’alaikum salam” “Ina kwana hajiya, fatan kun tashi Lafiya, wlh bana a kusa da wayar ne, kunata kira bansamu damar ɗagawa ba, da yake na ɗan shiga toilet ne” Aneeleeh dake zaune saman gado, dariyace ta kubce mata da sauri ta cakumi pillow ta toshe fuskarta dashi don kada sautin Ya fita, bakomai ne ya sanyata yin dariya ba face yadda zahara keyin waya kamar ƴar maroƙa, ga kumfa a jikinta. “Bawani abu ai, nayi maki uziri, dalilin dayasa na kira layin ki, last time da kukayi mana decoration aikin ku ya yi mana kyau, muna so za’a ƙara Yi mana wani next week, sannan muna so za’a fidda mana anko wanda zai dace damu” Da sauri zahra ta kar6e da cewa”in sha Allah hajiya komai kuke so za’ayi yadda ya dace, hada ƙunshi da kitso idan akwai mai buƙata” Hajiya saratu tace”okey, You can send me the list of your services and I’ll add what I want to the list, through text message zaki tura min” “Toh hajiya in sha Allah, Mun gode sosai, da kiranmu da ku kayi, kuma in sha Allah zaku same mu masu biyayya ga duk abunda kuke so,” bayan sunyi sallama da Hajiya saratu, Zahra ta sauke nauyayyar Ajiyar zuciya, Ta fasa ihu Tana faɗin”Alhamdulillah! lokacin Yin arziki na Yayi, wai yau ni ce Aunty saratu ta kira awaya? nayi mamaki wlh, matar tana burgeni bata ɗaukar raini, akwai harkar arziƙi. Ta saki baki sai sambatu take yi, Kumfar Jikinta duk ta bushe har ƙasan tiles ruwan ke zuba, sautin dariyar Aneelerh ne Ya fargar da ita, da sauri ta jefa wayar saman mattress din, ta ruga da gudu ta faɗa toilet tana dariya. Daƙyar Aneeleeh ta samu ta tsagaita da yin dariyar. Ta ɗago da kanta daga jikin pillow ta jingina bayan jikin head board. “Aneelerh” muryar Mamie ce ta ratsa kunnanta, zumbur ta sauko daga saman gadon ta nufi kofar ɗakin, shigowa ɗakin Mamie Ta yi suka ci karo da ita”oh dama kina anan? Inata kiranki na duba ko’ina ban ganki ba” Aneelerh na murmushi tace”mamie kema kinsan bani da wurin zuwa a gidan nan inba ɗakin Ƴar uwata zahra ba” “Okey, ina zahran”? “Ta shiga toilet yin wanka, amma takusa fitowa Mamie tace”Okey, idan ta fito, muna jiran ku a dining, ku zo muci abinci” Ta amsa mata da toh, bayan fitar mami ɗakin, komawa ta yi gefen gadon zahra ta zauna, bada jimawa ba zahra ta fito chest dinta daure da towel, da zolaya Aneelerh tace”Lashe money an fito lafiya”? Tuntsirewa zahra tayi da dariya tana fadin”aunty aneelerh kuɗi duniyane, Dole inso kuɗi, saboda sune maganin talauci, maganin ƙasƙanci da wulaƙanci, idan kina da kuɗi kin fi ƙarfin raini wlh, girmama ki za’a dinga yi kamar wata basarakiya, taya mutum bazai so kuɗi ba? Yanzu fa ko a dangi masu kuɗi sune masu faɗa aji, idan baka da kuɗi toh baka da banbanci da Allon bango” Fashewa Aneeleeh tayi da dariya, zahra ta zaƙe sai kora mata jawabi ta ke yi dangane da kuɗi. “Zahra wasu kuɗinfa ba alkhairi bane, suna kai mutun ga shagalar duniya har ya halaka” “Aunty Aneelerh, nima ai bana roƙon Allah yabani kuɗi kaitsaye batare da nace Allah yabani masu albarka ba, kuma ni burina inyi arziƙi don al’umar annabi su amfana da ni, Ina kwaɗayin inga na taimaki marasa ƙarfi....”. “Zahra Allah ya dubi kyakkyawar niyarki, inayi maki fatan Alkhairi” “Ameen auntyna” Shaf shaf ta kammala shiryawa, cikin riga da skirt, ta dawo gefen Aneeleerh ta zauna bayan ta ɗauki wayarta “Ki tashi muje muci abinci, su mamie suna jiran mu a dining” “Inaso ne in fara turama aunty saratu list na abunda mukeyi, zaki Iya zuwa kada su ji mu shiru” miƙewa Aneelerh tayi daga gefen gadon ta fuce daga ɗakin. Through text message ta tura mata saƙon kamar haka Here’s a list of services that “Zahra’s World of Beauty” could offer: - Bridal makeup and hairstyling - Event planning and decoration - Haircuts, color, and styling - Manicures and pedicures - Facials and skin care treatments - Massage and body treatments - Waxing and other hair removal services. Bayan ta kammala rubuta sakon a ƙalla saida ta maimaita shi yayi sau ashirin gudun kada ace tayi kuskure kafin ta tura mata, fuskarta ɗauke da murmushi ta ajiye wayar saman pillow, ta miƙe ta nufi falo domin Yin breakfast, fatanta Allah yasa Hajiya saratu ta mayar mata da martanin saƙon da wuri, taci buri sosai akan zuwa estate dinsu, ko dan ta haɗu da Owais idan Allah yasa lokacin ya dawo ƙasar. *KURKUKUN ƘADDARA* *AN YANKA TA TASHI☠️👹* Babban ɗakin tarone mai girman gaske, wanda akeyiwa laƙabi da fadar matsafa, Mallakin shuwagabannin kurkukun ƙaddara, ta ko’ina manya manyan matsafane maƙil acikin fadar, zazzaune saman kujeru dake a jere tsakiyar fadar, kowannansu yana sanye cikin shiga ta baƙaƙen dogayen riguna masu huluna, sunyi 6adda kama ta yadda mutun bazai ta6a Iya ganin koda ziririn gashin kansu bane, Hannayensu da ƙafafuwansu baƙaƙen safunane, Yayin da fuskokinsu sun sanya masu mask me suffar ƙwarangwal gwanin ban tsoro, saƙo da lungu ta fadar, Wasu Gabza gabzan giants ne daga masu ƙaramin miƙami har izuwa manyansu masu star uku a gaban kakinsu, wata irin ƙira garesu mai matuƙar ruɗarwa, rikitarwa da razanarwa da kuma tsoratarwa, kallonsu kaɗai zai Iyasa zuciyar mutun ta buga, Ga tsawo da Allah yayi masu tun daga kan tsayuwarsu zaka tabbatar babu ɗigon imani akansu. Daga can saman karagar fadar, wasu jigunannun arm chairs ne guda shidda ƴan ubansu, mutane shiddan dake zaune saman kujerun dogayen rigunane launin jajaye na maza a jikinsu masu huluna, baka ta6a Iya tantance suffarsu saboda sun 6oye ko’ina na jikinsu, hannyensu na ruƙe da Sanda wadda aka ƙerata da zallar zinari, daga gabansu zungureran teburi ne, samanshi maƙil Yake da kayan ciye ciye dana shaye shaye daga ciki hada Jinin mutun da farfesun naman mutun ga zungura zunguran kwalaban giya, da Kayan marmari nau’i kala kala, da gasasshen nama na dabbobi daban daban. Komai na fadar matsafan tun daga kan ƙofofi da tagogi da fentinta da jan carpet din dake shimfiɗe ƙasanta, gaba ɗaya Launin baƙi da Ja ne, saman rufin fadar wasu haɗaɗɗun fitilune masu haskaka cikinta. Zanunnukan dake a jikin bangon fadar, na kan ƙwarangwal ne, da yatsun hannun shaiɗanu masu akaifu zaƙo zaƙo da sauran zanunnuka masu ban tsoro. Daga gefe ɗaya tacan 6angaren da Arm chairs din nan suke Tanƙameman madubine wanda suke Kira da Allon tsafi, gaba ɗaya Hankalin matsafan yana akan Allon tsafin nasu, fadar tayi tsit tamkar mutuwa ta gifta, ga dukkan alamu wani abu suke kallo wanda yai silar ɗauke masu hankulansu.......... (Nima kuma na ɗauke alƙalamina) *Boss Bature✍️ Mu haɗu Monday Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*_ ~Middle step~ _The Prisoners E21🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* A ƙalla sun shafe mintuna suna kallon Allon tsafin, ga dukkan alamu sun girgiza da ganin abun da idanuwan su ke gane masu, Hankulan su sun yi matuƙar tashi, abun ya yi mugun ɗaure masu kai, bakomai bane suke kallo acikin Allon tsafin face Garkuwar kurkuku tare da Angel, duk wani motsinsu akan idonsu tamkar video haka suke ganinsu, lokaci ɗaya Allon tsafin yayi duhu hoton fuskokin su ya 6ace. Kowan nan su ya sauke Ajiyar zuciya, sun natsu suna jiran jin bayani daga bakunan shuwagaban nin su. Ɗaya daga cikinsu ne yai gyaran murya, da wata irin kakkausar murya mai sautin gaske tamkar bata mutun ba, ya soma Yin magana Cikin harshen su na shahararrun matsafa ni kuma ina fassara maku. “Wannan ne Karo na farko da muka yi babban kuskure arayuwar mu, wanda idan bamu miƙe tsaye mun nema ma kanmu mafita ba, to tabbas za’ayi nasara akan mu, Ko a tarihi ba’a ta6a samun prisoners ɗin da suka tsira daga kurkukun ƙaddara ba, su ne na farko kuma sune na ƙarshe, da farko sunyi nasarar ƙetare kurkuku da taimakon Garkuwarmu, Na biyu sun ku6uta daga dajin evil forest da taimakon shi, Babu wani mahaluƙin da ya isa ya iya ƙetare kurkuku da dajin evil forest salin alin ba tare da ya Rasa ranshi ba, amma saboda suna atare da garkuwar prison mun rasa cin galaba akansu saboda mu kanmu bamu isa mu Iya ja da shi ba, babu wata muguwar halittar data Isa ta tunkaresu muddin Yana atare da su, rashin baccin da baiyi ba shine Yaja har muka gaza tunkarar su, lokacin da baccin Ya ɗauke shi munyi nasarar yi mashi abunda ya dawo gare mu sai dai wani abun al’ajabi ya ku6uta daga hannunmu Ya koma ma gangar jikin shi, kamar yadda kuka gani a allon tsafin mu, shin me ya jawo hakan”? Yai tambayar yayin da yake gyaran zaman shi. Mutumin dake a gefenshi, Ya ɗaura da cewa”Yarinyar da ke atare da shi itace silar komai, kamar yadda yazo mana a allon tsafin mu, Cewa itace za ta yi silar tarwatsa tarihin kurkukun ƙaddara, gangancin da mu ka yi shine Haɗa su wuri ɗaya da garkuwar mu, sakamakon shaƙuwar da sukayi a tsakanin su, taja shi ga faɗawa tarkon sonta, mu kan mu bamu ta6a tsammanin Garkuwar prison zai Iya kamuwa da matsanancin so irin haka ba” dakatawa yai da yin maganar yana motsa yatsun hannunsa, kafin ya cigaba da cewa “Sai dai har yanzu bamu rasa power ɗinmu ba, Garkuwa namu ne har abada, mu ke ruƙe da masarrafin da zamu Iya sarrafa linzamin shi, mu kaɗai ne mu ke da iko da shi, ba zamu ta6a yin danasanin Ɗaura shi amatsayin magajin kurkukun ƙaddara ba, kuskure ɗaya da muka tabka shine sakacin da mu ka yi da har ya samu nasarar guduwa daga kurkuku, Ni ban damu da sauran Yaran da suka ku6uta ba, saboda basu da amfani a wurinmu, mun ci moriyar su, mutun ukun ne sune rauninmu, Na farko Garkuwarmu dole sai da shi za’a Iya Cin galaba akanmu, Na biyu ƙaddarar kurkuku, yarinyar ta fi sauran hatsari tun da har ta Iya Jan hankalin garkuwarmu, wanda nayi imanin da ace babu ƙauna a tsakanin shi da yarinyar ba zai ta6a taimakon sauran ƴan uwan shi don su gudu daga tarkon mu,” Ya faɗa yana mai jan dogon numfashi Ya fetsar da shi, ya cigaba da faɗin “Itace silar komai, kuma itace kaɗai zata Iya sarrafa shi bayan mu, idan kuwa hakan Ya faru zai Iya fallasa mana sirrin mu ya kuma taimaka wurin ruguza kurkukun ƙaddara”! Da ƙarfi Ya ambaci hakan Yana mai nuna fusatar shi. “Yarinya ta ƙarshe itace bugun zuciyar kurkukun ƙaddara, kamar yadda ya zo mana a allon tsafin mu, idan har muka samu nasarar Cire Zuciyarta daga ƙirjinta zamu samu ƙarfin Iko fiye da wanda muke da shi a yanzu, Ita kuma ƙaddarar kurkuku dole mu dawo da ita cikin mu idan har muna son ta zamar mana ƙaddara mai kyau, barin ta awaje shi zaisa ta zamto mummunar ƙaddara agare mu” Tamkar mayunwacin zaki haka yake kora masu jawabi yana fitar da huci. Bayan ya rufe baki Na gefen shi ya soma magana da wata irin murya ta dattawa waɗanda suka Shahara a fagen zalunci. “Tun fil azal, Banso Muka damƙa amanar mu ga tsohuwa tamira ba, dama tun lokacin Sai da na musa akan hakan, Ni dama nasani Jinin Habibullah ba zasu ta6a zama amintattun mu ba, sai gashi sun yaudaremu sunci amanar kurkuku, sun kashe mana Zafreen ɗaya daga cikin shuwagabannin mu, babu wanda ya ta6a tsammanin zasu Ci amanar mu ita da ɗanta Salsabeel, sai da suka bari mun basu yarda mu su kuma suka butulce mana, haƙiƙa Nayi takaicin rasa gangar jikin tamira, da ba abun da zai hana mu azabtar da ita, mu sa6ule naman jikinta sannan muyi farfesun shi muba ma Karnuka su shanye roman, amma duk da haka bamu makaro ba, Zamu huce haushin mu akan ɗanta Salsabeel” mutumin da yayi maganar babu ɗigon imani akansa. Bayan ya dasa aya a maganar shi, wani daga cikin shuwagabannin Ya numfasa tare da cewa”Garkuwa ya yi mana mummunar 6arnar da ba zamu Iya gyarata ba, bamu ta6a tsammanin zai Iya yi mana haka ba, sai dai ba zamu Iya hukunta shi ba, saboda shi jinin mu ne, abu ɗaya da zamu Iya yi mashi shine mu hana shi jin daɗin rayuwarshi da Yarinyar, mu shiga tsakaninsu, horon da zamu bashi kenan, sannan zamu ci gaba da sarrafa shi wurin azabtar da mutane, kafin muyi nasarar dawo da su Cikin mu, hikmar yin hakan mutane zasu fara tsoranshi suna nuna mashi ƙyamata, zai ji duk duniya kamar ba’a sonshi ne, kunga anan zai yi tunanin mu kaɗaine gatanshi, kurkukune kaɗai inda zai zauna yayi rayuwarshi ba tare da ƙuntata ba, daga lokacin daya fara wannan tunanin mu kuma zamu samu damar kwashesu su ukun mu dawo da su cikin mu”! Ya kai ƙarshen maganar tare da buga hannun arm chair ɗin da yake a zaune, gaba ɗaya matsafan suka fashe da dariya mai sautin gaske tamkar ana bubbuga ganga, jikinsu har jijjiga ya ke yi saboda tsabar yadda suke yin dariyar kamar dokuna. “Mun Fi ƙarfin mutun, Ko mutuwa tsoron tunkararmu take Yi, shiyasa muka daɗe muna sheƙe ayarmu, shan jinin mutune da cin tsokar naman su yanzu muka fara, Rainon Yara ba zamu fasa ba, zamu cigaba da tarasu a cikin kurkukun ƙaddara muna biyan buƙatarmu dasu domin samun ƙarfin ikonmu” Ihu suka dinga Yi sunayin shewa sautin muryoyinsu tamkar zasu fasa bangon Fadar, kusan atare matsafan suke miƙe tsaye suna taka rawarsu ta matsafa, kowan nan su, ya ɗauki abunda yake ra’ayin ci asaman table wasu giya, wasu farfesun naman mutun wasu jini wasu kuma naman dabbobi suke ci, Yayin da wasun su a tsaye suke saduwa da junansu kamar dabbobi wa’iya zubillah. *DAULAR OBIE ESTATE* *Dr. jazz❤* Ƙudundune yake acikin bargo, saman katafaren gadonshi na gidan Sir mubarak, cikin muryar raɗa yake yin magana a wayar shi. “I’m not working today, I’m at home. yanzu haka da ni ke yi maka magana Ina akwance saman gadona” shiru ya ɗanyi yana sauraron mutumin da suke yin wayarshi, can yaci gaba da cewa”Boss Man kasan bana wasa da aikin ka, idan ka bani umarni jiki na rawa nike yin shi, ko jiya na shiga gidan gonar na duba lafiyar kajin, sai dai muce Alhamdulillah, Jikin su yayi kyau baka ga yadda suke tafiya ba tsokar jikinsu har girgiza take yi saboda ƙoshin lafiyar dake gare su” ya ƙare maganar muryarshi da sautin dariya “My Boss Man, Amma dani da kai zamu ɗubi na azumi ko? Ko zamu bari sai sallah Ayi layya da su”? Tuntsirewa yayi da dariya jin amsar da mutumin ya bashi muryarshi cikin harshen turanci yake yi mashi magana. “Amma ai kasan nayi ƙoƙari, tun da na fara kiwon kajin nan wlh ko ɗaya ban ta6a gigin kamawa don in yanka ba, kuma miyau na ya biya fa” da shagwa6a ya ƙare maganar. Abun da bai sani ba, tun da ya fara yin wayar, Sir mubarak Ya shigo ɗakin jikinshi sanye da kakin sojoji, Hannunsa biyu ruƙe da faffaɗan plate, daga saman shi an jera Chocolate raspberry cupcakes. Ya shigo ɗakin ne da niyar ya faranta mashi, tun lokacin da turai ta faɗa mashi game da gorin da Hajiya saratu ke yi mashi akan cewa shi ba mahaifin shi bane sai yaji ya ƙara ƙaunar yaron yana matuƙar sonshi. Lamarin Ya ɗaure mashi kai, ba tun yau ba, Ya jima yana mamakin wayar da dr jazz ke yi akan Kajin gidan gona, cikin tafiyar sanɗa Sir mubarak Ya ƙarasa shiga ɗakin ya zauna gefen gadon shi hannun shi ruƙe da plate din, Ya kasa kunne Yana sauraron tattaunawar jazz da Boss man din shi. Jin shiru Jazz bai ƙara yin magana ba yai tunanin ko ya kammala yin wayar ne, Gyaran murya ya yi mashi. Jazz da ke ƙudundune cikin bargo yai lamo jikinshi ya kama yin kerma jin muryar Sir mubarak Hankalin shi ba ƙaramin tashi yai ba. “Jazz nasan idonka Biyu Ka tashi inason magana dakai” A hankali Ya zame bargon, Ƴar singlet ce ajikinshi tare da Gajeran wando, sumar kanshi duk ta hargitse. Yana faman mutsustsuke ido da hannu ya saci kallon Sir mubarak Muryarshi da kasala Ya furta “Daddy ina kwana, ka tashi lafiya, ya mommy’ adabarbarce ya ambaci hakan sam bai lura da plate din hannunsa ba. Babu alamun zai amsa mashi gaisuwar tashi, wani irin kallon tuhuma Yake jefa mashi, Ƴan kame kame jazz ya kama Yi, don Ya fahimci dadyn nasa yaji komai da ya ke faɗi a wayarshi. “Jazz, da wa ka ke yin magana a waya? muryar shi a kausashe Ya jefa mashi tambayar. Cikin rawar murya Jazz yace”daddy abokina ne dr fawan ai na faɗa maka tare da shi muka buɗe gidan kaji muna yin kiwon su’ yaƙi yarda su haɗa ido da uncle mubarak. Gyaɗa kai yai”Jazz zan ƙara jan kunnanka akan Ka kiyaye mutanan da za ka yi mu’amala dasu! Bana son kayi abunda zaka Yi danasani, Ni bana zargin ka da wani abu, Ina yi maka kyakkyawan zato My son, Nasihar da zanyi maka shine Kaji tsoron Allah komi za ka yi a duniyar nan kada ka manta Allah Yana ganin ka, kuma zaka koma gare shi ne, jin daɗin duniyar nan ƙalilan nan komai da muka samu anan zamu barshi, a kowani yanayi na rayuwa mutawa zata Iya riskar mutun, me yakamata muyi? Mu kasance muna aikata aikin Alkhairi akoda yaushe, sannan duk runtsi duk wuya kada ka ta6a karya zuciyar wanda ya aminta dakai.....” cikin kwantar da murya Sir mubarak Yake yi mashi nasiha, jikinshi duk yai sanyi, idanuwanshi sun cicciko tab da ƙwalla Ya ɗago Yana kallon fuskar Sir mubarak, Har Ila yau yana mamakin Halin Sir mubarak da Obinna suna da mutunci da daraja ɗan adam, duk da kasancewar shi ɗan mai aikin gidansu sun maida shi tamkar jinin su, tun kafin Ya mallaki hankalinshi suke yin ɗawainiya dashi, cin shi shan shi suturarshi da karatun shi sune suka ɗauki nauyin komai na rayuwarshi. Yayi zurfi acikin tunanin shi muryar sir mubarak ta katse shi”Ina magana ka tsareni da ido” da sauri Ya sunnar da kanshi ƙasa, Ƙwallar da suka taru cikin idonshi tuni sun soma gangarowa saman kuncinsa. “Jazz Why are you crying”? Ya faɗa yana duban face dinsa. cikin shessheƙar kuka ya soma magana”nagode sosai daddyna, ina matuƙar alfahari dakai, saboda ƙaunar da kuke nuna mun kai da baba, ban ta6a danasanin kasancewata acikin family dinku ba, Ina jin daɗin nasihar da ka ke yi min daddy, ka maidani tamkar ɗanka komai na rayuwa kana Yi min...” murmushin gefe fuska sir mubarak yaɗan saki. “My son ya isa Haka, share hawayenka, Ni dai fatana Ka ruƙe mutuncinka Jazz, Kada ka bani Kunya, inaso ka zama abunda duniya zata yi alfahari dakai” Jinjina kai yai tare da ɗago da kai Ya ɗaura rinannun idanuwanshi akan fuskar Sir Mubarak “In sha Allah, Nayi maka alƙawarin hakan, Zan kama mutuncina kuma bazan ta6a baka kunya ba” Miƙa mashi plate din hannun shi yayi “Your mother made this for you. I know how much you love cupcakes.” fuskarshi ɗauke da ƙayataccen murmushi Yake dubanshi, Hannun Dr Jazz Har kerma Yake yi wurin kar6ar Plate din “Kayi brush kuwa? Naga kamar yanzu ka farka daga bacci,” Girgiza kai yai”ban kaiga Yi ba, Yanzu zan shiga toilet din’ “Okey, Ka ajiye plate din idan ka fito sai kaci” ƙaƙaro murmushi yai akan face dinsa”Okay, Dad, I appreciate your care.” Miƙewa sir mubarak Yai”Ni zan wuce Office, ka kula mun da kanka” “Daddy Allah Ya dawo min dakai Lafiya, Allah ya tsare mun ya kare mun kai daddyna” Yaji daɗin maganar Jazz, har saida ya dan juyo ya kalle shi kafin Ya fuce daga ɗakin” Nauyayyar Ajiyar zuciya Jazz ya sauke, kalaman Sir mubarak sun tsaya mashi aranshi, Cikin sanyin murya ya furta”Am sorry My daddy, Na riga dana jefa kaina Cikin Tarkon da bazan Iya fidda kaina ba, addu’arka kawai nake buƙata Allah Ya bani ikon cinye jarabawar nan”!! Ya ƙare maganar tare da saukowa daga saman gadon ya ɗaura plate din hannun shi saman Table Ya nufi toilet Ya shige. *Hajjaty the head maids💋* A tsanake Take Yin tafiya tana nufar haɗaɗɗen garden din gidan, ta ɗauki wankan Sari Launin Ja, Hannunta biyu ruƙe da Tray na Kayan Marmari tare da mugs biyu na black tea, ta ko’ina ƙamshin turare ne ke fita a jikinta, tasha uban ado na sarƙar wuya da awarwaro, make up din fuskarta Ya ƙara mata Kyau. Tun kafin ta ƙarasa shiga garden din idanuwanta suka hango mata, Obinna tare da babban amininsa daya kawo mashi ziyara, kallo ɗaya zaka yi mashi ka gane Inyamuri ne, fari ne fat sumar kanshi da jagirarshi dukkansu hurhurace, hatta dogon Gemunshi fari ne fat kalar na Obinna, sunyi shigar Manyan Kaya na hausawa, zaman hular kanshi zai ƙara tabbatar maka da ƙabilar shi, suna a zaune saman shimdiɗar da Hajjaty tayi masu ta alfarma, kowan nan su ya tada kanshi saman tuntun kalar na sarakuna. Tun kafin ta ƙaraso gabansu, ƙamshin turarenta Ya daki hancinan su, abokin obinna Ya furta”masha Allah” Ya kafe ta da ido yana faman Jan gemunshi. Zuƙunnawa tayi agabansu Ta sauke tray din, cikin girmamawa ta gaishe da abokin”sannu da zuwa, ina wuni Ya iyali” lumshe idonshi yai tare da ware su kan fuskarta, Obinna dake kallonshi ya fahimci kamar baya a hayyacinsa, hajjaty ta tafi da imaninsa, har Ya gaza buɗe baki Ya amsa mata gaisuwarta, Sai faman bin jikinta yake yi da kallon ƙurulla duk tabi ta tsargu. “Ba ka ji tana gaishe ka ba ne”? Sai da obinna Ya ambaci hakan tukunna Ya iya motsa la66ansa wurin furta”Lafiyalou madam, fatan na same ku lafiya”? Muryarta na rawa ta furta lafiya lou “Obie, dama matarnan tana agidan nan har yanzu? Yayi tambayar ne saboda lokacin da tazo yi masu shimfiɗa bai kaiga zuwa gidan ba. Harara obinna ya ɗan watsa mashi a fakaice, kafin ya bashi amsar tambayar shi sai da ya fara kallon hajjaty yace”tashi ki tafi, mun gode” miƙewa ta yi tare da juya ta nufi hanyar fita garden din tsabar sauri kamar zatayi tuntube. Bayan tafiyarta obinna ya dubi aminin nasa”shegen bisa, faɗamin waya koya maka kallon mata? Ni dai ya iya sanina dakai mace bata agabanka, sai gashi yau kana neman zauce wa saboda kaga Mace” da zolaya ya yi mashi maganar. Tuntsirewa Inyamurin yai da dariya yana faɗin”Don kawai na gani na yaba, matar ce ba ƙaramin burgeni take yi ba, inason mace mai tsafta da iya ado, sannan kasan Ni ma’aboci son ƙamshine, gaskiya ta tafi da imanina, ka taimaka min inaso na mallake ta, dagaske nake ba wasa ba” Da mamaki akan fuskar obinna ya ɗan zaro idona yana kallon shi, yayi mamakin jin abun da ya furta, kuma ga dukkan alamu dagaske yake har cikin ranshi. “Amma dai zolaya ce wannan ko”? Jan gemun shi yai tare da cewa”na ta6a yi maka zolaya akan irin wannan maganar”? Girgiza kai Obie yai” Bamu ta6a ba, sai dai nayi mamakin kalamanka, tun da muka taso baka ta6a nuna kana buƙatar mace ba, ka haramtawa kanka tara Iyali, gaba daya rayuwarka akan kasuwancinka ta ƙare” Fuskar Inyamurin da fara’a ya yace”wannan karan dagaske nake, Inasonta da aure mutumina, ka yi min hanyar da zan samu shiga wurinta, don bana son abun ya ɗau lokaci” farin cikine tsantsa akan fuskar obinna abunda yajima yana yi mashi fata “In sha Allah, zanyi maka ƙoƙarin yin hakan, nima nayi maka sha’awar auranta, Matar tana da hankali da natsuwa” Cigaba da tattaunawa sukayi a tsakaninsu. A 6angaren Hajjaty kuwa, Jikinta duk yai sanyi tun da ta baro garden din gabanta ke faɗuwa, tsigar jikinta na tashi, duk akan kallon da abokin obinna yayi mata. Gaba ɗaya hankalin ta baya atare da ita, tafiya ta ke yi Zuciyarta nayi mata saƙe saƙe, har ta ƙaraso entry hall tana ƙoƙarin bi ta ƙofar palourn Cikin rashin sani suka bangaji juna ita da Hajiya saratu da ke ƙoƙarin fitowa daga falon, Ta kimtsa cikin shiga ta alfarma, da alama wurin aiki zataje. Da sauri Hajjaty ta ɗago su ka yi tozali da Hajiya saratu, Rass taji gabanta Ya faɗi, Muryarta na kerma ta furta”kiyi haƙuri ban lura dake ba...” daƙyar ta ƙare maganar ganin irin ƙasƙantaccen kallon da Hajiya saratu ke watsa mata. Tana huci ta furta”baki da hankaline? Ko makauniya ce ke? Wato tsabar nuna isa har kin kai matsayin da zaki iya haɗa kafaɗa ni ko”! Fuskarta a ɗaure tamau tayi maganar. Hankalin Hajjaty ba ƙaramin tashi yai ba, sam bata lura da pravin dake abayan Hajiya saratu ba, Ya shirya cikin black suit, hannunshi ruƙe da wayarshi daya kara a kunnanshi, Waya yake yi amma hankinsa na akan Hajjaty da hajiya saratu “Bada sanina na bangaje ki ba, hankalina baya atare dani” Harara Hajiya Saratu ta watsa mata tamkar ƙwayar idonta zata faɗo ƙasa”Ƴar rainin wayau, wai bana hanaki shafa mahaukacin turaren nan a jikinki ba? Ke baki da hankaline? an gaya maki Zawarci haukane” Rai a6ace ta faɗi hakan tare da ruƙo Mayafin Sarin Hajjaty da hannunta. Idanuwanta tuni sun ciko tab da ƙwalla. “Wlh daga rana irin ta yau idan na kuskura na ƙara jin ƙamshin turaren ƴan borin nan naki saina sauke maki kwandon rashin mutunci akanki,” Azafafe ta ƙare maganar, tare da ingiza hajjaty tayi taga taga zata faɗi, Pravin harya Yunƙura zai tarbeta, da sauri Ya fasa ganin matsiyacin kallon da Hajiya saratu ta watsa mashi “Wuce muje” cike da isa ta ba shi umarni, da sauri Yabi bayanta suka nufi parking space. Da ido hajjaty tabi su da kallo, hawaye tuni sun wanke fuskarta, jikinta na rawa ta nufi cikin gidan, masu aikine ke ta kai komo acikin babban palourn. Ba tare data bari sunyi tozali da wani ba, tayi saurin nufar bedroom dinta, harta kusa shiga taci karo da twins sunyi shirin zuwa office. Atare suka ɗago suna kallonta, muryarta na rawa ta furta”ina kwananku kun tashi lafiya” Harara Zayn ya watsa mata”ji wata tambayar rainin wayau nan, taya zaki tambayi mun tashi lafiya? Bayan gamu kin gan mu a tsaye kan ƙafafunmu” Zaid yace”Zayn, please watch your tongue Hajjaty tamkar uwa take agare mu,” a harzuƙe yace”what! ƴar aikin ce zata zama uwar mu? oh Ko dan saboda tana ƴar india? To ai mu ba indiyawa bane ubanmu ne ɗan can, Nifa baki burgeni saboda ban yadda dake ba, ina zargin hada ke ake cin amanar mahaifiyar mu” Afirgice Hajjaty ta zazzare ido tana duban fuskar zayn da yayi mata, tuni zufa ta soma tsastsafo mata. “Pls zayn ya isa haka, idan ba zaka girmamata ba, bai kamata kana gaya mata magana akan idonta ba” yai maganar tare da jan hannun Zayn suka nufi hanyar fita palourn. Ba zata Iya jure wulaƙancinsu ba, da sauri ta nufi bedroom dinta, tana shiga ta faɗa saman gado ta fashe da matsanancin kuka tamkar ranta zai fita. Hajiya saratu tuni ta shige cikin mota, pravin na atsaye ya ruƙe murfin motar”Lafiya? Ba zaka shigo bane”? Tayi maganar tana dubanshi ganin yaƙi motsawa Ya kafe ta da ido. “Bana so na 6ata maki lokaci, Ki tafi kawai Ni zanje a motata” da mamaki akan fuskarta tace”saboda me”? “Cikina ne Ya 6aci ina buƙatar shiga toilet, “ yai maganar yana shafa flat stomach dinsa Ta6e baki tai sam bata kawo komai aranta ba tace”Okey, saina dawo” duƙowa ya yi saitin fuskarta ya manna mata peck a fore head dinta”Ki kulamin da kanki My wife, zanyi missing dinki, Ni kona minti ɗaya banaso kiyi nesa dani” kwa6e fuska tayi “kalaman ka ba zasu hanani tafiya office ba, sai dai su 6ata min lokacina, pls ka kula min da kanka,” murmushin yaƙe ya sakar mata, Aranshi bai ji daɗin maganarta ba, halinta ne bata Iya kalaman soyayyaba kuma ba ta cika son yana yi mata ba. “please take care of ur self, ayi aiki lafiya”ya ƙare maganar tare da tura murfin motar ya rufe mata ita. Security din dake zaune a driver seat na motar yaja ta suka nufi shantalelen titin da zai fiddasu daga estate din. Shu’umin murmushine Ya bayyana akan fuskar Pravin, Jiki na rawa Ya juya ya nufi entry hall, adai dai lokacin twins sun fito hannunsu ruƙe cikin na juna suka ci karo da shi. Gaba daya suka tsareshi da ido suna kallon shi Fuskarshi da fara’a ya furta”Kyawawan samarina har Kun kammala Shiryawa za’a tafi office,” zaid ne yai ƙoƙarin faɗin”daddy, ina kwana ka tashi Lafiya” Ya amsa mashi da lafiyalou My son, kafin ya maida dubanshi ga Zayn da ya haɗe rai. “Lafiya zayn ka tsare ni da ido? Ko ba ka da lafiya ne”? Basarwa yai”lafiyata qalou daddy, just nayi missing dinka ne, amma ya akai daddy naga ka dawo gida? Ba aiki zakaje ba”? “Key ɗin mota ɗina na bari a ɗaki, shi zanje na ɗauko” zayn yace”bari na ɗauko maka key din” yai maganar yana ƙoƙarin juyawa a hanzarce pravin ya damƙi hannunsa”bana so ku makara yakamata ku wuce ku tafi office, zanje na ɗauko da kaina, Ku kulamin da kanku,’ bai jira amsar su ba, yabi ta gefensu ya nufi cikin falon. “Zaid sai da na faɗa maka matarcan baƙar munafuka ce, saboda ita daddy yayi mana ƙaryar zai je ya ɗauko car key a ɗaki” Yana huci yayi maganar Zaid yace”please bro, ka yi mashi kyakkyawan zato, bai kamata kana zarginsu ba” Tsoki Zayn yaja”wlh duk ranar dana gano ainihin abunda suke aiwatarwa saina tona masu asiri awurin mommy, ita kuma matar can saina koreta daga gidanmu ta koma can ƙauyansu na Indiya,” ya ƙare maganar tare da jan hannun zaid suka nufi motarsu. Hajjaty na akwance cikin mawuyacin hali, idanuwanta sunyi luhu luhu sun rune zuwa Ja, sai faman shessheƙar kuka take yi, Har ya shigo ɗakin bata sani ba, Haye wa yai saman gadon ya zauna daga gefenta, Cikin sanyin murya Ya furta”My heart beat” har cikin kunnanta ta ji muryarshi, sai dai takasa ɗagowa ta kalle shi, hakan Ya tabbatar mashi da ranta Ya 6aci. “kiyi hakuri, banji daɗin kalaman da saratu ta furta maki ba, ba yadda zanyi ne shiyasa ban dakatar da ita ba, nasan ranki ya 6aci but pls ki daure,” Cikin shessheƙar Kuka tace”bazan iya jurewa ba, nagaji nagaji nagaji da irin wulaƙacin da suke Yi mini, sun tsaneni basu ƙaunar ganina, ita da zayn shima yaci mutuncina, zaid ne kaɗai ke ƙaunata” Dafe kanshi yai da hannu ɗaya, Kafin Yace”pls Ki ɗago muyi magana” “Ai bana son kallonka, raina ƙara 6aci yake yi” lumshe idonshi yai haɗi da ware su saman Bayanta. “Ban ji zafin kalamanki ba, saboda laifina ne, Ni ne silar komai, “ sai da yai wannan furucin ta ɗago da kanta, tana fuskantar ceilling, taƙi Yarda su haɗa ido. Ba zato ba tsammani taji Ya kwanto da kanshi saitin fuskarta, ƙamshin turarensu ya addabi hancinansu. “Ki faɗamin me kikeso nayi maki wanda zai kwantar maki da hankalinki” Harara ta watsa mashi muryarta da shagwa6e ta furta”pls ka tashi ka tafi office, ka zauna kana 6ata lokaci akaina” “Saboda kin cancanta ne, lokacina nakine, har aikin sai in fasa zuwa idan kinaso” Yai maganar Yana kashe mata ido. Batasan ya akai ta tsinci kanta da sakar mashi murmushi. “Inaso na faranta maki, don haka ki shirya dama kin faɗamin kinason haihuwa” zare mashi ido tayi’acikin gidan nan? Salon aganni da ciki a tuhumeni” da zolaya yace”sai kice na Obinna ne, kinga shikenan kin kashe bakin magana’ fashewa sukayi da dariya cike da nishadi. “Idan hakan ta faru ko kowa zai ƙyaleni, Hajiya saratu saita kasheni” jan kumtunta yai da hannunshi”Ai ko dana kasheta nima,” lumshe ido tayi”pravin ka tashi ka tafi office aiki na jiranka. ‘Waya faɗa maki Ina yin aiki ni? Nifa salary kaɗai nake kwasa, bana yin Aikin komai ko naje office din, P.a dina ke taimaka min,” ya ƙare maganar tare da ɗaura tafin hannunsa ɗaya saman chest dinta, a hankali yaci gaba da yin squeezing dinsu, numfashintane ya soma canzawa ta soma cizon la66anta. “Faɗamin Ina kika je”? Cikin yanayi najin shauƙi ta amsa mashi da cewa”Garden naje kaima Obinna da amininsa Kayan marmari” ganin ya ɗaure fuskarshi yasa tace”lafiya’ “Mutumin bai kwantamin araina ba! Bana son kina zuwa wurin obinna idan abokanansa suka zo, dattawan nan shegen son mata garesu, musamman irinki babu namijin da zai ganki ya kawar da idon shi” Ta6e la66anta tayi yayin da suke kallon juna “Are you jealous of me?Meyasa shi obinna baka kishi da shi sai abokanan...” kasa ƙarasa maganar ta yi jin ya mannata da ƙirjinshi”saboda shi na yarda dashi, bazai ta6a nuna kwaɗayi akanki ba, dattijon yana da kamun kai, kuma baida burin ƙara aure tun da matanshi suka rasu, shi ko amininsa Jan kunne tsaf zai Iya cewa yana sonki” “Idan hakan Ya faru mai za ka yi mashi” tayi maganar tana shafa Wuyanshi da yatsun hannunta. Kashe mata ido ɗaya yai kafin Ya bata amsa da cewa “Gemun shi zan tsige” dariya suka saki, da sauri Ya haɗe bakinshi da nata, Hannayenshi Biyu tallabe da kanta tamkar zasu cinye harsunan junasu. *San Antonio Texas* *Army headquarter* Babbar headquater ce mallakin sojojin san antonio, Haɗaɗɗen gini mai girma da faɗi, launin fentin head quater din army green ne, Tun daga bakin entry way na shiga headquater din zaka fara cin karo da Giant soldiars Cikin ta da wajenta maƙil Yake da Gwarazan sojoji sadaukan Gaske masu ƙirar zakuna, kowan nan su Ya kimtsa cikin shiga ta Kakinsu, ƙafafuwansu sanye da army boots, sun ruƙe Jibga jibgan bindigu a hannuwansu, haka zaika ƙugunansu a soke suke da pistols, babu wasa akan fuskarsu cikin taku na majiya ƙarfi suke kewage ko’ina na Gate din shiga headquater din. Danƙareriyar motace Haɗaɗɗiyar gaske mai numfashi ƴar ubansu ƙirar Mercedes-benz S-class launin black ta sharoro da matsakaicin gudu kaitsaye ta nufi Bakin Hq din, tunkafin ta ƙaraso sojojin suka ƙura ido suna jiran ganin wani isasshen ne wannan ɗan kasada mai shirin zuwa lahira yake yi masu tuƙin ganganci a saman titin su. Sai da mai motar yakusa zuwa gabansu, Ya rage gudun motar, tamkar na cikin motar baisan da sojojin dake tsaron headquater dinba, Ya soma ƙoƙarin kutsawa zai ƙetare gate din, aiko kamar mayunwatan zakuna suka tunkari motar, Wasu fusatattu daga cikinsu tuni sun saita motar da bindigar hannusu, da kakkausar murya suke faɗin “Hey! Stop the car! Otherwise we’ll attack you”! Gaba ɗaya sun kewaye motar, Da ƙarfi wani baturen Soja Ya daki gaban motar da tafin hannunsa tamkar zai 6alle ta, A harzuƙe ya furta “Ka sauke glass ɗin motar, Idan ba haka ba zaka fuskanci horo mai tsanani daga gare mu” duk wannan suratan da sukeyi na cikin motar yaƙi fitowa babu alamun zai buɗe murfinta, Hakan ba ƙaramin hayaƙa su yayi ba” “You’re running out of time. I want you to come out of the car now! If you don’t, I won’t hesitate to shoot! This isn’t a game, I’m serious. you have five seconds!” baturen sojan da ya dafe motar da tafin hannunsa ne Ya furta hakan, Sai da suka gama harzuƙa Zuciyarsu a maƙogaro, a lokacin da basuyi tsammani ba, mamallakin motar Ya tura murfin Ya buɗe, Rai 6ace suka ƙura ido suna jiran ganin wani isasshen ne wannan uban Ji da kan. *Boss Bature✍️ Mu haɗu Gobe In sha Allah Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _~*BossLadiesWriters*~_ _*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*_ ~Middle step~ _The Prisoners E22🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* _UMMIN AMERICA🔥🔥🔥_ A hankali ta zuro ƙafarta ɗaya daga cikin motar wow, high hills ne launin army green sanye a ƙafarta, sunyi bala’en yi mata kyau, Launin fatar ƙafarta ka ɗai abun kallo ce, kai kace hasken rana bai ta6a shafarta ba, tsabar kyan fatar da salƙinta. Tun kafin ta ƙarasa fitowa sojojin suka sassauta fushin fuskarsu, Jikin kowan nan su yai la’asar ƙamshin shu’umin turaren jikinta ya daki hancinansu har cikin maƙoshin su fragrance din ya ratsa, Tabarakallahu ahsanul khaliƙin, gaba ɗaya ta tafi da imanin su, basu san sa’adda Bindugun hannunsu suka faɗi ƙasa ba, Ta yi matuƙar tafiya da hankalinsu, wani irin mayataccen kallo suke bin surar jikinta da shi kamar zasu kai mata hari. Black american ce, A zubin halitta tana da tsayi da jiki, Launin fatarta Chocolate colour ne, Bodycon ce a jikinta, long sleeved gown dai dai gwiwa rigar ta tsaya mata launin Army green, daga ganin ta kaga ƴar duniya hayaƙin taba, baƙar a shana ƙona gari, Irin Ruƙaƙƙun karuwan nan ne Waɗanda suka amsa sunansu A harkar Bariki,Wannan da kuke gani bakowa bace face UMMIN AMERICA, hamshaƙiyar macace mai zaman kanta, Idanuwanta A tsaitsaye suke, Bata da mutunci, kuma bata da kunya ko misƙala zarratin,Tun daga kan shigarta zaka shaida fitsararta, Gaba ɗaya rigar ta bayyana tsiraicinta, boobs ɗinta sun cika faffaɗan kirjinta, tamkar zasu fasa rigar su fito waje don atakure suke an matsesu. Flat tommy ɗinta tamkar ba’a saka abincin acikinsa tsabar ɗamewarsa, ga Uban qugu dake gareta tamkar ɗaura mata shi akayi saboda faɗinsa, ko kofi aka ɗaura a tudun mazaunanta tsaf zai zauna batare da ya faɗo ba. Wani irin daddaɗan ƙamshine ke fita saƙo da lungu na Jikinta. Round face gare ta,Tasha Uban make up, tamkar an zanata don kyau, Ga eye lashes da akayi mata fixing masu tsayi, dogon hancinta Na manne da Nose ring mai kyan gaske, Haka yatsun hannunta na dama na sanye da knuckle ring, long nails din yatsun hannunta fixing dinsu akayi. Sumar kanta tasha gyara, sai dai daga gani hair wing ne ta daura ba asalin sumar kanta ba, amma zai wuya mutun Ya iya ganewa. Hankalin maza fa ya tashi haiƙam, gaba daya sun rasa natsuwar su, sai faman haɗiyar yawu suke yi kamar zash lashe ta. Muryarta tamkar ana busa sarewa ta furta”Zan Iya shiga Ciki”? Har suna haɗa baki wurin bata amsa da cewa”You’re welcome” shu’umin murmushi ta sakar masu, har dimple din gefen fuskarta Ya lotsa, juyawar da za ta yi, mazaunanta suka girgiza gaba daya sojoji suka zabura tamkar zasu tallabe mata shi. Komawa Cikin motar tayi, kafin ta rufe motar, wani daga cikin sojojin yai saurin datse mata murfin, A tsanake taci gaba da yin driving ta nufi cikin head quarter din. Ta tafi tabar su da jarabar kallon surar jikinta da su ka yi, ba zasu iya jurewa ba ai ko da sauri suka nufi cikin head quarter din donsu samu damar ƙare mata kallo ko sun rage raɗaɗin da zuciyarsu ke yi masu. Bayan tayi parking ɗin motar, ta fito hannunta ruƙe da i phone dinta, Hankulan sojojin dake Zarya a headquarter din gaba ɗaya ya dawo kanta, kamar sun samu talabijin, Matarce akwai Iya jan hankalin maza da surar jikinta, duk idan Tayi taku ɗaya jikinta sai ya girgiza hakan ba ƙaramin hayaƙa maza yake yi ba. All eyes on her, Sojojin Tamkar zasu kai mata hari, sai dai ba damar Yin hakan,Wani irin ƙwarjini gareta, A fuska bata da wasa, Zazzafa ce, Me zaman Kanta. Ta wutsiyar ido take kallon masu ɗago mata hannu da masu yi mata alamar suna son yin magana da ita. Ko kallo basu ishe ta ba, jefi jefi takan ɗan wurga eye balls dinta akansu, da gangan take kashe masu ido ɗaya ko ta ciji lower lip dinta da harshe, ɗabi’arta ce Yin hakan, duk don ta ƙara hayaƙa su. Kaitsaye ta nufi hanyar da zata sada ta da office din commender domin amsa kiran da yayi mata, tasan ko’ina na headquarter din, don ba baƙuwarta bace, Ba yau bane rana tafarko da ta fara shigarta. Tun kafin ƙarasowar ta, tuni Anyi mata iso wurinshi, jiranta kawai Yake yi, yana daga zaune saman chair, acikin katafaren office dinsa, komai na cikinsa army green ne, hatta desk din gabanshi, dake dauke da computer dinsa, da wayar hannunsa tare da flag and map, daga jikin bangon office din akwai book shelf, da jerin hotunansa da awards dinsa, bashi kaɗai bane a office din hada Major. Shigowarta office din, Tuni sanyin Iskar A.c ɗin cikinsa ta gauraya da ƙamshin shu’umin turarenta. Har saida suka shaƙe shi sosai a hancinansu. Da kwarkwarsa ta ƙarasa gaban desk dinsa, kamar yadda ta saba yi mashi duk in tazo office dinsa haka yau ma tayi mashi, Ta buga ƙafa tare da sara mashi, hakan ba ƙaramin ƙayatar da shi yai ba, har sai da suka saki murmushi, tun kafin Ya bata iznin zama, ta zauna saman chair din dake facing dinsa, ta ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya, murmushi ta sakar mashi haɗi da ɗaga mashi gira ɗaya ta kashe mashi ido. A wayance ta soma yin magana cikin harshen turanci”fatan na same ku lafiya” lumshe ido commender yai tare da kai hannu ya gyara zaman wuyan rigar kakinsa. “Lafiyalou ummi, I’m glad to see u, Ina fata kiran da mukayi maki bai taƙura maki ba”? Ɗaga mashi gira tayi alamar eh ba tare da ta furta ba, a mutunce suka gaisa da junansu. Bayan kowan nan su ya natsu, Major Ya miƙe ya bi ta ƙofa ya fuce waje jim kaɗan ya dawo hannayen shi ruƙe da mugs na coffee guda biyu ya ɗaura su saman desk, ya ɗago da ido Ya kalli Ummi”zaki Iya sha” ta furta okey, kafin takai hannu ta dauki mug din ta soma kur6an coffee din, da alama ya yi mata dadi kusan sau uku tasha kafin ta ajiye mug din, ta dawo da dubanta ga commender”am all eyes” “Dalilin da yasa na kira ki ummi, Magana ce mai muhimmanci muke san yi da ke, Ina fata za ki bamu haɗin kai kamar yadda kika saba taimakon mu” cikin harshen turanci commender yayi maganar a tsanake. Hankalin major na akan ƙirjinta har wani ƙara leƙensu yake yi kamar zai zura kanshi cikin rigarta. Kallon da Commender ya watsa mashine yasa shi saurin kawar da idonshi ya kame mutuncin kansa “Babu takura, ko da yaushe ina maraba da ku, zaka Iya faɗin komai ka ke so kai tsaye” ta ƙare maganar tana shafa saman boobs dinta da yatsun hannunta. Yawu commender Ya haɗiya Kutt throat dinsa Ya bada sauti, shi kanshi daurewa yake yi, surar ummin America na neman kwance mashi masarrafinsa. “Ina so ki natsu ki fahimce ni kafin ki bani amsa” amsa mashi tayi da toh Bayani ya soma yi mata dalla dalla tun daga farkon tsintarsu Angel da su ka yi a Daji, har izuwa kawosu asibiti, da kuma abun da su ke buƙata daga gare ta, tunda commender ya fara labarta mata, ta natsu tana sauraronshi. “Muna so ki bamu haɗin kai wurin Kula da yaran ki ruƙe su tamkar ƴa’ƴanki, munsan zaki Iyane shiyasa muka za6e ki, tun da ba yau kika fara yi mana aiki ba, mun yarda dake ummi, burinmu ki tarairayesu ta yadda yaran zasu yarda dake har su Iya faɗamaki ainihin abun da ya faru arayuwarsu’ ya ƙarasa maganar idonshi akan fuskarta. Lumshe ido ta ɗanyi kafin ta waresu akan fuskarshi “ta ya ya zaku yi tunanin damƙa amanar yara har goma sha ɗaya a hannuna? Bayan kunsan wacece ni, Ban ta6a haihuwa ba, kuma ni banason Rainon ƴa’ƴa, ban ta6a sha’awar haihuwarsu ba, balle har in iya kula da yaran wasu, Ina mai baka haƙurin Cewa Ni bazan Iya wannan aikin ba! zaifi ku samu macen da tasan zafin haihuwa mai kamun kai ku bata rainon su” tana magana jikinta na jijjiga, major duk yabi ya susuce ya rasa natsuwarshi, ba dan commender na akusa ba da ba abun da zai hana ya damƙeta ko da zai sha mari ne. “Ummi, Ki sassauta kalamanki, Kina yi min magana da tsiwa, Ko kin manta a ina kike ne? Ki duba da kyau ki gani, nan ba club ba ne, ba kuma gidan karuwai bane, sannan ba ga6ar taku bane, Head quarter din sojoji ce” Ya yi maganar tare da zaro bindiga daga cikin drawer chest na desk din gabanshi Ya daurata saman desk din. Tuntsirewa Tayi da dariyar rainin wayau “Kai ma ka sani, Ummin america bata tsoron bingida, ni da ni ke yin mu’amala da masu ruƙeta, yanzu haka da nake yi maka magana shigowa ta head quarter din nan gaba ɗaya na tada masu jarabarsu, suna can waje, wandunan su sunyi masu nauyi’ cike da shaƙiyanci tayi maganar, ta riga ta gama raina su bata jin tsoron su ko kaɗan. Cikin kwantar da murya commender yace”is ok, kibar yi min wasa, Muyi magana ta hankali, ki taimaka ki kar6i buƙatarmu, kome kikeso zamuyi maki, sannan ɗawainiyar yaran da komai nasu mune zamu bada tallafin da za’a cigaba da kula da rayuwarsu, tun daga cinsu shansu, suturarsu, da karatunsu, Iya taimakon da muke so kiyi mana kija su a jiki ki zama tamkar mahafiyarsu” yamutsa fuska tayi tana faman wurwurga eye balls dinta tace”Kana nufin wai a gidana zasu zauna? Ka san gidana gidan mazane, a koda wani lokaci Ina busy wurin biya masu buƙatarsu, how ka ke tunanin zasu Iya samun kulawar data dace? Kuma naji kace yaran suna fama da depression hada me ciwon ciwo, gaskiga ba ƙaramar ɗawainiya bace kula da su, bazan Iya ba commender, kada ka tursasamin, kasan ina girmamaka saboda halaccinka agareni” Kallon major commender yayi, hakan ya bashi damar Yi mata magana “Ba zamu takura maki ba, amma kafin ki tafi Inaso zan nuna maki hotunan Yaran Ki gansu” Miƙewa Major yai daga saman kujerar da yake a zaune Ya zagaya ta 6angaren Commender Ya juyo mata da laptop din saitin fuskarta. Operating ɗinta Ya soma Yi, hotunansu Angel Ya buɗo, daga kan hotonta Ya fara Nuna ma Ummin america “Sunanta Angel” Ya ambaci hakan yana kallonta, da alamun mamaki akan fuskarta ta furta “wow she’s beautiful sai dai daga ganin bakinta za ta yi tsiwa, ni kuma bana sha’awar Yara masu masifa” ta faɗa haɗi da yamutsa fuska, still murmushi ne akan fuskar major da commender. Hoton Batul ya nuna mata, sai da ta ta6e la66anta kafin tace “tana da kyau, sai dai daga ganin fuskarta bata da masifa, wannan ko yatsa aka sanya mata abaki bazata Iya cizon shi ba” ta kare maganar tana hura hanci. Hoto na gaba fuskar Hanna ce, Ummin america tace”har ƙwara Yarinyar daka wuce akan wannan, taci ka sanyi daga gani babu kuzari a jikinta” yadda take fayyace ɗabi’unsu kamar ta ta6a ganinsu. Ko da akazo kan Hoton Parveen Ya cika screen din laptop din. Da buɗar bakin Ummi sai cewa tayi”yarinyar nan daga ganin kumatuntu mayyar abinci ce, zai yi wuya idan ba asame ta da shegen ci ba, Ni bana so mutun mai ciye ciye” murmushin fuskar Major da commender sai ƙara faɗada yake yi, don ba ƙaramin nishaɗi take basu ba. Hoton Jamimah Ya nuno mata, waro ido waje tayi hada sanya Hannu ta dafe saman ƙirjinta. “Major, ruƙon wannan Yarinyar ai sai likitan mahauka, shi kaɗai ne zai Iya sarrafa ta, ba dai ni ba, Ni ina zan Iya kula da ita, daga ganin bakinta zatayi tsiwa” Major yayi dariya tare da nuno hoton Azeeza, shiru tayi tana ƙare mata kallo, kafin ta ɗago da ido ta kalli Major”sai naga kamar ƴan biyu ne ita da Yarinyar da ka nuna min kafin ita, sunyi kama” Major yace”haka muke tsammani, sai dai muna hasashen azeeza tafi Jemimah shekaru kamar yadda ɗan uwansu ya faɗa mana” Yamutsa fuska Ummin america tayi”tana da kyau sai dai daga ganinta matsoraciya ce, wannan ko tsawa na daka mata zata Iya sakin fitsari a wando, gani da tsiwa bansan ya zamu ƙare da ita ba” ta fada tana ta6a baki tace”wai Iya matane Yaran”? Ta yi tambayar tana kallon Fuskar Major “akwai maza” ya bata amsa, a dai dai kan hoton Haris Ya buɗe mata shi. “Sunan shi Haris, shine yaron da commender Ya faɗa maki cewa Yana fama da ciwon zuciya” Ta6e baki tayi”nifa banason namiji mai raunin zuciya, daga gani baya da hayaniya ba laifi yana da kyan fata” ta faɗi hakanne saboda kasancewarta baƙar fata, tana son mutun me duhun fata. Wuce hoton Haris yai adai dai kan hoton Javed ya dakata Yana dubanta “Amma dai wannan Yaron ɗan south korea ne ko? Major yace”bamu da tabbacin ɗan Ina ne, duka yaran bamu san wani jinsi bane, sai dai sun faɗa mana cewa Ƴan Nigeria ne” da sauri ummin america ta girga kai tana fadin”Impossible, babu kalan waɗannan a nigeria, may be sun yi loosing memory ɗin su ne shiyasa su ka faɗi hakan” Hoton Naufal Ya budo mata, lumshe ido ta ɗanyi tare da waresu akan kyakkyawan fuskarshi “Wow, kaga Namiji, sumar kanshi ta burge ni, Yayi min kyau” ta yi maganar tana hura mashi kiss. “Yaro ne” Commender ne yace haka, Ummi tace”Ai shi namiji baya kaɗan, especially idan abunsa ya ruƙa, a wurina wannan ba yaro bane Namiji ne” murmushi suka saki, basu damu da abun da tace ba saboda sun san halinta, bata mu’amala da matasan samari, Sai mazan da su ke da aure waɗanda tasan idan ta bibiyesu za’ayi bala’i idan matansu suka kamata. Bayan Ya wuce hoton Naufal Ya buɗe mata hoton Gabriel, tunda ta kafe shi da ido bata ƙyaftaba sai faman jinjina kanta take Yi alamar mamaki Can dai ta numfasa tare da cewa”Allah Ya yayi halitta, gaskiya idan aka bani rainon yaran nan tamkar kun ba kura ajiyar nama ne, major idan akwai wani hoton nuna mini na ƙosa na ƙarasa ganinsu” Lokacin da Major Ya hasko mata hoton Danish daga zaune ta zabura ta miƙe tsaye tana duban fuskarsa data cika screen na laptop din, duk suna akwance akayi masu hotunan idanuwansu arufe. Muryarta tamkar tame Yin raɗa ta furta “Speechless! Major Ina kuka samun Kyakkyawar matashin nan mai kama da ɗan sarkin aljanu? Anya Cikakken mutunne? Ko dai A cikin Dajin da kuka tsintosu Aljana ta haife shi Ta yada” dariya kowan nan su ya saki jin sambatun ummi dama sai da ransu ya basu zata ruɗe idan taga hoton shi. Major yace”sai ma kin ganshi a zahiri, ba ƙaramin kyaune da shi ba” Ko da ta koma ta zauna, sam takasa ɗauke idonta daga kan fuskar Danish, Yayi matuƙar tafiya da imaninta, aranta har ta fara Ayyana koya surar shi zata kasance a zarihi? Muryar Commender ce ta fargar da ita ga dubanshi”dukansu ne muka nuna maki, shin kin canza ra’ayinka akan kula da su ko kuwa har yanzu kina akan bakanki” Shiru ta ɗanyi tana yanke shawara da zuciyarta, duk sun ƙagara da son jin amsarta. “Yanzu haka case din Yaran mun miƙa shi hannun shugaban isod, shine zai cigaba da jan ragamar bincike akansu, jiya muka samu amincewarshi na kar6ar case din nasu, sai dai ya nuna baya buƙatar 6ata lokaci yanason ya tafi tare da yaran can nigeria a jet dinsa, a satin da zamu shiga” Lokaci ɗaya ummin america ta canza fuskarta zuwa 6acin rai, da farko tayi murnar jin cewa Case din Yana a hannun chief na Isod, daga bisani daya furta komawa Nigeria ne taji komai ya fita aranta. “Naji kin yi shiru, baki ce komai ba” Ajiyar zuciya ta sauke kafin ta soma magana ranta a6ace”Idan har kuna so in ruƙe Yaran a hannuna, they should stay in America. I will not follow them to Nigeria,” Commender yace”amma meyasa? Ke kanki fa ƴar ƙasar Nigeria ce why baki son zuwa ƙasar Ki” Girgiza kai Tayi still fuskarta da 6acin rai ta furta”Ni ba ƴar nigeria ba ce, asalina ne acan, amma Ni black american ce, tun da nace banaso mubar maganar kawai, Ni zan koma gidan idan ka gama maganar ka” Yanayin fuskarta Ya canza sosai, 6acin raine tsantsa, sun fahimci kamar akwai wani abu daya ta6a faruwa da ita wanda har yajawo silar barinta ƙasar, kuma batason Anayi mata maganar komawa can” Ganin yadda ta haɗe rai babu annuri ko miskala zarratin akan fuskarta, Yasa Commender cewa”Shikenan ki kwantar da hankalin ki, ba zamu takura maki ba, Zaki Iya tafiya” ba don yaso ba ya ambaci hakan, duk basu ji daɗin canzawarta ba, muryarta a disashe ta furta”thank u” ta yunƙura ta miƙe ta nufi ƙofar fita daga office din, Har ta kusa ficewa Muryar Commender ta katse mata hanzarinta”duk da bansan abunda ya faru dake a ƙasarki ba da har yasa kika tsani jin an ambaci sunanta, da akwai wani abu da nike so in faɗa maki ummi” yayi maganar tare da miƙewa hannun shi ruƙe da mug na coffee, Ya kur6a kafin ya ɗaure da cewa”wannan dama ce agare ki, da zaki koma ƙasarki a karo na farko ki nuna ma waɗanda sukayi silar barinki ƙasar cewa Kina araye kuma kinsamu cigaba a rayuwarki ba kamar yadda sukayi tsammani ba, inaso ki basu mamaki ummi, sannan zuwanki Nigeri bana dundun bane na ɗan lokacine zaki dawo nan da zarar Mun samu nasara akan binciken Yaran, zamu dawo dake nan, saboda mu kanmu ba zamu so mu rasa nagartacciyar mace irinki ba, ke kanki kin sani muna ƙaunarki kuma muna daraja ƙimarki a idanuwan mu, ba zamu so abunda zai 6ata maki rai ba ummi, kina da damar da zaki Iya zuwa gida ki zauna ki yi tunani akan maganata kafin ki yanke shawara. Kalaman shi sun ɗan ta6ata, tuni zuciyarta ta fara sassautowa, ita kanta zataso wannan damar ta zuwa Nigeria ko dan taba waɗanda sukayi silar barinta mamaki. Numfasawa ta ɗanyi kafin a hankali ta juya tana kallon commender dake tsaye abayanta, kamar bata son furta maganar tace”babu buƙatar yanke shawara, Na amince Zan bi su zuwa Nigeria, Kuma nagode da karramawarku agareni, da zarar na gama aikin, zan dawo ƙasata” Murmushi major da commender suka saki, Jin abunda tace, har yanzu bata yadda ta kira Nigeria da sunan ƙasarta ba. Sun ji daɗin amincewarta, ba tare da 6ata lokaci ba, Commender ya dauko mata kundun dake ɗauke da bayanansu Angel, duka takardun akwai Signature dinsu a jiki, saura sanya hannunta suke buƙata, cikin ƙanƙanin lokaci su ka Ƙulla Yarjejeniya ta (guardianship agreement)atsakanin su da ita, sai da ta natsu ta karanta sharuɗɗansu dalla dalla akan irin rainon da suke so tayima yaran kafin ta sanya hannu a takardun, bayan ta kammala sun bata wasu takaddun yarjejeniyar da zata ruƙe a hannunta. Bayan tayi masu sallama, Ta fito daga office din, tana tafiya Sojoji Na binta da kallo, Yayin da ita kuma hankalinta na akan takaddun dake a hannunta, Fatanta Allah yasa Ruƙon Yaran da za ta yi da kuma zuwan ta Nigeria Ya zama alkhairi agare ta. Tun kafin ta ƙarasa gaban motarta da ta bari a harabar ajiye motocinsu, ta hango sojoji dadda6e sun kewaye motar suna jiranta, murmushin gefe fuska tasaki har dimple dinta Ya lotsa, ta fahimci tunda ta shiga office din commender suke ta jiran fitowarta don su yi mata magana, bata tsaya sauraron su ba, daƙyar ta samu suka ƙyaleta ta shiga mota, a tsanake ta tada motar, Ta juya sitiyarin da gudu ta fuce daga head quarter din. *EX-PRISONERS❤* Tun ɗazu da safe kowan nan su Ya farka daga bacci, sun wayi gari da jin kyakkyawan labarin farkawar Danish, saboda zumuɗin zuwa ganin shi babu wanda ya nemi breakfast acikinsu, gaba ɗaya sun Hallara a room dinsa, tun daga kan Haris, Javed, Naufal, Gabriel, Batul, Hannah, Jamimah, Azeeza, ƙwansu da kwarkwatarsu sun yi tsaitsaye cirko cirkon suna kallon shi, fuskokinsu ɗauke da Annurin farin Ciki, Ɗaya bayan ɗaya Danish Yabisu ya rungume su a ƙirjinshi, kamar sunyi shekara basu atare da juna, Haris hada kukanshi saboda murnar ganin Danish Ya farka. Sun tasa shi gaba suna kallonshi kamar zasu lashe shi, Musamman Azeeza da Jemimah, daɗi suke Ji Danish ɗinsu Ya farka. Muryar jamimah da shagwa6a tace”munyi fushi ma sai yau zaka farka, kullum sai munyi kukan rashin ka, ko bacci bamu Iya yi abincin ma ba mu ci” Harara Azeeza ta watsa mata”wlh ƙarya take yi Danish kullum sai taci abinci sau uku, kuma tana Yin bacci” Murmushi ya saki yana binsu da kallo, Haris dake zaune gefen gadon Danish ya ruƙe hannunshi a Cikin nashi ji yake kamar za a kwace mashi ɗan uwanshi. “Meyasa Angel Jiya daya farka baki tada mu daga bacci ba? Bayan kinsan irin ƙagarar da muka Yi na son ganin shi” Hanna ce tayi maganar, Gabriel Yace”Ni dai ba abunda zance sai godiya, saboda ba zamu Iya misalta farin Cikin da muke aciki ba, Yau babbar rana ce agaremu ɗan uwanmu abun alfarinmu Ya farka da ranshi da lafiyarshi” yana daga tsaye yake yin maganar Ya goye hannayenshi saman ƙirjinshi. “Allah sarki Rayuwa kenan, Har na tuna kokawar da Ku ka yi kaida Danish akan nace zan dire taga” gaba ɗayansu suka sanya dariya. Batul tace”ai mu bamusan abunda ya haɗa su faɗa ba” Parveen dake tsaye gefen Naufal hannunta ruƙe da Ayaba sai ci take Yi, Kunnuwanta akansu ta natsu tana sauraransu. Labari Angel ta basu na abunda ya faru lokacin da zata dire taga, ba ƙaramin nishaɗi su ka yi ba. Azeeza tace”munyi kuka lokacin sosai, Munyi tsammanin Danish ɗinmu zai rasa idonshi ɗaya, sai gashi Allah ya dawo mana dashi da ranshi da Lafiyarshi, gaskiya munji daɗi” da farin ciki akan fuskarta ta ƙare maganar, idanuwan Danish akan faces dinsu, ita da Jemamah. Parveen tace”ni banaso muna tuna baya, nafi so inji muna magana akan abunda zai faru agaba” Jemimah tace”Genie yaushe zamuje gidan daddyn naki? Ni na ƙosa mu koma can, waɗannan mutanan masu jan kumatun, kullum sai sun tsira mana allura a ɗuwawun mu” ta yi maganar tare da nuna ass dinta da indext finger dinta, gaba ɗaya suka tuntsire da dariya, Azeeza tace”Kai jamimah ki ji tsoron Allah, Jiya fa ba ayi mana allura ba, nurse ta faɗamin an gama yi mana ita, sai dai magani da zamu dinga sha na tsawon one month” turo mata baki Jemimah tayi Javed yace”Kufa baku gajiya da abun magana, Kun Cika ɗan uwanmu da surutu, Ko so kuke yi ya koma baccin” atare suka zaro ido haɗi da ɗan buɗe baki”A’a wlh bamu so Ya koma bacci,” “Alhamdulillah, Tun da yanzu mun haɗu mu dukanmu, Yakamata Muyi wa Allah godiya” Angel Ce tayi maganar, Tare da Ɗaga tafin hannayenta sama, Da sauri suma suka ɗaga nasu zasu yi addu’a, Mutun ɗaya ne bai ɗaga nashi hannun ba, Hatta Gabriel da ya ke Christian sai da ya ɗaga hannunshi don su yi addu’ar atare, Don shi a yanzu baida za6in addini, yafi ƙarfi ta 6angaren musulunci saboda Angel. Kallon fuskarshi Angel tayi”danish zamuyi addu’a, ba zaka ɗaga hannu ba” Girgiza mata kai Yayi alamar a’a, ɗaure mashi fuska tayi sai yayi tamkar baisan tana Yi ba Cikin sanyin murya Haris yace”Danish meyasa har yanzu baka goyan bayan addinin musulunci”? Shiru danish bai yi magana ba, Kuma babu alamun zaiyi ta. Damuwace ƙarar akan fuskokinsu “Pls danish just for today ka ɗaga hannu Muyi addu’a” Muyar Angel tamkar zata fashe mashi da kuka Tayi maganar. Marairaice mashi fuska Azeeza da jemimah sukayi”Bro pls, let pray together,” Runtse idanuwanshi Yai, ba tare daya buɗe su ba Ya furta”I can’t, ku daina yi mini magana akan Inyi, bana so” Sai lokacin Batul ta sanya baki”tun da ya nuna bayaso mu ƙyaleshi, damu da shi duk abu ɗayane, ko da ace baiyi ba mu zamu yi mashi, hakan ma ya wadatar” Angel bata ji daɗi ƙin Yin addu’a da yai ba, addu’oi’ ta soma karanto masu suna amsa mata da ameen ameen, idanuwanta sun cicciko tab da ƙwalla, bayan sun Kammala kowan nan su Ya shafa saman fuskarshi, banda Angel maimakon ta shafa addu’ar da tayi saman fuskarta, sai ta shafa ma danish saman sumar kanshi, a hankali ya ɗago da idanuwanshi yana duban fuskarta, harara ta watsa mashi tare da murguɗa mashi baki, hakan da tayi ba ƙaramin ƙayatar da shi yai ba, muryarshi ƙasa ƙasa ya furta mata”thank u” ta6e mashi baki tayi”kada ka yi tunanin na damu dakai,” ƙayataccen murmushin gefen fuska yasakar mata, Su Batul sun natsu suna kallonsu. Muryar Dr. laura ce ta katse masu hanzarinsu”Congratulation! My lovely Children Ina tayaku murnar farkawar ɗan uwan ku daga bacci, banjima da shigowa asibitin ba, dr Harry ke faɗamin cewa ɗan uwanku Danish Ya farka, wannan abun farin Ciki ne” ta ƙarasa maganar, a yayin da take ƙarasowa Gaban gadon Danish. Fararen idanuwanta dake asanye cikin farin glass ta ɗaura su kan face dinshi. “An sanar dani cewa Baya kula kowa sai ƴan uwanshi, dagaske ne masoyiya Angel? Tayi tambayar tare da kallon Angel Da fara’a akan fuskar Angel ta amsa mata da cewa “Jiya ne amma yau ya saki jiki, zai Iya magana da kowa” Dr laura tace”Anya kuwa? Naga ko kallona baisan Yi, danish Ya jikin naka? Ko akwai inda ke yi maka ciwo a jikin ka”? Tayi tambayar cikin ƙagara da son jin muryarshi Cikin raɗa Angel ta furta mashi”danish pls kayi mata magana, sun taimake mu, kuma suna da mutunci” kamar wanda akayi ma dole daƙyar ya iya motsa lips dinsa ya furta”da sauƙi babu inda keyi mini ciwo,” Dr Laura taji daɗin maganarshi”ina fata kaci abinci babu yunwa atare dakai”? Ɗaga mata kai yai alamar eh Ta furta”okey, amma meyasa jiya baka ba likitoci damar duba lafiyarka ba”? A takure yake yi mata magana”saboda lafiyata ƙalau, bana buƙatar a duba ni,” Jinjina kai ta ɗanyi tayi mamakin Halinshi, basu ta6a samun patient irin shi ba. Muryar Angel ce ta janyo hankalinta ga dubanta”Aunty, mun gode sosai da kulawarku agaremu, Allah ne kaɗai zai Iya biyanku,” tayi mata maganar ne don ta mantar da ita zancen yi ma Danish maganar duba Lafiyar Jikinshi. “kada ki damu masoyiya Angel, aikin mun e kula da lafiyarku kuma Alhamdulillah, Naga Jiki yayi kyau Allah ya ƙara Lafiya,” ta ƙare maganar tare da kallon Azeeza da jemimah”My twins, Ya jikin naku” atare suka haɗa baki” da sauƙi” kafin ta ɗaura idonta kan Parveen da sauri ta 6oye Ayabar dake a hannunta, dariya dr laura ta ɗan saki”hmm ai na gani dama kin daina wahalar 6oye mini” duƙar da kai Parveen tayi fuskarta ɗauke da murmushi. Kallonsu Gabriel Tayi”Ƴan samari, Jiki yayi kyau, badan sister dinku ta matsa akan son komawarku Nigeria ba, da a gidana zan killace ku, In cigaba da rainonku,” murmushi kowan nan su ya saki. “Zan Koma Office, Ku kula mun da kanku” har ta juya zata fuce Angel tayi saurin cewa”Aunty, har yanzu sojojin basu kira ba naji su shiru basu zo sun duba mu ba” Dr. Laura na niyar juyowa don ta bata amsa, ba zato ba tsammani, Suka hango Dr. Mark tare da dr. brown sun nufo ƙofar ɗakin, Kusan a tare suka shigo. Gaisawa suka Yi da dr laura, Cikin girmamawa su Angel suka gaishe da su, Bayan sun amsa masu, suka tayasu murnar farkawar ɗan uwansu Kafin daga bisani Dr Mark Ya soma Yin magana”Dr. Ke muke nema, Sojojin nan sun Kira Awaya, idan ba damuwa zamu Iya zuwa office muyi magana” Amsa mashi tayi da toh, ba tare da 6ata lokaci ba suka fuce daga ɗakin. Hankalin Angel yaƙi kwanciya burinta taji me zasu tattauna, fatanta Allah yasa su amince da maganar maidasu Nigeria. Bayan fitarsu ɗakin kaitsaye office din dr Laura suka nufa, kowan nan su ya samu wuri saman kujera Ya zauna suna fuskantar Juna da ita “Ina sauraronku, me sojojin suke ce ne”? A ƙagare ta tambayesu Dr mark Ne ya soma kora mata jawabi”Commender dinsu ne Ya kirani awaya, Ya sanar dani cewa Chief na Isod Ya Amince zai kar6i case din Yaran....” tunkan Ya ƙarasa maganar, dr laura tasaki murmushin farin ciki “Bayan haka, sun ƙulla Yarjejeniya tsakanin ita ummin american da su sojojin, zuwa Anjima zasu zo asibitin domin shirya yaran, zasu ɗauke su zuwa gidanta, sai dai zamuyi kewarsu saboda Commender din ya faɗamin next week chief na isod zai bar ƙasar tare da yaran” ya ƙarasa maganar idonshi Akan dr laura, mood din fuskarta ya canza zuwa damuwa, ba ta yi tsammanin zasu bar ƙasar da wuri ba, zaman da su ka yi da su na kwana huɗu ba ƙaramin sabo su ka yi da juna ba, sai dai ta wani 6angaren taji daɗi kodan saboda Angel da ta roƙe ta akan ta taimaka masu su koma ƙasarsu. “Dr lafiya? Naga kamar yanayin fuskarki Ya canza? Ko baki ji daɗin maganar bane”? dr. Mark ne yayi maganar ganin ta haɗe fuska, Murmushin yaƙe tasakar mashi “No ba haka bane, Na saba da yaran ne, banaso su yi nesa dani, banyi tsammanin zasu bar ƙasar da wuri ba, inaso zan nemi alfarma abar mana su ko da one month ne su yi anan kafin su tafi” Dr brown yace”ba zai yiwu ba dr, da ace case dinsu a hannun sojojin yake zamu Iya neman alfarmar abar mana yaran su zauna a wurinmu, sai dai kash sun riga da sun damƙa case din hannun chief na isod, kuma kinsan shi ba ɗan ƙasar nan bane, A ƙasar shi yake zaune Aiki ne mai muhimmanci ya kawoshi america, tun cikin weekend daya wuce yaso barin ƙasar, saboda case din Yaran Ya fasa tafiya, yanzu haka da nakeyi maki magana, yana shirye shiryen barin Washinton zai shigo garin mu saboda ya haɗa kan yaran ya tafi dasu, mutumin babu wasa a aikinsa, Baison 6ata lokaci. Jikin dr. laura ba ƙaramin sanyi yai ba, tana son su Angel, ganin duk ta damune yasa Dr mark kwantar mata hankali”Tafiyarsu ba yana nufin mun rabu da su ba, Kada Ki manta Sojojin ƙasarmu ne suka tsince su, bayanan su da komai Yana a hannunsu, kuma zasu cigaba da bibiyar rayuwar yaran, wannan dalilinne ma yasa suka haɗasu da Ummin america. Gyaɗa kai Dr Laura Tayi”Ni damuwata depression din dake damun yaran, da kuma Yaron dake fama da ciwon zuciya, Hankalina bai kwanta da Ummin america ba, Shin zata Iya bamu su kulawar da zata sanya su manta da damuwarsu? nafa santa bata da mutunci macace mai izza kuma ta shahara wurin Iya karuwanci.....” Damuwace ƙarara kan fuskar dr laura, idanuwanta tuni sun ciko tab da kwalla. “Yaran sunfi buƙatar kulawar mace wadda tasan ciwon haihuwa, bawai karuwa ba! Wadda ta saba ƙwacewa matan aure mazajensu tana fasiƙanci da su! Yakamata Kuyi tunani akan hakan, Ni zanyima Commender din nasu magana, akan su canza masu wadda zata raine su, Yara fa har goma sha ɗaya za’a damka ma karuwa, gaskiya basuyi tunani mai kyau ba, zata Iya 6ata su” ranta amuƙar 6ace take Yin maganar. Cikin kwantar da murya Dr mark yace”ina baki shawara dr, kada kice zaki shiga maganar nan! Tun ranar da major ya kawo shawarar abata kulawar yaran, Kin nuna kuskuren yin hakan, amma sai basu damu ba, saboda sunsan halinta, kuma sunsan zata Iya ne, kamar yadda yace ta saba yi masu aiki, so bai kamata ki damu ba” Dr brown ya ɗaura da cewa”sunfi mu sanin wacece Ita, Mu sanin da mukayi mata na karuwa ne, su kuma a matsayin ma’aikaciyarsu suke kallonta, ba zasu ta6a damƙa mata amanar yaran ba tare da sun aminta da ita ba” Gyaɗa kai Dr Laura Tayi”Shikenan na haƙura, bazan yi masu magana ba, amma inaso zan ba Masoyiya Angel Kyautar waya, saboda inaso mudinga Yin magana da ita akai kai” “Na fahimci kina son yaran sosai, Ni kaina na kamu da ƙaunarsu, Har na fara jin kewarsu” acewar dr. Mark Dr brown yace”aini har ƙasarsu zan Iya zuwa ganinsu idan naso, don haka banda damuwa, muna atare da su” Sun jima suna tattaunawa a tsakaninsu kafin daga bisani, Kowa ya koma bakin aikinsa. *DAULAR ALHAJI MUSA* *Dr Shureim❤* Ƴan kwanakin da yayi a gidan Uncle ɗin nasa Rayuwarshi ta fara canzawa, a yanzu dr. Shureim baida matsalar komai, ta kowani 6angare yana samun kyakkyawar kulawa, kullum yana acikin gida, idan ya gaji da zaman ɗaki yakan fito ya zagaye gidan tare da zeenatu, yana matuƙar jin daɗin kulawar da take bashi, sun shaƙu da juna kamar sunyi shekara atare, hatta abincin atare suke cin shi, sai dai akwai wani abu da ya fara damun zeenatu, hoton da yake yawan kallo awayar shi, abun yabi mashi jiki kamar ibada, Idan ya fara kallon hoton baya so kowa yazo kusa da shi, kuma baya son kowa yasan hoton menene yake kallo, duk idan ta faɗo ɗakin shi yana cikin kallon hoton da sauri yake danna power button na wayar ya kashe ta, ta rasa gane wacece yake yawon kallo? Don ta fahimci ba ƙaramin so yake yi mata ba, gashi ita kuma Allah ya jarabceta da masifaffan kishi, ba ta son ganin yana kallon hoton, Har kuka take yi a 6oye ba tare sanin kowa ba. A Kishingiɗe yake saman katafaren gadonshi, tun safe bai fita ko’ina ba, ko ƙofar bedroom dinsa bai leƙa ba, farin short ne ajikinsa, babu riga, gaba ɗaya hankalinsa na akan screen din apple laptop dinsa dake ajiye saitin kanshi daya ɗaura saman pillow, Sam bai ji takun tafiyarta ba, saboda hankalinshi baya atare da shi, wankan swiss lace ne a jikinta, launin ash colour riga da skirt sunbi shape din jikinta, kamar a jikinta aka ɗinka kayan, duk da bata ƙiba kayan sunyi bala’en Yi mata Kyau, Tani da Lami ne sukayi mata Make up, hatta ɗaurin ɗan kwalin kanta sune suka ɗaura mata shi, ziririyar sarƙar wuyanta ta diamond ce, stone din jikinta sai ƙyalli Yake Yi, ta yafa gyale a saman kafadarta, hannunta ruƙe da handbag, fragrance din turaren jikinta mai daɗin shaƙa ahanci. Hankalinta ba akwance yake ba, tun kafin ta shigo ɗakin tayi mashi sallama bai amsa bata ba, har ta gaji da yin sallamar shiyasa ta yanke shawarar shigowa don ta ga ko bacci yake yi ne Tun kafin ta ƙaraso gaban gadonshi blue eye balls dinta suka sauka akan screen din Laptop nasa Ras taji gabanta yai mugun faɗuwa, zuciyarta tamkar zata faso ƙirjinta saboda zafin da take yi mata, zeenatu tana da saukin kai sai dai tana da zuciya idan ta hasala, ranta ya 6aci sosai ganin abunda yake kallo, hoton da ta tsana a duniyar nan duk da batasan hoton menene yake kallo ba, ranta ya bata cewar budurwarsa ce yake kallo. Idanuwanta sun makance, bakomai suke hango mata ba face dr shureim ɗinta rungume da mace a kirjinsa. Runtse ido tayi da karfi ta fasa wata irin gigitacciyar ƙara wadda tayi silar firgitar da shi, da sauri Ya miƙe tare da wurga idonshi Kanta, tuni ta saki jakar hannunta ƙasa, Zafafan hawayene suka wanke fuskarta. Hankalinshi ba ƙaramin tashi yai ba, a hanzarce ya sauko daga saman gadon ya nufeta fuskarshi da alamun ruɗu ya furta”zeenatu! Lafiya? Meya faru? Girgiza mashi kai tadinga yi tana faɗin”kada ka matso kusa dani yaya shureim, inna lillahi wa’inna ilaihirraji’un” gaba ɗaya ta gama rikitar dashi”zeenatu ki natsu kiyi min bayani meya faru dake? Ko wani abu ne ya tsoratar da ke? Cikin shessheƙar kuka tace”yaya shureim bazan Iya jurewaba, zuciyata zata Iya bugawa, tun ɗazu mukayi magana dakai akan zamu fita yawo atare, kace min inje in shirya kafin in dawo kaima za ka shiga wanka ka kimtsa, ashe baka yi komai ba, ko wankan ma bakayi ba, ka zauna kana kallon hotonta saboda tafi ni mahimmanci awurinka, ba tun yau ba kullum ne saina ganka kana kallonta, wai wacece wannan ne? Dame tafi ni? Numfashinta na fita da hucin zafi ta ƙarasa maganar, tare da juyawa da gudu ta fuce daga ɗakin nashi. Hankalin shi ba ƙaramin tashi yai ba, idonshi akan bayanta harta 6ace ma ganin shi. Dafe kanshi yai da hannu ɗaya, har cikin ranshi baiji daɗin kalamanta ba, baiso yai silar 6ata mata rai ba, duk da bai fahimci inda maganganunta su ka dosa ba, lumshe idanuwanshi ya ɗanyi kafin ya ware su a hankali, yayin da zuciyarshi ke tariyo mashi furucin da tayi mashi, yasan bai kyauta mata ba, ta ƙwalla fa rai akan son su fita tun Jiya shi da kanshi yai mata alƙawarin yau zai ɗauke ta a sabuwar motarshi su fita yawo. Cikin sanyin murya ya furta”am sorry my zeenat, “ da sauri Ya nufi toilet don yai wanka. *Boss Bature✍️ Mu haɗu Gobe In sha Allah Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*_ ~Middle step~ سجن القدر❤🤍❤ _THE PRISONERS E23🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* Confusion of the heart💫 Sir mubarak ne zaune Cikin Motarshi, da su ka yi parking dinta a harabar ajiye motoci na asibitin Obinna,Tanƙameman asibiti ne Ya haɗu tamkar ba wurin Jinyar marasa lafiya ba, An zuba dukiya wurin gininsa, suna da ƙwararrun ma’aikata na gida Nigeria dana ƙasar waje. Su biyu ne acikin motar, Shi yana a back seat na motar Ya zauna a hakimce, A yayin da Driver-operator dake driving dinsa Yana zaune saman driver’s seat kowan nan su na sanye ciki kakinsa na sojoji, sun yi shiru, Sanyin A.c din motar na ratsa fatar jikinsu, ga dukkan alamu wani muhimmin abu ne ya kawo su asibitin, akwai wanda suke Jira Ya ƙaraso, tsawon mintuna Biyar, wani kyakkyawan matashin likita Ya nufo motar da saurin shi kamar zai yi tuntu6e. A gaban motar su ya dakata da yin tafiyar, ya kai hannu yai knocking glass din motar, turo ƙofar da a kayi ne Yasa shi yin saurin gyara natsuwar shi, Sam hankalin shi ba a kwance ya ke ba, tun da sir mubarak ya kira shi awaya ya sanar da shi game da zuwan shi asibitin gaba ɗaya ya rasa natsuwar shi, saboda sanin matsayin shi a ƙasar. “Dr fawan, shigo ciki mana “ muryar Sir mubarak ce ta fargar da shi, Jiki na rawa ya shiga motar, ya zauna yana faman zazzare idonshi yace”daddy, ina wuni Ya gida ya Iyali” sir mubarak yace”lafiya lou fawan, Ya aiki ya fama da marasa lafiya” tun da ya fara magana bai ɗago Ya daura idonshi akan fuskar fawan ba, Hankalin shi na akan Wayar hannun shi da yake daddanawa. Still muryarshi na rawa ya furta”Lafiya lou daddy, sai ga kiranka, Na ɗanyi mamaki” sai da ya ambaci hakan sir mubarak Ya ɗago da ido ya kalli fuskar fawan, duk da sanyin A c na motar, abun mamaki zufa ce ke tsastsafo mashi, kallon tuhuma sir mubarak yake jefa mashi, saboda zufar daya gani a saman goshin shi. “Ya akai naga kana zubar da gumi? Ko baka da lafiya ne”? Yawu fawan Ya haɗiya tare da cewa”babu komai, Lafiya ta ƙalau” Ta6e baki Sir mubarak Yai”Okey, Inaso ka kaini gidan kajin da kuke kiwo kai da Jazz,” da alamun ruɗu akan fuskar dr Fawan yace”Gidan kaji? Daddy ban fahimci abunda kake nufi ba, waye ya buɗe gidan kaji” yanayin yadda ya furta maganar, babu alamun yasan da zancen. Fuskar sir mubarak a ɗaure tamau yace”You know who I am. I don’t need to explain this to you, Don haka kada ka 6oye min gaskiya, wani gidan kaji ne kuka buɗe kai da jazz? Da kanshi ya faɗa mini cewa kun zuba jari don kuyi kiwon kaji, kusan kullum ne saina kama shi yana yin waya akan gidan kiwon kajin ku” Hankalin dr fawan ba ƙaramin tashi yai fa, Muyarshi na rawa ya furta”`wallahi thumma tallahi daddy bansan da zancen gidan kaji ba, sai dai ko ƙarya dr jazz yayi maka, ka ji na rantse maka da Allah...” Lamarin ya ɗaurewa Sir mubarak kai, Sojan dake zaune a driver seat Ya natsu Yana sauraron su, ta cikin ear-view mirror din motar Yake kallonsu. “Fawan, Ka faɗamin gaskiya, ni nasan Jazz ba zai ta6a yi mini ƙarya ba, na lura gaba ɗaya baka acikin hayyacin ka, idan ma saboda ni ne to ka kwantar da hankalin ka, babu abun da zan yi maka, ni dai buri na shine ka kai ni gidan Kajin ku, inaso in gansu, nayi maka alƙawarin idan ka rakani na gansu zan ƙara maku jari” cikin ruɗu dr fawan ya girgiza kai yana fadin”bazan yi maka ƙarya ba daddy, ina ganin ka tamkar uba agareni saboda ƙaunar dake a tsakanina da Jazz, wlh Daddy ni bamu ta6a yin maganar buɗe gidan kaji da dr jazz ba” Da kakkausar murya Sojan dake a gaban motar yace”Sir, this boy isn’t telling us the truth. Why don’t we take him to the headquarter? Maybe if we do, he’ll tell us the truth.”(yalla6ai Yaron nan bazai fada mana gaskiya ba, Me zai hana Mu shiga dashi headquarter Wata’ƙil idan mu ka je can Ya faɗa mana gaskiya) Zaro ido waje dr fawan yai, jin ance za’aje dashi headquarter, sir mubarak yace”kada ka damu ai basai munje headquarter ba, akwai bindiga a ƙuguna, “yai maganar tare da sanya hannu ya zaro bindigar Ya ɗaurata saman laps dinshi, tsabar tashin hankali ne tsantsa akan fuskar fawan. Sir mubarak yace”idan na kashe ka na kashe banza, sai dai idan munje lahira ayi mana hisabi, don haka ka faɗa min gasiya, idan ba haka ba zan tarwatsa kanka da bindigar hannuna” bawan Allah dr fawan duk sun tsoratar dashi da barazanar su, ƴan hanjin cikin shi sun kaɗa. Hawaye tuni sun soma wanke fuskarshi, cikin sanyin murya yace”ko da zaka kashe ni daddy, bazan fasa faɗa maka gaskiyata ba, wlh rantsuwar ɗan musulmi bani da masaniya akan maganar gidan kaji, daddy banyi niyar fada maka ba, amma don in kare kaina zan sanar dakai wani abu da baka sani ba” Hankalinsu gaba ɗaya yana akan fuskarshi. Numfasawa yayi kafin ya ɗaura da cewa “Daddy, jazz baya zuwa aiki, yau kusan wata ɗaya da sati, bansani ba ko kunsan da hakan, Ni kaina na damu da canzawarshi,”. Zuciyar Sir mubarak a hautsine Ya furta”idan kuwa har hakane Dr fawan baka kyauta mini ba! Meyasa tuntuni baka kira awaya ka sanar dani cewa baya zuwa aiki ba? Kusan kullum sai na ganshi ya shirya zai je asibiti, hakan na nufin ba aiki yake zuwaba wani wurin daban ya ke tafiya? Ya jefa mashi tambayar yana mai jin ɗaci acikin zuciyarshi. “Ka yi hakuri daddy, Bana son in shiga tsakaninka da shi, sannan ni bansan baku da masaniya akan hakan ba” “Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un!” Sir mubarak ne ya furta hakan, zuciyarshi tayi matuƙar karaya da jin cewa jazz baya zuwa aiki, Ya fara zargin shi akan ƙarairakin da ya ke yi mashi, bai ta6a tunanin Jazz zai yi mashi haka ba, duk da irin ƙaunar da yake nuna mashi. Idanuwan shi tuni sun kaɗa jawur, zuciyarshi ta motsa. “Bana so Jazz ya san cewa nazo asibitin nan! Ko nayi magana dakai! Kaja baki kayi shiru,” dr fawan ya amsa mashi da toh daddy, in sha Allah bazan faɗa mashi ba. “Ka share hawayen ka,” da sauri dr fawan ya zaro hanky ya soma goge fuskarshi. “Dr fawan, Na yarda da jazz sai dai a yanzu na fara zargin shi, wallahi If I find out that he’s doing something wrong, sai ya ɗanɗani kuɗar shi,” rai a6ace ya furta maganar, ya ƙara da cewa “dr fawan nagoda da bayanan da ka bani, zaka iya komawa bakin aikin ka” jiki na rawa dr fawan ya fito daga cikin motar, Bayan yayi masu sallama Ya nufi cikin asibitin yana faman sauke ajiyar zuciya. Shiru su ka yi babu wanda ya ƙara magana acikin motar, Lamarin ya ɗaurewa Sir mubarak Kai, Mamakin shi ƙaryar da jazz yai mashi na cewa Sun buɗe gidan kaji, da kuma zuwa aikin da yake yi ashe duk ƙarya ne. Driver-operator, Ya fahimci halin da sir mubarak ya shiga na damuwa, cikin kwantar da murya yace”Sir, pls kada hakan ya dame ka, nasan ba daɗi mutumin daka yarda dashi ya sa6aka, sai dai fa har yanzu bamu da tabbacin abun da dr jazz ya ke yi, mu kyautata mashi zato, sannan shawarar da na ke so in baka yalla6ai, me zai hana mu fidda rana ɗaya, Mubi bayan shi ba tare da sanin shi ba, a lokacin da ya shirya zai tafi aiki,” Ta cikin mirror din motar Yake duban sir mubarak, nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke tare da kallon drivern yace “Ka kawo shawara mai kyau, tabbas inason sanin me jazz yake aikatawa, nagode da shawararka, zamu Iya tafiya” Cikin girmamawa Ya amsa mashi da toh, sannan ya tada motar Ya fito da ita daga cikin harabar ajiye motocin, atsanake ya ke yin driving har suka haura saman titi, sir mubarak bai dai na cizon yatsanshi ba, saboda Ya damu da jazz, Ƙaunar da ya ke yi ma mahaifiyar shi ce ta shafe shi, ko ƴa’ƴan shi da ya haifa bai jin su kamar yadda yake jin jazz, hankalin shi ba zai ta6a kwanciya ba idan har bai gano abun da ya ke aikatawa ba, ya jima yana danne zuciyarshi akan ƙin amincewa da zargin yaron da ta ke yi, abun da ya jawo shi ga bincikar shi a yanzu ya fahimci aduk lokacin daya kama jazz yanayin waya da zarar Yaganshi yake rasa natsuwarshi, Jikinshi ya hau kerma, shiyasa ya fara suspecting dinsa. ❤ANEELERH❤ Tun kafin ta sallame sallar azahar wayar ta dake ajiye saman drawer take ta buga ringing, da zarar kiran ya katse wani ke shigowa, sai da ta kammala sallar ta ɗaga hannu tayi addu’a ta shafa a fuska, kafin ta miƙe da sauri ta nufi drawer ta ɗauki wayar, murmushi ta saki ganin sunan surukar arziƙi ya bayyana akan screen din wayar, aranta ta ayyana halan baby junaid ne ya matsa a kirani awaya. Bayan ta ɗaga kiran ta manna wayar a kunnanta, kafin ta furta sallama muryar junaid ta katse mata hanzarin ta. “Mommy, baby junaid ne, ni ne na kira ki awayar granny,” har sai da ta ji gabanta Ya ɗan faɗi, da mamaki tace”junaid da gaske kai ka kirani? Ina mommy adama? Ko dai itace ta baka wayar don ka yi mini magana” muryarshi da shagwa6a yace”mommy ai bata nan, suna a falo, Ni kaɗai ne a ɗakin...” tun kan ya ƙarasa maganar tace”Junaid bana hana ka ɗaukarwa mutane waya ba? Faɗamin ya akai ka iya buɗe mata waya”? “Mommy wasa nake maki, itane ta bani wayar, ta fita falo, ni kaɗai ne a ɗakin” A faɗa ce tace”ƙarya ka ke yi mini junaid, ba ita bace ta baka wayar, kaine ka ɗauka ka kira ni, maza ka aje mata wayarta tun kan na 6ata maka rai,” ta yi maganar tamkar ranta ya 6aci sai dai azahiri ta yarda bashi wayar akayi, kawai tana son ta hayaƙa shi ne. Sautin kukan shi ne ya cika mata kunnuwanta. “Mommy ba ki yi missing dina ba, shiyasa kike yi mini faɗa, Kin barni ni kaɗai agidan su, ni wlh gida zan dawo, ko dai kizo ki ɗauke ni ko kuma in gudu in 6ace kamar Angel” maganarshi tayi matuƙar bata dariya, cikin sigar lallashi tace”am sorry my baby boy, wlh nayi kewarka kamar zan zauce, yanzu dai ka yi haƙuri kadaina kuka, Mommyn ka bata son zubar hawayen ka” Cikin shessheƙar kuka yace”ni dai kizo ki ɗauke ni mommy, ko in gudu” hankalinta ya dan tashi, zuciya da saƙe saƙe saita dinga tunanin ko dai wani abu akayi mashi ne wanda ya 6ata mashi rai har yake neman dawowa gida. “Junaid, faɗamin meya faru? Basa baka abinci ne? Ko ba ayi maka wanka ne? Ko wani ya buge ka ne”! A jere ta furta hakan. “Ni ba su yi min komai, ina cin abinci kuma mommy adama tana min wanka har sau biyu safe da dare, ni kawai ke nakeso kizo ki dauke ni, ko in gudu” ajiyar zuciya ta sauke, hankalinta har ya ɗan kwanta. “My baby boy, ka kwantar da hankalin ka, zasu dawo mun da kai nan bada jimawa ba,’ Rigima ya sanya mata”Allah in baki zo ba saina gudu” dariya ce ta kubce mata, jin sautin dariyarta ba ƙaramin 6ata mashi rai ba. “Mommy dariya kike mini ko! Shikenan zan kashe wayar” da sauri tace”sorry nadaina, pls kada ka kashe min waya, Ina jin daɗin yin magana dakai, Yanzu faɗa min a kwance kake ko a tsaye” “Saman gado” ya bata amsa atakaice, har ta buɗe baki zatayi magana ya katse ta da cewa”Mommy, na tuna sunan mutumin nan da ya kira ki a waya, ran nan, amma ba zan fada maki ba, In kina son ji kizo nan” “Am sorry my baby boy, yakamata ka fahimce ni, babu yadda za’ai inzo, Zasu yi tsammanin ban yarda ɗazu bane shiyasa na biyo ka, dan Allah ka faɗa min sunan shi, ka ji yaron kirki” cikin ƙagara da sonji tayi mashi maganar. “Toh mommy, zan faɗa maki amma bana so kowa yaji har zahra” muryarshi da shagwa6a yake magana. “Junaid, Ni kaɗaice a ɗakin, Zahra bata nan taje wurin aiki, Mahboob ma baya acikin gida, Abie da Uncle basu dawo gida ba, mami da ummi ne kuma basa a ɗakin, suna a can palour suna fira” “To zan faɗa maki, amma kada ki faɗa ma zahra da mahboob” ta rasa ya za ta yi da shi, Yaƙi faɗa mata sai jan maganar yake yi kamar baya son fadi. Kukan ƙarya ta soma yi mashi tana fadin”dan Allah baby junaid dina ka faɗamin, zuciyata zata iya bugawa idan ban ji ba” tuntsirewa yayi da dariya yana fadin”mommy wasa kike ba wani kuka ai na ganoki” gajiya tayi da tsayuwar, ta koma gefen gado ta zauna, tamkar tana agabanshi ta marairaice mashi fuska tana fadin”pls my baby boy, ka faɗa min, komi ka ke so zan yi maka” “Zoben Angel, da ki ka ce zaki siya mini in bata tun da na maida ba mahboob nashi” “Kada ka damu, kafin ka dawo gida zan siya maka zoben, Nayi maka alƙawari, Yanzu faɗa min toh” Sai da ya mula ya ishe iska tukunna Ya furta”wai ma...waima daddyn Unaisah, haka yace min fa” shiru tayi jimm tana tunanin sunan daya furta mata daddyn unaisa? Wanene daddyn unaisa? Ita kanta unaisan wacece ita!, sunan ya shige mata, jin tayi shiru yasa Baby junaid ambaton sunanta”mommy kin yi shiru baki ce komai ba” “Junaid, na ruɗe ne, na kasa gane wanene daddyn unaysa, amma shi mutumin Iya abun da ya faɗa maka kenan”? “Eh, bai faɗa min komai ba, Mommy ki kira shi ki ji toh wanene shi, ko daddyn Angel dina ne?” lokaci ɗaya taji gabanta Ya faɗi Jin Ya ambaci ƙila daddyn Angel ne, nan take ƙwaƙwalwarta ta tunano mata sunan wacece Unaisa, a sukwane ta mike tsaye Tana faman zare idanuwanta, zurfi tunani ta shiga duk duniyar nan mutun ɗaya ta sani mai sunan daddyn unaisa, wato Tajuddeen, ta gaza yarda da abinda zuciyarta ke faɗa mata. La66anta na kerma ta furta”ka tabbata haka sunan yake? Ko dai abakina ka ta6a jin na ambaci sunan daddyn Unaisa? “Mommy wlh dagaske nike maki haka yace min wai in faɗa maki daddyn unaisa ne, mommy zan kashe wayar, ga mommy adama nan zata shigo dakin” kafin ta yi mashi magana yai rejecting kiran. Hakanan tadinga jin bugun zuciyarta na ƙaruwa, jiki asanyaye ta koma gefen gadon ta zauna, tsawon mintuna zuciyarta nayi mata kokwanton maganar da junaid Ya faɗa mata, har dai a ƙarshe ta yanke shawarar cire nombar daga black list, don ta kira ta ji wanene mutumin da junaid ya fada mata cewa daddyn Unaisa ne, fatanta Allah yasa Dagaske ne hasashenta. Yatsun hannunta har kerma suke Yi wurin daddana wayar, bayan ta cire number daga black list, ta danna call cikin sa’a Kiran Ya shiga, wayar ta fara ringing, tsabar zumuɗi jikinta har kerma yake yi, Har kiran yayi rejecting ba’a ɗaga ba, Miƙewa tayi tsaye ta zame dogon hijabin jikinta ta jefar saman mattress, safa da marwa ta cigaba da yi a tsakar ɗakin, ta ruƙe wayarta a hannunta, a Ƙalla Ta Kira layin kusan sau biyar Yana ringing ba’a ɗaga ba, Hankalinta yaƙi kwanciya burinta taji wanene mutumin nan daya kira kanshi da sunan daddyn Unaisah. Har ta fidda rai da za’a ɗaga Kiran, Unexpected A kira Na shida data yi mashi sai gashi Anyi picking call din. Cikin rashin natsuwa ta furta”Assalamu alaikuma” maimakon ta ji muryar Namiji sai taji muryar matashiyar mace tana yi mata magana da wani yare. “Baiwar Allah, bana jin harshen da kike yi mini magana dashi, Idan kina jin hausa mu yi magana da shi” Ko da Aneelerh ta ambaci hakan, matashiyar sai ta canza harshenta zuwa Yaren hausa ta ƴan koyo tace”wanene ke magana”? A ƙagare Aneelerh tace”sunana Aneelerh, dalilin dayasa na kira Layin, kwanakin baya ana yawan kirana dashi, Ina tunanin ko wani ne ke nema, pls ina neman me wayar” ta faɗi hakan ne don junaid ya fada mata cewa Namiji ne Ya daga kiran lokacin da aka kira. Matashiyar budurwar tace”Ni ce me wayar, wato irin kune ku ke bibiyar mazajen mu don ku ƙwace mana su ko”? Sakin baki Aneelerh tayi jin abun da matar tace. “Kiyi haƙuri, Nima matar aure ce kamar ke, kawai inason nasan ainihin wanene me wayar, ki taimaka min a ƙagare nake da son ji” da alama matashiyar Yarinyar Akwai ƙuruciya atattare da ita, tun daga kan kalamanta zaka shaida hakan. “Nace maki ni ce me wayar,” atsawace ta furta hakan, Aneelerh tace”ba wayar ki bace, saboda ke da kanki ki ka ce irina ne masu bibiyar mazajan mutane don mu kwace masu miji, hakan na nufin ba wayarki bace wayar mijin ki ce” sautin dariyar matashiyar ne ya cika mata kunnuwanta, lamarin ya ɗaure ma Aneelerh kai, gashi duk ta ƙagara a matse take da son jin wanene. “Ke dai zan faɗa maki gaskiya, tun da kin gano ni, ba wayata bace, wayar mijina ce, kuma baya nan Ya fita ni ka ɗai ce agidan” “Okey, pls Ko zan Iya sanin sunan mijin naki”? “A’a gaskiya, salon ki je ki kai ma boka sunan shi ayi maki asiri ki mallake shi” duk yadda Aneelerh ta kai ga jurewa saida ta fashe da dariya jin abun da Yarinyar tace, daƙyar ta sassauta da yin dariyar tace”wlh ni bana bin boka, Ko hanyar zuwa wurin shi bansani ba, Yar uwata ba duka aka taru aka zama ɗaya ba, ni bana ɗaya daga cikin matan dake zuwa wurin boka, saboda na dogara da Allah shi kadaine zai Iya biyamun buƙatuna” matashiyar tace”Ni ban yarda dake ba, mata dayawa suna son ƙwace mini mijina saboda kyakkyawa ne kuma yana da ƙarfi” Aneelerh tace”baiwar Allah na faɗa maki nima matar aurece, da mijina akan me zan nemi mijin ki”! “Oho nima bansani ba, idan kin gama magana zan kashe wayar” amsar data ba aneelerh kenan” Shiru aneelerh ta ɗanyi tana tunanin hanyar da zata 6ullo mata, ta fahimci Yarinyar bata da cikakken Ilmi da wayau sai a hankali. Dabara ce ta faɗo mata. Dariya ta fara saki, Matashiyar tace me kike yi ma dariya Aneeleh tace”Ai dole inyi dariya, ke yanzu baki gane muryata ba ne? Aneelerh fa ce matar abokin mijin ki Shu’aibu” Da buɗar bakin budurwar sai cewa tayi”ƙarya kike yi aini mijina basu nan shi shu’aib ba, TAJ ne sunan shi, Kina son ki yi mini wayau ne” Jin ta ambaci sunan Taj Yasa Aneelerh Tsayawa cak ta dakata da yin tafiya, yayin da bugun zuciyarta ya ƙaru, Muryarta na ɗan rawa ta furta”ƙarya kike yi, ba sunan mijin ki tajuddeen ba, so kike in yadda don kada ki faɗa min ainihin sunanshi, ai ni nasani Shu’aibu ne sunan shi” Matashiyar budurwar tace”To kada Allah yasa ki yadda ma, kuma wlh ma ƙarya kike yi mini cewa wai ke matar abokinsa ne baki da gaskiya,” da alama ranta ya 6aci ta fara harzuƙa. Sassauta murya Aneelerh tayi”Ki yi haƙuri, ba yadda ki ke tsammani bane, Dan Allah ki faɗamin ina mijin naki yake inason yin magana dashi” Dogon tsoki matashiyar Taja, kafin ta furta”ba kin ce ke matar abokinsa bane? To ki ce ma shu’aibun Ya kawo ki gidan mu,” kafin Aneelerh ta furta wani abu, Matashiyar ta katse kiran!” Hankalin ta Yaƙi kwanciya, Jiri ta soma gani acikin idanuwanta, a daddafe ta nufi gado, Ta haye ta kwanta, Yayin da idanuwanta ke fuskantar ceilling, zuciyarta ta shiga ruɗani, tun da Matashiyar ta ambaci sunan tajuddeen, natsuwarta tabar jikinta, taso ace tayi waya da shi don ta tabbatar da abun da take hasashe. Har ƙara jaraba kiran layin tayi amma matar taƙi ɗagawa. Dubara ce ta faɗo mata aranta, da sauri ta rubuta mashi saƙo cikin harshen turanci. _Idan ka karanta saƙona, dan Allah ka kira ni, Inason Yin magana da kai, saƙo daga Aneelerh muhammad falgore_ Ajiyar zuciya ta sauke Bayan ta kammala rubuta mashi sakon, Ta ɗaura wayar saman side drawer, A gogon ɗakin ta kalla ƙarfe Uku na rana, kwanciya tayi saman gadon tana jiran tsammanin Kiran me wayar. ❤ZEENATU❤ A 6angaren zeenatu kuwa tun da ta fito da gudu daga ɗakin Dr. Shureim ta koma ɗakinta, ta fada saman gado taci gaba dayin kuka tamkar ranta zai fita, cikin muryar kuka take fadin”yaya shureim ba sona yake yi ba, wata yake so daban, dama nasani babu namijin da zai yarda yaso ni saboda rashin natsuwata,” Idanuwanta sun kaɗa jawur, miƙewa tayi zaune ta soma cire lace jikinta a saman floor, ta watsar da kayan hada ribbon din da aka daure mata gashin kanta, iya undy ta bari a jikinta, ta jashi saman ƙirjinta, tana huci yayin hawaye ke cigaba da wanke mata fuskarta, saukowa tayi daga saman gadon ta nufi gaban dressing mirror dinta, cikin 6acin rai ta sanya hannu ta watsar da jerin turarurrukanta komai sai da ta wurgo shi ƙasa, bayan ta gama ta koma gaban wardrobe dinta, ɗaya bayan ɗaya sai da ta wurga da suturar saman floor, hankalinta bai kwanta ba har saida ta maida ɗakin kamar na mahaukata, tukunna ta koma saman gadon ta haye tare da jan bargo ta lullu6e zuciyarta na ta farfasa. Bayan Dr. Shureim ya fito daga wankan, kimtsa kanshi yai ciki shiga ta larabawa Ya feshe jikinsa da turare, Ya ruƙo wayar shi a hannun shi, tare da car key dinsa, walking quickly ya fito daga bedroom dinsa, Ya nufi ɗakin zeenatu, duk inda Ya gifta a paloun masu aiki ne suke Yin aikace aikacen su cikin girmamawa suke gaishe da shi. “Yalla6ai barka da fitowa” muryar Tani ce ta katse mashi hanzarinsa, dakatawa yai da yin tafiyar ya juya ya dubeta “Yawwa barkanki, Ya aiki” fuskarta da fara’a ta amsa mashi”Lafiyalou Alhamdulillah,” Har zai wuce ta Ya kuma tsayawa ya kalle ta”Ɗakin zeenatu nake nema” Da rawar Jiki ta ce”Yana a second floor, muje in nuna maka ɗakin” ta faɗa tare da yin gaba Yabi bayanta, Yayi matuƙar ƙagara da son ganinta, duk don Ya lallasheta akan laifin da yayi mata. Bayan sun hau elevator ta sauke su a second floor, Tani ta nuna mashi ƙofar ɗakinta. “ki shiga ki faɗa mata inason magana da ita” Tani ta amsa da toh, tana zura ƙafarta ɗakin zeenatu, gabanta Ya faɗi ganin irin 6arnar da tayi, hankalin ta ba ƙaramin tashi yai ba, jiki na rawa ta nufi gefen gadonta. “Zeenatu! Lafiya meke damunki ne? Meyasa kika hargitsa suturar ki”? Shiru zeenatu bata tanka mata ba, saima ƙara ƙudundune kanta da take yi cikin bargo. “Dan Allah zeenatu kiyi mini magana, nasan 6ata maki rai akayi ki fada mini wanene” Jin tayi shiru ba ta yi mata magana ba yasa tace”ba zan takura maki ba, Yanzu ki tashi Yayan ki shureim Yana a ƙofar ɗakin ki, shine yace in yi maki magana yana son ganinki” Kamar jira ta ke yi Tani ta ambaci sunan shureim, Cikin shessheƙar kuka tace”Tani, I don’t want to see him. Please tell him I won’t come. Yaya Shureim doesn’t love me wata yake so daban, tun jiya yayi min alƙawarin zamu fita yawo atare, yau kuma da kanshi yace min inje in shirya kafin in dawo zai yi wanka ya shirya, Tani da naje ɗakin shi babu abunda yayi, yana akwance saman gado yana kallon hoton girl friend dinsa a laptop....” daƙyar ta ƙare maganar. Jikin Tani yai sanyi, duk sai taji ba daɗi, sai yanzu ta gane dalilin dayasa ta shiga halin da take aciki. “Kiyi haƙuri zeenatu, ki tashi ki gyara jikinki, Yace yana son magana dake nasan yazo ne don ya baki haƙuri, kuma naga ya shirya hada key din mota a hannunshi....” Katse ta Zeenatu tayi”Na fasa zuwa ki faɗa mishi bazan je ba, tun da bayaso na” Cikin muryar raɗa Tani tace”yana fa jin ki, bai kamata kina ɗaga murya ba, sannan ke in banda abunki waya fada maki budurwashi ce yake kallo awayar? “Ai naga hoton da yake kallo, Yana a kwance saman gado ya rungumeta a kirjinsa” ta fada tana jan numfashi taƙi fitowa daga bargon. “Zeenatu, kiyi mashi kyakkyawan zato, yaya shureim yana sonki fiye da yadda kike son shi, Ni shawarar da zan baki shine kada ki bari ya gane kina son shi, idan kika kwantar da hankalin ki da kan shi zai furta maki kalmar so” Sassauta muryarta tayi”Tani, zan iya jure wannan amma bazan Iya jure kallon hoton budurwarshi da Yake Yi ba,” Dafe kai Tani tayi da hannu ɗaya”zeenatu baki da tabbacin budurwashi ce, pls kibi komai a sannu zamu gano ainihin wacece Yake kallo awayarshi, Yanzu Ki tashi muje Yana awaje yana jiranki’ “Tani ki daina wahalar da kanki, Nifa ba inda zanje, Ki fada mashi bana Jin daɗi bacci Nike Yi” Duk yadda Tani taso ta lallashe ta akan ta tashi ta je gare shi taƙiya, a dole ta ƙyaleta ta juya ta fuce daga ɗakin. A tsaye ta same shi Ya jingina bayanshi jikin bango. Harya fara Gajiya da tsayuwa “Ka yi haƙuri, Zeenatu tayi fushi bansan meya haɗa ta dakai ba, nayi ƙoƙarin In lallasheta amma taƙi amincewa ta amsa kiran ka, ban ji daɗi ba shureim, duk da bansan meya haɗa ka da ita ba, amma bai kamata tun yanzu afara samun rashin jituwa a tsakaninka da ƙanwarka, zeenatu tana da haƙuri sai dai tana da zuciya idan aka 6ata mata rai’ Tun da ta fara magana Ya natsu yana sauraronta, sai da ta kai karshen maganar tukunna yace”Inaso zan shiga ciki” bai jira amsar da Tani zata bashi ba yai saurin haura ƙafarshi cikin ɗakin zeenatu. Dafe kai tayi da hannu ɗaya tunawa da 6arnar da zeenatu tayi a ɗakin, gashi kuma Ya shiga hake zai je ya same shi kamar bola, can kuma ta ayyana aranta cewa ɗan uwanta ne, daga haka ta ƙara gaba. A tsanake Yake bin ko’ina na ɗakin da kallo, yayi mamakin ganin yadda ta hargitse komai, ta rikita mashi tunanin shi, Ya rasa gane fushin menene take yi da shi? Don shi a tunanin duk akan fitar da yace za su yi ne. Sam bai lura da lace din data cire ta jefar saman floor, idanuwanshi na akan gadonta, bargon da ta lullu6e dashi sai kerma yake kamar wadda sanyi ya kama. daddaɗan ƙamshin turarensa ne Ya daki hancinta, Nan take ta fahimci Ya shigo ɗakin nata. Gefen gadonta ya zauna Yana dubanta, calmly ya furta”Zeenat ina son yin magana dake Shiru tayi bata tanka mashi ba, tayi tunanin Tani ta fada mashi cewa bacci take yi kamar yadda tace ta gaya mashi. “Nasan Kina Jina zeenatu, Ki amsa mini, nazo ne don in baki haƙuri, nasan ban kyauta maki ba, Yanzu haka da nike yi maki magana na kammala shiryawa ke nake jira mu tafi” Cikin disasshiyar murya tace”yaya shureim bana jin daɗin jikina, bazan iya fita ba, sai dai zuwa gobe” “am sorry zeenatu, fushi kike yi da yayan naki? Ba za ki yi mini uziri ba? “Yaya shureim ni ba fushi nike yi dakai ba, fitarce na fasa, Bana jin daɗi” Ya rasa ya zai yi ya shawo kanta don ta amince su fita. Yanke shawarar Yaye Bargon Jikinta yai don ya samu damar lallashinta dakyau. Tsautsayine Yakai hannun shi saman bargonta, Ya ruƙo shi tare da jan shi, Ras yaji gabanshi ya faɗi da sauri Ya maida mata bargon a jikinta, Yana faman jan numfashi da ƙarfi da ƙarfi, miƙewa yai da wani irin Yanayi ya nufi ƙofar fita daga ɗakin Yayin da la66ansa ke ambaton sunan Allah, Har ya kusa kaiwa ƙofar ɗakin Muryar zeenatu ta katse mashi hanzarin shi. “Yaya shureim kai da kanka ka faɗa mini cewa baka ta6a yin soyayya ba, amma meyasa kake kallon hoton wata awayarka” Ta gaza haƙura har saida ta amayar masa da abunda ke cikinta, shi kuwa Man din duk ya rasa natsuwarshi, tunda Yaja bargonta Yayi arba da undy din jikinta shara shara Hakan ba ƙaramin tada mashi hankalin shi yai ba, ga dukkan alamu ita batasan ma ya buɗe bargon ba saboda ta ƙudundune kanta, idanuwanta suna arufe. “Zeenatu, abun da na faɗa maki da gaske ne, banyi maki ƙarya ba, Ni ban ta6a yin soyayya ba” A hankali Ya ɗan Juyo yana dubanta, a lokacin ta fiddo da kanta daga Cikin bargon, Yalwatacciyar sumar kanta, ta rufe mata gefen fuskarta, Jan bakin data shafa ya dame fuskar saboda kukan da tasha, har saman kumatunta jan bakin ne, duk da kwalliyar fuskarta ta 6aci ba ƙaramin kyau tayi mashi ba. Muryarta da shagwa6a tace”ka faɗamin wacece ka ke kallo awayarka? Idan ba budurwar ka bace. Ƙayataccen murmushine Ya bayyana akan fuskarshi, sai yanzu ya gane dalilin dayasa take haukan nan, wato kishin shi take Yi saboda yana kallon hoton wata wayarshi, aranshi ya ayyana da ace tasan hoton wacece yake kallo da batayi haukan nan ba. “Zeenatu, dama saboda hoton wayata kike kuka”? Ɗaga mashi kai tayi alamar eh. “Okey, Ki kwantar da hankalin ki, ba budurwata ba ce,” maƙe mashi kafaɗa tayi”ni ban yadda ba yaya shureim, idan har dagaske kake yi min ba budurwan ka bace to ka nuna min hoton in gani” Lumshe idonshi ya ɗanyi tare da waresu kan fuskarka, duk da tazarar dake a tsakanin su, ba ƙaramin Kyau take yi mashi ba musamman yanzu daya fahimci irin zazzafan son da take yi mashi. Ganin ya tsareta da ido, ba tare daya furta komai ba yasa tace”Yaya shureim magana fa nake yi maka, kayi shiru baka ce komai ba, Ni dama nasani baza ka nuna min hoton in gani ba” Yadda take yin maganar tana jujjuya eyes balls dinta ne suka ƙara rikitar da shi. Gyaran murya ya ɗanyi kafin yace”Idan har Ki ka amince zaki shirya mu fita, Ni kuma zan nuna maki wacece nake kallo awayata,” zum6ura mashi baki tayi”toh, amma ka fara yi min alƙawari,” “Nayi maki alƙawari” “Yanzu zan shirya yaya shureim,” ganin tana ƙoƙarin miƙewa tsaye yai saurin fuce wa daga ɗakin gudun kada Ya ƙara ganin abunda zai hana shi Runtsawa. Fitowa ya yi daga cikin gidan Ya nufi harabar ajiye motocin su, Wasu danƙara danƙaran motoci ne na Alhaji musa a killace a ƙalla sun haura goma shabiyar, kuma dukansu babu motar ƙasa da miliyan talatin, Manya manyan motocine tsadaddun gaske masu numfashi. Motarshi Ya buɗe Ya shige Ciki Ya zauna a driver seat haɗi da ɗaura kanshi jikin headrest, bakomai Yake tunawa ba face maganar da Alhaji musa ya faɗa mashi akan Aiki da kuma aure, A yanzu ya fara tunanin ta yadda zai 6ullo mashi da zancen auran zeenatu, yafi buƙatar auren akan komai, saboda yanason ya samu natsuwar cigaba da gudanar da rayuwarshi, zeenatu ta kwanta mashi aranshi ɗari bisa ɗari, kuma yana da tabbacin zeenatu zata maye mashi gurbin abunda ya rasa. Almost 15 mins, ƙamshin turarenta Ya doki hancinsa, Nan take ya fahimci ƙarasowarta, buɗe motar Tayi tare da samun wuri ta zauna gefenshi” ɗaura idonshi yayi akan face dinta, babu make up, zallar kyan da Allah yayi matane, ta canza kayan jikinta zuwa turkish gown launin black gray, Ta yafa mayafi akanta, Idanuwanta sun kumbura saboda kukan da tasha. Kallon Juna suka somayi kamar zasu haɗiye kawu nan su, Ko ƙyaftawa basa yi, kunyar shi ce ta kama ta, da sauri ta daura kanta saman laps dinta. “Zamu Iya tafiya” da shagwa6a tace”a’a yaya shureim, nafi so ka fara nuna mini hoton in gani” Zaro wayarshi yai daga cikin aljahu Ya daddanata, Kafin Ya miƙe mata wayar”kar6i ki ganta, Kyakkyawa ce tafi ki kyau, ita nike da burin aure” Gabanta na faɗuwa ta ɗago, tare da sanya yatsun hannunta dake kerma ta kar6i wayar da ya miƙo mata, idanuwanta rufe tabarsu, Gudun kada taga abun da zai hanata kwanciyar hankali. Dr. Shureim dake kallonta, murmushine ɗauke akan fuskarshi “Meyasa ki ka rufe idonki”? Muryarta na rawa ta furta”bana son inga abunda zai hanani bacci” “In sha Allah ba zai hanaki yin bacci ba, sai daima ya sanyaki yin bacci cikin kwanciyar hankali, now Open your eyes slowly and look at the picture,” She took a deep breath and tried to slowly open her eyes kamar yadda ya bata umarnin ta bude su a hankali.....” (Kaɗan daga cikin na sati mai zuwa idan Allah yakaimu da rai da lafiya🤣 sai dai Allah yakaimu zamu gani, Very soon In sha Allah Zamu shiga Takun ƙarshe na labarin kurkukun ƙaddara) *Boss Bature✍️ Mu haɗu Monday In sha Allah Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya, Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*_ ~Middle step~ سجن القدر❤🤍❤ _THE PRISONERS E24🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* Confusion of the heart💫 lokacin da ta ware idanuwanta akan screen din wayar wani irin sanyine ya ratsa zuciyarta ganin fuskarta, hotonta ne tun tana ƴar shekara goma sha ɗaya a duniya, tsabar farin ciki Ya hanata rufe baki, hada hawayenta saboda farin cikin ganin hotonta ne yaya shureim yake kallo, bata kawo komai aranta ba saboda ta yarda da shi. Ɗagowa tayi idonta acikin nashi ta furta”yaya shureim dama hotona kake kallo”? Ɗaga mata gira yai alamar eh, ta kuma cewa”yaya shureim wannan ai tsohon hotona ne a ina ka same shi” Fuskarshi ɗauke da murmushi yace”nima tsohuwar ajiyace a cikin memory dina, saboda inason hoton bana so na rasa shi, bama shi kaɗai ba akwai sauran hotunanki a gallery ɗin wayar zaki Iya dubawa ki gani” Yatsun hannunta na kerma ta bubbuɗe sauran hotunan tana kallonsu hada wanda tun tana jaririya akayi mata shi, abunda ya ɗaure mata kai gaba daya gallery na wayarsa hoton mutun biyune acikinsa daga hotonta saina ƙanwarshi benazir. “Yaya shureim tun yaushe kake kallon hotuna na”? ta faɗa da mamaki akan fuskarta. Muryarshi ƙasa ƙasa tamkar tame yin raɗa ya furta mata”tun lokacin dana fahimci kece ƙaddarata” wurga mashi blue eye balls dinta tayi akan face dinsa. “Ƙaddararka? Kamar yaya kenan”? Cikin rashin fahimtar kalaman shi ta ambaci hakan. “Lokaci zai ƙure mana zeenatu, ki bari idan muka dawo gida zan fahimtar dake abunda nake nufi” amsa mashi tayi da toh, haɗi da miƙa mashi wayarshi Ya sanya hannu ya kar6a, ya turata a aljhu, har cikin ranshi ba ƙaramin daɗi yaji ba, ganin bata kawo komai aranta ba, Duk da ya 6oye mata ainihin hoton da yake kallo. “Allah sarki aunty benazir, nayi missing dinta Yaya shureim, tsawon lokaci babu ita, Allah dai yasa aganta da ranta da lafiyarta” cikin sanyin murya zeenatu ta yi maganar, ya amsa mata da ameen. Yana ƙoƙarin tada motar, ba zato ba tsammani yaji zeenatu ta kwantar da kanta saman kafaɗarshi, wata irin kasalace ta soma baibaye shi sakamakon ƙamshin turarenta dake kashe mashi jiki. A hankali motarsu ta miƙi Hanyar babban gate din gidan, Gate security officers ɗin dake tsaron gidan suna ganin motarshi gaba ɗaya suka yunƙuro suka nufo motarsu, hannunsu ruƙe da jibga jibgan bindigu, ba arziƙi dr. shureim Yaci burki, Jin ya dakata da yin driving din yasa zeenatu ɗago da kanta daga saman kafadarshi ta dube shi. “Yaya shureim meyasa ka dakata da yin driving din” “Masu tsaron gidan nan ne suke tunkaro mota ta,” ya bata amsa a takaice. Dafe kai tayi da hannu ɗaya”Namanta ban faɗa ma daddy ba, Ni nasan daƙyar zasu bari mu fita, idan har bai basu umarnin su ƙyale mu ba, gashi baya agidan, Mommy ma har yanzu bata dawo daga office ba” ta faɗa tana faman zare ido. “Yaya shureim ka kira daddy awaya ka sanar dashi” a tsoroce take yi masa maganar don ita kanta mugun jin shakkar masu tsaron gidan nasu take ji, ƙirar jikinsu kaɗai abun tsoratarwa ne, sannan basa wasa da aikinsu, gashi babu annurin akan fuskokinsu. Kafin dr shureim Ya zaro wayarshi tuni sun cimma masu, ƙawanya su ka yi mata motarshi. Ɗaya daga cikin su ne yai knocking glass motar, da kakkausar murya yake ya ce “wanene acikin motar? Muna baka umarnin ka zuge glass din motar ka” zeenatu ce ta sauke glass din, Ya zuƙunno Yana dubansu A tsanake miryarta na rawa tace”yanzu zai kira daddy awaya, yayana ne shureim zamu fita yawo ne” Security guard ɗin yace”oh, meyasa baki faɗa mashi ba’a fita dake waje ba tare da iznin daddyn ki ba”? Still muryarta arude ta furta”ai mantawa nayi ban fada mashi ba” jinjina kai mutumin yai”okey, Muna jiran umarninsa” Kusan Sau uku dr shureim yana jaraba kiran layin Alhaji musa bai ɗaga ba, zeenatu tace dashi”ka jaraba kiran Layin mommy, idan tayi masu magana zasu barmu mu fita” kiran Layin Hajiya sarah yayi ringing biyu ta ɗaga, bayan sun gaisa ya sanar da ita halin da suke aciki, tace dashi yaba ma Security guard din waya suyi magana da shi. Miƙa masu wayar yai, bayan sun kar6a ya dubi zeenatu, yayi mamakin ganin zufa na wanke fuskarta duk da sanyin A.c na motarshi, ya fahimci tsoron su take ji. “Ki kwantar da hankalinki zeenatu kina atare dani” cikin sanyin murya ya ambaci hakan, muryarta tamkar zata fashe da kuka tace”yaya shuriem ni bana son tashin hankali, duk laifin daddyne ni banga amfanin ajiye waɗannan ƙattan ba acikin gidanmu, ai Allah ne ke tsare bawansa bawai mutun ba” da shagwa6a ta ƙare maganar, ruƙo hannunta yai acikin nashi, da sauri ta mayar da kanta saman kafaɗarshi tare da lumshe idanuwanta tana faman sauke ajiyar zuciya. Miƙo mashi wayar Security guard ɗin yai”an baku iznin fita, amma bisa sharaɗin zaku koma mazaunin baya na motar, Ni zanyi driving dinku duk inda zaku je” zeenatu tamkar zata fashe da kuka tsabar jin takaicin jin abunda Security guard din ya fadi. Dr shureim yace “ba damuwa mun gode da kulawa,” ya faɗa yana buɗe murfin motar, fitowa su ka yi daga front seat suka koma back seat na motar suka zauna,” security guard din ya shiga ciki Ya zauna a driver’s seat, Ya tada motar Ya fuce dasu daga cikin gidan lokacin da suka haura saman titi, security guard din ya tambaye su ina zasu je ne, zeenatu ce ta zayyana mashi wuraren shaƙatawar da zasu je, kafin dawowarsu gida sai da suka mori lokacinsu, kamar karsu dawo gida. *EX-PRISONERS❤* After two days (bayan kwana biyu) Idan muka koma 6angaren prisoners sai dai muce Alhamdulillah, domin kuwa tafiya ta kankama, tun bayan da sojoji suka ƙulla yarjejeniya da ummin america, A ranar wuraren ƙarfe shidda na marece, sojojin suka zo kawo masu ziyara domin duba lafiyarsu, a ɗakin hutawar dr Laura, suka tattarasu gaba ɗayansu, sunyi matuƙar jin daɗin ganin Yaran sun samu sauƙi musamman Danish da suka barshi Yana ta faman sharar bacci, dama sun ƙwallafa rai akan son ganin ya farka, duk da bai sakar masu fuska ba sai da suka ja shi ajiki, kafin tafiyar sojojin sai da dr laura ta nemi izni akan tana so abata dama ta ɗauki Yaran zuwa gidanta na tsawon kwana uku, saboda tana so gobe zata kai su saloon agyara masu jikinsu da sumar kansu, sannan tana so zata siya masu suturar da zasu sanya, sojojin basu amince da buƙatarta ba, saboda chief na Isod Ya hana a fita da yaran ko’ina, yace kada a kuskura a fitarsu daga asibiti sai Airport idan zasu tafi, Sun bata haƙuri akan ƙin amincewa da buƙatarta sun kuma nuna mata illar yin hakan tun da su Yaran suna hasashen cutar da su akayi kuma dole asamu masu bibiyarsu, ba dan taso ba ta haƙura, sai dai kamar yarda tace zata siya masu suturar sanyawa tayi ƙoƙarin yin hakan duk da Commender yace kada ta wahalar da kanta, Chief na isod Ya ɗauki ɗawainiyar yaran duk wani abu da zasu buƙata a duniyar nan shi zaiyi masu, dr laura tace taji amma dole ta siya masu wani abun da zasu dinga tunawa da ita akai akai, commender yace mata ba damuwa, bayan tafiyar sojojin, tsabar farin Ciki awurin Angel kamar zata zuba ruwa ƙasa tasha, dr laura ce ta faɗa masu komai dangane da tafiyarsu Nigeria, da kuma damƙa case ɗinsu a hannun Chief of Isod, daren ranar da aka faɗa masu ko bacci bata yi ba, kwana tayi tana yin Nafilfili, har sai da idanuwanta suka kumbura saboda hawayen dake fita acikinsu, ƙafafuwanta suka fara yi mata zogin azaba, tukunna ta dakata dayin sallar asaman prayer mat bacci ya ɗauke ta. Tsawon kwana Biyu Kacal, a tsakani Shugaban Isod, Ya shigo birnin San Antonio Texas, Ya kama Yau kenan Monday, Kuma A yau din zasu Bar America, Da zarar ya fito daga meeting din da suka shiga ahead quarter tare da Chief of army staff, da commender da sauran sojojin dake da alhaki akan Tsintar Yaran A daji, tattaunawa ce ta musamman da zata dauki tsawon awa nni suna Yinta. *UNAISERH ANGEL💋* Mutuniyar tun da ta farka, bakinta awashe kamar wadda akayima Albishir da gidan Aljanna, sai faman zarya take Yi a ɗakin ta kasa zama, jefi jefi ta kan wurga eye balls dinta kan wall clock dake a ɗakin don ganin lokaci idan yana tafiya, ta ƙosa su kammala meeting din azo a ɗauke su, don ita a takure take da zama america. Ta zuba hannayenta biyu acikin aljihun wandonta, bakomai take tunawa ba face Aunty Aneelerh da daddynta, ta sanyawa ranta cewa idan suka koma Nigeria, zata ganshi a gidansu. Zame hannayenta tayi daga cikin aljihun wandonta, ta goya su saman ƙirjinta, abun nayine. “Masoyiya Angel,” muryar dr Laura ce ta fargar da ita ga kallonta, har batasan lokacin da ta furta”Sun gama meeting din”? Fuskar dr Laura dauke da murmushi ta ƙaraso ciki, hannunta ruƙe da ƙatuwar shopping bag. A gefen gado ta ɗaura jakar kayan, tare da miƙa hannu ta rungumo Angel a jikinta. “Zanyi missing dinki masoyiya Angel, sai dai na lura kamar ke ba za kiyi kewata ba ko”? Ta fada tana raba jikinta daga na Angel. Duƙar dakai Angel tayi cikin jin kunyarta tace”Idan nace bazan yi missing dinki ba, Nayi ƙarya, ba ma ke kaɗai ba, duka nurses da likitocin da suka taimaka mana wurin samun lafiyarmu, zamuyi kewarku sosai” Shafa gefen fuskarta dr. laura tayi da tafin hannunta. Cikin karyayyar murya ta furta”masoyiya Angel, saura mintuna ƙalilan suka rage maku a asibitin nan, Ƴan uwanki duk sun shirya cikin sabbin Kayan da na Siya masu, Kema ga naki nan” ta faɗa tana nuna mata jakar kayan data ajiye mata saman mattress. “Sannan akwai Waya dana siya maki, na yi maki Saving phone number dina tare dana Dr brown dana dr mark, da duk numbers na nurses da suka kula da ku, idan kin sanya layi akan wayar ki kira mu pls” Daƙyar ta karasa maganar, idanuwanta sun cicciko tab da ƙwalla, Jikin Angel duk yai sanyi, zuciyarta ta karaya. Cikin murya tamkar tame Yin raɗa, dr laura taci gaba da cewa”Abu ɗaya da ban faɗa maku ba, dama na yanke shawarar Sai mun ke6e dake in sanar da ke, saboda Na yaba da hankalin ki da kuma kaifin basirarki da wayon ki,’ Angel ta natsu tana sauraronta. “Matar da sojoji suka damƙa amanarku a hannunta, Mistress ce,” kai tsaye sunan Ya daki dodon kunnan Angel, cikin rashin fahimtar ma’anar hakan ta maimaita kalmar mistress. Jinjina kai Dr Laura Tayi”tantiriyar ƴar bariki ce mai zaman kanta, shaidaniyace a fagen iya karuwanci, ta shahara sosai, babu wanda baisanta ba, tayi ƙaurin suna a America, maca ce mai haɗarin gaske, Namiji baya Iya ganinta Ya kawar da idonshi, saboda kyawun surar dake gareta, Nayi ƙoƙarin Fahimtar da sojojin Akan illar damƙa amanarku a hannunta amma sunƙi su amince min Angel, ni nasan da wuya ta Iya baku kulawar daya ce, in ma bata gur6ata maku rayuwarku ba, Musamman Ƴan uwanki maza........” Hankalin Angel Ba ƙaramin tashi yai ba, duk da Sanyin A.c na ɗakin zufa ce ke tsastsafo mata saman goshinta, idanuwanta azazzare take kallon fuskar dr Laura dake kora mata jawabi. “Ni damuwata depression din dake damunku, da kuma ɗan uwanku mai fama da ciwon zuciya, idan har aka cigaba da ƙuntata maku zaku Iya rasa rayukanku, shiyasa banso suka damƙa amanarku a hannun karuwa ba, donni a sanina da matar masifaffiyace tana da girman kai, bata ta6a yin aure ba, kuma bata san ciwon haihuwa ba, abunda ta sani shine ƙwacewa matan aure mazajensu tayi fasiƙanci da su, matar ta zama tamkar annoba, ta raba aure da dama saboda hatsabibancinta” dakatawa tayi da yin jawabin idonta akan Angel, tsantsar tashin hankali take gani acikin ƙwayar idonta, Jikin Ta ƙaura Yai la’asar, An gudu ba’a tsira ba. Muryarta Na rawa ta furta”Aunty, amma meyasa suka damƙa amanar mu a hannunta? Babu wata ne sai ita? Kuma ai mu bamu buƙatar wadda zata kula damu, idan ma akwai abunda zamu buƙata bai wuce jami’an da su bamu tsaro ba....” bata ƙarasa maganar ba dr laura ta katse ta da cewa”dalilin dayasa suka damƙa amanarku a hannun ummin america, kamar yarda major ya sanar dani, matar tamkar ma’aikaciyarsu take, ta saba yi masu aiki wurin jan hankalin tantiran ƴan ta’addan da suka gagara a ƙasa, suna yin amfani da ummi wurin ɗana masu tarkon da zasu kamasu, kuma suna cin nasara, Masoyiya Angel ban faɗa maki hakan donna tada maki hankali ba face don ki dage damtse wurin Yin yaƙi da ita akan ƴan uwanki, kada ki kuskura ki bari ta ke6e da ɗaya daga cikin Samarin dake a jikinku, Idan ba haka ba za’a Iya samun matsala, saboda bata da linzami matar, duk da A yanzu ina kyautata mata zo, tun da har sojojin suka aminta da ita suka damƙa mata amanar ku, hakan na nufin sun san zata Iya ne, Bayan haka sun ƙulla yarjejeniya da ita akan baku kula ta musamman da kuma gujewa duk wani abu da zai 6ata maku rai, kamar yarda na gani dai dai da tsawa tayi maku babban laifine, don haka Zan tura maki sharuddan da sojojin suka gindaya mata akanku ta whatsapp, saboda inaso kiyi amfani da su wurin ja mata kunne idan ta sa6a maku,” jinjina kai Angel tayi alamar toh ta ƙara da cewa “bansan da wasu kalmomi zanyi amfani ba wurin yi maki godiya, Allah ne kaɗai zai Iya biyanki, saboda kyautatawar da kukayi mana, gashi kun ɗauke mu tamkar ƴaƴan ku, “ Shafa sumar kanta dr Laura tayi”Kada ki damu yana daga cikin aikin mu!, Yanzu ki shiga kiyi wanka, Mintuna ƙalilan suka rage maku,” amsa mata tayi da toh, Bayan fitar dr Laura, Angel ta nufi Jakar Kayan, zuciyarta a hautsine ta girgiza da jin wacece matar da aka damƙa ma amanarsu, ita babban abunda ta ke jima fargaba garkuwarsu, tunawa da lokacin da aka kawo masu unaiza a kurkuku, yarinyar ta ruɗe shi da big boobs dinta, balle kuma matar da taji ance tana tafiya da imanin namiji saboda dirin jikinta, tashin hankalin da ba’a sanya mashi date. (🤣) Har ta fara Imagining abun da zai faru, a gidan da zasu zaune atare da ita, tayi tunanin sun samu sauƙine komawarsu Nigeria ashe akwai sauran rina akaba. A hankali ta ruko hannun jakar Kayan, ta zaro kayan dake acikinta, wata haɗaɗɗiyar A-line gown ce launin red colour mai round neck ƴar ubansu awurin haɗuwa, Rigar tayi mata kyau a ido, sai faman jujjuyata take yi, aranta tana ayyana yau wata rana zata sanya kaya na mutunci wanda ba uniform din prison ba, wannan abun farin ciki ne agare ta. Bayan ta gama kallon rigar, ta ɗaurata saman mattress, ta zaro kwalin takalman dake a cikin jakar tare da kwalin sabuwar wayar da dr laura ta siya mata, ƙirar iphone 15 pro, Takalman kuma Ankle strap ne masu tsini launin black, hada face mask da mayafi aka basu wanda bakowa bane Ya tsara hakan face chief na Isod, Lokacin da dr laura ta bukaci zata siya masu kaya Sai da aka nemi izininshi, yace ya amince bisa sharaɗin idan zasu sanya kayan a haɗa masu da Niƙab ko face mask da zasu rufe fuskokinsu, a ƙalla ta shafe tsawon mintuna biyar tana kallon kayan, bakomai yafi burgeta ba face wayar da aka bata kyauta, tunawa da lokaci yasa tayi saurin nufar toilet ta shige ciki, shaf shaf tayi wanka kafin fitowarta, Nurse jessica ta shigo ɗakin hannunta ruƙe da gift kit ƙaramin akwati na kayan shafa, ta ɗaura shi gefen gadon Angel, ta zauna saman kujera tana Jiran fiowarta, bayan ta fito daga wankan, suka gaisa da nurse din cikin girmamawa, daga bisani tayi mata bayani game da care kit din data kawo mata donta gyara jikinta, godiya Angel tayi mata bayan ta ɗauki kayan shafar da rigar ta juya ta nufi toilet dasu saboda jin kunyar kada aganta tana sanya kaya, murmushi nurse jessica tayi yayin da take binta da kallo. Bayan ta shafe ko’ina na jikinta da body oil mai tsadar gaske, skin dinta har glowing take yi, rigar tayi bala’en yi mata kyau, duk da bata da jiki tana da tsawo, white in red abun ba’a magana, lokacin da ta fito daga cikin toilet ɗin, ita kanta nurse din sai santin kyan Angel take Yi, daga saman rigar ta tsuke daga ƙasanta bazace daga ta jujjuya rigar take bubbuɗewa kamar ana hura mata iska, bayan ta kammala shiryawa nurse ta feshe mata jikinta da turaren desired destiny, fragrance din turaren mai daɗin shaƙa a hanci. Face mask din da ta sanya black colour ne launin takalmanta, har saman karan hancinta mask din ya haura, Gray eyes dinta ne kaɗai suka Bayyana. Ɗaura Mayafin rigar tayi asaman kanta tayi rolling dinsa, gyalen yana da tsayi ba laifi, Har saman gwiwar hannayenta yakai mata, shima launin takalmanta ne. “Kin yi kyau masoyiya Angel, sai ki ka yi mini kama da Cinderella saboda rashin ƙibarki,” Ƙayataccen murmushine kwance saman fuskarta, “Na lura kin ƙosa ki bar ƙasar nan, Ni kuma gashi bana son ki tafi, saboda na saba da ke masoyiya Angel,” cikin sanyin murya Nurse jessy tayi maganar tana duban fuskarta. “Dr. laura ta bani kyautar waya, kuma ta faɗa min akwai phone numbers din ku aciki, zan dinga kiranku akai akai muna gaisawa saboda ni kaina bana son mu rabu don ya zamar mana dole ne mu tafi” Sai da tayi maganar Nurse jessica ta wurga eye balls dinta kan kwalin wayar, zaro ido ta ɗanyi haɗi da cewa”wow, gaskiya dr. Laura tana Ji da ke shalelenta, wannan waya haka mai kyau da tsada, Ina taya ki murna masoyiya Angel, Kuma naji dadi da ta baki wayar, Kinga zamu dinga kiran juna muna gaisawa, harma muyi video call” fuskarta dauke da matsanancin farin ciki, ta nufi gefen gadon ta ɗauki kwalin wayar a hannunta, tana ƙare mashi kallo, Angel dai sai murmushi take saki, bakinta yaƙi rufuwa kamar ta fasa ihu Haka take ji tsabar murnar yau zasu Bar america zuwa ƙasarta ta gado. “Yakamata mu tafi masoyiya Angel, Ƴan uwanki suna Jiranki a waje” cike da ƙagara Angel ta amsa mata da toh, shaf shaf ta zura takalman a ƙafarta masha Allah, wankan Angel yabi jiki. A hannu ta ruƙe wayar bayan ta curo ta daga kwalin, atare suka fito daga ɗakin. Tun kafin ta ɗago da idonta, Muryar Jemimah ta katse mata hanzarinta”Genie gamu nan ki dube mu da kyau, mun yi kyau” Da sauri ta wurga idonta kansu, masha Allah har saida gabanta Ya faɗi tsabar kiɗima da ganin Kyawun da suka Yi acikin sabbin kayansu, jemimah da azeeza launin gown dinsu Royal blue ne, hannah da parveen launin punch pink, Ita kuma Batul launi ɗayane dana Angel, red colour, kowaccensu akwai Face mask a fuskarta, Anyi masu rolling Veil a saman kawunansu, takalman kafarsu flat ne ba kalar nata ba, ɗaya bayan ɗaya take binsu da kallon mamakin Kyawun da suka Yi, mutun ɗaya ne ke babu a cikinsu, Mazan su huɗune, kowannansu ya kimtsa cikin shiga ta mutunci ta kece raini wato shigar hadaddun Slim fit suit, sun manna mask a fuskokinsu, kwantacciyar sumar kawunansu ta kwanta luf, ƙafafuwansu na sanye cikin tsadaddun takalman fata, ta ko’ina ƙamshin turarensu ne ya karaɗe ward din da suke. Ganin tayi tsaye tana kallonsu bata motsa ba, yasa kowan nan su sanya hannu a lokaci ɗaya suka Zame mask din dake a saman fuskokin su, sai faman washe mata baki suke yi, wani irin farin ciki ne Mara misaltuwa ya kamata, tun daga kan yadda suke shaƙar iskar ƴan ci zaka tabbatar da kwanciyar hankali da natsuwa atattare da su, su kansu sun yaba da kyawunsu, sai faman shafa kayan jikinsu suke Kamar zasu lashesu. Jemimah ce ta ruƙo hannun Azeeza suka watso da gudu zuwa gabanta, Atare suka fada saman jikinta, Hugging dinta su ka yi suna tiƙar dariyar murna, tuni idanuwanta suka cicciko tab da ƙwalla, ko a mafarki bata ta6a tsammanin zata ga wannan ranar ba, yau gata ga ƴan uwanta cikin shiga ta alfarma ba uniform din kurkuku ƙaddara ba. A hankali Batul da sauran ƴan uwan nasu suka nufo wurin Angel, ɗaya bayan daya take rungumo su saman chest dinta, suna matuƙar ƙaunar junansu, nurses da likitocin dake tsaitsaye cirko curko sai kallonsu suke yi gwanin ban sha’awa. “Angel, Kinga yadda ki kayi kyau? Rigar nan tayi maki kyau, wlh duk munyi kyau,” Batul ce tayi maganar tana shafa gaban rigarta da hannunta. “Nayi tunanin abinci kaɗaine abu mafi kyau a duniyar nan, ashe sutura ma abu ne mai ƙayatarwa, gaskiya bazan iya misalta farin cikin da nake a ciki ba, Daɗi Nake ji kamar In buga tsalle sama in dira ƙasa,” Parveen ce tayi maganar, sautin dariyarsu yacika ko’ina, kasancewar suna Yin firar cikin harshen hausa babu wanda ya fahimci abunda suke tattaunawa a tsakaninsu, sai dai Abi la66ansu da kallo. “Ban ta6a ganin kalar kayan nan ba, Mun saba da Uniform kala daya na prison, Yau sai gashi mun tsinci kanmu acikin sutura mai kyan gaske, godiya ta tabbata ga Allah, domin kuwa shine silar komai, dama kin ta6a fada mana cewa mahaƙurci mawadaci, sannan duk tsanani Yana tare da sauƙi, kuma babu yanayi na rayuwa da yake kasancewa Na dundundun, Yau mun shaida hakan Angel” tun da Haris Ya fara magana Suka natsu suna kallonshi, tamkar ba mara lafiyan nan ba, Jikinshi Yayi kyau ɗan black beauty da shi, Kalamanshi sun tunama Angel deeja, Yarinyar akwai tawakkali duk da bata da zurfin ilmin addinin musulci tayi imani da Allah, fiye da wani musulmin daya taso acikin musulunci, tunawa da deeja ne yasa ƙwallar idonta suka soma gangarowa saman kuncinta, a fakaice ta sanya hannu ta share su, haƙiƙa taji zafin mutuwarsu, ga salsabeel daya tsaya mata aranta, bawan Allah ko awani hali yake ayanzu? Ya rayu ko ya mutu? Allah masani!. “Angel, Ina fata Yanzu hankalinki ya kwanta, babu sauran damuwa tun da yau zamu koma Nigeria” Gabriel ne yai mata maganar Haɗi da ɗaga mata gira ɗaya, hakan ba ƙaramin dariya yaso ya bata ba, Javed yace”ni fa duk atakure nake jin kaina, mutanan nan sai kallon mu suke Yi,” Naufal Yace”ka gode ma Allah tun da ba Giants din kurkukun ƙaddara bane suke kallon ka,” gaba daya suka sanya dariya cikin nishaɗi. Gabriel yace “kyau suke kallo, wankan da muka ɗauka ne Ya burgesu, mu kanmu mun burge kanmu balle kuma su” Hanna tace”Wannan abun da aka sanya mana a fuska yafi komai 6ata min rai, Duk ya toshe mun ƙofofin hancina, wai ba yadda za’ai mu tafi batare da mun sanya shi ba”? Tana faman yamutsa fuska tayi tambayar tana kallon Fuskar Angel. Kafin tayi yunƙurin bata amsa Gabriel ya riga ta cewa”saboda tsaro, shiyasa aka bamu shi don mu sanya, sunanshi face mask,” Javed Yace”ai na gane shi, kalar wanda tsohuwa zafreen take sanyawa ne” harara parveen ta ɗan jefa mashi”Ni bana so kuna maganar matar nan, na tsaneta kamar mutuwa ta” “Ina danish yake ne? Shi bai fito ba ne”? Angel tayi tambayar tana leƙen ƙofar room dinsa. Haris yace”Suna can ɗakin shi suna ta fama dashi akan ya sanya kayanshi yaƙiya, kinsan mutumin da taurin kai kamar ƙashin nama, bansan Ya suka ƙare da shi ba, Har lalla6a shi nayi na nuna mashi kayan dake a jikina amma yasa kafiya akan bazai sanya ba” Mai hali bazai ta6a canzawa ba, aranta ta ayyana hakan, Kallon su azeeza tayi”our twins ku sakar min rigata, zanje ɗakin danish” Azeeza tace”toh, mu tafi atare zamu biki” Ruƙo hannayensu tayi a cikin nata, suka nufi ɗakin Danish, Su Haris ma suka bi Bayansu, har sun kusa shiga Muryar dr laura ta katse masu hanzarinsu. Cikin harshen turanci take yi masu magana “Duk inda na kalla kyawawan ƴan mata ne da samari nake gani, kunyi kyau sosai, Kamar in sace ku” gaba ɗaya suka sanya dariya, Miƙa ma Haris hannu tayi”zonan My baby boy, Ya jikin naka”? Zuwa yai gabanta ta sanya hannu biyu ta rungume shi a ƙirjinta kamar yaron cikinta “Allah ya ƙara maka lafiya Haris, zamu yi kewarku sosai, Ku kula mana da kanku, zamu dinga kira akai akai don mu gaisa da ku” cikin karyayyar murya ta ƙare maganar, tare da raba shi daga jikinta, idanuwansu duk sun ciko da ƙwalla. Voice dinshi na rawa ya furta”mun gode sosai da kulawarku agare mu, Kune mutune na farko da kuka fara jan mu a jiki kuka bamu kulawa ta musamman, akanku muka fara yarda cewa akwai mutanan kirki a duniya ba duka aka taru aka zama ɗaya ba” murmushi tasakar mashi tare da kai hannu ta shafa sumar kanshi”nayi magana da Angel, Nasan zata baka kulawar daya dace, duk wani abu da kakeso kayi mata magana” amsa mata yai da toh. Angel da su jemimah duk suna a tsaye da sauran nurses da doctors dake kallonsu. Miƙa ma Su hannu tayi”ku zonan my twins, Inason jin ɗuminku a jikina, gaskiya zanyi kewarku” da sauri jemimah da Azeeza suka isa gareta hannu biyu ta sanya ta rungume su tighly. Bayan ta raba jikinta daga nasu ta kalli parveen da zolaya tace “Oh, Ji ra kike saina ce kizo ki rungumeni? Ko dan baki ga abinci a hannu na ba”? Tuntsirewa su ka yi da dariya gaba ɗayansu da gudu parveen ta ƙarasa ta rungumeta, shafa kanta dr laura tayi’ki kula mun da kanki, a duk lokacin da kika ji yunwa, kiyi ma Angel magana zata baki abinci, kada ki zauna da yunwa” lumshe ido parveen tayi ji take kamar karsu rabu da juna, don ba ƙaramun so suke Yima matar ba. “Pure heart, my beautiful daughter zo ki rungume mommynki” ta faɗa tana kallon Batul, da ɗan sauri ta je gabanta ta faɗa saman chest dinta sosai ta rungumeta. “Ki kula mun da kanki, Allah ya tsare mun ku, zanyi kewarku” Batul tace”muma zamuyi kewarku, idan muka samu dama zamu dinga zuwa muna ganin ku,”dr laura tace”kada ki damu basai kunzo ba, muma zamu Iya zuwa dubaku har ƙasar taku” Batul taji dadin kalamanta, ɗaya bayan ɗaya sai da tabisu ta rungumesu tana mai ƙara jaddada masu akan su kula dakan su. Lokacin da tazo kan Angel, Har ta miƙa hannu zata rungumota, Ba zato ba tsammani Garkuwa Ya fito daga room dinsa, adai dai lokacin Jami’an Isod sun shigo ward din, Cikin shiga ta black suits, Hannayensu da ƙafafuwansu sanye cikin baƙaƙen safuna, takalman ƙafarsu leather shoes ne fuskokinsu duk sun sanya face mask, ƙirar su bata da banbanci data jami’an kurkukun ƙaddara, Giants ne wani irin faffaɗan kirjine dasu, na ban mamaki, suna tafiya cikin taku na ƙasaita, kai daga ganinsu zaka shaida ƙarfin da suke dashi damtsen hannunsu tamkar zai fasa rigar jikinsu a murmurɗe suke, azafafe suke yin takunsu tamkar zakuna, Suna tafiya tsokokin jikinsu na motsawa da ƙaƙƙarfan kuzari na majiya ƙarfi. Lokaci ɗaya ward din Yai tsit tamkar mutuwa ta gifta, bakomai ne Ya jawo hakan ba face fitowar Danish daga room dinsa, tare da dr brown da dr. Mark jackson, Tabarakallahu ahsanul khalikin, ko a mafarki basu ta6a yin tozali da mutumin da sutura ta raina kanta a jikinsa ba irin Danish ! Wankan daya ɗauka na slim fit suit dinsa sunyi bala’en yi mashi kyau, ya fito a garkuwarsa, Garzon namiji mai jini ajika, sannan kuma mai ji da kyau da ƙarfi, haɗaɗdar sumar kanshi dark brown curly sun gyara mashi ita, sunyi cutting dinta sun ɗaure mashi ita, ta sauko saman dogon wuyan shi, takalman ƙafarsa leather shoe ne launin black suit dinsa. Fuskarshi tamkar anyi mashi make up tsabar haɗuwa, ga wani irin zazzafan ƙamshin turare dake kurɗaɗowa saƙo da lungu na jikinsa kamar wanda aka tsamo daga cikin kogon turare, Agogon hannunsa silver ce sai ɗaukar ido take Yi, wani abu da zai baka mamaki duk irin haɗuwar da yai acikin kayan babu annuri akan fuskarshi ko misƙala zarratin Ya haɗe rai kamar wanda aka ɗaura ma aure da mutuwa, Yana tafiya a bubbuɗe kamar wanda zai Yi dambe, Kyawun surar danish yayi matuƙar tafiya da Imanin Nurses din dake a kewaye da wurin da likitoci, all eyes on him ba matan ba mazan ba, kowa kallonshi yake yi kamar zasu haɗiye shi, kai hatta Jami’an isod sai da gabansu ya faɗi sunyi matuƙar girgiza da ganin shi, har dai wani daga cikin su ya gaza jurewa muryarshi ƙasa ƙasa cikin harshen turanci Ya furta”Nayi tsammanin daga Chief din mu angama halittar Namiji mai kyan fuska da sura, ashe ba haka bane nayi kuskure, a yau naci karo da namijin duniya kamar garzonmu OWAIS, wannan Yaron Bai da mararraba da shi, banbancinsu Launin fata” *💋ABBAN SOJOJI💋* *💋KURKUKUN ƘADDARA💋* *Assalamu alaikum, fatan mun wuni lpy, ga masu son abban sojoji complete 400 da kuma kurkukun ƙaddara wanda nake cikin rubutawa, ga number da zasuyi mini magana da ita, new number ce wadda nake da ita me 08103884440 whatsapp din ya samu matsala, ga wadda za’a same ni da ita (08134387050) ayi mini magana ta whatsapp, message from Boss Bature* *✍️ Mu haɗu Gobe In sha Allah Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya, Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*_ ~Middle step~ سجن القدر❤🤍❤ _THE PRISONERS E25🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* Confusion of the heart💫 Jami’in dake gefen wanda yai maganar ne ya daura da cewa”Ni kaina na girgiza da ganin matashin saurayin nan, Gaba ɗaya ma na rikice, na tabbata ko shi Boss Owais din Yai arba da wannan Yaron sai yayi mamakin shi. Amenity Ward Ya ruɗe da sambatun mutane akan kyawun Garkuwa, shi ko Dan tahalikin Duk yabi ya rikice A rayuwarshi ya tsani kallo saboda Yana affecting din natsuwarsa, Yana Hayaƙa shi, idanuwanshi sun makance neman Angel Yake yi, Gata akusa dashi amma ya kasa ganewa, sai ƴan waige waige yake yi a ƙoƙarinsa naya gano ta, An rasa me Iya buɗe baki yayi mashi magana acikin ƴan uwan nashi, baisan cewa shine ya ruɗe su ba, Ya canza masu sosai cikin sabuwar shigarshi. Sai da Haris Ya ɗaga murya Ya furta”Danish gamu anan” tukunna ya wurga reddish eye balls dinsa akan fuskokinsu, cikin takun sauri Ya nufe su yana ƙarasawa ba yi ƙasa a gwiwa ba Ya rungume Angel a saman broad chest dinsa, Ya cusa fuskarshi saman kafaɗarta Yana faman sauke ajiyar zuciya, lumshe idanuwanta tayi lokacin da ƙamshin turarensa Ya daki hancinta, gaba ɗaya taji ta a wata duniya tacan sama jannati, in a throaty voice ya furta mata”bana son kallo, Ki faɗa masu su daina kallo na, suna cutar dani” Sam takasa yin magana, saboda yayi tighting dinta a kirjinshi, ya zagayo da arms dinsa saman bayanta, mutanan dake awurin sai faman sakin murmushi suke yi kamar zautattu, bakomai ne ya burgesu ba face hugging din da Danish yai ma Angel, sunyi tamkar ma’aurata, kayan jikinsu sun yi fitting dinsu black and red, kamar furanni. Gyaran Murya ɗaya daga cikin Jami’an isod Yai masu, muryarshi a bubbuɗe ya furta”Zamu Iya tafiya, amma kafin nan Shi wannan Yaron Ina face mask dinsa Yake”? Ya yi tambayar Yana nuna Danish da indext finger. Da sauri Dr Mark, ya tura hannu cikin front pocket din coat dinsa, Ya zaro face mask, Ya nufi Danish, yana fadin “Handsome man, namanta ban sanya maka mask dinka ba, Kar6i ka sanya” kamar yayi magana da gunki, Ko motsi Baiyi ba, tunda ya ƙanƙame Angel dinsa yayi shiru kamar maiyin bacci. Numfasawa dr laura tayi sai lokacin ta samu damar buɗe baki tace”Danish yana yi maka magana, kaga sauran ƴan uwanka duk sun sanya nasu face mask din, Kaima ya kamata ka kar6a ka sanya, jami’an isod suna jiran ku zasu ɗauke ku zuwa Airport ne” Lamarin Ya ɗaure masu kai, Babu alamun zai motsa, Ga Angel tana so ta raba jikinta daga nashi don ta lallashe shi, yaƙi bari tayi hakan saboda matsetan da yayi a chest dinsa, hatta numfashinta daƙyar take Iya fitar dashi” Cikin ƙagara Haris Yace”dan Allah Danish ka sake ta, Ka kar6i abun fuskar kai ma ka sanya ko mun samu mu tafi” Magiya suka dinga yi mashi akan ya saki Angel Amma Yaƙiya ko kallo basu ishe shi ba” Ɗaya daga Cikin Jami’an Isod Ne yai nazari akan Yaron, kasancewar suna da kaifin basira, nan take Ya fahimci wani abu dangane da shi, ɗaya bayan ɗaya ya kalli nurses din dake a ward din da likitocin da suka tsaya suna kallon su, Muryarshi a kausashe Ya furta”Idan ba damuwa kowa Ya koma bakin aikinsa”! Jin hakan yasa kowan nan su Juyawa suna tafiya suna waiwayon prisoners, Mutun Biyar ne suka rage, dr laura da mark da brown sai nurse jessica da nurse rebecca. Tun kafin Jami’in Ya tambayi lafiya su basu tafi ba? Dr laura tace”Muna so muyi masu rakiya har zuwa airport, nasan suma Yaran zasu so hakan” Jinjina kai yai tare da ɗaura eye balls dinsa kan Bayan Danish. “Danish, likitocin da suka duba lafiyar ku ne su ka rage sai kuma mu jam’an da muka zo domin tafiya da ku, babu kowa bayan mu, muna jiranka please kada ka 6ata mana lokaci”! Cikin kwantar da murya yai mashi magana. Sai da Ya ambaci hakan tukunna daƙyar Ya raba jikinshi daga na Angel, numfashinta da sauri sauri Yake fita, hada tarinta saboda mugun shaƙar da tayima turarensa ya sarƙeta. Dr mark ne Ya sanya mashi mask din saman fuskarshi, da zolaya jami’in yace”ka tabbatar ka rufe mashi hada idonshi, don wannan idan mutane suna kallon shi tsab zai haɗa mana traffic jam a saman titi” Gaba ɗayan su suka sanya dariya, ban da Danish, sam babu kwanciyar hankali atattare da shi, Hakanan Yake jin haushin mutane babu gaira babu dalili, ji yake kamar ya rufe su da bugu har sai sun mutu. Su Batul kuwa duk sun sha jinin jikin su, ganin Jami’an Isod suke Yi tamkar mutanan prison, tun da suka shigo ko motsin kirki sun gaza yi, Sai faman binsu da ido suke yi, ko magana jami’an su ka yi sai sun razana babu wanda Ya lura da hakan. Bayan Dr. mark ya kammala sanya mashi mask din, ya juya ya ruƙo hannun Angel acikin nashi, a jere suka nufi Hanyar fita daga ward din Yayin da dr laura da mark da brown suke Abayansu, su kuma jami’in Isod suna a kewaye da su, domin basu tsaro, duk inda suka gifta a sibitin ido na akansu, ba marasa lafiyan ba, ba ƴan zuwa dubiyan ba, ba Ma’aikatan cikinsu ba, kowa hankalin shi na akan su, Danish sai ƙara matse mata hannunta yake yi a cikin nashi, hankalin ta ba akwance ya ke ba don ta fahimci akwai wani abu dake damun shi. Kaitsaye suka nufi parking space na asibitin, wasu danƙara danƙaran motoci ne masu numfashi jigunannun gaske, a killace a harabar, da su akazo ɗaukarsu, hankalin su Batul Ba ƙaramin tashi yai ba, Basu ta6a ganin abu irin wannan ba, Motocin dake a killace aharabar suke ta faman bi da ido, Angel ce tayi amfani da harshen hausa wurin yi masu magana akan su natsu kada su tsorata, abun hawa ne da akeyin anfani dasu wurin tafiya mai tsayi wadda ƙafa bazata Iya yinta ba, sai da tayi masu bayani cikin kwantar da murya tukunna suka fara sakin jikinsu. Kafin su shiga motar sai da aka fara sanya kayan su a boot, akwatuna ne da duffle bags kusan guda biyar, Suturar da dr laura ta siya masu ce, tare da Takalmansu da magungunan da zasu dinga sha, da sauran care product da zasu yi amfani da su. Bayan an kammala shigar da kayan cikin motocin ɗaya bayan ɗaya jami’an suka bude masu car doors din, motar farko Danish ne da Angel sai Batul suka zauna a mazaunin Baya, Mota ta biyu Gabriel ne tare da Haris da Hanna, Mota ta uku Naufal ne da parveen sai Javed. Dr. laura ta nemi alfarmar jami’an akan tana son su bata damar ɗaukar jemimah da Azeeza a motarta, Jami’an suka ce mata zata Iya ɗaukarsu ba wani abu, A back seat na motarta, Azeeza da Jemimah suka shiga, Ita kuma ta zauna A driver seat domin Yin driving dinsu, Dr mark da dr bown suma hada su za a tafi kaisu airpot din, A cikin motocinsu zasu tafi tare da Nurse jessica da rebecca. Tun da prisoners suka shiga cikin mota, suke ta ƴan kalle kalle wa yaga baƙauye yazo birni, duk sun sha jinin jikinsu, Fargaba suke Yi kada a cutar dasu, badan Angel ta kwantar masu da hankalinsu ba, da kuwa Anga hauka, kusan A lokaci ɗaya masu tuƙa motocin suka tada su, Jemimah ta rungume Azeeza jin sautin tashin motarsu, Jikin su ya hau yin kerma kamar waɗanda sanyi ya kama, Dr laura dake kallonsu ta madubin motar, fuskarta ɗauke da murmushi ganin yadda suka ƙanƙame tace masu su kwantar da hankalin su, babu abunda zai same su. A motar su Parveen Ta ƙanƙame naufal saboda tsoron da taji, hada javed sun haɗu sun mannewa juna kamar kifayen gwangwani. A motar su Gabriel kuwa, Hannah da Haris sun ƙanƙame shi, sai faman tiƙar dariya yake yi, shi dama wayayye ne bakomai ne Ya manta na memory dinsa ba, Hannayen shi biyu ya sanya saman bayansu Ya ƙara tighting dinsu ajikinshi yana kwantar masu da hankalinsu. Danish kuwa tun da suka shiga motar, ya kwantar da kanshi saman kafaɗar Angel, ko motsi baiyi, Yana zaunea left hand dinta, yayin da Batul take a zaune saman seat din dake a right hand dinta, Ganin yadda Batul ta ruɗe jin tashin mota, Hannayenta biyu ta ɗaura saman kanta, kamar zata fasa ihu da sauri Angel ta damƙo hannunta tare kwantar mata da kanta saman laps dinta, ƙanƙameta tayi sosai tana faman sauke ajiyar zuciya, abun ne yazo masu wani iri basu saba ba. Slowly motocin suka nufi hanyar babban gate din asibitin, gaba da bayansu motocin Jami’an isod ne, Sun sanya motocin da aka ɗauko su dana su dr. laura a tsakiyar nasu motocin domin basu tsaro. Da matsakaicin gudu motocin suka haura saman titi, prisoners sun ga abunda yafi ƙarfin idanuwansu, Ta glass din window su ke Hangen danƙara danƙara gine ginen birnin san antoni, masu ƙayatarwa, ga wuraren shaƙawata da kuma mutanan dake zarya ta ko’ina, sun natsu suna kallon ikon Allah abun ya ɗaure masu kai. “My man, bacci zaka yi”? angel ce tayi mashi magana tana duban fuskarshi, tayi mamakin ganin zufa na tsastsafo mashi saman forehead dinsa, duk da sanyayyan Sanyin A.c na motar, Batool tuni ta miƙe daga saman laps din Angel, ta koma bakin windown motar tana kallon Ikon Allah. In a low voice ya furta mata”Am not feeling well, ina jin wani iri a jikina kamar wani abu zai faru dani” shafa sumar kanshi tayi da hannunta”In sha Allah ba abunda zai faru da kai My Man, Ina atare dakai, so ka kwantar da hankalin ka, bari nayi maka addu’a” ta faɗa haɗi da manna la66anta saman lallausar sumar kanshi, addu’o’i ta soma karantowa tana tottafa mashi asaman kanshi. Muryar Batul ce ta katse mata hanzarinta”Angel wai su mutanan duniya dama haka suke da gudu kamar zasu tashi sama”? Dariya ce ta kubcewa Angel, ta wurga idonta kan batul data mannewa glass din tagar motar, ta ƙura ido tana kallon al’amurra. “Batul ba mutane bane suke Yin gudu, Abun hawan da muka hau ne ya ke yin gudu damu” Ba tare da batul ta juyo ta kalle ta ba tace”Oh, yanzu na fahimta” daga haka bata ƙara cewa komai ba. *UMMIN AMERICA💋* A hankali motar su take tafiya saman shantalelen titi, tana a zaune saman front seat, ta ɗauki wankan pant suit sunyi bala’en yi mata kyau, dogon wandone fari da sexy vest fara ta matse ta kirjinta Ya fito sosai, don ma ta ɗaura Blue coat daga sama, ta canza launin sumar kanta zuwa blue, light make up ne asaman face dinta , fararen idanuwanta suna a manne da farin glass hakan ba ƙaramin ƙara mata kyau ba, Matar dake driving dinta, ƙawarta ce *NATASHA* baturiyar England, Aminnan junane, sai dai daga ganinta babu digon imani a zuciyarta, fitsararrace ta bugawa a jariga. Kayan dake a jikinta da su da babu duk ɗayane, doguwar rigarta tamkar net take shara shara kana Iya hangen inners din ta, A yayin da take zaune saman driver’s seat, Cigrette ce a hannunta na hagu, ɗayan hannun kuma da shi take juya sitiyarin motar daga gani ta ƙware a iya driving, Tsabar Iya shan taba harta hanci ta baki take huro hayakinta. fira suke ɗan ta6awa a tsakaninsu cikin harshen turanci. “Zanyi kewarki ummi, yanzu idan kika tafi yaushe zaki dawo? Natasha ce ta jefa mata tambayar. Numfasawa tayi kafin calmy ta furta “bazan daɗe ba, temporary guardianship ne ba permanent ba, da zarar na kammala yi masu aiki zan dawo America” Dariyar shaƙiyanci Natasha ta saki, tana mai cigaba da hura hayakin tabarta. “idan ki ka yi wata ɗaya baki dawo ba, zan biyoki Nigeria don bazan Iya jure rashin ki ba” ta fada tana duban fuskar Ummi. “Zaki tafi ki barni da mutananki, don nasan ba zasu ƙyaleni ba, da zarar sunji ki shiru ni zasu tuntu6a,” Ummi tace”Zaifi ki canza layin wayar ki, kafin in dawo, don bana so kowa yasan da zancen barina ƙasar nan ko kuma inda zanje, Yana daga cikin sharuɗɗan da sojoji suka gindaya mini.” “Ai nayi mamaki da kika amince zaki kar6i jagorancin kula da yara har goma sha ɗaya, idan nice bazan Iya ba, kema nasan ba hakanan kika kar6i aikin ba. akwai wata manufa a ƙasa” ta ƙare maganar tana dariya. Ummi tace”kamar kin shiga zuciyata, tabbas inaso naje Nigeria ne don karan kaina bawai don aikin da sojoji suka bani ba, nima akwai abun da zai kai ni, da ba don haka babu abun da zai sa in bar America. Natasha tace”yayi kyau mutuniyata, ina fata zaki cigaba da sheƙe ayarki, bana so silar zuwan ki ƙasarki ki shiryu nafison ki ƙara lalacewa ki 6ata masu mazajen auransu,” dariya suka sanya gaba ɗayansu. Ummi tace”Yaran fa da aka bani in jagoranta kyawawane fa akwai wani zazzafan Yaro acikinsu, yana da kyawun sura” lumshe ido natasha tayi muryarta tamkar ta mashayin giya tace”kice yaron babbar harka ne, tun kafin ma in ganshi na ƙyasa” Ummi na dariya tace”yadda kike shaiɗaniyar nan nayi imanin idan kika ganshi daƙyar zaki Iya runtsawa, kallon shi kaɗai zai tada maki da maitarki, Natasha nayi mu’amala da maza kala daban daban amma shi wannan Yaron na musamman ne, Kamar dai Chief Owais, kinsan shima Yana da zazzafar sura. Natasha tace”Har yau ban daina kallon hotonshi ba saboda bana gajiya, aduk lokacin dana rasa abokin harka hoton shi nake kallo in rage zafi, gayen ya haɗu duniyace shi” cikin jin shauƙi Tayi maganar” Ta ƙara da cewa”ƙawata zan baki shawara, matasan Yaran da za’a baki rainon su, kada ki raga masu, idan jarabarki ta motsa kibiya buƙatarki da su, ai ke wannan Aikin da sojoji suka baki gaba ta kai ki, in banda abunsu sun ta6a ganin inda aka ba kura ajiyar nama”? Da shaƙiyanci ta faɗa tana sakin shu’umin murmushi na tantiran ƴan duniya. Ummi ta ɗan zaro ido haɗi da cewa”ba zai yiwu ba natasha, ke kin san wanene Chief owais, yafi bomb bala’i, akan shi na fara jin tsoron namiji a duniyar nan, Mutumin bai da fara’a Yana da kamun kai, sannan bai da imani idan ya damƙi Mara gaskiya, idan har na kuskura na ƙetare Iyakata akan Yaran wlh tsaf zai Iya kasheni har lahira, ni ko dai ban shirya mutuwa ba, akwai sauran bururrukan da nakeson cimmawa. Fashewa Natasha tayi da dariya fararen haƙoranta a jere kamar gonar auduga, sam firar su bata ɗauke mata hankali ga yin driving din da take Yi ba, har ta zuƙe tabar hannun ta duka. “Dole kiyi mini dariya ƴar rainin wayau” ta fada tana hararar ta. Tsagaitawa Natasha tayi da yin dariyar ta dubi fuskar Ummin america”mutuniyata, Kina ta zumuɗin zuwa Nigeria, banji kina maganar mutumin ki ba” cikin rashin fahimtar kalamanta ta furta”Wa? Kashe mata ido ɗaya Natasha tayi”Boss Man, ko kina nufin har kin manta da shi? ta faɗa tana duban hanya. Yamutsa fuska Ummin america tayi”Allah ya raba ni da alaƙaƙai, bana fata wani abu ya ƙara hada ni dashi, jarababbe kawai” Natasha na dariya tace”haba ummi, mutumin fa ya mutu akan ƙaunarki, nayi ƙoƙarin ganin na maye gurbinki acikin zuciyarshi sai dai Ya nuna mun cewa ke kaɗai ce za ki Iya sarrafa shi yadda ki ke so, kuma yana nan akan bakansa na cewa ba zai ta6a barinki ba har abada ke tashi ce” Mood din fuskarta ne ya canza zuwa 6acin rai. “Natasha, I don’t even want to hear his name, bawai don bana son shi ba, kawai ni bana son mutumin da zai nuna ƙarfin iko akaina, kamar wani ubana, yaushe rabona da shi tun lokacin dana ɗauki cikinsa na zubar ba tare da saninshi ba, muka samu sa6ani dashi ban ƙara ganin ƙeyarsa ba, Kin san fa mutumin akwai zuciya ga girman kai, nasan zai neme ni ne tun da baya gajiya dani” Natasha tace”kina wasa da damarki ummi, da Ace nice na samu matsayin da kika samu acikin zuciyarshi, bana tunanin zan iya bijire mashi, biyayya zanyi mashi sau da ƙafa”” Ta6e baki ummi tayi”nima ba gudunshi nake yi ba, Ciki ke bana so, saboda zai 6ata min shape din jikina, kuma ni tun kafin mu ƙulla alaƙa dashi sai da na faɗa mashi sharuɗɗana, nace mashi bana ra’ayin yin aure kuma bana son ciki, ban damuwa ba idan zamu shekara munayin sharholiyarmu da shi in dai zaiyi min biyayya” Murmushin gefe fuska Natasha tasaki”Ummi kenan, Yanzu mu ajiye zacenshi a gefe, ni dai shawarar da zan baki shine idan kika koma ƙasarku, kada ki kuskura ki kula ƙasƙantattun mutanan da su ka yi silar barin ki Nigeria, bana so ki nuna kin san su, inaso ki nuna masu cewa kwandon shara yafi su mahimmanci a awurin ki” Maganar Natasha ta ta6a zuciyarta ummi, tuni ta ɗaure fuskarta, tunawa da wani abu da ya faru a rayuwarta. “Please, stop talking about them, i don’t wanna hear it” rai a6ace ta furta hakan, jinjina kai Natasha tayi”shikenan nadaina mutuniyar saboda bana son 6acin ranki” mood din fuskar Ummi Ya canza sosai, abubuwan da suka faru arayuwarta take tariyowa, masu daɗi da marasa daɗi. “Mutum biyu masu mahimmanci arayuwata, ina fata na sake haɗuwa da su, Yarinyar dana bari inason na ganta duk da bani da tabbacin tana araye ko ta mutu, ba dan bana son ta ba, na tafi na barta, tun tana jaririya, shi kaɗai ne danasanin da zanyi arayuwata” A cikin zuciyarta ta furta hakan ba tare da sautin muryarta ya fita ba, tuni idanuwanta suka cicciko tab da ƙwalla. Afakaice ta zaro hanky daga hand bag dinta ta share ƙwallar idonta. Sun jima suna tattaunawa da ƙawarta Natasha, A lokaci ɗaya motar su, da motocin jami’an da suka ɗauko su Angel suka ƙaraso katafaren Airport din, slowly Ummi ta zuge glass din motar don ta samu damar ƙare ma Yaran kallo ita da Natasha, kafin fitowarsu daga mota, suka soma Jin jiniyar motar sojoji, kusan guda uku suka nufi wurin da sukayi parking din nasu motocin, bayan sunyi parking din motocinsu, Commender ya fito daga motarshi, tare da Major da captain da sauran sojojin da su ka zo da su. kowan nan su yana sanye cikin kakinsa, ga dukkan alamu sunzo Yi masu bankwana ne. Jami’in dake tuƙa motarsu Angel ne ya fito da sauri Ya zagaya Ya buɗe masu kofa, Angel ce ta fito hannunta ruƙe dana Danish, duk da face mask din dake akan fuskokinsu hakan bai 6oye tsantsar kyawun idanuwansu ba, Hankalin Natasha ba ƙaramin tashi yai ba lokacin da idanuwanta su ka yi tozli da kyakkyawar surar Danish, tun kan ummi ta faɗa mata wanene shi tayi saurin cewa”kamar Yaron da kika faɗa min ko”? Ummi na murmushin shaƙiyanci tace”may be shine, ai ni fuskar shi na gani a hoto, naga wannan ya sanya face mask, amma dai ina da tabbacin shi ɗin ne, masha Allah ƙaramin mutum da babbar harka, Ni ma ban ta6a ganin shi ido da ido ba sai yau, Nayi tsammanin jin shi yafi ganinshi, ashe ganin shi yafi jinshi,” lashe baki Natasha tayi da harshenta kamar wata mayya tace”Ya tafi da imanina, Ya za’ai ummi? Anya bazan biyo ku Nigeria ba? Kinga ke sai ki dinga rainon su ni kuma Ina biyan buƙatata da su” Ummi tace”bismillah zaki Iya bin mu amma ki sani komai ya faru dake kada ki nemi ni, Chief owais sai yayi jajjagen namanki, idan kika ta6a mashi ƴa’ƴanshi” Har ta ƙarasa maganar, Natasha batasan me take cewa ba, idonta akan Danish, Bayan fitowarshi da Angel, Batul ta fito, Sauran Jami’an suka fito tare da bubbuɗe masu motocin. Gabriel ya fito tare da Haris da hannah, Naufal ya fito da parveen da javeed, dr laura ta fito daga motarta, ta bude masu Azeeza, suka fito suma, Nurses din dake atare da su da dr mark da brown kowan nan su Ya fito waje. Prisoners sun baza ido suna kallon inda suke, tun kafin su shiga cikin Airport din. Ummi America da natasha sun tsaresu da ido “Yaran Fa akwai kyau, Yanzu ummi har kina Iya zama wuri ɗaya dasu ba tare da kin rage zafi ba”? Shiru ummi tayi mata ba tare data tanka mata ba, hankalinta na akan prisoners, ta ƙura masu ido, hakanan ta dinga jin bugun zuciyarta na ƙaruwa, ba tare da sanin dalilin daya haifar mata da hakan ba, jikinta yai wani irin sanyi, ɗaya bayan ɗaya take bin su da kallo, yayin da suke gaisawa da sojojin cikin raha suke amsa masu. Sai daga bisani Ummin America ta buɗe murfin motarsu, atare suka fito ita da Natasha, Hankalin su Angel Ya dawo kansu, Kallo ɗaya tayi mata sai da gabanta ya faɗi, kuma nan take ta gane wacece ita, tun da taga uban hips dinta da boobs dinta da suka cika ƙirjinta, ranta ya bata cewar tabbas itace matar da aka damƙa ma amanarsu, tun da ta fito hankalin kowa ya dawo kanta, taku ɗaya girgiza goma, wankan suit din jikinta ya tafi da imanin kowa dake awurin. Kallon kallo suka soma bin juna da shi, tsakanin prisoners da ummin america, da kuma dr. Laura, da jami’an isod, da sojojin da suka halarta, sama sama suka soma gaisawa da ita, Dr laura ta haɗe rai kamar yadda itama ummin american ta ɗaure mata fuska, bayan sun gama gaisawa da juna, jami’an suka buɗe boot na motocin da suka zo da su suka ɗauko suitcases dinsu tare da jakunkunan kayansu, gaba ɗayansu suka ɗunguma zuwa cikin departure gate din Airport, ta inda suka samu sauƙi, Jirgin da zai ɗauke su privet jet ne mallakin Jami’an isod, babu buƙatar jira ko wasu shaidu, An riga An shirya masu komai su kawai ake jira domin tafiya, duk inda suka bi darewa akeyi abasu hanya saboda sojojin dake atare da su, prisoners sai ƴan kalle kalle suke Yi, sunga wuri mai kyan gaske ga mutane launi daban daban suna ta yin zarya acikin wurin, Yankin da jirginsu zai tashi fili ne na musamman aka ware shi domin tashi da safkar jirage masu zaman kansu. Tanƙamemen Privet jet ne Aka tanadar masu, Mallakin Chief of isod, Aljannar duniyace ƴar ubansu a wurin haɗuwa, tun daga wajen jirgin zaka fara cin karo da sunan ISOD da aka rubuta da manyan haruffa ajikinsa. Idan ka shiga cikin jirgin kamar ka shiga haɗaɗɗen villa ne saboda haɗuwar kayan alatun dake acikin sa, akwai Falour wanda yaji hadaddun leather seats masu numfashi, tare da ƙayatattun tables, ga fine carpet shimfiɗe saman floor na jirgin, bayan shi akwai large flat-screen TV, ga Conference table domin yin meeting, a kewaye yake da kujeru, ga kitchen da bathroom, and privet bedroom da kuma dining area, Komai fa akwai shi acikin jirgin babu ce kaɗai ke babu, ta ko’ina sanyin A.c ka ratsa cikinsa. Bayan sun sauka abakin jirgin, Hankalin su Batul Yaƙi kwanciya tun da su ka yi arba da jibgegen jirgin dake agabansu, ko a mafarki basu ta6a yin tozali da abu kamar wannan ba, duk sun bi sun rude, sai faman zazzare idanuwa suke yi, badan Angel na atare da su ba, da tuni wasu daga cikinsu sun zauce saboda tsabar kiɗima, bankwana suka somayi da sojojin da suka rako su, Dr laura hada hawayenta na rabuwa da su, ɗaya bayan ɗaya saida ta rungume su, tana yi masu fatan alkhairi, Jemimah da Azeeza sunji ɗacin rabuwa da ita, sun sha kuka hawaye duk Ya 6ata fuskokinsu, lallashinsu ta dinga yi tana kwantar masu da hankali, tace kada su damu zata iya zuwa har Nigeria tagan su, babu wanda bai ji kewar rabuwa da su ba, Dr mark da brown suma sun matse ƙwallarsu, hatta nurse jessica da Rebecce sai da su kayi kukan rabuwa da su, musamman masoyiya Angel kowa ya saba da ita, suna sonta sosai, ummin america tuni tayi sallama da ƙawarta Natasha, bayan sun gama ƴan rungume rungume, sojojin da ke atare dasu sunyi masu fatan sauka lafiya, lokacin da zasu hau matakalar jirgin daƙyar suke taka staircases din, har dai suka samu damar shiga ciki, al’ajabi ya kama su ganin haɗuwar jirgin, kowan nan su Ya samu wuri saman tausasan leather seats din suka zazzauna, tun da suka shiga jirgin ummin america bata tanka masu ba, sai dai kallon kallon da suke Yi a tsakanin su, ita dai Angel damuwarta Danish ɗinta, Ya ƙanƙameta, babu alamun lafiya atattare da shi, jikin shi yai zafi rau. Lokacin da jirgin Ya soma tafiya Yana bin hanya kafin Ya ɗaga sama, Hankalinsu Azeeza ba ƙaramin tashi yai ba, jami’an Sunyi ƙoƙarin kwantar masu da hankali, ganin yadda su ka ruɗe jikin su ya hau yin kerma, sun fahimci mugun tsoro ne da su, Angel ce ta tunasar dasu akan suyi addu’a, aiko atare suka hada baki suna karanta addu’o’in data koya masu. Cikin ƙanƙanin lokacin jirgin Ya ɗaga sama Ya keta hazo can cikin sararin samaniya, Ajiyar zuciya kowan nan su ya sauke kamar an yaye masu tsoron da suke Ji, hankalin kowan nan su ya kwanta tun da aka kunna masu kallo a tv, ban da na Angel, Yanayin fuskarta ya canza, sakamakon maganganun da taji Danish yana furta mata acikin kunnanta, muryarshi arauna ce yake fadin baya son mutane, haushin su yake ji, yana ji kamar ya kashe su, jinin su yake sha” ƴan hanjin cikin ta ba ƙaramin kaɗawa su ka yi ba, sai faman zazzare ido take yi, babu wanda ya lura da halin da take a ciki, sauƙin ma acikin kunne yake yi mata raɗa, sautin muryar baya fita, kuma akwai tazara tsakanin seats dinsu dana sauran ƴan uwansu, ɗaya daga cikin jami’an isod ne Ya ɗauko mashi eye mask ya miƙa ma Angel don ta sanya mashi a tunanin shi hasken jirgin ke bayaso shiyasa ya cusa kanshi saman kafadar Angel may be ko yana son ya runtsa ne. Tun da ta sanya mashi eye mask taji yayi shiru ya daina magana alamar bacci ya dauke shi, a ƙalla ta sauke ajiyar zuciya yafi a ƙirga, addu’o’i taci gaba da karanto mashi tana tottofa mashi saman sumar kanshi, fatanta Allah yasa ba wani mugun abun bane zai faru da shi, gashi ta manta bata nemi takardar dake ɗauke da address din gidansu salsabeel, duk da bata tunanin ma ko sunje zasu samu abunda suke so. A Kishingiɗe yake saman shimfiɗeɗan full-sized bed dinsa dake acikin privet room na jirgin, ya ɗaura kansa saman tattausan pillow, Shin wanene wannan kyakkyawan matashin saurayin? A jin farko afagen kyau da ƙasaita, Namijin duniya, A halitta madai-dai ci ne, mai wani irin faffaɗan ƙirji a buɗe yake, ga wannan six pack din nasa baro baro, Vest din jikinsa tayi tighting dinsa, kana iya ganin zanen ƙirjinsa, Ko ɗan wrestling bazai nuna mashi ƙirar ƙarfi ba, in ka kalli damtsen hannunsa sai ka tsorata, mutun ne mai ji da ƙarfi, Allah yabasa kyawawan idanuwa farare tass ga su so sexy, masu ɗauke da launin ƙwayar ido reddish brown, har shining suke yi, ga wani kwantaccen saje mai shegen kyau, eye brows ɗinsa kuwa tamkar an zana ta, tayi wani irin shape ga gashi cike da ita, kiris ya rage jagirarsa su haɗe da juna saboda Yana da yalwatacciyar suma, lallausar sumar kanshi tasha gyara anyi mashi Military haircut yayi bala’en yi mashi kyau, abun da yafi komai jan hankali a jikin shi tsadaddiyar launin fatar shi, chocolate colour, har wani glowing take yi, hutu ya zauna mashi, jikinshi ya wanku da dollar, duk inda namiji yakai to ya zarce nan, komai nashi na kece raini ne ba wasa a tattare dashi, kuma burin kowace ƴa mace ne shi, a 6angaren wadatar arziki kuwa basai an faɗa maka ba, su kan su kuɗin raina kansu suke yi agabanshi, duk da tarin dukiyarsa baida girman girka, mutum ne shi da bai ɗauki duniya da zafi ba, Allah ya bashi kaifin basira, Yana da ilmin addini dana zamani, ta ko’ina Allah ya hore mashi, yana matuƙar jin ƙan talaka, Yana da tausayi ga son taimako, shi sam abun hannunshi bai rufe mashi ido ba, kyawawan halayansa da ɗabi’unsa abun burgewa ne, shiyasa ya fita daban ko acikin jikokin family ɗinsu, ya shahara aduniya sosai, babu inda ba’a sanshi ba, mutane basa gajiya da yabon shi, burin kowane ya yi tozali da shi, babban abunda ya tsana a duniyar nan shi ne yaga mugun mutun mara imani acikin mutane Yana zalunci, In kuwa ya damƙi irin su, mai ƙwatar su sai Allah, shiyasa mutane masu irin halin suke mugun jin shakkar shi, dai dai da sunan shi aka fada sai gabansu ya fadi, don baya yi masu da kyau, ni nasan bazan Iya misalta ƙasaitaccen Namijin nan ba, Kaɗan ne na Iya faɗa maku sauran ku biyo ni acikin labarin, Yanzu ne wasan Ya fara. Tun da ya ɗaura lumsassun idanuwanshi akan tsadaddar laptop din gabanshi ƙirar Apple macbook pro bai ƙyafta idon shi ba, Hannun shi na dama na sanye da wrist watch ƙirar Rolex submariner haɗaɗɗar gaske, ya tattara dukkan natsuwar shi akan abun da yake kallo, duk wani motsin prisoners dake acikin jirgin yana kallon su ta cikin laptop dinsa, Ƙayataccen table din dake agaban gadon shi ɗauke ya ke da Mug na cofee ga fresh fruit da aka ajiye mashi, daga gefen shi saman mattress, suit jacket dinsa ce daya cire launin Navy blue, trouser din ta ne a jikin shi, hankali a kwance bai da wata damuwa. Awanni da suka ɗauka acikin jirgin ba ƙaramin daɗi suka ji ba, saboda an gatanta su, sunci abinci har sau biyu, sun yi bacci sun tashi, komai suke so yi masu ake yi, Danish ne kaɗai baici komai ba, tun da bacci ya ɗauke shi bai farka ba. *💋ABBAN SOJOJI💋* *💋KURKUKUN ƘADDARA💋* *Assalamu alaikum, fatan mun wuni lpy, ga masu son abban sojoji complete 400 da kuma kurkukun ƙaddara wanda nake cikin rubutawa, ga number da zasuyi mini magana da ita, new number ce wadda nake da ita me 08103884440 whatsapp din ya samu matsala, ga wadda za’a same ni da ita (08134387050) ayi mini magana ta whatsapp, message from Boss Bature* *✍️ Mu haɗu Gobe In sha Allah Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya, Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin* First bank 3196407426, *Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai* _~*BossLadiesWriters*~_ _*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*_ ~Middle step~ سجن القدر❤🤍❤ _THE PRISONERS E26🔥💫_ *Daga alƙalamin Boss Bature* Confusion of the heart💫 Tun da Aneelerh ta turawa numbar saƙo har yau ba’a tuntu6eta ba, abun ya dame ta, ta rasa ina zata tsoma ranta taji daɗi, kullum ne sai ta ƙara jaraba kiran layin ko za’aci sa’a mamallakin wayar ya ɗaga amma wani iko na Allah a kashe take samun layin duk ta damu da son jin wanene. Fitowa ta yi daga cikin ɗakinta hannunta ruƙe da wayarta, ɗakin zahra ta nufa da niyar ta faɗa mata halin da take ciki wata’kil ta bata shawara akan abun da ke damunta. A bakin ƙofar ɗakin ta fara yin sallama, shiru ba’a amsa mata ba, kusan sau uku tana kwaɗa sallama zahra bata amsa ba, tunani ta soma yi ko dai ta koma wurin aiki ne? Ko kuwa baccin lalacin da ta saba yi ne, wata’ƙil kuma wanka ta shiga. Haura ƙafa ta yi ta shiga ɗakin zahra, tun abakin ƙofar room din ta fara cin karo da takalmanta da jakarta da mayafin ta gaba ɗaya ta watso su saman floor, nan take hankalin Aneelerh ya tashi da sauri ta ɗago da ido tana kallon gadonta, duvet dinta da pillow dinta duk ta watso su ƙasa, Komai na ɗakin ta tarwatsa shi. Aneelerh ta fahimci babu lafiya wani abu ya faru da ita, Zahra da ta sani Mai tsafta dagangan dai bazata ta6a barin ɗakinta a hargitse ba. Cikin tashin hankali ta soma ƙwala mata kira”Zahra! zahra!!” shiru babu amsa, ranta ne Ya bata cewar ko dai bata agidan ne ko kuma ta shiga ɗakin ummi, da sauri Aneelerh ta fuce daga ɗakin, Har zata gifta ta falo ta wutsiyar ido ta hango Mami da ummi zaune suna fira, juyawa tayi da sauri ta nufe su, babu wanda Ya lura da ita acikinsu har saida ta furta”ummi mami Ina zahra” kusan atare suka ɗago suna kallonta, gaba daya sun fahimci babu kwanciyar hankali atattare da ita. Ummi tace”kin duba ɗakinta baki ganta ba”? Kafin ta bata amsa mami tace”Aneelerh wai lafiya? Ya akai naga kamar bakya acikin natsuwarki” Muryarta na ɗan rawa ta furta”bakomai, na duba ɗakin zahra ne ban ganta ba” Mami tace”shine duk kika ɗaga hankalin ki? Sai kace yau ta fara fita daga gidan, kema kinsan zahra idan har ba wurin aiki taje ba toh tana acikin gida” Ummi tace”tun ɗazu fa ta dawo, ki kwantar da hankalin ki, bata wuce cikin ɗakinta, Ki koma ki sake dubawa” Juyawa tayi da sauri ta nufi ɗakin donta ƙara dubawa. Bayan tafiyarta ummi ta dubi mami”ƙawancen Aneelerh da zahra ba ƙaramin burgeni ya ke yi ba, har mamaki nake yi idan naga yadda Aneelerh take jan zahra a jiki, duk da ta girme ta” Mami na murmushi tace”ai shi ƙawance ba a shekaru yake ba, indai mutum Ya mallaki hankalin shi ko da ya girme ka zaka Iya ƙawance da shi, Ni kaina ba ƙaramin burgeni suke Yi ba, Allah dai Ya bar zumunci” Ummi tace Ameen ameen. Daga haka su ka ci gaba da tattaunawa a tsakaninsu. Afujajen Aneelerh ta faɗo ɗakin zahra tana faman Yin haki, ta kware murya tana ambaton sunanta”Zahra! zahra! Nasan kina jina, Dan Allah kiyi mini magana” Still babu alamar za’a tanka mata, ranta ne ya bata cewar wata’ƙil ta fita ne ba tare da sanin kowa ba, Har ta juya zata fuce daga ɗakin ba zato ba tsammani ta soma jin shessheƙar kukan zahra, da sauri Aneelerh taci burki, a sukwane Ta juya tana bin ko’ina na ɗakin da kallo, a ƙoƙarinta nata gano inda zahra ta 6uya, hankalinta yafi karkata akan toilet din ɗakin, da sauri ta ƙarasa bakin kofar ta kara kunnanta, sosai take jin kukan zahra mai matuƙar tsuma zuciya. Muryarta na rawa ta furta”Zahra meya faru dake? Wanene ya ta6a min ke? Dan Allah ki faɗamin zahra, ashe kina jina shine kika ƙi tanka mun ko?” cikin shessheƙar kuka zahra tace”...Aunty Aneelerh babu abun da ke damuna, kawai bana son kowa ne a kusa dani” “Ki fito daga cikin toilet din muyi magana zahra, ni bana so inganki acikin damuwa, kema kin sani har farin cikina zan Iya sadaukarwa saboda ke, don haka ki fito muyi magana” cikin kwantar da murya Aneelerh take yi mata magana. “Zahra ke nake jira ki fito muyi magana, wlh idan kika bari na haura ƙafa ta daga cikin ɗakin nan to kada ki yi tsammanin zan waiwaye ki, haba dan Allah, ina amfanin irin hakan? Ashe dama baki ɗauke ni kamar yadda na ɗauke ki ba? Har zaki Iya ke6e kanki cikin damuwa ba tare da kin neme ni ba”? A faɗace Aneelerh ta ambaci hakan, duk don ta samu zahra ta buɗe ƙofar toilet din. Bugun ƙofar tayi da hannunta”kada Allah yasa ki buɗe ƴar rainin wayau” ta faɗa tare da juyawa ta nufi ƙofar fucewa daga dakin, Buɗe ƙofar toilet din zahra tayi, Fuskarta sharkaf da hawaye idanuwanta har sun kumbura, kumatunta sunyi jawur dasu, Short ne a jikinta tare da farar vest, Sumar kanta kamar ta mahaukaci sabon kamu. Da gudun gaske ta nufi Aneelerh dake ƙoƙarin fita daga ɗakin, Gaba ɗaya ta faɗa saman bayanta ta rungume tana cigaba da yin shessheƙar kuka. Ajiyar zuciya Aneelerh ta sauke, tare da kai hannu ta ruƙo damtsen zahra ta zagayo da ita, har saida gabanta ya faɗi ganin yadda hawaye suka wanke mata fuskarta tamkar ba zahra ba, damuwace ƙarara akan fuskarta, kwantar da kanta Aneelerh tayi saman kirjinta, a hankali take shafa sumar kan zahra da yatsun hannayenta. “Ya isa zahra, ki daina kuka bana son ganin hawayenki,’ cikin murya kuka tace”Aunty Aneelerh ba zaki gane ba, Ni kaɗai nasan halin da nake aciki, Allah ji nake kamar in haɗiyi zuciya in mutu kowa ya huta” Kalaman zahra sun ƙara ɗaga mata hankali, tabbas akwai gagarumar matsala, Yarinyar da koda yaushe fuskarta dauke da murmushi komai zaka yiwa zahra a duniyar nan baka isa ka 6ata mata ranta ba, sai gashi a yau itace take Yin kuka har tana faɗin kamar ta haɗiyi zuciya ta mutu. “Kiyi haƙuri zahra, bai kamata kina yin wannan furucin ba, Idan ma wani abune ke damunki meyasa ba zaki kai kukan ki ga Allah ba? sai kawai ki kulle kanki a toilet kina kuka? Hakan ya dace? Kina tunanin shine mafita a gare ki? Ga ummi ga mami, ga mahboob, ga abie da uncle uwa uba ga kuma ni meyasa ba zaki tuntu6i ɗaya daga cikin mu ki faɗa masa damuwarki ba? Kin tsaya kina yin zurfi ciki a ƙarshe ki yi wa kanki illa amma faɗamana da zakiyi shi zaisa ki samu maslaha na abunda ke damunki, ko da ace bamu da abun da zamu taimaka maki wurin yaye damuwarki zahra zamu Iya baki shawara ko mutayaki da addu’a akan Allah ya yaye maki” Faɗa Aneelerh tayi mata, sai faman sauke ajiyar zuciya take Yi, ruƙo hannunta Aneeleeh tayi”wuce ki shiga toilet ki wanke fuskarki Ina jiranki” ta faɗa tare da sakin hannun zahra, baiwarAllah jikinta duk ba ƙwari tana tafiya tana waiwayon Aneelerh, yayin da hawaye ke cigaba da fita a idonta. Kafin fitowarta Aneelerh ta bar ɗakin ta nufi falo, fridge ta buɗe ta dauko mata ruwa me sanyi. Cikin tafiyar sauri ta nufi ɗakin. “Aneelerh kinga zahran ne”? Muryar mami ce ta katse mata hanzarinta, ba tare da ta juya ta kallesu ba ta bata amsa da cewa”Eh mami, ashe toilet ta shiga” Bayan ta shiga ɗakin, ta daura ruwan a gaban mirror, ta koma bakin door din ɗakin ta soma tattara kayan da zahra ta watsar ta maida su a ma’ajiyarsu. Ba ta jima da zama a gefen gadon ba, Zahra ta fito daga toilet, ta wanke fuskarta kamar mara gaskiya ko haɗa ido da Aneelerh bata son yi, saman mirror chair ta zauna tana fuskanta Aneelerh, sai dai ta taƙi ɗagowa su haɗa ido da ita. “Ga ruwan nan ki sha” ta faɗa tana nuna mata robar ruwan, data ajiye mata, Yatsun hannunta na kerma ta ɗauki bottle water din ta cire murfin ta soma ɗaɗɗakar ruwan kamar zata haɗa da robar duka ta shanye, bayan ta gama sha ta maida murfin robar ta daurata gaban mirror. “Zahra ina sauraronki, Ki natsu ki fadamin meya faru dake? Da har yaja kika kulle kanki a toilet, bana so ki furta mun kalmar babu komai! Ranki zai Iya 6aci” fuskarta a ɗaure tamau tayi mata maganar. Zahra na faman sunnar dakai, idanuwanta akan yatsun hannunta muryarta adabarbarce ta soma magana. “Aunty aneelerh zan faɗa maki amma kada ki faɗa ma kowa dan Allah,” jinjina kai Aneelerh tayi”in sha Allah” Cigaba da yin magana tayi”dama akan decorating company dinmu ne, ban ta6a faɗa maki cewa banawa bane, mallakin mamansu ƙawata ne, Ni a lokacin dana kammala karatu ina neman aiki bansamu ba, Nayi ma daddy magana akan ya taimaka mini in buɗe Beauty saloon nawa nakaina, amma sai yace min shi baida halin da zai Iya taimaka mani, bayan ni nasan yana da arziƙin shi kawai baison bani ne kusan halin shi ɗaya da mahboob in dai wurin maƙone ko mami fama take yi dashi, dawowar ku gidan nan ne ma ya fara sakin hannunshi gudun kada ku gane halin shi,’ Aneelerh ta natsu tana sauraranta. Numfasawa zahra tayi kafin taci gaba da cewa”akwai wata rana da naje gidansu ƙawartawa, muna zaune a falo muna fira akan yadda zamu buɗe beauty saloon da zamu gudanar da kasuwancin su, har take ce min mommynta tana da kuɗi sai dai itama maƙone da ita ba ta Iya fidda kuɗi ta bata hakanan idan ba abun da ya shafi karatunta bane, amma da zata amince mana ko da bashine ta bamu idan muka samu kuɗi tun da kusuwancin ana samu sosai indai mutun ya samu kar6uwa awurin mutane, sai na zaro ido nace mata a’a ni bana so muci bashi muzo mu kasa biya, na faɗi hakanne saboda sanin halin mahaifiyarta masifaffiyace bata da mutunci in dai akan kuɗin ta ne, Aunty Aneeleh fatima ta matsa mini akan muje muyiwa mommynta magana tasan idan na sanya baki zata bamu tallafin da zamu buɗe, saboda muna mutunci da ita, duk cikin ƙawayen fatima tafi sakewa dani har idan nayi kwana biyu banzo gidan su ba takan tambayi fatima ina ƙawarnan taki mai dimple da yake haka take kira na, sai tace mata zata kira ni idan tana son ganina, Aunty aneelerh tsautsayi ne ya kai ni ga amincewa da maganar fatima, muka kwasa muka je wurin mommynta, muka fada mata dangane da beauty salon din da muke so za mu buɗe gashi bamu da kuɗi, matar nan tayi dariya tace mana ai ba wani abu, ta ji daɗi da mu ka yi tunani mai kyau, ita tana son mutun me burin ya nemi na kansa, don haka zata buɗe mana company da zamu dinga gudanar da kasuwancin mu harma mu zuba ma’aikata acikin sa da zasu dinga taya mu aiki, idan yaso zamu dinga raba riba da ita, a lokacin munyi mamakin jin zata buɗe mana company mu da muke maganar buɗe ƙaramin beauty saloon, ni bansan da wata manufa a ƙasa ba, Ni da fatima munyi murna muka dinga yi mata godiya da addu’o’i, tun da ta buɗe mana companyn bata ta6a kar6ar ribar da muke rabawa ba, duk in muka kai mata kasonta sai tace mana mu ruƙe a hannun mu zata nema yanzu bata buƙatar kuɗi, Aunty Aneelerh tun muna tara mata kuɗin har dai fatima tace min mu kashe kudin ai mommynta bata buƙatarsu shiyasa bata kar6a ba, in yaso daga baya in muka tara wasu kuɗin sai mu biyata, zuciya ta ɗebeni muka haɗu ni da fatima mu ka kashe kuɗin, acikin su na cika da nawa kuɗin na sayi mota, Na canza wayata na sayi iphone 15, wayar da kika ga ina ruƙewa a hannuna, Na ciri dubu ɗari uku naba ummin mu nace gashi nan tasa mun albarka kasuwanci yayi kyau, ummi taji daɗin kuɗin nan, dama tana buƙatarsu daddy baya bata kuɗin da zatayi hidindimu dasu, duk nice fa nake taimaka masu idan na samu kudi, shi kawai ta 6angaren abinci ne yake yi mana ƙoƙari, sai kuma kayan sallah idan tazo amma inba sallaba babu abunda daddy yake yi mana, kudin shi sai dai muga wasu suna ci, acikin kuɗin naba mahboob dubu hamsin shima yai ta yi mini godiya hada ƴar ƙwallar shi saboda daɗin da yaji....’ dakatawa ta ɗanyi da yin maganar hawaye nabin fuskarta, tun kafin ta ƙarasa jikin Aneelerh yai sanyi don tasan ƙarshen zancen bamai daɗi bane. Jinjina kai zahra ta ɗanyi kafin ta daura da cewa”Aunty aneelerh saida na tabbatar kuɗin sun ƙare tukunna hankalina Ya kwanta, sai kwanan nan da Hajiya saratu ta kira awaya suna buƙatar ayi masu decoration da kitso da ƙunshi, lokacin dana duba asusun mu, ba mu da isassun kuɗin da zamuyi order na kayan da za’ayi masu amfani, dama dai ita hajiya falmata itace take yi mana hanyar da ake shigo mana kayan adon daga dubai, muka zauna nida fatima mukayi shawara sai tace min zatayi ma mom dinta magana, bayan sunyi magana da ita, sai ga fatima tazo wurin aikin mu idanuwanta jawur dasu, hankalina atashe na tambayeta lafiya meya faru da ita, cikin shessheƙar kuka tace min mominta tace idan har muna so tayi mana order din kaya mu fara tura mata ribar da muka tara mata a hannun mu, tana buƙatar kuɗin da gaggawa, tun anan fatima tace mata ai babu kudin nan mun kashe su, tsabar 6acin rai ta zazzaga mata masifa tamkar ba ƴar ta ba, hada mari ta kwasa mata a fuska, ko lokacin da tayi mini magana fuskarta da sahun yatsun hannun mahaifiyarta, Hankalina ba ƙaramin tashi yai ba, saboda ni bansan inda zan samu kuɗi na biyata ba, daga ni har fatiman bamu da kuɗin a hannun mu, Aunty Aneelerh nasan bamu kyauta ba tunda ba kyauta ta bamu ba, amma muka ta6a mata kudinta bayan yarjejeniyace muka ƙulla da ita akan duk in aka samu riba zamu raba kaso uku, matsalar da aka samu kuɗin data bar mana a hannun mu taƙi kar6arsu har saida tsautsayi yasa muka ta6a su....” fashewa tayi da kuka Aneelerh ta natsu tana dubanta. “Nayi ƙoƙarin Na saida motata don na samu na biyata kuɗinta sai dai bansamu wanda zai siya ba, Jiya ina kwance saman gado na gama shan kuka na sai ga kiran fatima awaya, na ɗaga muka gaisa da ita, tace min mominta tana son Yin magana dani inzo in same ta agida, hankalina ya dan tashi don tunda muƙe nuƙu nuƙu akan yadda zamu biyata kudin bata ta6a yin maganar dani ba, tsakaninta ne da fatiman, nace mata zuwa gobe zanzo gidan nasu, jiya ko bacci banyi ba, da sassafe na shirya babu wanda ya san na fita daga gidan nan naja mota naje gidansu fatima babu kowa afalon gidan saida mai aikin gidan ta fito daga kitchen muka gaisa take ce min ai hajiya ta faɗa mata game da zuwana in shiga ɗaki tana jirana, da sauri na juya na nufi ɗakinta gabana na faɗuwa abakin kofar ɗakin nayi mata sallama, muryarta ƙasa ƙasa tace min wanene? nace mata zahra ce ƙawar fatima mai dimple, tace in shigo ciki.....” dakatawa ta ɗanyi da yin maganar tana faman ƙyafƙyafta ƙwayar idanuwanta. Cikin ƙagara da sonjin ƙarashen zancen Aneelerh tace”naji kinyi shiru? Me tace maki ne”! Yawu zahra ta hadiya muryarta na ɗan rawa ta ɗaura da cewa”Ina shiga ɗakin na same ta kwance saman gado daga ita sai ɗan undy shara shara ajikinta, arude na juya zan fuce da sauri ta kira sunana zahra zonan, cak na tsaya ba tare dana juya na dube ta ba, ta sauko daga saman gadon ta nufo inda nake a tsaye ta tsaya daga bayana ta soma yi min magana . Ya maganar kuɗina da zaku bani? Nayi magana da fatima tace min atare kuka kashe kudin meyasa zahra? Ban ta6a tunanin za ku yi mini haka ba, Na yadda daku na damƙa maku amana amma kuna nema kuyi mini wasa da dukiyata, ko dan ba ku san zafin nema bane”? faɗa sosai tayi mini bansan lokacin dana fashe mata da kuka ba ina roƙonta akan tayi hakuri nayi mata alƙawarin zan biyata kuɗin ta cikin satin nan, Aunty Aneelerh ba zato ba tsammani naji ta sanya hannu ta ruƙo hannuna, ta juyo dani ta rungumeni a ƙirjinta, ban ɗauka da wata manufa ba sai da naji tana matse ni a kirjinta gabana yaci gaba da faɗuwa, cikin dabara ta miƙa hannu ta bayana ta datse ƙofar ɗakinta da jamlock, ba tare da sanina ba....” ganin yadda Aneelerh ta zaro ido waje yasa zahra ta dakata da yin maganar la66anta na kerma. Aneelerh tace”zahra ke nake sauraro uban me tayi maki” a kausashe Aneeleeh ta furta mata hakan, cikin ruɗu zahra tace”nayi ƙokarin raba jikina da nata amma saita ƙara tighting dina, ta zame mayafin dake akaina, ta sanya hannu tana shafa sumar kaina cikin raɗa take furta min”meyasa nake yi mata kuka? Ko dan saboda tayi mini faɗa akan kuɗinta ne, muryata na kerma nace mata ta yi haƙuri zan biyata kudinta, tace min in kwantar da hankalina ai ba dole saida kuɗi zan Iya biyanta ba, A jikina ma ina da abun da suka fi kuɗi daraja, idan na amince na bata haɗin kai zata yafe mana bashin harma ta yi mana order na kayan decoration din da muke so, cikin rashin fahimtar maganarta nace mata ni ban gane me kike nufi ba? Menene yafi kuɗi daraja a jikina? Kuma wani irin hadin kai kikeso in baki”? Har lokacin bata raba ni da jikinta ba, saima nishi da naji tana saki, tace min tana buƙatata jikina kawai takeso, zatayi amfani dani. Saboda yarda da nayi da matar saina dauka wasa take yi mini, Cikin sanyin murya nace mata mommy amma dai zolayata kikeyi ko”? Na fada ina kokarin raba jikina daga nata saidai taƙi bari inyi hakan, kamar zata maidani cikinta. Babu alamun wasa a kalamanta tace min” Zahra na ta6a yi miki wasa irin wannan? Nace mata a’a, tace min toh dagaske take, dama ta jima tana kwaɗayin son kasancewa tare dani bata samu damar yin hakan ba don ta lura kamun kaine dani kuma ni ba ƴar harka bace, shiyasa ta yi dabarar amincewa da buƙatarmu ta buɗe mata company kuma taƙi kar6ar kuɗin ribarta dake a hannun mu, Ashe maƙarƙashiya ta shirya mini saboda tasan zamu iya ta6a kuɗin, Ni ban ta6a tunanin matar zatayi mini haka ba. Aunty Aneelerh data faɗamin hakan tsigar jikina ta tashi, na rasa uwar ubana, na soma kiciniyar ƙwace kaina daga ruƙon da tayi min ina fadin ni ki sake ni in tafi gida, wlh kin ban mamaki na dauke ki tamkar mahaifiyata saboda ƙaunar dake a tsakanina da fatima ashe nayi babban kuskure, Ni bazan ta6a baki haɗin kai don mu aikata sa6on Allah ba, kema inayi maki fatan Allah ya shiryeki,’ sai da nasha wahalar bangajeta, da gudu na damƙi ƙofa zan buɗe naji ta a garƙame kafin in zare jamlock din Naji ta damƙeni ta wurgar dani saman gado tana fadin”baki isa ki kubcemun ba zahra, dama nasan zakiyi min taurin kai shiyasa na biyo maki ta wannan hanyar, wlh idan har kika bijirema buƙatata zan saki dole ki biyani kuɗina a yau ɗin nan idan ba haka ba zan damƙa ku hannun lawyer dina, sannan zan rufe companynku,” Ina kuka nace mata naji ta bani lokacin da take son kuɗinta In sha Allah zan biyata amma ni kada ta kuskura tace zata ta6a jikina, ta jira taga idan ban biyata ba sai ta yi mini duk abun da ta ga dama, tana faman sakin shu’umin murmushi tace min bataso inyi danasani, don tasan banda arziƙin da zan Iya biyanta, tasan wanene mahaifina karen ƴan siyasane sai yayi masu wahala suke watsa mashi hatsin da zai samu ya tsastsaga harma ya ɗan mana, raina ya 6acin sosai jin irin wulaƙancin da take yi mini nasan nina ja ma kaina, dama ance kwaɗayi mabuɗin wahala, sannan idan har kace zaka dogara da wani kana tare da wahala, sai dai ba yadda zanyi ne tun farko da nasan wacece ita wlh daban amince ta buɗe mana company ba, daƙyar na samu ta ƙyale ni abisa sharadin gobe da safe ƙarfe 7 tana jiran alert na kuɗinta, wlh idan daddy yaji maganar nan sai ya kusa kasheni, ni bansan ya zanyi ba” Zuciyar Aneelerh tayi matuƙar karaya, tayi mamakin Hajiyarsu zahra me halin bunsuranci. “har nawa ne kudin”? Zahra na matsar ƙwalla tace”kusan fa miliyan shidda muka raba ni da fatima” Zaro ido waje Aneelerh tayi tana mai jinjina kai tace”tabɗijancan, ashe da rabon zahra ki kwana a cell, don kuwa babu abunda zai hanaki zuwa gidan Yari, Ni har na hangoki cikin uniform dinsu” fashewa zahra tayi da kuka jin abunda aneeelerh take faɗi. Cikin shessheƙar kuka tace”Aunty aneelerh kidaina banso, bakisan halin da nake aciki bane shiyasa kike zolayata, wlh saboda tashin hankalin da nake aciki tun safe ko ruwa ban sha ba” Tsananin tausayinta ne Ya kama Aneelerh, idanuwanta sunyi jawur dasu kamar an watsa mata barkono, muryarta na rawa tace”Aunty aneelerh ko zaki taimaka mini mu je mu nemo wanda zai sayi motata da wayata kafin lokacin Ya cika” Jikinta na kerma tayi magana. “Lokacin da ku ka yi yarjejeniyar buɗe companyn kinyi shawara da wani? Ina nufin Uncle ko Ummi akwai wanda kika faɗa mawa”?! Girgiza kai zahra tayi”Ni ban faɗa ma kowa ba, babu wanda ya sani, kawai dai na faɗa masu na samu aiki a company, sun tayani murna kuma sun yi min fatan akhairi, ummi ma ta ta6a tambayana ya akai companyn yaci sunana? Kamar nawa, sai nace mata banawa bane, Yarinyar me companyn ce takwarata shiyasa aka sanya mashi Sunan Zahra world of beauty” Jinjina kai Aneelerh tayi”Kinyi babban kuskure Zahra, Matar nan Tayi maki wayau, Nafi ganin laifin ki, ke fa da kanki kikace kinsan halinta masifaffiyace amma ahaka kika biyewa fatima ku ka kashe kuɗi har miliyan shidda bayan kinsan ba gadon ɗan iya bane, Idan ita yarinyar bata da wayau ai ke da hankalin ki, kuma ita dukiyar mahaifiyarta ce, ke kuma fa? Baki haɗa komai da ita ba,Yanzu ai gashinan taja maki bala’e, ko dai ki biyata kuɗinta ko ta maka ki kotu, Ni dai shawarar da zan baki shine kije ki yi mata abun da take so!” hankali akwance aneeelerh tayi mata magana, tayi tsammanin zata taimaka mata ne donsu nemi mafita amma sai taji tana fadin hakan, zuciyarta ta karaya sosai, har batasan sa’adda ta fashe da kuka ba, ta sauko daga saman kujerar ta zube saman gwiwowinta Cikin shessheƙar kuka take fadin”Na shiga uku aunty aneelerh, amma dai wasa kikeyi mini ko? Ni nasan bazaki ta6a bani shawarar in aikata zunubi mai girma irin wannan ba, wallahi ina tsoron Allah, Ina tsoron ranar da zan koma gare shi” Ɗaure mata fuska Aneelerh tayi”Idan har baki amince mata ba zahra tayaya kike tunanin zaki Iya biyanta? Kinsan halin mahaifinki bazai ta6a biya maki kudin nan ba, Ummi kuma bata da kuɗi, zahra ƙwara ki bata haɗin kai, nayi maki alƙawarin babu wanda zai ji abunda ya faru, daga ni sai ke, kinga tace zata ƙara maku wasu kudin harma tasa ayi maku order na kayan da zaku yi amfani da su daga dubai, wallahi zahra ki amince mata idan ma don baki saba bane zaki saba a Hankali, Allah kuma gafurirrahim ne, zaki iya tuba ko daga baya ne in ta gama amfani dake” Zazzare ido waje zahra tayi yayin da take kallon Aneelerh, cikin matsanancin tashin hankali da ruɗani, Muryarta na rawa ta furta”Aunty Aneelerh dagaske kike? In bata hadin kai”? Murmushi Aneelerh ta sakar mata hadi da ɗaga mata gira alamar eh, girgiza kai zahra tayi idanuwanta cike tab da ƙwalla tace”wallahi aunty Aneelerh bazan Iyaba, koda kuwa duniya zata mallaka mini don in biya mata buƙatarta bazan ta6a amincewa ba, da in sa6ama Allah na ƙwammace in rasa komai dana mallaka don In biyata kuɗin ta, ina tsoron Allah kuma ina jin tsoron ranar da zan koma gare shi, yanzu idan na mutu kafin in tuba fa”? ta faɗa yayin da hawaye ke cigaba da wanke fuskarta, kallon da take bin Aneelerh da shi, kallone na mamaki da al’ajabin shawarar da ta bata, har ta fara kokwanton Anya kuwa Aneelerh ce wannan? Ko dai Aljanu sun shige ta ne? Gyaɗa kai Zahra tayi cikin rauni na murya ta furta “Aunty Aneelerh ki daina wannan maganar kina rikita mini tunanina, idan har ba zaki taimaka mini mu nemi mafita ba bai kamata kina tunzurani akan in aikata zunubi mai girma irin wannan ba, har kin sa nafara kokwanto akanki duk da nasan wacece Auntyna” Ta6e baki aneelerh tayi haɗi da watsa hannayenta tace” Zahra, we don’t have any other solution besides this, ina ƙara jaddada maki, ki hanzarta zuwa ki biya mata buƙatarta, idan ba haka ba zata kai ƙarar ki kotune sannan ta rufe maku companyn ku, amma idan kika bata hadin kai, kinga zaki ci riba biyu da farko zata yafe maki bashin da take bin ki, na biyu kuma zata yi maku order na kayan amfani daga dubai, wannan fa babbar dama ce agare ki!!!” da sauti mai ƙarfi ta ƙarasa maganar, fuskarta babu annuri, ta yunƙura ta miƙe tsaye, Zahra ta saki baki tana kallon ta da rinannun idanuwanta. “Ni kinga tafiyata, Idan kin canza ra’ayin ki kina iya zuwa ɗaki ki same Ni, zan taimaka maki da mayukan da zaki gyara mata jikin ki” ta hankaɗe kafaɗa ta juya ta nufi kofar fucewa daga ɗakin. Kamar sakarya haka zahra tabi bayan Aneelerh da kallo har ta 6ace ma ganinta, hannu biyu ta ɗaura saman kanta, tana faman ambaton kalmar Inna lillahi wa’inna ilaihirraji”un” Tsantsar tashin hankaline akan fuskarta, wani irin azababben zazza6ine ya lullu6eta, saman floor ta kwanta, idanuwanta na fuskarta ceilling, yau Aunty aneelerh ta bata mamaki, ta karya mata zuciya, duk da har yanzu ta kasa yarda da abunda zuciyarta ke faɗa mata dangane da ita, batasan ya zatayi ba? Don ita har ga Allah bata jin zata amince da shawarar Aneelerh ta ƙwammace ta tattara duk wani abu data mallaka taje ta biyata kuɗinta zaifi mata kwanciyar hankali akan ta sa6a ma Allah, tazo tana danasani mara amfani, babban abunda take jima takaici asarar da zatayi na zuwa gidan Obinna, On friday na satin da suke ciki Za’ayi shagalin birthday na babansu, already sun fidda masu anko, decoration ne da kitso suke buƙatar ayi masu jibi, tasan tarasa wannan damar, Hajiya falmata baza ta bari ta cigaba da yin aiki a companynsu ba muddin bata amince da buƙatarta ba, gashi ita bata da komai, dole ta haƙura tama riga da ta fidda rai, shawarwari ta shiga yankewa da zuciyarta, a karshe ta yanke shawarar Zata yi magana da mahboob watakil ko cikin abokanan sa asamu wanda zai sayi motarta da wayarta, da wannan tunanin baccin wahala ya ɗauke ta, babu ci babu sha tun safe baiwar Allah. *DAULAR OBIE ESTATE* Zayn ne kwance saman shimfiɗeɗen gadonsu, daga shi sai short a jikinshi, tun da suka dawo daga office yake ta sharar baccin shi kamar matacce, toilet door din ɗakin aka buɗe Zaid ne Ya fito waist dinshi ɗaure da towel, jikin shi da alamun danshin ruwan wankan da yayo, tun kafin ya ƙarasa gaban gadon ya soma ambaton sunan zayn. “Bro, get up, I want to have an important talk with you, please,” ya faɗa ayayin da yake ƙokarin zama gefen gadon, hannu yakai yana bubbuga ƙafarshi”pls ka tashi zayn, baccin ya isa haka sai kace mai sleeping sickness, tun da muka dawo daga office kake ta sharar bacci ko dai ka sha ƙwaya ne”? Ya faɗa yana cunkulin kafar zayn da mugunta, dogon tsoki Zayn yaja, yana faman yamutsa fuska ya furta” “Zain, I don’t want to be stressed, please, let me rest, I’m tired,” Rai a6ace yai maganar ba tare daya buɗe idanuwanshi ba. Zain na murmushi yace”Haba babyn mommy, you should wake up, you’ve had enough sleep. I know it’s not just work tiredness that made you sleep, because your secretary told me that you’re not doing anything other than gathering girls in your office. Ko nayi ƙarya?” He spoke jokingly, looking at Zayn’s face, tamkar bai ji me yace ba, Ya haɗe fuska babu annuri. “Dole kayi shiru, tun da baka da abun cewa, adai dinga jin tsoron Allah, taƙamarka kana da kyan fasali shiyasa kake maƙure Ƴan matasan mata a office kana zare masu ido, don kasan dole suyi maka biyayya tunda suna aiki a ƙarƙashin ikon ......” bai ƙarasa maganar ba, sakamakon zaburar da zayn yai ya miƙe tare da damƙar pillow, ya buga mashi akai, Ya janyo wani pillow ya dinga bugunshi ta ko’ina, Muryarshi tamkar zai fashe da kuka yake fadin”zaid ka takura ma rayuwata, kai ma ka sani wallahi nafi ƙarfin in maƙure ƴa’ƴan mutane a office, Ni bana yima mace dole in ba ita ta nuna tana buƙatana ba, kai ne dai bunsuru da baka Iya gani ka kauda idonka, Ni da aji na matane suke kawo kansu wurina bani nake kiran su ba” ya faɗa yana hararansa”shashasha kawai mai kama da daddy” Ya ƙare maganar Yana haki kamar wanda yasha gudu, idanuwanshi sun kaɗa jawur saboda baccin da bai ishe shi ba. “Zayn? Ni ne bunsuru? Kuma mai kama da daddy? Kana nufin shima daddyn mu bunsurun ne”? Fuskarshi a ɗaure yayi maganar. Ɗaga mashi gira zayn yai”ƙarya nayi ne? Babyn daddy, Nifa ba ina nufin bunzuru na dabba ba, No, just ina kwantanta Namiji mai bin mata ne da sunan bunsuru, kasan shima bunsurun haka ɗabi’unsa suke, duk inda yaga mace sai ya bita, shiko namijin da mata suke kawo kansu gare shi bazai yiwu ba a kirashi da bunsuru, sannan Ni bance hada daddy ba, kai kaɗai na ce” a fusace zaid yace”kada ka manta, dani dakai bamu da banbanci ko a murya, idan ina kama da daddy then you look like him too, and you’re a he-goat as well. gwalo zayn yai mashi”Oho dai, ai kwanan nan zanje ayi mini surgery amaida mun kamannin fuskata irin na mommyna, donni bana son abunda zai haɗa ni da ku” da zolaya yake yi mashi magana, amma shi zaid sai yake ganin kamar baison shi ne, ganin yadda ya haɗe fuska ne yasa zayn saurin cewa” wasa fa nake yi maka, kaima ka sani ni da kai abu ɗayane, na fadi hakanne don in 6ata maka rai kamar yarda ka tada ni daga bacci” Yamutsa fuska Zaid Yai”naji, yanzu dai mu ajiye wannan gefe, Ya maganar zuwanmu america”? Yai tambayar yana duban fuskar Zayn “Bamu da isassun kuɗi a account, Ni dai na hakura, ƙwara kaima ka haƙura kawai muyi zaman mu a ƙasar mu ta gado,” Girgiza kai Zaid yai”bazai yiwuwa ba, zayn bakasan yadda naci burin haɗuwa da Ummi ba, Jiya har mafarkin ta nayi, na kasa gogeta acikin zuciyata” Ta6e baki zayn yai”faɗamin acikin mafarkin me kuka aikata” “Bamu aikata komai ba, kawai dai mun hadu a jabi lake mall, har nake tambayarta yaushe ta shigo ƙasar? Kafin ta bani amsa ka katse mini bacci ka tada ni kana fadin lokacin sallar asuba yayi” Murmushi Zayn ya sakar mashi”kace nayi maka buƙulu, wata’kil da har kiss ta manna maka da hug” Harara zaid ya jefa mashi atakure yace”ya zamuyi ni dai? Ko dai mu kar6i Atm din daddy daya ce zai bamu”? da sauri zayn ya girgiza kai Yana fadin”No, ba zamu kar6a ba” zaid yace”why? Ni bansan meyasa baka son mu kar6i Atm dinsa ba, maƙudan kuɗi ne fa zayn zasu ishe mu muje duk inda muke so, wai kai kafi son muyita wahalar jiran salary”? “Eh, ƙwara mu jira salary, akan mu kar6i kudin da ba mu san inda aka same su ba, ka yi amfani da hankalin ka mana, ina daddy yake da arziƙin tara waɗannan millions of dollars din? Abun da baka sani ba, Dana zauna na lissafa dukiyar mommy ko rabin tashi bata kai ba, ita da ta gaji arziƙin kenan, da farko nayi tsammanin ko kuɗinta ne ta bashi ajiya amma daga bisani na zauna nayi nazari sosai na gane cewa kuɗin nan fa bana mommy bane, kuma ba albashin daddy bane suka tara mashi su, Ni tsorona kada mu je mu kar6i kudin sai mun gama sharholiyarmu asiri ya tonu agano daddynmu yana aikata wani abun, duk da ina kyautata mashi zato, amma gaskiya ni zaid ban yarda da kuɗin nan ba, bada guminsa ya tara su ba, akwai dai wani abun a ƙasa” Damuwace ƙarara akan fuskar zaid sam babu alamun Ya fahimci zancen twin bro dinsa. “Na lura zayn baka son daddy, baka ƙaunar shi, kafi son mommy, sai kace bashi bane ya haife ka, na tabbata da ace mommyne ta baka atm dinta jiki na rawa zaka kar6a ka yi amfani da kuɗin amma da yake na daddy ne shine kake neman yi mashi ƙazafi, wallahi kaji tsoron Allah zayn, mahaifin mu babu abunda yake aikatawa da guminsa Ya tara kuɗin shi, wata’kil dama can me arzikine Ya dai 6oyene don baison agani, amma nidai ina kyautata mashi zato, kuma atm daya bamu don yaga muna buƙara kuɗine Yana so ne Ya faranta mana” Zayn ya natsu yana kallon dan uwan nashi ya haƙiƙance Yana yi mashi magana, sai da yakai ƙarshen Aya tukunna zayn yace”baka amfani da ƙwaƙwalwa, ta inda muka banbanta kenan, Zaid ka faɗa min wani ubane zai ɗauki maƙudan kuɗi irin wadannan yaba ƴa’ƴanshi don suyi sharholiya? Ba tare daya tambayi me zasu yi da kuɗin ba? uba na gari bazai ta6a aikata hakan ba, Ni bani ke bansan daddy ba, shine baison mu zaid! Saboda tun da muke dashi bai ta6a zaunar damu a matsayin shi na mahaifinmu yayi mana nasiha akan rayuwar duniya ba, ko lahirarmu, komai mu ka yi dai dai ne a wurin shi, Mommy ce kaɗai take tsawatar mana idan mu ka yi ba dai dai ba......” Tun da Zayn ya fara magana muryarshi a kausashe, idanuwanshi sun kaɗa sun ciko da ƙwalla, zaid dake sauraron shi, Yayi shiru yana kallon shi, Jikin shi ya fara yin sanyi, dakatawa ya ɗanyi yana faman fitar da huci, kafin ya ɗaura da cewa”idan har dagaske kuɗin shi ne meyasa be yi amfani da su ya gina mana gida na kanmu ba? bayan yasan duk irin gorin da ake yi mashi, hmmm kawai baison asan Yana da kudin ne don yasan za’a tuhume shi ina ya same su, shine kawai,” shiru su kayi ɗakin Yayi tsit na ɗan wani lokaci, “Kaina harya fara ciwo, Inaso in kwanta In huta” Zaid ne ya ambaci hakan tare da miƙewa Ya nufi closet din Kayansu dake acan cikin ɗakin, Kwantawa zayn yai saman mattress yayin da idanuwanshi suke fuskantar ceilling, abun ba ƙaramin ƙona mashi rai yake yi ba, Yana matuƙar jin ɗacin irin rayuwar da mahaifinsu yake yi. *Hajiya Saratu ❤* A tsaye take gaban mirror, jikinta sanye da Jallabiya, babu mayafi akanta, hakan ya bayyana kitson zanan dake akanta, hannunta ruƙe da wayarta ta karata a kunnanta, fuskarta da fara’a, ga dukkan alamu magana take yi da wani awaya. “Nayi mamakin ganin kiranki, Allah dai yasa lafiya, don nasan hakanan baki nema na, ba tare da wani ƙwaƙƙwaran dalili ba” On the other hand matar da suke yin waya ta soma magana, Daga jin muyarta babbar macace mai ji da qasaita. “Oh, saboda kada na fara yi maki ƙorafin baki kirana shine kika rigani yin magana”? Hajiya saratu na dariya tace”wallahi ba haka bane Hajiyata, abubuwane suka yi min yawa, amma duk da haka ai ina ƙoƙarin tura maki saƙon barka da juma’a, ke dai ce baki nemana, amma nayi maki uziri saboda hidindimun al’umma da kuke fama da su, nasan sune suka sanyaki busy” “Hakane, amma kada ki damu, dama dalilin dayasa na kira ki, game da zuwanmu gidane, Naga saƙon ankon da kika tura mini nagode, so abunda nikeson kiyi mini, Inaso ki fada min me baba yafi so”? murmushi saratu tasaki, Har cikin ranta taji dadin tambayar da tayi mata. “Gift ne zaki shirya mashi na birthday dinshi”? “Eh, na tambayi yayanki akan ya faɗa min me yafi so, kinsan halin shi, cewa yai shi baisani ba, Duk abunda yayi mini in siya mashi, Ni kuma nafi son abun zai burge shi sosai” Dariya hajiya saratu tayi tana fadin” Gaskiya baba ni kaina bazan Iya cewa ga abunda yafi so ba, amma kwanakin baya naji yana magana da abokinshi akan yana son suturar su na al’adar inyamurai, tun lokacin dai banji sun ƙara magana ba, kuma ba akawo kayan ba, idan har kika shirya mashi su a matsayin gift dinsa, Nasan zai yi farin ciki sosai kuma zaiyi mamaki” “Okey, Send me his measurements through WhatsApp, and please don’t let anyone know. I want to surprise him.” ta amsa mata da toh nima agaida mun da yayan nawa, ko na kira shi sai yaga dama yake ɗagawa, Ina nan ina jiran shi zamu haɗu ne” sautin dariyar hajiyarne ya cika kunnanta da ba’a tace”Ai kin fi kowa sanin yayan naki, sai dai ki ba wani labari” Sun jima suna waya kafin daga bisani sukayi sallama, Ajiyar zuciya ta sauke, tana ƙoƙarin zama gefen gadonta, Muryar Hajjaty ta katse mata hanzarinta, tayi mamakin jin sallamarta, don koda gigin wasa bata ta6a tako ƙafarta zuwa ɗakinta ba, Jim ta ɗanyi kafin ta furta”Wacece” ta fada tamkar bata gane me magana ba” “Hajjaty ce” jinjina kai Hajiya saratu tayi tuni mood din fuskarta Ya canza, jim ta ɗanyi kafin tace”zaki Iya shigowa” A hankali ta turo ƙofa ta shigo ɗakin, tun daga ƙasa hajiya saratu ta soma binta da wani matsiyacin kallo, pakistan ne ajikinta farare, ta ca6a uban ado, sai dai babu ƙamshin turaren nan, sai ka matsa kusa tukunna zaka Iya jin shi, hannunta biyu ruƙe da wooden tray, kayan abincine shaƙe asaman shi. Lamarin ya ɗaurewa Hajiya saratu kai, tayi sototo tana kallon ta Muryarta na ɗan rawa ta furta”Ina wuni” yamutsa fuska tai”da ban wani ba kin ganni, shin wai ma me ya akawo ki room dina? Makuwa ki kayi ne”? Fuska adaure ta mata maganar. Duk tasha jinin jikinta, adabarbarce ta furfa”am..umm...dama abincine na kawo maki, Ni na girka shi da kaina abincin ƙasar mu ne...” daƙyar ta ƙare maganar a tsananin tsoroce. Murmushin yaƙe hajiya saratu ta sakar mata”dama ke ce kike kawo min abinci? Ina masu aikin gidan ne? Ko sunyi yaji ne” “Suna a kitchen suna aiki, kawai nayi ra’ayin in kawo maki ne da kaina, nasan zaki ji daɗin girkin tun da baki saba cin kalar shi ba” hankalin ba akwance ba take yin maganar, Ruƙe ha6a hajiya saratu tayi tana faman jinjina kai tace”To fa, sabon salo, tanan kika biyo? An gaya maki bani da hankali ne da zanci abincin da kika girka da hannun ki? Wato bokan ki ya haɗo ki da maganin barbaɗe kin zuba min aciki shine ki kawo mun don inci in mutu saboda kinsan abinci ne lago na ko”? Hankalin Hajjaty ba ƙaramin tashi yai ba, cikin sanyin murya tace”Allah shine shaidata, tun da nake arayuwata ban ta6a takawa naje wurin boka ba, kuma ni banzo da niyar in cutar dake ba, abincine kawai na kawo maki, dan Allah ki kar6a ki ci......” Kafin ta ƙarasa maganar, Hajiya saratu ta dakata mata tsawar data firgitar da ita, jikinta ya kama kakarwa, nuna mata hanyar fita tayi daga ɗakin”Fuce min daga ɗaki tunkafin Inyi ƙwallo da tray din hannun ki, Ƴar rainin wayau, wallahi na fi ƙarfinki ba za ki ta6a cin galaba akaina ba, tunda can baki ta6a girka abinci kin kawo min don inci ba sai yau da kika shirya kashe Ni”? Tuni idanuwan Hajjaty sun cicciko tab da ƙwalla, cikin shessheƙar kuka tace”meyasa kika tsaneni? Laifin me nayi maki? Duk cikin masu aikin gidan nan ni kaɗaice ke bakiso, idan laifi nayi maki ki faɗa min sai in gyara” A tsawace Hajiya saratu tace”wai ke baki da hankali Ne? Kin manta wacece ni acikin gidan nan? Ko kin fara shaye shaye ne? Ni narasa gane wani tsautsayin ne ya kawo ki cikin ɗakina, I don’t know where you get the nerve to talk to me face to face, ke ga ta6ararra dallah fuce ki ban wuri” Juyawa Hajjaty tayi da sauri ta fuce daga ɗakin, Kamar zatayi tuntu6e, gutun tsoki Hajiya saratu taja tare da samun wuri ta zauna gefen gado, tana mai mamakin ƙarfin hali irin na Hajjaty. _~*✊💋BossLadiesWriters💋✊*~_ ~The return of Benazir~ سجن القدر❤🤍❤ Bayan fitar Hajjaty daga ɗakin Hajiya saratu, zafafan hawaye ne su ka wanke fuskarta, taji ɗacin maganganun da saratu ta faɗa mata, ita har ga Allah bada nufin komai taje kai mata abincin ba, dama Pravin ne ya bata shawarar ta rinƙa kyautata mata, wata’ƙil ta fara ƙaunarta, saboda ta faɗa mashi tana son su dinga shiri da matarshi. Kafin tabar ƙofar ɗakin sai da ta ajiye tray din ƙasa, ta share ƙwallar fuskarta, tukunna ta ɗauka ta nufi ɗakin twins da niyar ta kai masu abincin wata’kil su ci. A lokacin Zayn yana zaune saman gado Ya tasa laptop dinsa agaba Yana operating dinta, zaid kuma Yana a kwance gefenshi hannun shi ruƙe da Wayar shi Yana daddanna ta. Sallamar hajjaty ce ta janyo hankulan su ga duban ƙofar ɗakin. Zayn tamkar bai ji ba yai shiru yaƙi amsawa sai zaid Ne ya amsa mata tare da bata Iznin shigowa ciki, A hankali ta shigo da tray muryarta asanyaya tace”barkan ku da hutawa, fatan kun wuni lafiya” da fara’a akan fuskar zaid ya ce”lafiya lou auntyn mu, yau ke ce da kan ki ki ka zo kawo mana abinci”? Ya yi maganar tare da ajiye wayar shi ya sauko daga saman gadon Ya nufe ta, zayn ko kallo bata ishe shi ba, baiwar Allah taji daɗin sakar fuska da zaid ya yi har cikin ranta taji ta ƙara ƙaunar shi. “Abincin ƙasar mu ne, ni na girka shi da kaina, na kawo maku ne don ku ɗanɗana” hannu biyu zaid yasa ya kar6i tray din Daga hannunta yana fadin”gaskiya kina ji da ƴa’ƴan nan naki, wallahi munji daɗi, kamar kinsan kuwa yunwa muke ji, Yanzu nake shirin kira akawo mana abinci mu ci” Asaman table ya ɗaura tray din, sai faman sakin murmushi take Yi yayin da take kallon fuskar zaid, buɗe warmer ya fara yi, ƙamshin Abincin ya daki hancinsa, Jinjina kai yai tare da ɗago da ido Ya kalle ta”Aunty, Ya sunan wannan haɗin”? “Chicken tikka masala” ta faɗa still da murmushi kan face dinta. “Daga jin ƙamshin abincin zai yi daɗi, balle ma daya kasance hannu mai albarkane Ya girka sa” ya fada yana nade hannun rigarsa. “Zaid! Kada ka kuskura ka ci abincin nan! Kai baka da hankaline”? Ras taji gabanta ya fadi jin abun da zayn yace. Fuskar zaid a ɗaure ya dube shi”kaga bana son zancen banza, babu ruwanka dani, Kaja baki kayi shiru idan bazaka ci ba” Ya ƙare maganar tare da maida dubansa ga hajjaty “mun gode Aunty, Idan nagama cin abincin zaki ji feed back dina” jiki asanyaye ta amsa mashi da toh, da sauri ta fuce daga ɗakin tana faman sauke ajiyar zuciya. Ƙamshin Abincin da Zaid ke ci duk Ya cika mashi hanci da maƙoshi, dauriya ce kawai Yake yi, Yana danna laptop Haɗi da satar kallon Zaid, da gangan yake cuko spoon da abincin Yana turawa abaki, hada sambatun shi”wannan abinci kamar a aljanna aka dafa shi? Kai ka ji wani ɗanɗano mai daɗi, gaskiya duk wanda baici abincin nan ba an barshi a baya” Harara Zayn ya watsa mashi sam bai lura ba, saboda Ya bashi Baya. Ajiye spoon din ya yi cikin abincin, ya tsiyaya lemu mai sanyi acikin glass, Ya ɗauka Yasha rabi, Ya ajiye. “bari na ɗan shiga toilet” ya faɗa hadi da miƙewa da sauri Ya nufi toilet door ya shige, shigar shi ke da wuya Zayn ya janye laptop dinsa, cikin sanɗa Ya rarrafa saman mattress din zuwa gaban table din, Yana faman yamutsa fuska Ya ɗauki spoon Ya zura a plate din abincin aranshi yana fadin ba lallai ma abincin yai daɗi ba, mutuminka tun da yayi one spoon abaki, Tsabar daɗi kunnanshi har motsi suke yi, Yana ci yana satar kallon ƙofar toilet gudun kada Zaid Ya riske shi Yana cin abincin Hajjaty, a ƙarshe Ya ajiye spoon din Ya duma hannu ya ɗauko cinyar kaza Yadinga cizga Yana ci, Kusan Rabin abincin plate din ya cinye, ya ɗauki lemu Ya kur6a, Jin motsin za’a buɗe ƙofar toilet Yasa shi yin saurin sauke glass din lemun saman table, ko hannun shi bai goge ba, Da sauri Ya koma can saman gadon Ya jingina bayanshi jikin headboard ya ɗauki laptop dinsa Ya cigaba da operating dinta. Fitowa zaid Yai daga toilet, Yana faman yarfa hannun shi, Satar kallon fuskar zayn yayi, mutumin Ya haɗe rai babu annuri, Sai dai Ya manta bai goge bakinshi ba, yayi dama dama da maiƙon abincin da ya ci. Ƙayataccen murmushi zaid ya saki aranshi ya ayyana”babyn mommy ai nasan zaka aika, shiyasa na shiga toilet don na baka damar ka ci, ɗan rainin wayau anaso ana kaiwa kasuwa” Ya faɗa Yana zama bakin gadon, da zolaya yace”Zayn ya akai naga abincin dana rage an ci shi”? Muryar zayn ba wasa yace”ka tambayi wanda kaba ajiya, Ni meye ruwana aciki”? Gumtse dariya Zaid yai”amma dai da kunya wallahi, Ni dai nasan babu 6era agidan nan” rai a6ace zayn yace”ban san iya shege zaid, Uban waye 6eran”? “Ai ni ban kama suna ba, kawai nayi maganata ne” dogon tsoki Zayn yaja yana faman hura hanci, Aranshi ya ayyana Ina ma zaid Ya rage abincin da kuwa ya cinye shi duka, don ba ƙaramin daɗi yayi mashi ba. *SIR MUBARAK🤍* A Hankali Yake tafiya Yana tunkarar ɗakin Dr. Jazz, Daga shi sai short A jikin shi da singlet, Tura ƙofar Yayi baiga kowa a ɗakin Ba, shiga Ciki Yai Yana bin ko’ina da Kallo zanin gadonshi a hargitse Takalman shi Yashe saman floor, tunani ya shiga yi aranshi ko ina ya shiga? Ko dai yana a toilet ne Ko ya shiga Garden, Yanke shawarar zuwa garden ɗin ya yi don Ya dubo shi, Ahanzar ce Ya juya da niyar ya fuce kwatsam Muryar Jazz ta katse mashi hanzarin shi. “Oh tsayawa za ka yi Kana kallonta? Babu abun da zaka Iya yi mata? Sai kace ba ka san Hanyar da zaka kashe ta ba idan haukanta Ya motsa”! wani irin bugu zuciyar Sir Mubarak Tayi Jin Kalmar Kisa, A firgice ya juya baya Yana bin toilet door ɗin ɗakin da kallo, don Ya fahimci acikin toilet yake Yin wayar, Cikin tafiyar sanɗa Sir Mubarak Ya nufi ƙofar toilet Ɗin Ya kanga kunnan shi Yana sauraron shi. “Ai ba dole Saina zo ba, Kaima zaka Iya sarrafata, Idan taƙiya Kawai ka bi Hanyar da nace maka, ka kashe ta kowa Ya huta,” shiru Ya ɗanyi can kuma yaji yaci gaba da cewa”ba yadda za’ai inzo, Ina tsoron asirina Ya toni, hmm bakasan halin da nake aciki ba, ko jiya saida na kamo Hanya zanzo gidan, ganin ana bin motata yasa na karya kwana na nufi asibiti, saboda raina ya bani akwai wanda ke bin diddigina dole Inyi takatsantsan” Hankalin Sir Mubarak Ba ƙaramin tashi yai ba, sai faman jinjina kanshi yake Yi, Bai ta6a tsammanin Jazz Yana da wayau ba sai Yau, Har yasan Ana bibiyarshi wato shine Ya canza Hanya, Hakan ya ƙara tabbatar mashi da zargin shi akanshi. “What are you doing here, baby?” Muryar Turai ce ta ratsa kunnanshi, Hatta dr Jazz dake a toilet, Sai da Ya ji sautin muryar mutun a ɗakin shi, a yayin da yake atsaye gaban sink, wandon crazy jeans ne da shirt a jikin shi, da sauri Yai rejecting call din Ya tura wayar cikin aljihun wandon shi, Jikinshi Ya hau Yin kerma, Tsananin fargabane Ya kama shi, A hankali Yake tafiya yana nufar ƙofar fita, Kafin fitowarshi da sauri Sir Mubarak Yai wuff Ya nufi Turai dake kallonshi da mamaki akan face dinta ganin Yadda ya ke yima Jazz la6e a ɗaki, Harta buɗe baki zata ƙara yin magana ya yi saurin sanya faffaɗan tafin hannunsa Ya toshe mata bakinta, tare da janta zuwa wajen ɗakin. Lokacin da Jazz ya fito daga toilet din zufa na bin fuskarshi, ya dubi ko’ina baiga mutun ba, Nauyayyar ajiyar zuciya ya sauke, har wajen ɗakin Ya leƙa bai ga kowa ba, Hakan yasa shi kokwanton wata’ƙil Kunnuwanshi ne suka jiyo mashi ba dai dai ba, hankalinshi ya kwanta, komawa ya yi cikin ɗakin Ya kwanta saman gadonshi, yayin da idanuwanshi ke fuskantar ceilling, ga dukkan alamu wani abu yake tunanowa wanda yasa shi fitar da ƙwalla a idon shi. A bedroom Sir mubarak Ya shigar da turai suna tsaye suna kallon juna, kallon tuhuma take bin shi da shi. “Nayi mamakin ganinka a ɗakin Jazz kana yi mashi la6e, meyasa”? Fuskarshi a murtuke babu annuri yace”laifi ne don uba ya shiga ɗakin ɗanshi”? Aruɗe tace”ba laifi bane, amma meyasa kake yi mashi la6e”? Shiru ya yi yana duban fuskarta, A yadda suke atsaye suna fuskantar juna, Ko kafaɗarshi bata kai ba, saboda ƙarantarta, doguwar rigace a jikinta ta shan iska, ta tufke blonde hair dinta da ribbom. “Ka tsare ni da ido kana kallona, Baka bani amsar Tambayata ba”! a ƙagare ta faɗa, Ya rasa ya zaiyi ya kawar da hankalinta daga tambayar da take yi masa. Dubara ce ta faɗo masa, da sauri Ya sanya Hannu biyu ya ruƙe waist dinta, sama ya ɗaga ta kamar ɗiyar roba Ya kwantar da ita saman gadon shi Rumfa ya yi mata da faffaɗan kirjin shi, tuni tasha jinin jikinta. “Kin tsareni da tambaya ke ga mai ɗa ko? Ni da ke waye yafi wani iko da shi? Yawu ta haɗiya muryarta na ɗan rawa ta furta”kai” “Kinsan da hakan shine kike yi min tambayoyi kamar ƴar jarida”? Shiru tayi mashi tana faman zazzare green eyes dinta. “Jibarki ƴar mitsila dake kamar in matseki nake ji” dariya ce ta kubce mata, natsuwa yai yana kallon fararen haƙoranta. “Yanzu dai faɗamin me kike shiryawa a birthday din Baba? Ba za kiyi kitso da ƙunshi ba”? “Idan zaka kai ni inda za’ai min kitson da ƙunshin inaso, sai dai anko din da zasu sanya nasan hajiya saratu bazata barni in shiga cikinsu ba ko da na siya” a marairaice ta ƙare mashi maganar. Jan hancin ta ya yi da hannun shi”Ina ruwanki da ita? Ai ba dole sai kin shiga cikinsu ba, babban tarone fa za’ayi akwai manyan baƙi da zasu zo, kema zaki samu ƙawaye acikin su” Da shagwa6e ta furta”baby ba zaka gane ba, hajiya saratu bata son ganina, ita fa haryan zu kallon ƴar aiki take Yi mini, hada faɗa min wai ba ata6a canzawa tuwo suna, ni dai inajin fargabar ta disgani acikin su, ƙwara Inyi zamana acikin gida zai fiye min kwanciyar hankali” daƙyar ta ƙare maganar ganin yadda ya tsare ta da ido, kallon so da ƙauna ya ke yi mata. “Meyasa kike kira na baby? Ko kunya bakya ji? Nayi maki kama da ƙaramin Yaro ne?” fuskar shi a ɗaure yai mata maganar. Kashe mashi ido ɗaya tayi”I call you baby because you’re like a baby to me, and I still take care of you kuma ina feeding dinka” ɗan zaro mata ido ya yi da sauri ta rufe baki tana faman zazzare mashi ido. Da zolaya ya furta”raini ya fara shiga tsakanina dake, saboda ina tu6e kaya agabanki ko”? Runtse mashi ido tayi tana faman tiƙar dariya. Jinjina kanshi yai”ki saurare dakyau, daga yanzu idan saratu ta faɗa maki magana ki dinga mayar mata da martani, ki daina nuna kina jin tsoronta shiyasa ta rainaki, Kina jina ko”? Tana faman zumbura mashi pink lips dinta tace”ni bazan Iyaba, saboda ta girmeni ko a shekaru kuma ƙanwarka ce,” “Umarni nake baki ba shawara ba, kada na kuskura na ƙara ganin kin dawo gidan nan kinayi min jan ido akan saratu tayi maki wani abu, idan ba haka ba zaki kar6i horo mai tsanani daga gareni,” muryar shi a kausace yake yi mata maganar Kama kunnanta ya yi da yatsan hannun shi”Idan kunne Ya tsira”? Da sauri ta ƙarasa mashi karin maganar”Jiki Ya tsira My baby” murmushi yasaki tare da manna mata kiss saman soft lips dinta. *GIDAN ƊAN IYA* Zahra ce zaune saman prayer mat, ta zumbula dogon Hijabi, fuskarta sharkaf da hawaye, tun da ta kammala sallar Magrib bata motsa ba, hannunta ruƙe da cazba sai faman janta take Yi, damuwar duniya ta isheta, tun ɗazu data farka daga bacci ta kasa Yin wanka ko abinci bata ci ba, babu kuma wanda yai tunanin ya leƙo ta, tayi trying kiran layin mahboob yaƙi picking call din, har yanzu bai leƙo cikin gidan ba, ga lokaci yana ta tafiya gani take yi kamar ana ƙara gudun agogon ɗakinta, hannayenta biyu ta ɗaga sama tana jera addu’o’i akan Allah Ya kawo mata mafita. Muryar Aneelerh ce ta ratsa kunnanta”Yar uwata rabin raina, tun safe baki ci komai ba, Ga abinci na kawo maki” Shafa tafin hannunta tayi saman fuskarta, Rai amatuƙar 6ace ta yunƙura ta mike haɗi da fuskantar Aneelerh, dake tunkarota, hannunta ruƙe da madaidaicin tray, mai ɗauke da plate din shinkara da ƙaramar warmer ta miya, tare da lemu mai sanyi. Kafin ta ƙaraso zahra ta dakatar da ita ta hanyar yi mata magana”Aunty Aneeleeh idan kin kawo abincin nan domin in ci ne to ki maida shi kitchen! Bana buƙata” a faɗace ta furta. “Haba zahra, kashe kanki ki ke so Ki yi ne? Tun safe baki ci komai ba, Ni kaɗai na damu dake, dan Allah ki kar6a ki ci” Harara zahra ta wurga mata cikin 6acin rai tace”Ai ni kingama zubda girmanki a idona, tun da har kika iya bani shawarar In amince wurin aikata sa6on Allah, Kin ban mamaki aunty aneelerh, bansan haka kike ba” tana magana tana jan majina. Jinjina kai Aneelerh tayi”Laifina ne zahra, Ni da na damu dake shiyasa kike gaya min magana son ranki, daga taimako? Daga yau ka da ki kuma tsammanin zan ƙara baki shawara idan har baki kar6i abincin nan ba” wani ɗan iskan kallo Zahra ta watsa mata, har saida ta dasa aya amaganarta tukunna zahra ta ruƙe qugu kamar ana tunzurata tace”Idan har kin damu dani, meyasa ba zaki taimaka mu nemi mafita atare? Saima ƙoƙarin da ki ka yi don ganin kin sanya ni a gur6atacciyar hanyar da zan lalata duniyata da lahirata, ke ba mai ƙaunata bace aunty Aneeleeh, bana sonki kuma bana son ganin ki!, Yakamata ki nisanta kan ki dani, Idan ba haka ba zan yi maki rashin mutuncin da baki ta6a tsammani ba!!” A kausashe Ta furta maganar tana nuna Aneelerh da cazbahar hannunta kamar zata rufe ta da bugu. Gyaɗa kai Aneelerh tayi tama rasa bakin magana, kalaman zahra sun bata mamaki, bata ta6a tunanin zahra zata Ya furta mata su ba. Juyawa ta yi da sauri ta nufi ƙofar fita, adai dai lokacin Mahboob yana ƙoƙarin shigowa ɗakin suka ci karo da Aneelerh, har gaishe ta ya yi amma ko kallon shi ba ta yi ba, hakan yasa shi tsammanin ko wani abu Ya faru ne. Zahra na jin sallamar shi da sauri ta sanya hannu biyu ta share hawayen dake akan fuskarta, komawa tayi daga gefen gadonta ta zauna tana dubanshi. Riga da wandon shadda ne ajikinshi, hannun shi ruƙe da key din motar shi. “Zahra Lafiya ki ke yi mini kiran talauci? Ina akan hanyar dawowa gida naga miss calls dinki, Allah dai yasa lafiya” Cikin sanyin murya tace da shi”ka zauna mahboob mu yi magana” zama yai da ɗan mamaki akan face dinsa yace”meyasa ki kuka? Naga idanuwanki sun kumbura wanene Ya ta6a ki? Ko ke da aunty Aneelerh ne”? A hanzarce ta girgiza mashi kai tana faɗin”bakomai, banajin daɗi ne kaina ke ciwo” “Kin sha magani” cikin kulawa yake yi mata magana, ɗaga mashi kai tayi alamar eh ta ƙara da cewa”Aunty Aneelerh ce ta bani maganin” Gyaɗa kai yai”okey, Allah ya sawaƙe sister yanzu dai faɗamin me kike buƙata ne Kin dai san ban da ko sisi” Murmushin takaici tasa kar mashi jin abinda yace “Mahboob ba kuɗi zan roƙe ka ba, taimako nakeso kayi min dan Allah, bana son ka tambayeni dalili kawai ka yi abun da nace maka, kuma bana son kowa Ya sani daga ni sai kai” “Kada ki damu, Ina jin ki” a ƙagare Ya furta mata hakan “Inason zan siyar da motata ne da wayata, saboda ina buƙatar kuɗi ko akwai wanda ka sani da zai Iya siya a yau din nan’? Ta jefa mashi tambayar tana duban fuskarshi. Mamakine ƙarara akan fuskarshi, Har saida Yaɗan saki baki da ido Yana dubanta Kafin yace”ke kuwa me zai ja ki siyar da motarki da wayarki? Runtse ido ta dan yi hawaye na ƙoƙarin cin ƙarfinta tace dashi”Mahboob banason tambaya! Kawai ka taimaka mun in zaka Iya in kuma ba za ka yi ba to ka tashi ka tafi kaban wuri” “Shikenan Naji, nayi shirun, amma dai kinsan kowa zai saye su sai kin faɗi ko? Ba lallai asamu wanda zai siya da mutunci ba” Ɗaga mashi kai tayi”Ni wannan ba damuwata bace, indai kuɗin zasu kai 4m Ya wadatar” “Okey, amma ni shawarar da zan baki mai zai hana ki bada motar da wayar taki jingina? Idan kika samu halin biyan kuɗin sai ki Kar6o Kayan ki, zahra kinsan babu mai siya maki su idan kika rasa na hannunki kuma ni bazan juri ara maki motata ba” Ya faɗa Yana yamutsa fuskarsa, Harara ta watsa mashi da rinannun idanuwanta”kai fa banza ne wlh, Ni ina ruwana da motarka? Koda zan rasa abun hawa mahboob bazan ta6a aron kayanka ba” Murmushi ya ɗan saki tare da miƙewa yace”to Aunty zahra, Ni zan tafi, in sha Allah zan samu wanda zai siya, amma ki sani zamu kasa kuɗin gida uku, Ki kwashi kaso biyu ni kuma ɗaya....” Tunkan ya ƙare maganar zahra ta rarumi pillow aguje tabi shi da gudu ya fuce daga ɗakin Yana tiƙar dariya muryarta ashaƙe take fadin”wallahi mahboob ka fita idona, Ni ba tsarar wasanka bace, kuɗin nan da gumina na tarasu bada gumin wani ba’ rai a6ace take yin maganar, bayan ta gama zazzaga mashi masifar ta juya ta koma cikin ɗakinta tana faman tallabe cikinta dake yi mata kukan yunwa. Safa da marwa ta soma Yi A tsakar dakin duk ta ƙagara da jiran kiran mahboob, Fatanta Allah yasa asamu wanda zai sayi motar. Wuraren ƙarfe 8 na dare, Kiran mahboob Ya shigo wayarta jiki na rawa ta ɗaga ta kara a kunnanta, Anan yake sanar da ita cewa abokinsa Ya ce yana so harma sunyi cinikin motar akan miliyan uku da rabi zai siyeta, ita kuma wayar zai siyeta dubu ɗari biyar idan ta bari ahakan zuwa gobe da safe zai kai mashi Motar da wayar, daga nan zai tura mashi kuɗin, tsabar farin Ciki kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha, duk da tayi asara ba kaɗan, saboda an karya kuɗin motar da wayar, amma hakan bai dameta, burinta ta sauke nauyin dake akanta, Bayan sun gama wayar, ta zuƙunna takai goshi ƙasa tana godiya da Allah, daga bisani ta mike tana tiƙar rawa, da gudu ta fito daga ɗaki ta nufi kitchen, ta ciko plate da abinci, ta buɗe frigde ta dauko lemu mai sanyi kafin ta dawo ɗakinta, ita kadai ta zauna tsakiyar gado tana ci tana sakin murmushi, baƙin cikinta ɗaya ta rasa damar da take da ita na zuwa Obie estate, tunawa da wannan yasata rushewa da kuka ga abinci cike abakinta. *JOS CITY* Dare ya tsala sosai, Gari yayi duhu, a lokacin da kowani mahaluƙi yake a makwancinsa domin runtsawa, baka jin sautin komai saina kukan tsuntsaye dana karnukan Layi dake Hargowa. A hankali take tafiya Hannunta ruƙe da trolley, doguwa ce a halitta, siririya bata da ƙiba sai dai tana da hips, doguwar jallabiyace a jikinta, ta sanya niƙab ta rufe fuskarta, abun da zai baka mamaki ita kaɗai take Bin santar babu alamun tsoro atattare da ita, da taimakon street light ta ke samun damar ganin ko’ina, Har Allah Ya nuna mata gidan da take nema, Katafaren Villa ne Mai gingirimeman gate. da sassarfa ta nufi gate din, tana zuwa gabanshi, Takai hannu ta soma ƙwanƙwasa ƙofar, tun tana yi a hankali har takai ga tsunto dutse ta cigaba da bugun ƙofar da shi kamar zata 6alle gate din’ Security officers din dake tsaron gidan guda Biyu ne cikin kakinsu suka fito daga ɗakunansu jiki na rawa suka ƙara so gaban gate din, da alamun mamaki akan fuskokinsu suka haɗa bakin wurin furta Wanene ke buga mana ƙofa a dai dai irin wannan lokacin”! Da fargaba suka furta maganar. Cikin shessheƙar kuka da muryarta mai tsiwa ta furta”BENAZIR CE” kallon Juna Officers din suka Yi, ɗaya yace”Wanene kuma haka? Mutun ko aljan? Wa ki ka zo nema agidan ko dai kin yi 6atan Hanya ne” Tamkar zata fashe da kuka tace”dan Allah ku buɗe mun gate in shigo, ni ce benazir ɗiyar Alhaji ubaid”! Ba ƙaramin ɗaure masu kai lamarin yayi ba, kasancewar su tsoffin masu gadin gidan, sunsan wacece benazir Yarinyar uban gidansu data 6ace tsawon shekara goma sha shidda, kokwanto suka soma Yi anya kuwa itace? Officer mai gemu yace”kai, Da wuya ya zama gaskiya yarinyar da babu tabbacin tana araye kota mutu”! Ɗayan kuma yace”Ai ni banma yarda ba gaskiya, Kusan shekara goma sha shidda da 6atanta sai Yau ƙarfe sha biyu na dare zata dawo! anya kuwa ba tarko bane aka ɗana mana”? Mai gemu yace”amma kuma muryarta sak kalarta hajiya layla, Har tsiwar iri ɗaya da tayi maganar” Jin sunƙi buɗe mata kofa yasa ta rushe masu da kuka mai sautin gaske a faɗa ce ta ke fadin”wai baza ku buɗe mun gate ba, na gaji da tsayuwa wallahi idan baku buɗe ba na shigo cikin gidan saina Sa an kore ku” Yawu suka haɗiya atare mai gemu yace”Ke baiwar Allah, ba yadda za’ai mu buɗe maki gate ba tare da mun sanar da masu gidan ba, dan haka ki ƙara haƙuri mu faɗa masu” Kafin suyi yunƙurin zuwa cikin gidan su sanar masu, ba zato ba tsammani suka ji ta bangaje ƙofar jikin gate din dake a kulle, nan take ƙofar ta buɗe, hankalin su ba ƙaramin tashi Yai ba, A firgice suke dubanta yayin da take shigowa ciki da akwatinta, Ko kallo basu isheta ba, da sauri ta nufi cikin gidan. Kasa motsi suka yi Kamar an dasa masu Aya, tuni zufa ta wanke fuskokinsu, Mamakin su Taya akai ta Iya bugun ƙofa da ƙarfi Har jamlock mai ƙarko Ya zame kanshi! Tabbas suna hasashen ba mutun bace aljana ce, tuni suka sha jinin jikinsu. Tana tafiya tana bin ko’ina na gidan da kallo, abubuwa da dama sun canza mata ba kamar yadda ta tafi tabarshi ba. Adai dai lokacin Zainab mai aikin gidan tana a palour hannunta ruƙe da floor wiper tana goge tiles, ta saba ba tun Yau idan bata son aiki Yayi mata yawa takan fito har tsakar dare Tana aikace aikacen ta don ta rage wasu ayyukan na safe duk idan taji ƙarfi a jikinta. Tamkar da rana saboda hasken Ƙaton kwan dake a falon Ya gauraye ko’ina, Hankalinta kwance ta duƙufa tana gudanar da aikinta ba zato ba tsammani taji an banko ƙofar falon. A firgice Zainab ta ɗago tana kallon matar da ta fado cikin falon afujajen, tsabar firgitar da ta yi har batasan sa’adda ta jefar da wiper din hannun ta ba, tun daga ƙasa har sama take kallonta, Hankalin ta ba ƙaramin tashi yai ba, tsananin tsoro Ya kamata, Jikinta ya hau yin kerma, Muryarta na rawa ta furta”baiwar Allah wacece ke? taya ya akai kika shigo gidan nan? Ƙarfe sha biyu na dare”? Aruɗe take jefa mata tambayar. Shessheƙar Kukan matar ne Ya ƙara firgitar da ita, ta soma Ja da baya tana ƙoƙarin guduwa cikin gidan don ta faɗo ma Hajiya layla abun da ke faruwa sai dai kafin Ta juya muryar Matar ya ratsa kunnanta cikin harshen larabcin take faɗin. “AUNTY ZAINAB NI CE BENAZIR!! INA ABBANA! INA UMMI NA! INA MIJINA DA ƳA TA!!! A jere ta jefa mata tambayoyin. Har abada ba zata ta6a mantawa da muryar nan ba, koda kuwa amafarkine Ta jita tabbas zata shaida mamallakiyarta. A hargitse Ta juya Tana dubanta, A hankali benazir ta ɗaura ziraran yatsun hannun ta farare tas ta ruƙo ƙasan niƙab ɗin fuskarta ta ɗage shi sama” tsabar kiɗima da ganin fuskar da tayi kimanin shekaru sha shidda ba ta yi tozali da ita bane yasa Jikinta ya hau yin kerma, tsantsar mamaki da al’ajabi ne akan fuskarta, ta zazzare idonta akan kyakkyawar fuskar benazir, sam takasa yarda da abun da idanuwanta ke nuna mana gani take yi tamkar mafarki ne take Yi!! Tayi wani irin haske Kamar ka ta6a jini ya ɗigo, Fuskarta sharkaf take da hawaye ta ko’ina, ga zufa dake tsastsafo mata sam babu kwanciyar hankali atattare da ita. Tsantsar tashi hankaline Akan fuskar zainab, Muryarta adabarbarce ta furta”be..be..nazir! Dagaske ke ce ko dai idanuwana ne suke nuna min ba dai dai ba”? Da ƙarfi ta furta”Ni ce Aunty zainab! Ki amsa min tambayoyin da nayi maki”! Tana faɗin hakan Nan take Ta yanke jiki Ta faɗi ƙasa a sume, akwatin hannunta ya kife saman floor. Juyawa Zainab tayi da gudun gaske ta nufi ɗakin hajiya layla, Hada yin tuntu6e tsabar sauri, tunkafin ta ƙarasa ta soma ƙwala mata kira na fitar hayyaci tamkar maƙoshin ta zai 6allo waje. “Hajiya layla! hajiya layla” Kaitsaye kiran ya daki dodon kunnuwan su daga ita har Alhaji ubaid dake kwance saman katafaren gadonsu, A firgice suka farka a lokaci ɗaya suka miƙe zaune suna ambaton Sunan zainab. Doguwar jallabiya ce a jikin alhaji ubaid wuyan rigar ya karkace, Hajiya layla kuwa Rigar Bacci ce a jikinta, da sauri Alhaji ubaid ya kunna bedside lamp din ɗakin. Sam babu kwanciyar hankali atattare da su, duk sun ƙura ido suna jiran ganin ta inda zainab zata 6ullo. Kamar daga sama suka ji ta banko ƙofar ɗakin tana faman Yin haki. Da mamaki Akan fuskar Layla tace”Zainab baki da hankali ne? Ko kin makance ne? Taya zaki faɗo mana ɗaki a irin wannan lokacin ba tare da kin nemi iznin shigowa ciki ba”! Kafin zainab ta bata amsa Alhaji ubaid Ya katse mata hanzarinta da cewa”Zainab Lafiya kike ƙwala mana kifa? Kowani abun ne Ya faru”? Cikin rawar murya ta furta”dan Allah kuyi haƙuri ku yafe ni, bana acikin kwanciyar hankalina ne shiyasa na faɗo maku ɗaki ba sallama nasan bai dace ba” dogon tsoki Layla Taja”Ba dogon bayani na tambaye ki ba, Ki faɗi min uban mi Ya kawo ki ɗakin mu? Bata kai ga ƙarasa maganar ba, Alhaji ubaid Yai saurin katse ta da cewa”Ya isa haka, Haba kin cikata da faɗa, Kin ƙi bari tayi mana bayani dangane da abunda ke faruwa” tsuke fuska Layla Tayi. Cikin sanyin murya zainab tace”dama BENAZIR ce ta dawo!” Kallon juna Alhaji ubaid da layla suka Yi lokaci ɗaya, kafin suka dawo da dubansu ga zainab, Har suna haɗa baki wurin tambayar wacece Benazir!! Tsabar ruɗanin da suka shiga Zainab tace”benazir ƙanwar dr shureim Ƴar wurinku itace ta dawo, Yanzu haka tana acikin palour ta yanke jiki ta faɗi a sume. Girgiza kai layla tayi haɗi da cewa”baki da hankali zainab, dama na fara zargin kin fara shan ƙwaya, In ba haka ba, ta ya ya benazir da ta gudu da ƙafafuwanta zata dawo gida! bazai yiwu ba. Alhaji ubaid Yace”ko dai mafarki ki ka yi ne zainab? Girgiza mashi kai tayi hada hawaye akan fuskarta tace”wallahi dagaske nake yi zaku Iya zuwa palourn ku duba benazir ce da kanta ta dawo” Kusan atare suka sauko daga saman gadon, da sauri zainab ta basu hanya suka fuce har suna bange juna tsabar sauri. Tunkafin su ƙarasa falon suka soma hango mutun kwance saman floor da baƙaƙen Kaya ga trolley dinta a gefe ɗaya, kasancewar ta yaye niqab din fuskarta hakan ya basu damar ganin fuskarta, wani irin mahaukacin bugu zuciyarsu tayi A matuƙar gigice suka furta sunanta”BENAZIR” adai dai lokacin gate security officers din gidan suka shigo falon da sallama sam babu kwanciyar hankali akan fuskokinsu ganin Yanayin mutanan gidan yasa suma suka ƙame suna faman zare ido. Muryar Hajiya layla Na rawa ta furta”wallahi itace Benazir ɗina ce, Yarinya tace data 6ata, itace ta dawo da kanta” ta ƙare maganar jiki na 6ari ta nufi gaban Benazir dake kwance ta zube saman gwiwowinta tare da kai hannu ta ruƙo niƙab din fuskarta ta ƙarasa cire mata shi, Kowa dake a falon saida yai matuƙar Al’ajabin ganin Benazir, yalwataccen gashin kanta har gadon bayanta Ya nannaɗe kamar taliyar indomie, babu alamun wahala atare da ita, sai ma hutun dake kwance saman farar fatarta, wani iko na Allah, gaba ɗaya Jikinta Ya jiƙe da ruwan zufar dake tsastsafo mata, hatta baƙar jallabiyar jikinta ta manne ma fatarta saboda zufar data wanketa, ga wata zufar dake kurɗaɗowa ta cikin sumar kanta ta jiƙe sharkaf duk da sanyin A.c din falon. Rushewa da kuka Hajiya layla tayi haɗi da ɗaura Hannayenta biyu saman kanta tana fadin”Inna lillahi wa’inna ilaihirraji’un! Dan Allah kuyi wani abu akai mana kun tsaya kuna kallonta, sai kace baku gane ta ba, ɗiyata ce benazir Allah Ya dawo mun da ita da ranta” Sautin kukan ta ya cika ɗakin, Zainab ma tuni ta fashe da kukan farin ciki, security officers dake tsaye Jikinsu ya yi mugun yin sanyi, da farko sunyi tsammanin ba mutun bace amma daga bisani Bayan ta shigo cikin gidan suka dudduba ƙofar donsu tabbatar mutun ce ba aljana ba, ashe Jamlock ɗin ƙofar gate dinne basu kulle shi ba sun manta, shiyasa har ta samu damar sanya ƙarfi ta bangaje ƙofar ta shigo ciki. Mamaki da al’jabi sun Hana Alhaji ubaid motsawa Ya kafe fuskar Ƴar tashi da ido Yana kallonta, ruwan hawaye ne kwance acikin idanuwanshi haƙiƙa ya yi farin ciki mara misaltuwa kusan shekara goma sha shidda Yau rana ɗaya Allah Ya kaɗo masu da hankalinta ta dawo wurinsu, Allah ne kaɗai Yasan uwa duniyar data shiga. Cikin shessheƙar kuka zainab tace”yakamata muyi wani abu akai, Benazir tana buƙatar taimakon gaggawa, ga dukkan alamu wani abunne Ya faru da ita wanda Ya haifar mata da fitar da gumi a jikinta” Da sauri Alhaji Ubaid Ya sanya Hannayenshi biyu, Ya cuccu6eta Ya juya ya nufi sofa mai mazaunin mutun uku Ya kwantar da ita, kallon zainab yai”je ki ɗauko min wayata a ɗaki” ta amsa mashi da toh, da ɗan gudunta ta nufi bedroom dinsu. Jiki amace layla ta miƙe ta koma saman sofa hand din da benazir ke akwance ta zauna tana duban fuskar ƴartata Kamar Ta haɗiyeta haka take ji. “Alhaji kun tabbata benazir ɗinmu ce ta dawo”! Mai gemu ne Yai mashi Maganar, Jinjina masu kai Yai”babu shakka itace Allah ya dawo mana da ita” Ajiyar zuciya kowan nan su Ya sauke tsantsar farin ciki Ne Ya kamasu. “Muna tayaku murna, ita kuma muna yi mata fatan Allah Ya bata lafiya, Ubangiji Allah yasa ƙarshen wahalarta kenan, sannan Alhaji Muna baku shawarar a kira malamin da zai dubata don yanayinta dana gani a matsayina na wanda yake da sani a 6angaren sihiri, Yarinyar ka ba likita take buƙata ba, Malami take buƙata saboda duk wasu alamomi na jikinta sun nuna kamar sihirine daya daɗe a jikinta ya kwance !!! A firgice Alhaji Ubaid Da Hajiya layla suka ɗago suna duban mai gemu da yayi maganar, jinjina masu kai yayi”ba yau na fara ganin irin hakan ba, ina da tabbacin Yarinyar nan kurciya aka yi mata, amma idan kunaso ku gasgata zance na ku kira babban malamin da zai dubata” sam sun kasa magana sai bin shi da kallo da su ke Yi. Daƙyar Hajiya layla Ta iya buɗe bakinta la66anta na kerma tace”amma benazir da ƙafafuwanta ta gudu tabar gidan tajudden Bayan ta haihu tabar mashi jinjira a cikin kwamin wanka, tayaya hakan zai yiwu? Wanene zai yi mana hakan? Girgiza kai mai gemu yai”haka zakuyi tunani saboda bakusan dalilin tafiyarta ba, amma abun duba anan tayaya Uwa zata gudu tabar jinjirin ɗan da ta haifa ta hanyar raya sunna!! Duk irin soyayyar dake tsakanin uwa da ɗanta? Sannan idan har dagaske benazir ta gudu don son ranta tsawon shekara goma sha ɗaya meyasa zata dawo da ƙafafuwanta ba’a cikin Hayyacin ta? Ga zufa duk ta wanke suturar jikinta, Nidai shawarar da zan baku shine a tuntu6i malamin da zai dubata” Jinjina kai Alhaji ubaid ya yi shi kanshi jikin shi ya yi sanyi da zancen Mai gemu, saboda akwai ƙamshin gaskiya a kalamanshi. Shigowa falon Zainab tayi hannunta ruke da wayar Alhaji ubaid Ta miƙa mashi, Yasa hannu Ya kar6a. “Dare Yayi yanzu, kada mu katse ma wani baccin shi, shawarar da zan bada shine a ɗebo ruwa a yayyafa mata in sha Allah zata farka, zuwa asuba sai a kira malamin da zai dubata” mai gemu ne Yayi maganar, muryar Alhaji ubaid a sanyaye yace”Inaso zan kira Dr shureim ne, saboda a irin wannan lokacin baya runtsawa Idonshi biyu Yana tashi domin Yin nafilfilin dare” ya ambaci hakan tare da Danna wayar hannunshi ya buga ma dr shureim Kira ta soma ringing. Kallon zainab Hajiya layla tayi idanuwanta sun kaɗa jawur tace”ɗauko mun ruwa a fridge “ amsa mata zainab tayi da toh, da sauri ta nufi hanyar kitchen. Dafe kai Hajiya layla tayi da hannu ɗaya, Sumar kanta duk ta tarwatse saman bayanta, ta manta da yanayin jikinta, don ma babu wanda ke acikin natsuwar shi, hankalinsu na akan Benazir. Bayan zainab ta dawo, hannunta ruƙe da bottle water me sanyi ta buɗe murfin ta miƙa ma Hajiya layla, Yayyafa mata tayi saman fuskarta, nan take ta sauke nannauyar ajiyar zuciyata muryarta da tsiwa take fadin”ina mahaifiyata Ina mahaifina! Ina mijina da ƴata Ina yayana shureim, suna ina ! Na shiga uku na bani na lalace Na rasa kowa nawa, wayyo Allahna na shiga Uku wallahi gida zan koma Nabar Yarinyata cikin Jini, tajuddeen kai na bama amanar ɗiyata nasan bazaka bari rayuwarta ta wulaƙanta ba. Dan Allah ka bani Ƴata ita nake son gani’ tunda ta fara sambatun nan zainab da hajiya layla suka fashe da kuka suna kallonta, ta runtse idanuwanta sai faman ciccije le6enta take Yi da haƙoranta tuni suka soma faffashewa, jini Ya soma tsastsafowa, dunƙule hannu tayi tana buge buge, da sauri zainab da hajiya layla suke rurruƙeta sosai suna ambaton sunanta *DR.SHUREIM❤* Lokacin da Kiran Alhaji Ubaid ya shigo wayarshi, Yana a zaune saman darduma cikin shiga ta larabawa, Yayi nisa acikin karatun qur’nin dayake yi Kiran Ya daki dodon kunnanshi, Hakanan yaji gabanshi Na faduwa, aranshi ya ayyana kowa ne ne ke kiranshi a tsakar daren na! ya salam, Sai da yakai ƙarshen Aya tukunna Ya zabura Ya miƙe Ya nufi wayar dake ajiye saman side drawer ya ɗauke ta yana duban Screen din, Hankalin shi ba ƙaramin tashi yai ba ganin sunan Abie dinsa Ya bayyana, kafin Ya ɗaga kiran saida Ya fara kallon agogon bango ƙarfe ɗaya da rabi na dare, picking call ɗin ya yi muryarshi na rawa ya furta”Assalamu alaikum Daddy!!!” muryar Alhaji ubaid Babu natsuwa Ya furta mashi”shureim Ƴar uwarka ta dawo gida daren nan cikin mawuyacin hali”! Da alamun ruɗu akan fuskar dr shureim Yace”bangane wa kake nufi ba daddy” muryar shi da sauti mai ƙarfi Yace”BENAZIR!! nake nufi ta dawo gida cikin daren Nan, Gatanan kwance tana buge buge zufa duk ta wanke jikinta, mun rasa ya zamuyi da ita” Zafafan Hawaye ne suka wanke fuskar dr. shureim, tsabar farin ciki baisan sa’adda Ya zube saman gwiwowinsa Yayi sujjada, sosai ya fashe da matsanancin kuka mai tsuma zuciya, Alhaji Ubaid Yana jiyo sautin kukan dr shureim Kamar ƙaramin Yaro. “Shureim ba kuka yakamata kayi ba, dan Allah ka natsu muyi magana, hankalin mu ba’a kwance Yake ba, Ƴar uwarka bata acikin Hayyacinta, Mai gemu ya tabbatar min da cewa Kurciya ne akayi mata, saboda alamomin dake a jikinta na fitar sihirine” Jin wannan maganar ta Mahaifin nasa ne yasa shi saurin ɗagowa daga sujjadar, arab turban dinsa tuni ya warware Yabar saman kanshi. Manna wayar yai saman kunnanshi da alamun kiɗima ya furta”Sihiri kuma!! Alhaji ubaid Yace”to haka dai mai gemu Ya faɗa mana, baka ga yadda jikinta ke fitar da gumi ba kamar wadda aka tsamo daga kogon ruwa, bari na kanga maka wayar kaji haukan da take Yi mana” on the other hand Alhaji Ubaid Ya matsa gaban benazir Ya saita wayar abakinta. Muryarya ce ta ratsa kunnuwan dr shureim”Ni ku sake ni, Ku ƙyaleni ku daina ruƙe mun hannuna, wurin Mijina zanje nabar mashi ƴata a gida ita nake son gani, wallahi ku rabu dani dole in tafi” Jikin taƙaura yai la’asar, a sukwane Dr shureim ya miƙe tsaye da waya kare a kunnanshi. Muryarshi na rawa Ya furta”daddy najima ina zargin hakan, innalillahi wa’inna ilaihirraji’un, wallahi da ina da halin da zan Iya zuwa Jos acikin daren nan da babu abun da zai hana inzo don in cece rayuwar ƴar uwata, amma duk da haka daga nan ɗin ma zan Iya taimakawa, Daddy Idan Aunty zainab tana akusa ka miƙa mata wayar!” Jikin Alhaji ubaid na 6ari ya miƙa ma zainab Wayar yace ta kar6a dr shureim ne ke son Yin magana da ita, da sauri ta sanya hannu ta kar6i wayar tana fadin”dr shureim kaga wani ikon Allah ko? Tsawon shekara goma sha shidda Yau benazir ta dawo gida, wlh tsabar farin ciki bansan inda zan tsoma kaina ba, sai dai na damu da yanayin da take aciki” Numfasawa dr shureim Yai tare da cewa a tsanake”Aunty zainab, yanzu bani da natsuwa, zuwa gobe da sassafe zan shigo Jos din, amma kafin nan ki duba ɗakina a cikin drawer chest na bedside drawer gida na uku, akwai robobin ruwan zam zam da wani malamin mu na ƙasar egyp ya bamu su don mu dinga yin amfani da su muna taimakon mutanan da suke fama da matsalar sihiri, ki ɗauki ɗaya Kije ki buɗe bakin benazir Ki matsa mata shi ki tabbar ta shanye shi duka in sha Allah, sauran sihirin dake ajikinta zai barta ne kafin goben mu ƙaraso” amsa mashi tayi da toh, yace ta miƙa ma mahaifiyarshi wayar da sauri ta miƙa mata, yatsun hannun layla na kerma ta kar6i wayar. Cikin shessheƙar kuka tace”shureim benazir ɗinmu ta dawo gida, sai dai kamar bata acikin hayyacinta, duk ta faffasa la66anta da haƙoranta. Cikin kwantar da murya dr shureim Yace”Ki sanya handsfree Inason daddy yaji maganar da zanyi” da sauri layla ta mayar da wayar handsfree, zainab tuni ta shige ɗakin dr shureim neman ruwan zam zam. “Mommy daddy, dan Allah ku kwantar da hankalinku, wallahi Allah ne ya taimaki rayuwar baiwar Allah nan Ya Karya sihirin dake a jikinta, kuma ya dawo mana da ita da ranta, wani mugun aka samu mara imani mai zuciya irin ta kafuran farko Yai silar rabata da danginta tsawon shekara goma sha shidda, wallahi tun lokacin dana ji yanayin da benazir ta gudu tabar gida raina ya bani cewar wani abunne Ya faru da ita, haƙiƙa munyi sakaci wurin kula da ita, gaba ɗaya mun ɗaura mata lafin guduwarta babu wanda ya ta6a yi mata kyakkyawan zato akan meyasa ta gudu tabar jinjira acikin kwamin wanka, Kuma bata nemi kowa ba ta kama hanya tayi tafiyarta, anyi amfani da halayanta na rashin jin magana da rashin Kunya da take dashi anyi mata abun da yasa tabar mu saboda ansan kowa zai yi tsammanin ita ta gudu dakanta tunda dama bata jin magana, da ya ke Allah ba azzulumin bawansa bane sai gashi ya dawo mana da ita a lokacin da bamuyi tsammanin ganin ta ba” gaba ɗaya sun natsu suna sauraron muryar dr.shureim, hatta security officers din gidan duk suna sauraron shi ga dukkan alamu suna gamsuwa da bayananshi duba da yadda suke gyaɗa kawunansu. “Banaso wani daga cikinku Ya tambayeta meyasa ta tafi, ko kuce zakuyi mata faɗa dan Allah kada kuyi mata hakan, Kuma kada ku faɗa mata abun da ya faru da mijinta da ƴarta, naji tana ambaton sunansu, ku sanar da ita cewa suna nan kuma zaku haɗata da su idan ta kwantar da hankalinta, idan ba haka ba zata Iya zaucewa idan taji cewa babu su” Kamar malami da ɗalibansa haka shureim keyi masu magana suna amsa mashi da toh. “Zuwa da safe kafin mu ƙaraso, a kira likitan gidanmu Ya duba lafiyarta,” suka amsa mashi da toh. “Mommy idan zainab ta bata ruwan zam zam din, in dai bacci bai ɗauke ta ba, ki taimaka mata tayi wanka taci abinci, idan kuma tayi bacci ku ƙyale ta kada ku takura mata” layla ta amsa mashi da toh. Shigowa falon Zainab tayi hannunta ruƙe da robar zam zam ta ƙara so gaban sofa din da benazir ke akwance tana sambatu, muryarta harta disashe fuskarta ta kumbura suntum. Zuƙunnawa tayi agaban sofa din, ta cizge murfin robar, da sauri Alhaji ubaid ya rurruƙe mata hannuwan Benazir, daƙyar ta Iya buɗe bakinta ta kafa mata ruwan zam zam din ya dinga shiga cikin ƙaramin bakinta, gaba ɗaya ta shanye ruwan, ko mintuna biyar ba’ayi ba da bata ruwan bacci mai nauyi ya ɗauketa, sai faman sauke ajiyar zuciya take yi, zufar jikinta tuni ta soma daskarewa, addu’o’i zainab ta dinga karantowa cikin harshen larabci tana tottofa mata saman fuskarta da jikinta, hakan ba ƙaramin daɗi yayi ma iyayenta ba, tuni layla tayi sallama da dr shureim ta miƙa ma Alhaji ubaid wayarshi ya sanya hannu Ya kar6a ya tura a aljihun jallabiyarshi, security office din dake atsaye bakin ƙofar falon suka yi masu sallama da niyar gobe da safe zasu dawo duba jikin benazir, Alhaji ubaid yai masu godiya kafin suka fice daga falon. Hajiya layla ta dubi zainab kije ki kwanta mun gode sosai, dan Allah gobe da a suba ki shirya mata lafiyayyan breakfast din da zata ci” amsa mata tayi da toh, ta mike ta nufi room dinta, ya rage saura Alhaji ubaid da Hajiya layla a falon, kallon juna sukayi lamarin Ya girgiza su, abun daya ɗaure masu kai wanene yayi masu wannan muguwar aika aikar!!! Atare suka ɗaura idanuwansu kan benazir tsantsar sonta da ƙaunarta ne Ya kamasu, Har cikin zuciyarsu basu ji daɗin ƙaddarar data afka mata ba, tayi matuƙar basu tausayi ganin irin mayuwacin halin da take aciki, fatansu Allah Ya toni asirin baƙin azzulim daya yi silar barinta gida!!! yadda suka ga Rana haka suka ga dare, babu wanda Ya runtsa acikin zukatan nan guda huɗu, Hajiya layla da Alhaji ubaid, Dr shureim da Zainab, akan kunnuwansu aka fara kiran sallar asubahi!!!! Dr.shureim Tun bayan daya dawo daga sallar asuba Yake ta faman shirye shiryen tafiya jos, tuni Yayi wanka ya kimtsa cikin shigar shi ta larabawa Yabi ko’ina na jikin shi Ya feshe da turare, Hannun shi ɗaya ruke da wayar shi ɗayan hannun Yana ruƙe da car key dinsa, takalmasa Ya zura a ƙafa Jiki Na rawa ya nufi ƙofar fita daga ɗakin bayan ya fito bai nifo ko’ina ba sai part din Alhaji musa don Ya sanar mashi da zancen bayyanar benazir da kuma tafiyar da zaiyi zuwa jos, abakin ƙofar ɗakin ya dai daita natsuwarshi, ya ɗaga murya yayi mashi Sallama, kusan sau uku kafin muryar Alhaji musa ta amsa mashi “Wa’alaikum salam shureim shigo ciki mana” ajiyar zuciya ya sauke, tare da sanya hannu Ya ture ƙofar ta buɗe, baiyi tsammanin zai ganshi tare da wani ba, ashe bashi kaɗai bane, su biyune shi da Hajiya Sarah suna zaune saman Sofa ɗin ɗakinshi, An jera masu kayan breakfast a saman sofa table din gabansu, mutumin babu annuri akan fuskarshi, Jallabiyace a jikin shi hajiyar tashi kuwa ta ca6a uban adon lace a jikinta, ta kashe ɗaurin kallabinta, wutsiyar gashin kanta ya sauka har saman wuyanta Fuskarta da fara’a take kallon shureim”barka da safiya My son, fatan ka wayi gari lafiya” shureim na murmushi yace”yawwa mommy, ina kwananku’ ta amsa mashi da Lafiya lou, tare da nuna mashi wuri saman armchair ta ɗakin tace”bismillah ka zauna mana” tun da ya shigo Alhaji musa bai ɗago Ya kalli fuskarshi ba, Hankalin shi na akan abincin da Yake ci, plate ne agabanshi shaƙe da farfesun nama Yaji ƙayan hadi sai ƙamshi Yake Yi, a tsanake Yake cin abun shi. Kasa zama shureim yayi idanuwanshi akan fuskar Alhaji musa Yace”uncle barka da safiya” kamar bazai amsa mashi ba ya furta”lafiya” da ido Hajiya sarah tayi alamar yayi haƙuri da halin uncle din nashi, murmushi shureim ya sakar mata yaɗan jinjina mata kai “Ko zaka Bari idan Ya gama cin abinci sai ku yi magana, don bai cika son yana cin abinci ana yi mashi magana ba” hajiya sarah ce ta fada, Kafin dr shureim ya bata amsa muryar Alhaji musa ta katse mashi hanzarinshi”Shureim ina jin ka, faɗi abunda ya kawo ka” Ba ƙaramin daɗi Yaji ba, da fara’arshi ya fara magana”uncle bansani ba, ko daddy ya kira ka awaya ya sanar dakai abun farin cikin daya faru a daren Jiya” sai da ya ambacin hakan tukunna alhaji musa Ya ɗago da ido yana dubanshi alamar yana son jin ƙarashen zancen “Ƴar uwata Benazir ta dawo gida a daren Jiya ƙarfe goma sha biyu na dare!!!” Tsantsar mamaki da al’ajabi ne Ya bayyana akan fuskar alhaji musa, sai dai babu alamun zai furta magana sai faman jinjina kanshi yake yi. Hajiya sarah kuwa Tsabar farin ciki mikewa tayi tsaye tare da ɗaga hannyenta sama tana ambaton”ALHAMDULILLAH!! wayyo Allah shureim Allah Yasa ba wasa kake Yi min, dagaske Benazir ta dawo gida da ƙafafuwanta ko kawota akayi”? Shureim na murmushi yace”da kanta ta dawo gida, kuma abun mamaki tana ta sambatu tana ambaton sunan daddy da mommy da mijinta da ƴarta, kuma muna hasashen kurciya ne akayi mata da har ta gudu tsawon shekaru bata dawo gida ba, shiyasa nake so inje jos din Yanzu.......” Hawayene suka wanke fuskar Hajiya sarah, Muryarta na rawa ta furta”shureim nima zan bika muje jos din, nasan shima uncle din naka zai je sai mu tafi atare...” kafin ta ƙare maganar Alhaji musa ya dakatar da ita ta hanyar cewa”Ya isa haka? Kinsan bana son shouting” shiru suka yi gaba ɗayansu, duk suka sha jinin jikinsu. Kallon shureim yayi”ina zaka je da safen nan, naga ka shirya ga key din mota a hannu”? Cikin sanyin murya yace”jos zan tafi, Inason ganin benazir” Ta6e baki Alhaji musa yayi, tsawon mintuna ɗakin yai tsita, saida ya mula yasha iska tukunna yace”zanyi waya da yaya ubaid din, basai kaje jos din ba, zansa su zo nan abuja...” har saida gaban shureim Ya faɗi jin abinda Yace, bashi ba hatta Hajiya sarah arude take duban fuskarshi, kallon mara hankali take binshi da shi don wanna Yafi ƙarfin a kira shi da izzah, Tayaya zai nuna ƙarfin iko akan Yayanshi? Waye ya dace yazo gidan wani? Almost 16years yarinya ta 6ace sai Jiya ta dawo ƙarfe sha biyu na dare ko kaɗan bai nuna danuwarshi ba, kuma babu alamun zai je ya taya yayanshi murnar ganin yarsu da suka yi? Muryarta na rawa ta furta”am..amma hakan bai dace ba, nayi mamaki daka furta wannan maganar, kodai baka ji abunda shureim Yake faɗi bane? Ƴar wurin Yayanka benazir ce data 6ace tsawon shekaru ta dawo gida a daren jiya ƙarfe goma sha biyu na dare Yakama ka tashi ka shirya mu tafi” da buɗar bakinshi sai cewa yai”Umarni kike bani”? Da ƙarfin hali Ta furta”A’a kawai ina ƙoƙarin faɗa maka abunda Ya dace ne” tamkar zaki Haka ya yunƙura ya miƙe Ya dubi fuskar shureim da mamaki Ya gama kamashi “Nace bazaka je jos ba, ka koma ɗaki ka zauna, zansa Iyayen naka su zo tare da ƴar uwar taka abuja” gyaɗa kai dr shureim yayi jiki amace yace”toh uncle, na hakura, zan jira su zo ɗin” ƙwalla ce ta ciko idanuwanshi da sauri Ya juya ya fuce daga dakin. Bayan fitarshi Alhaji musa Ya nuna Hajiya sarah da Yatsan hannunshi”koda gigin wasa kada ki kuskura ki ƙara shiga tsakanina da shureim idan muna magana, abune da ya shafeni da dangina banaki ba, don haka ki kiyaye” yana gama fadin hakan a fusace yakai hannu ya yago tissue ya goge bakinsa ya nufi cikin dakin. Jiki asanyaye hajiya sarah ta zauna saman sofa din, lamarin Ya ɗaure mata kai, wannan rashin adalcin har ina? Meyasa zai dinga iko da yayanshi? Ko dan Yana da dukiya ne? girgiza kai tayi ahankali ta furta”wannan ba adalci bane” ta faɗa haɗi da miƙewa ta nufi hanyar fita daga ɗakin. Bawan Allah dr shureim abun duniya ya isheshi, Uncle musa Ya bashi mamaki, bai ta6a jin haushinshi ba sai yau daya nuna ƙarfin iko akan iyayenshi, Ya fahimci ma bai damu da dawowar benazir ba saboda babu annuri akan fuskarshi duk da yasan halin shi ne hakan, amma yaji ɗaci aranshi, don me zai dinga juya mahaifinshi son ranshi bayan shine agaba dashi, ko a shekaru Alhaji ubaid Ya zarce Alhaji musa nesa ba kusa ba saboda shi ba wasu shekaru gare shi ba, shiyasa ko a jam’iyarsu ake kiranshi da ƙaraminsu babbansu. Abun ya ɗaurewa Dr. Shureim kai, har ya fara tunani kodan Yana da dukiyane shiyasa yake sarrafa kowa yadda yake so? In banda rashin ta ido har zai Iya buɗe baki yace zai kira iyayan nashi suzo abuja maimakon shi ya tattara iyalansa suje can jos din su tayasu murnar dawowar ƴar su, Anya kuwa Uncle musa bai fara shan ƙwaya ba”? Saƙe saƙe zuciyar shureim take Yi mashi hakanan ya samu kanshi da kokwanton uncle din nasa. “Shureim dan Allah ka yi hakuri da abunda uncle dinka Ya faɗa maka, wallahi banji daɗi ba, bai kyauta ba, wannan ai ba adalci bane, bansan meyasa yake yin haka ba” Muryar Hajiya sarah ce ta katse mashi zancen zucin nashi, har ya kusa shiga ɗakin shi Ya ci burki tare da Juyowa baya yana dubanta Damuwace ƙarara akan fuskarta, kamar yadda shima tashi fuskar damuwarce Murmushin yaƙe ya ƙaƙalo akan fuskarshi da karyayyar murya ya furta”kada hakan ya dame ki mommy, da ace bansan halin uncle din nawa bane, amma nasani, shiyasa nake yi mashi uziri, bakomai zan jira su zo din kamar yadda ya fada” Gyaɗa kai hajiya sarah tayi har cikin ranta bataji daɗin abin daya faru ba “Bari na kira maka zeenatu, nasan zata ɗebe maka kewa, kafin isowarsu” still da murmushi akan fuskarshi Yace toh, zan jirata Bayan tafiyarta, Ya shiga dakin shi, asaman gado ya jefar da key din hannun shi, Ya tu6e arab tur6an dinsa Ya jefar saman gado, Ya zauna daga gefe hannu bibbiyu ya zabga uban ta gumi takaici Ya ishe shi, mahaifinshi Yafi 6ata mashi rai saboda shine silar komai, da ace tun farko bai bari uncle musa ya raina shi ba da duk hakan bata faru ba. Yayi zurfi acikin tunanin shi muryar Zeenatu ta katse shi “Yaya shureim ɗina” a hanzarce ya ɗago da ido yana dubanta, ta zumbula dogon hajibi har ƙasa Yake ja, ta ruƙo round plate mai ɗauke da mug, sai faman sakar mashi murmushi take yi, kwata kwata babu natsuwa atattare da ita, kafin shigowarta ɗakin mommynta ta faɗa mata xancen ganin benazir shiyasa take ta yin farin ciki, ita fa tun da take bata ta6a ganin benazir ba a hoto kaɗai tasanta saboda kafin guduwar benazir tana ƴar jinjirarta. Ganin yadda take tafiya babu natsuwa yasa shin saurin motsa la66ansa da niyar ya dakata da ita, sai dai ina kafin yai yunƙurin yin hakan tuni tayi tuntu6e da takalmanshi daya cire a tsakar ɗakin, Mugs din data dauko yai tsalle sama Ya dira daman ƙafarta ruwan coffee mai zafi Ya ɗalli ƙafarta, zafin da tajine yasa ta jefar da plate din hannunta, ta duƙe saman floor tana kuka, da sauri Ya miƙe ya ƙarasa gabanta, ya zuƙunna tare da kai hannu ya damƙi ƙafafuwanta Ya soma tottofe su da addu’o’i, ta dage sai kuka take yi mashi, abunka ga farar fata wurin da ruwan coffeen Ya ta6a yayi jawur kamar zai fashe. Kukanta duk Ya cika mashi kunnuwanshi, a hankali ya ɗago Yana dubanta, hawaye sun wanke fuskarta, lokaci ɗaya ya soma tariyo sambatun benazir tuni yaji jikinshi yai sanyi, haƙiƙa Yana matuƙar tausayin rayuwar ƴa mace, fuskar benazir ce ta dinga yi mashi gizo akan fuskar zeenatu, har baisan sa’adda Ya rungume ta a kirjinshi Ya zagoya da hannanyeshi saman bayanta, Yana ɗan bubbuga shi cikin sigar lallashi, ƙanƙameshi zeenatu tayi kamar zata koma cikin cikinsa, daddaɗan ƙamshin turarenshi ba ƙaramin kashe mata jiki yayi ba, tuni ta haɗiye kukan da take yi, tayi kwance abunta sai faman sauke ajiyar zuciya take yi, dr. Shureim sam ya manta dawa ya rungume a jikinshi, kewar benazir duk ta addabe shi, Ya jefa zeenatu cikin yanayi najin shauƙin shi, yayin da shi hankalinshi nacan wani wurin daban............... Idan muka koma 6angaren zahra, tun wuraren ƙarfe shidda Mahboob Ya shigo mata da jakar kuɗin motarta da wayar da aka saida mata, shaf shaf ta shirya cikin jallabiya ta yafa mayafi akanta, tace da mahboob ya taimaka ya kaita gidan Hajiya falmata, yace zai kaita amma bisa sharadin zata bashi nashi kason, tunda ai yayi mata ƙokari, a lokacin taƙagara da taje tace mashi ta amince su tafi kawai, kafin su bar gidan saida ta fara cire miliyan ɗaya ta ajiye su cikin drawer, ya rage saura 3m dai dai kuɗin da zata bata. Tana zaune a back seat na motar mahboob, yayin da shi kuma yake zaune a mazaunin driver, a tsanake yake yin driving har Allah Ya kawo su gidan Hajiya falmata. A parking space mahboob yai parking din motar yace da ita ta shiga yana jiranta, ta amsa mashi da toh, ta buɗe motar ta fito ta nufi ƙofar shiga babban falon gidan” Murmushin gefen fuska Mahboob ya dan saki yayin da yake bin Bayan zahra da kallo, ya zuro ƙafarshi daga cikin motar daya bar murfinta abuɗe Wayarshi ce tayi ringing daga cikin aljihu da sauri Ya zura hannu ya duba mai kiranshi sunan Aunty Aneelerh ne Ya bayyana Picking call din yai ya kara wayar a kunne”Babbar yayanmu, mun karaso gidan fa, Yau zahra zata sha mamaki, wallahi bakiga yadda take ta zubda uban gumi ba, kamar wadda tayi ma sarki ƙarya fadawa suka kamo ta” tuntsirewa yayi da dariya, Muryar Aneelerh da sautin dariya tace”baiwar Allah, ina fata yau hankalinta zai kwanta, naji daɗi da nasarar da muka samu, ubangiji Allah Ya ƙara tsare mata ita” ya amsa mata da ameen Ta kuma cewa”Idan kuka dawo gida, ka faɗa mata cewa motarta da wayarta jingina ka bada su, idan tanaso ta baka kuɗin za’a dawo mata da su, sannan please bana so tasan cewa jiya munje gidan hajiya falmata, ya amsa mata da toh, daga haka sukayi sallamar. Tun da zahra ta shiga gidan, takasa zama, tana a tsaye tana jiran fitowar hajiya falmata don ta miƙa mata kuɗinta, mai aikin gidan ce ta fito daga part din dakin nata ta dubi zahra”ki zauna mana gatanan fitowa” galla mata harara zahra tayi’ba zama nazo yi ba” murmushi mai aikin tasaki kafin ta wuce ta nufi kitchen Jim kaɗan, Hajiya falmata ta sauko down stairs, sleeping dress ne a jikinta riga da wando ta yafa mayafi akanta. Fuskarta babu walwala ta dubi zahra”zauna mana” tayi maganar tana nuna mata sofa Harara zahra ta watsa mata”ba zama nazo yi ba, kuɗinki na kawo maki” tayi maganar a fadace ta ajiye mata jakar gaban kujerar da take a zaune Har ta juya zata fita muryar hajiya falmata ta katse mata hanzarinta “Zahra! Dan Allah ki zauna inaso muyi magana badan halina ba” Batayi mata gardama ba tace”dan kin haɗani da Allah, shiyasa zan zauna badan haka ba wallahi ko kallo baki ishe ni ba” murmushi hajiya falmata tasaki. Bayan zahra ta zauna tana faman haɗe rai tace”ina sauraronki sauri nake yi in tafi” “Nasan zakiyi mamaki zahra, kuma ba lallai ki yarda da abunda zan faɗa maki ba, abunda Ya faru a tsakanina dake badagaske bane, jarabaki nayi saboda wani dalili nawa....” da mamaki zahra take dubanta, jinjina kai hajiya falmata tayi”tabbas ba halina bane, nayi ƙoƙarin jan ra’ayinki ne don insan dawa ƴata take tarayya” Tunkan ta kare maganar zahra tasaki dariyar rainin wayau tana fadin”dallah malama dakata! Banason zancen banza, harni zaki raina ma wayau? Ki gama zubda mutuncinki agabana kuma ki dawo kina fadin jarabani kikayi akan me kenan? A tsiwace ta furta hakan Numfasawa hajiya falmata tayi”zahra dalilin dayasa nayi maki hakan, Mun samu sabani nida wata aminiyata hajiya naja’at akan ƴarta dake bin mata, ta laƙafa mun sharrin cewa ƴata fatima ce ta koya mata, saboda ita kaɗaice suke tarayya, sannan ita taba yarta tarbiya tasan bazata ta6a aikata hakan ba, faɗa sosai mukayi da ita, ta zageni taci mutuncina, damuwar duniya ta isheni, lokacin dana dawo gida narasa ya zanyi in tuhumi fatima saboda nima ina tsoron ace ƴata tana aikata kalar abunda Yarinyar aminiyartawa take yi, nasan zaiyi wuya fatima ta faɗa min gaskiya, kinji dalilin dayasa na yanke shawarar yi maki hakan saboda nasan ke kaɗaice aminiyar fatima, duk wani abu da zatayi saida shawararki, atare kuke yin komai, Ni a tunanina ta hanyar dana 6ullo maki zan samu abunda nake nema na gano abunda ƴata take aikawata ashe ba haka bane nayi babban kuskure zahra, dan Allah Ki yafe min” fashewa tayi da kuka hawaye nabin fuskarta, baiwar Allah zahra tuni zuciyarta ta karya, sam bata kawo komai aranta ba, ta yadda da kalaman hajiya falmata, cikin shessheƙar kuka tace”Amma meyasa zaki yi jarabawar dani? Kin hanani bacci kin hanani cin abinci, kin jefa rayuwata cikin matsanancin tashin hankali, babban abun takaicina shine karya min zuciya da kikayi saboda na ɗauke ki tamkar mahaifiyata ina ganin girmanki, ashe dama duk plan ne kika shirya min”? Hajiya falmata na matsar ƙwalla tace”kiyi hakuri zahra nasan ban kyauta maki ba, dan Allah ki rufe min asiri kada kowa Yaji maganar nan, saboda banaso ayi tsammanin nima ina aikatawa ne sannan, maganar kuɗin da nake binku ni tuntuni na yafe maku, wallahi na bar maku su babu abunda zanyi dasu, sannan maganar yin order na kaya daga dubai in sha Allah gobe zasu iso Nigeria, inaso kuci gaba da gudanar da aikinku a companyna ke da fatima, don bazanso in rasa mace mai nagarta da tawakkali irinki ba, komai kuke so zanyi maku zahra, ni dai fatana ki manta da duk wani abu daya faru a tsakanina dake, Ki cigaba da daukata tamkar mahaifiyarki” Rushewa zahra tayi da kuka, kamar ranta zai fita, bata ta6a tsammanin komai zai zo mata da sauƙi ba, harta fidda ran cigaba da aiki a companynsu da kuma damar zuwa obie estate ashe da rabon mafarkin ta ya zama gaskiya. Cikin shessheƙar kuka tace”In sha Allah mommy babu wanda zaiji maganar nan, komai Ya wuce amma dan Allah kada ki ƙara yi min wasan nan, ni kaɗai nasan raɗaɗin da naji acikin zuciyata” Jinjina kai hajiya falmata tayi da karyayyar murya tace”bazan ƙaraba zahra, nima nayi danasani, dan Allah ki tsaya mu yi breakfast atare kada kice zaki tafiya” Zahra tace”sauri nake yi wata rana zan dawo, Ina fatima take”? Hajiya falmata tace”bata nan, jiya ta tafi gidan uncle dinta amma yau zata dawo saboda aikin da zakuyi tare” murmushin farin cikine Ya bayyana akan fuskar Zahra, sai faman washe bake takeyi harta fara tunanin irin rashin mutuncin da zatayi ma Aneelerh idan ta koma gida, Godiya sosai hajiya falmata tayi mata, itama zahra tayi mata godiya da fara’a suka rabu. Ta ruƙo jakar kuɗinta a hannu, tana fitowa daga falon da gudu ta nufi motar mahboob tana dariya haɗi da yin rawa tana jujjuya, Mahboob tamkar baisan komai yace”zahra kin haukace ne? Lafiya kike dariya kamar wadda ta zauce ga hawaye akan fuskarki” da sauri ta share hawayen da gyalen jallabiyarta Tace dashi”bro ka tayani murna yau ina cikin farin ciki, amma fa kada ka tambayeni meyasani shiga yanayin nan” Mahboob na murmushi yace”shakuruminki aini ba ɗan jarida bane da zan tsareki da tambaya, Yanzu dai shiga mota muje gida muyi magana akan haƙƙina,” Da farin ciki tace”ai mahboob kamar yadda Allah Ya rufa min asiri kaima zan rufa maka asiri, kai dai muje gidan” ta faɗa haɗi da shiga motar, ya tada suka nufi Hanyar komawa gida. *EX-PRISONERS🥳* *At abuja Nigeria🛬* Alhamdulillah Matafiya sun samu damar sauka Lafiya basu wayi gari ba sai acikin Katafaren Luxury Villa Mallakin Chief Owais sharafuddeen Obinna! haɗaɗɗiyar Daular arzƙi ce wadda zamu Iya kiranta da Aljannar duniya saboda Kayan alatun dake acikin ta, Katafaren gini ne mai girman gaske ta 6angaren tsayi da faɗi Yana ɗauke da Sassa Uku acikinsa, a ɗaya daga cikin Part din gidan aka yima Prisoners masaukinsu, A hankali nake bin ginin da kallo domin in ƙarasa ga cikinsa, ta ko’ina na kalla ƙyalƙyalin gilassai ne suke kashe min idona da kyawunsu, wasu irin haɗaɗɗun floor-to-ceiling Glass windows ne masu mamaye bango, daga ƙasa har sama glass ne, Kana Iya hangen Katafaren Main falo din dake acikin sashen ta glass windows din, Ga wasu sliding doors ƙofofi masu zuge kansu da zarar sun gama tantance mutun saboda gidan Yana da mugun tsaro ba iya mutane ba hada na’urori ke sarrafa shi, ba za ka ta6a Iya ƙetare Gingirimeman entry way din gidan ba tare da An tantance ka ba, daga ƙasa har sama, bana tunanin ko aljani zai Iya shiga salin alin ba tare da na’ura ta haska shi ba, salon kuma ace nayi karya (😂) Dafa ƙofar glass din Nayi da hannuna ɗaya, Na’ura ta tantance ni aka bani iznin shiga ciki, Slowly glass din Ya soma zugewa, Na baza ido ina kallon tsaruwar Falon da kallon shi kaɗai zai Iya faranta zuciya, launukan painting cikinsa black, gold and white, An ƙawata shi da manya manyan sectional Chersterfield sofas, saiti biyu ne a palourn, Ƴan ubansu masu numfashi masu tafshi da daɗin zama ga jerin Throw pillows launuka daban daban saman kowace sofa, daga tsakiyar Katafaren falon wani faffaɗan Glass table ne daga saman shi an ɗaura flowers Vase, Furannin har ƙyalli suke Yi masu launi daban daban, bayan haka a kowani sofa hand din akwai Round glass table, mai dauke da kayan ƙyale-ƙyale na ado, daga saman jigunan ceilling din falon wasu ƙayatattun Crystal chandeliers ne masu girman gaske, An ƙawatasu da ado, kusan guda Uku ne a saman silin din, Haskensu Ya mamaye ko’ina tamkar da rana, Idan ka kalle su sai ka yi tsammanin zasu rubzo maka saman kai, sobada girman su, ga wata faskekiyar flat screen tv wadda idan kana kallo da ita sai ka yi tsammanin mutanan ciki zasu fito waje saboda girmanta, Bayan sofas din falon akwai hamshaƙan armchairs har guda biyu, hatta saman floor din falon Kayan adone aka ɗaura samansu, sparkling floor lamps ne ajiye a kasa suna bada nasu hasken mai ƙyalƙyali, akwai Kayan jin sauti, Ga Dogayen labulaye dake kewaye da falon an zuge su, A ƙalla Part din Yana ɗauke da Faluka sun kai Uku, bayan wanda na zayyana ma ku, daga cikin falon farko kana Iya hangen furniture din da ke a cikin falo na biyu ta hanyar Glass window, komai zaka Iya gani, Gidan fa Ya haɗu Ga glass elevator gefen twins stairs din dake a falon, ta ko’ina sanyayyan sanyin A.c ne ke ratsa fatar jikin bil’adama mai ni’imar gaske, bayan haka ta cikin glass din falon zaka Iya hango Sashen da tanƙameman swimming pool din gidan Yake, ruwan dake acikinsa launin sky blue ne, da wasu kujerun shaƙatawa a gefenshi, da sauran ababen more rayuwa, Idan muka koma Dining room wato ɗakin cin abincin gidan abun ba’a magana, shima a kewaye yake da floor-to-ceilling glass windows, kana Iya hangen abubuwan dake wakana daga wajen ɗakin cin abincin, An ƙawata shi da haɗaɗɗun dining tables, na farko zungureren table ne mai mazaunin mutun goma sha biyu, da me mazaunin mutun shidda, da kuma tabur mai mazaunin mutun uku, kowan nan su saman shi an ƙerashi da zallar glass, ƙafafuwansu kuma wooden legs ne, wasu haɗaɗun gujerune kewaye da tables din, daga saman ceilling din ɗakin cin abincin ƙaton kwan fitila ne ke haskaka cikinsa, ga kuma Zungureriyar floor lamp, Itama nata hasken Daban Yake, agurguje zamu leƙa Cikin Bedrooms din dake a part din, A ƙalla ɗakunan kwanan dake a cikin part din sun kai goma sha biyar, Just for one part, ƙofar shigar kowani ɗaki ta glass ce sai dai baka Iya hangen abunda ke ciki idan har na cikin ɗakin ya zuge curtain dinsa ba, ƙofar da kanta take zugewa da zarar mutun Ya kusance ta take sliding a hankali, Idan ka shiga ɗakin idanuwanka zasu fara Yin Arba da wallpaper ta bango mai matuƙar jan hankali, kowani room Yana ɗauke da hamshaƙan king-side beds masu tausasan Katifu kalar wanda ko mutun bai jin bacci idan Ya hau su sai dai aji sautin minsharin shi, saman gadon shimfiɗe yake da tausasan bedsheet, da jibgegen bargon lullu6a kafi mage laushi, ga jerin matassan kai daga gaban gadon. Gefe da gefen gadon nightstands ne, wadanda ke ɗauke da bedside lamps, daga bakin gadon faffaɗan wooden table ne mai ɗauke da drawer chest a jikin shi, ga wani haɗaɗɗen rag carpet shimfiɗe ƙasa mai dumbujejen gashi gashi ajikinshi tsaf mutun zai Iya kwanciya saman shi saboda laushinshi, ga wani ƙayataccen dressing mirror gabanshi haɗaɗɗiyar kujerace, daga can cikin ɗakin akwai dressing room, aljannar duniya kamar ka shiga company saboda haɗuwar Large walk in closet din daya mamaye kowani bango na dakin sanya suturar, suturun sanyawa ne an jera su, daga waje zaka Iya ganin kayan dake a cikin closet din, 6angaren Kayan bacci, dana Dogayen riguna, 6angaren english wears dana atamfofi ga laces, da jerin coat, ga 6angaren takalma kala kala, dana jakkuna, kai komai fa an zuba shi babu ce kaɗai ke babu, shima ɗakin Yana da nashi dressing table, mai ɗauke da oval-shaped mirror, Mai Kyan gaske. Ataƙaice Idan fa nace zan tsaya zayyana daular Owais sharafudden tabbas zamu ƙare littafin akan bayyana kyawunsa, sai dai mun shiga cikin labarin sannu a hankali zan ƙarasa zayyana maku haɗuwar wasu 6angarorin na gidan. *CHIEF OWAIS✊* Gajiyar tafiya ta hana shi ta6uka komai, ga6o6in jikinsa sunyi mashi nauyi, tun da ya fito daga bathroom yake a kwance saman katafaren king bed dinsa, ya lullu6e surar jikinshi da Cashmere robe launin dark navy, Iya gwiwarsa rigar ta tsaya mashi, ya ɗaure igiyarta daga saiting flat waist dinsa, mutumin fa akwai ƙirar ƙarfi, Kyawawan idanuwanshi A lumshe suke tamkar maiyin bacci, Yalwatattun eye lashes dinsa sun kwanta luf, a hankali Yake motsa soft thin lips dinsa tausasa launin pink, dogon hancinsa Yayi tsaye babu lanƙwasa Yayin da yake fitar da numfashi cikin kwanciyar hankali, ya zagayo da hannun shi ɗaya ta saman yalwatacciyar sumar kanshi, ba za ka ta6a gane a wani yanayi yake aciki ba, ya tada kansa asaman tattausan pillow. Alert ne ya shigo wayarshi, tamkar baisan motsawa A hankali ya miƙa ziraran yatsun hannunsa na dama ya janyo wayar dake ajiye saman nightstand, daƙyar yake iya buɗe eyes dinshi akan screen din wayar, Doorbell alert ya gani alamar wani yana son shigowa room dinsa, unclock button ya danna, a hankali ƙofar room ɗin ta zuge, mutun biyu ne sanye cikin kakinsu, baƙaƙen kaya, dogon wando tare da black shirt, daga sama sun ɗaura long coat, kowannansu ya 6oye fuskarshi da face mask, idanuwansu ne kaɗai zaka Iya gani, suna da faffaɗan ƙirji, agaban gadon shi suka dakata da yin tafiya, cikin girmamawa suka haɗa baki wurin furta “Barka da safiya Yalla6ai, fatan ka tashi lafiya, Ya gajiyar tafiya” tun da suka fara magana basu ɗago da ido sun kalle shi ba, saboda a ƙa’ida shi ba’ayi mashi magana ana kallon cikin idon shi, hakan babban laifi ne. Bai da niyar yi masu magana, bai kuma buɗe idanuwanshi ba tun da ya lumshe su, aran su su ka ayyana yau qasaitar tashi ce ta motsa, kamar gumaka Ya shanyasu a tsaye suna jiran amsar shi, sai da ya mula yasha iska kamar baison motsa la66ansa Ya furta”Lafiya” muryarshi tamkar ana busa sarewa. Big Guy yace”Sir, is there anything you need?” ya tambaye shi ne don shi a ƙa’ida ba’ayi mashi abun da bai ce yana so ba, ko da kuwa abinci ne ka kawo mashi duk mun yunwar da yake ji in dai bashi yace yana so ba to zai ce maka ka koma dashi inda ka ɗauko shi sai in yaga dama ya ke kar6ar shi” Jin yayi shiru yasa Big Guy kuma cewa”yalla6ai zamu Iya yin magana ta waya”? Sai lokacin Ya ɗaga mashi kai alamar eh, ajiyar zuciya Big Guy ya sauke tare da kallon mutumin dake a gefen shi wanda suke kira Boss Man, murmushi su ka sakar ma junan su, sun ƙwammace su yi magana dashi ta text message saboda wahala yake basu in dai a baki zai furta masu magana. Slowly ya ware reddish brown eyes dinsa akan screen din iphone dinsa, a tsanake yake yin typing. Jin ƙarar shigowar message ta wayar Big Guy ne yasa shi yin saurin curo wayar daga cikin aljihun coat dinsa Ya duba abun da Chief ya rubuta mashi _I need My breakfast right now_ cikin girmamawa big guy yace “I’ll bring it to you immediately,” Ya faɗa tare da Juyawa ya fuce daga ɗakin, Boss Man daya ya rage a tsaye ya natsu yana jiran jin me zai ce. A lokacin da bai yi tsammani ba, muryar Chief ta katse shi”Have a seat” wuri ya samu saman doguwar sofa din ɗakin Ya zauna “Check your phone, I sent you a message.” Ya bashi umarni. Da sauri Boss Man Ya zaro wayarshi daga aljihu ya soma karanta saƙon chief din nasu. “Ya kake fatan ka tashi lafiya” murmushi ya saki har saida ya ɗago dakai Ya kalli fuskarshi, Yana matuƙar yin mamakin girmama shi da yake yi duk cikin waɗanda ke aiki a ƙarƙashinsa shi kaɗai Owais Yake gatantawa, suna mutunci da juna. “Lafiyalou Alhamdulillah, Ina fata kaima lafiya, don na lura kamar gajiyar tafiya bata sake ka ba” abaki Ya furta mashi maganar, shi kuma Ya bashi amsa ta text message. “Nagaji sosai, amma alhamdulillah, lafiyata ƙalou, Ina fata ka leƙa wurin Ƴar taka, “ Still fuskar Boss man da murmushi yace”ban kaiga zuwa ba, Yanzu nake shirin shiga na duba ta” Text ya rubuta mashi”Make sure you give her a big hug. I know you’ve missed her for a long time.” Idanuwan shi ne suka cicciko tab da ƙwalla, tuni jikinshi yai sanyi, cikin sanyin murya ya furta”in sha Allah, zanyi hakan, daren jiya ko runtsawa banyi ba saboda jiran ƙarasowarku Nigeria, duk don saboda Inyi tozali da ita, sai dai ban samu damar Yin hakan ba, saboda Bayan nayi sallar asubahi a masallaci bacci Ya dauke ni, saida na shigo gida nake jin labarin ƙarasowar ku......” dakatawa ya ɗanyin da yin maganar, ganin text din da owais Ya tura mashi. “Don’t let the tears fall from your eyes, Otherwise, I won’t let you see your daughter.” fashewa yayi da dariya jin abunda yace mishi, har saida ya ɗago ya dubi fuskar Owais, Hankali kwance sam idanuwanshi basa akan fuskar Boss Man ɗin. “Kana da mutunci, shiyasa muke ƙaunarka, wallahi tunda nake arayuwata ban ta6a ganin matashin saurayi mai wadatar arziƙi, da kyau da asali, mara girman kai irinka ba, saboda kowa naka ne, babu ruwanka ka ji daɗin rayuwarka, bazan ta6a mantawa da alheran da kayi mun ba, nasan bazan Iya biyanka ba amma ina fata Allah Ya wadatani da abunda zan faranta maka da shi” Tunda ya fara magana Chief owais Ya natsu yana sauraron shi, idanuwanshi akan screen din wayarshi. Tambaya ya jefa mashi”What’s her full name?” cikin girmamawa Boss Man yace”UNAISAH ZAHEER TAJUDDEEN” lumshe idanuwanshi yayi, ƙamshin turaren jikinsa yana ƙara daɗaɗa hancinsa. “She looks like you” dariya Boss Man ya saki yana duban fuskarshi Yace”tayaya akai ka sani? Kaida baka kallon mutane, Ni nasan baku haɗu da ita ba” Kafin Owais Ya furta magana, alert Ya shigo wayar shi, unclock button ya danna, door room din ta zuge, Big Guy ne ya shigo da food trolley, Ya gunguro shi zuwa gaban wooden table din gadon Owais, a saman shi Ya jera mashi kayan Lafiyayyan breakfast dinsa, Bayan ya gama da zolaya Boss man yace”Big Guy, mutumin fa yau baya iya cin abinci da kanshi, ko zaka mashi abaki”? Big Guy na murmushi yace”If he gives me the opportunity to do that, I’ll do it har wanka zan dinga yi mashi....”daƙyar Ya ƙare maganar ganin yadda Chief owais Ya ɗago da sexy eyes dinsa akan fuskarshi, cikin jin kunyar maganar daya furta ya sunnar dakai ƙasa Yana faɗin”afwan Sir, su6ul da baka nayi” Fuskarshi a ɗaure Ya furta”If you ever repeat this mistake, you’ll spend the rest of your life in prison.” Dariya Boss Man yayi jin abunda chief yace, Big Guy na murmushi aranshi Yana fadin”Ai bazan ma ƙaraba, Yanzun ma albarkacin boss man naci” Ajiye wayarshi yayi saman nightstand, Ya yunƙura Ya miƙe Yana faman Yamutsa fuskarshi, Big guy dake satar kallon damtsen hannun shi sai faman jinjina kanshi Yake Yi, dawowa yayi end bed din Ya zaune gaban glass table din dake shaƙe da abinci. Serving dinshi big guy Ya fara Yi, Ya miƙa mashi mug na coffee, Kafin Ya fara sha sai da Ya fara fadin”Boss bismillah” Man na murmushi Yace”A’a yalla6ai, Ni ina na isa In haɗa Kafaɗa dakai wurin cin abinci, kaima ka sani bamai yiwuwa bane, sannan Ni a ƙoshe nake, Madam ta girka min abinci na cika ciki na” Ta6e baki Chief Owais Yai, ba tare daya ƙara furta komai ba. “Yaran fa har Yanzu bacci suke Yi yalla6ai, na lura ba ƙaramin gajiya suka yi ba, musamman Kyakkyawan matashin nan dake acikinsu, mai kama dakai,’ yamutsa fuska owais Yai jin ance mai kama da shi. Fresh fruit ya soma ɗauka Yan sha, duk wani motsin shi akan idon Boss Man, Yaron ba ƙaramin burgeshi Yake Yi ba, ƙaramin mutun da halin girma, Idan kaji shekarun chief owais zaka sha mamaki, girman jikine kawai dashi da kuma babban matsayi da Allah Ya bashi, uwa uba Ya iya dattako. Boss man Yace”An kammala shirya masu breakfast dinsu, masu aiki suna can suna aikin jera masu, Yanzu su kaɗai muke jira su farka don su ci” ya faɗa yana duban fuskar chief, Jinjina kanshi ya ɗanyi batare daya ɗago da idona ba ya furta”hakan Yayi kyau” Miƙewa Boss Man Yayi”Ni zan shiga Cikin gidan, Ka ci abinci Lafiya our chief” Ya ambaci hakan tare da Juyawa Ya fuce daga ɗakin, Ya rage saura Big guy dake saving dinshi. *🤍EX-PRISONERS❤* Kwance take saman katafaren gadon ɗakin Danish, tun daren Jiya da suka ƙaraso kowannansu aka ware mashi ɗakin shi, mutun biyu ɗaki ɗaya, Danish ne kaɗai Aka mallaka mashi bedroom ɗaya saboda shine babbansu, Angel da Batul ɗakinsu daban, Azeeza da jamima ɗaki ɗaya, Parveen da Hanna suma nasu daban, Gabriel da Naufal room ɗaya, Javed da haris a ɗaki ɗaya. Saboda Rashin lafiyar danish yasa ta gudo daga ɗakinsu ta dawo nashi tana matuƙar jin tausayinshi batasan wani abu ya same shi, gani take kamar idan tayi nesa dashi wani abu zai faru da shi, gown din Jiyace a jikinta red colour, tayi uban squeezing, hatta sumar kanta a haukece take babu gyara sunsha bacci kamar ba za su farka ba, daɗin lumbutsetsiyar katifar gadonne Ya sanya suka shagala, daga ita har shi garkuwan, ya cire suit jacket din jikinshi Iya farar shirt dince Ya bari, da gajeran wando fararen laps dinshi kamar ka ta6a jini ya ɗago tsabar hasken fatar, ya ɗaura kanshi saman wuyanta, yayin da hannayenshi biyu ke a ruƙe da waist dinta, zafin jikinshi ya daidaita bakamar da suna acikin jirgi ba zazza6i ya lullu6e shi, Yanzu ya samu sauƙi numfashinshi na fita cikin kwanciyar hankali, Sanyin A.c din dakin ya ƙara masu ƙaimi wurin Yin baccin nasu kamar matattu. Mutsu mutsu ya soma yi alamar zai farka, wata irin matsiyaciyar yunwace ta addabe shi, tun Jiya baici ko mai ba, ko ruwa bai gifta maƙoshin shi ba, Dogon numfashi yaja idanuwanshi sunyi mashi nauyi Ya gaza buɗe su, da wata irin kasalalliyar murya ya soma ambaton sunanta”My Angel! My Angel” badan la66ansa na akusa da wuyanta ba da kuwa zaiyi wuya ta iya jin muryarshi. Kamar an zungureta, a firgice ta farka tana faman zare gray eyes dinta haɗi da ambaton sunanshi”Danish are u okey? Ko jikin ne”? Daƙyar Ya iya janye head dinsa daga saman wuyanta Ya daura shi saman tattausan pillow, a hanzarce ta yunƙura Ta miƙe zaune tana faman mutsistsike idanuwanta da hannunta donta samu damar ƙare mashi kallo. “My man, yunwa ko”? Tun kafin ma ya faɗa mata abunda Yake Ji ta riga shi faɗi. Ɗaga mata gira yai alamar eh, murmushi ta ɗan sakar mashi har dimple dinta Ya lotsa”Danish banga ka yaba kyan ɗakinka ba, ko da yake baka acikin hayyacinka, saboda kana Jin Yunwa, bari naje naga ko zan samo maka abunda zaka ci, kafin in dawo ka shiga toilet kayi wanka, sai ka canza kayan jikinka” kamar ƙaramin yaro haka takeyi mashi magana. Wurga eye balls dinshi yayi akan katafaren ɗakin nashi, kamar na ɗan shugaban ƙasa tsabar haɗuwarshi. Saukowa Angel tayi daga saman gadon, tana tafiya tana waiwayon shi, daɗi kamar ya kashe ta, haƙika taji daɗin canjin rayuwar da suka samu, har ta fara tsara masu irin rayuwar jin daɗin da zasuyi, sai dai ta ɗan shafa’a da zancen kurkukun ƙaddara. Tun da ta fito daga ɗakin take faman ƙwala ido tana kallon haɗuwar katafaren falon, Cikin sanɗa take Yin tafiya kamar 6arauniya, fararen ƙafafuwanta babu takalma, bata nufi ko’ina ba sai ɗakin su Azeeza a hankali ta zuge ƙofar ta faɗa cikinsa, tayi mamakin ganinsu a tsaitsaye saman bed mattress kowacce ta ruƙe pillow a hannunta, sai tsalle suke Yi suna fadin”gamu agidan daddyn Genie” dariyace ta kusa kubce mata da sauri ta toshe bakinta da tafin hannunta, wato su duk a tunaninsu gidan daddyn Genie ne aka kawo. yara sun zama ƴan hutu. Fitowa tayi daga ɗakinsu ta nufi ɗakin Parveen tana shiga ta sameta a zaune tsakiyar gado, bacci yaƙi sakinta ga yunwa tana ji sai faman yin hamma take Yi, sumar kanta kamar ta mahaukaciya duk ta yamutsata, ta gimtse eyes dinta, hannah na akwance gefenta sai sharar baccinta take Yi. Ƙumshe dariya Angel tayi da sauri ta fito ta nufi ɗakin su Haris don ta duba su, lokacin data shiga ɗakin gaba ɗayansu bacci suke yi daga shi har javed duk sun cire suit jacket dinsu sunbar shirt da gajeran wando. Fitowa tayi dakinsu ta nufi, ɗakinsu Naufal, adai dai lokacin Gabriel Ya fito daga wanka, daga shi sai short, Ya ruƙe short toilet Yana tsane sumar kanshi, Naufal kuma yana zaune saman mirror chair Ya ƙura ma madubin ido da alama gabriel din Yake jira ya fito daga wankan shima Ya shiga. Gaba ɗaya basu lura da Angel ba, da zolaya gabriel Yace”mutumin kyau kake kallo a madubi naga tun ɗazu ka tasa shi agaba ko ƙyafta ido baka Yi” Ba tare daya juyo ya dube shi ba yace”Kai nake jira ka fito daga toilet din nima wankan nake son Yi” Gabriel Yace”amma dai kasan toilet din nan ba kalar na prison bane, akwai ruwan zafi dana sanyi kada kaje ka ƙona fatarka, kazo in nuna maka Yadda zakayi amfani da shi” Harara Naufal Ya watsa mashi”bana buƙata, nima zan Iya dakai na” gabriel na dariya yace”bana so ka yi danasani” miƙewa naufal yai ya nufi toilet din Ya shige, shigar shi ko minti ɗaya ba ai ba sai gashi ya fito Yana haɗe rai Ya kalli gabriel”nifa bangane komai ba” dariya ce ta kufce ma Angel gaba ɗaya suka juya suna kallonta, har ta juya zata gudu Gabriel Yai saurin zuwa ya ruƙo hannunta”Sister yaushe kika shigo? Ba sallama? “6atan Hanya nayi, ni banma san na faɗo ɗakinku ba” Naufal Yace”kindai shigone yi mana leƙen asiri, kuma kinga abunda kikeson gani, gashi har kina dariya” girgiza kai tayi”wallahi ni ba abunda nashigo gani, ba ri ma in tafi” ta faɗa tare da Juyawa da sauri ta fuce daga ɗakin, Kallon Naufal Yai”muje ko” sai da ya fara murguɗa mashi baki, kafin Ya Juya suka nufi toilet din, Ya nuna mashi yadda zaiyi amfani da komai, kafin Ya baro shi a cikin toilet din. Tana cikin tafiya Muryar Batul ta katse mata hanzarinta”Angel”a firgice ta Juya tana kallonta, buɗe baki tayi haɗi da zare idonta, ganin Batul ta fito tana faman Yin hamma haɗi da Yin miƙa duk a lokaci ɗaya “Yaushe kika tashi”? “Yanzu, na duba ɗakin banganki ba ashe kina anan” tunda ta fara magana idonta ba akan Angel Yake ba, Katafaram Falon take ƙarema kallo, kamar maijin tsoron shi, sai faman ƙyafƙyafta idanuwanta take Yi, bakinta hada Miyan bacci, kwata kwata babu natsuwa atare da ita, musamman sumar kanta tafi komai haukacewa. Miƙa mata hannu Angel tayi”idan zaki bini taho mu tafi, Nima kitchen nake nema, danish ne Yake jin yunwa” da sauri batul ta ƙarasa ta nufeta ruƙo hannunta tayi acikin nata, Har sun ɗaga ƙafa zasu motsa kwatsam muryar Ummin america ta katse masu hanzarin su”Where are you all going? Wa ya Baku iznin fitowa daga ɗaki”? Har saida gabansu Ya faɗi, duk suka sha jinin jikinsu, A hankali take saukowa down stairs, kimono robe ce a jikinta har ƙasa rigar takai mata, Tabi shape din jikinta, takalman ƙafarta high hills ne, hair wing din dake akanta launin black ne. Tana tafiya Hips dinta na jujjuyawa kamar ana kaɗasu, agabansu ta tsaya haɗi da Goya hannayenta saman tudun kirjinta tana kallonsu, idan ta kalli Angel sai ta kalli Batul, kamar wasu munafukai sunyi wuƙi wuƙi da ido, musamman Batul duk tasha jinin jikinta, saboda mugun jin shakkarta take ji, har ƙwara Angel ashirye take da tayi mata rashin kunya idan har ta ƙetare iyakarta. “Ke! Meye sunanki”! Ta jefa ma batul tambayar, muryarta na rawa ta furta”BATUL”! ta6e baki ummi tayi tare da daura idonta kan Angel”ke fa”? Ɗaure mata fuska Angel tayi kamar bazata tanka mata ba tace”UNAISAH” “Me kuke nema ne”? Angel ce tayi ƙarfin halin bata amsa da cewa”ɗan uwana ke jin yunwa, shine na fito don in sama mashi abun da zai ci” Ta6e la66a ummi tayi”An shirya maku breakfast din ku a dining, dama ku nake jira ku farka” ta faɗa tana nuna masu dining room da hannunta, atare su ka kai idonsu ita da batul suka kalli ɗakin. “Ku koma ku tada sauran ƴan uwan naku, su fito mu yi breakfast, idan mun kammala inaso zanyi magana da ku” Amsa mata su ka yi da toh, da sauri suka juya suka nufi bedrooms din ƴan uwansu, tana a tsaye tana bin bayansu da kallo, bakomai yafi bata mamaki da yaran ba face doguwar sumar kansu data lullu6e bayansu kamar hijabi, aranta ta ayyana ɗawainiya da yaran nan ba abune mai sauƙi ba, gyaran gashin kansu kaɗai wata wahalar ce mai zaman kanta, gashi an faɗa mata babu shige babu fuce balle tace zata kai su saloon, kuma babu damar a gayyato masu yi din suyi masu, dole sai dai ita ce za ta gyara su. Daya bayan ɗaya suka bi ɗakunan yan uwansu suka shiga domin tada wadanda basu farka daga bacci ba, saida suka taimaka ma Azeeza da jamimah suka wanke fuskokinsu da bakunansu, tukunna suka fito daga ɗakin, Kayan jiya ne a jikinsu sai mayafin da suka yafa akansu, Hankalin su ba ƙaramin tashi yai ba, musamman azeeza tun da tayi tozali da ƙwan fitilun falo jikinta Ya hau yin kerma, duk ta firgice, Parveen kuwa baki yaƙi rufuwa kamar lefen sakarai sai faman zazzare idanuwa suke Yi, saboda yanzu ne suka samu damar ganin ko’ina na cikin gidan dakyau, Hanna kuwa daƙyar take taka tiles din floor, da takalmi ta fito amma saboda tsabar ruɗu a hannu ta ruƙe takalman ta rungumesu a ƙirjinta, gani take kamar in ta taka ƙasan da takalman zai fashe, Naufal da Javed har tuntu6e suke yi garin yin kalle kalle gidan yayi matuƙar ruɗar dasu, shi ko Haris jiki sai kerma yake yi basa ban ban, shima crystal Chandelier din ceilling ne Ya ruɗar da shi ga sanyin A.c da yayi mashi yawa, hatta gabriel dake da wayewa yau dai an ƙure shi, sai faman jinjina kai Yake yi yayin da yake bin katafaren falon da kallo, abunda zai baka mamaki jamimah hankalinta kwance babu abunda ya ruɗe ta koya tsoratar da ita, sai faman washe baki take Yi komai ta kalla saita nuna shi da yatsa tace”menene wancan” ta ishe su da tambaya kamar rainon ɗan jarida, Ummin america dake a tsaye bakin ƙofar shiga dining room din, lamarin ya ɗaure mata kai, tayi matuƙar yin mamakin ƙauyancin su, gasu dai a halitta kamar ƴa’ƴan masu kuɗi, tafiya suke yi tamkar suna jin tsoron taka floor, sunƙi maida hankali su shigo su ci abinci, sai faman ƴan kalle kalle suke Yi kamar wuyansu zai cire. Mutum ɗaya ce babu acikinsu, Angel da ta tafi bedroom ɗin Danish, Batul dai tana atare da su Haris. Gyaran muryar da ummi tayi masu ne ya janyo hankalinsu ga kallonta. Da hannu ta nuna masu ƙofar shiga”ku zo ku shiga” ba tare da sun tanka mata ba, suka nufi ɗakin cin abincin, koda suka shiga sai suka koma suna bin ko’ina da kallo, Parveen ce ta furta”La’ha’ilah! Wannan duk namune”? Ta jefa tambayar tana nuna kayan breakfast din dake a jere saman zungureran table. Ummi ce ta bata amsa da cewa”naku ne, kowa ya samu wuri ya zauna” su parveen anga banza, tuni taja kujera ta zauna, ɗaya bayan ɗaya kowannansu Ya samu wuri ya zauna, sai faman baza ido suke Yi suna bin komai da kallo, jamimah tana jinjina kai tace”Yau zamu ci daɗi, wallahi munji daɗi muma mun zama ƴan gayu, gidan daddyn genie akwai abinci da kayan wasa” Azeeza taƙi ɗagowa dakai, ta ƙanƙame jikinta saman kujera, ita kwan fitila ne damuwarta, na ɗakinsu bai kai na falo dana dining room girma ba, sun hanata sakat, Gabriel dake kallonta cikin muryar raɗa ya ambaci sunanta”My azeeza” ɗagowa tayi da ido tana kallon shi sai faman yamutsa fuska take Yi “Meke damun ki”? Da index finger ta nuna mashi saman ceilling ba tare da ta kalla ba, muryarta ƙasa ƙasa tace”zai Iya faɗowa saman kanmu” Murmushi ya sakar mata”ki kwantar da hankalin ki, ba zai ta6a faɗowa ba, idan ma zai faɗo sai na tare maki shi, hakan yayi maki”? Sai lokacin ta ɗan saki murmushi jin abun da yace ta jinjina mashi kai alamar eh. Parveen sai faman haɗiyar yawu take yi ta ƙosa su fara ci, sai dai sun gaza sanya hannu ganin yadda Ummin america ta tsare su da ido ko kyaftawa ba tayi, tana daga tsaye bakin glass door din dakin, ta lura basu cika ba shiyasa ta tsaya tana jiran sauran su ƙaraso don su fara ci. “Menene wannan abun” jamimah ce tayi tambaya tana nuna wata roba Kallon robar Gabriel yai a jikinta an rubuta Honey. “Zuma ce a ciki, kin ta6a sha”? Girgiza mashi kai tayi alamar a’a, ta kuma nuna dafaffan ƙwai tace”wannan luluyayyan abun fa”? Harara ya dan jefa mata”Ƙwai ne, pls ki daina yi min tambaya baki ga ana kallon mu ba”? Ta6e mashi baki tayi”to aini inason in sani ne ko,” har tayi shiru can kuma kamar an cikare ta tace”Gabriel kace ƙwai ne, to shima kamar ƙwan fitila mai bada haske Yake”shiru yayi yana kallonta ba tare daya furta komai ba, (abun da yasa take tambayarshi saboda bakomai ne suka sani dangane da nau’ikan abinci, ko a kurkuku snacks da nama suke ci da kayan marmari, haka zalika a asibiti da suka zauna bakomai ne suka sani ba yawanci duk kalar abunda suke ci a prison ne, yau sunci karo da wasu nau’ikan abincin dana sha wanda basu ta6a yin tozali da su, shiyasa jemimah ta tsare shi da tambayoyi kamar ƴar jarida) Batul dai sai satar kallon ummi take yi ita kanta ummin ta lura da kallon ƙurullan da Batul take Yi mata, shiyasa ta tsaida idonta akanta, tunda tayi hakan batul ta saddar da kanta ƙasa cikin jin kunyarta. Abun da Ya faru, Lokacin da suka kammala tada ƴan uwansu Angel ta nufi ɗakin Danish, shigarta keda wuya ta taras dashi atsaye gaban mirror Yana faman yin haki Ya dunƙule tafukan hannayensa kamar wanda zai yi dambe, Kafin ta buɗe baki ta tambaye shi lafiya, idanuwanta suka sauka akan madubin daya fasa, ƙwaƙƙwaran naushi ya kai mashi gaba ɗaya ya zube ƙasa ya tarwatse. Rass taji gabanta Ya faɗi, a tsananin tsoroce ta furta”Na shiga uku! danish meyasa zaka fasa masu madubi? Kasan kuwa tsadar dake gare shi? Wai meke damunka ne? So kake kaja mana bala’i daga zuwa gidan mutane har ka fara yi masu 6arna” hankalinta atashe tayi maganar tana duban bayanshi. A hankali Ya jiyo yana kallon cikin sanyin murya ya furta”mutun na gani aciki Yana kallona, shiyasa na naushe shi” Zaro ido waje tayi can kuma ta tuntsire da dariya hada dafe ciki, ɗaure mata fuska yai ganin tana yi mashi dariya. Nuna shi tayi da yatsa tana fadin”mutumin da ka gani acikin madubin kaine ba wani ba, ai saida naso in nuna maka kanka a mirror amma kaƙiya, ka nuna baka son kallon shi gashi nan Yanzu ka fasa masu madubi mai tsada, Ni dai ba ruwana” ta faɗa fuskarta da murmushi. Kallon rashin fahimta yake binta da shi, ya rasa gane me take nufi, kamar bata fahimci abunda ya faɗa mata ba. Gudun kada wani ya shigo ya taras da 6arnar da Danish yayi yasa tayi saurin juyawa tana yan dube dube cen idonta ya sauka kan wani abu yayi mata yanayi da tsintsiya da sauri ta ɗauko ta tattara broken glass din ta turasu kasan gadon shi dan bataga dust bin a dakin ba ajiyar zuciya ta sauke Kafin ta ɗago tana dubanshi”kai kaɗai muke jira, zamu yi break fast, ka shiga toilet ka wanke face dinka da bakinka, idan mun gama cin abincin sai kayi wankan” toilet door Ya nufa, har ya kusa kaiwa ƙofar ta tuna da madubin toilet, da karfi ta furta”dakata danish” cak ya tsaya da tafiya, da sauri ta nufi ƙofar toilet din ta buɗe ta shige ciki, towel ta ɗauko ta rufe madubi, saboda tsaro tasan zai Iya Fasa shi kamar yadda ya fasa na room dinsa. Fitowa tayi tana faman sauke ajiyar zuciya ta dubi fuskarshi”nasan idan ka shiga ciki zakaga towel na lullu6e wani abu dashi, kada ka buɗe shi, madubi ne bana so ka fasa shi kamar yadda ka fasa na ɗakin ka, Idan ba haka ba zasu ce saika biya su ne kuma kaga bamu da kuɗi, kai ba kama san menene kuɗi ba, Ni zaka bari da aikin biyansu” ta faɗa tana yamutsa mashi fuska, bawan Allah yayi tsaye yana kallonta. “Ina jiran ka, kada ka daɗe ka yi sauri ka fito suna jiran mu” Amsa mata yai da toh, kafin ya bude kofar ya shiga, Ƴan mintuna ya fito daga ciki, har yayi brushing teeth dinsa, daga kasa har sama take bin shi da kallo, a ganinta basai ya tsaya sanya kaya ba tun da ba wanka yayi ba, Ruƙo hannun shi tayi acikin nata kamar wani ƙaninta”muje ko”? Ta faɗa tana ƙoƙarin janshi. Adai dai lokacin da suka sauko falon, ƙofar shigowa cikinsa ta zuge a hankali, atare Angel da Danish suka juya baya jin takun tafiyar mutun. Basu san wanene ba, amma saida taji gabanta Ya faɗi, ganin kakin dake a jikinshi na baƙaƙen Kaya, kuma ya rufe fuskarshi da face mask, 6oyewa tayi bayan Danish ta ƙanƙame shi tana leƙen mutumin da ke tunkaro su. Bugun zuciyarta na ƙaruwa kamar zai fasa ƙirjinta. Miƙa ma Danish hannu yai da niyar su gaisa, Danish Yaƙi bashi hannu saboda rashin yardar da shi, gyaran murya ya ɗanyi kafin ya soma magana a tsanake”zaku Iya kira na da Boss man, ina ɗaya daga cikin masu kula da ku,” ya faɗi hakan ne don su saki jiki da shi. Ajiyar zuciya Angel ta sauke, jin muryarshi ta kamilallun mutane. Dawowa tayi daga gaban shi ta tsaya tana dubanshi, ido cikin ido suke kallon juna ba tare da ƙyaftawa ba. Tsawon mintuna kafin ta furta”Ina kwana,” ya amsa mata”lafiyalou Angel, kin tashi lafiya? Ya kuma gajiyar tafiya” Tace”lafiyalou, gajiya tabi jiki, mun gode da kulawa” da alamun jin daɗin maganarta ya furta”Naji daɗin ganinki da ranki da lafiyarki, ina fata baki da wata damuwa” maganarshi taɗan so ta ruɗar da ita, amma sai ta basar tace”nima haka” da ƙyar ta furta ganin irin kallon da yake binta dashi, duk saita sha jinin jikinta, ta rasa gane kallon menene yake yi mata, dauriyace kawai yake yi, yaso ace zai iya bayyana mata kanshi a yanzu sai dai bazai yiwu ba. “Ciki zamu shiga Ni da Danish, suna jiranmu a dining” ta fada don ta samu damar guduwa daga kallon da mutumin yake binta da shi. Ɗagowa yai da ido ya dubi fuskar danish, har saida yaɗan ji gabanshi ya faɗi ganin yadda ya ɗaureta tamau babu annuri, dama tunda ya shigo falon yake mamakin kyawunshi da body structure dinshi don shi sai yanzu ya samu damar ganin shi, abakin abokan aikinsa yaji suna zuzuta kyan yaran da kamanninsu da Chief dinsu. “Ɗan uwan naki bai magana ne? Yaƙi bani hannu mu gaisa” murmushin yaƙe tasakar mashi”rashin sabone, Yana da wuyar sha’ani amma idan kuka saba zai saki jiki da kai” Jinjina kai boss man yai”okey, mu shiga ciki, Nima can zanje” a fakaice ta yamutsa fuska, aranta ta ayyana wannan mutumin zai takura mata ga shi da kallon tsiya kamar zai lashe mutun” a fili kuma taja hannun dashi suka nufi dining room din, Boss man na abiye da bayansu, kwata kwata babu alamun ƙauyanci atattare da Danish, sai dai jefi jefi yake satar kallon kayan alatun dake acikin katafaren falon. Lokacin da suka shiga dining room din da sallama abakunansu, gaba ɗaya hankulansu Baful Ya dawo kansu, Ummin america tuni ta samu wuri ta zauna, ganin Angel da suka yi da danish nan fa suka fara sakin murmushi kamar wasu zautattu, kujera taja ma danish ya zauna Yana fuskantar ummi, ita kuma Angel ta zauna daga gefen shi, Sai daga bisani su Gabriel suka lura da Boss man daya shigo, kallon juna suka yi da alama sun ɗan tsorata da ganinshi saboda dressing din jikin shi yayi shige dana Giants din kurkukun ƙaddara. Sai da Angel tace”ku gaishe shi, sunan shi Boss man, Yana ɗaya daga cikin waɗanda zasu dinga kula da mu” har suna haɗa baki wurin furta mashi gaisuwa, a mutunce ya amsa masu yaji daɗi yadda Angel tayi masu bayanin wanene shi. Ummi ta dube shi awayance tace”barka” ya amsa mata da”yawwa ya kike fatan kin wayi gari lafiya” a yayin da yake ƙokarin zama gefen kujerar dake a kusa da ita, wadda ke fuskantar Angel, don yaji daɗin kallonta. Ummi tace “Lafiyalou,” daga haka ta miƙe ta soma yin serving dinsu, a plates ta zuzzuba ma kowannansu abinci, ta dauki cups ta tsirara masu tea dake acikin flask, Bayan ta gama ta koma ta zauna” Yatsun hannun parveen har karma suke yi wurin ɗaukar cup din tea, duka ta kur6e shi, ta soma cin wainar kwai hannu baka hannu ƙurya. Batul kuwa wani sabon salon ƙauyanci, tunda ta dafi plate din noodles tasha romo da kayan haɗi, da hannu take ɗaukar indomie din tana Jujjuyata kafin ta turata abaki, ɗaya bayan ɗaya Angel ke kallonsu, Kunya duk ta kamata, koda ta daura idonta kan Jamimah robar zuma ta ɗauka ta dinga matsata a tafin hannunta ta sanya harshe tana lasa hada tanɗar baki, Angel ji take kamar ta fasa ihu. Ummin america da boss man duk suna kallonsu sai faman sakin murmushi suke Yi. Gyaran murya ya yi masu jamimah ta dago tana kallon shi yace”kidaina shan zumar ita kadai, ga mahaɗinta nan ki zuba asama sai ki ci” ya faɗa yana nuna mata plate din pancakes da robar yougurt’ washe mashi baki tayi tana fadin”wallahi zaƙi gareta, kunnuwana har motsi suke yi” gaba daya suka sanya dariya, Ummi kamar zata shaƙe tsabar dariya, Angel dai abin duniya ya isheta, ita ala dole mai aji kada a zubda mata mutunci su kuwa ba ruwansu bayin Allah basu san ma menene ƙauyancin ba. “Malama, ki dauki spork da shi zakiyi amfani ki ci noodles din ba hannu ba” ummi ce tayi maganar tana nuna batul da spoon din hannunta, bata Iya cin abinci da cokali ba cos sunfi sabawa da hannu, jiki asanyaye batul ta ke faman ƴan kame kame ta rasa ina zata ɗauki cokali, Angel ce ta ɗauko shi ta miƙa mata, ta kar6a ta tsoma shi cikin indomie din batasan yadda zata kwasota ba, ganin yadda ummi take yi masu dariyar shaƙiyanci yasa ran Angel ya 6aci ta haɗe rai, muryarta aƙula tace da batul”idan bazaki Iya ci da shi ba, Ki ajiye shi ba dole” kallonta ummi tayi aikuwa ta galla mata harara, mamaki ya kama ummi ganin abun da Angel tayi mata. Batul kuwa ta ajiye cokalin taci gaba da ci da hannunta, Maganar Angel ta burge boss man, sai ƙara dubanta yake yi, abinci yake ci amma hankalin shi na akanta. Haris dai tun da ya dafi chips babu maijin motsinshi, sai idan anyi magana ya ɗago da ido Ya dube su. Mutun ɗayane baya cin abinci, Ya rasa sukuninsa, saboda mutun biyu dake zaune acikinsu, bayason baƙuwar fuska, uwa uba ummi dake ta kallon shi jefi jefi take bin shi da kallo kamar zata haɗiye shi. Sam Angel bata lura da yanayin da yake aciki ba, sai da Boss Man ya furta”meyasa baka cin abinci ne”? Tukunna ta ɗago ta dubi Danish don ta gane dashi yake magana. “Bakomai yake iya ci ba, danish me kake son ci”? Ta jefa mashi tambayar, shiru bai bata amsa ba, kamar tayi magana da kurma. Ummi tana yamutsa fuska tace”ai na lura kamar mune muka takura mashi, ƙwarama ka saki jikin ka, saboda atare zamu cigaba da rayuwa acikin gidan nan” Boss man yace”baya son baƙin fuska ne, amma tunda naga yafi sakewa da shi, Ki jaraba bashi wannan muga idan zaici” yai maganar tare da ruƙo plate din farfesu ya miƙa mata, bayan ta kar6a ta furta mashi”thank u” ta tura plate din agaban Danish. Cikin muryar raɗa tace”pls ka saki jiki ka ci, tunda gani atare dakai, banason kana damuwa” jinjina mata kai yai alamar toh, duk don ya saki jikin shi yasa ta sanya hannu a plate din ta soma ci shima ya sanya hannun shi suka cigaba da ci atare. Sun dauki lokaci suna cin abincin, sunyi kulu wash rabu hani’an kafin daga bisani ɗaya bayan ɗaya suka fara miƙewa, Masu aikin gidanne suka tattara kayan abinci, bayan sun kwashe komai suka gyara dining room din tamkar ba’a ta6a 6ata shi ba. Falo suka koma, kowannansu ya zamu wuri saman sofa ya zauna, kamar yadda Man Ya basu Umarni, yana daga zaune shida ummi suna fuskantar su, sanyin A.c sai ratsa fatar jikin su ya ke. Sun natsu suna jiran jin me zaice”da farko dai Ina yi maku barka da zuwa gidan nan, ina fata kunji daɗin kasancewa acikin shi” ya faɗa yana dubansu. Amsa mashi suka yi da eh, yace “good, ina fata zaku bamu haɗin kai, mu zauna peacefully babu faɗa babu cacar baki,” ɗaga mashi kai sukayi alamar eh. Ya ƙara da cewa”na fahimci bakomai ne kuka sani ba, to duk abunda baku gane ba kada kuce zakuyi gamon kanku, hakan zai iya haifa maku matsalar da bama fata, idan kunga abu kunaso kuyi amfani dashi baku san yarda akeyi ba, Ga auntyn ku nan yai maganar yana nuna ummi dake zaune saman sofa ta ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya. “Ku tambayeta zata koya maku, kada kuji shakkar komai, ku ɗauke mu tamkar iyayenku ko yayyanku, ina fata kuna jina”? Jinjina mashi kai su ka yi, Angel tayi shiru tana kallonshi, muryarshi ta tsaya mata aranta, ji take kamar tasan me irin muryar sai dai takasa gano komai. “Zaku Iya tambayar Ƴar uwarku Angel itama, don na fahimci kamar tafi ku sanin wasu abubuwan” amsa mashi su ka yi da toh. “Sannan duk abunda kuke buƙata ta 6angaren aike ni zaku yi ma magana, in sha Allah zanyi maku shi, Idan time din sallah yayi zanzo in tafi da mazan dake acikin ku muyi sallah akwai wurin da muke yin ibada acikin gidan nan, ina fata gaba ɗayan ku musulmai ne” ya faɗa yana dubansu Parveen tai karaf tace”banda Danish da Gabriel sunƙi kar6ar shahada” zaro ido ya ɗanyi yana duban fuskar Danish daya haɗe rai babu annuri. Gabriel Yace”nifa ƙarya take yi min, Nima musulmin ne” Da zolaya boss man yace”idan har dagaske kai musulmi ne to ya akai naji sunanka bana musulmai ba”?sunnar dakai ƙasa Yai yana faman sakin murmushi. Angel tace”nice namanta ban biya mashi shahada ba, ya faɗamin yana so ya musulunta shima” jinjina kai boss man yai, ya dawo da dubanshi gareta”shifa danish? Wani addini yake yi”? “Bashi da addini” dafe kai boss man yai”Eyyah banji daɗin jin hakan ba, kuma bashi da ra’ayin ya musulunta kamar Gabriel”? Girgiza mashi kai Angel tayi”bayasoma anayi mashi maganar ai, ranshi 6aci yake yi, shiyasa muka ƙyale shi” “Okey, kada hakan ya dameku, in sha Allah asannu zamuja ra’ayin shi” ta6e baki Danish yai jin abunda boss man yace. “Gabriel na dawo gareka, tunda kana so ka musulunta, babu buƙatar 6ata lokaci, Zan biya maka kalmar shahada saika maimaita da kyakkyawar niya” murmushi gabriel yasaki bashi ba hatta sauran ƴan uwanshi sunji daɗi, ba tare da 6ata lokaci ba, Ya biya mashi kalamar shahada, wani irin daɗine ya lullu6e su Angel, shima Gabriel din daɗin yake ji sai faman washe baki yake yi. “Ina taya ka murnar shiga addininmu, ko kana buƙatar na canza maka suna? tun kafin gabriel ya bashi amsa su Batul su ka yi saurin cewa”Eh wallahi acanza mashi, sunan shi wahalar faɗi yake yi mana,” dariya boss man yasaki jin abunda suka ce. “Okey, daga yau zamu dinga kiranshi da.....”bai ƙarasa sunan ba yai shiru yana kallon fuskar Gabriel duk sun ƙagara da suji wani suna za’a sanya mashi. “SAJEED” wani irin ihun farin ciki suka saki, Sunan yayi bala’en yi masu daɗi musamman Azeeza. “Ina fata sunan yayi maka”? Jinjina mashi kai Gabriel yai”eh, nagode sosai” Boss man yace”okey, daga yanzu sunan da zaku dinga kiran shi da shi kenan wato Sajeed, Kefa Angel meye asalin sunanki” farfari tayi mashi da ido kafin ta bashi amsa da cewa”Unaisah” Tamkar baisan sunan ba yace”wow suna mai daɗi, mai zai hana kema mu dinga kiranki da asalin sunanki” zumbura mashi baki tayi ba tare data furta komai ba, tana son asalin sunanta sai dai tafi son sunan Angel saboda daddynta ne ya za6a mata shi. “Dan Allah Angel ki amince mu dinga kiranki da Unaisah Yafi daɗi Allah” Batul ce tayi maganar, Hannah tace”nima nafison Unaisah din yana da daɗi” Haris ma yace”nima shine za6ina, Unaisah” Ta6e baki Angel tayi tare da kallon fuskar Danish don taji me zaice, batasan boss man na kallon ta ba, Ya fahimci tafi ƙaunar Danish akan sauran ƴan uwanta, saboda yadda take bashi muhimmanci. Da ido tayi mashi alamar ta amince da sunan ko kuwa”? Ɗaga mata gira yai alamar eh. Dawo da dubanta tayi akan fuskar Boss man”shikenan na amince, adinga kirana da Unaisah” Murmushi ya saki ba tare da sun gani ba saboda mask din fuskarshi. Javed ne yace “um sallah ma Angel ta koya mana amma bamu taba yi ba dama tace in muka zo zamu rinqa sallah da karatu” Jinjina kai yayi tare da fadin “karku damu zamu rinƙa karatu tare in sha Allah komai zaku iya wanda ya shafi addinin muslunci” Da alama sunji dadin maganar Jemimahh tace”wai kai ba zaka cire abun fuskarka ba”? Girgiza mata kai yai”a’a” tace “to meyasa baka son mu ganka? Ko dai mummuna ne kai baka da kyau”? Dariya ce ta kubce mashi. Azeeza tace”bakya jin magana jemimah ina ruwanki da shi? Ke komai sai kin nuna zaƙewa” harara jemimah ta watsa mata”Ni ki ƙyale ni,” ta faɗa tana duban shi”dan Allah ka cire muga fuskarka” Javed yace”nima inason naganka, tun da kace atare zamu rayu agidan nan, please ka cire mu ga fuskar ka. Girga mashi kai yai”Ku yi haƙuri ba yanzu ba, tunda muna atare wata rana zaku ganni” Angel tace”babu komai, Allah ya nuna mana lokacin, Ni sai na ke jima kamar nasan muryarka don dai kace ba yanzu zaka buɗe fuskarka ba ni kuma da saina gane wanene kai” hakanan ta faɗa bada wata manufa ba, tasan batasan shi ba. Murmushi yai ba tare daya tanka mata ba, kallon Ummi yai, tun da ta zauna tana sauraron su bata ce komai ba “Ba abunda zaki faɗa masu ne”? Yamutsa fuska tayi kamar bata son furta magana tace”naso yau in taimaka masu su gyara kansu, amma nabari sai zuwa gobe ko jibi, idan na ƙara hutawa” Yace”okey, ku tashi mu tafi inaso zan nuna maku ko’ina na cikin part dinku, duk abunda kuka gani wanda kuke neman ƙarin bayani akanshi Ni zaku tambaya” suka amsa mashi da toh. Miƙewa sukayi Ummi ma ta miƙe don tana son itama ta ƙarema ko’ina na part din kallo, cikinsa da wajensa. Yinin Ranar sunsha yawo, Sunga abubuwan ban mamaki dana Al’ajabi, ido ya samu abinci, kamar karsu dawo cikin gidan, Boss man yasha tambayoyi kamar ƴan jarida, duk abunda basu gane ba sai sun tambayeshi ba ƙaramar wahala yasha ba, itama ummi tana taimaka mashi wurin amsa masu tambayarsu, duk yawon da suka sha basu leƙa wajen gidan ba, kuma basu shiga sauran part din ba. *JOS CITY* Idan muka koma 6angaren Alhaji ubaid, tunda garin Allah Ya waye da sassafe Benazir ta farka tana sambatu akan mijinta da ƴarta, Alhaji ubaid Ya jira kiran Dr.shureim sai dai shiru, har kiran layin wayarshi yai amma bai ɗaga ba, ya kira Alhaji musa akaci sa’a kiran ya shiga kusan sau goma tana ringing ba’ayi picking ba, gashi lokaci yana ta tafiya babu alamun zuwan Shureim, daga bisani suka kira likita domin duba lafiyar benazir, bayan ya duddubata ya faɗa masu cewa lafiyarta ƙalau, sai dai akwai abun da ta ƙwallafa rai akanshi yaji tana fadin mijinta da ƴarta yace to kada su kuskura suce zasu faɗa mata zancen babu su, don a halin da take aciki yanzu bazata Iya jurewa ba, zata Iya samun ta6in hankali, zaifi suja baki suyi shiru, sannan suci gaba da kwantar mata da hankali har zuwa lokacin da zata samu natsuwa sosai, tukunna su faɗa mata, sunji dadin shawarwarin da likitan ya basu, bayan tafiyarshi cikin ikon Allah, Benazir ta dawo hayyacinta a lokacin da basu yi tsammani ba, ganin Iyayenta a gefe da gefen gadon da take akwance yasa ta rushe da kukan farin ciki tana ambaton sunayensu haɗi da roƙon yafiyarsu akan babban laifin da ta aikata na guduwar da tayi ba tare da sanin su ba, tayi mamakin jin suna kwantar mata da hankalinta, sukace su basu ruƙeta aransu ba, sun yafe mata, ta daina kuka komai ya riga daya wuce, tuna baya baida amfani tun da ya riga da ya faru, ƙaddarace da babu wanda ya isa ya canza ta, haƙiƙa taji daɗin kyakkyawar tarbar da ta samu awurinsu tayi tsammanin zasu koreta ne idan sun ganta, saima suka koma suna lallashinta haɗi da tarairayarta, abinci ma abaki hajiya layla ta bata shi, duk bayan ƴan mintuna sai ta tambayesu ina mijinta da jinjirar data bari a cikin kwamin wanka? tana son tagansu, idan suna agida dan Allah su taimaka su kaita wurin su, hajiya layla ta bata haƙuri da cewa sunyi tafiya basa a ƙasar amma tana da tabbacin sun kusa dawowa, sai lokacin tace toh ita yarinyar ta rayu? Waye ya rene ta harta girma? Kuma ya sunanta”? Hajiya layla tace”ta rayu mana, kyakkyawar budurwa ta ɗauko hasken fatarki, kamannin fuskarta ne dai ta ɗauko na daddynta, hankalinta ba ƙaramin kwanciya yayi ba, tana ta faman sauke ajiyar zuciya tace”baki faɗa min sunanta ba? Kuma tasan ni? An faɗa mata sunan mahaifiyarta? Kuma Kuna nuna mata hotona”? Shiru hajiya layla tayi don batasan amsar da zata bata ba, ita kanta ba zumunci take yi da tajuddeen ba, saboda bada son ranta ya auri Benazir ba, shiyasa ko zuwa gidan bata ta6a yi ba, tun lokacin da suka koma dubai da zama, a hotone ma ta ta6a ganin Angel din, taji nauyin amsar da zata ba benazir, daƙyar ta Iya furta mata sunanta Angel, tana faman murmushin yaƙe tace ai tasanki ya za’ai mu ƙi nuna mata hotonki, duk in tajudden ya kawota gidan nan sai mun nuna mata hotunanki, Yarinyar tana sonki sosai, kullum maganarta ina mamanta take? Yaushe zata dawo? Meyasa kika tafi baki waiwaye ta ba’ jin hakan yasa benazir ta fashe da kuka, Hajiya layla duk tasha jinin jikinta, fargabarta ranar da Allah zai haɗa benazir da ƴarta idan har tana araye tabbas zaiyi wuya yarinyar ta amince da ita, ga kuma ƙaryar data faɗa mata. Cikin shessheƙar kuka benazir tace”amma dai baku fada mata a yanayin da na tafi nabarta ba ko”? Hajiya layla tace eh bamu faɗa mata ba, mun dai ce mata kin 6ace ne ba’asan inda kika tafi ba, to dayake yarinyar tana da tawakkali kuma tana samun kulawar tajo da kuma kulawar da muke bata hakan bai dameta sosai ba” baiwar Allah benazir jikinta duk yai sanyi, tace Ina aneelerh da mijinta”? Hajiya layla tace ai mijin aneelerh baya nan shima tare suka yi tafiyar, ta matsa lamba akan tana son akaita gidansu Aneelerh don taganta, Alhaji ubaid ya sanar da ita cewa ai basa garin jos sun koma abuja da zama, badan taso ba ta haƙura, damuwar hajiyar laila ɗaya kada tace su nuna mata hoton ƴarta saboda babu maishi acikinsu, har ƙwara Alhaji ubaid wata’ƙil asamu hutunanta na yarinyata saboda yana son yarinyar, cikin ikon Allah benazir bata tambayesu game da hoton Angel ba, saboda halin damuwar data shiga gani take kamar bazata ta6a ganin mijinta da ƴarta ba, duk da mommynta ta kwantar mata da hankalinta. Masu gadin gidan kusan sau uku suna shigowa cikin gidan domin duba lafiyar benazir, duk sun damu da ita, haka zalika zainab takasa samun sukuni duk bayan ƴan mintuna saita leƙo ta dubata, hakan ba ƙaramin daɗi yayi mata ba ganin yadda kowa ya damu da ita. Tana akwance saman gadonta, hajiya layla tana a gefenta, a lokacin Alhaji ubaid Ya koma dakinshi, damuwar duniya ta ishe shi, tun da ya jaraba kiran layin shureim dana Alhaji ubaid basu ɗaga ba, ya rasa sukuni, sai faman yin zarya yake yi acikin ɗakin shi, kaf family dinsu babu wanda yasan da dawowar benazir, saboda bai sanar da su ba, hatta mutanan da suke zumunci da su bai faɗamawa ba, saboda mai gemu ya basu shawarar su dan jinkirta tunda ba’asan wanene yai silar yi mata asirin ba, zasu Iya ƙara cutar da ita idan suka ji cewa tana araye kuma ta dawo gida, da ace Iyayensu na araye da kuwa sune mutun na farko da zai fara sanarmawa donsu taya shi murna sai dai babu su, mutum biyu ne yafi yarda dasu ƙanin shi Alhaji musa sai ƙanwarsu autar gidansu Hajiya Laurat, second wife din mai girma sharafuddeen obinna, itama ya jaraba kiran layin wayarta bata yi picking ba, abun duniya duk ya ishe shi. tunda tayi wanka ta canza kayan jikinta zuwa rigar shan iska bata ƙara saukowa daga saman gado ba, ta tsare hajiya layla da tambayoyi “Mommy shifa yaya shureim ko baya kasar ne”? “Yana agidan uncle dinki” “Baku faɗa mashi na dawo ba ne? “Mun faɗa masa tun jiya da daddare shima yayi farin ciki hada kukanshi, yace ma yau zaizo saboda ke’ murmushi tasaki”naji dadi Allah ya kawo shi lafiya, nayi missing din yayana” Hajiya layla ta amsa mata da ameen. Kafin benazir ta ƙara furta wani abu, Alhaji ubaid ya shigo da sallama abakinshi, atare suka ɗago suna kallon shi, da sauri benazir ta miƙe zaune tana ambaton sunanshi Murmushin yasakar mata kafin ya zauna daga gefen gadon yana dubansu yace”Bansan meya faru ba, Ina ta kiran layin shureim dana musa babu wanda ya ɗaga acikinsu, Har laurat na jaraba kira itama bata ɗaga ba” kafin wani ya furta magana acikin su ba zato ba tsammani, sautin ringing din wayarshi ya daki kunnuwansu, hajiya layla tace”wata’ƙil wani daga cikin su ne yake kiranki” da sauri ya ciro wayar daga aljihun shi ya duba sunan me kira, murmushi ne ya bayyana akan fuskarshi “Wanene”? Layla ce ta tambaya ganin yadda ya saki fuska “Musa ne Ke kira” ya faɗa tare da picking call din Ya kara a kunnan shi Saboda ji da kai na Alhaji musa sai da Ubaid Ya fara yi mashi sallama tukunna ya amsa mashi da cewa”wa’alaikum salam, ina kwana yayana fatan kun wayi gari lafiya” Alhaji ubaid na faman washe baki yace”lafiyalou, ya iyalin naka”? “Suna lafiya” atakaice ya amsa mashi, tun da ubaid ya fara waya, layla da benazir suka zuba mashi ido suna kallon shi duk da basa Iya jin me alhaji musa yake fadi “Shureim bai faɗa maka zancen dawowar benazir ba”? Ya tambaya ne don yaji baya da niyar yi mashi maganar Da gadara Ya furta”ya faɗa min, tun ɗazu da safe, na tayamu murna, Ina fata tana lafiya” Alhaji ubaid yace ai gatanan ma zaune kusa dani, Ko in bata wayar kuyi magana ne”? Da sauri yace”No need, basai munyi magana da ita a waya ba, dama dalilin da yasa na kira naga missed call dinka ne, ɗazu da safe shureim ya shirya zai taho nan jos, Ni na hana shi, nace mashi ya bari zanyi maka magana kuzo nan abujan gidana” da mamaki Alhaji ubaid yace”amma dai wasa kake yi min ko? Tayaya zakace min in kwaso iyalina inzo gidan ka? Ni dakai waye ya dace yazo gidan wani? ai nayi tunanin idan na fada maka dawowar benazir jiki na rawa zaka kwaso iyalinka kuzo nan domin tayani murna sai kuma naji akasin hakan” Alhaji musa yace”bazan Iya zuwa jos din bane, saboda Ina da ayyuka dayawa da zanyi, shiyasa nace kuzo nan ɗin,” Mamaki da al’ajabi ne akan fuskar hajiya layla, don taji martanin da alhaji ubaid Ya bashi. “Baikamata kace min haka ba, yanzu ayyukanka har sunfi ganin ƴata da za ka yi muhimmanci? Babu alamun damuwa a muryarshi yace”yaya kasan banason jan magana, meye aciki don nace kazo gida na? Laifine? Alfarma nake nema bawani abuba, idan ba zaka yi min ba zan aje waya” Gyaɗa kai alhaji ubaid yai”shikenan, zamu fidda lokaci mu shigo abujan” Ya amsa da yawwa, sannan bana buƙatar ku zo a mota, Ni zan shirya maku komai na tafiyarku” amsa mashi yai da toh, daga haka Alhaji ubaid yayi rejecting call din, yana mai mamakin Halin Alhaji musa. “Me ku ka tattauna ne”? Layla ce ta jefa mashi tambaya Muryarshi a raunace ya furta”yace bazai samu damar zuwa nan ba, shine ma ya hana shureim zuwa saboda yafi son muje can gidan shi” Ta6e baki hajiya layla tayi”shine kai kuma sai ka ce mashi zamu samu lokaci muje can din ko? Jinjina mata kai yai alamar eh, masifa ta soma zazzaga mashi”kasan Allah babu inda zamuje sai dai kai daya gama asirce ka kama hanya ka tafi,Ni ban ta6a ganin mutun mara kunya irin shi ba, yarinyar ta 6ace tsawon shakaru sai jiya tsakar dare ƙarfe shabiyu tadawo bata ahayyacinta shine zaice mu kwasa mu tafi gidansa saboda muke son yaganta? Kwata kwata bashi da tunani kuma baida hankali, kaida kakeyi mashi biyayya gayanan shi bai damu da ƴarka ba, ...” tun da tafara faɗa, jikin benazir yai sanyi duk sai taji ba daɗi, Cikin sanyin murya tace”mommy dan Allah ki yi haƙuri, kada hakan ya dame ki, Ni banga laifin shi ba saboda ai ni na gudu da kaina ba korata akayi ba, wata’kil Yana jin haushin abunda na aikata shiyasa yace muje can....” Katseta hajiya layla tayi”benazir ba abunda kike tunani bane, mutumin nan baya ƙaunarki, saboda bai damu dake ba, tun lokacin da kika 6ace bai ta6a magana akanki ba, Mune kaɗai muka damu dake munyi nemanki har mungaji mun fidda rai da kina araye, amma musa bai ta6a sanya baki akan maganar 6atanki balle har ya taimaka wurin bada gudummuwar mu nemo ki.....” Muryar Alhaji ubaid ce ta katse mata maganarta”kidaina faɗa mata wannan maganar, bai dace ba, taya zakice kawunta ƙanin mahaifinta bai sonta? Akan wani dalili? Shiya furta maki da bakin shi” Harara layla ta watsa mashi”alama nagani shiyasa nace haka” Idanuwan benazir ne suka cicciko tab da ƙwalla, cikin sanyin murya tace”Ni ban damu ba, koda ace baya sona, tun da Iyayena suna sona Alhamdulillah, soyayyarku kaɗai ta ishe ni sai kuma ta mijina da ƴata, da kuma Yayana, sannan Ni na amince zanje abujan bawai don saboda shi ba, saboda inason ganin Aneelerh” Girgiza kai layla tayi”bafa zan ta6a bari ki je gidan mutumin nan ba, Saboda Ni ban yarda da shi ba, Idan kuma kika takura akan kinason zuwan bazan hanaki ba sai dai ki sani bazan biku ba” babu alamun wasa akan fuskarta tayi maganar. Magiya benazir ta dinga yi mata akan ta amince suje da ita, don ita batason suyi nesa da juna, daƙyar layla ta amince zata bisu abujan, da wata manufa a ƙasan zuciyarta don taci alwashin idan sukaje gidan Alhaji musa saita fada mashi baƙaƙen maganganun da zasu hana shi sukuni, yanzu dai sun tsaida magana zuwa jibi zasu yi tafiyar. Aranar shureim ya samu damar kiran Alhaji ubaid ya fada mashi uzirin daya hana shi ɗaga kiran shi, bayan sun gama magana, har benazir yace abata waya su gaisa, sun jima suna waya da ita kusan awanni suka kwashe, kafin daga bisani yayi masu sallama. Idan muka koma 6angaren zahra tun bayan da ta koma gida, babu mutunci a tsakaninta da Aneelerh ko gaisuwar arziki bata haɗa su, ta canza mata bata sakar mata fuska ba kamar yarda suke ada ba, aranar mahboob yai mata maganar motar ta da wayarta yace dama jingina yabada su, idan tana so zata bada kuɗin adawo mata dasu, farin ciki kamar zata zuba ruwa ƙasa tasha dama bada Son ranta ta bada su ba, ta haɗa mashi kudin ta bashi, a daren ranar ya dawo mata da su, tuni ta fara amfani da wayarta bayan ta mayar da sim dinta. A washe garin ranar laraba suka fara shirye shiryen fara aiki a Obie estate tare da sauran Interior designers dake aiki a ƙarƙashin company dinsu, tuni kaya sun iso daga dubai, Hankalin zahra ya kwanta bata da sauran damuwa yanzu, ta ƙagara gobe tayi don suje su fara gudanar da aikinsu saboda gagarumin taro ne zasuyi idan obie zai yi birthday kamar shagalin biki saboda dukiyar da suke kashewa wurin ƙawata gidan, shiyasa zasu fara yi masu aiki tun alhamis kafin Juma’a da za’a gudanar da shagalin ❤🤍❤🤍❤🤍❤🤍❤🤍❤🤍❤ ❤ANEELERH❤ A zaune take saman mirror chair, bata jima da fitowa daga wanka ba, ta zauna ne domin gyara jikinta, ƴar rigar wanka ce a jikinta, ta kasa ta6uka komai hannunta na a ruƙe da wayarta layin hajiya adama take dannawa kira, phone din na fara ringing taji sanyi ya ratsa zuciyarta, bayan hajiya adama tai picking call din Aneelerh ta yi mata sallama, on the other hand muryar Hajiya adama ta bayyana da alamun kasalar bacci”wa’alaikum salam daugher in-low, ya ki ke ya gidan yasu mami da ummi” Da fara akan fuskar Aneelerh tace”Lafiya lou mommy, yasu daddy fatan duk kuna lafiya” “Alhamdulillah Aneelerh, halan kin ji ni shiru yau ban neme ki ba shiyasa kika kira” Cikin jin kunyar maganarta Aneelerh tace”haka ne dama nakira ne don mu gaisa” da zolaya Hajiya adama tace”kodai kin kira ne don ki faɗa min jibi zaki zo ɗaukar baby junaid tun da time ya cika” Ƙumshe dariya Aneelerh tayi kamar tana agabanta sai faman noƙe kai take yi, jin tayi shiru yasa Hajiya adama cewa”dama nasan ba zaki faɗamin ba, to ki kwantar da hankalinki, in sha Allah friday zanzo dashi gidan naku” Abeelerh taji dadin maganarta”nagode mommy, Allah yakaimu lafiya. “Nima ngde ki kulamin da kanki, ki kuma gaishe min da su mami, junaid din bacci yake yi zuwa anjima idan ya farka zan kira ki video call ku gaisa, dama yanata sambatu yana ambon shi wurin mommy zaije” Murmushi Aneelerh tadan saki kamar tana agabanta”zasuji nima agaishe da daddy, “ daga nan suka yi sallama da juna. ❤A washe garin ranar Alhamis❤ Wuraren sallar Asuba Unaisah tana zaune saman darduma ta zumbula hijabi, Batul tana akwance agefenta saman dardumar, tun jiya da suka fara sallah da zarar sun gama sai ta kwanta wahala take ji idan tana yin sallah hada ƙarin rashin sabo har ƙwara ita akan su azeeza masu yin kalle kalle in suna yin sallah, mazan cikinsu sunfi natsuwa shi kanshi Boss man yayi mamakin yadda suka Iya sallah da karatunta ya ƙara jinjinama Unaisah akan ƙoƙarinta, yanzu karatun addinine zasu ƙara koya masu dana boko kafin asanyasu makaranta bayan kammala bincike akansu. Tafin hannayenta biyu ta ɗaga sama tanayin addu’a muryarta abuɗe take fadin “Ya Allah ka jiƙan ƴan uwanmu da suka rigamu gidan gaskiya, Ya Allah kakai rahama ƙabarinsu, Ya Allah kabamu ikon cinye jarabawarka, Ya Allah ka bamu haƙuri da juriyar rungumar duk wata ƙaddara da zata riske mu mai kyau ko mara kyau, Ya Allah ka tsare min sauran ƴan uwana da nake atare dasu da sauran al’ummar musulmai, ya Allah ka bamu nasara akan burinmu da muke son cimmawa na ganin mun kawo ƙarshen azzaluman mutanan da suka ƙasƙantar da rayuwarmu suka cutar damu Allah kada ka basu nasarar cigaba da aiwatar da zalunci..........” cikin shessheƙar kuka ta ƙare maganar, hawaye tuni sun wanke fuskarta tunawa da rayuwar sauran ƴan uwansu ƙananun yara da ake cutarwa a cikin kurkukun ƙaddara, tasan ba zasu fasa cin zarafinsu ba suna lalata rayuwarsu kamar yadda su ka yi silar mutuwar ƴar uwar su Unaiza ƴar gidan daddy da Majnoon yaran da ba suji ba basu gani ba. Sautin kukan Unaisah ya karaɗe cikin ɗakin, batul ko motsi batayi ba, tunda ta kifa kanta saman darduma bacci mai dadine yai awon gaba da ita ko addu’a bata samu damar yi ba. “Bazan ta6a mantawa da wasiƙar da kika bani ba, kuma bazan manta sunan mugun mahaifinki ba, In sha Allah zan ɗaukar maki fansa koda kuwa zan jefa rayuwata ne cikin haɗarin da zaiyi silar mutuwata ne.....” cikin karyayyar murya take furta kalaman masu ta6a zuciya, idanuwanta sun kaɗa sunyi jawur, hawaye sun kwanta saman fatar fuskarta har zuwa gaban hijabin dake a jikinta. “Ya Allah ka bayyana min daddyna idan yana araye, Inason nasake ganinshi shi kaɗaine nake da burin haɗuwa dashi a duniyar nan” Tunda ta fara karanta addu’o’i, yana la6e bakin ƙofar dakinsu Yana sauraronta, basu jima da dawowa daga sallar asuba ba, ya rakosu Sajeed ne tuni sun nufi bedroom dinsu. Zuciyarshi ta karaya da jin kalamanta, abubuwa dayawa sun so su rikitar dashi, kamar yarda take zubar hawaye haka shima yake zubar da su saman fuskarshi, farar jallabiyace a jikin shi ya sanya mask akan fuskarshi, Ji yake kamar ya faɗa ɗakin Ya rungumota a jikinshi, duk a tunaninshi Unaisah ta manta dashi ashe ba haka bane yana aranta har addu’a tana yi mashi, haƙiƙa yayi farin ciki mara misaltuwa, cikin sanɗa Ya juya zaibar ƙofar ɗakinsu kwatsam muryar Jemimah ta tona mashi asiri da ƙarfi ta furta”BOSS MAN!!!” cak Ya dakata da tafiya, hatta Unaisah dake a ɗaki saida taji sautin sunanshi da jemaimah ta ambata, aiko da sauri ta miƙe ta nufi kofar fitowa daga ɗakin. A hankali Ya waiwaya baya yana duban jemimah, tasha dogon hijabi ajikinta kamar zatayi tuntube da gudu ta nufo shi, Azeeza ma ta fito tabiyo bayanta itama hijabin ne a jikinta. Kallon da yake binsu dashi tamkar kallon da uba yake yiwa ƴa’ƴanshi ne, saboda yana matuƙar ƙaunar yaran ya dauke su kamar jininsa, musamman yadda suka fara nuna mashi yarda, Jiya izuwa yau sun saki jiki dashi, duk in zai gifta sai sun ambaci sunanshi kamar su suka raɗa mashi. Jemimah na ƙarasowa ya sanya hannu biyu ya ɗagata sama, ta kama tiƙar dariya tana fadin”dan Allah kada ka sauke ni ƙasa” Fuskarshi dauke da murmushi yace”raini ya fara shiga tsakanina dake ko? Tun jiya badama kiga na gifta sai kin ƙwala min kira kamar wani tsaran wasanki, bakisan ni baba ba ne”? Tace”to aini daɗin sunan nake ji, Boss man shiyasa nake kira,” tana magana yana kallon jajayen kumatunta bakomai yake tunawa ba face Angel ɗinsa, lokacin ƙuruciyarta yaci wuyarta yakuma ji dadin shiriritarta. “Jemimah Ina fata yau kinyi sallah ta hankali, don jiya Azeeza ta faɗa min abun kunyar da kika yi” ya faɗa yana sauketa ƙasa, duban Azeeza yai har ya miƙa hannu zai ɗauke ta ganin ta tsare shi da ido yayi tunani ko itama so takeyi ya daga ta sama, da sauri ta maƙe mashi kafaɗa tana fadin”ai ni ba ƙarama bace, Na girmeta da shekaru” dariyace ta kubce ma Boss man. “Oh saboda kin girmeta shine bakyaso in ɗauke ki? To aini a wurina jinjira nake kallonki” ya faɗa tare da ɗaukarta ya ruƙeta a hannunshi, Kunyar duniya ta cika Azeeza sai faman noƙe mashi kai take Yi. “Kasan Allah Boss man itama Azeeza bata Iya sallaba, ko karatun sallah ma bata iyaba, idan nayi ƙarya kace ta maimaita maka Rabbighfir li” tuntsirewa yai da dariya. Ran Azeeza ya 6aci tace”wallahi ƙarya take yi min, ai acikin zuciya nake yin karatun sallah tayaya har tasan abunda nake faɗi acikin zuciyata” gwalo jemimah tayi mata”oho dai, ni dai duk rashin Iya sallana nasan yadda ake karatun sallah” Idanuwan Azeeza tuni sun cicciko da ƙwalla, boss man yace”badai kuka zakiyi min ba”? Cikin shessheƙar kuka tace”wallahi ƙarya take yi min na iya karatun sallah, kaji na rantse maka, idan ma kanaso sai in faɗa maka kaji, itace fa bata Iya komai ba, jiya muna sallar isha’i tana buga min dundu abayana, kuma ban rama ba” Kwantar da kanta yai saman kafaɗar shi haɗi da daura hannun shi saman kanta Yana lallashinta. Idanuwanshi akan jemimah dake ta dariya, dama tun jiya da yayi tozali da fuskarta ranshi ya bashi daƙyar in bata iya rashin ji ba, kamar dai Angel dinsa da tana ƙarama . Lallashinta yai”yi hakuri my daughter, kuruciya ke damunta dama kince min kin girmeta don haka inaso ki ruƙe girmanki kada ki biye mata, idan tayi ba dai dai ba kiyi mata nasiha a matsayinki na babba mai hankali da tunani, in sha Allah wata rana zata daina ne” tunda ya fara magana Azeeza take amsa mashi da toh, jemimah kuwa sai faman ta6e mashi baki take yi hada ruƙe qugu, tana fadin”tab ita ɗin zata min nasiha, Allah ya kiyaye, ai ni bana jin maganar kowa idan bata Unaisa ba” Mamaki jemimah take bashi gata ƴar ƙarama idan tana magana sai kayi tsammanin ta ɗare shekarunta. Sauke Azeeza yai saman floor, yace da ita”ki ruke hannun ƴar uwarki ku tafi ɗaki, da anjima idan nashigo zamuyi magana” ta amsa mashi da toh nagode, kafin ta ruƙo hannun jemimah tuni ta watsa da gudu ta nufi hanyar komawa ɗakinsu duk don kada azeeza ta ruƙe hannunta. Murmushi ya saki yayin da yake bin bayansu da kallo, Har ya ɗaga ƙafa zai nufi hanyar fita ɗakin, Muryar Unaisah ta dakatar dashi”Boss” A hankali ya juya baya yana dubanta tun ɗazu tana tsaye tana kallon su, sai da ta bari su Azeeza sun tafi tukunna ta yanke shawarar yi mashi magana. Ta wanke hawayen fuskarta, tana tafiya hijabinta na ja da ƙasa, har gabanshi ta ƙarasa ta tsaya, tsananin tausayinta ne Ya kamashi, ji yake kamar ya rungumeta koya rage radadin da yake ji acikin zuciyarshi, sai dai ba halin yin hakan yasan yadda take da masifa idan Ya kuskura yai hugging dinta tsaf zata mare shi tunda batasan wanene shi ba. Ido cikin ido suke kallon juna, tsawon mintuna kafin ta numfasa tace”ina kwana? Ka tashi lafiya? ya fama da mu” Cikin sanyin murya yace”lafiyalou Unaisah, ya akai naga idanuwanki sun canza launi, ko baki da lafiya ne”? Girgiza mashi kai tai, cikin disasshiyar murya ta furta”lafiyata qalou, kasalar bacci ce,” Jinjina kanshi ya ɗanyi, ji take kamar tace mashi ya cire face mask dinshi sai dai bata son ta takura mashi don ta fuskanci bayason su san wanene shi. “Kin tsare ni da ido kina kallona ko akwai wani abu da kike son fada min ne”? Murmushin gefen fuska ta saki, Har dimples dinta suka lotsa, “Dan Allah taimako nakeso kayi min sai dai bani da ko sisi a hannuna” “Kada kiji komai ki faɗi koma menene zanyi maki shi in sha Allah” Tana faman noƙe kai tace”um dama waya ce da Aunty laura ta bani kyauta ɗaya daga cikin likitocin da suka kula da lafiyarmu a america, to wayar babu sim aciki gashi inason in fara amfani da ita” ta faɗa tana duban fuskarshi, ya natsu yana sauraronta idan tana magana kuruciyarta yake tunawa, yarinyar data sanya shi ciwon kai da zazza6i, cikin ikon Allah yanzu ta ƙara girma ta zama kamilar mace ta mallakin hankalinta. “Sim kaɗai kike buƙata”? Girgiza mashi kai tayi”a’a, da Allah kada kace na takura maka, “ aranshi ya ayyana takura kuma ta nawa My Angel, nida nayi jinya gadon asibiti saboda ke” “Cikin Kayan da aka tsunto mu da su a daji, akwai backpack ɗina inason jakar, gadonmu ce bansani ba ko sojoji sun haɗo mana da su” ta tambaya tana dubanshi. “Duk wani abu naku yana atare damu, saboda muna buƙatar abubuwan da zasu taimaka mana wurin yin bincike tamkar shaidune agare mu, amma kada ki damu zan ɗauko maki backpack din, da anjima zan shigo maki da ita tare da sim din da zaki sama wayar” wani irin farin cikine Ya lullu6e Unaisah, godiya tadinga yi mashi, yace mata yaji daɗin ganin farin cikinta, juyawa tayi da niyar ta koma ɗaki, hijab din jikinta dake jan ƙasa ta harɗe ƙasan takalmin ƙafarta, gaba ɗaya ta tafi zata kife kasa da zafin nama Boss man Ya ruƙo damtse hannunta Ya janyota ta faɗa saman kirjinsa, har saida taji gabanta ya fadi, ƙanƙameta yayi da hannayensa biyu daya zagayo dasu ta bayanta, Jikinta yai wani irin sanyi kamar wadda aka zare ma laka, bawan Allah tunda ya rungumeta yai tighting dinta kamar karya saketa, ita kanta takasa raba jikinta daga nashi, saima hannayenta data zagayo dasu saman bayanshi, ta ƙankameshi, Jini ɗaya ba wasa ba, sai faman sauke ajiyar zuciya suke yi at same time, batasan ya akai ba ta tsinci kanta da jin hawaye sun cicciko idonta, shi kuwa tuni sun wanke face mask dinshi.A hankali yake ɗan bubbuga bayanta kamar yana lallashinta, tsawon shekaru rabon daya ji ɗumin jikinta anashi, bazai ta6a manta ƙaddarar data afka masu ba, wadda tayi silar rabuwarsu, bazai ta6a manta sautin shesshekar kukanta da muryarta a lokacin da yake gudu dasu cikin mota tana daddy hancina jini, haka zalika bazai ta6a manta lokacin da ya jefar da ita cikin ruwa ba duk don ya ceci rayuwarta Sai gashi cikin ikon Allah ta rayu Allah ya tsare mashi ita, Allah kaɗai yasan irin wahalhalun rayuwan data fuskanta da ƙananun shekarunta..... Kamar yadda yake tariyo rayuwarsu haka itama take tunano daddynta, ji take kamar shine ya rungumeta, shiyasa ta ƙara narke mashi tayi lamo saman wide chest dinshi...... Gaba ɗayansu sun shiga yanayi mara misaltuwa, ba zato ba tsammani Boss Man yaji dirar wani abu saman bayanshi, da sauri ya ɗago da kanshi idanuwan shi sun canza launi sun kada jawur kamar mai fama da ciwon ido, yayi mamakin ganin pillow da aka jefo mashi ya fadi ƙasa, da sauri ya ɗaga ido sama don ganin wanene ya wurgo mashi pillow saman bayanshi, karaf idanuwan shi suka sauka akan Danish dake tsaye can second floor, hannun shi ruƙe da wani pillown Yana niyar ƙara jeho mashi, fitowar shi kenan daga ɗaki idanuwanshi suka hango mashi Angel ɗinsa rungume da wani ƙato, shine fa yaje ɗaki ya ɗauko fululluka har biyu Ya jeho mashi ɗaya. Ya haɗe fuska babu annuri, kayan bacci ne ajikinshi riga da wando launin pink sunyi bala’en yi mashi kyau. Harara ya watsa ma boss man, ganin Angel taki barin ƙirjin mutumin yasa shi ƙara daddagewa ya wurgo mata pillow, da sauri boss man Ya tarbe pillown a hannun shi, Lamarin ya ɗaure mashi kai, sai yanzu ya gane dalilin dayasa yaron yaƙi sakar mashi fuska tun jiya yake daure mashi fuska, ashe kishi ne ke damun shi. “Unaisah”! Jin boss man ya ambaci sunanta yasa ta ɗago da kanta tana kallon shi, mamaki ne ya kamata ganin pillow a hannun shi, da ido yai mata nuna da bayanta, da sauri ta juya don ganin wanene, a tsaye ta hango shi ya ruƙe qugu yana aiko masu da harara. Batasan sa’adda ta tuntsire da dariya hada dafe ciki, da zolaya boss man yace”kishine ya addabe shi shiyasa yake jifar mu da pillow, faɗa min meke a tsakaninki dashi. Tana dariya tace”babu komai, shaƙuwace a tsakaninmu, baya son yaganni tare da wani idan ba ƴan uwanmu ba, haushi yake ji” “Kice ƙwara in lalla6a in gudu, tunkan ya sauko don wannan har buguna zai Iyayi, “ ya fada tare da damƙa mata pillow din hannun shi, Ya juya da sauri ya nufi ƙofar fita Yana faman sakin murmushi, bai ta6a ganin namiji mai kishi ba irin Danish. Zukunnawa tayi ƙasa ta ɗauki ɗayan pillow, ta haɗa dana hannunta, ta nufi upstairs, Har tsoron tunkarar shi take Ji, saboda yadda ya kumbura fuska, soft red lips dinsa sunyi suntum da su” Koda ta haye up din, taga Ya dunƙule hannu kamar zai nausheta, wurga mashi pillows din tayi saman faffadan kirjinshi, da gudu ta sauko down tana tiƙar dariya, akan idonta ya tattara pillows din ya nufi dakinshi ya shige. Yau da wuri suka yi breakfast dinsu, saboda gyaran jikin da ummi zatayi masu. A Katafaren Home beauty station ɗin dake a cikin part dinsu, saboda su aka tadani komai na cikinsa, ɗakin Ya haɗu, bangon dakin beauty shelf ne An jera Kayan gyaran jiki kala kala, dana gyaran gashi acikin kowani shelf, hada foot care product and skin care product, Ga wani faskeken mirror a jikin bango, daga gabanshi wasu hadaddun kujerune kusan guda takwas, A saman kujerun kowa Ya samu wuri Ya zauna su shidda ne matan dake acikinsu, banda mazan tun bayan da suka kammala yin breakfast suka tafi ɗaukar karatu a inda suke Yin sallah. Suma matan acan za’a dinga yi masu karatu. Kowaccensu tana sanye da bathrobe a jikinta, Ummi ce ta basu rigunan, saboda da taji daɗin gyara masu sumar kansu. Kujerar farko Unaisah ce zaune asamanta, ta biyu batul ce akusa da ita, sai Parveen itama ta hakimce saman tata kujerar, daga gefenta Jemimah da Azeeza ne saman nasu kujerun bayan su sai Hannah. sun natsu suna kallon faces dinsu ta cikin madubi sai faman sakar ma juna murmushi suke yi kamar wasu zautattu, daɗi suke ji za’a gyara masu sumar kansu, har sun fara imaginning din kyawun da zasuyi babu mai magana acikin su, saboda ummi tana acikin dakin ta hanasu surutu tana a sanye da dogon wando ƴar rigar data sanya daƙyar ta rufe cibinta, babu mayafi akanta. “Dawa zamu fara” ta faɗa tana dubansu, har suna haɗa baki wurin furta Ni, “bari in za6a da kaina” ta fada tana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya, a ƙarshe ta tsayar da idonta Kan Unaisah da Batul, daku zan fara, saboda yawan sumar kanku” saukowa su ka yi daga saman kujerun, ta juya ta nufi Corner din da Sink Yake, gefen shi beauty cabinet ne mai ɗauke da jerin shampoo da conditioner da suran mayukan gyaran gashi. Taci baƙar wahala wurin gyara masu gashi, musamman mutun biyun nan Unaisah da Batul, saboda yawan gashinsu ga tsawo, da ruwan zafi ta jika sumar bayan ta jiƙu ta shafa shampoo ta cuccuɗa ko’ina na gashin, bayan ta wanke shampoo din ta sanya conditioner na tsawon mintuna kafin ta wanketa, tayi masu amfani da Hair dryer ta busar masu da sumar kansu, ta fara shafa masu smoothing serum ta ɗauki comb taci gaba da sharce gashin, tunkafin ta kammala take santin kyawun sumar kansu, bayan ta gama sharce gashin ta kwarara masu hair oils kala daban daban saman sumar taci gaba da cuɗasu da hannuwanta, tuni gashin ya ciza launin shi dark brown sai ƙyalli yake yi da ɗaukar ido, ƙamshin hair oils din data shafa masu Ya cika hancinansu. Lokacin da suka kalli sumar kansu ta cikin madubi, Ihun farin ciki suka saki suna faman yi mata godiya tace su koma zu zauna, bata gama gyara masu ba, su Azeeza sunyi zuru suna jiran suma ayi masu, sai faman santin su Unaisah da Batul suke Yi har suna fadin suma kalar nasu za’ayi masu. Ummi tayi ƙoƙari wurin gyara su, Yara kamar ƴa’ƴan wani shege maiji da raina, saida tayi amfani da almakashi ta datse sumar kansu ta rage tsayinta ta dawo dai dai tsakiyar bayansu, hair style din da tayima Batul da Unaisah Triple twist half up ne, Bayan ta gama dasu ta bi sauran ɗaya bayan ɗaya ta wanke masu sumar kansu kamar yadda tayi masu Unaisah haka suma tayi masu banbancin wurin hair style ne, saida ta miƙar masu da gashinsu ta hanyar yin amfani da Straightener, kafin ta ɗaure ma Azeeza da Jemimah gashinsu da ribbom guda biyu gefe da gefe wutsiyar gashin ta sauko har saman kafaɗunsu. Duk wannan gayun da akayi masu, Jemimah bata gode ba, ta sanya rigima akan sai an maida launin gashinta kalar nasu Batul, Ummi taci dariya, bata ta6a tsammanin zata ji ƙaunar yaran ba sai yau, su kansu sunyi mamakin yadda ta dage damtse wurin Yi masu hidima, Abu kamar wasa Jemimah ta fashe masu da kuka, ita damuwarta launin gashinsu Yafi nasu kyau, da ita da azeeza sumar kansu blonde ne kalar na turawa, ita Azeeza bata damu ba sai murna take yi an gyara mata gashi, jemimah daice ta matsa lamba, ummi harta fara tunanin ta canza mata launin gashin da yake suna da Hair dye cikin jerin Kayan gyaran gashin su, Unaisah ce tace abar mata launin gashin kanta, saboda yana dakyau ba lallaima idan aka maida mata kalar nasu yayi kyau ba,” daƙyar suka lallashi Jamimah tadaina yi masu kuka. Tsawon lokaci kafin Ummi ta kammala Gyara su, hatta skin dinsu da akaifunsu da tafukan ƙafafuwansu duk saida ta gyara masu, ko’ina ka kalla na jikinsu saiya burgeka, kamar basu ta6a shan wahalar rayuwa ba, tun bayan da aka gama kowannansu Ya koma bedroom dinshi, bacci mai nauyi ya dauke su, duk don saboda gyaran gashin da akayi masu kada Ya 6ace yasa suka kwanta ta rubda ciki. *OBIE ESTATE* Danƙara danƙara motocine masu numfashi suke ta kurɗaɗowa ta cikin babban gate din Obie Estate a ƙalla sunkai goma sha wani abu gaba da bayansu motocin fusatattun sojoji ne sun mimmiƙe tsaitsaye hannayensu ruƙe da manyan bindigu, jiniyar motocin jami’an ta karaɗe ko’ina na yankin, da matsakaicin gudu suka haura saman titin da zai sada da su da Airport, Motar farko zungureriya tana ɗauke da dattijon arziƙi tare da Dr.Jaz, mota ta biyu sanate president lateef ne zaune a mazaunin baya shi da Iyalansa Hajiya madina da ya’yan ta biyu Ziyad da zuhra, Mota ta uku Hajiya saratu ce a cikinta tare da twins zayn da zaid, da shi kanshi pravin din, Motar bayansu Sir mubarak ne tare da Hajiya Turai, daga motarsu sai ta sauran ƴan uwa da abokanan arziki da suka hallara domin zuwa tarban babban baƙonsu, kowan nan su yayi shiga ta alfarma, mazan cikinsu shaddojine ajikinsu, matan kuma wankan abaya suka ɗauka, har sun kusa isa Airport din ba zato ba tsammani suka soma hango wasu hamshaƙan motocin daban sun biyo ta titin da zai jagorance ka zuwa Aso Villa, Ƙarshen Haɗuwa ta glass din motocinsu suke hangen su, tunkafin suga su wanene acikin motocin ransu ya basu Mr.president ne tare da muƙarrabansa shima yazo tarban ɗan uwan nashi, abun yayi matuƙar ƙayatar dasu, basu yi tsammani zai halacci zuwa Airport din ba, zuwan bazata yai masu, Motocin shugaban ƙasa na ƙarasowa suka haɗe da nasu motocin Yawan adadin motocin suka ƙaru, hankalin kowannansu akwance yake sun ci burin haɗuwa da babban baƙon nasu, duk sun ƙagara su ƙarasa Airport din. “Ziyad Ina fata baka faɗa ma Ƴan uwanka ƴan jarida ba ko”? Sanate lateef ne yai maganar a yayin da yake zaune gefen Hajiya madina a back seat na motarsu. Ziyad na murmushi yace”ai daddy tuni na sanar dasu ku jura zuwansu kawai” Buɗe baki sanate yai”amma dai wasa kake min ko? Kadai san Kawun naka bai san taron ƴan jarida,” Ziyad na sakin murmushin shaƙiyanci ya zuge mashi glass din motarsu, har sai da gaban Senate yadan buga ganin motocin ƴan jarida birjik sai faman sharara gudu suke yi har sunfi nasu motocin sauri duk dan su ƙarasa su dauki rahoto. Dafe kai Senate yai”ziyad kana da matsala, yanzu menene na gayyatar waɗannan mutanan ina amfanin yin hakan”? Sai lokacin Hajiya madina ta sanya masu baki a maganarsu”ai indai ziyad ne dama ka daina damun kanka, ka riga da kasan halinshi, jikin shi har 6ari yake yi idan ya samu abun daukar rahoto” Dariya ziyad yai jin abunda mommyn shi tace, shi dai senate lamarin ya ɗaure mashi kai. Kusan atare motocin suka yi parking a wurin da aka tadana domin ajiye motoci, jami’an suka diddiro daga saman motocinsu suka soma bubbuɗe masu murfin motocin, ɗaya bayan ɗaya suke fitowa, Ƴan jaridan ma suka fito Hannayensu ruƙe da Cameras, wasu a wuya suka rataya cameran su, wasu kuma sun ruƙe welcome sign a hannun su duk da akwai tazara a tsakanin su saboda mugun tsaron dake wurin dan ma yan jarida ne masu naci da ba wanda ya isa ya tsaya a wurin. Lokacin da Sharafudden Ya fito daga cikin Motarshi gaba ɗaya ido Ya dawo kanshi, mutumin babu wasa a fuskarshi, kamanninshi sak da mahaifinshi Obinna, launin fatarsu ne ba ɗayaba, Yana da hasken fata sai dai bai kai na Obie ba, nashi yadan yi duhu, fatarshi taji hutu, babban mutunne mai cikar kamala, ya iya dattako ga wadatar arziƙi, kusan duka halayan Owais shiya ɗauko babu abunda ya bari mashi, hatta kyawun fuskarshi na mahaifinshi ne, Yana da tsawo da fadin ƙirji, wankan suit ne a jikinshi, ya manna farin glass a idonshi, security detail din dake take mashi baya sunyi mashi rumfa, Cikin takun ƙasaita Ya nufi mahaifinshi dake ta faman aiko mashi da sakon murmushi, rungume juna sukayi, ƴan jarida kamar jira suke yi nan fa suka fara daukarsu hotuna, bubbuga bayanshi obie yai da hannun shi yana fadin”Nayi kewarka son, tsawon lokaci ka hanani ganinka sai yau, da yake ɗan uwanka zaizo yanzu zan dinga ganinka akai akai”dagowa yai da kanshi daƙyar yake murmushi kamar yana yi mashi wahala ya motsa baki ya furta”aymin afwa baba, kana araina koba dan shi ba, nayi niyar shigowa gidan yau saboda nayi kewarka” obie yaji dadin kalamanshi, da hannu ya nuna mashi sauran ƴan uwanshi, Jiki na rawa dr jazz da twins suka ƙaraso suna gaishe shi cikin girmamawa, ɗaya bayan ɗaya yake amsa masu, bayan sun kammala ƴan gaishe gaishen nasu, suka ɗunguma gaba ɗayansu suka shiga Arrival area din, duk Inda suka gifta ma’aikatan airport din sara masu suke yi, sau da ƙafa suke Yi masu biyayya, a katafaren waiting area kowannansu Ya samu wuri Ya zauna sun natsu suna jiran ƙarasowar jirgin baƙon nasu. Jami’an suna a kewaye da su, Ƴan jaridan ma suna a tsaitsaye acen baya suna jiran Ya ƙaraso don su fara ɗaukar rahoto. Vip Area din Ya cika maƙil da ɗaruruwan mutane wasu ma daga baya suka zo, Ko’ina ka kalla kawunan Bil’adama ne, kowanene wannan Babban baƙon daya tara dubban jama’a dake cike da ɗaukin ganinshi? lallai ba ƙaramin mai farin jini bane, shi ɗin na musamman ne. Agogon bangon Nigeria Yana bugawa ƙarfe goma shabiyu adai dai wannan lokacin sautin katafaren jirgin shugaban ƙasar dake shawagi bisa sararin samaniya Ya karaɗe Kunnuwan mutane, gaba ɗaya ransu ya basu cewar jirginshi ne Hakan yasa su ka fara sakin murmushin farin ciki, A katafaren Filin tashi da safkar jirage masu zaman kansu, Jet din ya sauka a hankali Yake bin runway har Ya ƙaraso dai dai Inda zai dakata, tsawon mintuna kafin ƙofar Jirgin ta buɗe matattakalar shi ta sauko ƙasa, hadadden red carpet, ma’aikatan airport din suka shimfiɗa mashi tun daga bakin stair din har izuwa entry din Vip area, mutanan dake aciki tuni sun mimmiƙe suna atsaitsaye curko curko suna jiran ƙarasowarshi. Musamman Ƙungiyar masu daukar hoto da ‘yan jarida sun Harzuƙa Jira suke kawai Ya duro da ƙafarshi waje don su fara haska shi da kyamarorinsu kowa burinshi ya kasance mutun na farko da zai fara ƙyalla mashi camera, Jami’an sun kewaye Jirgin saboda su bashi tsaro, Maimakon mutumin da suke tsammani Ya fara saukowa sai suka ga Security detail dinshi Royal Canadian Mounted Polices suna fitowa daga cikin jirgin, zaratan Maza Ƙarfafa Masu Ƙira Irinta zakuna, Sanye Cikin kakinsu, Qugunansu a soke da bindigu Pistols, A bakin stairs ɗin Suka Tsaya sun haɗe da sojojin Nigeria dake a bakin jirgin. Lokacin da Ya zuro ƙafarshi dake sanye cikin wasu hadaddun leather shoe Hankalin kowa ya dawo kanshi, tabarakallahu ahsanul khalikin, ƴan jarida har goga kafada suke Yi garin yin saurin haska shi da camera, A hankali Ya ƙarasa fitowa, Babban mutunne ya fito sanye Cikin tailored suit, sun zauna mashi, Sunbi shape ɗin Jikinshi, Fari ne Ba irin sosai ɗinnan ba, daga ganin fatarshi hutu ya zauna mashi, kanshi babu hula, Sai ka rantse da Allah matashin saurayi ne, saboda haɗuwarshi da iya ɗaukar wankanshi, sumar kanshi akwance take tasha gyara, tsakiyar gashin kan nashi akwai siraran hurhurar gado, da akayi gayu da ita, ba ƙaramin kyau tayi mashi ba,Yana da tsayin fuska, Manyan idanuwa, ga dogon hanci, bakowa bane wannan face PRIME MINISTER HATEEM OBINNA! namijin zaki uban dawa, ɗaya tamkar da dubu, gwarzon Namiji mai ɗauke da suffofin jagwaranci, mutun mai daraja da ƙima a idon al’umma. yana da farin jini ba Iya kasarshi ba a ƙasashe da dama rububin shi suke Yi saboda kyawawan ɗabi’unshi da halayanshi, mutumin maƙurane a 6angaren Kyau, ilmin addini dana zamani, uwa uba Ya fito daga babban Gida, kallo ɗaya zakayi mashi ka shaida ruwa biyune, gashi Hamshaƙin Mai kuɗi Ya shahara Aduniya. Cikin dattako Yake taka matakalar benan, All eyes on him mutanen dake can nesa suna hangenshi kamar zasu ƙetare Iyakarsu su faɗo gabanshi donsu Tarbe shi, Fitowarshi Keda Wuya Uwar Gidan shi Gimbiya Mujeedat ta sauko daga cikin jirgin, nan fa kallo Ya koma Kanta, Hankalin maza ya tashi, Ko mace ta kalleta saita girgiza balle Namiji, ahaka ma ta sanya Arab gown launin fara ajikinta, Ta rufe fuskarta da Niqab, dirin Jikinta Yafi komai jan hankali, da kuma kyawawan idanuwanta da suka bayyana sun sha uban ado farare ƙyal, price din takalman ƙafarta kaɗai sun ishi wani talakan jari, hatta hannayanta Safa ce ta sanya, Mijinta yana matuƙar jin kishinta shiyasa duk inda zasuje da niƙab a fuskarta, bayan ta fito, matasan ƴa’ƴansu biyu suka fito tare da Faryat ƴar gidan saratu, sunyi shiga kala ɗaya data mahaifiyarsu dukansu matane, dogaye masu kyan sura, atare dasu akwai advisors dinsa, manyan mutane masu bashi shawara, sun hada da chief of staff, national security advisor, Fararen turawa sun ɗauki wankan black suit, kowan nan su ya manna sunglases a idanuwanshi, ajere suke taka shimfiɗaɗɗan red carpet din da zai jagorance su zuwa Vip arrival area, lokacin da suka karasa jama’a kamar zasu haɗiyesu tsabar murnan ganinsu, Bawan Allah bai nufi kowa ba sai Mahaifinshi Obinna, Hannu bibbiyu ya rungume shi ajikinshi, tsawon shekara basu ganaba sai yau da Allah Ya nufa zai samu damar zuwa Nigeria, Wata irin runguma yayi ma Obinna, gaba daya mutane suka sanya ihu suna tafa masu, Ƴan jarida Sun dage sai daukarsu hoto suke Yi, sautin ƙarar kyamarorinsu ya cika airport din ji kake kyat kyat, Gimbiya Mujeedat, da fara’a akan fuskarta ta rungume Hajiya saratu, kamar ƴan uwan juna, Faryat kuwa da gudu ta faɗa jikin Zayn tana dariya, bayan ta rungume shi ta kuma rungume Zaid, sai daɗi take ji taga ƴan uwanta, Nazli da Yazrin kuwa kamar basu son ganin mutane, dama suna da wuyar sha’ani har ƙwara Yazrin tafi sakin fuska akan Ƴar uwarta nazli, daƙyar suke rungumar ƴan uwan mahaifinsu, izzace ta bala’e suke fama da ita, su ala dole ga jinin sarautar daular larabawa, Bayan prime minister Ya saki mahaifinshi, Ya rungume ya’yanshi sharafudden kamar zasu koma mutun ɗaya tsabar yadda suka hade jikinsu. Tuni ƙwalla ta cicciko tab a idanuwansu, daƙyar suke yima juna magana, ɗaya bayan daya saida yabi ƴan uwanshi ya rungumesu, kafin ya soma gaisawa da sauran manyan mutanan da suka zo tarbarshi, yaji dadin ganin daruruwan al’ummar da suka taru domin shi, wannan abun farin ciki ne, Obie ne yai mashi magana akan Yan jaridan da ke son yin magana da shi, A hankali yake bin welcome sign din dake a ruƙe a hannunsu. Rubutun dake ajiki ya soma karantawa acikin zuciyarshi kamar haka _The entire country of Nigeria, welcomes Prime Minister Obinna with open arms!_ _A very special welcome to Prime Minister Hateem Obinna, on behalf of the entire nation!_ _- Prime Minister Hateem Obinna, we are delighted to have you in our country!_ _We’re happy to extend a sincere and heartfelt welcome to Prime Minister Hateem Obinna!_ Ƙayataccen murmushine ya bayyana akan fuskarshi, ƙwallar da yake 6oyewa baisan sa’adda ta soma gangarowa saman kuncinsa, farin cikine Ya cikashi, yaji dadin kyakkyawar tarbar daya samu, mintuna ƙalilan yayi jawabi ma ƴan jarida yayi masu godiya da irin tarbar da suka yi mashi Daga bisani Jami’an dake bashi tsaro suka yi mashi ƙawanya da iyalinshi zuwa wurin da aka tanadar masu da jigunannun motocin da zasu yi jigila da su, bayan kowan nan su ya shiga cikin mota, kusan atare drivers din dake tukasu suka tada su, A hankali suke driving dinsu zuwa hanyar komawa Obie estate. Duk inda suka gifta Jiniyar motocinsu ya karaɗe ko’ina, cikin ƙanƙanin lokaci suka ƙaraso Cikin estate din, a harabar ajiye motocinsu suka yi parking, gaba ɗaya kowa ya futo suka dunguma zuwa cikin katafaren falon gidan, Jami’an da yazo dasu tuni an ware masu part din da zasu zauna a babban masaukin baƙin gidan, haka zalika advisors dinshi suma An basu nasu Yankin da zasu zauna, bajimawa zasuyi a kasar ba, Ƴan kwanaki ne zasuyi kafin su koma Canada, masu aikin gidan sai safa da marwa suke Yi wurin kai masu kayan abincin da aka shirya masu, idan zasu gaisa da mutane harshen turanci suke Yi, har yaren french suna jin shi sosai, Gimbiya mujeedat kuma Tafi jin larabci da turanci, haka ƴa’ƴanta ma hausa wahala take yi masu, faryat dai ce ta ƙware wurin yin hausa sai turanci, Prime minster ma Yana jin harshen hausa amma yafi ƙwarewa wurin Iya yaren mahaifiyarshi turanci da faransanci, sai spanish. Yinin Ranar gidan Ya cika maƙil da jami’ae, sojoji da ƴan sanda, sun kewaye ko’ina na sashen Estate din, tsaron gidan Ya ƙaru, Kafin mutun ya samu damar shiga estate din sai sun tantance shi da na’ura daga kasa har sama zasu bincike shi kafin ya samu damar ƙarasawa ciki, babu mahalukin daya isa Ya shiga gidan koya fita lami lafiya batare da jami’ae sun cacike shi ba, tun karfe ɗaya na rana Ƴan uwa da abokanan arziki suke ta taruwa domin Yima baki barka da zuwa. Wuraren ƙarfe huɗu Na marece, Lokacin mutane sun ɗan ragu, motocin ma’aikan Companyn su Zahra suka ƙaraso Estete din, basu ta6a ganin tashin hankali irin na yau ba, sun girgiza da ganin jami’ae a kewaye da estate din, Zahra Sarkin tsoro duk tasha jinin Jikinta, Kafin abasu damar shiga estate ɗin saida jami’ae suka basu umarnin su fito daga cikin motocinsu, ɗaya bayan ɗaya suka firfito matasan ƴan mata Ansha gayu, daga ƙasa har sama jami’an suka bincikesu hatta kayan decoration din da suka zo da su a mota. Saida suka duddubasu suka tabbatar babu makami ko wani abun cutarwa tukunna suka basu iznin shiga cikin gidan. Da taimakon Hajiya saratu suka ƙarasa 6angaren da zasu fara aikin nasu, saida aka fara tarbarsu da lafiyayyan abinci suka cika cikunansu tukunna suka fara aikin tsara decoration din, acikin wani katafaren ɗakin taro dake acikin gidan suka hallara gaba ɗayansu interior designers din, Zahra da fatima sune gwanaye basu aiki sai dai su nuna ma sauran matasan ƴan matan yadda zasu tsara kayan adon suyi kyau, kasancewarsu ƙwararru a fagen Iya decoration tuni wurin Ya fara ɗaukar ido Ko’ina ka kalla kayan adone ke kyalkyali da walƙiya kamar zasu kashe idon bil’adama. *CHIEF OWAIS✊❤* Wuraren ƙarfe takwas na dare, Ya fito daga bedroom dinsa, har yayi shirin kwanciya bacci, sleeping dress ne a jikinshi launin sky blue, rigar tabi shape din broad chest dinsa, ta bayyana strong arms dinsa, walking gently ya nufi bakin handrail, Ya ɗaura faffaɗan tafin hannunsa asaman shi, A hankali yake buɗe kyawawan idanuwanshi Yana ƙare ma ko’ina na downstairs da kallo, tun da ya diro nigeria har Yau bai leƙa cikin estate dinsu ba, kuma babu wanda yasan da zuwanshi, ni’imtacciyar iskar wurin Ba ƙaramin sanyaya mashi zuciya take yi ba, abubuwa da dama sunayi mashi yawo acikin kanshi. “Barka da fitowa yalla6ai” muryar Big guy ce ta katse mashi tunanin shi, Yana daga tsaye gefen shi, Ba tare daya juya ya kalle shi ba, Ya amsa mashi da yawwa. Cikin girmamawa yace”yalla6ai ina fata kana lafiya” ya tambaya ne don ganin yanayin daya fito daga daki cikin shiga ta kayan bacci. “I need coffee” abunda ya furta mashi kenan maimakon amsar tambayar da yai mashi. Da sauri big guy ya juya domin ya kawo mashi abunda yake buƙata. Badajimawa ba sai gashi ya dawo hannunshi ruke da Mug sai tiriri coffeee din Yake yi, Ya miƙa mashi bayan ya kar6a, sai da ya ɗauki lokacin kafin Ya fara kur6ar shi. “Yalla6ai yaushe zamu shiga cikin gida ne”? Tamkar bazai amsa mashi ba Ya furta”tomorrow”Jinjina kai Big guy yai kafin ya kuma cewa”Yau kawunka na ƙasar kanada ya shigo ƙasar bansani ba ko ka gani a labarai” Yamutsa fuska yai da alama surutun big guy ya fara takura shi, daƙyar ya furta”Nasani” Gyaɗa kai big guy yai”bari nabarka ka huta yalla6ai, mu kwana lafiya” ya amsa mashi da okey. Juyawa yai da sauri Ya nufi down stairs. Yana cikin shan coffee dinshi, yayin da yake bin ko’ina da kallo, Karaf idanuwanshi suka sauka Akan Danish dake ƙoƙarin fitowa daga ɗakin shi, Ya zuba hannayenshi cikin short pockets dinsa, damuwar duniya ta isheshi, Ya kasa runtsawa, saboda rashin ganin unaisah, tun ɗazu yake jiran zuwanta bata leƙo ɗakinsa ba, shi kuma bai Iya takawa yaje ɗakinsu, Kamar anyi mashi Iyaka da shiga, ko falo bai Iya zuwa idan ba Angel ta janyo shi ba, rashin sabone ke damunshi, kasancewar suna fuskantar juna hakan ya bashi damar ganin shi da kyau, duk da akwai tazara a tsakaninsu, dukansu suna a second floor na bene. Kamar yadda Owais Ya jingina da handrail haka shima Danish ya ɗaura gwiwowin hannunsa saman handrail, da farko bai lura da shi ba, sai da ya wurga eye balls dinsa saitin inda yake fuskanta tukunna suka yi tozali da juna, ɗaure fuska danish yai, tunkafin ma yasan wanene shi yaji baiyi mashi ba saboda shi baya ƙaunar yaga Namiji idan har ba cikin ƴan uwansu maza ba, duk don saboda Babe Unaisah dinshi, yaji haushi ɗazu da asuba dayaga wani ƙato Ya rungumeta, har zazza6i saida ya lullu6e shi, ko abincin dinner dinshi baici ba, yaso ace Ya damƙeta da babu abun da zai hana ta yabama aya zaƙinta. Chief Ya natsu yana kallon shi, abun da ya ɗan bashi mamaki Da yaron girman jikinshi, saboda yasan shekarunshi da sojoji suka faɗa mashi a bayanin da Gabriel Ya basu, bai wuci 20 years ba. Tsawon mintuna suna kallon kallo a tsakaninsu, kafin daga bisani chief Ya juya mashi baya ya nufi bedroom dinsa ya shige, saukowa down Yai cikin sanɗa yake yin tafiya yana neman room dinsu Unaisah, ya rasa ta wace hanya zaibi ya gano ɗakinsu. Firgita yai sakamakon Jin hannun mutun saman Bayanshi, abunka ga mai ji da ƙarfi, yayi tunanin wani ne zai cutar dashi, aiko ya damƙo hannun mutumin da niyar ya wurgo shi ƙasa sai kuma Ya fasa, Ya juya a hankali don ganin wanene, Boss man ne atsaye hannunshi ruƙe da Backpack din unaisa, Da mamaki akan fuskarshi yace”Sannu Iliya ɗan mai karfi, au da buguna zakayi daga kawai na dafa kafaɗarka? Haka ɗazu da safe ka dinga jifana da pillow saboda na rungume ƴar uwarka ko”? Cikin jin kunyar maganarshi Danish ya sadda kanshi ƙasa, ba tare daya furta komai na. Murmushi boss man ya saki tare da miƙa mashi backpack din hannun shi”kar6i nan, ka kaima Masoyiyar taka Unaisah kace inji boss man, ta duba cikin aljihun jakar zata ga sabon sim dana sanya mata” Hannu yasa ya kar6i backpack din, daƙyar ya iya furta mashi thank, kafin ya juya yanufi inda yake tunanin zai samu ɗakinsu. Boss Man yana atsaye yana bin bayanshi da kallo, Har ya 6ace ma ganin shi kafin Ya juya ya nufi ƙofar fita. Yayin da Danish keta faman neman ɗakinsu Angel, tana acan cikin toilet gaban madubi, daga zuwa Yin uziri taci karo da abun arziƙi a kirjinta, Duk tabi ta ruɗe ta rasa ina zata tsoma ranta don farin ciki, batasan yaushe breast suka fara fito mata ba, bata ta6a lura ba sai yau data tsaya gaban madubi tana bin jikinta da kallon ƙurulla, guntuwar rigar bacci ce a jikinta, Daƙyar ta rufe gwiwarta, sai faman ɗaɗɗage rigar take Yi tana ƙara leƙensu, sunyi ƙananu dasu basu fara nuna ba, kamar wadda akayi ma albishiri da gidan Aljanna sai faman sakin murmushi take Yi, itama yau irin abin ƴar gidan daddy sun fara fito mata, taci alwashin bazata bari Danish yagansu ba, sai sun ƙara girma sunkai kamar na unaiza tukunna, da gudu ta fito daga toilet ta nufi closet dinsu ta buɗe ta dauko ƙaramin mayafi ta koma cikin toilet, ta tu6e wuyan rigar, ta ɗaure kirjinta tamau da mayafin kafin ta maida wuyan rigar tana faɗin”Allah na gode maka, nan bada jimawa ba nima zan zama budurwa” Duk wannan haukan da takeyi, batul tana akwance saman gadonsu, tayi nisa acikin baccinta, Adai dai lokacin zata fito daga toilet din tana zuro ƙafarta, tayi arba da danish tsaye bakin ƙofar dakin, Hannun shi ruƙe da backpack, Sai faman baza ido Yake yi don ya ganota, daƙyar ya samu ya gane dakin nasu, Jin motsin mutun yasa shi yin saurin ɗaura idonshi akan fuskarta, ido cikin ido suke kallon juna, wani abu daya ɗaure mashi kai, shu’umin murmushin daya gani kwance saman la66anta, hada ruƙe qugu da hannu ɗaya. ❤EX-PRISONERS❤ Sam ya kasa ƙarasawa gare ta, slowly yake bin jikinta da kallo, tun daga kan fararen ƙafafuwanta har izuwa saman gwiwowinta da suka kasance jawur da su kamar bata ta6a yin rarrafe ba, ɗagowa yai da eye balls dinsa zuwa saman Waist dinta da ya faɗaɗa, ganin irin mayataccen kallon da yake binta dashi ne yasa ta juya da gudu ta nufi can cikin dakin wurin closet dinsu, har sai da yaji gabanshi yaɗan faɗi lokacin data watsa da gudun mazannanta suka girgiza rigar ta bayyana shape dinsu, yawu ya haɗiya adam’s apple dinsa Ya motsa sama da ƙasa. Yaɗan ji shock ganin baƙon al’amari ajikin Babe unaisah dinshi, bai ta6a ganin girmanta ba sai yau da yai tozali da ita cikin short gown, Kayan arzuƙa sun fara ha66aka. Cikin sanɗa take tafiya tana tunkaroshi, idanuwanshi akan fuskarta, still shu’umin murmushin nan take sakar mashi, hatta Yanayin tafiyarta ya canza, dogon wandon bacci ta zura a jikinta duk don Ya daina kallon mata jikinta. Dab dashi ta tsaya tana duban backpack din hannunshi, har cikin ranta taji dadin ganin jakar, daɗi kamar zai kasheta, haɗa ido sukayi da shi, mutumin duk ya susuce kamar wanda aka zare ma laka, sam babu kuzari a jikinshi tunda yai arba da hips dinta. Harara ta jefa mashi haɗi da murguɗa mashi soft pink lips dinta, muryarta da shagwa6a tace”kallon ya isa haka, bani jakar nagode” ta faɗa tana ƙoƙarin ruƙo hannun backpack din, da sauri ya ƙanƙameta a wide chest dinshi, alamar bazai bata ba, ɗaure mashi fuska tai”wai meye haka? Baka ga dare yayi ba, yakamata kaje ka kwanta, ni bansan ma ya akai boss man ya baka back pack din ba, ai daya sani shiya kawo min da kanshi” bada wata manufa ta furta maganar ba, amma da yake jarabar kishi ce dashi, sai yaji kamar tana nufin tafi son ganin boss man akanshi shiyasa tace haka, aikuwa nan take Ya haɗe rai, babu annuri ko misƙala zarratin, ganin ya fusata yasa tace”meye faru my man”? Wurgar mata da jakar Yai ƙasa, da sauri Ya juya Ya nufi ƙofar fita kamar zaiyi tuntu6e, Jiki na rawa tabi bayanshi tana ambaton sunanshi”My man! Dan Allah ka tsaya muyi magana, Ni ce na bata maka rai ko? Pls am sorry bazan ƙara ba, Ka yafe ni pls, bazan Iya bacci kana fushi dani ba” Har ya kusa fucewa daga ɗakin, Can kuma sai ya dakata kamar mai tunanin wani abu, Ba zato ba tsammani taga ya juyo a sukwane, ƙiris Ya rage ta hade kirjinta da nashi, gadan gadan Ya tunkarota hakan da yai ba ƙaramin tsoro yaso ya bata ba, Juya tayi da niyar ta faɗa toilet, ta 6oye sai dai kafin ta kai ga shiga taji Ya damƙi waist dinta da ƙarfi Ya ɗaga ta sama kamar ɗiyar roba, tadinga ihu tana fadin Am sorry my man dan Allah kada ka 6alla ni” Batul dake a kwance tana sharar bacci, koke koken Angel ya fara takura mata sai faman mutsu mutsu take Yi alamar zata farka. ya tsareta da reddish eyes dinsa da launinsu Ya ciza tamar zallar red, da kakkausar murya ya furta”meyasa kike son 6ata min rai”? Ya fada batare daya sauke ta ƙasa ba, Jikinta na kerma tana faman wutsil Wutsil da ƴan ƙafafuwanta tace”danish dan Allah ka ƙyaleni, kaga Batul dake bacci tafara takura da surutunmu, kuma ni bansan laifin me nayi maka ba, amma ina baka haƙuri ka tafi ɗaki ka kwanta” Ta6e la66ansa Yai alamar bai damu ba, kafin ya sassauto da Voice dinsa”Kin hana zuciyata sakat, tunda safe da kika rungume ƙaton nan Hankalina ba akwance yake ba, nakasa samun sukuni, ni kaɗai nasan irin raɗaɗin da nake ji, ke ko ajikinki, baki leƙo dakina kin duba halin da nake aciki ba,saboda ke banci dinner dina ba, baki damu dani ba, ko nema na bakiyi ba, saboda kin samu wanda yafi ni ko” Runtse idanuwanta taɗanyi, hadi da dafe kai da hannu ɗaya, dama saida ranta ya bata bazai ƙyaleta ba, saboda jarabar kishinshi, shiyasa yau ta hana shi ganinta, duk dan ta tsira daga fushin shi. Shirun da tayi mashine Ya ƙara 6ata mashi rai, Baisan sa’adda Yai zazzafan taku Ya nufi Saman shimfidedan gadonsu, Ya jefar da ita Ta faɗa saman lallusar mattress din, da sauri ta juyar da jikinta tai kwanciyar rubda ciki, gudun kada Gyaran gashin da akayi mata ya tarwatse, Cikin shessheƙar kukan ƙarya Take Fadin”Nifa bada son raina ya rungume ni ba, Hijab din jikina ce ta taɗiyoni na tafi zan kife ƙasa shine Ya tarbeni na faɗa chest dinsa, kaima ka sani bani marmarin kasancewa da wani ɗa namiji idan bakai ba, dan Allah kadaina tayar da hankalinka akaina, saboda Ni taka ce kai kaɗai, shi mutumin ma da kake Yin kishi akanshi babbane ba matashi ba, Ya isa ya haifemu nida kai” Tun da ta fara yin magana, Ya rasa sukunin shi, Gyaran gashinta Yai matuƙar jan hankalin shi, kamar princess, twisting din da akayi mata guda biyu saman gashin ya ƙara mata kyau, sam bata ji motsinshi ba, ta dage sai haƙuri Take bashi, jin hucin numfashinsa a jikinta Yasa tai wuff Ta juyo Tana fuskantar shi, har saida gabanta Yaɗan fadi ganin Yadda yai mata rumfa, tuni tasha jinin jikinta, muryarta na rawa ta furta”meye haka” Lumshe mata ido yai tare da waresu saman fuskarta, abun ya ɗaure mata kai, Yana neman ya rikitar da ita. Ganin dagaske kamar wani abu yake so yai matane yasa ta fara canza mashi fuska, zuwa ainihin true colour dinta, runtse ido tai da masifa tace”danish ka tashi ka tafi ɗaki, wallahi kada ka bari na buɗe ido na ganka ranka zai Iya 6aci” saida ta gama zazzaga mashi faɗan ta buɗe ido a hankali don taga idan ya tafi, ko gizau baiyi ba yana nan yadda yake, Cikin zafin nama ta daddage ta ɗaura hannayenta saman ƙirjinshi da niyar ta ingije shi, sai dai takasa yin hakan sakamakon wani abu daya tayar mata hankali, a ruɗe take kallon shi ayayin da take kokarin mikewa zaune ta jingina bayanta jikin headboard na gadon, Cikin sanyin murya ta furta sunanshi”My man” Idanuwanshi tuni sun fara canza launi, numfashinshi na fita da huci hucin zafi. “Faɗamin meke damunka? Baka da lafiyane? Meyasa naji zafi ajikinka”? Da wata irin kasala Ya kwantar da kanshi saman mattress dinsu, kasancewar Gadon Yana da fadi Batul tana daga can 6angare guda. “Kayi shiru baka bani amsa ba, kasan bana so Ina magana kana shareni,” Daƙyar Ya iya buɗe baki Ya furta”am sorry idan na 6ata maki rai, yanzu zan tafi na kwanta” ya ambaci hakan tare da miƙewa ya sauko daga saman gadon, da sauri ta biyo bayanshi tana ƙwala mashi kira, sai dai kafin ta isa gare shi, tuni Ya fuce daga ɗakin, ƙofar tayi locking, kwantar da kanta tayi saman glass door Din, Jikinta yai mugun yin sanyi, hankalinta Ya tashi ssai, ta girgiza da jin zafin jikinshi tamkar hucin garwashin huta, taya zata iya runtsawa bayan bata da masaniya akan halin da yake aciki? Gashi ya faɗa mata baici dinner ba duk don saboda da ita! Ruwan hawaye ne suka taru acikin idonta, da sauri ta juya tana duban hadaddiyar wall clock din dakin ƙarfe 10 na dare, badan taso ba ta haƙura da bin bayanshi amma taci alwashin da asuba zata je ta dubashi, kamar yadda taga rana haka taga dare, bacci ya ƙaurace ma idanuwanta, sai faman juyi take Yi saman gadonsu, duk ta takura kanta ta hana zuciyarta sakat. *FRIDAY MORNING🥳💃💃💃* Bayan tasowa daga sallar asuba, dattijon arziƙi Ya nufi Sashen da bedroom dinsa Yake hannun shi ruƙe da sanda, Farar Jallabiyace a jikinshi, lokacin daya ƙarasa bedroom dinshi, da sandar hannun shi Ya tura ƙofar shigar shi keda Wuya kafin ƙyaftawar ido Hasken ɗakin Ya ɗauke, duhu Ya mamaye idanuwanshi, Abunka ga tsoho duk Yabi ya ruɗe, muryarshi Adabarbace yake fadin”subhanallah, Waye ya kashe min hasken ɗaki? jazz bana son shaƙiyanci nasan kai kaɗaine zaka Iya min haka? Wai jazz baka ji Ina magana” ya fada Yana cigaba da yin tafiya cikin duhu, Ya daura hannu ɗaya jikin bango Yana laluban Switch don Ya kunna hasken dakin, Cikin 6acin rai Yake Fadin”Jazz wallahi kada ka bari in kunna hasken ɗakin nan, ranka zai 6acine, wato raini Ya fara shiga tsakanina dakai shiyasa har kake Yi min shegantaka ko”? Daƙyar Ya samu Ya shafo switch din, a harzuƙe Ya danna button din, A hankali Hasken ɗakin Ya soma gauraye ko’ina, tamkar da rana, Juyawar da zaiyi unexpected Yaga abunda Ya bashi mamaki da al’ajabi, wato gaba ɗaya furannine launin ja da yellow tun daga saman head boad har izuwa saman zanin gadonshi, An ƙawatasu masu kyan gaske har ƙyalli suke Yi, tamkar a mafarki Yake kallon ikon Allah, A hankali yake dogara sandarshi Yana tunkarar gadon tamkar maijin tsoronshi, saida Ya matso kusa Ya ƙura ido Yana so ya gane rubutun me akayi da furannin, karantawa yai *”HAPPY 80TH BIRTHDAY TO OUR BACKBONE”* Lokaci daya ya sauke nauyayyar ajiyar zuciya, Farin ciki mara misaltuwa ya lullu6e shi, Sai faman sakin murmushi yake yi kamar wani zautacce, daga end bed din Ya zauna, Yana ƙarewa furannin kallo, ranshi yana bashi cewar ƴa’ƴanshine suka shirya mashi furannin, tabbas sune, Yayi mamaki babu wanda ya sanar dashi zasuyi mashi hakan, Kuma atare dasu ya dawo daga masallaci, tun a babban falon gidan suka rabu da juna kowa ya kama hanyar part dinsa. Yayin da yake bin adon furannin da kallo, cikin sa’a idanuwanshi suka yi mashi tozali da birthday cards birjik aka ajiye mashi don Ya karanta, kusan guda bakwai daga saman kowani card an ɗaura fure, hayewa yai saman gadon har zuwa gaban cards din Ya ɗago dasu a hannunshi kowanne yana da tittle dinsa da kuma sunan mamallakinsa, Card din farko Sunan senate lateef ne, buɗewa yai ya soma karantawa kamar haka. _”To my dear father, thank you for always being there for me, guiding me, and making me the person I am today. Your support, love, and encouragement have made me who I am, and I’m so grateful for that”_ tuni idanuwanshi sun cicciko da ƙwallar farin ciki, Ajiye card din lateef yai, ya buɗe card na biyu mallakin Sir mubarak Yana duban sakon cikin shi _”From the bottom of my heart, I want to wish you a very happy birthday, Dad! Your wisdom, kindness, and sense of humor have always brightened my days” annurin fuskarshi sai ƙara nunkuwa yake Yi, haƙiƙa sunyi matuƙar faranta mashi da daɗaɗan kalamansu, Yana matuƙar ƙaunar ƴa’ƴanshi. Ajiye card din sir mubarak Yai, ya buɗe Na Sharafuddeen calmly ya ke reading dinsa “Happy birthday, Dad! You are the best father in the world and we are so lucky to have you. May your day be filled with happiness and love.” hawayen da suka taru acikin idanuwanshi tuni sun jiƙa fuskarshi, sumbatar card din Yai, kafin Ya daura shi saman wadanda ya karanta, Ya duba sakon Prime minister _”I’m so glad to have a father like you, who has been a rock of support through the ups and downs of life. You’ve always encouraged me to be the best I can be, and that means the world to me. On this special day, I just want to say thank you for everything you’ve done for me. Happy birthday Baba tsoho much love”_ Dariya ya saki har fararen haƙoranshi suka Bayyana, Kalmar ƙarshe ta saƙon Hateem ne Ya bashi dariya daya ce baba tsoho. Lumshe idanuwanshi yaɗanyi yayin hawaye ke cigaba da wanke fuskarshi, abu ɗaya ne yake fargaba a duniyar nan ranar da zai barta saboda ƴa’ƴanshi, bai sani ba tsakanin shi da su wanene gawar fari, bai fata ma Wani daga cikinsu Ya riga shi tafiya, bazai Iya jurar rashinsu ba, Ya ƙwammace mutuwa tafara Yin awon gaba dashi. Sumbatar card din Hateem Yai, kafin Ya buɗe na saratu - On this special day, I want to let you know how much I appreciate everything you’ve done for me, Dad. You’ve always been my biggest fan and supporter, and I can’t thank you enough for that. Wishing you a very happy birthday, with lots of love My Baba, Allah yabarmun kai, madubin dubawata” manna ma card din kiss Yai kafin Ya duba na sauran ƴa’ƴan nashi, waɗanda basu kaiga ƙarasowa Gidan ba, suma sun bada saƙon da aka rubuta masu a cards dinsu. Farin cikin duniya ya cika Obie, kwanciya yai saman furannin idanuwanshi na fuskantar ceilling. Ba zato ba tsammani Yajiyo sautin muryoyinsu acikin kunnuwanshi, Suna faɗin”Happy Birthday To You, Happy birthday to You, Happy birthday to our Baba” zumbur Obinna Ya yunƙura ya miƙe daga saman gadon Yana duban ƙofar room dinshi. Dr. jazz ne Ya fara shigowa hannunshi ruƙe da madaidaicin Cake mai hawa huɗu daga saman shi an jera candle, ga cake knife gefe ɗaya. Shigowar dr.jazz ke da Wuya, Manyan ƴa’ƴan shi suke shigo ajere kowannansu sanye da hadaddun jallabiyoyi, Mutun Na farko Sir mubarak ne daga bayanshi Senate lafeef ne, wanda ke abiye dashi His excellency Abdul Razak ne Gomnan Jihar lagos, baisan Yaushe Suka shigo garin abuja ba, Yayi mamakin ganinsu, zuwan bazata suka yi mashi, ga kuma His excellency Deen Obinna Na jihar kaduna state, Daga bayanshi mai girma sharafudden Obinna ne, Hannun shi ruƙe dana ɗan uwanshi Prime minister hateem obinna, abun gwanin ban sha’awa, bayansu sai Saratu data shigo itama jallabiyarce a jikinta ta yafa mayafi akanta, Fuskar kowannansu ɗauke da annurin farin ciki, maimakon Ya taso Ya karaso garesu, sai kawai su ka ga ya fashe da kuka, haɗi da sanya tafukan hannayenshi biyu Ya rufe fuskarshi. Jikinsu duk Yai sanyi, duk da ransu yana basu cewar kukan farin Cikine Ya ke yi, gefe da gefen gadon kowan nan su ya zauna kamar masu neman gafara, Senate lateef Ne Ya fara magana “Baba meyasa ka yin kuka? Dan Allah kada ka karya mana zuciyoyin mu, munci burin mu faranta maka a wannan ranar mai albarka rana mafi daraja agaremu, ranar da abun alfaharinmu Yazo duniya” ta tsakankanin yatsun hannunshi Yake satar kallonsu, Muryar saratu da shagwa6a tace”baba please kadaina wallahi bamu jin daɗin ganin hawayenka masu tsada suna zuba ƙasa” “Baba idan baka daina kukan nan ba, muma zamu fara” acewar Sir mubarak Mr.president sharafudden Yace”Daddy ka bamu dama mu share maka hawayenka da hannayenmu please” His excellency Deen Ya kar6e da cewa”daddy saboda kai, muka kamo hanya tunda duku duku muka shigo abuja, saboda muhimmancinka agare mu, dan Allah ka buɗe fuskarka ko mun samu damar ganinka, munyi kewar mahaifinmu” kalamansu ba ƙaramin karya mashi zuciya suke Yi ba, sai dai yakasa cire takufan hannayenshi daga saman fuskarshi, Allahu akhbar, wato Iyaye dabanne, duk mun muƙamin mutun shi bakomai bane agaban Iyayenshi, gaba ɗayansu nan manyan mutanene masu ruƙe da manyan muƙaman ƙasa, masu ƙima da daraja a idon duniya, Yau gasu zazzaune gefen gadon mahaifinsu, sun tasa shi agaba suna lallashinshi, abun da yake ƙara haddasa mashi jin ƙaunarsu Biyayyar da suke yi mashi, tun suna ƙanana har zuwa girmansu bai ta6a danasanin kasancewarsu a matsayin ƴa’ƴanshi ba, basu ta6a sanyashi ciwon kai ba, samun ƴa’ƴa nagartattu irinsu abune mai wuya a zamanin nan, damuwarshi tasu ce, suna matuƙar ji dashi suna gatanta shi suna kyautata mashi shiyasa suke damun cigaba arayuwarsu saboda albarkar dayake sanya masu. Muryar His excellency deen Ce Ta katse mashi tunaninshi “Baba munji kayi shuru baka ce komai ba, Idan akwai abunda ke damunka please Ka faɗa mana, baka da tamkar mu a duniyar nan, ashirye muke da mu share maka hawayenka” da zolaya Sir mubarak Ya dubi jazz”faɗamin gaskiya kodai kaine ka 6ata mashi rai”? Jazz na murmushi yace”wallahi bani bane...” daƙyar ya ƙare maganar ganin irin kallon tsiyar da hajiya saratu take watsa mashi, Muryarta a kausashe tace”tunda ka kawo cake din miƙo min shi ka fuce kabamu wuri,” Jiki asanyaye Jazz Ya nufeta Ya miƙa mata tray din, Tasa hannu ta ƙarba tana faman jifarshi da harara, sam bayason barin Ɗakin, idan Yana atare da su ji yake kamar Yana acikin danginshi mantawa yake yi da shi bakowa bane a family dinsu. Har Ya juya zai fuce Muryar Hateem ta dakatar dashi”Zonan jazz” dakatawa yai dayin tafiyar da sauri Ya koma gaban gadon, Hateem Ya sanya hannu ya kar6i cake din hannun saratu Ya miƙa mashi”kamar yadda ka kawo shi kai nake so ka fara bashi” ɗaure fuska hajiya saratu tayi badan tana jin shakkar Yaya hateem ba da kuwa babu abunda zaisa ta bashi cake din, bawan Allah Jazz sai faman sakin murmushi yake yi, ya kar6a Yana fadin”nagode daddy hateem,” jinjina mashi kai Yai batare daya ƙara furta komai ba. Baba, zamu tafi bamusan ko mune ke bakason gani ba, His excellency abdul razak ne Ya furta hakan, Sai lokacin Dattijon arziƙi Ya zame tafukan hannayenshi daga saman fuskarshi, tsufanshi Ya ƙara bayyana sosai, tamoji tamoji duk Ya kame fatarshi, Zaro hanky Sir mubarak Yai daga cikin aljihun shi, Ya soma share mashi hawayenshi, Bayan Ya kammala yasoma dubansu ɗaya bayan ɗaya, bi da bi, gaba ɗaya kamannin fuskarshi suka ɗauko, Musamman sharuffudeen da hateem tamkar yai kakinsu, hatta hasken fatarsu kalar nashi ne, launin idanuwansu ne dai kalar na mahaifiyarsu reddish brown. Ganin yadda duk suka damu ya sanya shi sakar masu fuska, cikin sanyin murya yace”kai nifa ba wani abu ke damuna ba, Farin Cikin ganinku ne ya sanya ni kuka, don haka ku kwantar da hankulanku, Jazz miƙo min cake din nan” Ya faɗa Yana ƙoƙarin saukowa daga saman gadonshi, mimmiƙewa sukayi tsaitsaye suka kewaye shi, Tuni damuwar fuskarsu ta washe Miƙa mashi cake din Jazz Yai, sai da suka fara kirga mashi one two three kafin Ya hura Iska Candles din jiki suka mutu, tafa mashi hannu sukai, sai faman sakin murmushi yake Yi, “Wazai fara bani cake din” ya fada yana dubansu, Matsa ma jazz hanya sukayi Ya matso kusa dashi, Hajiya saratu ji take kamar ta ingiza ƙeyarshi taji haushin kasancewarshi acikinsu, aganinta bashi ya dace Ya shigo cikinsu ba, Ina laifin su twins suda su ke jikokinshi. Shikuwa Hannunshi Har kerma yake yi wurin daukar wuƙa, Ya gutsiro cake din Ya miƙa mashi abaki, Ya soma ci atsanake Yana duban Jazz hada ɗaga mashi gira Ya furta”Waye ya haɗa min wannan? Yai min daɗi” Jazz yace”mommyna ce ta haɗa maka shi” jinjina kai yai”amma ta iya na jinjina mata” daɗi jazz yaji An yabi cake din mahaifiyarshi, saratu kuwa takaicin duniya ya isheta. Daya bayan ɗaya suka soma bashi cake din Yana ci, Kafin shima Ya kar6a Ya bi kowannansu Ya bashi abaki, Bayan sun kammala ci, Ya daura cake din saman table, Rungumarsu Ya fara yi ɗaya bayan ɗaya yana bubbuga bayansu da hannayenshi kamar yadda ya saba yi masu tun suna Yara. Saman gadonshi Ya koma ya zauna yace masu duk su zazzauna yana son yaita kallonsu, hakan ba ƙaramin daɗi yai masu ba, kamar yadda ya basu umarni haka suka samu wuri saman mattress din suka kewaye shi. Banda jazz wanda tuni Yajima da komawa ƙofar ɗakin, ganin irin kallon barazanar da hajiya saratu take Yi mashi kamar zata shaƙe shi. Tun wuraren ƙarfe goma sha biyu na safe, Hamshakan motoci keta kurɗaɗowa cikin gidan tunkafin lokacin da za’a fara gudanar da shagalin Ya gabato, sun Cika gidan, kasancewar Baba Obie mutunne mai tarin jama’a, wasu ma ba a ƙasar suke zaune ba, amma aranar sai gasu sun shigo Nigeria duk don saboda su halacci taron taya murnar ranar haihuwarshi, Masu aikin gidan sai zarya suke Yi wurin Kaima baƙi abinci dana sha, kitchen ya zama Dandalin magulmata, Bakunansu ko gajiya ba su yi da surutu. “Yau zamu ba idanuwanmu abinci har su ƙoshi” Safa ce tai maganar, Sophia tace”Hmm, aini yin aiki agidan nan gaba ta kai ni gobarar titi ajos, waiku kunga haɗuwar Prime minister Hateem da matarshi! Wow masha Allah, Allah Yayi halitta” Marwa tace”shi kaɗai kika gani kenan, baki ga Mai girma sharafudden ba, ai hadashi jiya cikin waɗanda sukaje airport tarbo prime minister, wallahi mutumin ba ƙaramin burgeni yake Yi ba, dashi da ɗan uwanshi hateem, mutanan badai aji ba, komai nasu da dattako suke Yin shi. Abla tace”yau zamuci uwar sabada, zamu tashe mu watse, Mu raƙarƙashe don nasan dole agayyaci mawaƙa da makaɗa, Ni nama rasa wani kaya zan sanya wallahi” da zolaya safa tace”kalar dangi, Uban wa kike tunanin zai barki ki shiga hall din taron? Ke kin isama? Sannu isassa mai walkin sa, ai kawai ki tsaya a iya matsayinki, Ta ina zaki nemi haɗa kafaɗa da Manya manyan hamshaƙan attajiran masu kuɗi, ai idan kin ganki a hall din can to amatsayin mai raba abinci zaki je” dariya suka saki. Abla tace”Nima fa da wasa nake wallahi, Ai ni tsoronma shiga zan ji, jiya izuwa yau bani da kwanciyar hankali saboda jami’an sojojin da suka kewaye estate din ciki da waje, nasan duk zuwan hateem ne yasa aka ƙara tsaro har haka” Marwa tace”niko inaso na tambaya, abun yaɗan tsaya min araina,” har suna haɗa baki wurin tambayarta menena, Numfasawa tayi kafin ta soma magana”kunsan ni ban jima da fara aiki acikin gidan nan ba, abun da yaɗan ɗaure mun kaina, taya akai hateem da yake ɗan kasar Nageria Yake mulkar ƙasar turawa mai girma kamar canada, dama hakan yana iya yiwuwa? Ta tambaya tana duban fuskokinsu, Safa ce tafara Kora mata jawabi”bazai yiwu ba sai dai idan ya kasance, shima ɗan kasarne, Misali kamar idan acan canada aka haife shi, kinga yana da ƴancin da zai Iyayin duk wani abu da ɗan kasar zai yi, ko kuma idan mutun ya zauna a wata ƙasa wadda ba tushen shi ba, har na tsawon adadin shekarun da zai iya cika duk wasu sharudda daya cancanta ya zama ɗan kasar shima yana da right da zai Iya aiwatar da duk wani abu da ɗan ƙasar zaiyi, shi kuma Hateem da kika gani asaline dasu a kasar canada, tushen mahaifiyarsu ne, Allah yajiƙanta, ta fito daga babban family daya shahara a ƙasar canada, bakomai nasani dangane da tarihinsu ba nima hajjaty ce tafara bani, kinsan mahaifinsu yayi yawon duniya sosai, kuma yana da farin jinin al’umma, duk inda ya shiga saiya samu kyakkyawar tarba, Ya zauna a kasashe daban daban tunkafin Ya auri matarshi ta farko, mariganya Hajiya kudirat, Allah yakai rahama ƙabarinta, itace ta haifa mashi Yan ukun shi, Senate lateef, sir mubarak da abdul razak na lagos, bayanshi sai Deen obinna, da kuma saratu autarta, Hajiya kudirat jinin sarauta ce, ta fito daga tsatson sarkin yarbawan jihar lagos, marwa tace”Ikon Allah shiyasa hajiya saratu take da jinkai, Ashe suma Izzar sarautace a jininsu” murmushi kowannansu ya saki, Safa ta numfasa kafin ta ɗaura da cewa”sharafuddeen kuma da Hateem uwa ɗaya uba ɗaya suke, Idan kika lura sunfi kamanceceniya da juna, duk da gaba ɗaya ya’yan obie dashi suke kama, babu wanda ya ɗauko mahaifiyarshi, har ƙwara Saratu ta ɗauko kama da Hajiya kudirat, bari in baki amsar tambayarki, Hateem dai a hannun dangin mahaifiyarshi can ƙasar canada Ya taso acan aka haife shi, kuma acan aka raineshi, mahaifiyarsu bata ta6a zama a kasar nigeria ba, Idan kinga tazo to zamane na ɗan lokaci, sai dai shi obie din ya taka yaje inda take tare da ahlinsa, shiyasama har family house garesu a ƙasar canada, shi kuma sharafudden da kika ga Ya taka matsayin shugaban ƙasa a nigeria bayan mahaifiyarsu ta haifeshi a canada, to shi ba a kasar aka raine shi ba, Ya zauna a hannun dangin mahaifinshine anan nigeria tun Yarintarshi har zuwa girmanshi, Idan kina neman ƙarin bayani game da hateem, Ki binciki tarihin Barack obama tsohon shugaban ƙasar america Kusan tafiyarsu ɗaya kinsan shima mahaifinshi ba ɗan kasar america bane, tushen mahaifinshi daga africa ne” murmushi kowannansu Yasaki, Marwa tace”ai basaima na bincika ba, Na gamsu da bayaninki sosai, Kin wayar min dakaina, Da ina kokwanton taya haka zata yiwu ɗan nigeria ya mulki wata ƙasa, amma yanzu kin goge min kokwantona, gaskiya abun Ya ƙayatar dani, balle shi hateem ma da ba Iya haihuwarshi acan akayi ba, Tushen mahaifiyarshi ne” firar da sukeyi bata dauke masu hankali Ga yin aikinsu ba, kasancewar sunada yawa, akwai wadanda ke zaryar kai abinci, ba iya su kadai bane. “Ni dai fatana Allah yasa uban Ƴan ji da izzar nan yazo yau” sophia ce tai maganar, Abla tace”Ai ga ƴar uwarshi nan uwar ji da Izza, Itama ta duro gidan, zanso inga haduwarsu” Safa tace”Kina nufin Nazli”? Jinjina kai Able tai”ita nake nufi, Yarinyar badai Ji da kai ba, ta Iya haɗe fuska bata da fara’a, Har ƙwara Yazrin tafi sakewa da mutane duk da itama bakowa take hulda dashi ba” Marwa tace”ke kuwa ai dole suyi izza, jinin sarautar dubai, Jikokin sarkin sarakai, Ga uba shugaban ƙasa sukutun da guda, uwa uba ga kyau kamar su suka tsara halittarsu, Ni wallahi burgeni suke Yi, takun tafiyarsu kadai abun kallone” Safa tace”ga kuma Hindu, nasan itama yau zata shigo gidan, itada mahaifiyarta Hajiya sarauta, mace mai ji da izza” Ta6e baki Sophia tayi”Um, nifa mutun ɗayace bana son ganinta, Hajiya laurat saboda bata da mutunci matar, ƙyamar talaka gareta” Dariya Abla tasaki tana fadin”kin kuwa san dole ta halacci taron nan, zata haɗu da ƴar uwarta Aunty masifatu, mu kuma mun shiga uku” dariya suka sanya gaba ɗayansu kafin suka maida hankalinsu akan aikin dake gabansu. *HAJJATY❤* A kwance suke saman gado, manne da juna, yahanata sakat tun ɗazu take son leƙawa kitchen pravin Ya hanata motsawa, ga tarin ayyuka dake jiranta, tun asuba ya shigo ɗakin. Muryarta da kasala take ambaton sunanshi”Pravin pls ka tashi ka tafi ɗakin matarka, baccin Ya isa haka, Ina da ayyukan da zanyi kada aji ni shiru a matsayina na babba acikin masu aikin gidan nan” A hankali Ya buɗe idanuwanshi da suka kaɗa jawur yana dubanta dasu. Sai faman lumshe su yake yi, don ba ƙaramin nauyi suka yi mashi ba, Short ne ajikinshi babu riga jallabiyar shi tana a saman mattress din, Ita kuma Iya undy ne tayi daurin gaba dashi, shara shara kana Iya ganin tsiraicinta. Kamar baisan furta maganar yace”dan Allah ki ƙyaleni, bana jin daɗin jikina ne, ki kwantar da hankalin ki babu wanda zai damu don baki aiki” Ya faɗa haɗi da ɗaura hannunshi saman sumar kanta dake akwance saman bayanta, a hankali yake shafa gashin Muryarta tamkar zata fashe da kuka tace”Na roƙe ka, ka tashi ka tafi dan Allah, Matarka zata Iya nemanka” “Meye damuwarki aciki, duk kin wani ɗaga hankalinki” Murguɗa mashi baki tai”Pls my baby boy, kasan yau babbar ranace agaremu, yakamata mu shiga cikin dangi ai hidima tare damu” Jinjina mata kai yayi’okey, naji zan tafi but before that, Inaso zan gargadeki, kinga yau akwai manyan mutanan da zasu halacci taron nan, banason inga gifcinki awurinsu, don na lura ba ƙaramin jan hankalinsu kike yi ba” Farfari tayi mashi da ido”idan kaga banje wurinsu ba to bana numfashine, hakanan kawai kake min baƙin ciki, don kada in samu mijin aure, kai kayi aure ni kuma ka hanani sakat” da zolaya tayi mashi maganar. Lumshe mata ido yai, ya tsare kirjinta da kallo kamar ba yanzu ya gama tsotsarsu ba. “Nidai na faɗa miki kuma na ƙare maganata, idan kika ƙara yi min irin wannan maganar zanyi maganinki ne” “Ashirye nake dana kar6i kowani irin hukunci da zakayi min, nasan dai bazaka Iya cutar dani ba” ta faɗa tana tura mashi kirjinta, aiko da karfi Yakai masu cafka, ta fasa ihu tana dariya, kutsa kanshi yai cikin undy dinta Ya cigaba da wasa da jikinta, tsawon mintuna kafin ya fito da kanshi ya haɗa uban gumi, sai faman sakin nishi take Yi tana haki kamar wadda tasha gudu “Ki rakani toilet muyi wanka, jikina ya 6aci sosai” harara ta jefa mashi”ni bazan bika ba, kaje wurin hajiya saratu tayi maka wanka” zaro ido yayi”ahaka ɗin” ɗaga mashi gira tai alamar eh. ‘Idan ta tambaye ni waye yai silar jefa ni yanayin Nan me kikaso in fada mata” Da shagwa6a tace”saika fada mata nice” da karfin hali ta furta hakan Dariya pravin yai”aiko da wa’adin aikin ki agidannan Ya ƙare, har kashe ki zata Iyayi, don ba ƙaramin kishine da ita ba, daga ni harke zata yi mana korar kare” “Kaga sai mu koma ƙauyanmu na indiya mucigaba da yin bautar shanu” dariya suka sanya gaba dayansu Bayan sun lafa ya sanya hannu biyu ya cuccu6eta Ya nufi bathroom da ita, Jim kadan Ya fito da ita ya ɗaurota saman kafadarshi, asaman gado ya kwantar da ita Yasanya mata bargo ya lullu6eta yana fadin”ki kwanta ki huta pls, bana son kina aikin wahala, inyaso da anjima saiki shiga cikin gidan” amsa mashi tayi da toh badan taji maganarshi ba. Shaf shaf Ya zura jallabiyarshi Yai mata sallama kafin ya fuce daga Cikin ɗakin, Fitarshi keda wuya wayar shi daya manta saman bedside drawer ta soma yin ringing, Ba tare data futo daga cikin bargon ba, Ta mika hannu tana laluban wayar har tayi nasarar Cafkota, ta fiddo da kanta tana duban screen din A tsanake ta furta sunan daya bayyana da manyan haruffa. *Jan le6e* ta6e baki ta ɗanyi aranta ta ayyana kowane ne wannan mai suna jan le6en? Sunan ma dariya yaso ya bata wai jan le6e, bazata Iya picking call dinba saboda Ya hanata ɗaga mashi phone idan aka kira, ko wayar bai bari ta ta6a ba, Sau ɗaya kiran ya shigo tai rejecting ba’a ƙara kira ba. Ajiye mashi wayar tayi saman drawer, ta dan lumshe idanuwanta yayin da zuciyarta ke tariyo mata fuskar kyakkyawan ɗansu da suka rasa, taji baƙin cikin mutuwarshi har yau idan ta tuna shi sai hawaye sun cika idanuwanta, tana matuƙar ƙaunar yaron, tsawon mintuna kafin ta yunƙura ta sauko daga saman gadon, donta kimtsa ta nufi kitchen. Idan muka koma 6angaren Unaisah, tun bayan kammala sallar asuba, ta nufi ɗakin danish ba tare da sanin kowaba, tana shiga ta same shi kwance saman lallausar carpet din dakinshi amaimakon saman gadonshi, dogon hijabi ne a jikinta launin maroon, zuciyarta duk ba daɗi, daga gefenshi ta zauna tana duban kyakkyawar fuskarshi, lokaci ɗaya taji gabanta na faɗuwa, sakamakon ganin yadda yake firgita acikin baccin shi, da sauri ta ɗaura Hannayenta saman ƙirjinshi Nan fa hankalinta Ya ƙara tashi Jin temperature dinshi, kamar na daren jiya, lamarin Ya ɗaure mata kai, Ga sanyin A.c har yayi yawa amma shi zafi ne a jikinshi, babu sassauci, Muryarta na rawa ta soma ambaton sunanshi”Danish! my Man? Wake up! Meke damunka? Why nake jin jikinka da zafi” can cikin baccinshi yake jin miryarta. “Dan Allah ka tashi kayi min magana meke damunka? Baka da lafiyane”? Daƙyar ya samu damar ware idanuwanshi Akan fuskarta, A daddafe ya samu Ya miƙe zauna yana dubanta, Short din Jiyane a jikinshi da singlet. Yaji dadin ganinta a room dinshi, Jiya yai zaman jiranta yai tunanin zata zo gare shi har bacci yai awon gaba da shi bata leƙo ba, till now. “Kayi shiru baka ce min komai ba, danish zafin jikin ka yai yawa, kodai inje in faɗa ma Boss Man Yazo Ya duba ka”? Girgiza mata kai yai, kafin ya motsa la66ansa Ya furta”babu abunda ke damuna, Lafiyata qalou, kece kika 6ata min rai” Hankalinta bai kwanta da kalamanshi ba, aɗan ruɗe ta furta”ba haka bane danish, dole akwai abunda ke damunka ba Iya 6ata maka rai da nayi bane, cos babu yadda za’ai Jikinka yadau zafi rau batare da dalili ba, Please ka faɗamin idan ba haka ba hankalina bazai kwanta ba, sannan kayi hakuri dan Allah, abunda ya faru Jiya wanda ya 6ata maka rai, In sha Allah bazan ƙara bari Hakan Ya faru ba” Cikin kulawa take Yi mashi magana, Jinjina mata kai yai”kiyi min alƙawarin ba zaki ƙara rungumar wani ƙato a jikinki ba, idan bani ba koda su Naufal ne” kiris ya rage ta saki dariya jin abunda yace Jinjina mashi kai tayi”in sha Allah My man kai kaɗai kawai,” ajiyar zuciya ya sauke Ya samu sassaucin radadin da zuciyar shi ke yi mashi “Tunda naga yanzu hankalin ka ya kwanta fada min meke damunka? Menene ya haddasa maka zafin jikinka”? Ta faɗa tana duban ƙwayar idonshi, la66ansa duk sun bushe ƙamas. “Dagaske nake Yi maki babu abunda ke damuna, Nima bansan ya akai jikina ya ɗauki zafi ba” “Nidai hankalina bai kwanta ba, ka ba ni dama inje in faɗa ma boss man halin da kake aciki,” haɗe mata fuska yai jin ta ambaci sunan boss man, sam bayason ji. “Bana buƙatar kowa ya dubani, ki kwantar da hankalin ki, zafin jikina baiyi min illa ba, don haka kija baki kiyi shiru” Jinjina mashi kai tay”maganar abinci fa? Jiya kace min ba ka ci dinner dinka ba, ni sam Na shafa’a” Yamutsa mata fuska Yai, hada jifarta da harara, murmushi tasakar mashi “Bari naje na duba dining, idan an shirya mana abincin breakfast dinmu, zan shigo maka da naka a ɗaki tunda baka son fita” ɗaga mata gira yai alamar okey. Miƙewa tayi da sauri ta fice daga dakin ta sauko down stairs, koda ta duba ɗakin cin abincin ba a jera masu komai ba, saboda time din da suke zama Yin breakfast bai cika ba” yanke shawarar neman ɗakin Ummi tayi don ta fada mata game da ɗan uwansu dake jin yunwa, wata’ƙil ta sama mashi abunda zaici kafin a shirya masu abincinsu. Batasan ina zata nemo room din ummi ba, tadaisan acan upstairs Yake, cos ta ta6a ganin tana saukowa saman bene, da sauri ta nufi stairs din tana tafiya Hijabin Jikinta naja da ƙasa, babu kowa a palourn duk suna adaki. A hankali take taka stair cases din Har ta samu ta haura can sama, Ta rasa wace hanya zata bi wadda zata sada ta da bedroom din Ummin america, Tafiya taci daga dayi tana bin ko’ina da kallo, aranta tana ƙara jinjina haɗuwar ginin, tana ta ƴan kalle kalle kamar baƙauya harta zagayo ta 6angaren Hagu batare data gano hanyar da zatabi ba, Ƙofar wani katafaren room Ta dakata da yin tafiyar, aranta ta tace”idan kuwa wannan ne ɗakin aunty ummi duk Yafi namu kyau” Ta cikin glass din ƙofar take hangen zallar haɗuwar kayan alatun cikinsa, kifa kanta tayi jikin ƙofar har ta danna madannin Jikinta batare data an kare ba, da alama mamallakin ɗakin Yayi recieving alert na neman iznin shigowa shiyasa ƙofar tafara ƙoƙarin zugewa slowly take sliding, da sauri Unaisa Ta saki glass din Jin yana motsi, abunka game karanbani, ganin ƙofar ta wage, sai kawai ta haura ƙafarta ciki, yau ta ga maƙurar aljannar duniya a ɗakin data faɗo, wuyanta kamar zai 6alle, tana tafiya tana ƴan waige waige kamar zatayi tuntube, tayi mamakin dukiyar da aka narka wurin tsara Kayan furniture din dakin, Yana da fadi da tsayi, ga wannan floor to ceilling window din a left hand din bangon ɗakin, Ta jikin glass din zaka Iya hangen wajen ginin Harma da manya manyan gine ginen dake acikin burnin abuja, bayan haka daga cikin bedroom ɗin zaka Iya hangen komai na cikin bathroom ta glass din ƙofar, sai dai da alama ba haka akeyin wanka acikinshi ba, da akwai hanyar da ake rufe glass din yai duhu idan mutun zaiyi using dashi. Sai faman jinjina kai Unaisah take Yi, tajima tana mamakin wanene mamallakin daular nan da suke acikinta, bata ta6a yin tozali da shi ba, tadai ta6a jin sunan Chief of isod abakin Dr Laura. Tabbas Da ace tasan ɗakin wanene da batayi gigin shigarshi ba, ta zaƙe sai kurɗaɗawa take Yi can ciki ta shige kamar ɗakin baba tajo, shi kanshi bedroom din Yana da katafaren falonshi Har yaci uban na down stair haɗuwa, tana ƙoƙarin giftawa ta wata ƙofa dake a ɗakin, kwatsam kunnuwanta suka soma Jiyo mata sautin daddaɗan kiɗa Yana tashi, na taken waƙar satisfya Wani irin daddaɗan ƙamshi Ya ratsa hancinta sosai ta shaƙeshi, a hanzarce ta ɗaura idonta saman kofar ɗakin rubutun sama ta karanta kamar haka *Gym room” nan take ta fahinci dakin menene, wato wurin motsa jiki ne” aranta ta ayyana bari ta dan leƙa taga wanene Ya kunna sautin kiɗa. Kasancewar ƙofar abuɗe take, Unaisah ta zura kai kamar 6arauniya tana bin ko’ina da kallo, an ƙawata room din da injinan motsa jiki, kala kala, ga kayan jin sauti, sam bata lura da shi ba, kamar yadda shima bai lura da mutun ba, Yadaisan akwai wanda ya shigo dakinshi saboda alert din da yai recieving awayarshi, saida Ya bada iznin shigo ciki tukunna ƙofar ta buɗe. Sai faman wurwurga eye balls dinta take tana bin ko’ina da kallo, lokacin da tayi arba dashi wani irin mugun bugu ƙirjinta Yai, har saida ta dafe shi da hannu, tayi matuƙar firgita da ganin shi, Ya tattara hankalinshi gaba ɗaya akan Punching bag din da yake kaima naushi da hannayensa waɗanda ke sanye cikin boxing gloves, Cikin zafin nama yake motsa jikinshi, Ya haɗa uban gumi, zufa ta ko’ina take tsattsafo mashi, ƙirar ƙarfinshi Ta bayyana ga wannan sick pack din ƙirjinshi ruɗu ruɗu, Damtsen hannayenshi sun murmurɗe, Yana naushin jakar motsa jikin Breast muscles dinshi na shaking, babu riga ajikinshi, black short ne kaɗai Ya sanya wanda Ya tsaya mashi dai dai gwiwarshi, bata samun damar ganin fuskarshi dakyau ba, saboda ba ita Yake fuskanta ba. Ta natsu tana kallonshi, Ko idonta bata ƙyaftawa, ba zato ba tsammani taji an damƙi wuyanta ta baya, harta buɗe baki zata fasa Ƙara taji anyi saurin toshe mata baki, tsoro Ya kamata jikinta ya hauyin kerma, ɗungurugum taji an dagata sama Anjata zuwa cikin bedroom din, sai faman wuntsila ƙafafuwanta take Yi a ƙoƙarinta nata kwace kanta daga hannun mutumin daya dauketa, har ƙofar ɗakin Ya fito da ita Ya direta ƙasa, A firgice take dubanshi, bakomai bane face Big guy, kayan kakinsu ne a jikinshi, ya sanya face mask a saman fuskarshi, idanuwanshi na akan fuskarta, La66anta na kerma ta furta”wa..wa.. Wanene kai? Meyasa ka daukoni? Idanma saboda nashiga ɗakinne aini bansan ya akai na shiga ba, rashin sanine, ɗakin aunty ummi nake nema, danish ne Yake jin yunwa jiya baici dinner din shi ba kuma na duba dining ba’a shirya mana abinci ba” tsabar ruɗune yasa take yi mashi zuba har abunda bai tambayeta ba, taƙi barima Yai mata magana Sai da ta dasa aya tukunna Ya soma yi mata magana cikin muryar raɗa”kinsan ɗakin wanene kika shiga”? Girgiza mashi kai tayi alamar a”a gyaɗa kai yai”kada ki kuskura ki ƙara yunƙuri shiga ciki, Idan ba haka ba jikin kine zai gaya maki, Ni nayi mamakin ma taya akai kika samu damar shiga bayan ita kanta ƙofar sarrafata akeyi, Kodai ba mutun bace ke”? Ya fada haɗi da ɗage mata gira alamar yana jiran amsarta. Duk tabi tasha jinin jikinta, sai faman zare mashi gray eyes dinta take Yi, daƙyar Ta iya fadin”nifa bansan komai ba, ai na fada maka dakin aunty ummi nake nema” ta ƙare maganar tana murguɗa mashi baki. Har murmushi yasakar mata batare data gani ba saboda mask din fuskarshi, dama Yaji labarin rashin jin maganarta, gashi yanzu ya tabbatar dahakan” “Okey, ki koma ɗaki, yanzu zanzo in kawo maki abunda shi ɗan uwan naki zaici, kafin Ashirya maku naku abincin” amsa mashi tayi da toh, jikinta har rawa yake Yi wurin yin saurin haura ƙafa ta kama hanyar komawa ɗakin danish, tana tafiya haɗi da waiwayan big guy, Yana atsaye yana kallonta har saida ta 6ace ma ganin shi, tukunna ya kawar da idonshi daga gareta. Tun da ta koma ɗakin danish bata daina tariyo suffar mutumin da tayi tozali dashi a gym room ba, Ya tsaya mata aranta, taso ace sunyi ido biyu da shi, don ta samu damar ƙare ma fuskarshi kallo, shin wanene shi? Tabbas tanaso ta sani! Bada jimawa ba, Big guy yai sallama dakin danish, hannunshi ruƙe da tray din Kayan abinci ashake, bayan ta kar6a tayi mashi godiya, asaman carpet suka zauna ita da danish, ta dinga bashi abaki Yana ci, suna kallon juna yayin da acan ƙasan zuciyarta tunanin ɗan ta halikin nan take Yi, shi kanshi danish Ya lura da canzawarta, saboda tsabar tunani har a hanci tai ƙoƙarin cusa mashi abinci, saida ya damƙo hannunta tukunna ta ankara, yace mata me take tunanine tace mashi bakomai, badan ya yarda ba ya ƙyaleta, A ɗakinshi ta zauna duk don ta faranta mashi, sai da tasanyashi yai wanka ya canza kayan jikinshi tukunna hankalinta ya kwanta, damuwarta ɗaya yanzu zafin jikinshi sai ƙara ninkuwa yake Yi. *Obie Estate* Wuraren ƙarfe huɗu da rabi Estate din Ya cika maƙil da mutane babu masaka tsinke, manya mutane masu faɗa aji duk sun hallara, kama daga Ƴa’ƴan jam’iyarsu ta Action progressive party ministoci, sanatoci, gomnoni, da sauransu, Kowannansu Ya ɗauki wankan expensive shadda ta kece raini na shiga tsara, jikokin Obinna Na ƙasa nigeria da wadanda ma basa ƙasar saboda shagalin nan sun dawo Nigeria A yau din nan, daga cikinsu akwai ya’yan sir mubarak mazauna kasar canada, zaratan samari Zaki shine babban ɗanshi mai bi mashi Ibad, bayansu sai ƴa’ƴan His excellency abdul razak, babban danshi Yasir, tare da ƙanwarshi Yusra, sunzo ne tare da mahaifiyarsu Her excellency hajiya muhibbat, bayan su sai Ya’yan his excellency Deen, babban ɗanshi Justice Nadeem mai bi mashi Dr. nawaz tare da mahaifiyarsu suka zo Her excellency hajiya Jamila, bayansu kuma sai ƴar gidan mai girma sharafudden Hindu ƙanwar Chief Owais, tare da matayanshi suka zo Hajiya Malikat sarauta uwar gidanshi da kishiyarta Hajiya laurat, da kuma ƴar wurin Lateef zulaihat kanwar ziyad, gaba ɗayansu dai kowa Ya hallara ga yan matan hateem Nazli and Yazrin, gaba ɗaya matan sun ɗauki wankan Swiss cord lace yayi bala’en Yi masu kyau, A babban hall din dake acikin gidan aka gudanar da shagalin, An ƙawata cikinsa da kayan alatu, ko’ina ka kalla furannine da ƙyalƙyalin sparkling chandeliers, ga Banquet chairs da aka tanada domin baki su zauna, kowani table saman shi an ɗaura bouquet of flowers, tare da Crystal glasses and silverware, da sauransu, floor din hall din kuwa an shimfiɗe shi da ƙayataccen red carpet, daga can gaban hall din Gingirimeman Cake stand ne an ƙawata shi sosai, Mawaƙa da makaɗa hada maroƙa sun hallara, domin suma su kwashi rabonsu, an shirya kayan abinci saman zungureran table kala daban daban, sai mutun Ya za6a ya darje, duk haɗuwar taron nan mutun ɗayane bai hallaraba, Hakan ba ƙaramin ta6a zuciyar obie yai na, Yaci buri akan zuwanshi amma shiru babu shi babu alamarshi, mutane sai tambayar shi suke Yi, ya akai basu ganshi ba? Iyayenshi sun rasa amsar dazasu basu, sai dai suka dinga cewa bai kaiga zuwa ƙasar ba, farin jini gare shi shiyasa duk wanda yazo sai ya tambayi ina owais Yake, Taro Yayi albarka, Anci ansha anyi kullu wash rabu hani’an, Anyi harka ta arziƙi ta kece raini, daruruwan mutanan dasuka kawo mashi kyauta taban mamaki basu ƙirgiwa, baba obie Ya mori lokacin shi, Yayi farin cikin dabazai Iya misalta shi ba, Ƴan uwa da abokanan arziƙi sun faranta mashi rai, sun gwangwajeshi da Kyaututtuka na ban mamaki, Sun taka rawar girma, sai dai muce Alhamdulillah taro Ya tashi Lafiya, gab da magrib baƙi suka ragu waɗanda suka rage ƴan uwane na jini, da kuma mutanan Hateem. *WAIWAYE ADON TAFIYA💫* (Abunda ya faru bayan zahra ta faɗa ma Aneelerh halin da take aciki, Na kuɗi da hajiya falmata take binta bashi, bayan ta koma ɗaki damuwa ta isheta, tayi ƙarfin haline kawai wurin bata shawara akan ta amince da buƙatar hajiya falmata saboda tana son ta jaraba zahra ne don taga idan tana da hankali, tunani ta soma yi ta wace hanya zata Iya taimakonta? Nan take zuciyarta ta bata shawarar tayi amfani da sauran kuɗin nan da jami’an sirri suka bata, har yau bata ƙarar dasu ba, tamkar tana jin tsoron ta6a su, tun dai data siya ma baby junaid kayan wasa bata ƙara cirar ko naira biyar ba. Ba tare da sanin kowa ba Aneelerh ta tuntu6i mahboob, a ɗakin shi ta same shi, ta tambaye shi koya san gidan hajiya falmata mahaifiyar ƙawar zahra? Yace mata eh yasan gidan, sun ta6a zuwa tare da zahran ma, tace toh so nake ka rakani gidan, da mamaki akan fuskarshi yace amma me zakiyi acan din kinsan ta ne? girgiza mashi kai tay alamar a’a, kawai inaso ka rakani muje, idan mun fita zan faɗa maka komai, amma kafin muje gidan zaka fara rakani banki, akwai wasu kuɗi da nakeson in cira, Jin ta ambaci kuɗi yasa mahboob saurin amincewa zai kaita gidan, a cikin motarshi ya dauki aneeleeh saida suka fara biyawa banki ta ciri kuɗin kafin suka nufi gidan hajiya falmata. Lokacin da suka karasa gidan, A parking space mahboob Ya tsayar da motar, Aneelerh tace dashi ya jirata anan, ya amsa mata da toh, da sallama abakinta ta shiga palourn gidan, adai dai lokacin mai aikin gidan ta fito daga kitchen ta yi arba da aneelerh, fuskarta da fara’a suka gaisa tace mata wurin hajiya falmata tazo, Allah yasa tana nan, Mai aikin tace bata jima da dawowa daga office ba, ki zauna bari naje in sanar da ita, da sauri mai aikin taje ta fado mata, jim kadan ta dawo ta sanar da aneelerh sakon hajiya tace ta jirata gata nan zuwa, aneelerh ta amsa mata da toh, kusan mintuna biyar Aneelerh tana a tsaye ta ruƙe qugu tana jiran fitowarta, cikin jin fargabar ganin matar, sai faman bin palourn take yi da kallo. Sautin takun tafiyarta ne Yaja hankalin Aneeleerh ga kallonta, A hankali take saukowa down stair, ta ɗauki wankan tsadaddan leshi, kanta yasha ɗaurin ɗan kwali, ta manna farin glass a idonta, Babbar macace tana da jiki, tana tafiya tsokokin jikinta na motsawa, Fatar jikinta tasha hutu har ta gaji, daga ganin fuskarta masifaffiyace, idanuwanta mitsi mitsi da su kamar na mutanan Yankin china, hancinta kuwa abaje yake, ga big mouth dinta yasha man baki. Ta6e baki Aneeleerh tayi aranta ta furta jibarta dan Allah, ƙatuwar banza da ita kamar buhun masara, a haka take lalata rayuwar matasan ƴan mata, Allah dai ya shirya, wasu mutanan sunyi asarar rayuwarsu. Lokacin da hajiya falmata ta ƙarasa saukowa daga saman benan, idanuwanta suka Yi mata tozali da kyakkyawar fuskar Aneelerh nan take taji ta burgeta, tayi mamakin ganin baƙuwar fuska agidanta, bakomai yafi tafiya da imaninta ba face Kyawun surar Aneelerh. Ganin Yadda Ta tsareta da idone Yasa Aneelerh tayi saurin gyara mayafinta ta rurrufe jikinta, Aranta ta furta A’uzubillahi minasshaidanirrajin, Aniyarki ta biki baƙar mayya” Saman sofa din dake fuskantar Aneelerh Hajiya ta zauna, tana dubanta da wani irin mayataccen kallo. Yamutsa fuska Aneelerh tayi fuskarta ba wasa tace”barka da Yamma” Hajiya falmata ta amsa mata da”barka dai, bismillah ki zauna mana” Ɗaure fuska Aneela tayi”bana zama agidan da ake aikata sa6on Allah, saboda ni tsarkakakkiya ce, bai kamata in goga ma jikina najasa ba”!! Mamakine Ya kama hajiya falmata, a hankali ta sauke glass din dake saman fuskarta don ta samu damar ƙarewa Aneelerh kallo. “Bansan wacece ke ba, sai dai na fahimci haukan talauci ne ke damunki shiyasa kika kwaso ƙafa kika zo gidana don in taimaka maki” Dariyar rainin wayau Aneelarh Tayi kafin tace”ki kalleni daga ƙasa har sama, kema kinsan nafi ƙarfin ki kira ni da talauci, Ni banzo don nayi cece kuce dake ba saboda bani da lokacinki, Maganar kudin zahra da kike bin ta bashi ne” Shu’umin murmushi ne Ya bayyana akan fuskar Hajiya falmata da shaƙiyanci ta furta”oh, kinzo ne ki fanshe ta, shiyasa kika kawo min kanki? Donni banga alamun zaki Iya biyan kuɗin ba” Girgiza kai Aneelerh tayi ranta a6ace tace”wato shi dai jaki duk yadda akai dashi sai yaci kara, idan kina tunanin na kawo maki kaina ne don in fanshi zarah to ki daina, domin kuwa nafi ƙarfin ƙasƙantacciyar mace ballagaza jahila kuma daƙiƙiya irinki, Mace mara tsoron Allah, me yin amfani da dukiyarta don lalata rayuwar matasan ƴan mata masu neman nakansu, Wlh kinji haushin rayuwar......” gigitacciyar tsawa Hajiya falmata ta daka ma Aneelerh, tamkar damusa ta yunƙura ta miƙe tsaye tana duban Aneelerh da mummunar fuskarta babu annuri ko misƙala zarratin ta nuna mata Hanyar fita da yatsan hannunta”Ke Fuce kibar min gidana, tunkafin ranki Ya 6aci, matsiyaciyar banza masu ƙashin tsiya” Aneelerh da ƙarfin Hali tace”idan kinga na fita gidan nan to nagama faɗin ta cikina ne, Kuma wallahi koda gigin wasa kika ce zaki ta6a lafiyar jikina saina naƙasa ki bakisan wacece Ni ba” ta faɗa tana jefa mata harara, lamarin Ya ɗaurewa Hajiya falmata kai, ganin karfin hali na Yarinyar nan data zo gidanta tana Yi mata rashin Kunya. Goya hannayenta tayi saman ƙirjinta”ina sauraronki, Me ya kawo ki gidana!” Gyaɗa Kai Aneelerh Tayi”zuwa nayi don Inyi maki nasiha, don na fahimci Wadda iyayenki suka yi maki tuni shaiɗan Ya hure maki kunne, dan Allah Jibarki cikin shiga ta mutunci kamar wata mutuniyar arziƙi, al’halin nan kuwa fuska biyuce ke, A fili musa a zuciya fir’auna, Haba baiwar Allah, Da hankalinki da tunaninki da shekarunki kika za6i ki sa6awa Allah don kawai ki ji daɗin duniya? Kin manta da Allah yana ganinki kuma zaki mutu ki koma gareshi, a ko’wani yanayi mutuwa tana iya riskarki, idan taƙamarki kuɗine ki tuna Allah ne Ya baki Arziƙin bake kikayi ma kanki ba, Idan yaso zai Iya ƙwace wa, kuɗi da kike gani wallahi masifane Idan baka tafiyar dasu ta hanyar da ta dace ba, Ita kuma rayuwar duniya jin daɗinta ƙalilan nan bata da tabbas, bakisan yaushe zaki mutu ba, kin sanya mugunta aranki saboda Allah Ya azurtaki, Kina cutar matasan Ƴan mata, waɗanda Iyayen su suka sha wahalar basu tarbiya ke kuma kina gur6ata masu rayuwarsu, Allah kaɗai yasan adadin Ƴan matan da kika 6ata, kin goga masu jarabar da bazasu Iya gogeta ba, Kin cutar da rayuwarsu mutane suna kuka da su saboda sun addabi rayuwar al’umma kuma ire-iren ku ne ku ka yi silar lalacewarsu, wallahi kiji tsoron Allah kamar yarda ba zaki so ayi da ƴar ki ba to kema kada Kiyi da ɗan wani, duk da naji irinku Harda ƴa’ƴan naku kuke Yi, saboda shafewar basira da neman duniya kun makance bakwaji bakwa gani ku ala dole saikun siyama kanku tikitin shiga wuta”? Tun da Aneelerh ta soma Yi mata magana da faɗa haɗi da tsiwa take ta faman zare ido tana binta da kallo, tun da take arayuwarta wani ɗan adam bai ta6a gigin tunkararta Ya faɗa mata magana game da abunda Take aikatawa ba sai Yau da Allah Ya haɗa ta da Auntyn Zahra mai dimple, Ayoyin kur’ani aneelerh ta soma karanto mata tana fassara mata, kamar an rufe mata baki takasa dakatar da ita duk irin masifar da take da ita yau an kashe mata bakinta “Allah Yana son bayinshi waɗanda suka aikata 6arna suka tu6a saboda tsoronshi suka koma gareshi, dan Haka ina baki shawarar tunkafin lokaci Ya qure maki Hajiya falmata ki Gyara Halayanki, Ni bance zan sanyaki ki shiryu ba don nasan irinku taurin kaine daku kamar kwakwa, ko malamai sunyi maku nasiha bakwaji bakwa gani sai ranar da Allah Ya damƙe ku tukunna zaku gane kurenku, Ni in banda ma shafewar basira, wai ku bakwa tuna mutuwa da kwanciyar ƙabari ne? Baku tuna duk abunda kuka mallaka zai ƙare, daga kai sai halinka za’a binne ka a ƙabarin ka fa? Ke yanzu kin za6i ki mutu kina aikata mummunan zunubi na bin Ƴan uwanki mata? Ga hakkin Iyayen da kika sanyasu zubar da hawayensu ta silar lalata masu rayuwar ƴa’ƴa da ki ka yi ga kuma Matasan ƴan matan da kika gur6ata ma rayuwa, wannan fa zunubine mai cigaba da yaɗuwa ko bayan kin mutu zaki cigaba da samun kamasho acikin shi, saboda kinbar tarin ƴan matan da kika gur6ata agari suna aikata fasadi, wallahi kiji tsoron Allah tunkafin lokaci Ya qure maki, Ina ƙara jan hankalinki ki tuba ki koma ga Allah tunkan mutuwa ta risƙe ki don ita bata kwankwasama mutun ƙofa balle Yace zai shirya mata” Wata irin zuface ta soma wanke goshin Hajiya falmata, Haƙiƙa kalaman Aneelerh sun fara karya mata zuciya, sai faman zare ido take Yi, batasan ya akai ta tsinci kanta da jin maganar Aneeleerh ba, Yarinyar tayi matuƙar burgeta kuma ta bata mamaki da har ta iya yi mata nasiha batare da jin shakkarta ba, saboda mutane dayawa basa Iya yin magana agabanta, amma Ita wannan ido cikin ido take furta mata magana . “hajiya falmata, duk runtsi duk wuya kada ki Karya zuciyar wanda Ya aminta dake! Ina magana akan zahra da ta dauke ki tamkar mahaifiyarta saboda ƙaunar dake a tsakaninta da ƴarki fatima, Kin karya mata zuciya, naji daci lokacin da na sameta ta kulle kanta acikin toilet tana Yin kuka babu ci babu sha ita kaɗai batare da kowa ya sani ba, Kin hanata runtsawa saboda taƙi baki haɗin kai ku aikata sa6on Allah, haba baiwar Allah, idan kece akayima yarki haka zakiji daɗi! Don kawai mutun Na buƙatar agazawarka sai kayi anfani da dukiyarka donka cutar dashi? Babu wanda yafi ƙarfin ya nemi taimako a duniyar nan, koda ba a wurin mutun ɗan uwansa ba, zai nema awurin Allah Idan har baka agazama bawansa ba tayaya kake tunanin zai agaza maka? Jinjina kai Aneelerh tayi, Tuni zafafan hawaye sun wanke fuskarta cikin muryar kuka taci gaba da cewa”Kin ƙona mata rai, zahra ta yarda dake fiye da tsammaninki, tana kuka tana fadamin yadda ta aminta dake amma kika karya mata zuciya, Zahra da kike gani tafi ki Hankali, Yarinyar tana da tawakkali, tana jin tsoron Allah, Na jarabata don inga ko tana da wayon jure ƙaddara idan ta sameta, Ni dakaina nabata shawarar ta baki haɗin kai, da buɗar bakinta sai ce mun tayi ita ko duniya za’a mallaka mata bazata ta6a amincewa ta sa6ama Allah ba, saboda tana jin tsoron shi kuma tana jin tsoron ranar da zata koma gare shi, Hajiya falmata kin ta6a tunanin hakan? A matsayinki na babbar mace wadda ta haura shekara arba’in da ɗuriya a duniya? Shekaru sunja amma baki tsoron mahaliccin ki? Kina amfani da dukiyarki wurin Gur6ata duniyarki da lahirarki, maimakon kiyi amfani da su wurin taimakon bayin Allah marasa ƙarfi wadanda zasuyi alfahari dake ko bayan ba ranki kuma ki samu lada awurin Allah, Yanzu ina amfanin irin wannan rayuwar da kika daukarwa kanki”!? Ƙafafuwanta ne suka gaza ruƙeta, Jiri Ta soma gani a cikin idanuwanta, adaddafe ta nufi sofa ta zauna tana faman fitar da numfashi. Hankaɗe Kafaɗa Aneeleerh Tayi”Alhamdulillah nagama faɗar ta cikina, duk wanda yayi da kyau don kanshi, akwai mutuwa akwai hisabi, maganar kuɗi Kuma nazo maki da su miliyan Uku Cuf, Idan ma kina son ƙari zan ƙara maki, saboda inaso kisan muba jinin faƙirai bane idan arziƙine muma mun gaje shi gaba da Baya” Ɗaga murya Aneelerh Tayi da ƙarfi ta furta sunan Mahboob, shigowa ɗakin Yayi hannun shi ruƙe da jaka baƙa, tunkan ya ƙarasa yake bin ko’ina da kallo, ganin haɗuwar falon gidan aranshi Ya ayyana Lallai hajiyar nan ta tara shiyasa take tsula tsiyarta son ranta saboda tana da arziƙi. “Zoka ajiye mata tsiyarta,” Aneelerh ta faɗa tana nuna mashi gaban Hajiya falmata, Ta zabga uban tagumi da hannu biyu, da alamun nadama atattare da ita. Koda mahboob Yayi arba da fuskarta saida yasha jinin jikin shi ganin yadda ta haɗe rai, ga gumi na fita a goshinta. Kamar mai jin tsoronta Haka Ya ajiye mata jakar agabanta. Aneelerh ta ruƙo hannun shi acikin nata, har sun ɗaga ƙafa zasu bar falon muryar Hajiya falmata ta dakatar da su “Dan Allah Ku tsaya”!! Kusan atare zuciyarsu ta buga, a sukwane suka waiwayo suna dubanta, Gabansu ba ƙaramin faɗuwa yayi ba ganin ta fashe da kuka, miƙewa tayi daga saman sofa din ta nufe su tana fadin”wallahi nayi nadama, dan Allah kuyi haƙuri da abun kunyar dana aikata, Nima ba halina bane ƙawayene suka tunzurani har na faɗa harkar” zubewa tayi saman gwiwowinta agaban aneelerh tana kuka tace”Tun da nake a rayuwata wani ɗan adam bai ta6a yi mini nasihar data ratsa zuciyata ba sai akanki, bansan wacece ke ba, amma nayi sha’awar In yi koyi da kyawawan halayanki, duk naji na tsani kaina, na zubda mutuncina da girmana a idon zahra, wallahi naji kunyar da ban ta6a jin taba, Naji ƙuncin Halin dana jefa zahra, saboda ni tagaza runtsawa Na hana baiwar Allah yin bacci na hanata cin abinci, na jefa rayuwarta cikin ƙunci batare da nayi tunanin raɗaɗin da zataji acikin Zuciyarta ba, wallahi nayi nadama koda ace bazaku yarda dani ba, Na tuba kuma in sha Allah bazan ƙara aikata zunubin nan ba, angama bi’iznilillahi, saboda inaso Inyi kyakkyawan ƙarshe kuma inaso in tsira ranar gobe ƙiyama, In sha Allah daga yanzu nagama yin amfani da dukiyata don in sa6awa Allah, da kuma gur6ata tarbiyar ya’yan mutane.....”daƙyar ta ƙare maganar tana faman jan magina. Ba Aneelerh ba hatta Mahboob Yayi mamakin wannan Ikon Allahn, sun yi sototo suna kallonta kamar sakarkaru duk ta zama abun tausayi tsoron Allah ya shigeta, wata’ƙil dama itace silar shiriyarta shiyasa Allah Ya haɗasu da ita. Muryar Hajiya falmata na rawa tace”Ku taimaka mun dan Allah, inason in wanke kaina awurin zahra, saboda inason taci gaba da kallona kamar yarda tasanni ada, Nayi alƙawarin zan taimakamata, kuɗin da ku ka zo dasu na yafe mata ku ɗauka ku maida mata su, Sannan inaso taci gaba da yin aiki a company dina, Kayan da suke son ayi masu order A dubai gobe in sha Allah zasu iso Nigeria” Kallon juna mahboob da Aneelerh suka ƙara Yi, Atare suka furta Alhamdulillah, Aneelerh tace”nagode ma Allah daya bani baiwar Iya tsara kalamin da har suka ja hankalinki, Naji daɗi dana zama silar shiriyarki, Ina fata zaki canza rayuwarki daga Yau ki koma ta gari, wadda kowa zaiyi alfahari da ita” Jinjina kai Hajiya falmata tayi Cikin sanyin murya tace”in sha Allah,” ruƙo hannayenta aneelerh tayi acikin nata, miƙewa tayi tsaye suna fuskantar juna “Ki godema Allah, saboda Yana son ki da shiriya shiyasa Ya baki damar gyara rayuwarki tun da sauran numfashinki,” Jinina Kai Hajiya falmata tayi. Aneeleerh ta ƙara da cewa”sai dai kiyi haƙuri, ba zamu maida kuɗinba, nariga dana kawo maki dasu, Ki ruƙe su a hannunki, zahra kuma bazata ƙara Yin aiki a companynku ba, zan nema mata aiki awani wurin”!! Magiya hajiya falmata tadinga yi mata akan tayi haƙuri su koma da kuɗin, ta yafe masu, amma Aneelerh taƙi yarda, mahboob ne yace ta jira zasu yanke shawara a tsakaninsu, ruƙo hannun Aneelerh yai acikin nashi yajata zuwa gefe ɗaya akwai tazara tsakaninsu da hajiya falmata, tayi kasake tana kallonsu “Aunty aneelerh tunda tace ta yafe kuɗin mu koma dasu kawai, ai ba roƙonta mukayi ba” Girgiza kai aneelerh tayi”nidai hankalina bai kwanta da matar ba, wallahi irinsu shaiɗanune Mahboob, inajin tsoron ace wani tuggun zata kitsa mana shiyasa tace ta yafe kuɗin, ƙwara mu maida mata aniyarta” Yamutsa fuska mahboob yai”aunty aneelerh just ki gane, ni dai na yarda da ita, sau dayawa zaki ga mutun yana aikata ba daidai ba idan Allah yaso shi da rahama saiki ga ya shiryu cikin sauƙi batare da ansha wahala ba, Yanzu ki duba matar can, hada fa kukanta kuma har zuƙunnawa tayi saman gwiwowinta tana roƙonmu, why bazamu yafe mata ba? Komai ya wuce, ita kanta zahran ba ƙaramin daɗi zataji ba saboda tana son fatima ƴarta aminnan junane tun tuni, sannan taci burin zuwa obie estate, bayan haka aikin nan da take Yi a companyn su ba ƙaramin ƙaruwa take Yi ba, ita kanta tana faɗi da bakinta irin alheran da take samu ta silar aikin da suke Yima mutane, idan ma da wata manufa tace hakan to mu barta da Allah, In sha Allah babu abunda zata Iya yi mata,” gyaɗa kai Aneelerh tayi”shikenan na amince da buƙatarta, mu koma mu faɗa mata” komawa sukayi cikin falon, bayan sun sanar da ita shawarar da suka Yanke ta dinga yi masu godiya farin ciki duk Ya cikata, kafin tafiyarsu saida ta roƙe su alfarma akan su taimaka mata, tana so zahra taci gaba da ganinta a matsayin mahafiyarta, tasan ayanzu bata da sauran mutunci a idonta. Aneelerh ce tabata shawarar yadda zata tsara ma zahra, duk don ta amince da cewa ba halinta bane, sun jima agidan kafin daga bisani sukayi mata sallama, sunyi rabuwar mutunci da hajiya falmata, har musayar number sukayi da Aneelerh saboda acigaba da zumunci. ( kunji abun da Ya faru, kafin washe garin ranar da zahra taje kaima Hajiya falmata kuɗinta) Wuraren ƙarfe takwas na dare, motar drivern da yaje dauko su Alhaji ubaid daga airport ta kunno kai gate din gidan, tunkafin ƙarasowarsu, Dr Shureim da zeenatu suna atsaye bakin Entry hall din falo, hannunsu ruke cikin na juna, daga ita har shi jallabiyace ajikinsu, ta yafa mayafi akanta, tsantsar farin cikine akan fuskokinsu, sunyi matuƙar ƙagara da son ganinsu. Zeenatu sai faman washe baki take Yi, tunda tayi tozali da motar dake shigowa tana tunkaro bakin entry hall din Da zamudi tace”ya shureim kana ganin aunty benazir zata Iya gane ni kuwa? Saboda mommy ta fadamin tun ina jaririya ta 6ace ba’a ganta ba” Fuskarshi dauke da murmushi yace”idan ma bata gane ki ba, da zarar anyi mata bayani zata shaidaki, zan faɗa mata cewa zeenatu ce ɗiyar uncle musa, and my wife to be” tuntsirewa tayi da dariya taji daɗin maganarshi, muryarta da shagwa6a tace”amma ya shureim ai ni banaso ka faɗa mata, wallahi kunya nake ji, ko mommy layla ma kada ka fada mata please da daddyn ku” ta faɗa tana duban face dinshi. “Ai ni nafiso suji My zeenatu, saboda a fara shirye shiryen shafa fatihar auranmu” zaro mashi blue eyes dinta tai kafin tai saurin sanya tafukan hannayenta biyu ta rufe fuskarta cikin jin kunyar maganarshi ta furta”dan Allah yaya shureim dina kada ka fada masu yanzu, nidai kunya nake ji” “Kunya kamar bafullatana, kin manta mommynki baturiya ce, daddy musa kuma Hausa fulanine, kakarmu bafullatana ce kakan mu namiji kuma bahaushe ne, Ni bansan inda kika gado Kunyar nan taki ba, a haka zamuyi aure kina jin kunyata”? Kafin ta bashi amsa, motarsu Alhaji ubaid ta ƙaraso gab dasu, bayan drivern yai parking, da sauri Dr shureim Yaja hannun zeenatu suka ƙarasa bakin motar, yakai hannu ya buɗe masu murfin back seat, a hankali ta zuro da ƙafarta dake sanye cikin takalma, ƙarasa fitowa tayi tun daga ƙasa dr shureim yake binta da kallo, wankan atamfa ne a jikinta riga da skirt, ta kashe daurin dankwalinta, yalwatacciyar sumar kanta ta sauka gadon bayanta, gyalen asaman kafaɗa ta yafa shi, idan kaganta ahaka bazaka ta6a ce wa ta ta6a yin aure ba, kamar budurwa saboda babu abunda ya canza a jikinta, dama bata ta6a shayarwa ba. Wani irin kallon so da ƙaunar ƴan uwantaka suke jefa ma juna tsakanin ta da shureim, idanuwan kowannansu ya ciko tab da ƙwalla, La66anshi na kerma ya furta sunan ta”be.. Nazir! Yar uwata rabin raina, Jinin jikina Dagaske ke ce idanuwana suke nuna min? Fashewa tayi da matsanancin kuka, gaba ɗaya ta faɗa saman chest dinshi, ya zagayo da hannayenshi biyu ya rungumeta tamkar zai mayar da ita cikin cikinshi, Zeenatu dake tsaye tana kallonsu hawaye tuni sun wanke fuskarta, tsananin tausayin benazir ne Ya kamata, Fitowa Alhaji ubaid yai daga cikin motar shida Hajiya layla, ya dauki wankan shadda, itama layla Atamfar ce ta sanya sunyi anko da benazir hatta daurin dan kwalinsu da mayafin da ta daura a kafaɗa iri dayane dana benazir, idanuwansu na akan dr shureim da benazir, sun ƙanƙame juna sai kuka sukeyi kamar waɗanda suka rasa mafaɗi a duniya, zagayawa zeeenatu tayi ta 6angaren da su hajiya layla suke koda sukayi arba da ita, Hajiya layla ta buɗe mata hannu da fara’a akan fuskarta take fadin”Zonan My daughter zeenatu” kamar jira take yi da sauri ta ƙarasa ta faɗa jikin Layla, rungumeta tayi sosai, tana dan bubbuga bayanta ta furta”kin ƙara girma daughter, tsawon lokaci bamu haɗu ba, Daddynki Ya hanaki zumunci da ƴan uwanki, baison kina taka wajen mu, gashi mu kuma muna ƙaunarki” ta faɗa tana raba jikinta da na zeenatu, fuskokinsu dauke da annurin farin ciki, kallon Alhaji ubaid tai”sannunku da zuwa daddy” miƙa mata hannu yai da sauri ta ƙarasa gare shi, Yai hugging dinta yana fadin”fatan mun same ku lafiya,” ɗagowa tai da kanta tana fadin”Lafiya lou daddy mu shiga daga ciki” Drivern daya daukosu Yana daga tsaye ya jingina bayanshi jikin motar, Yace”yalla6ai ku ƙarasa shiga gidan, za’a shigo maku da kayan naku” amsa mashi sukayi da toh, layla tace da su shureim ayi haƙuri adaina kukan ya isa haka mu shiga cikin gidan inyaso kun ƙare kukan naku acan” Alhaji ubaid na murmushi yace”ke ko kibarsu mana, An daɗe ba’a haɗu ba, Jini ɗaya ba wasa ba, mundai godema Allah daya bayyana mana ita da ranta da lafiyarta ubangiji Allah Ya ƙara tsare mana ita, layla da zeenatu suka amsa mashi da ameen, Gaba suka fara Yi, Ya rage saura zeenatu data ƙura ma benazir da shureim ido. Ta kwantar da kanta saman kafadarshi, yayin da hawaye masu ɗumi suke cigaba da wanke fuskarta, cikin muryar kuka take fadin”yaya shureim nayi danasanin duk wani abu daya faru arayuwata, wallahi nayi danasani mara amfani, bansan meke damunaba, hakanan na tafi nabar dangina nabar mijina, babban takaicina ƴar jinjirar dana bari cikin jini, na haura ƙafa na tafi nabarta saboda rashin hankali irin nawa, bansan meyasa na aikata hakan ba” cikin jin ƙunar rai ta ƙare maganar. Ɗaura hannunshi yai saman bayanta cikin rauni na murya ya soma magana”kiyi haƙuri benazir, wallahi ba laifinki bane, ni nasan duk rashin jin maganarki bazaki ta6a iya aikata hakan ba, Ina yi maki kyakkyawar zato, ki kwantar da hankalinki My sister” cikin kwantar da murya yake lallashinta Shessheƙar kukan zeenatu ne Ya janyo hankalinsu ga kallonta, idanuwanta sunyi luhu luhu, da mamaki akan fuskar benazir ta furta”yaya shureim a ina muka samu kyakkyawar matashiyar baturiya”? Fuskarshi dauke da murmushi yace”zeenatu ce, nasan ba lallai kisanta ba, saboda ba’ajima da haihuwarta ba ki ka tafi, ɗiyar uncle dinmu ce, ki kalli fuskarta dakyau” Farin cikine Ya lullu6e benazir, Yarinyar ta burgeta, Gata ƴar kyakkyawa da ita, miƙa mata hannu tai zonan ƴar uwata, Ina fata an fada maki wacece ni, idan ma ba’a sanar dake ba toh nidai sunana benazir, Ƙanwar dr.shureim” fashewa Zeenatu tayi da dariyar farin ciki, Hawaye nabin fuskarta. “zonan In rungumeki ajikina, Nima yau inji ɗumin ƴar uwata” jiki Na rawa zeenatu ta nufi benazir suka rungume juna kamar zasu koma mutun ɗaya Cikin shessheƙar kuka Zeenatu take fadin”Aunty benazir munyi kewarki sosai, Mommyna tana bani labarinki, najima ina son ganinki arayuwata, duk da bamu ta6a haɗuwa ba amma kullum idan nayi sallah sai nayi maki addu’a Akan Allah Ya bayyanar mana dake idan kina araye, Idan bakya araye Allah Yajiƙanki yakai rahama agareki, ashe da rabon zamu haɗu....”dakyar ta ƙare maganar saboda kukan daya cimmata, daga ita har benazir din kukan sukeyi, Kalaman zeenatu sunyi matuƙar ta6a mata zuciyata, tayi mamakin irin ƙaunar da take Yi mata, ita da bata ta6a ganinta ba, labarinta kaɗai aka bata, haƙika taji dadi mara misaltuwa, kaunar zeenatu ta shigeta, tayi fatan Ace itama ƴarta data bari tana yi mata addu’a. “Aunty benazir dan Allah kada ki ƙara tafiya kibarmu, wallahi muna kaunarki nida mommyna” sosai benazir ta fashe da kuka tana fadin”in sha Allah bazan ƙara tafiyaba, nadawo kenan zeenatu, naji dadin kalamanki agareni, ƴar uwata rabin raina” Dr.shureim Ya natsu yana kallonsu, idanuwanshi sun kaɗa jawur, hawayen dake gangarowa saman kuncinshi sai ƙara ninkuwa sukeyi. Cikin sanyin murya yace dasu’Mu shiga cikin gidan” amsa mashi sukayi da toh, hannun benazir acikin na zeenatu suka dunguma zuwa babban falon gidan. Lokacin da suka ƙarasa ciki, Alhaji ubaid da Hajiya layla suna a zaune saman sofa mai mazaunin mutun biyu, a yayin da Hajiya sarah ta zauna saman 3 sita, Alhaji musa yana daga zaune gefenta, kamar kullum fuskarshi babu annuri, kamar wanda akayiwa albishir da ranar mutuwarshi, shaddar jikinshi ta zauna mashi launin blue sky, daddadan kamshin turarenshi Ya karade hancin kowa, Hajiya sarah Lace ne ta sanya kalar shaddarshi, head dinta kalar takalman ƙafarta, sunyi kyau abunsu kamar sabbin ma’aurata Jin takun tafiyarsu yasa hajiya sarah ta ɗago tana dubansu, wani irin farin cikine ya lullu6eta ganin benazir, Jiki na rawa ta miƙe tana faman sakin fara’a fararen hakoranta tarr dasu ta nufi benazir tana fadin”ashe rai kanga rai? Benazir dagaske kece idanuwana suke nuna min? Wayyo Allahna, Idan ma mafarki nake Yi toh kada atadani abarni in tayi dan Allah” Rungume juna sukayi, Benazir ta fashe da wani sabon kukan bata ta6a tsammanin zata samu kyakkyawar tarba a wurin ahalinta ba, Tabbas sun bata mamaki tayi tunanin kamar yadda ta gudu babu wanda zai saurareta donta dawo gare su. Hajiya layla sai faman sakin murmushi take Yi ita da Alhaji ubaid hankalinsu na akan Hajiya sarah data rungume benazir, Shi kuwa Alhaji musa ko kallo bata ishe shi ba, tamkar baisan sun shigo falon ba. “Allah sarki benazir, Ashe da rabon zamu sake ganawa a duniyar nan! Tsawon shekaru sai yau Allah Ya nufa zan ƙara Yin tozali dake” ta fada tana duban benazir da hawaye suka gama wanke fuskarta Cikin shessheƙar kuka tace”Aunty Sarah nayi danasani, naji haushin kaina, naji na tsani kaina saboda komai ya faru arayuwana laifina ne, tunda nida kaina na gudu na tafi batare da nayi shawara da kowa ba, Dan Allah ku yafe min, nasan na 6ata maku rai” Idanuwan hajiya sarah tuni sun cicciko tab da ƙwalla, kasancewarta mace mai tausayi. Cikin karyayyar murya ta furta”dan Allah ki daina fadin hakan, Komai ya riga daya faru kuma ya wuce” Kafin benazir ta kuma yin magana muryar Alhaji musa ta katse masu hanzarinsu “Idan kun gama jimamin, ku ƙaraso ku zauna” cikin isa Ya furta hakan, sai lokacin Benazir ta ɗago da ido tana dubanshi, Ya haɗe rai babu annuri sam a fuskarshi, gani take kamar baiyi farin ciki da dawowarta ba. Ruƙo hannunta Hajiya sara tayi acikin nata, suka ƙarasa tare da samun wuri kowannansu ya zauna, zeenatu da dr shureim suna zaune saman lallausan carpet, Benazir kuma tana agefen hajiya sarah, ta ƙankame hannunta. A tsanake Alhaji musa Yasoma yin magana batare daya ɗago da ido ba “Da farko, Inayi maku barka da zuwa, yayana da kuma hajiya layla,’ kwa6e fuska layla tayi aranta tace”dallah jibarshi ɗan rainin wayau” Numfasawa yai tamkar bayason buɗe baki Ya furta”benazir,” amsa mashi tayi da na’am. Dawo nan ki zauna” yai maganar yana Nuna saman carpet daga gefen hannun sofa din da yake zaune, jiki asanyaye ta miƙe ta dawo inda ya bata umarni ta zauna. Kowa ya natsu yana jiran jin me Alhaji musa zaice da ita. “Meyasa kika gudu daga gidan auranki har na tsawon shekaru baki nemi kowa ba”? Kafin benazir ta bashi amsa hajiya layla tayi saurin cewa”Bai kamata kayi mata wannan tambayar ba, kodai mu da muke Iyayenta bamu tambayeta komai ba, duba da halin da tadawo gidan” Ranshi a matuƙar 6ace ya dago da ido Yana binta da matsiyacin kallo batare daya furta komai ba Sai Alhaji ubaid ne yace”wannan maganar bata shafeki ba, tsakaninshi da ɗiyarshine don haka ki daina sanya masu baki” harara ta wurga ma Alhaji ubaid”kaima ka sani bazan ta6a rufe baki na ba, akan me zai tambayeta meyasa ta tafi? Lokacin da ta gudun ya nuna damuwane akanta? Ko kuwa ya bada gudummuwar da za’a nemota ne eye? Daga zuwanmu gidanshi zai tsareta da tambaya? Dama ya kira mune don Ya tuhumi ƴar mu badan Ya tayamu murnar ganinta ba” tunda tafara zazzaga masifa hankalin hajiya sarah dana zeenatu ya tashi haiƙam, shi kanshi shureim jikinshi yai sanyi laƙwas, benazir dai ta saddar da kanta ƙasa hawaye na cigaba da wanke fuskarta. Lallashinta Alhaji ubaid Ya soma Yi, Alhaji musa kuwa sai faman jinjina kanshi yake Yi, Yama rasa bakin magana Hajiya sarah na faman yarfa hannu tace”dan Allah kiyi haƙuri aunty, idan ranki ya 6aci, nasan ba’a kyauta ba, Ni tun farko banso yace kuzo nan ba, har magana nayi mashi akan mu yakamata mu taka muje tayaku murna amma ya hanamu zuwa....” daƙyar ta ƙare maganar ganin irin kallon da Alhaji musa ke binta dashi, ba arziƙi taja baki tayi shiru Jinjina kai yaɗanyi kafin ya ɗaura da cewa”Allah Ya huci zuciyarki Hajiya layla, Naji bazan ƙara tambayarta ba,” tayi mamakin jin abunda yace, har saida ta kalli cikin idonshi, murmushin gefen fuska yasakar mata afakaice, kafin Ya maida dubanshi ga benazir”ina yi maki barka da zuwa My daughter, naji daɗi da kika yi tunanin dawowa gida, ki kwantar da hankalinki, kuma ki share hawayenki, abunda ya faru ya riga daya wuce” Ajiyar zuciya benazir tadan sauke, cikin sanyin murya ta soma magana”nagode uncle, sannan idan na 6ata maka rai, kayi hakuri, nasan komai ya faru laifinane, dana kama hanya na tafi” Lumshe idanuwanshi yadanyi kafin ya waresu akan fuskarta”kada ki damu ni ban ruƙe ki araina ba, kawai dai banji dadin guduwar da kikayi bane na tsawon shekaru batare da kin tuntu6emu ba, amma yanzu tunda kin dawo da ranki da lafiyarki falillahil hamdu, sai dai fatan Allah ya kyauta gaba, In sha Allah zanyi ƙoƙari dan ganin na inganta maki rayuwarki, duk wani abu da kike buƙata ki sanar dani zanyi maki shi, kada ki ƙara yunƙurin guduwa saboda muna buƙatarki, zaifi ki sanar damu idan ma wani abune ya 6ata maki rai a tsakaninmu zamu Iya sama maki solution, Ina fata kina jina” Ɗaga mashi kai tayi alamar eh, lamarin Alhaji musa ya ɗaurewa hajiya layla kai, bata ta6a tsammanin ya iya tsara kalami irin haka ba, hatta Alhaji ubaid yai mamakin yadda ya sakar ma benazir fuska yana yi mata magana cikin lallami, aranshi ya ayyana wata’ƙil tsananin tausayinta ne Ya kamashi, yaji dadin hakan, hankalin hajiya sarah ya kwanta dana zeenatu, sai faman sakin murmushi suke Yi, haka zalika dr.shureim shima murmushi ne akan fuskarshi. “In sha Allah uncle bazan ƙara yunkurin guduwa ba, duk runtsi duk wuya zan zauna atare daku, nima nayi danasanin abunda na aikata, Gyaɗa kanshi yai, Hajiya sara tace”tun ɗazu fa na sanya masu aiki sun shirya maku lafiyayyan abinci, yakamata muje muci kada ya huce” da fara”a akan face dinta ta furta hakan, Miƙewa sukayi atare suka dunguma zuwa dining room, benazir ta girgiza da ganin daular uncle musa, Gidan Ya tafi da imaninta. Saman dining chairs suka zazzauna, ga kayan abinci an jera masu saman table,” Tani da lami ne suka zo domin yin serving dinsu, Bayan sun gaishe da alhaji ubaid da hajiya layla, suka soma zuzzuba ma kowannansu abunda yake ra’ayin ci, hankalinsu kwance suke ci baka jin sautin komai saina ƙarar cokulansu. Jefi jefi zeenatu take satar kallon benazir da zarar sun haɗa ido sai ta sakar mata murmushi, Ta fahimci yarinyar ba ƙaramin so take Yi mata ba, Dr shureim na kallonsu, shima murmushine akan fuskarshi, Hajiya layla dai taƙi sakewa, itafa har yau har gobe bazata ta6a yadda da alhaji musa ba, gani take yi kamar akwai wata manufa atare dashi, abincin ma daƙyar take cin shi” Bayan sun kammala cin abinci, Hajiya sarah ta rakasu zuwa masaukinsu da zasu zauna, Hadaddun bedrooms aka ware masu, Zeenatu ta hana benazir sakat, tsabar Iyayi hada ɗauko bargonta da pillow ta dawo down stair dakin benazir donsu dinga kwana atare, Hakan ba ƙaramin daɗi yayi mata ba, *SIR MUBARAK✊* Yana acikin dangi suna ta yin firar yaushe rabo tare da Ƴan uwanshi, Wayarshi dake acikin aljihunshi ta soma Yin ruri, kusan sau uku kiran na shigowa yana yin rejecting batare daya ankare ba, saboda hayaniyar ƴan uwan shi da suke Yin fira a tsakaninsu, a babban katafaren falon gidan, a kira na huɗune, Senate lateef dake zaune gefenshi ya ankarar dashi ta hanyar yi mashi magana ka duba wayarka tun dazu nake jin sautin ringing ɗinta, amsa mashi yai da toh, sai da ya fara curo wayar ya duba sunan mai kiran nashi tukunna ya mike yai masu sallama Ya nufi ƙofar fita daga babban falon, bayan ya fitone Ya dakata da yin tafiya, Yabi kiran da aka yi mashi, bugu ɗaya aka ɗaga kiran “Major, ince dai lafiya? Naga miss call dinkane” On the other hand major yace”yalla6ai yaron nan na wurinka jazz Ya fita daga gida Yanzu haka da nakeyi maka magana munbiyo bayanshine muna asaman titi,” Cikin saurin murya sir mubarak yace”gani nan zuwa, kubi a hankali kada ku bari yaganku yaron wayau ne dashi, yanzu zamu biyo diddiginku” tunkafin maijor ya amsa mashi yai saurin yin rejecting call din, Ya dannawa driver dinshi Kira bugu ɗaya ya daga”Ina jiranka abakin entry hall na gidan baba, kazo da mota ka daukeni” Ya ƙare maganar tare da kashe kiran, Jikin shi har tsuma yake yi fatan shi Allah ya basu nasarar kama jazz don ganin menene yake aikatawa, Badajimawa ba baƙar mota ƙirar Range rover ta shararo da matsakaicin gudu bata nufi ko’ina ba sai bakin entry hall adai dai nan Tiger Yai parking dinta, Jiki na rawa sir mubarak Ya buɗe front seat na motar ya shige tare da bashi umarnin su tafi, reverse yai kafin ya karya kwana Ya nufi tanƙameman gate din fita daga estate din dake a kewaye da jami’ai, tunda suka hango sir mubarak ta tagar motar basu yi gigin dakatar dasu ba, kaitsaye motarsu ta haura saman titi, da gudun gaske tiger yake driving dinsu tamkar zasu tashi sama, sir mubarak yai amfani da phone dinsa wurin bin diddigin su major, cikin sa’a suka samo location din da suke, dare ne tamkar da rana saboda hasken street light daya gauraye ko’ina, hanyar da suka biyo kwata kwata babu mutane, sababbin gine gine ne a unguwar, wani ginin ma ba’a kammala shi. Rage gudun motar tiger yai ta hanyar glass din motarsu suka hango motar major tana tafiya a hankali ga dukkan alamu sun ƙaraso inda dr jazz Yake shiyasa suka rage speed din motar, bayan major yai parking din motarsu, kusan atare suka fito shida wani matashin saurayi dukansu suna asanye cikin kakinsu na sojoji, daga bayan motarsu Tiger yai parking din tasu motar, fitowa sukayi atare shida Sir mubarak, koda su Major sukayi arba dashi a hanzarce suka buga ƙafa tare da sara mashi, Jinjina masu kai Yai yayin da yake bin gine ginen da kallo Ya ce”ina ku ka ga jazz din Ya shiga”? Ya jefa masu tambayar cikin ƙagara da sonjin amsarsu. Major yace”Wancan gidan mai jan gate Ciki Ya shiga” yai maganar yana nuna wani katafaren gida, Da sauri Sir mubarak Ya nufi gate din, Major da Army din da suke atare kowannansu Ya zaro bindigarshi, shima Tiger Ya curo tashi pistol din, gefe da gefen sir mubarak Suka Jera sun saita bindugunsu saboda tsaro gudun kada akawo masu hari tunda basusan adadin miyagun da yake mu’amala da su ba, Cikin sanɗa suke tafiya suna bin ko’ina da kallo, ta ƙofar jikin gate din da aka bari abuɗe suka shiga, babu kowa abakin gate din tamkar anyi shara, Sir mubarak yace”Anya major akwai mutane acikin ginin nan? Naji shiru babu motsin komai, kodai kunyi kuskurene”? Girgiza kai major yai”Yalla6ai tabbas cikin ginin nan ya shigo, ba mu yi kuskure ba, akan idonmu ya fito daga cikin motarshi Ya buɗe gate kafin Ya koma ciki Yajata zuwa cikin gida” Gyaɗa kai sir mubarak Yai”okey mu ƙarasa ciki” kaitsaye suka nufi katafaren ginin da suke tsammanin zasu samu hanyar shiga cikin gidan, adai dai bakin wata ƙofa, suka dakata A hankali Major Ya turo ƙofar cikin sa’a suka sameta abuɗe, ɗaya bayan ɗaya suke shiga, Hadadden palour ne An ƙawata shi da furniture, ga sanyin A.c ta ko’ina mai ratsa fatar jikin mutun. Sunyi mamakin ganin babu kowa a palourn, ko motsin mutun babu, daga cikin falon akwai bene da zai kai mutun up stair, yanke shawarar haurawa saman benan sukayi, Cikin sanɗa suke tafiya kowa ya saita bindigarshi saboda tsaro, a second floor suka dakata da yin tafiyar suna bin ko’ina da kallo, ƙofofin ɗakunane ta ko’ina, Sam sun kasa motsawa saboda sunfara kokwanton anya akwai mutane agidan Tiger yace”shirun yayi yawa, kada fa ace tarkone aka ɗana mana don mu afka” Major yace”ai shi soja da kasada akasanshi, Idanma tarkon ne suka shirya mana to bamu bane zamu rufza aciki ba, sune zasu afka, wata’kil watan tonuwar asirin su ne Ya kama” Sir mubarak Ya natsu Yana sauraronsu, ya rasa madafa sam bayason suyi kuskuren shiga gidan mutane, don ya fara kokwanto. Army yace”yakamata mu fara dudduba ɗakunan nan wata’ƙil mu same shi aciki” Ya furta hakan tare dakai hannu Ya buɗe ƙofar ɗaki Ɗaya, karaf idanuwanshi suka sauka akan matasan Ƴan matan dake akwance saman bedmattress, cikin shiga ta kayan bacci”a matuƙar ruɗe ya juya yana kallon Sir mubarak Ya furta”yalla6ai ƴan matane kwance saman gado, Anya kuwa bamuyi kuskure ba”! Matsawa sukayi zuwa bakin ƙofar da Army yake a tsaye, kowan nan su Ya leƙa Sun yi mamakin ganin kyawawan ƴan mata kwance suna sharar baccinsu farare tass dasu kamar jinsin larabawa. Rai amatuƙar 6ace sir mubarak ya dubi Major”kace min nan jazz ya shigo to yana ina? Waɗannan ƴan matan alamace dake nuna cewa Gidan wani ne muka faɗo” Tuni major yasha jinin jikinshi, Muryarshi adabarbarce ya furta”yalla6ai wallahi da idona naganshi Ya shigo gidan nan, Ga army nan ka tambaye shi, ai tare dashi muka shigo, kuma shima yaga jazz din” Yai maganar yana nuna army da hannun shi Kallon Army sir Mubarak Yai, da kakkausar murya ya furta”idan har kukasa naji kunya wallahi zakuji ajikin ku ne” hankalinsu ba ƙaramin tashi yai ba, Jin abunda yace masu, Guntun tsoki Yaja tare da juyawa da niyar Ya fuce daga gidan, kwatsam ba zato ba tsammani, kunnuwansu suka soma Jiyo masu shessheƙar Kukan mace cikin murya mai ƙaraji take fasa ƙara tana fadin”Bana so! Ka ƙyaleni Nace maka banaso, Ni ka ƙyaleni, ka sake ni ka rabu dani....” sautin gigitacciyar ƙarar data fasa gaba ɗaya Ya cika ginin, Kallon juna sojojin sukayi kafin da gudun gaske suka nufi Hanyar da suke jiyo sautin kukan Yarinyar, Sir mubarak kamar zai yi tuntube, cikin zafin nama suka haɗa ƙarfi wurin bangaje ƙofar ɗakin, A tsiyace ƙofar ta bude, Hankalin sir mubarak Idan yai dubu to ya tashi, A matuƙar gigice sojojin suke kallon abun da ke faruwa, Lamarin yai matuƙar ɗaga hankulansu, musamman Sir mubarak Ya gaza yadda da abunda idanuwanshi suke nuna mashi, Tuni zufa ta soma wanke fuskarshi, Sam baiji motsin shigowar mutane ɗakin Ba, Ya duƙufa akan abunda Yake aikatawa, Rigar shaddar shi da wandonshi gaba daya suna asaman floor, Singlet ce kaɗai a jikinshi sai gajeran wando Fari, Ya haɗa uban gumi, matashiyar yarinyar daya danne saman gado sai kuka take Yi, tana bugun bayanshi da hannayenta, A wahalce take harba ƙafafuwanta cikin fitar hayyaci kamar ranta zai fita, ta gama galabaita, tuntana kukan neman agaji har muryarta tafara disashewa, wani irin kukan kura sir mubarak Yai cikin zazzafan taku Ya kutsa kai Cikin ɗaki, da hannayenshi biyu ya damƙo wuyar singlet din Jazz da ƙarfin gaske Ya wurgar dashi kasa gaba ɗaya ya kife kanshi ya daki tiles, Jiki na kerma ya ɗago yana dubansu ɗaya bayan ɗaya kafin ya tsayar da idanuwanshi akan fuskar Sir mubarak dake tsaye kanshi tamkar mayunwacin zaki, hankalinshi yai matuƙar tashi da ganinsu duk yabi ya ruɗe ya susuce, jikinshi ya hauyin kerma, sai faman zazzare idanuwanshi yake Yi, Muryarshi na kakarwa ya furta”daddy....” bai ƙarasa maganar da zaiyi ba, Sir mubarak Ya damƙo wuyanshi ya ɗago dashi tsaye cikin rauni na murya ta wanda ya karaya yake fadin”Jazz ka kasheni, Ka cuceni, dama abunda kake aikawata kenan? Ƴan mata kuke tarawa acikin gida, donku lalata rayuwarsu sannan ku kashe su? Nasha kama ka kanayin waya kana fadin kaji ashe mutanene kajin, Inna lillahi wa’inna ilaihirraji’un” cikin jin ƙunar rai yace”Wallahi baka isa ka ɗaura min hawan jini baa, Kafin ka kasheni ni zan fara kasheka don ubanka, Mugu azzalumi fasiƙi, Jazz ka bani mamaki, ka cuce ni kuma ka cuci mahaifiyarka,’ Cikin shessheƙar kuka Sir mubarak Yake furta maganar, Ya shaƙe wuyan Jazz sai faman mutsu mutsu yake Yi, don ya ƙwaci kansa. Yayin da sojojin suke a kewaye da gadon da yarinyar take, duk tabi ta tsorata jikinta sai kerma yake Yi, short gown ce a jikinta, yalwatacciyar baƙar sumar kanta duk ta rufe gefe da gefen fuskarta, tamkar wadda tasha gudu sai faman yin haki take Yi. Sautin ƙarar da jazz Ya fasane Ya janyo hankulansu ga duban shi, wani irin radadin azabane Ya ziyarce shi sakamakon buga kanshi da sir mubarak Yai jikin Mirror din dakin, gaba ɗaya madubin Ya zube, Jini Ya wanke fuskar Jazz hatta gaban farar shirt din jikinshi Yayi ca6a ca6a da jinin shi, daddafe kanshi yai da hannu bibbiyu cikin mawuyacin hali Yake sambatu “Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un! Daddy ka kashe ni, Na shiga uku na bani na lalace, daddy ka rabani da rayuwata” Yarinyar dake zaune saman gadon, ganin yadda suka raunata shi yasa ta fasa ƙara da ƙarfi ta furta”yaya Jazz, Wayyo Allah na kun kashe min shi, mugaye azzumai baiyi maku laifin komai ba amma kuna cutar min dashi” Da gudun gaske ta duro daga saman gadon ta kife ƙasa, sam babu natsuwa atare da ita, da rarrafe ta ƙarasa gabanshi, Ta sanya hannu biyu ta ɗago dakanshi ta daura saman laps dinta, Cikin shessheƙar kuka take fadin”Wallahi Allah bazai barku ba, Ku baku da burin daya wuce ku cutar da rayuwar waɗanda basu ji ba basu gani ba, Sai Allah ya saka mashi, ku dukanku sai kun shiga wuta” ta fada tana nuna su da yatsan hannunta, kallon juna sojojin sukayi, sunyi matuƙar girgiza da jin kalaman Yarinyar, sun fara kokwanton Anya kuwa Zargin da sukeyi mashi gaskiya ne? Tayaya yarinyar da ake cutar da rayuwarta, kuma take fada don an ta6a mutumin dake ƙoƙarin rabata da mutuncinta!! Fashewa tayi da kuka Hannayenta tuni sun 6aci da jinin dr jazz tana kuka tana ambaton sunanshi”yaya jaz dan Allah kada ka mutu kabarmu, wallahi idan ka mutu nima saina kashe kaina” Zuciyar sir mubarak ce ta soma harbawa da ƙarfin gaske, Jiri ya soma ƙoƙarin kwasarshi, Gaba ɗaya ya gama rikicewa, Hankalinshi atashe Yake kallon Kwalaben alluran dake ajiye saman bedside drawer tare da sirinji, hada magunguna, Adaddafe Ya nufi drawer din da niyar Ya duba kwalaban don ganin na menene, sautin ringin wayar Jazz ne Ya dakatar da shi, da sauri ya daura rinannun idanuwanshi inda yake jiyo sautin daga cikin aljihun wandon shaddarshine, Major ne yai saurin daukar wandon Ya binciko wayar cikin aljihun, Ya miƙa ma sir mubarak, yatsun hannun shi na kerma ya ruƙe wayar, batare daya duba sunan mai kira ba Yai picking call din Ya sanya kiran handsfree. Sautin muryar mutumin dayaji tayi matuƙar gigitar dashi, har baisan sa’adda Ya saki wayar jazz ta fadi saman floor, sojojin dake atare dashi duk sun sha jinin jikinsu, kallon kallo suka soma Yi a tsakaninsu, cikin matsanancin tashin hankali, sautin shessheƙar kukan matashiyar ya cika dakin, dr jazz tuni Ya jima da sumewa. *EX-PRISONERS💔* Gaba ɗayansu sun hallara a dining room, domin cin abincin Dinner dinsu, mutun ɗaya ne ke babu acikinsu, Yana can dakin shi, mazan suna fuskantar matan, sunyi shiga kala ɗaya wandon jeans da farar shirt,matan kuma dogayen rigunane a jikinsu, Aunty ummi ce kaɗai ta banbanta dasu, riga da skirt ne ajikinta sun matseta, shape din jikinta Ya bayyana muraran, babu mayafi akanta, sa6anin su Batul da sukayi rolling veils. tunda suka zauna Unaisah ta kasa samun sukuni, yanayinta tamkar na mara lafiya, sai faman jujjuya spoon take Yi acikin plate din gabanta, da ke shaƙe da abinci, damuwar duniya ta isheta, sam babu sukuni akan fuskarta, A hankali ta ɗago da ido tana duban fuskokin Ƴan uwanta, tun daga kan Sajeed dake fuskantar Azeeza, suna cin abinci suna kallon juna, har zuwa kan Haris dake fuskantar Hannah, kafin ta kawar da idonta daga kansu ta maida su kan fuskar Naufal da javed, sun natsu suna cin abincinsu, hasken musulunci ya fara shigarsu, komai nasu cikin natsuwa suke yin shi, mayar da idanuwanta tayi akan face din jamimah, bakinta duk ya 6aci da maiƙo, ta samu cinyar kaza saici take Yi kamar tsohuwar mayya, ta cinye tsokar naman, Ƙashin take gwaigwaya kamar babu sauran naman alhalin gashinan saman tray guda aka jera masu chicken legs, girgiza kai tayi kafin ta mayar da dubanta kan Batul dake gefenta, ita dai duniya babu abunda ke burgeta irin taliyar indomie, tun ranar farko data fara cinta, kullum ne in zasu ci abinci saita ci ta, sam bata gajiya, da hannu take nannaɗota kafin ta tura abaki, rantane ya raya mata ana kallonta, dai dai time dinda ta tura taliyar abaki ta ɗago da ido suka kalli juna ita da Angel, da sauri ta haɗiya taliyar, cikin muryar raɗa ta tambayeta lafiya take kallonta? Ko tayi ƙauyancine”? Girgiza kai Angel tayi babu komai kawai burgeni kikeyi idan kina cin noodles da hannu” Gyaran murya ummi tayi masu atare suka ɗago suna kallonta. “Unaisa tun ɗazu na lura kamar bakya jin daɗi, meke damunki ne”? Murmushin yaƙe ta sakar mata”babu komai aunty ummi, ko kinga wani abu ne” ɗaga mata gira tai”ƙwarai kuwa, tun da gashinan kin kasa cin abincinki” Kafin unaisa ta ƙara furta wani abu, Muryar Haris ta katse su “Kodai Danish bashi da lafiyane? Tun jiya da rana ban ƙara ganin ya leƙo waje ba, naso naje na duba shi sai dai karatu Ya mantar da nayi yin hakan” Cikin nuna damuwa Sajeed yace”wallahi yana araina, tun ɗazu da muna awurin kar6ar karatu nake ta tunaninshi, bansan dalilin dayasa baya son zuwa cikin mu cin abinci ba, naga dazu da rana ke kika kai mashi lunch dinshi a dakin shi” ya faɗa yana nuna Unaisah da spoon din hannunshi. Naufal Yace”to me zai hana mu tashi muje ɗakin nashi mu duba su? Ni abunda ke damuna da danish baya son sakewa cikin mutane” Yai maganar fuskarshi dauke da damuwa. Javed yace”ai halinshine tun fil azal, kaima kasan Danish bai cika son zama cikin mutane ba, baison surutu kuma baison ana kallon shi” Gyaran murya Ummi tai masu, Hankalinsu Ya dawo kanta sun natsu suna jiran jin me zatace “Koda ace halinshi ne hakan bai kamata ku ƙyale shi ba, cos barinshi acikin ɗaki zai Iya haifar mashi da wata damuwar, duk da naga Unaisah tana ƙoƙarin dubashi, amma a ƙalla yakamata kuma kuna zuwa wurinshi kodan ku dinga ɗebe mashi kewa, kafin zuwa lokacin da zai saki jikinshi, nasan rashin sabone ke damun shi” Jinjina kai sukayi alamar gamsuwa da bayaninta, Sajeed yace”ku tashi muje dakinshi Inyaso sai mu tafi da kayan abincin mu ƙarasa ci acan” Yai maganar tare da miƙewa, da sauri Unaisa tace”a’a basai mun tafi mu duka ba, Ku zauna ni zanje in taho da shi” amsa mata sukayi da toh, da sauri ta miƙe ta nufi ƙofar fita daga dining room din Miƙewa Batul tayi Ummi tace Ina zuwa? Cikin sanyin murya tace ina so zanbi Unaisah ne” “Ki koma ki zauna, ai tace zasu dawo atare dashi ko”? Amsa mata tai da toh jiki asanyaye ta koma ta zauna. Shiru suka ɗanyi, abincinma sun dakata da cin shi, hakanan suke jin zuciyoyinsu na bugawa, Jemimah kadaice ke cin abinci ta cika masu kunnuwa da sautin taunar abincinta, da gangan take yi duk don ayi mata magana. Harara Azeeza ta watsa mata”dan Allah ya isa haka, ba zaki Iya ci a hankali bane”? Hanna tace”ki daina wahalar da bakinki, dagangan take yi duk don ayi mata magana” tuntsirewa tayi da dariya tana fadin”Eh din kuma gashi kunyi min maganar ba” girgiza kai ummi tayi fuskarta dauke da murmushi take dubanta, hankalinta kwance take yin magana. Kallon da naufal ya jefa matane yasa tai shiru tana ƴan ƙunƙuni. “Kuna burgeni, gaba ɗayanku” ta fada tana nuna su da spoon din hannunta. Batul tace”aunty ummi, kina nufin kina sonmu”? Jinjina mata kai tayi”haka nake nufi,” murmushi su naufal suka saki jin abunda tace, Parveen na faman siɗar hannu tace”Aunty ummi ke baki haifi ƴa’ƴa bane, kamar yadda daddyn unaisah ya haife ta? Ko kuwa ita mace bata haihuwane sai maza”? Da mamaki Ummi ta dan zaro ido tana kallon parveen da tayi maganar, sam babu wasa akan fuskarta ita bilhakki take Yin maganarta. “Amma baki da hankali parveen, Kin manta labarin da unaisa ta ta6a faɗa mana ne? Macace take haihuwa ba namiji ba, itama Mommyntane ta haifeta ta jefar da ita cikin wannan abun kalar na toilet din gidan nan, namanta sunanshi” Batul ce tai maganar, Azeeza tace”eh kuwa hakane, Macace ta haifi unaisa ba namiji ba, to aunty ummi ke kin ta6a haihuwa”? tayi tambayar tana kallon ummin america wadda mamaki da al’ajabi suka cikata, sai kallonsu take Yi ɗaya bayan ɗaya, sajeed Ya duƙar da kanshi ƙasa sai faman sakin murmushi yake Yi jin wautar parveen. “Aunty ummi kinyi shiru baki ce komai ba, kina ta kallonmu” Hanna ce ta jefa mata tambayar, ta ƙura masu ido tana binsu da kallon mamaki, “wai kuna nufin bakusan komai ba, game da zamantakewar aure? Atare suka haɗa baki wurin furta”Aure kuma”? Gudun kada suyi wata 6aran 6aramar yasa Sajeed yin saurin cewa”aunty Ummi, Yakamata mu maida hankali akan abunda muke Yi yanzu,” Ta6e baki taɗanyi kafin ta furta”okey, “ ta fahimci baison maganar dama ta lura yafi su hankali shida Unaisah, bata ta6a ƙagara da sonjin labarinsu ba sai yau, tabbas tana son tasan tarihin rayuwarsu! Ya akai har suka kai wannan shekarun basusan komai dangane da zamantakewar aure ba? batun Yauba ta lura da ƙarancin wayewarsu, kamar babu ƙwalwa akansu, basu iya komai ba, In banda cin abinci da kwanciya bacci sunfi ƙwarewa a 6angaren nan. _(Ummin america batasan su wanene prisoners ba, Mutanan da suka juri rayuwar kulle tun suna jarirai, basu ta6a ganin hasken rana ba, dare da rana basu da abunyi daya wuce idan ankawo masu abinci sau ɗaya suci sai kuma idan lokacin baccin su Yayi su kwanta, badan Allah Ya ƙaddara zuwan unaisah kurkukun ƙaddara ba, da kuwa abunda zasu aikata sai yafi hakan saboda su din tamkar baƙine a duniyar mutane, basusan komai ba, unaisah itace ta wayar masu da kansu dangane da mutanan duniya da wasu abubuwan da suka shafi rayuwar ɗan adam shiyasa ma har suke Iya sakin jiki suyi rayuwa acikinsu)_ Shin meya faru bayan Unaisah ta fita daga Dining room? Cikin sauri ta nufi upstair, tunkafin ta ƙarasa ƙofar ɗakin danish ta dinga jin faɗuwar gaba, tamkar zuciyarta zata faso ƙirjinta, jiki na rawa ta nufi ƙofar room dinshi, zura ƙafarta keda wuya cikin ɗakin, taga babu kowa wayam har saman gadonshi babu mutun, sai faman baza ido take Yi tana faman ambaton sunanshi tamkar makoshinta zai 6allo”Danish! danish! my Man! Kana ina”? Shiru babu alamun zai amsa mata, ƙofar toilet dinshi ta tunkara lokaci ɗaya taji sautin gurnaninshi mai matuƙar firgitarwa ya cika ɗakin, cikin jin faɗuwar gaba ta sanya hannayenta biyu da ƙarfi ta ingiza ƙofar ta buɗe, tun daga bakin ƙofar toilet din ta ci karo da singlet dinshi, A hankali take bin ko’ina da kallo har tayi nasarar cin karo dashi kwance acikin kwamin wanka, wanda ke akewaye da glass, ya ƙunshe kanshi cikin kwamin, jikinshi sai kerma yake yi, faɗawa cikin toilet din tayi, Cikin sanyin murya take fadin”My man meke damunka? Meyasa kake yin gurnani? Baka da lafiyane” idanuwanshi dake a lumshe ya buɗesu sun kaɗa jawur dasu tamkar an wanke ƙwayar a cikin jini, Hankalinta ba ƙaramin tashi yai ba, sam bata damu da yanayin da zata riske shi ba, Jiki amace ta shiga inda kwamin yake ta zuƙunna agabanshi tana dubanshi, fatarshi tayi wani irin haske naban mamaki, Ya cika kwamin da ruwa mai sanyi, amma saboda tsabar zafin jikinshi yasa ruwan ya koma na zafi. Idanuwanta tuni sun cicciko da ƙwalla muryarta na rawa ta furta”My man dan Allah kayi min magana meke damunka? Meyasa ka shigo toilet ka kwanta cikin bathtub”? Ta faɗi hakan ne donta fahimci ba wani uziri bane ya shigo dashi toilet dinba, saboda bai cire short dinshi ba, Ahaka ya shiga cikin ruwan duk don ya sassauta zafin da jikinshi yai mashi. Da wata irin kakkausar murya ya furta”Kiyi nesa dani, zan iya cutar dake, bani bane, Ki tafi ki ƙyaleni, bana so in ta6a lafiyar jikinki” zazzare idanuwanta tayi waje tamkar ƙwayar idanuwan zasu faɗo ƙasa, muryarta adabarbarce ta furta”me..meyasa kace haka danish? Idan bakai bane to wanene? Nashiga ukuna! dan Allah kadaina furta waɗannan kalaman, Ni nasan bazaka Iya cutar.....” kasa ƙarasa maganar tayi sakamakon ganin sa6ar macijin dake tsastsafo mashi saman fatar wuyan shi, Kafin ƙyaftawar ido danish ya rikiɗa ya zama Giant snake fari sol, Jikinsa yana da tsayi da kauri, mai santsi, Ya nannaɗe kanshi cikin kwamin wankan, Wani irin narkeken maciji danƙareran gaske yana da doguwar jela da siraran harshe, tsabar firgici da ruɗanin ganin abunda bata ta6a ganiba Ya hanata motsawa, jikinta ya hauyin kerma zufa ta wanke fuskarta, ko amafarki bata ta6a ganin mutun ya rikiɗa ba sai yau da Allah Ya nuna mata Danish ɗinta Ya canza halittarshi zuwa maciji, girgiza jikinshi yai nan take kwamin wankan da yake acikin shi Ya tsastsage Ya tarwatse, Ya faɗo ƙasa, aikuwa da gudun gaske Unaisah ta fito daga dakin, ta fasa razananniyar ƙara, tana gudu haɗi da yin tuntu6e, a matuƙar gigice ta fado saman bene, Mayafin kanta tuni yajima da barin jikinta, Sumar kanta duk ta rufe fuskarta, cikin tashin hankali take tattaka matakalar benan, tana kuka haɗi da ambaton sunan ƴan uwanta Adai dai lokacin Chief Owais Yana saukowa down ta cikin glass elevator, ya kimtsa cikin Dark jeans, daga sama ya sanya button-down shirt, yayin da ƙafafuwanshi ke asanye cikin patent leather shoe, gefenshi Big guy ne hannunshi ruƙe da car key, karaf idanuwan big guy suka sauka akan unaisah dake Faman zumbula gudu tana tunkaro down, ta cikin glass elevator din yake kallonta, kafin yai yunƙurin buɗe baki Yai magana, unexpected danƙareran macijin Ya kunno kai daga ɗakin ya daka tsalle Ya haura ta saman handrail din benan Ya rigata saukowa ƙasa, da buɗar bakinshi sai cewa yai”yalla6ai anya ban fara samun matsalar gani ba kuwa? Kodai tsufane Ya fara kamani”? THE GIANT SNAKE😳🔥 Tamkar Chief Owais bai ji me big guy yace ba, Hankalinshi baya akanshi, har saida Ya furta”Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un! yalla6ai maciji nake gani, gashi can Yana tafiya”a matuƙar ruɗe big guy yai maganar, sai lokacin Chief owais Ya ɗaura idanuwanshi kan narkeken macijin dake ta faman jan jiki yana bin floor, Lamarin yai matuƙar ɗaga mashi hankali, tsantsar mamaki da al’jabi ne suka kama shi, Fitowa sukayi daga cikin elevator din tamkar a mafarki suke kallonshi sun gaza motsawa, tsabar ruɗi Yasa Unaisah ta rasa inda zata tsoma kanta, Hannayenta bibbiyu ta ɗaura saman kanta ta ƙware murya da ƙarfi ta furta”wayyo Allah na, nashiga ukuna! danish dina ya koma maciji, dan Allah ku taimaka min” sautin muryarta ya karaɗe ko’ina, hatta su Ummi dake a dining saida suka Jiyota, aiko Da gudun gaske suka soma fitowa daga dining room din, Hankalinsu a matuƙar tashe suka ɗaura idanuwansu akan fuskarta kafin wani yai yunkurin tambayarta lafiya meya faru, Giant snake din Ya daka uban Tsalle Ya haura ta ƙarafunan jikin bene Ya kurɗaɗa hawa Na uku Yabi jikin bango yaci gaba da tafiya ga dukkan alamu hanya yake nema. Tsabar firgici da tsorone Ya kama su Batul, Azeeza tuni tajima da silalewa ƙasa ta sume, Ummin america jikinta sai kerma yake Yi, tamkar wadda sanyi ya kama, batul kuwa zufa ce ta soma tsastsafo mata, Parveen tuni ta saki fitsari a cikin wando, Jikin jemimah na kakarwa ta ƙanƙame naufal ta fashe da kuka tana fadin”mun shiga uku, wannan katon abun menene, Hankalin kowa ya tashi, da rarrafe Hannah ta lalla6a ta 6oye ƙarkashin dining table. Unaisah dake atsaye Jiki ba ƙwari sai kuka take Yi tamkar ranta zai fita, Cikin zafin rai take Fadin”Danish ne ya zama maciji dan Allah ku taimaka min banaso wani abu ya same shi, za’a iya cutar dashi nasan bakowa bane zai yarda cewa mutum ne Ya rikiɗa” Girgiza kai Gabriel Yai, Iduwanshi akan macijin La66ansa na kerma ya furta”taya haka zai yiwu? Danish ya zama maciji? Ko a tarihi ban ta6a ji ba”! Fashe masu tayi da matsanancin kuka”wallahi shine akan idona Ya canza halittarshi, ina maku magana kunƙi ku fahimceni, yakamata muyi wani abu akai danish zai Iya komawa prison” tana magana Hawaye nabin fuskarta, shatun Jijiyoyin wuyanta sun fito ruɗu ruɗu saman fatarta,gana saman goshinta. Chief Owais yayi tsaye a yayin da yake bin macijin da kallo, babu alamun tsorata ko firgita atare dashi, sai dai tsantsar mamaki da al’ajabi da ruɗanin da suka kamashi, big guy Har ya yunƙura zai zaro bindigar daya soke a waist dinshi Chief Yai saurin dakatar dashi ta hanyar ɗaga mashi hannu, A hankali Ya furta”Don’t shoot him! Can’t you hear what she’s saying? Zufa nabin fuskarshi yace”yalla6ai zai iya cutar damu, Maciji ne fa kodai baka ganshi bane”? Batare daya dube shi ba yace”naganshi” Gaban sune yai mugun faɗuwar ganin yadda macijin Ya haura saman taga ya faffasata Gaba ɗaya glass din Jikinta Ya zazzago ƙasa, Jami’in dake kula da cctv footage din gidan ne suka watso da gudun gaske Cikin shiga ta kakinsu, hannunsu ruƙe da manyan bindigu, kafin owais yai yunƙuri dakatar dasu tuni sun Haura upstairs, sai dai kafin suyi yunƙurin kai mashi hari, Ya daka uban tsalle Ya fado saman floor na down stairs Yabarsu atsaye can saman third floor kamar sakarkaru, Hankalin Unaisa Idan yai dubu toh Ya tashi, Agigice ta fasa ƙara tana fadin”kada ku harbeshi! Ba maciji bane mutunne! Ɗan uwanmu ne danish, dan Allah na roƙe ku kada ku kashe mana ɗan uwanmu, wayyo Allah na Ya Allah ka kawo mana dauki” Chief Ya kasa buɗe baki Ya dakatar dasu daga yunƙurin harbin shi da suke Niyar yi, Tuni sun saita shi, Kusa atare suka fara Sakar mashi alburishi, tamkar baisan sunayi ba, saima nannaɗe kanshi da yai a tsakiyar falon, Jikin ummi na rawa ta dinga ingaza su batul cikin dining room, da gudu sajeed dasu naufal dukansu suka koma dining din, har zata rufe ƙofa Sajeed Yai saurin furta Azeeza tana awaje, fitowa yai jiki na 6ari ya cuccu6i azeeza ya shigar da ita dining room din, Ummi taja kofa ta datse, duk da haka hankalinta bai kwanta ba, zufa duk ta wanke fuskokinsu, parveen kusan sau uku tana sakin fitsari awando, ta jiƙe sharkaf, bakinta cike da donut data tura takasa ƙarasa haɗiyeshi, kowa fa yasha jinin jikinshi. Da kakkausar murya ɗaya daga cikin jami’an isod dake acan third floor Ya daka ma Unaisah tsawa haɗi da furta”ki matsa daga nan, Ki koma cikin ƴan uwanki” Fashewa unaisa tayi da kuka tana fadin”wallahi babu inda zanje, saidai ku haɗa dani ku kashe, Nace maku ɗan uwan mu ne ya rikiɗa ba yin kan shi ba ne” Muryarta adisashe ta ƙarasa maganar, sam bata lura da chief Owais ba saboda bata acikin hayyacinta, tayi tsaye tana faman yin shessheƙar kuka, Umarni Chief Yaba big guy”ka kawar da ita daga gabanshi” cikin jin faɗuwar gaba Big guy ya nufi wurin Unaisah, kafin ya ƙarasa macijin Ya warware jikinshi daga nannaɗewar da yai, da wani irin sauri yake jan jiki Yana nufar ƙarshen falon inda glass door din nan take, fasa ƙara unaisa tayi har ta yunƙura zata bishi big guy yai saurin cafkota, aiko ta daddage ta gartsa mashi cizo a hannunshi azabar zafin da yaji ce tasa shi sakinta, a lokacin jami’an isod Sun watso da gudu sun sauko down Sai faman harba mashi bullets suke Yi, tsabar mamakine Yasa suka koma kokwanton macijin, da zarar harsashin ya daki fatarshi Yake faɗuwa ƙasa batare daya huɗa fatarshi ba, hakan ba ƙaramin tayar masu da hankali yai ba. Wani irin bahagon tsalle ya daka saman glass din Ƙofar, Ya faffasa shi Yabi ta ƙatuwar huɗar daya 6ula Ya dira tacan Bayan gini, da gudun gaske unaisah tabi bayanshi, tamkar zata tashi sama, sam bata acikin hayyacinta, ba ta ji bata gani ta makance, gani take kamar hanyar komawa kurkukun ƙaddara yake nema. Gaba ɗaya jami’an sunbi bayanshi aguje, Sai dai sun kasa cimmashi, unaisa tana gudu haɗi dayin tuntu6e har tafi jami’an sauri, duk inda ya nufa tana abiye dashi, sai faman ƙwala mashi kira take Yi tamkar ranta zaifita......... Moving quickly Chief Owais Ya fito daga part din, Big guy yana abiye dashi, hankulan kowannansu Ya tashi, kaitsaye suka nufi Harabar ajiye motoci na gidan, wata dankareriyar mota suka nufa, Big guy ya buɗe mashi kofar ya shiga ya zauna shima Ya zauna, yai ma motar key, sai da yakusan ƙure speed din motar tamkar zasu tashi sama tsabar yadda take yin gudu direction din da macijin yabi suka nufa............. *OBIE ESTATE🏙* *HAJIYA SARATU❤* A tsaye take gaban Dressing mirror, bata kaiga cire Swiss cord lace din Jikinta ba, babu mayafi akanta, hakan ya bayyana kitson zanan da akayi mata, fitowa pravin yai daga toilet jikinshi sanye da bathrobe fara ƙyal, da alama wanka Yai, sam bata lura dashi ba ta dai ji motsin mutun abayanta, amma dayake hankalinta ba akanshi yake ba shiyasa bata samu damar waigowa ta kalle shi ba, A hankali Yake ƙarema bayanta kallo, Kayan sun ɗanyi tighting dinta sun bayyana dirin jikinta, musamman faska faskan hips dinta. Ba zato ba tsammani taji ya kwanto da kanshi saman wuyanta, ta baya ya rungumota, ya zagayo da hannayenshi saman flat stomach dinta. muryarta tamkar tame jin bacci ta murya”pravin meye haka”? Manna mata kiss Yai saman wuyanta, “Ba tambayata yakamata kiyi ba, ɗazu ina kallonki cikin taro, Kin saki jiki sai tiƙar rawa kikeyi Alhazawan nan masu dogon gemu sun tsareki da mazuran idanuwansu sunata kallon jikinki” Ɗaure fuskarta tayi tamau, tare da sanya hannayenta biyu ta damƙi hannunshi dayake ƙoƙarin ɗaurawa saman ƙirjinta. “Kaga Bana son surutu, Yanzu na dawo cikin gidan nagaji ina buƙatar in huta,” yaƙi bari ta ƙwace kanta daga ruƙon da yai mata. “Bansan meyasa kike Yi min haka ba! Sam baki darajani a matsayina na mijinki, bakya jin shakkar fadamin kin fita ba tare da iznina ba” a faɗace ta fusge kanta daga jikinshi ta juya tana dubanshi. “Oh gidan Yaya hateem din ne saina nemi izinin ka zan shiga? Sai kace na tafi wata uwa duniya, ko kamanta ne? Acikin estate din nan gidanshi yake, na shiga wurin matarshi ne don mu ƙara gaisawa, shi kenan komai zanyi dole saina faɗa maka”? Ta faɗa tana jifarshi da harara, bawan Allah Ya tsare ta da ido yana kallonta, Idan tana yi mashi magana tamkar zata rufe shi da bugu Guntun tsoki taja”ka daina kallona, ka wani tsareni da ido kamar zaka lasheni, ni bansan meyasa kake son zama ɗaki ba kamar wani munafuki, gasu baba can a falo ka shiga wurinsu ka zauna ayi fira dakai” Shiru yai bai tanka mata ba, babu alamun zai daina kallon nata. Ta6e baki tayi”Idan baka da abunyi ni inada shi, don haka bani wuri In wuce” ta faɗa tana ƙoƙarin bi ta gefenshi da niyar ta tafi, ba zato ba tsammani taji ya damƙi damtsen hannunta, ruƙo bana wasa ba, har saida ta ɗago idanuwanta azare take dubanshi. “Kidaina yi min faɗa, bafa tsoronki nake ji ba, Ina raga miki ne saboda ƙaunar da ke atsakanina dake” har saida taɗanji gabanta ya faɗi rass, ganin yadda ya haɗe fuskarshi, kwata kwata babu annuri tamkar bai ta6a dariya ba. “Ke komai baki Iya ba dangane da zamantakewar aure? Sai kace ba mace ba? Baki Iya soyayya ba sannan baki da lokacina sai idan kinga dama zaki bani hakki na? Abu kaɗan saiki rufeni da faɗa kamar ɗan cikinki? Ko kin manta matsayina awajenki? Idan kin manta bari na tuna maki, Ni mijinki ne a ƙarƙashin ikona kike, Nafi kowa Iko dake hatta mahaifinki, Aljannarki tana a ƙarƙashin ƙafata idan har bakiyi min biyayya ba tayaya kike tunanin zaki sameta”? cikin jin ƙunar rai Ya furta hakan, maimaikon yaga nadama akan fuskarta sai gani yai ta tuntsire da dariya har fararen hakoranta suka bayyana, fisge hannunta tayi daga ruƙon da yai mata. Ta ruƙe qugu ta matsa dab dashi kafin ta soma magana”Naji abunda kace babyn baby, sai dai akwai gyara a kalamanka, bani ce nake a ƙarƙashin ikonka ba, Kaine kake a ƙarƙashin ikona, ko kamantane, agidanmu kake zaune, cin ka shan ka suturarka dama komai nice nake kula dasu, baka da wata power pravin, babu yadda za’ai nayi maka biyayya sai dai kai kayi min saboda nina cancanci hakan, Nice hula kaine ɗan kwalin, aljanna kuma ta mai rabo ce” da wulaƙanci take furta maganar, lamarin ya ɗaure mashi kai, a iya saninshi saratu tana da ilimin addini amma idan tayi wasu kalaman ba ƙaramin mamaki take bashi ba, Ƙululun bakin ciki Ya hana ya furta mata magana, idanuwanshi sun kaɗa jawur dasu, Ranshi Ya 6aci sosai a fusace Ya juya ya fuce daga ɗakin, ta6e baki tayi aranta ta ayyana”matsalarka ce koda yake laifina ne dana auri dangin kirishna, masu bautawa soyayya” ta faɗa tana dariya. ❤🤍❤ A Zazzaune suke saman tattausan carpet, ɗan ubansu zubin kafi mage Laushi dake A cikin katafaren falon gidan baba obie, daga tsakiyar Royal sofa set din falon carpet din Yake a shimfiɗe hadadden gaske, tamkar shimfiɗar sarakuna, an kewaye bakin carpet din da tuntun, asaman su dattijon arziƙi Ya ɗaura kanshi, Prime minister Hateem Yana a kishingiɗe shima ya ɗaura kan nashi saman tuntun, Basu kaɗai bane saman carpet din akwai senate lateef tare da his excellency deen da kuma His excellency abdul Razak duk sun kishingiɗa kansu saman tuntun, kowan nan su jabbiyace a jikinshi, ta obie data hateem launi ɗayane ruwan toka, hateem ya manna farin glass a idanuwanshi hannunshi na dama hadaddiyar Agogon azurface mai kyan gaske, zobenta ne a yatsun hannun shi. Jallabiyar sharafuddeen data his excellency deen launin brown ce, yayin data Senate lateef ta kasance milk colour, hankalinsu kwance suke shan firarsu, sun baro iyalansu a makwancinsu, yayin da su kuma suka haɗa majalissarsu afalo. Babban tray ne aka ajiye masu kan carpet din, Saman shi Tea pot ce mai ɗauke da green tea, ga jerin kofuna, suna fira suna shan abunsu “Baba mun cika ka da surutu ko”? Senate lateef ne Yai maganar yana duban fuskarshi. Ɗaura hannu yai saman gemunshi tamkar yana kitsa shi Yace”Ni ai banƙi kuyita surutu ba daga yau har gobe, wallahi bana gajiya da sauraronku, Ina jin daɗin ganin ku atare dani, nayi kewarku sosai” Murmushi kowan nan su Ya saki, In ka cire hateem daya lumshe idanuwanshi ga dukkan alamu bacci yake ji. “Kamar yadda baka gajiya da sauraronmu muma haka bama gajiya da faranta maka,” acewar his excellency deen lumshe idanuwanshi yadanyi hadi da jinjina kanshi His excellency abdul razak Yace”baba, akwai wata magana mai mahimmanci da nakeson Yi dakai, tunda yanzu duk mun haɗu agaban ka, Inaga Yakamata muyi anan idan ka bani dama”! Mayar da hankali obie Yai akan abdul razak”ina sauraronka” “Dangane da matasan family dinmu, bai kamata mu zuba masu ido muna kallonsu ba, yakamata kowan nan su ya fidda matar da zai aura” His excellency Deen Yace”Ni kaina abun yana damuna, wani abin ɗaure kanma Yaran tamkar basu da ra’ayin ajiye Iyali, kaga Justice namu da dr nawaz sam basu son Inyi masu zancen aure” Murmushi obie Yasaki yana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya. Senate yace”har ƙwara Ziyad, idan nayi mashi maganar aure sai kaji yace inada wannan burin baba in sha Allah nan bada jimawa ba zan fidda matar da zan aura ka tayani da addu’a Allah ya bani mace ta gari” Mai girma sharafuddeen dake sauraron yayyan nashi, hannun shi ruƙe da mug na tea da yake kur6a, da alama yana jin dadin tattaunawarsu. Deen yace”su kuwa waɗannan ba’a maganar ƴa’ƴansu, dama ance magaji mafiyi, akansu na fara shaidar hakan” yai maganar Yana nuna Sharafuddeen da Hateem. Gyaran murya sharafudden yai kafin ya soma magana atsanake”lamarin Owais namu sai addu’a, Ni bana gane kanshi, mace bata agabanshi, na ta6a yi mashi zancen aure sau ɗaya sai ce min yai baya son ya ɗaurawa kanshi nauyin da bazai Iya sauke shi ba” Murmushi kowan nan su ya saki, Obie yace”kada ku takura kanku akansu, lokacin yin auran nasu ne baiyi ba, da zarar time yayi babu wanda zan saurara acikinsu sai dai kawai suji sanarwar ɗaurin auransu a masallaci” Jinjina kai sanate Yai”baba ka kawo shawara mai kyau, mu haɗa kowan nan su da abokiyar rayuwarshi, tunda muna da ƴan mata a family namu” His Excellency abdul razak Yace”wai Ina ɗan uwa mubarak Yaje ne”? Senate lateef Ya bashi amsa da cewa”ɗazu dai muna zaune naji wayar shi na ruri har nace mashi ya dubata ana kiranshi, tun da ya fita har yanzu shiru bai dawo ba, wataƙil ya wuce gidanshi” “Mu ma yakamata muje mu kwanta, mu huta” acewar deen. Daura ido obie yai akan fuskar Hateem babu alamun Yana sauraronsu. Gyaran murya yai mashi haɗi da zungurin kafaɗarshi da hannu, firgigit Ya ware idanuwanshi Yana faman yamutsa fuska”Idan bacci kake Ji yakamata kaje ka kwanta” girgiza kai yai”a’a ba bacci nake ji ba, Ina sauraronku” da zolaya senate lateef yace”Oh, mu ka maida shashashu mun saki baki munata surutu ka kasa kunne kana sauraronmu, Wato kafi ƙarfin ka tanka mana” Mai girma sharafudeen Yace”bacci yake ji fa, ba sauraronmu yake yi ba, tun ɗazu na lura dashi, baba ne Ya farkar da shi,” ya faɗa yana duban hateem”malam ka tashi kaje wurin Iyalinka ka kwanta ka huta” Yamutsa fuska Hateem yai”Na faɗa maka ba bacci nake ji ba, idona biyu” ya faɗa yana zare mashi manyan idanuwanshi, dariya suka saki gaba ɗayansu. Kafin wani Ya kuma furta kalma, kwatsam ba zato ba tsammani, kunnuwansu suka Jiyo masu sautin fashewar glass, Baba obie Yace”kuna jin abunda nake ji kuwa? Ko dai kunnuwana ne suka jiyo mun badai dai ba” Senate yace”kamar fashewar glass, bari in duba” ya faɗa yana mikewa tsaye, karaf idanuwanshi suka sauka akan Giant snake din dake ƙoƙarin faɗowa ta ƙofar glass din wani ɗaki dake acan upstair hawa na Uku, ras yaji gabanshi Yai mugun faɗuwa, Muryarshi na rawa ya furta”inna lillahi wa’inna ilaihirraji’in!” Jin ya zabga salati yasa Sauran ƴan uwan nashi sukayi saurin miƙewa, tare da daura idanuwansu saitin inda senate Yake kallo, tashin hankalin da ba’a sanya mashi date, sunyi matuƙar firgita da ganin danƙareran macijin dake bin jikin bene Yana ƙoƙarin saukowa down, jikin baba obie Ya hau yin kerma abunka ga tsoho, Ido Ya raina fata, lamarin ya ɗaure masu kai, Deen yace”maciji kuma? Tayaya akai ya shigo gidan nan? ina jami’an dake tsaronshi? Wannan wani irin ganganci ne”? Kafin wani ya bashi amsa, kwatsam suka jiyo takun tafiyar jami’an isod, da gudun gaske suke shigowa cikin falon, hannayensu ruƙe da bindigu, atare suka hada baki wurin furta”yalla6ai ku kwantar da hankalinku, zamu kawar maku dashi,” A matuƙar ruɗe baba obie yace”baku da hankali, taya akai kuka bari maciji Ya shigo gidana? A haka kuke fadin mu kwantar da hankalinmu? Kun makance ne baku ganin girman shi? tayaya zaku Iya kamashi”! Da sauri Senate ya tari nunfashinshi”baba kayi haƙuri, zasu fitar dashi, mubarsu suyi aikinsu” Daya daga cikin jami’an yace”kayi hakuri yalla6ai ba laifinmu bane, mu kanmu bamusan tayaya akai Ya faɗo cikin estate din nan ba, babu wanda yasan daga ina Yake” da hannu deen Ya nuna masu hanya”ku shiga kuyi aikinku” da sauri suka nufi benan. Adaidai lokacin Unaisah dake ta faman gudu ta shigo cikin falon tana haki, duk ta fita hayyacinta, kusan atare suka ɗaura idanuwansu akanta, da mamaki akan fuskokinsu suke dubanta, kafin wani yai yunkurin yi mata magana, Chief owais Ya faɗo falon tare da big guy, sunyi mamakin ganinshi babu wanda yasan yana a ƙasar, tsabar firgici da tsoro Ya hana Obie furta sunanshi sai faman binshi Yake Yi da kallo. Umarni yaba big guy akan ya dauki Unaisah ya maidata gida, jin ya furta hakan yasa ta watsa da gudu cikin falon bata nufi ko’ina ba sai saman benan da zai sadata da macijin, da gudu big guy yabi bayanta, cikin shessheƙar kuka take fadin”dan Allah kada ku kashe shi, wallahi ba maciji bane, ɗan uwanane danish” damƙo hannunta big guy yai, tadinga kiciniyar ƙwace kanta ranta amtuƙar 6ace ta soma zazzaga masu masifa tana fadin”wallahi babu inda zanje, nace maku dan uwanane, ku ƙyale shi ku daina harbinshi tunda bai cutar da kowaba, wayyo Allah na danish ɗina” Sautin koke kokenta Ya cika gidan, hatta sauran mazauna gidan baba obie saida suka jiyota, ɗaya bayan ɗaya masu aikin gidan suke fitowa daga makwancinsu, Pravin bai jima da shiga ɗakin hajjaty ba ya jiyo sautin Kukan mutun agidan, sai gashi ya fito hajjaty na abiye dashi, Hajiya saratu kuwa jin sautin kukan Yasa ta fito daga ɗaki ta shigo falon, koda tayi arba da unaisa ga jami’ae da kuma shirgegen macijin dake bin bango, hannayenta biyu ta ɗaura akai tana ambaton Inna lillahi wa’inna ilaihirraji’un! Maciji acikin gidan nan? Wacece wancan Yarinyar? Ya akai ya shigo? Aruɗe ta furta hakan Kowa Ya shiga ruɗani, Jami’an sun dage sai antaya mashi Harsashi suke Yi, Ganin suna ƙoƙarin yi mashi illa yasa Unaisa tayi wani irin kukan kura, ta bangaje big guy da iya ƙarfinta na ƙarshe, ta haura sama da gudun gaske, duk yadda suka so su kawar da ita sun gaza yin hakan har saida tayi nasarar ƙarasawa inda yake, tsawa suka dinga dakata mata suna korarta daga gabanshi amma taƙi matsawa, macijin yabi ya nannaɗe kanshi Ya dunƙule waje guda saman floor, lullu6e shi tayi da bazar rigarta, tana kuka tana fadin”danish dan Allah ka saurareni, ka taimaki rayuwata, bana so na rasa ka, ka canza halittarka ka tabbatar masu da cewa kai mutunne ba maciji ba, idan ba haka ba zasu Iya kashe mun kai” cikin jin ƙunar rai take Furta maganar, ta ƙanƙameshi kamar zata maida shi jikinta, jami’an sun natsu suna kallon ikon Allah, Hajiya saratu sarkin tsoro sai faman baza idanuwanta take Yi, baba obie Yana la6e bayan Mai girma sharafuddeen, Senate Ya ruƙo hannunshi dake tayin kerma, A hankali Hateem Ya zare farin glass din dake asaman fuskarshi Ya ruƙe ahannunshi, komai ke faruwa akan idanuwanshi, tamkar amafarki suke kallon lamarin, an rasa wanda zai janyeta daga jikinshi. Abunda ya ɗaure masu kai babu alamun macijin zai cutar da ita. Duk da baya iya furta mata magana, ranta yana bata cewar yana son ya rikiɗa ya koma mutun sai dai ya kasa yin hakan, jikinshi ya ɗau zafi sosai, cikin sanyin murya ta soma yin magana, hawaye naci gaba da wanke fuskarta “Ɗan uwana rabin raina, dan Allah ka canza halittarka, idan ba haka ba babu wanda zai yarda cewa kai mutunne zasu ci gaba da cutar min dakai” ta faɗa tana ƙara kankameshi a Jikinta. umarni Owais Ya ba jami’an akan su daina yunƙurin harbinshi, amsa mashi sukayi datoh, ya fadi hakanne saboda ya fara kokwanton mutunne kamar yarda ta faɗi, a faɗace hajiya saratu tace”akan me zaka basu umarnin su daina harbinshi? idan ya cutar da wani fa”? Ko kallo bata ishe shi ba, muryar baba obie Na rawa ya furta”Ku kashe macijin nan, bana son ganinshi, ku kawar mana da shi” “Baba ka kwantar da hankalinka, Ni na yarda da maganar yarinyar ba maciji bane mutunne” mai girma sharafudden ne yai maganar. A harzuƙe Obie Yace”tayaya mutun zai zama maciji? hakan bazai ta6a yiwuwa ba, Ni bazan ta6a yarda ba, ku kawar mana dashi kawai, idan baso kuke zuciyata ta buga ba, Ita kuma waccan Yarintar mai kasada ƴar wacece? Ku ɗauke ta mana daga Jikinshi kada ya sare ta”yai maganar yana nuna Unaisah da sandar hannunshi. Duk yabi ya furgice masu, big guy ne ya kutsa ta cikin jami’an Ya nufeta, muryarshi ƙasa ƙasa tamkar tame Yin raɗa ya furta”Unaisah, ki tashi mu tafi gida, za’a dawo maki dashi” maƙe mashi kafaɗa tayi, la66anta duk sun bushe sun faffashe. “Babu inda zanje, Ina atare dashi, Idan nayi nesa dashi, ba zaku Iya sarrafashi ba, zai Iya guduwa ya nufi wani wajen” magiya ya dinga yi mata akan ta miƙe amma taƙi tashi, hakan Yasa Chief owais motsawa ya haura saman benan Ya nufe su, Darewa jami’an suka dinga yi suna bashi hanya har ya kaiga ƙarasawa inda suke, faffaɗan tafukan hannaye shi ya ɗaura saman unaisa ya ɗaɗɗagota tare da ɗaurata saman broad shoulder dinshi, juyawar da zaiyi da niyar ya tafi da ita, giant snake din Yai wata irin girgiza da gudun gaske yabi bayan owais daya ɗauketa. Jami’an suka saita shi da bindiga owais Ya hana su harbeshi yace masu su barshi akwai dalilin dayasa yayi hakan, Yana tafiya macijin Yana bin bayanshi, kasancewar ya ɗaurata saman kafadarshi tana Iya kallon giant snake din daketa ta faman jan ciki Yana nufosu, hawayenta tamkar zasu ƙare muryarta shaƙe take ambaton sunan Danish. Ganin macijin zai sauko down yasa Hajiya saratu ta watsa da gudu zaninta har yana kwancewa ta ruƙo shi ta nufi hanyar part dinsu aguje ta shiga ɗaki ta datse kofa, tabi tagogi duk ta rufesu, a karshe cikin toilet ta shige tayi locking kanta. Hankalin baba obie yai matuƙar tashi sai ƙara ƙankame jallabiyar mai girma sharafuddeen yake yi, Hateem kuwa ko kadan baiji tsoron macijin ba, tsabar mamakine Ya hana su furta magana, kowa ya baza ido yana kallon ikon Allah, duk inda owais yai da ita sai macijin yabisu, fucewa yai daga falon Ya nufi motarsu da su ka yi parking dinta abakin entry hall, Ya buɗeta Ya shigar da unaisah aback seat na motar, ya buɗe front seat a mazaunin driver Ya zauna yai mata key, da gudun gaske Ya fusgi motar, ta cikin glass din motar take kallon macijin daketa binsu da ƙarfi Ya daka uban tsalle Ya haura saman motar Yai kwanciyarshi. Ajiyar zuciya ta sauke ganin yana atare dasu, bai nufi ko’ina ba sai sashen da gidansu yake, ta gate din Baya ya shigar dasu a bakin entry hall chief Yai parking din motar, Ya fito Ya buɗe back seat din Ya cuccu6i unaisah Ya ɗaurata saman kafaɗarshi Ya nufi Babban falo da ita, hankalin shi kwance tamkar baisan da zaman macijin ba, saukowa yai daga saman motar yabi bayansu da gudun gaske yake jan jiki. Cikin takun sauri Owais Ya haura upstairs da ita, kafin Ya ƙarasa second floor, macijin Ya riga shi isa, wani wawan tsalle ya daka Yabi ta jikin bene Ya faɗo tagabansu, ƙoƙari yake ya nannaɗe ƙafafuwan owais sai dai yakasa yin hakan saboda owais bai bashi damar ruƙe mashi ƙafa ba, sai kakkauce mashi yake Yi, a haka ya ƙarasa bedroom din Danish Ya shiga daga ciki, Ya kwantar da ita saman gado, Shigowa ɗakin macijin Yai yana faman huci kamar zai kai mashi hari, saman gadon Ya haye Yana faman bin mattress din. Owais dake a tsaye ya goya hannayenshi saman wide chest dinsa, Ya natsu yana kallonsu. Giant snake din Ya nannaɗe jikinshi agaban unaisah ya ɗago da kanshi Yana kallon owais, duk a tunaninshi wani abu zaiyima unaisah shiyasa Yabiyosu, shi kuma owais daya fahinci Baya iya cutar da ita shiyasa yai dabarar daukota sai gashi yaci nasara akanshi” Fitowa yai daga ɗakin Yaja ƙofar Yai locking dinta, Yabarsu su biyu adakin Ya nufi down. Hankalinta ba ƙaramin tashi yai ba, zuciyarta sai dukan uku uku takeyi, tsananin tsorone Ya kamata, amma saboda ƙaunar da take yi mashi takasa motsawa, duk tasha jinin jikinta, muryarta na rawa ta furta sunan shi”danish ɗina” juyowa macijin yai da kanshi Yana dubanta, jikinta na kerma saboda ƙarfin hali ahaka ta miƙa mashi hannunta, jan jiki ya somayi yana nufarta, saman kirjinta ya nannaɗe kanshi, wani irin sanyi taji ya ratsata, lokaci ɗaya tadaina jin bugun da ƙirjinta keyi mata, asaman fatar shi ta ɗaura hannunta, a hankali take shafashi duk don ta kwantar mashi da hankalinshi, ita kaɗaice zata Iya fahimtarshi a halin da yake ciki. Walking quickly chief Ya nufi Ƙofar fita daga part din, Kafin Ya ƙarasa Muryar Boss man ta katse mashi hanzarinshi”yalla6ai” cak Ya tsaya da tafiya ya waiwayo yana dubansu, su biyune suka fara shigowa shida big guy, daga bayansu sauran jami’an isod ne da suka Biyosu, hankalinsu duk ba a kwance yake ba, musamman Boss man da yaji labarin abakin big guy shigowar shi kenan gidan duk wannan budurin da akeyi baida masaniya yana a part dinsa. Fuskar chief owais ta canza zuwa yanayi na damuwa. “Yalla6ai Ina macijin yake”? Big guy ne ya jefa mashi tambayar. Daƙyar Ya iya buɗe baki Ya furta”yana adakin shi, tare da yarinyar na kullesu” waro ido waje sukayi suna kallon shi Muryar boss man na rawa ya furta”kana nufin tare da Angel ka rufe su aɗaki? Idan ya cutar da ita fa”? Gaba ɗaya yabi ya ruɗe. Big guy yace”ka kwantar da hankalinka, Ni na fahimci hikimar yin hakan, da ace bai daukota ba macijin bazai dawo gidan ba, bamusan inda zai shiga ba, amma yanzu kaga mun kulleshi aɗaki ta dalilinta” Cikin rashin fahimtar kalaman big guy Boss man yace”bazai yiwu ba, Ƴata fa aka kulle aɗaki ɗaya da maciji, Idan ya kashe min itafa” dafa kafaɗarshi Owais Yai da hannu ɗaya”kadaina kiranshi maciji, mutunne, bazan iya yin abunda zai cutar maka da ƴarka ba, Kamar yarda kake jinta nima haka nake jinta, fatan ka fahimce ni” gyada kai Yai still hankalinshi bai kwanta ba. “A wani daki ka kulle su”? Atakaice owais Ya furta”A dakin shi” jiki na rawa boss man Ya watsa da gudu ya nufi upstair. Chief owais Ya maida dubanshi ga Big guy, “Things are starting to get out of control, and I don’t know what to do now. But I want to see his brother, maybe he can control him. kaje ka zo dashi” ya faɗa in a cool voice, amsa mashi yai da toh, da sauri Ya juya ya fuce daga ɗakin, Kallon sauran jami’an yai”ku koma bakin aikin ku, ku tabbatar kun kula sosai” Cikin girmamawa suka amsa mashi da toh, juyawa sukayi da sauri kowa Ya nufi hanyar komawa bakin aikinsa. Shafa sumar kanshi yai da tafin hannun shi nadama, yanke shawarar komawa gidan obie yayi, yasan suna can hankali duk Ya tashi, ba lallai su iya runtsawa ba. Cikin takun sauri Ya fita daga part din, Ya nufi ɗaya daga cikin motocinsu, wani jami’i ne Ya nufeshi da sauri Ya buɗe mashi motar ya shiga a mazaunin baya, shi kuma ya zauna a driver’s seat, yai ma motar key ya tashe ta, suka nufi cikin Obie estate...... Unaisa tana akwance idanuwanta sun kumbura suntum, kumatuntu sunyi jawur saboda kukan da tasha, busassun hawayene saman fuskarta, ta lumshe idanuwanta akan giant snake din daya ɗaura kanshi saman kirjinta, karatun qur’ani take raira mashi cikin disasshiyar muryarta daƙyar sautin ke fita, macijin Yayi lamo sai ƙara narke mata yake Yi, ga dukkan alamu yana sauraronta. Da karfi tajiyo muryar boss man Yana kwaɗa mata kira daga waje Unaisah, Unaisah!!. A hankali tasoma ƙokarin raba jikinta daga na macijin, ta lalla6a ta sauko daga saman gadon tana cigaba da yin ƙira’ar al’qur’anin, agogon bangon ɗakin ta kalla almost 10 na dare. A jikin glass door din Boss man Ya jingina yana leƙensu. Ƙarasowa tayi gaban ƙofa suna fuskantar juna, batasan sa’adda ta fashe mashi da kuka ba, Cikin shessheƙar murya take fadin”kaga irin ƙaddarar da ta sami ɗan uwana ko? Nayi ƙoƙarin na fahintar dasu cewa mutunne amma sunƙi su gane, sai harbinshi suke Yi da bindiga” Tsananin tausayine ya kamashi ganin yadda ta canza saboda damuwa. Cikin kwantar da murya yace”Yana ina “? Matsawa tayi daga bakin ƙofar, karaf idanuwanshi suka sauka akan giant snake din dake nannaɗe saman gadon kamar bacci yake yi. “Unaisa bai cutar dake ba”? Tambayar daya jefa mata kenan, Girgiza mashi kai tayi”a’a baiyi min komai ba, dan Allah ka taimaka mashi, nasan kai kaɗaine zaka Iya fahimtana,” Jinjina kanshi yaɗanyi”okey, Ki kwantar da hankalin ki, kidaina kuka bana son ganinki cikin damuwa” Fuska amarairaice tace”dole in damu boss man, rayuwar ɗan uwana abun tausayice, bazasu ta6a ƙyale shi ba, tun yana jariri suke cutar dashi har izuwa girmanshi sunƙi su ƙyale bawan Allahn nan, mugaye in sha Allah bazasu ta6a yin nasara akanshi ba” Idanuwanshi tuni sun cicciko tab da ƙwalla “Dan Allah ka taimaka mashi, akwai ruwan zamzam da ake bashi na addu’a ina da tabbacin idan yasha zai dawo dai dai” Cikin sanyin murya yace”A ina za’a same shi”? “Ɗan uwanmune Ya bani address din gidan da zamu ɗauko, namanta takardar acikin aljihun uniform dina, ai kace min kayan suna a hannunku, idan ka duba zaka ga wandona launin baƙi, mu uku keda kalar kayan dani da batul saina danish, pls ka bincika ka dauko ta, Allah yasa bata faɗi ba, nasan ma zaiyi wuya asamu zam zam din koda an samu takardar adreshin” “In sha Allah za’a nemo zam zam din, ki koma ki zauna amma pls kada ki bari ya cutar min dake” amsa mashi tayi da toh” ajiyar zuciya ya sauke, tamkar karya tafi yabarta haka yake ji, duk da Ya yarda Yaron bazai Iya cutar da ita ba, tunda gashi ya same su asaman gado ɗaya batare daya sare ta ba, shi tausayin yaron ma yake Ji. Juyawa yai da sauri Ya nufi down stair. Komawa tayi saman gadon ta haye, ta kwanta daga gefenshi taci gaba da yi mashi karatun qur’ani. Da matsakaicin gudu motar chief ta ƙaraso bakin entry hall na shiga babban falon gidan baba Obie, dasauri jami’en Ya fito daga motar Ya zagaya other side Ya buɗe mashi murfin car din, Ya zuro kafarshi Ya nufi Cikin gidan da sauri, Kamar yadda yabarsu haka ya same su a tsaitsaye cirko cirko , damuwace ƙarara akan fuskokinsu, hankalinsu bazai ta6a kwanciya ba idan har ba gawar macijin suka gani ba. “Owais”! Obie ne ya ambaci sunan shi da mamaki akan fuskarshi. Dagowa yai da kyawawan idanuwanshi ya daurasu akan faces dinsu, kamar yadda yake kallonsu haka suma suke binshi da kallo, Kamar yaune rana ta farko da suka fara ganin juna” “Owais Ina macijin”? hateem ne ya jefa mashi tambayar. Calmly ya furta”mun fitar dashi daga gidan” ajiyar zuciya kowan nan su ya sauke, Senate lateef Yace”Wacece yarinyar dake atare dashi? Munji tana kuka tana fadin ɗan uwanta ba maciji bane shin dagaske ne”! Jinjina kanshi yai alamar eh, ya ƙara da cewa”Ƴar uwarshi ce, ba maciji bane mutunne kamar kowa, ƙaddara ce ta afka mashi” “Wai kana nufin ɗan mutunne ya rikiɗa ya koma maciji”? His excellency deen ne Ya jefa mashi tambayar, gaba dayansu sun ruɗe da jin maganar, Abdul razak Yace”bazai yiwu ba, owais kodai ka fara shaye shaye ne? In bahaka ba ta ina mutun zai Iya komawa dabba kamar maciji? Ai sai dai idan ya kasance ba mutun bane shi” Obie duk Yafi su firgita jikinshi yaƙi daina yin kerma “Owais bana son ganin macijin nan, ku tabbatar kun fitar dashi daga gidan nan, Idan ba haka ba zai Iya cutar da rayuwar ahalina” “Baba ka kwantar da hankalinka, zuwa gobe in sha Allah zan shigo muyi magana, nasan yanzu ko nayi maku bayani ba lallaibane ku fahimceni ba, ni kaina hankalina ba a kwance yake ba” Girgiza kai obie yai”owais idan kaga na kwantar da hankalina to macijin nan baya acikin gidan nan, Ni ban ta6a ganin tashin hankali irin na yau ba, wai yaushema ka dawo kasar? Ita yarinyar dake tare da macijin ƴar wacece? A ina take zaune”? Shiru yai yana duban face dinshi, sam bayason yawan surutu, abu kadan ke hasala shi, baisan amsar da zai basu ba, don ya fahimci hankulansu ba akwance suke ba. Gyaran murya mai girma sharafudden Yai, hankalin owais ya dawo kan mahaifinshi”kada ka damu, ka koma bakin aikin ka My son, Ni na fahimce ka, kaje kawai zuwa gobe zamu nemaka donka zo ka warware mana rudanin da muke aciki” lumshe ido owais yai haƙika yaji dadin maganar mahaifinshi, dama yasan shi kadaine zai Iya fahimtar halin da yake aciki Kafin Ya juya saida ya fara kallon Obie, wanda tuni idanuwanshi sun kaɗa jawur, tausayin tsohon ne Ya kama shi, yayi matuƙar yin kewar kakanshi. Matsawa yai kusa dashi Ya rungume shi saman faffadan ƙirjinshi, baba Obie Ya kankame owais tamkar zasu koma mutun ɗaya. Cikin sigar lallashi yake yi mashi magana”nayi kewarka baba, kana araina, nasan ban kyauta maka ba, amma in sha Allah idan komai Ya lafa zuwa gobe zan shigo gidan” cikin sanyin murya obie Ya amsa mashi da toh, ji yake tamkar karya tafi yabarshi, yana matuƙar ƙaunar jikannan nashi. Iyayenshi dake kallonsu, murmushi ne saman fuskokinsu. Raba jikinshi yai daga na baba obie, yakai hannu Ya shafi dogon gemun shi, da zolaya ya furta”kakana nakaina, nifa da jarumta nasanka, kai ɗin Namijin duniya ne, dan Allah kada ka bani kunya, kada ganin macijin nan ya hanaka rintsawa adaren yau, kayi bacci ka huta gobe jikanka zaizo gareka, sabon cake zamu yanka atare” Farin ciki Ya cika obinna, yayin da yake duban owais, yana dariya yace”ka wahalar dani, bakasan irin kewarka da nayi ba, Na ƙwallafa raina akan son ganinka, ka manta dani owais, gobe idan kazo har tsallan kwaɗi zan sanyaka” dariya Iyayenshi suka sanya, Owais yace”kowani horo zakayi min bazan musa ba, Na cancanci fiye da hakan, Ni zan tafi, ku kulamin da kakana, Make sure he sleeps peacefully tonight.” ya faɗa yana duban iyayenshi, fuskokinsu dauke da annurin farin ciki, owais ba ƙaramin burgesu yake Yi ba, saboda yana son mahaifinsu. Juyawa yai da sauri ya nufi ƙofar fita daga falon, idanuwan kowan nansu akan bayanshi, Harya ɗaga kafa zai fuce, muryar prime minister ta dakatar dashi “Owais! ina son yin magana dakai” a hankali Ya juya yana dubanshi, da sauri Hateem Ya nife shi, babu mai Iya jin abunda suke cewa saboda sunyi nesa da sauran mutanan. Dafa kafadarshi yai da hannu ɗaya, tunkafin hateem yai magana owais ya riga shi furta”uncle sai kunyi hakuri dani, ka zo kasar bansamu lokaci nazo gaishe ka ba” murmushin gefen fuska yasakar mashi”ni wannan ba damuwata bace, nayi maka uziri saboda nasan yanayin aikin ku,’ ya faɗa yana dubanshi kafin yaci gaba da magana. “Inaso ka faɗamin dagaskene macijin nan mutunne”? Jinjina kai owais yai”dagaske ne mutunne ya rikida, matashin saurayi” Shiru hateem yaɗanyi kafin ya kuma cewa”Ya sunanshi”? “Danish” ataƙaice ya bashi amsa. “Duk da bansan abunda ke damunshi ba, amma idan har mutunne ya rikida hakan na nufin aljanune atare dashi ko”? Ɗaga mashi kai owais Yai”haka muke tsammani” Hateem Ya numfasa kafin Yace”Inason ganinshi idan yadawo suffarshi ta ainahi, sannan Yakamata a kira sheikh imam ya duba shi, ina da tabbacin zai Iya taimaka mashi” Amsa mashi yai da toh, daga haka sukayi sallama owais ya fuce daga falon. Bayan tafiyar owais, su Hateem suka raka baba obie bedroom dinshi, babu yadda basuyi dashi ba akan ya kwanta ya runtsa amma Yaƙiya gani yake tamkar macijin zai faɗo ɗakinshi, duk yabi ya firgice, adole mutun biyu suka tayashi kwana, Sharafudden da senate lateef, sauran kowa Ya nufi masaukin shi. Hankalin Hateem Yaƙi kwanciya, Macijin Ya tsaya mashi aranshi, ya ƙwalla fa rai akan son ganin yaron, ko bayan daya koma Gidanshi dake a estate din, a ɗaki ya tarar da gimbiya mujeedat, tana faman yin zarya, ta kasa kwanciya saboda rashin dawowarshi, babu wanda yasan abunda ya faru a gidan baba obie sai wadanda ke zaune agidan. Bai sanar da ita komai ba, Saman gadonsu Ya haye ya kwanta yayin da idanuwanshi ke fuskantar ceilling, tayi mamakin ganin damuwa atattare da mijin nata, har tambayarshi tayi meke damunshi amma sai yace mata babu komai, bacci yake ji, ƙoƙarin faranta mashi tayi har saida ta tabbatar ya fara yin bacci tukunna hankalinta ya kwanta. *SIR MUBARAK✊* Babu wanda ya motsa acikinsu, tun da suka ji muryar mutumin daya kira layin jazz, Jikin kowannansu yai sanyi laƙwas tamkar an zare masu laka, har sun fara danasanin jahilin bugun da sir mubarak yaiwa jazz domin kuwa sun tabbatar sune sukayi kuskuren yanke hukunci batare da sun fara bincikarshi ba. Yarinyar dake a zaune dirshan idanuwanta sun kaɗa jawur yayin da hannuwanta ke asaman fuskar jazz. kafin Sir mubarak Yai ƙwaƙƙwaran motsi, Muryoyin yaran dake tunkaro ɗakin Ya karaɗe kunnuwan sojojin Kusan atare suka ɗago suna kallon baƙin ƙofar shigowa ɗakin. Matasan ƴan mata ne kowaccensu sanye cikin rigunan bacci, babu huluna akansu sai zallar sumar kansu mai tsayi har gadon bayansu, namiji ɗayane acikinsu shima kayan baccin ne ajikinshi, fuskokinsu a yamutse sai hamma suke Yi, ga dukkan alamu kukan ƴar uwarsu ne Ya farkar dasu daga bacci. “Meya faru da yaya jazz dinmu? Su wanene ku”? Har suna haɗa baki wurin tambayar sojojin. Cikin shessheƙar kuka Yarinyar dake ruƙe da dr. Jazz ta kware murya tana kallon ƴan uwan nata tace”Sun kashe mana shi, bansan su wanene su ba, kawai sun shigo mana gida sun kama bugunshi” Fashewa sukayi da kuka kamar gidan mutuwa, da gudu suka nufi inda yarinyar take a zaune, a kewaye da dr jazz suka zuƙunna Suna ambaton sunanshi tamkar ransu zai fita. Ba zato ba tsammani, sojojin suka jiyo muryar babban mutun Yana fadin”meke faruwane? Su wanene suka shigo gidan”? Fadowa cikin ɗakin Yayi, daga shi sai short a jikinshi babu riga, yana da faffaɗan kirji ga ƙirar ƙarfi kamar ɗan dambe, kallon ɗaya zaka yi mashi ka shaida farar fatane, fatarshi jawur take daga gani bature ne. Lokacin da yai arba da su sir mubarak a ɗakin Ras yaji gabanshi yai mugun faɗuwa, adabarbace ya furta”su wanene ku? Meya kawo ku cikin gidan nan”? Kafin wani ya furta kalma, Mutumin ya wurga idanuwanshi akan yaran dake kuka. Zaro idonshi waje yai ganin yadda suka raunata jazz, da ƙarfi yace”don ubanku ku faɗamin su wanene ku? Uban me yayi maku da kukayi mashi wannan bugun? Waye ya turo ku? Babu alamun tsoro akan idanuwanshi, sai ma dunƙule hannayenshi da yai da niyar yakai masu hari, An rasa me magana tsakanin Sir mubarak da su tiger. Gigitacciyar tsawa ya daka masu Yana fadin”bakuji ina magana ba? Idan har baku faɗamin ba, daya bayan ɗaya zan salwantar da rayuwarku” A harzuƙe tiger da Major suka zaro bindigunsu tare da saita shi, maimakon yaji tsoron bindigar hannunsu sai gani sukayi Ya sanya hannu ya daki ƙirjinshi da ƙarfi Yana fadin”Kunyi kuskuren shigowa gidan nan, abun hannunku bai isa yasa inji tsoronku ba, tunda kuka ta6a jazz sai kunyi danasanin haihuwarku da uwarku tayi acikin duniyarnan, kawai saboda zalunci saiku faɗo gidan mutane kukama bugun mutun baiyi maku laifin komai ba”? Tamkar mayunwacin zaki haka yake yi masu magana yana fitar da huci mai ɗumi Daƙyar sir mubarak Ya iya sarrafa kanshi, muryarshi a haushine ya furta”dan Allah ka faɗamin wanene kai, Ni da kake gani mahaifin jazz ne, mun shigo gidan nan batare da sanin shi ba, saboda mu atunaninmu wani mugun abun yake aikatawa.....” a tsanake sir mubarak Ya kwashe duk abunda Ya faru dangane da zargin da yake yima jazz ya sanar da matashin saurayi Lokaci ɗaya sukaga ya sassauta fushin fuskarshi, ga dukkan alamu ya fahimce su. “Amma baku kyauta mashi ba, shiyasa akace zato zunubi koda ya kasance gaskiya, jazz dai ba mugu bane, mutumin kirkine fiye da tunaninka, waɗanda yaran kuma dakuka gani marayune basu da gata aduniyar nan daya wuce Allah sai kuma waɗannan bayin Allahn da suka taimaki rayuwarsu” yai maganar yana nuna jazz da hannunshi, Yaran dake sauraron su idanuwansu sunyi luhu luhu sunsha kuka kamar ransu zai fita don ba ƙaramin ƙaunar jazz suke Yi ba Cikin karyayyar murya sir mubarak yace”kana nufin Chief owais shine ke kula daku? ya tambayeshi saboda yaji muryar owais a wayar jazz yana da tabbacin shine Ya kira layinshi Jinjina kai mutumin yai”ƙwarai kuwa, a ƙarƙashin kulawarshi muke gaba ɗayanmu, shi kuma jazz shine likatan daya dauki nauyinshi don kula da marasa lafiyan cikinsu, Yarinyar nan kuma daka ganshi atare da ita saman gado, bata da koshin lafiya, tana da ta6in hankali, ga magungunanta can saman drawer da alluran da yake yi mata, abunda yasa kuka same shi asaman kanta, ni nasan saboda babu mai iya rike mashi itane, idan dare yayi bayason tashina daga bacci, ni ne nake taimaka mashi wurin ruƙeta ayi mata allura saboda buge bugen da take Yi, idan har ba a ruƙeta ba baza a iya yi mata allura ba, tana da ƙarfine, kunyi zargin jazz yana aikata fasiƙanci da ita bahaka bane abunda na faɗa maku shine gaskiyar zance’ Dafe kai Sir mubarak yai da hannu ɗaya, Wani irin matsanancin ciwon kaine ya farmashi, su tiger sunyi danasanin zargin jazz da sukayi jikin taƙaura yayi la’asar “Dan Allah ku taimaka mashi kada ya mutu, har yanzu baidaina bleeding ba” ɗaya daga cikin matasan yaran ce tayi maganar, fashewa sir mubarak yai da kuka tamkar ƙaramin yaro, cikin rauni na murya yake fadin”Inna lillahi wa’inna ilaihirraji’u! Jazz baka kyautamin ba, meyasa baka sanar dani ba, kabar ni inata zarginka gashi har nayi maka illah! Yanzu ya zanyi? Me zan faɗama mahaifiyarshi? Matar da ko bacci bata iyayi idan har bai dawo gidaba saboda ƙaunar da take yi mashi! Juyawa yai da sauri ya nufi inda yaran suke, bai bi takansu ba, ya sanya hannayenshi biyu ya cuccu6i Jazz Ya ɗaura shi saman kafadarshi, ya dubi su Tiger da rinanun idanuwanshi yace”major muje mu kaishi asibiti, kai kuma Tiger ka tsaya atare da army ku lallashi yaran dan Allah” ya ƙare maganar da sauri ya nufi ƙofar fita, Major yabi bayanshi bayan ya kar6i key din motar a hannun tiger. Har sun kusa futa daga dakin, matashiyar nan mai fama da ta6in hankali ta fasa ƙara hadi da yunkurawa ta mike aguje tabisu tana fadin”mugaye ku dawo mana da ɗan uwanmu kada ku kashe shi, wayyo Allahna Yaya kana gani zasu gudu dashi “ har takusa fucewa daga ɗakin, Mutumin Ya damƙo damtsen hannunta, Ya rungumeta a chest dinshi yaci gaba da lallashinta. Tiger ne ya soma lallashin ƴan uwanta dake kuka “Kuyi haƙuri, kuskure mukayi wurin bugunshi, mu ba mugaye bane kamar yadda kukayi tsammani, mutumin daya dauki jazz mahaifinshine ba wani ba, kuma asibiti zasu kaishi inda za’a duba lafiyarshi, da zarar yaji sauƙi za’a dawo maku dashi” cikin shessheƙar kuka suka amsa mashi da toh, banda mahaukaciyar yarinyar daketa ɗura masu ashar, kamar zata bugesu, mutumin ya ƙankameta ya hana ta kubce mashi. Kusan rabin awa da tafiyar Sir mubarak, motar Big guy ta shararo da gudu cikin unguwar, tunkafin ya ƙarasa bakin gate din gabanshi ya fara faɗuwa ganin ƙofar gate din abude kusan ƙarfe goma sha ɗaya na dare, nan take ranshi ya bashi cewar wani mummunan abunne ya faru watakil shiyasa lokacin da chief Ya kira wayar jazz yace mashi ya ɗaga baiyi mashi magana ba!!!!😳😳😳 *DAGA ALƘALAMIN BOSS BATURE✊✍️💋🤍* A tsiyace yai parking din motar, tsabar sauri a buɗe yabarta, da gudun gaske ya nufi cikin gidan batare da jin shakkar komai ba, Shigar shi keda wuya cikin falon ya soma jiyo sautin kukan yarinyar nan mai fama da ta6in hankali, ta dage sai zazzaga masifa take yi tana fadin”wallahi saina tona maku asiri ranar lahira, dukanku sai kun shiga wuta tun da ku ka ta6a min yaya jazz ɗina”. Zuciyarshi ce ta soma dukan uku uku, zaro bindigarshi dake soke a ƙugunshi yai, cikin sanɗa yake tafiya yana tunkarar Upstairs, Ya haura second floor, daga ƙofar ɗakin Ya la6e Yana sauraronsu. “Ki daina magana mana, bakiji suna bada hakuri ba? Kuskure suka yi wurin bugunshi, bada son ransu ba” Jin muryar mutuminsu yasa shi yin wuff Ya afka cikin ɗakin, Jin takun tafiyarshi ne Ya janyo hankulansu ga dubanshi, kusan atare suka ɗago suna kallon shi. Nauyayyar ajiyar zuciya big guy ya sauke haɗi da furta”Ya Allah” kafin Ya daura eyes dinshi akan face din mutumin yace”meke faruwa ne ? Waya ta6a khadeeja take kuka? ya akai naga yaran duk sun farka daga bacci”? A ruɗe yake jefa mashi tambayoyin, sam bai lura da Sojojin ba, waɗanda tun da ya shigo suke dubanshi da mamaki. da ido mutumin Yai mashi nuni da sojojin”gasu nan, mahaifin Jazz ne yazo tare dasu, wani abune ya faru na rashin fahimta da yajawo har suka bugi jazz shine take ta kuka” A hanzarce ya mayar da dubanshi ga Sojojin, Kusan atare suka buga ƙafa tare da Sara mashi. Jinjina kanshi yaɗanyi da mamaki ya furta”Tiger ! Army Boy! Ya akai kukazo gidan nan? “Tsautsayi da ƙaddara” acewar Tiger, Army ya kwashe duk abunda ya faru ya sanar da Big guy, sai lokacin ya lura da jinin dr jazz daya daskare saman floor, ga kuma Dressing mirror da daya fashe ta silar buga kan jazz jikinshi, cikin matsanancin tashin hankali ya furta”Inna lillahi wa’inna ilaihirraji!” Cikin sanyin murya Army Boy yace”sai haƙuri yalla6ai, rashin sanine, tabbas munyi kuskure, amma shima jazz din hada laifinshi, Yakamata ace komai zai yi ya sanar da Sir mubarak a matsayin shi na mahaifinshi bawai yayi gamon kanshi ba, kuma a yanayin yadda Sir mubarak yake riskarshi Yana yin waya ta sirri, kalaman da yake furtawa sun yi kamanceceniya dana masu safarar mutane” Tiger ya ɗaura da cewa”yanzu haka sun tafi asibiti dashi, Muna jira muji daga gare su, In sha Allah zaiji sauƙi” Numfasawa big guy yai, jikinshi duk yai sanyi kamar wanda aka zarewa laka, babban tashin hankalin shi halin da suka jefa jazz basu ta6a tsammanin abun zai jaza mashi matsala ba. Tuni idanuwan big guy sun kaɗa jawur tamkar zai fashe da kuka Ya soma yin magana”ba laifin shi bane, laifinmu ne da muka hanashi yasanar ma kowa dangane da aikin da muka sanya shi, saboda bama son kowa ya sani” komawa yai daga gefen gadon dakin Ya zauna, Yana duban Yaran dake raku6e jikin bango, idanuwansu sunyi luhu luhu. Mai ta6in hankalin tuni tayi shiru, sai faman zazzare idanuwanta take Yi tana dubansu. Tiger yace”shi kanshi Chief Owais bazai ji dadi ba, ranshi zai Iya 6aci amma nasan zai fahince mu” Ganin yadda yaran suketa Yin hammar bacci, yasa Big guy yi masu magana”Kuje ku kwanta, Zuwa gobe idan Jazz Yaji sauƙi zamu dawo maku dashi” Miƙewa su ka yi a jere suka nufi hanyar fita daga ɗakin jikinsu babu ƙwari, hankalinsu ba kwance yake ba saboda Jazz dinsu da babu lafiya. Har sun kusa fita daga ɗakin, Big guy ya kwaɗawa ɗaya daga cikinsu Kira “Hawwa! zonan, matashiyar daya kira da hawwa ta juyo tana dubanshi, Ki ruƙe hannun khadeeja ku tafi da ita daki ta kwanta” ya fadi hakanne don yasan su kadaine zasu Iya control dinta har asamu tayi bacci. Muryarta ashaƙe take fadin”ni bazan bisu ba, kuma bazan Yi baccin ba, wallahi sai kun dawo mun da jazz dina” Lallashinta mutumin dake ruƙe da ita ya somayi”kinsan dai bazanyi maki ƙarya ba khadeejata, da kaina zan dawo maki dashi, Yanzu dai kije ki kwanta gobe zaki ganshi, amma idan har bakiyi bacci ba, toh bazan dawo maki dashi ba” Kwa6e mashi fuska tayi”kayi alƙawari”? Jinjina mata kai yai”in sha Allah” ta amsa mashi da toh, sakarni inje in kwanta” sakinta yai, tafiyarta sam babu natsuwa da sauri ta nufi su hawwa ta ruƙe hannunta acikin nata suka fuce daga ɗakin. Bayan fitarsu, Big guy ya miƙe ya dubi mutumin”Muna buƙatarka da gaggawa, ka koma ɗaki ka sanya sutura a jikinka, idan kuma zamu Iya tafiya haka toh,” ya fada yana nuna gajeran wandon jikin shi da hannu. Mutumin yace”bari naje na sanya jallabiya, ƙwara aganni da mutuncina” da zolaya ya faɗa, murmushi sojojin suka saki, fice wa yai daga dakin. “Yalla6ai wani abu na faruwane”? Tiger ne ya jefa ma Big guy tambaya”kusan haka sai dai kasan yanayin aikin mu” jinjina kai big guy yai don ya fahimce me yake nufi Shigowa ɗakin matashin saurayin yai, Jikinshi sanye da jallabiya fara tayi mashi kyau. Miƙewa big guy yai tare da kallon su tiger”zamu tafi gidan chief, babu tabbacin zamu dawo yau, wani muhimmin aikine me girma agaban mu, dan Allah ku kula da yaran, babu wadataccen tsaro agidan” amsa mashi sukayi da toh, army boy yace”Amma yalla6ai zaku sanarma chief abunda ya faru tsakanin Jazz da sir mubarak”? Big guy yace”ya zama dole mu sanar dashi, sai dai ba yanzu ba tunda shi kanshi hankalin shi ba akwance yake ba, amma idan komai ya lafa zamu fada mashi” gyaɗa kai army yai”okey, Allah ya tsare hanya” Amsa mashi yai da ameen, kafin Yaja hannun mutumin suka fito daga gidan, jin ƙarar tashin motarsu, Yasa Army da tiger suka sauko down, zuwa sukayi bakin gate din gidan suka datse shi, kafin suka koma palour suka zauna saman sofa suna fuskantar juna Army boy yace”tiger ya kaga yaran? Nayi mamakin kyawunsu, Allah yasa oga ya amince min in samu matar aure acikinsu” tunkan ya ƙare maganar tiger ya wurga mashi kallon harara”amma baka da hankali, kai waɗannan yaran sunyi maka kama da matan yaku bayi? Ka manta matsayinka ne? Karfa ka cika zaƙewa, wallahi yazu kaji ka a saman kujerar lantarki kana kar6ar punishment, ni kaina ƴan matan sun burgeni, gaskiya Oga ya iya kiwo, fatarsu har ƙyalli take Yi sunji hutu abunsu, yara kamar matan aljanna gashi har gadon baya, gaskiya dakyar idan iyayensu ƴan nigeria ne” Ya fada yana yin hamma”ni yanwa ma nake ji, Allah yasa suna da abinci agidan, nasan ba za’a rasa farfesu ba tunda Chief owais ne ke kula da cinsu nasan za’ayi harka ta arziƙi, duba mana kitchen dinsu” yai maganar Yana duban Army boy, miƙewa yai da sauri ya nufi hanyar kitchen, har zai wuce yaci karo da freezer, buɗewa yai ya leƙa ciki, Kayan marmarine nunannu, da drinks” washe baki yai yana faman shafa ciki yace”mutumin yaufa kakarmu ta yanke saƙa” Tiger yace”ba kallo zaka tsaya yi ba, ka shiga kitchen ka dauko tray ka kwaso mana sauran abincin da suka rage” amsa mashi yai da toh, da sauri ya shiga kitchen. Jim kaɗan sai gashi ya fito hannunshi ruƙe da katon tray, daga saman tray din plate biyu ne, ɗaya na fried rice daya kuma na chicken wings, saida ya fara tsayawa agaban freezer ya buɗe ya dauko masu kayan marmari ya jera gefen plates din ya ƙara da robobin juice masu sanyi, tiger sai faman haɗiye yawu yake yi,. Zama su ka yi saman lallausar carpet din falon, kamar masu fama da ciwon yunwa haka suka dumbuza hannu, sunaci suna fira. Kamar daga saman suka jiyo muryar matashiyar nan mai fama da ta6in hankali tana fadin”wayyo Allah, mayu zasu cinye mana abincinmu!” afirgice suka ɗago suna kallonta, daga can saman bene take zazzaga masu masifa, gashin kanta duk ya rufe gefe da gefen fuskarta, da gudu ƴar uwarta hawwa ta fito daga ɗaki, Taja hannunta suka koma ciki, ta rufe kofar ta yadda bazata sake fita ba. Tiger yace”jarababba, wallahi hartasa gabana ya fadi” ya fada yana dariya Army yace”ai daga ganinta anyi rashin ji a ƙuruciyarta, kunnuwanta tsaitsaye suke irin na zomo, gata kyakkyawa da ita” cigaba da cin abincinsu sukayi hankalinsu kwance, bayan sun kammala army boy ya tattara kayan abincin ya maidasu kitchen, a saman sofa suka kwanta ga sanyin A.c, sufa ashar kakarsu ta yanke saƙa. *Daular Alhaji Musa* *BENAZIR💔* Tayi nisa acikin baccinta, ba zato ba tsammani taji an shaƙe mata wuyanta, shaƙa bata wasaba, nan take numfashinta ya soma kiciniyar ɗauke wa, mutsu mutsu ta somayi yi tana harba ƙafafuwanta, hannayenta biyu ta daura saman wuyanta a ƙoƙarinta nata kwace kanta daga hannun mutumin dake yunkurin kasheta, wata irin zuface ta soma tsastsafo mata saman goshinta, zuciyarta tashiga harbawa da ƙarfi da ƙarfi, ta zazzare idanuwanta cikin duhu bata Iya ganin komai saboda sun kashe ƙwan dakin, duk yadda taso ta ƙwaci kanta ta kasa, an toshe mata baki babu halin ta ƙwala kira don azo ataimaketa, hannunta tadinga lalubawa saman mattress cikin sa’a ta cafko hannun zeenatu dake akwance gefenta, cikin fitar hayyaci take tsunkulinta har saida zeenatu ta farka tana shessheƙar kuka ta furta”wai.. wanene ke cunkulina” tunda zeenatu tayi magana, Benazir taji an sakar mata wuyanta, fashewa tayi da matsanancin kuka, sakamakon raɗaɗin azabar da taji wuyanta nayi mata, a matuƙar ruɗe zeenatu takai hannu saman bedside drawer ta kunna fitila haskenta ya haskaka saman gadon, muryarta adabarbarce take fadin”Auntyna meya faru kike kuka? Baki da lafiya ne”? da rarrafe ta ƙarasa gaban benazir tana duban fuskarta, a lokacin ta zabura a furgice ta mike zaune tana faman sauke ajiyar zuciya hannunta biyu ruƙe da wuyanta, fuskarta tayi sharkaf da zuba, maƙoshinta ya bushe ƙamas, tsananin rudanine ya kamata, kokwanto ta somayi akan abunda ya faru da ita shin dagaske ne wani ya shaƙe mata wuyanta ko kuwa mafarkine take yi”? “Aunty Benazir dina, dan Allah kiyi min magana, meyasa ki yin kuka? Ko kinyi mafarki ne? Sam takasa buɗe baki tayi ma zeenatu magana sai faman zazzare manyan idanuwanta take Yi tamkar kwayar zasu faɗo kasa, haƙika ta shaƙi ƙamshin mutuwa. Dafa kafaɗarta zeenatu tayi”mafarki kikayi aunty? ko wuyanki yana yi maki ciwo ne” ta fada cikin kulawa da nuna damuwa take duban fuskar benazir. Dogon numfashi benazir taja yayin da zuciyarta ke harbawa da sauti mai ƙarfi, tsantsar tashin hankaline da fargaba akan fuskarta, gaba ɗaya ta dabarbace tarasa gane meke shirin faruwa da ita! Idan mafarki ne tayi an shaƙe mata wuya meyasa take jin raɗaɗin bayan tafarka daga bacci? Shessheƙar kukan zeenatu ne Ya fargar da ita, tana faman haɗiyar yawu idanuwanta da fargaba take duban zeenatu Daƙyar ta iya buɗe baki ta yi mata” magana”zeenatu ruwa! Ruwan zan sha” Tsagaitawa zeenatu tayi da yin kukan jiki na rawa ta sauko daga saman gadon, ta nufi ƙaramin frigde din ɗakin, ta buɗe ta ɗauko mata bottle water me sanyi ta dawo ta haura saman gadon ta miƙe ma benazir, yatsun hannunta na kerma ta kar6i roba ruwan tacire nurfin ta kafa abaki tana sha, maƙoshinta har sauti yake badawa kwat !kwat!. zeenatu ta natsu tana kallonta, gaba ɗayansu sleeping dress ne ajikinsu. Bayan ta gama shanye ruwan ta daura bottle din saman drawern gefen gadon, Ajiyar zuciya tadan sauke, kafin ta dubi zeenatu data kwa6e fuska idanuwanta sunyi luhu luhu bacci bai isheta ba an tashe ta daga bacci “Aunty ki faɗamin meke damunki” Lumshe ido benazir tadanyi kafin ta waresu akan fuskar Zeenatu “Babu komai ƙanwata, mummunan mafarkine nayi” Ajiyar zuciya zeenatu tasauke”amma aunty kin tada min hankalina, nayi tsammanin wani abunne ke damunki ko baki da lafiya, kuma naji kina cunkulina” ta fada tana nuna mata damtsen hannunta, fatar wurin tayi jawur saboda tsunkulin da benazir tayi mata kiris ya rage ta fashe. Jikin benazir ba ƙaramin sanyi yayi ba, ganin irin illar da tayi mata “Kiyi haƙuri ƙanwata, bansan nayi ba, cikin magagin baccine na cunkule ki” Murmushi zeenatu tasakar mata”kada ki damu auntyna, na fahimce ki,” ƙaƙalo murmushi benazir tayi yarinyar ba ƙaramin burgeta take Yi ba, ta damu da ita sosai, “Ki koma baccinki, kada ki makara a school gobe” Muryar zeenatu da shagwa6a tace”ae bana zuwa makaranta tunda na kammala secondry school daddy ya hanani cigaba da karatu, yace wai sai idan nayi aure mijin da zan aura ya amince min in cigaba da karatu tukunna zani barni” Jinjina kai benazir tayi har yanzu bata warware daga fargabar abunda ya faru da ita ba, dauriyace kawai take Yi don kawar mata da damuwar dake atare da ita. “Idan kina son karatun, meyasa ba zaki fidda miji ba? Duk da ni aganina kinyi ƙaranta da aure, gaskiya uncle bai kyauta maki ba” Sunnar dakai ƙasa tayi cikin jin kunyar benazir tace”to ai nima inason nayi auran kuma ma ina da mijin da zan aura” da zolaya Benazir ta zaro idanuwanta masu dauke da bacci, da sauri zeenatu ta daura kanta saman pillow tana dariya Kallon bayanta benazir tayi fuskarta dauke da murmushi, “Faɗamin sunan saurayin naki inji idan yayi mani” Muryarta ƙasa ƙasa tace”ki tambayi yaya shureim, yasan shi zai fada maki sunanshi” benazir bata kawo komai aranta ba, tace”to zan tambayeshi idan Allah yakaimu gobe, yanzu dai mu kwanta muyi bacci” amsa mata tayi da toh, atare suka kwanta, hankalin benazir yaƙi kwanciya gani take tamkar abunda ya faru a mafarkinta zai faru gaske, hakan yasa ta rungume Zeenatu ajikinta, gudun kada aƙara shaƙeta, addu’o’i ta karanto ta tottofa masu kafin ta lumshe idanuwanta. Bakomai take tariyowa ba face fuskar tajuddeen, da fuskar baby din data bari acikin kwamin wanka, tuni hawaye sun wanke fuskarta, taƙosa su dawo ƙasar, fatanta Allah Yasa taj dinta baiyi aure ba, da wannan tunanin bacci yayi awon gaba da ita. *Ex-prisoners💔* Tsoro da fargaba ya hanasu runtsawa, sunyi zazzaune saman dining chairs, ummin america bata ta6a ganin tashin hankali irin na yau ba, sam takasa samun natsuwa, jefi jefi takan dago da ido ta dubi su Batul, Har yanzu hanna bata fito daga ƙarƙashin table ba. Jemimah tana azaune saman laps din Haris Ta ƙankameshi tuni bacci yajima da yin awon gaba da ita, abun duniya ya ishi Parveen, Jikinta sai rawar ɗari yake yi saboda ruwan data watsa ma rigarta, ta jiƙe sharkaf, ga sanyin a.c abu goma da ashirin, azeeza data suma ta farfado tun bayan da sajeed Ya yayyafa mata ruwa, sai faman firgita take Yi, macijin tamkar Yana yi masu gizau, ga bacci a idanuwansu sai dai sun kasa runtsawa, kowa da abunda ke damunshi basu san meke wakana acikin gidan ba. “Dan Allah Ku bani mayafinku In lullu6e jikina sanyi nake ji” parveen ce tayi maganar, babu musu Batul Ta curo mayafinta ta miƙa mata ta sanya hannu ta kar6a ta lullu6a shi ajikinta. “Ni nakasa gane meke faruwa! ya akai maciji Ya shigo gidan nan? Ummi ce ta jefa ma kanta tambayar da bata da amsarta. Shiru sukayi babu wanda ya tanka mata, babban abunda suke jima fargaba kada ace mutanan prison ne suka kawo masu hari, shiyasa duk jikinsu yayi sanyi. “Ni abunda ke damuna, Danish dinmu da unaisah, bansan awani hali suke aciki ba, Allah yasa babu abunda ya same su” In a cool voice Batul ta furta maganar. Tamkar ta tsokano Jemimah, cikin bacci ta fashe da kuka tana sambatun”wayyo Allah genie dina, dodo zai cinyeta, kuje ku dauko mun ita” da sauri Haris Ya toshe mata bakinta da tafun hannunshi”kiyi mana shiru, ko so kike dodon Ya jiyo kukanki yazo wurinmu”? Ba tare data buɗe idanuwanta ba tace”a’a amma genie fa? Tana can ita da Danish dodo zai cutar dasu, Ni dai ku ƙyaleni inje wurinsu” ta faɗa tare da buɗe kumburarrun idanuwanta, da ƙarfin hali tasoma kiciniyar saukowa daga saman laps din haris don ta fita daga dakin Ummi tace”kada ka bari ta sauko ka ruƙeta, idan ba haka ba zata iya janyo mana macijin nan” Amsa mata yai da toh, ya rurruƙe jemimah ajikinshi. “Ki kwantar da hankalinki, babu abunda zai samu Unaisah, ai naga mutanan nan masu baƙaƙen kaya, wata’ƙil ma harsun kashe shi” Javed ne yayi maganar, jemimah dai taƙi haƙura, tacika masu kunnuwa da shessheƙar kuka. Ƙwanƙwasa glass din ƙofar da akayine ya firgitar dasu, arazane suka dago duka a tunaninsu macijin ne Ya daki glass ɗin, ganin Boss Man yasa suka sauke ajiyar zuciya, jiki na rawa Ummi ta miƙe ta nufi ƙofar, ta bude mashi bai shigo ba daga waje Ya tsaya. “Ina macijin”? Tambayar data fara jefa mashi kenan” Yayi mamakin ganin yadda jikinta ke rawa, har saida yadan saki murmushi ta cikin face mask dinshi “Haba ummi tsoronshi kike ji kema”? Ta6e baki tadanyi kafin tace”bazaka gane bane, wallahi na firgita macijin yayi girma dayawa” “Ki kwantar da hankalinki, ba maciji bane mutunne nasan ko nayi maki bayani ba lallai ki fahimce ni ba” Zaro ido waje tayi”what! Kana nufin mutunne? Tayaya haka zata yiwu”? A rude ta jefa mashi tambayar “Kodai kana nufin abunda naji unaisa tana faɗi gaskiyane? Na cewa Danish ne ya zama maciji”! Jinjina mata kai yai”hakane, gaskiya ta faɗi” Cikin jin faɗuwar gaba ummi tace”ni dama najima ina zargin yaron nan ba mutun bane, saboda kyanshi yayi yawa ashe aljanine” Boss yace”ba aljani bane, mutunne shi kamar kowa, yanzu bani da isasshen lokaci, zuwa gobe da safe zanyi maki bayani,” tsantsar mamakine Ya kamata. Muryar Jemimah ce tajanyo hankalinshi ga kallonsu”Boss man ina genie ɗita? Dodon nan ya cinye min ita ko” Shiga cikin ɗakin yai, sam sun kasa motsawa suna jin muryarshi sai dai tsoro Ya hana su je gare shi Ɗaya bayan ɗaya yake dubansu, “Dan Allah ku kashe abunnan bamu son ganinshi duk ya firgitar damu” parveen ce tayi maganar tana dubanshi Batul tace”boss ina ƴan uwanmu suke ne? Bamusan awani hali suke ciki ba” Goya hannayensa yai saman ƙirjinshi Yana dubansu “Basai nayi maku bayani ba, unaisah ce zata faɗa maku komai, abunda nakeso daku Yanzu ku kwantar da hankulanku, Ku tashi muje na raka ku ɗaki ku kwanta kuyi bacci, dare yayi sosai kusan ƙarfe goma sha daya da rabi” “Nidai bazan kwanta bacci ba, sai naga genie dita” acewar jemimah Azeeza sarkin tsoro tace”bazan Iya kwana aɗaki ba, wannan abun zai Iya faɗowa ɗakin Ya cutar damu” Dama yasan da wuya su iya kwantar da hankalinsu. Kallon Ummi yai”please ki tafi da dasu ɗakinki su kwana kafin zuwa gobe idan komai ya lafa, sai su koma nasu ɗakin” “Badamuwa, ku tashi mu tafi” acewar ummi. Miƙewa sukayi daga saman kujerun, matan dake acikinsu, Batul azeeza da jamimah, Boss Yace”Ina ƴar uwarku Hannah”? “Gatanan ƙarƙashin table,” sajeed ne ya faɗa tare da duƙawa ya janyota da ƙyar, ta ƙudundune kanta kamar kifin gwangwani,. “Hanna ki tashi ku tafi” daƙyar ta miƙe tsaye zufa duk ta wanke fuskarta, “Sannu da jiki” boss ne yai mata maganar, sai faman zazzare idanuwanta take Yi. “Zanje na rakasu ɗaki, Sajeed ka tafi da sauran ƴan uwanku maza” amsa mashi yai da toh, Tamkar karsu fita daga dining room din, gani suke kamar macijin zai dawo masu, badan boss na atare dasu ba dakuwa babu wanda zai Iya fitar dasu saboda tsoratar da suka Yi, asaman bayanshi Ya goya azeeza, ummi ta dauki jemimah abayanta, Batul ta ruƙo hannun parveen dana Hannah, Ahaka suka jera suna tafiya har suka ƙarasa ga second floor, a ƙofar dakin ummi suka dakata dayin tafiyar, ta buɗe kofar suka shiga daga cikin, bayan boss Ya sauke azeeza daga saman bayanshi yayi masu sallama ya juya ya fuce. Sai faman baza ido suke Yi, Yau gasu adakin Ummi, Bedroom ɗinta Ya haɗu kamar na amarya, an zuba mata kayan alatu. Ganin ya fuce daga ɗakin Yasa tayi saurin zuwa tayi locking din ƙofar, tabi windows din dakin ta zugesu, tukunna hankalinta Ya kwanta. Dubansu tayi sunyi tsaitsaye curko curko suna jiran umarninta “Parveen ki shiga toilet ki ƙara tsarkake jikinki” amsa mata tayi da toh, a tsorace ta shiga toilet din. Kallon jamimah da azeeza tayi”akwai wadda takeyi fitsarin kwance acikin ku”? Girgiza mata kai sukayi alamar a’a “Ke fa”? Ta jefa ma batool tambayar Itama tace a’a, Gyaɗa kai tayi”okey, amma gadon bazai ishemu ba, Ni ban saba kwana atakure ba, mutun biyune zasu samu damar hawa gado, Biyu sai su kwana saman carpet” tayi maganar tana nuna masu carpet din dake a shimfiɗe. “Ga kuma Sofa wazai kwana asama”? Ta fada tana dubansu Maƙe kafaɗa jemimah tayi”ni wallahi bazan kwana saman carpet ba, tsoro nake ji,” “Nima bazan Iya kwana ƙasa ba, dan Allah kibari mu kwana saman gadon mu duka” Azeeza ce tayi maganar tana marairaice mata fuska don taji tausayinta. Ta6e baki Ummi tayi”takura ke bana so, na saba kwana ni kadai asaman gado” Cikin sanyin murya batool tace”ni da parveen zamu kwana saman carpet din, Azeeza da jemimah sai su kwana saman gadon” Ummi tace”kinyi kyan kai, haka akeson babba yakasance mai sadaukarwa ga ƙannansa” ta fada tana sakin murmushin shaƙiyanci. “Kuje ku kwanto tom and jerry” ruƙo hannun jemimah Aziza tayi suka nufi gado atare suka haye saman mattress din. Fitowa parveen tayi daga toilet, duk ta jiƙe jikinta “Dakata daga nan kada ki 6ata min ɗaki da ruwa, meyasa baki tsane jikinki ba”? da wulakanci take Yi masu magana. Shiru parveen tayi batare datace komai ba sai batul ce tace”kiyi hakuri dan Allah, parveen ki koma toilet ki tsane jikinki, aunty ummi ki taimaka mata da kayan da zata sanya kafin gobe” Yamutsa fuska ummi tayi jin abunda batul tace”wato raini yafara shiga tsakanina daku ko?! Ke ba ki ji kunyar cewa In ara mata kayana ta sanya ba”! Idanuwan batul tuni sun ciko tab da ƙwalla “Kiyi haƙuri in na 6ata maki rai” tsoki ummi taja, Atsawace tace”kai ni dallah kuzo ku kwanta inaso zan kashe hasken ɗakina” Jikin parveen yai sanyi ga sanyi da take ji, gani suke kamar ummi ta canza masu kodan saboda sunzo kwana dakinta ne shiyasa take yi masu wulakanci” “Aunty ummi dan Allah ki kashe mana sanyin ɗakin kodan saboda parveen” harara ummi ta watsa mata “Bana iya kwana babu a.c, sai dai kuyi hakuri” ta faɗa tana faman sakin shu’umin murmushi. Gyaɗa kai Batul tayi tare da kallon parveen tace “bari na baki rigata ki sanya, ni saiki bani taki” dariyar shaƙiyanci ummi tasaki jin abunda batul tace “Kibarshi batul ke kuma fa”? Idanuwanta acike tab da kwalla ta furta hakan Murmushin yaƙe batul tasakar mata”kada ki damu dani, zan iya jure sanyin muje cikin toilet din ki canza rigar” Komawa cikin toilet din sukayi, Batul ta cire rigarta taba parveen ta sanya ita kuma ta zura rigar parveen da ruwa ya jiƙeta, ahaka suka fito hannunsu ruƙe dana juna. A kishingiɗe suka sami ummi saman gado ta ɗaura kanta saman pillow. Jemimah da azeeza suna can gefe ɗaya sun rungume junansu bacci tuni yajima dayin awon gaba da su. Ko kallon inda take basuyi ba, tabasu mamaki ga uban space a gadon amma ta hana su kwanciya. Asaman carpet suka kwanta, sanyi ya fara ta kurama Batul, Jikinta ya hau yin kakarwa, don mugunta ashe bayan shigarsu toilet ummi ta ƙara gudun A.c din dakin, tasan dole su nemi alfarmar ta basu bargo su lullu6e, don taji dadin zabga masu rashin mutunci Kasa runtsawa batul tayi atakure ta miƙe zaune tana faman ƙanƙame jikinta, tace”aunty ummi ki taimaka mana da bargo, sanyi muke ji” Tamkar bata ji me batul tace ba, saima ta runtse idanuwanta kamar mai yin bacci. Batul tayi tunanin bacci takeyi hakan yasa ta ƙara ɗaga murya tana fadin”Aunty ummi bargo dan Allah” banza tayi da ita, a ƙarshe sai dai batul ta haƙura, jikinta nata kakarwa ahaka ta kwanta, sanyi tamkar zaiyi mata illa, bacci ya ƙauracewa idanuwanta, ita kadaice acikinsu batasamu damar runtsawa ba, parveen tuni ta nutsa cikin baccinta. Sai da ummi ta tabbatarwa kanta cewa bacci ya ɗaukesu tukunna ta sauko daga saman gadonta, leƙen fuskokinsu tadinga yi don taga idon akwai wanda baiyi bacci ba, a lokacin batul ta runtse idanuwanta, sai tayi tsammanin tayi bacci. Lalla6awa tayi a hankali ta nufi jikin bango ta kashe switch din ɗakin, kafin ta dawo ta nufi gaban dressing mirror inda ta ɗaura wayarta ƙirar iphone Shu’umin murmushine dauke akan fuskarta, wayar ta dauka ta shiga call logs ɗinta ta dannama wata number kira bugu uku kafin mai wayar ya ɗaga Muryar babban mutunce ta dako mata sallama. “Yalla6aina ina da labari mai daɗi agareka”. 😳😳😳😳 The appearance of SALSABEEL😳🔥 On the other hand ƙasaitacciyar muryar mutumin ta furta mata”babu buƙatar ki sanar dani, na riga da nasan da zuwanki Nigeria”! Cikin nuna isa Ya furta mata hakan. Yayi matuƙar bata mamaki, muryarta da alamun ruɗi tace”tayaya akai kasan nazo nigeria? Bayan ni ban faɗa ma kowa ba”! “Saboda ina kallonki, duk wani motsinki a tafin hannuna yake Ummi” “Okey, idan har dagaske kana gani na, Yanzu faɗa min wasu kayane na sanya a jikina”! Ta faɗa yayin da take shafa kirjinta da hannu ɗaya. Ba zato ba tsammani taji yace”skirt launin yellow, tare da riga white colour sun yi tighting dinki, sun bayyana zazzafar surar jikinki mai jan hankalina” Har saida gabanta ya faɗi rass jin ya canka dai dai, tsabar ruɗu kiris Ya rage ta saki wayar hannunta, a firgice ta juya tana ƴan waige waige don taga ko yana acikin ɗakin ne! Muryarta adabarbace ta furta”am... ma tayaya akai kasan launin kayan dake a jikina”? Sautin wata shu’umar dariyar daya saki ce ta karaɗe kunnuwanta, “Meyasa kake yi min dariya? Ka amsa min tambayar dana maka”? “Kin manta dawa kike yin waya? Idan kin manta bari na tuna maki.....” bata bari ya ambaci ƙarashen zancen ba, tayi hanzarin katse shi da cewa”ni ba wannan na tambayeka ba...” Da kakkausar murya ya furta sunanta”Ummi!” amsa mashi tayi da na’am babe. “Duk duniya babu macen da ta isa ina magana ta katse ni sai ke! Meyasa”? Farfari tayi da ido tamkar tana agabanshi tace”saboda ka mutu akaina, babu yadda ka Iya dani, na zame maka ƙarfen ƙafa, mutu karaba takalmin kaza, sannan ni kadaice macan da zata Iya sarrafa ka cikin sauƙi nake rikatar dakai” ta ƙare maganar tana cizon lower lip dinta da tongue dinta, cikin jin shauƙin shi. Duk wannan wayar da take Yi, Batul tana sauraronta, baiwar Allah, jikinta ya gama sandarewa da sanyi, sai kakarwa takeyi, tuni azababbiyar mura ta rufeta, kasa jurewa tayi gani take kamar sanyin zai halakar da ita, hakan yasa ta yunkura ta miƙe cikin duhu ta nufi ƙofar fita daga ɗakin ta fuce ba tare da sanin Ummi ba. Sautin hucin numfashinshi har ta cikin kunnanta, shiru bai tanka mata ba, Hakan Yasa tace”Naji sautin numfashinka Ya cika min kunne na, ko jarabar taka ce ta motsa? gashi bana akusa balle in ɗebe maka kewa” Muryarshi ƙasa ƙasa ya furta”Ummi, muryarki kaɗai tayarmin da jarabata take Yi, abuƙace nake dake, Inason ganinki ayanzu ya za’ae” Shu’umin murmushi tasaki, muryarta da kwarkwasa tace”babu halin ganina, nayi maka nisa, kayi tunanin zan baka damar ganina cikin sauƙi? Bayan irin wahalar daka bani? Ka tafi ka barni da kewarka, ba ka damu dani ba, kasa ina kokwanton anya dagaske kana ƙaunata? Saboda kawai mun samu sa6ani shine ka nesanta kanka dani? Ka hana rayuwata sukuni.....” bata samu damar ƙare maganar ba, ya katse mata hanzarinta”bazan iya jurewa ba, nayi kewar jikin ki, nasan ni mai laifine agare maki amma inaso ki sani kina araina. Ta6e baki tayi tana sauraron shi “Ki bani dama, zan gyara kuskura na, adaran nan” dariyar shakiyanci tasaka mashi”fadamin me zaka yi min” “ zan kiraki video call, i wanna show u something that will make u happy” Murmushin gefen fuska tasaki”okey my baby, amma fa kada ka nuna min abunda zai hanani runtsawa adaren nan” ta ƙare maganar tare da juyawa ta nufi toilet ta bude kofa ta shige ciki. *CHIEF OWAIS✊❤* Babu alamun zai iya runtsawa a daren yau, duba da abubuwan da suka sha mashi kai, idan har bai shawo kan matsalar ba to kuwa hankalin shi bazai ta6a kwanciya ba, halin shi ne hakan. Safa da marwa yake yi a room dinsa, Ya zura hannayensa biyu cikin aljihun short dinsa, babu riga a jikinshi hakan ya bayyana zazzafar surar ƙirjinshi, jefi jefi yakan dan wurga eye balls dinsa kan wall clock din dakin domin duba lokaci, akan kyawawan idanuwanshi ƙarfe 1:30 na dare ta buga, a hankali ya kau da idanuwan daga kan agogon. Alert ne Ya shigo wayarshi, a hanzarce Ya nufi wayar tashi dake ajiye saman bedside drawer, ya duba ta, ƙofar room dinsa ne ake buƙatar shigowa, Unclock button ya danna, nan take ƙofar ta soma zugewa, agaban dressing mirror Ya tsaya yana jiran ƙarasowar su. Big guy ne tare da Mutumin nan, nesa da bayanshi suka tsaya tare da Buga ƙafa suka sara mashi atare, cikin girmamawa Big guy ya soma yi mashi magana “Assalamu alaikum Sir Barka, yanzu muka samu damar ƙarasowa gidan, aimin afwa na 6ata lokaci” Koda big guy yai maganar, basu samu damar ganin fuskarshi ba, saboda Ya juya masu baya, ta cikin mirror yake dubansu. “Yalla6ai fatan na same ka lafiya” mutuminne ya furta maganar. Lumshe idanuwanshi ya ɗanyi kafin calmly ya furta”barka da zuwa, ina fata Big guy ya fada maka komai, Dangane da halin da ɗan uwanka ke a ciki” Jinjina kanshi yai cikin girmamawa yace”eh yalla6ai, ya sanar dani komai, Inaso na fara ganin shi” “Okey, Big guy you can take him to the room, but before that....” gently ya waiwayo baya batare daya kallesu ba. Ya ɗaura da cewa”Ina so na saurari komai da zaku tattauna” Amsa mashi yai da okey. “You Can Go” amsa mashi sukayi da toh, kafin suka juya suka nufi ƙofar fita dakin. Bayan fitarsu, hayewa yai saman shimfiɗeɗɗan gadonshi, yayin da yake fuskantar jigunannan ceilling din room nashi. Slowly ya daura wayar hannunshi on his broad chest, yadan lumshe sexy eyes dinshi. Idan muka koma 6angaren big guy da mutumin, cikin takun sauri suka nufi elevator, bayan sun shiga tayi sama dasu zuwa second floor ta sauke su, fitowa sukayi daga ciki, a hanzarce suka nufi bedroom din Danish. Abakin ƙofar dakin suka dakata dayin tafiyar. “Ina buƙatar face mask” mutuminne Ya furta maganar. Kallon shi big guy yai”meyasa? Ko bakasan taga fuskarka ne” Jinjina kanshi yai alamar eh big guy yace”bazai yiwu ba, dalilin dayasa nace hakan, yarinyar bata da kwanciyar hankali daga ita har yaron, silar ganinka da zasuyi shi zaisa suji sauƙin radadin abunda ke damunsu, Ina fata ka fahimce ni” Gyaɗa kanshi yai”na fahimta ba damuwa mu shiga ciki” Dafa ƙofar room din dakin big guy yai da tafin hannun shi, a hankali ƙofar ta zuge kanta, shi yafara shiga kafin mutumin yabi bayanshi, tunkafin su ƙarasa shiga ya hango abunda ya basu mamaki da al’ajabi, har kallon juna sukayi kafin suka mayar da dubansu garesu, wato abunda yabasu mamaki ƙarfin halin Unaisah, Ta lullu6esu da bargo daga ita har Giant snake din, kana Iya hango ƙafarta da jelarsa. “Ban ta6a ganin ƙauna irin wannan ba, arayuwar mu ta zahiri, ƙarfin halin unaisah da jarumtakarta ba ƙaramin burgeni suke yi ba” big guy ne ya fada. Mutumin yace”Ni shaida ne akan ƙaunar dake a tsakaninsu, tamkar anta da jini ....” bai ƙare maganar ba, big guy yai mashi nuni da abun sauraron daya sanya a kunnanshi, da sauri Yaja baki yai shiru don ya fahimci abunda yake nufi wato chief yana sauraronsu ta hanyar earbuds din kunnan big guy. Abakin gadon suka dakata suna ƙare masu kallo. Kiran sunanta big guy yai”Unaisah! Muna son yin magana dake” shiru babu alamun zata farka Ɗaga murya yai da karfi ya ambaci”Unaisah Angel, ki tashi zamuyi magana” Har cikin dodon kunnanta kiran ya kai mata, firgigit tafarka tana sambatun ambaton sunan Danish, saboda ta kwanta dashi aranta, jin shi ajikinta yasa taji hankalinta Ya kwanta, sai kuma ta fara tunanin wanene ke kiran sunanta, kafin brain dinta ta tariyo mata muryar mai magana ya kuma cewa”Ni ne Big guy, ki fito daga cikin bargon muyi magana” ya fada ne don ya lura tafarka duba da yadda bargon da suka lullu6a yake motsi. Ta rasa ya zatayi ta raba jikinta daga giant snake din, Ya shige mata sosai, sai faman jan numfashi take Yi da sauri da sauri. “Kinyi shiru Unaisa!” muryarta da kasalar bacci ta soma magana “Ƙoƙari nakeyi in fito, ya rurruƙeni ne” murmushin gefen fuska mutumin ya saki jin muryar daya daɗe yana kewarta. Kallon big Guy yai”bari na taimaka mata” clapping hands dinsa yai sau uku, wani abun mamaki macijin ya farka, Ya warware jikinshi daga nannaɗetan da yai, ya soma ƙoƙarin yakice bargon don ya fito, hannu mutumin yakai Ya ruƙo ƙarshen bargon ya yaye shi gaba daya ya jefar dashi gefe ɗaya. Biji biji Unaisah take dubansu, idanuwanta sun kumbura sunyi mata nauyi bata iya ganin su dakyau, a kasalance ta miƙe zaune tana faman sauke ajiyar zuciya, baiwar Allah gyaran gashin da take ta kaffa kaffa dashi don kada ya tarwatse tuni yafara fita hayyacinshi. Abun da ya ɗaure ma Big guy kai, ganin yadda macijin duk yabi ya ruɗe, ƙoƙarin saukowa yake Yi daga saman gado, kuma ga dukkan alamu wurin mutumin yake son zuwa, Allah sarki ɗan uwa yaga ɗan uwanshi. Hawa saman gadon mutumin yayi, agaban giant snake din Ya tsaya, cikin rauni na murya furta”ko baka furta min ba, nasan halin da kake aciki Danish! Saboda ina jin raɗaɗin acikin zuciyata, amma kada ka damu, Allah yana atare dakai muma kuma muna atare dakai, wallahi duk runtsi duk wuya ba za su ta6a cin galaba akanka ba, tunda har su ka yi kuskuren haɗaka da ƙaddararka wadda tayi silar barinka *GIDAN KURKUKUN ƘADDARA!!* Tun da ya fara magana Unaisa ta dabarbar ce, tarasa gane a ina ta ta6a jin muryarnan, sai da yazo ƙarshen maganarshi ya amabaci sunan kurkukun ƙaddara, tamkar ya buga mata guduma a kirjinta, la66anta na rawa ta soma ambaton sunanshi”SAL... SABEEL! SALSABEEL! MAFARKI NAKE YI KO GASKE NE KUNNUWANA SUKE JIYO MUN MURYARKA” amatuƙar ruɗe sai faman ƙoƙarin murza idanuwanta take da yatsun hannunta duk don ta samu damar ganinshi. Muryarshi ce ta dakatar da ita daga ambaton sunanshi da take Yi “Angel! Nine ba mafarki kike yi ba, SALSABEEL ƊINKU NE NA GIDAN KURKUKUN ƘADDARA” daƙyar ta iya ware idanuwanta akan fuskarshi, kwamtsa duk ta kakkama idanuwanta saboda kukan da tayi idon ciwo yake mata, sosai ta zazzaresu tana dubanshi tamkar wadda taga abun tsoro, ruɗani ya hana ta yi magana, lamarin yayi mugun ɗaure mata kai, ko amafarki bata ta6a tsammanin hakan zata Iya faruwa ba, kamar yadda take kallonshi haka shima yake kallonta, fuskarshi dauke da murmushi, yayin da idanuwanshi suka cicciko tab da ƙwalla, macijin kuwa tuni Ya ɗaura kanshi saman laps din salsabeel. Miƙa mata hannu yai alamar tazo gare shi, ta zabura ta nufeshi, haɗi da faɗawa saman kirjinshi ta ƙanƙameshi, lokaci ɗaya ta fashe da matsanancin kuka mai tsuma zuciya. Big guy dake atsaye yana kallonsu zuciyarshi tuni ta karaya, duk irin dauriyar shi baisan sa’adda ƙwalla ta cika idonshi ba. Muryarshi arauna ce ya furta”Sir, are you listening?” On the other hand, chief owais dake a kwance saman tattausar mattress na gadon shi, Ya amsa mashi da”Yes, I’m listening.” Ajiyar zuciya big guy ya sauke, ya fahimci sautin kukan Unaisah ba ƙaramin ta6a zuciyar chief yai ba, tun daga kan yanayin muryarshi. Bubbuga bayanta Salsabeel yai da hannun ɗaya cikin sigar lallashi, yayin da ɗayan hannun nashi yake asaman kan giant snake din” Tamkar yana ƙara tunzurata, kuka take yi na fitar hayyaci. Big guy dake amanne da earbuds, muryar Chief ce ta janyo hankalinshi ga sauraronshi” “Tell her to stop crying, I don’t want to hear it.(Ka faɗa mata ta daina kuka, bana son ji”) amsa mashi yai da toh, kafin ya ɗaga murya yace da salsabeel”ka lallashi ƴar uwarka, tadaina yin Kuka, umarni ne daga chief” Jinjina mashi kai yai, da karyayyar murya ya ambaci sunanta”Unaisa, Ki daina kuka, danish baya jin dadi, ya fadamin idan baki daina ba shima zai fara kukan saboda kina ƙara tayar mashi da hankali” jin wannan maganar yasa tayi saurin haɗiye kukanta, a hankali ta dago da kanta tana duban fuskar salsabeel, tsananin tausayinta ne Ya kamashi, kumatunta sunyi jawur, pink lips dinta sunyi suntum dasu, tasha kuka baiwar Allah. Cikin shessheƙar kuka take fadin”Sal... Sal... Sabeel, ka fadamin ya akai ka tsira daga gidan kurkukun ƙaddara? Ina ƴan uwana suke? Ina deeja take da mubeen? Suma sun rayu ko sun mutu? Inaso nasani, gaba ɗaya na rikice” Shafa gefen fuskarta yai da hannun shi, Cikin sanyi murya yace”Unaisah, ki kwantar da hankalinki, yanzu bana acikin natsuwar da zan Iya yi maki bayanin komai, nayi maki alƙawarin zan fayyace maki komai idan Danish ya dawo mutun, amma fa sai kin daina yin kuka, kin kuma natsu” jinjina mashi kai tayi alamar zata daina. “Danish yana yi min magana, yanzu haka” ba ta yi mamakin jin abunda yace ba, tunawa da cewa shima giant ne, abune mai yiwuwa suyi magana ta sirri acikin zuciyoyinsu harma su Iya jin juna, big guy ne kadai al’ajabi ya cika shi, tun yana daga tsaye har yakai ga samun wuri saman sofa din dakin ya zauna yana dubansu “Ina son jin me yake fada maka” acewar big guy A lokacin Unaisah ta mayar da kanta saman kirjinshi, ya tallabeta da hannu ɗaya, zazza6i jikinta sai ƙara nunkuwa yake yi. Calmly Salsabeel Ya soma faɗa masu tattaunawar da suke Yi da danish. “Ya faɗamin bayason unaisah tana yin kuka, Zuciyarshi tana karaya, sannan yana roƙona akan in taimaka mashi ya rikiɗa ya koma mutum baya son ganinshi a suffar maciji, yana jin ƙyanƙyamin kanshi, yana acikin mawuyacin hali na ƙunci da raɗaɗi, idan har ya ɗauki tsawon lokaci bai dawo mutum ba Giant’s heart dinshi zata motsa ne, idan kuwa ta motsa gaba ɗayanmu zai Iya cutar damu, saboda awannan matakin babu wanda zai Iya sarrafa shi har ita unaisah” hankalin Unaisah ba ƙaramin tashi yai ba jin abunda salsabeel yake fadi, ita azatonta giant’s heart dinshi ne ya motsa shiyasa har ya iya rikiɗa ashe ba zuciyar bace ta motsa. Ba ita ba hatta big guy ya ɗan girgiza da jin kalaman salsabeel, har saida ya daura eye balls dinshi akan macijin dake a nannaɗe saman gadon har yanzu bai ɗago da kanshi daya daura saman laps din salsabeel. Cigaba da yin magana yayi”danish yana acikin damuwa, ina jin shessheƙar kukanshi, roƙona yake yi akan mu taimaka mashi ya canza halittarshi ya gaza rikiɗa baisan ya zaiyi ba, bayason ƴan uwanshi su guje shi, idan kowa ya ƙyamace kamar yadda ya ƙyamaci kanshi hakan zai yi silar motsawar giant’s heart dinshi kuma idan ta motsa zai nesanta kanshi da kowa saboda baya son ya cutar da mu, zai koma inda yasan baza a ƙyamace shi ba, yana nufin tushen shi gidan kurkukun ƙaddara....” tunkan salsabeel Ya ƙare maganar, Unaisah ta tari numfashinshi “A’a danish, ka daina fadin zamu ƙyamace ka, Ni yanzu ma nafara ƙaunarka saboda ina tausayin rayuwarka nasan cewa bayin kanka bane, mugayan mutanan can ne suka assasa faruwar hakan duk don ka koma garesu, sunyi maka hakanne don mutane su guje ka kai kuma kaji ka ƙyamaci kanka saboda sunsan ta wannan hanyarne kadai zakaje gare su, Ni kuma wallahi bazan ta6a bari hakan ta faru ba, Yanzu nafara sonka, Danish ba maciji ba, kowace irin halitta zaka koma a duniyar nan ina atare dakai, har abada har ƙarshen numfashina, kai koda ace zaka dinga cutar danine bazan rabu dakai ba, sai inda ƙarfina ya ƙare, akanka babu gudu babu ja da baya wallahi bazan barka ba.......” kukane yaci ƙarfinta har ta kasa ƙarasa maganar. Macijin yana sauraron duk abunda take cewa, ya ɗago da kanshi daga saman laps din salsabeel, mitsi mitsin idanuwanshi na fuskantarta. Big guy bazai Iya jurar tausayinsu da yake ji ba, Jikinshi yai sanyi laƙwas kamar wanda aka zare ma laka. Duk abunda ke faru Chief Owais Yana sauraronsu, yayin da yake a kwance cikin bedroom dinshi saman gadonshi, Muryar unaisah ta cika mashi kunnuwanshi tamkar agabanshi take Yin kukan, A hankali ya dauki wayarsa daya daura saman broad chest dinshi ya dawo da ita saitin kunnanshi, don yaji dadin sauraronta dakyau. Shafa sumar kanta Salsabeel yai da hannunshi”Ki daina kuka yace min in fada maki bayaso” da sauri ta hadiye kukanta tana fadin”toh na daina, bazan ƙara ba my Man,” ta faɗa tana kallon macijin har girgiza mata kai yake yi, batasa sa’adda tasaki murmushi ba, ta fahimci lallashinta yake yi. “Abun da Unaisah ta faɗi gaskiya ne, tsammaninmu yazo ɗaya, azzaluman kurkukun ƙaddara ne suke sarrafashi ta ƙarfi da yaji bada son ranshi ba, kuma sunayi mashi hakanne don mutane su ƙyamace shi kowa ya gujeshi, shi kuma zaiji ya tsani kanshi saboda ƙyarar da mutane suke yi mashi, daga haka zai fara tunanin komawa prison wannan shine abunda suke ƙoƙarin yi” Tun da yafara magana big guy yake jinjina kanshi alamar gamsuwa da jawabin shi, Muryar chief ce ta sa shi dakatawa yana sauraronshi, babu mai iya jin voice dinshi sai shi da yasanya abun sauraron akunne. Cikin harshen turance yace “Ka faɗa mashi, muna atare dashi, bazamu ta6a rabuwa dashi ba har iya ƙarshen numfashinmu, babu wanda zai ƙyamace shi, duk runtsi zamu kasance atare dashi don mu bashi ƙwarin gwiwa kuma zamu tallafa masa don ganin mun raba shi da miyagun dake atare dashi, in sha Allah komai yazo ƙarshe ya kwantar da hankalinshi” Jinjina kai big guy yai haƙiƙa yaji daɗin kalaman Chief owais, magana yasoma yi masu”chief yace in isar mashi da sakonshi zuwa ga Danish .....” mayar da hankalin sukayi akanshi suna sauraronshi, a tsanake ya faɗa masu abunda chief yace. Wani irin farin cikine ya lullu6e Unaisah, har cikin ranta taji daɗin kalaman shi duk da batasan wanene shi ba, ba ta ta6a ganin fuskarshi ba, ko ɗazu da taji an dauketa lokacin data lullu6e Danish da bazar rigarta batasan wanene ya dauketa ba saboda bata acikin hayyacinta, idanuwanta sun makance. “Wanene chief? Yaushe ya faɗa maka sakon”? Ta jefa ma Big guy tambayar yayin da take dubanshi. Nuna mata earbuds din kunnanshi yai da yatsan hannun shi, nan take ta gane abun jin magana ne a ear dinshi tanan suke yin communicating da shi. Nauyayyar ajiyar zuciya ta sauke muryarta adisashe ta furta”idan na samu natsuwa zaka kaini wurinshi muyi mashi godiya” Big guy yace”a’a shi ba’ayi mashi godiya, sai dai idan kinason ganinshi zan nema maki izni daga gare shi, amsa mashi tayi da toh inaso” Kallon salsabeel Yai”menene mafita? Muna son musan wani hali yake aciki” kafin ya bashi amsa unaisa tayi saurin cewa”nayi magana da boss man, na fada mashi inda na ajiye wasiƙar adreshin gidanku daka bani, inda zamu samu ruwan zam zam din” Fuskarshi da matsanancin damuwa yace”ai babu zamzam din nan! Tun lokacin da kuka faɗa hannun sojin america suka damƙa case dinku hannun hukumar Isod, nasan da zamanku, munyi ƙoƙarin samu ruwan zam zam saboda gudun kada giant’s heart dinsa ta motsa, sai dai kash lokacin da muka je gidanmu na kaduna tare da jami’an isod bamu samu komai ba, Gidan ma an canza mashi kamanni, magada ne suka koma da zama cikinshi, su kansu da mukaje basu san Wanene ni ba, munyi ƙoƙarin yi masu bayani amma sai suka fada mana cewa babu komai na habibullah dayai saura agidan....” aruɗe Unaisah tace”ya zamuyi yanzu”? Ta faɗa tana zazzare idanuwanta. Salsabeel yace”akwai hanyoyi da dama, da zamu Iya samun ruwan zam zam sai dai bamusan wasu irin addu’o’ine ko ayoyin alƙur’ani ake amfani dasu ba wurin tofe ruwan ba” ya faɗa yana dubanta. “da za’a samu babban malamin addini kamar mahaifina habibullah ina da tabbacin zai iya taimaka mashi” Shiru suka ɗanyi suna kallon kallo atsakanin Salsabeel da Unaisah, ga macijin yayi kwance saman jikinshi daya nannaɗe. Chief Owais dake a kwance saman bed matress dinsa Yana sauraronsu, ƙarar shigowar message ce ta janyo hankalinshi ga buɗe eyes dinshi, phone dinsa Ya ɗago da ita yana duban screen din. Text message ne aka turo mashi, yayi mamakin ganin saƙon Uncle dinsa, A irin wannan lokacin ƙarfe biyu da rabi na dare, hakan na nufin bai runtsa ba. Karanta text message din Ya soma yi acikin zuciyarshi. _”My son, I can’t sleep because of that child, I don’t know why I’m so worried about him. Please help me. I want to see him before I go back to Canada next week. na jaraba kiran layin Sheikh imam munyi magana dashi ashe baya kasar ya tafi sudan, na nemi alfarmar inason ganinshi da gaggawa, yace min in sha Allah zai dawo ƙasar a gobe, saƙo daga Prime minister Hateem Obinna_ Bayan kammala karanta message din, Owais Yai mashi reply kamar haka _”Nima ban runtsa ba kawuna, saboda yaron, ƙoƙarin da muke Yi kenan don ganin mun taimaka mashi ya canza halittarshi zuwa ta suffar mutane, amma inaso ka kwantar da hankalinka ka yi bacci, in sha Allah zaka haɗu dashi kafin komawarka kanada, har ma kuci abinci atare”_ Tura mashi sakon yai, within minutes saiga wani sakon daga prime minister _thank u, sai mun hadu gobe da wuri zan shigo gidan naka idan sheikh iman ya ƙaraso_ Lumshe ido owais yai, A hankali ya furta sunan big guy, on the other hand big guy ya amsa mashi da na’am yalla6ai” “Sako ya shigo min daga Uncle Hateem, Zuwa gobe da safe Sheikh Imam zaizo Nigeria, yayi tafiya ne zuwa sudan, ka yi ma brother din yaron nan magana ya tambaye shi idan yana jin yunwa ya fadi me zai iya ci akawo mashi” amsa mashi yai da toh. Ya mayar da dubanshi ga su salsabeel”tun da yana jin maganarka ka tambayar mana shi me zai Iya ci akawo mashi, sannan pls kace mashi ya kwantar da hankalinshi zuwa gobe insha Allah sheik imam zai shigo Nigeria, shahararran malamin addinine muna da tabbacin zai Iya taimaka mashi” Gyaɗa kai salsabeel yai”ay yana sauraronka, Yanzu haka magana yake yi min. “Meyasa kuka harbe shi? Duk da harsashin bai fasa jikinshi ba yayi mashi illah saboda babu kakin giant a jikinshi” Hankalin Unaisah dana Big guy ya tashi matuƙar, muryarta na rawa ta furta”meya faru dashi? Yaji ciwo ajikin shi” “Bazan Iya sani ba, sai ya dawo suffarshi ta mutane tukunna zamu ga illar da yayi mashi, sannan ya fadamin yana son kayan marmari su kadai yake sha’awar sha” Damuwace ƙarara akan fuskar Angel”meyasa bazai Iya cin abinci ba”? Ta fada tana duban salsabeel. “A halin yanzu Danish dinki, ba mutun bane Giant snake nake, bazai Iya cin kalar abincin mu ba, har sai ya dawo cikakken mutun. Kwa6e fuska tayi tana duban kan macijin, har yanzu bai dagoba tunda ya kwantar da kanshi saman jikinshi daya nannaɗe. Miƙewa tsaye big guy yai”ka zauna atare dasu, zan je na kawo mashi kayan marmarin” amsa mashi salsabeel yayi da toh. Bayan fitar big guy, ta ƙura ma salsabeel ido, har yanzu mamakin ganinshi take yi, abubuwa dayawa sun cunkushe mata brain dinta, tana son jin ya akai ya tsira daga kurkukun ƙaddara? Shin ya sauran ƴan uwansu suka ƙare sun mutu ko sun rayu? Tayaya Akai Ya haɗu da jami’an da suke kula dasu? Ko dai dama shima jami’insu ne!? ta ɗaura mashi alamar tambaya, tadai haƙura ne har zuwa time din da danish zai rikiɗa ya dawo mutun donjin amsar tambayoyinta, kamar yadda take kallon Salsabeel haka shima yake kallonta, yayi kewarsu sosai, kuma yaji dadin ganinsu, da ransu da lafiyarsu, bakomai yake tunawa ba face ranar daya fara haduwa da ita har yakaita dakin da suka tattauna, da kuma ranar da ya ceci rayuwarta lokacin da matsafa sukayi mata wanka da jini, ranar da ta azabtu ta galabaita, Allah kenan mai yadda yaso mai jujjuya al’amurra, yanzu tamkar ba’ayi ba, tayi haske abunta gwanin kyau har girma ta ƙara mashi akan yadda suka yi rabuwar ƙarshe a kurkuku. Murmushi yasakar mata, itama ta mayar mashi da martanin murmushin, ya fahimci aƙagare take da son jin labarin ƴan uwanta daga gare shi. *PRISONERS💔✍️* Tun bayan fitowar Batul daga ɗakin Ummin america, a tsakar dare ta nufi down stair, baiwar Allah tana tafiya jikinta na kakarwa, hatta haƙoranta kerma sukeyi suna hadewa jikin juna, tsoro take ji ita kaɗai kamar aljana, sai faman firgita take yi gani take yi kamar macijin zai kawo mata hari. Daƙyar take iya taka ƙafarta saman floor din falo, ga wani azababban tari daya farmata. Sam ba ta ji takun tafiyar mutum ba, saboda hankalinta ba akwance yake ba, sai ƴan waige waige take yi tana faman hadiyar yawu. Yayi mamakin ganin ɗaya daga cikin yaran tana yawo a tsakar dare, babu mayafi a jikinta, ƙura mata ido yai a ƙoƙarinshi naya gano wacece acikinsu, ya rasa gane batul ce ko Unaisah, saboda launin gashinsu kala ɗaya ne ga kuma nannaɗewar sumar kan nasu daya kasance iri ɗaya, zuciyarshi ce ta raya mashi cewa Unaisah tana adaki fa ya barota tare da salsabeel wannan ba ita bace sai dai ko ƴar uwarta ce Batul. Da ƙarfi ya ambaci sunanta”Batul” rass taji gabanta Ya faɗi, a firgice ta waiwayo don ganin wanene, karaf idanuwanta suka sauka akan fuskar big guy dake sanye cikin face mask,l. Tsabar tsoro da ruɗu yasa ta zabura zata watsa da gudu, sai dai kafin tayi hakan yai saurin haura ƙafa ya damƙo damtsen hannunta ya janyota zuwa jikin shi, ƙanƙame shi tayi atsorace ga tari da take yi. Lamarin ya ɗaure mashi kai, ɗago da kanta yai daga saman ƙirjinshi ya furta”ke! Daga ina kike? Ya akai kika fito daga ɗaki”? Daƙyar ta Iya buɗe baki tace”sanyi nake ji babu bargo shine na fito zani ɗaki in ɗauko” “Awani ɗaki kike”? “Ɗakin aunty ummi, boss man ne yace muje can mu kwana, saboda munajin tsoron kwana ana mu dakin” “Meyasa baki tambayeta ta baki bargo ba”? A tsoroce take yi mashi magana”tayi bacci ne, kafin ta kwanta ma saida nace ta taimaka ma parveen da kaya ta sanya saboda tayi ma nata fitsari sunjiƙe sharkaf amma taƙi bata sai dai ni na cire nawa muka yi musanya ta bani nata, kuma ɗakinta sanyi sosai” Tunda tafara magana Big guy yake jinjina kanshi, ga dukkan alamu ya fusata matuƙa, bashi ba hatta chief owais dake acan room dinsa yana sauraron maganganunsu. Ruƙo hannun Batul yayi acikin nashi ya juya da ita suka nufi ɗakin. A lokacin Ummin america tana ƙoƙarin fitowa daga cikin toilet, ta gama sheƙe ayarta da gardin daya kirata awaya, sai faman sauke ajiyar zuciya take yi, zura ƙafarta keda wuya hasken ɗakinta Ya kama, a firgice takai idanuwanta kan masu shigowa ciki, tunda tayi arba da big guy tare da batul gabanta yai mugun faɗuwa. Wani irin kallon tuhuma yake jefa mata, ranshi amatuƙar 6ace ya soma magana. “Ke baki da hankaline? Kin ajiye yara aɗaki kin kure masu sanyin A.c ? Idan ƴa’ƴankine na cikinki zaki Iya yi masu haka”? Muryarta adabarbarce tace”am..ba haka bane ni ai bansan basu iya jure sanyin A.c din ba, na saba kwana.....” bata ƙare maganar ba, Ya daka mata tsawar data firgitar da ita, sakin hannun batul yai ya matsa kusa da ita, abunda wani ɗa namiji bai ta6a gigin yi mata ba, da yatsan hannunshi ya nuna ta”ki shiga taitayinki, This is the last time I’ll warn you. Don’t be reckless in your work. We don’t accept mistakes, koda gigin wasa kada ki kuskura ki ƙara maimaita laifin nan” yana huci ya faɗa “Yarinya harta fara mura tana tari! Ke ko ajikinki ai nayi tunanin zanzo na sameki kina bacci ashe idonki biyu hakan na nufin da gangan kika kure sanyin A.c din dakinki, Ke bari kiji bana so gobe da safe inji yarinyar nan tana yin mura, ki san yadda zakiyi ta dawo daidai, bama itaba hatta sauran ƴan uwanta kada ki bari ɗaya daga cikinsu ya tashi da mura, idan ba haka ba zaki fuskanci hukunci mai tsanani daga hannun chief.. “ hankalin ummin america ba ƙaramin tashi yai ba, duk tabi ta susuce musamman daya ambaci sunan owais, muryarta na rawa take fadin”na kar6i laifina bazan ƙaraba, kuma aini bansan sanyin zaiyi masu illa ba...” bai bari ta ƙare maganar ba ya dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannu”bana sonji, kawai kiyi abunda ya dace don ki ceci kanki, nabarki lafiya” afusace ya juya zai bar dakin har ya kusa fita karaf idanuwanshi suka sauka akan parveen dake kwance saman carpet tana yin bacci, Arude ummi ta furta”yanzu zan maida ta saman gado, bansan ya akai ta faɗo ƙasa ba” wani ɗan iskan kallo big guy ya watsa mata. Kafin ya maida dubanshi ga batul”ke ina yar uwarku take? ya akai naga ku huɗune? Where’s hannah”! Sai daya ambaci hakan batul ta tuna da babu hanna acikinsu, waige waige ta soma yi jikinta na rawa tace”bansan a ina take ba, tare da ita muka nufo dakin aunty ummi, ni na ruƙo hannunsu ita da Parveen bansan ta kufce min ba, dama aruɗe take” Gyaɗa kanshi yai”okey, wuce kije ki kwanta, zanje na nemota” ya faɗa tare da juyawa ya kalli ummi dake ta rawar jiki”ina ƙara jaddada maki kada ki bari yaran nan su wayi gari babu lafiya, idan kunne yaji jiki ya tsira” yana fadin hakan ya haura ƙafa yabar ɗakin. Fitar shi keda wuya, Ummi ta ɗaure fuskarta tamau babu annuri, ranta ya 6aci matuƙa, hankalin batul ba ƙaramin tashi yai ba ganin tana tunkarota, girgiza kai tadinga yi tana nufar bango harta kure mashi, “Dan Allah kada ki ta6ani, bani da lafiya...”daƙyar ta furta maganar, “Ni ki ka kai ƙarana a wurinsu? Yaushe kika fita daga dakin munafukar banza, harni zakija ma bala’i ina zaman zaman lafiyana? Kinsan wacece ni? Don ubanki! Girgiza kai batul tayi tuni hawaye sun wankan fuskarta”aunty ummi kiyi hakuri bazan ƙaraba, dan Allah kada ki ta6ani” Tsawa ta daka mata”kashe ki zanyi, kinyi kuskura batul da kika gaya mashi abunda ya faru tsakanina daku, wallahi sai kinyi danasanin sanina da kikayi, don kuwa daga rana irinta yau bazaki ƙara dariya ba zan ƙuntata maki har sai kinji kin tsani kanki” Fashewa batul tayi da kuka mai tsuma zuciya, saboda rashin imani ummi ta sanya hannu ta shaƙi wuyanta tamkar zata kashe ta, “Jibarki dallah, jahila dake, bakisan komai ba sai cin abinci da bacci, ni ban ta6a ganin daƙiƙiya ba irinki” “Batul ! Batul! Meyasa kike kuka”? Jin muryar Parveen yasa ummi yin saurin sakin wuyan batul, jiki ba ƙwari ta sulale ƙasa tana cigaba da yin kuka “Kiyi min shiru idan kika bari wani yaji wallahi saina naƙasa ki wawuya” da sauri batul ta haɗiye kukanta, baiwar Allah hada sanya hannu ta share hawayen fuskarta. Shu’umin murmushi tasaki kafin ta juya tana kallon parveen data farka tana faman mutsustsuke idanuwanta “Ke tashi ki koma saman gado ki kwanta” muryar ummi ce ta fargar da Parveen ta ware idanuwanta sosai akan fuskokinsu Muryarta da kasalar bacci tace”batul make faruwa? Meyasa kika zauna a ƙasa”? Tai maganar tana kokarin miƙewa da niyar taje wurin Batul, ummi ta dakatar da ita”cewa nayi kije ki kwanta saman gado, babu abunda ya sameta, kaya zan bata ta sanya ajikinta” jiki asanyaye parveen ta nufi gadon donta kwanta sai dai hankalinta bai kwanta ba da yanayin data riski batul “Parveen ki kwanta kiyi bacci, lafiyata ƙalau, yanzu aunty ummi zata bani kaya in canza na jikina sai inzo mu kwanta a gadon” ajiyar zuciya parveen ta sauke jin batul tayi mata magana, hayewa tayi saman gadon ta kwanta batare data rufe idanuwantaba. Ta6e baki ummi tayi tare da mayar da dubanta kan Batul, badan taso ba tace”shashasha, Ki jirani in dauko miki kayan” cikin sanyin murya batul tace”toh” Wuce wa tayi cikin ɗakin can inda katafaren closet dinta yake, ta bude ta dauko jibgegiyar sweater tare da dogon wando, ta haɗo da duvet, ta nannaɗosu ta dawo inda batul take a zaune ta wurga mata su saman jikinta “Salon kuma kiyi min ƙazanta, ni bana sharing kaya da wani don yazamarnin dolene” ta faɗa tare da juyawa ta nufi gaban mirror inda ta daura A.c remote ta kashe ta gaba daya, ta kunna masu room heater, duk don saboda gudun kada gobe aji basu lafiya, shiyasa tayi hakan. Miƙewa batul tayi hannunta ruke da sweater din, ta zame hannun doguwar rigar jikinta, da dabara ta zura sweater din, tayi mata girma, haka wandonma yayi mata faɗi, ahaka ta sanya su, kafin ta cire rigar jikinta, anan ƙasa tabarta, ta nufi saman gadon ta haye gefen parveen ta kwanta, ta lullu6e masu bargon su dukansu, kafin ta rungume parveen a jikinta, duk don ta samu sauƙin raɗaɗin da take ji, ta tsorata da ummi kalaman da tayi mata sun tsaya mata arai, fargabanta kada ta kashe ta, tuni idanuwanta sun cicciko da ƙwalla Cikin muryar raɗa parveen take yi mata magaba”batul tayi maki wani abu ko? Ni naji ajikina” daƙyar ta iya furta”kiyi shiru parveen kada tajimu, ni batayi min komai ba, bana jin daɗin jikinane” Sautin kuskus din da suke yi ne yaja hankalin ummi ga kallon bargon da suka lullu6a dashi atsawa tace”kada in kuskura in ƙarajin maganarki! Ko tari bana sonji” tsit sukayi shiru suna faman ƙanƙame junansu ......... *Daga Alƙalamin Boss Bature💋✍️* Idan muka koma 6angaren Hajiya saratu data garƙame kanta acikin toilet, tsoro da fargaba sun hana ta sukuni, ta haɗa uban gumi zufa ta ko’ina take tsastsafo mata, ga wani takurarran bacci daya addabi idanuwanta, ta rasa ya za ta yi, ta kasa tsaye takasa zaune, sai zarya take yi acikin toilet, jin shiru tsit babu sautin komai daga waje hakan yasa tayi tsammanin ko dai jami’an sun kashe macijin ne, cikin sanɗa take yin tafiya tana tunkarar toilet door, ta ruƙo handle din ƙofar ta buɗeta, shigowa ɗaki tayi ta nufi wayarta dake ajiye saman bedside drawer takai hannu ta ɗauke ta tana ƴa waige waige duk tabi ta ruɗe. Layin pravin ta danna ma kira, kusan sau uku bai ɗaga ba, hankalinta ashe take fadin”pravin ka ɗaga kirana mana” Sake kiran layin tayi, a lokacin da kiran ya shigo mashi yana a kwance saman shimfiɗeɗɗan gadon hajjaty, sleeping dress ne ajikinta, shi kuma shorts ne babu riga, ya rungumeta a kirjinshi, sun manne ma juna, duvet din daya lullu6a masu iya saitin kafaɗunsu ya tsaya. Bacci ya ƙaura ce ma idanuwan hajjaty, tun da tayi tozali da narkekan macijin nan, lallashinta yake yi duk don ya samu ta kwantar da hankalinta. “Pravin wayarka fa tana ringing yakamata ka duba me kiranka” “Nasan wa ke kira na, bai wuci hajiya saratu bace, ta gama ci min mutunci shine yanzu take kirana saboda ta tsorata da ganin maciji, wallahi ba zan je ba, nafi so taji a jikin ta” Muryar hajjaty ƙasa ƙasa tamkar me yi mashi raɗa ta furta”please, matarka ce, yakamata kana darajata” “Ni ma ai batasan darajata ba, saratu bata girmamani, tayi min gori ta gaya min maganganun da suka ƙona min rai, sauƙin ma ba ita ka ɗai bace Ina dake” Lumshe mashi ido hajjaty tayi, Yaci gaba da cewa”kina ƙaunata tsakani da Allah, baki ta6a guduna ba, kin rabu da kowa naki kin biyoni Nigeria, a zaman da mukayi dake ni baki ta6a yi min laifi ba...” ƙayataccen murmushi tasakar mashi. “Ina fata kai ma ba zaka ta6a guduna ba, Kuma ba zaka ta6a yi min laifi ba, pravin bani da kowa a halin yanzu Allah ne gatana sai kuma kai, dan Allah ka ruƙe min amana kada ka aikata abun da zaiyi silar rabuwar mu, ka ji tsoron Allah a dukkan lamuranka na rayuwa, idan kana tunawa da mutuwa zaka ƙara jin tsoron Allah, bana so wata rana muyi abun da zamu yi danasani arayuwarmu...” Bai bari ta ƙare maganar ba yai hanzarin katse ta”my woman, bansan yaushe kika fara yin wa’azi ba, idan ban manta ba, Ni ne na koya maki alwala ko” Dariya ta saki jin abunda pravin yace, kafin ta ƙara cewa wani abu ya rigata fadin”muyi bacci please dare yana ƙara nutsawa” da shagwa6a hajjaty tace”ni dai ka tafi ɗakin matar ka, ita yakamata ace kana atare da ita bani ba” “Bana so in bar ki ne saboda na lura haryanzu jikin ki bai daina kerma ba” “Amma itama saratun ai tsoron take ji, tana buƙatarka agefenta, pls ka tafi wajenta, Ni nafiso kana kamanta adalci a tsakanin...” bai bari ta ƙare maganar ba, yai saurin haɗe bakinsu, ya zura hannayenshi biyu cikin rigar baccin jikinta, sarrafata ya soma yi cikin ƙanƙanin lokaci ya fara caza mata kai, yayi mata hakanne don ya mantar da ita zancen tafiyar da take yi mashi, kuma yaci galaba akanta, bai rabu da ita ba har saida yaji ta fara yin bacci tukunna ya ƙanƙameta. Phone dinsa sai ringing take yi, tana daga can gefe daya saman mattress din, a hankali ya raba jikinsa daga nata. Ya laluba hannu ya damƙo wayar, murmushin mugunta ya saki kafin ya ɗaga kiran. Ko sallama babu hajiya saratu tace”pravin ina ka shiga? Ina ta kira baka picking! Ba zaka dawo daki ka kwanta ba ne”? Tun daga kan muryarta ya fahimci babu natsuwa atare da ita “Me zan dawo nayi maki? Ni da bani da amfani awajenki”? Muryarta tamkar zata fashe mashi da kuka tace’kaga ni ba wannan na tambayeka ba, ina son ganinka ka, pravin, hankalina ba akwance yake ba, nasan kaga abunda ya faru ɗazu” Tuntsirewa yayi da dariyar mugunta, ran hajiya saratu ya 6aci matuƙar masifa ta soma zazzaga mashi sai da tayi mai isarta tukunna ya katse ta da cewa”saratu kenan, kefa da kanki kikace nine ɗan kwali ke ce hula, hakan na nufin kece namiji ko? To meyasa kike neman mace donta baki kariya? A tunanina ni yakamata inji tsoro bake ba, shi namiji da jarumta aka san shi bada ragwantaka ba”! Takaicin duniya ya ishi hajiya saratu, cikin lalama tace”pravin dan Allah ka dawo ɗaki, idan saboda abun da na fada maka ne ya 6ata maka rai, zan baka haƙuri” “Bana buƙatar haƙurin ki saratu, lokacin daya dace ki lallasheni ki tarairayeni ki bani hakuri bakiyi ba till now da buƙatar kan ki ce ko? An gaya maki ni shashashane bansan ciwon kaina ba”? Shiru bata tanka mashi ba, kuma tana sauraronshi. “Ko gobe kada kiyi tunanin zan dawo gida, ni yanzu haka ma gani akwance tare da wadda tafi ki iya tarairayar miji.....”tsawar da ta daka mashi ce ta sanya shi yin shiru, tamkar zata fasa mashi screen din wayarshi”ya isa haka! Ya isa! Kada ka ƙara maimaita min maganar da kayi idan ba so kake ranka ya 6aci ba......” bata ƙare maganar ba, yai rejecting kiran, Ya jefar da wayar saman mattress, Ya janyo hajjaty a jikinshi, ya daura hannunshi saman sumar kanta, har cikin ranshi yana ƙara jin ƙaunarta, bai da tamkarta a duniyar nan, saboda kyautata mashin da take Yi, yana matuƙar ƙaunarta, kiss ya manna mata saman forehead nata, kafin ya cusa kanshi gefen wuyanta, ƙamshin turarenta ya daki hancinsa ahaka bacci yai awon gaba da shi. Jefar da wayar hannunta tayi saman gado, ranta ya 6aci matuƙa pravin ya ƙona mata rai, kishine da ita, gani take kamar dagaske ne abun da ya faɗa mata yana can shida wata suna sheƙe ayarsu, kokwanton maganarshi take Yi, ta riga ta yarda da pravin tasan bazai Iya cin amanarta ba, wata’kil ya faɗa mata hakanne don ya huce raɗaɗin abunda tayi mashi. Damuwace ƙarara akan fuskar hajiya saratu, adaddafe ta nufi gado ta haye ta kwanta idanuwanta suna fuskantar ceilling, babu alamun zata runtsa adaren Yau. *Hajiya Turai💔* Safa da marwa take Yi acikin ɗakinta, Hannunta ruƙe da wayarta, night gown ce a jikinta. Fuskarta tayi jawur tamkar wadda tasha kuka, musamman kumatuntu, green eyes dinta kuwa sun ciza launinsu, tarasa ina zata tsoma ranta taji daɗi, since wuraren ƙarfe goma take kiran layin dr.jazz babu alamun zai ɗaga, gashi har dare ya nutsa bai dawo gida ba, ta kira layin Sir mubarak kusan sau talatin shima Bai daga ba tamkar ta fasa ihu haka take ji. “Mom” kamar daga sama taji an ambaci sunanta, tsabar ruɗi sai taji kamar muryar jazz ne. A firgice ta juyo don ganin wanene, Yana daga tsaye bakin ƙofar ɗaki, cikin shiga ta kayan bacci ya zura hannayenshi cikin aljihun wandonshi, matashin saurayi ne kamanninshi sak dana Sir mubarak. “Ibad kai ma baka yi bacci ba”? Muryarshi da kalasa ya furta” How can I sleep, Mom? Jazz hasn’t come home yet. na jaraba kiran layukan wayarsu duk akashe, bansani ba shi jazz ko aikin kwana yake yi a asibiti, nazo ne naji ko sun faɗa maki meya hana su dawowa gida”? Ta lura da yanayin shi tsantsar damuwace akan face dinsa, batayi mamaki ba saboda ƙaunar da suke yi ma Jazz, sun dauke shi tamkar shaƙiƙinsu “Ibad, I don’t know why they haven’t come home yet, I’ve been trying their phones since 10 o’clock, and nobody is picking up. I’m really worried, inajin fargabar ace wani abun ne ya faru da su” tuni idanuwanta sun ciko tab da ƙwalla. Ruƙo hannunta Ibad yai”haba mommy, kada ki zubda hawayenki please, ki kwantar da hankalin ki, Everything is going to be okay. They’ll come home safely.” girgiza mashi kai tai”basu ta6a yi min haka ba ibad, daga jazz din har daddyn naku, kullum ne idan zasu kai dare awaje, sai sun kira awaya sun faɗa min, amma yau shiru babu wanda ya tuntu6eni” muryarta na rawa ta furta maganar, tausayinta duk ya kama ibad, jinta yake yi tamkar mahaifiyarsu data rasu. Gyaran muryar da akayi masu ne Ya janyo hankulansu ga duban shi, tafiya yake yi yana tunkarosu tamkar baisan da su ba, Hannun shi ruƙe da apple laptop dinshi, daga shi sai short a jikinshi, Ƙirar jikinshi da komai kalar na daddynsu ne, sai dai shi yafi ibad da daddynsu hasken fata nashi chocolate colour ne mai kyan gaske, sumar kanshi tasha gyara luf ta kwanta saman bayanshi, Yana da kirar karfi kamar ɗan wrestling, wani irin daddaɗan kamshin turarene ke fita sako da lungu na jikinshi, komai nashi da aji yake yin shi, mutunne shi maiji da kanshi, baida wasa a aikinshi, yana ruƙe da muƙamin CEO na babban Companynsu dake a ƙasar canada. Kafafuwanshi suna asanye da slippers, magana ya somayi tamkar baisan furtata “Mom, yanzu major ya kira ni awaya, ya fadamin suna atare da jazz wani aiki ne mai muhimmanci ya tsayar da su, so they couldn’t come home tonight. But they’ll be back early tomorrow” Ajiyar zuciya ta sauke, har cikin ranta taji dadin jin hakan, Murmushi Ibad ya saki yana fadin”mun samu nutsuwa yanzu, Mom ki koma daki ki kwanta, ƙarfe 3 fa ta buga, gobe nasan zakiyi ramuwar bacci, murmushi tasakar mashi”bari na koma ciki, mu kwana lafiya My Sons,” ta faɗa tare da juyawa ta nufi ɗakinta, saman gado ta haye idanuwanta suna fuskantar ceilling, bakomai take jimawa ba face kwanan da za ta yi ba tare da mijinta ba, sun saba faranta ma junansu kafin su runtsa yau kuma babu shi atare da ita, ga kuma ɗanta da take jin kewarshi, Pillow ta janyo ta rungume a ƙirjinta. “Babban yaya nan fa ba kasar canada bace, taya zaka dinga yi mana yawo da short a tsakar falo? Kai ala dole ga bature ko? Ko kunyar mommy baka ji,” Ibad ne ya fada da zolaya. Ko kallo bai ishe shi ba, saman Sofa mai mazaunin mutun uku ya kishingiɗa kanshi saman sofa hand, Ya daura laptop dinsa saman flat stomach dinsa. In a husky voice ya furta”ibad! Ina buƙatar abun sha” Ruƙe qugu Ibad yai sam baya gajiya da zolayar yayan nashi duk da tazarar shekarun dake atsakaninsu, domin kuwa Zaki ba ƙaramin mutun bane “nan fa ba canada bace, Nigeria ce daddy Ya hana ana aikena idan dare yayi” yamutsa fuska Zaki Yai Ibad ya fara hayaƙa shi. Calmly ya furta”Don’t make me repeat myself” kama kunne ibad yai”sorry big bro, na tuna kada ka hanani silallan kashewa” ya fada tare da nufar frigde Ya bude ya dauko mashi coke mai sanyi, ya dawo Ya daura mashi saman sofa table din gabanshi. “Babban yaya gashi na kawo, Ni zan cire maka murfin?” banza yai mashi tamkar baiji me yace ba. Bottle opener yaje ya dauko ya zuƙunna agaban table din Ya soma kiciniyar bude murfin, sai nishi yake yi, sam bai saba da wahala ba, ibad mugun sangartacce ne yayanshi ya 6ata shi da hutu, dogon tsoki zaki Yaja, ya yunkura ya miƙe Ya ajiye laptop din gefe ɗaya, ya kai hannu ya kar6e coke din da bottle opener din, sau ɗaya ya murɗa murfin ya cire. Washe baki Ibad Yai”babban yaya ba za ka yi bacci ba? kana buƙatar hutu fa, kai kullum aiki baka gajiya”! Banza yai dashi baice komai ba, a tsanake yake kur6ar coke din me sanyi, Ibad ya ƙura mashi ido yana kallon bakinsa har haɗiyar yawu yake yi. Janye coke din yai daga bakinshi, Ya galla mashi harara”meyasa kake kallona kana haɗiyar yawu kamar wani maye? Idan so kake kasha bakasan inda zaka dauko bane” Kwa6e mashi fuska ibad yai”Ai ni nafi so kasha ka rage min” Sakin baki yai galala yana dubanshi”oh dole sai na baka ragowa na zaka sha” ɗaga mashi gira yai alamar eh. Babu musu Ya miƙa mashi, don ya san rigimar ibad idan har ba bashi ragowar yai ba to kuwa zasu kwana azaune” Yana sha yana kallon fuskar Zaki, aiku sarkin ɗumi. “Big bro, where’s my sister pretty ? You told me she came back to Nigeria. When can we see her? Should we go to their house, or will she come to ours? (Babban yaya Ina sister pretty dina? Ba ka ce min ta dawo Nigeria ba, to yaushe zamu haɗu da ita? mu zamuje gidansu ko ita zata zo gidanmu?) Dafe kanshi yai da hannu ɗaya”Ibad, I don’t like making noise, Please go to your room, lie down on your bed, and sleep.” “Shikenan zanje na kwanta amma kafin nan inaso ka fadamin gaskiya, dagaske babu soyayya atsakaninku”? Ji yake tamkar ya dauki laptop din gefenshi Ya kwalama ibad saman kanshi, Ya takura mashi. “Ka yi shiru bakace min komai ba”! Miƙewa zaki yai ya dauki laptop dinsa Ya nufi sashen bedroom dinsu, da sauri Ibad Yabi bayanshi, har yakusa shiga dakin ya ɗan dakata da yin tafiyar, in a cool voice ya soma magana “Ibad, she is married and even has a daughter, And she loves her husband. But there is no love between me and her. taimakon da nayi mata dan Allah nayi shi” Da mamaki Ibad yace”babban yaya kana nufin duk tsawon shekarun data dauka a canada a gidanka, da auranta? To ya akai ta gudu tabar mijinta da ƴarta? kuma take rayuwa agidanmu harma kuke rungume juna ai ina ganinku idan kuna shan soyayya....” kafin ya ƙare maganar, afusace zaki ya waiwayo da niyar ya kwaɗa mashi laptop din hannunshi da gudu Ibad Yabar wajen yana dariya. Guntun tsoki Zaki Yaja, Ya faɗa katafaren room dinsa, saman gadonshi ya kwanta, haɗi da daura laptop dinshi on his broad chest, hoton fuskarta dake akan wallpaper din laptop nasa ya ƙurawa ido yana kallonta, bazai Iya misalta ƙaunarta da yake ji ba, yana sonta baya jin zai iya son wata ƴa mace aduniyarnan kamar yadda yaso baiwar Allahn nan, sun rayu na tsawon shekaru tamkar ma’aurata rana ɗaya Allah ya ƙaddara rabuwarsu, yana fatan sake haɗuwa da ita, da tunaninta bacci yai awon gaba da shi. *ANEELERH❤* Kiran sallar asubar farko, ringing din wayarta ya daki kunnanta, firgigit ta farka daga bacci tana faman sauke ajiyar zuciya, yayin da la66anta ke ambaton sunan baby junaid, mafarkin da tayi da shi ya ɗaga mata hankali, a ruɗe ta mike zaune, rigar baccin jikinta duk ta yamutse, haka zalika sumar kanta a hautsine take. Daukar wayar tayi dake ajiye gefenta, ta duba me kiranta, missed calls ta gani sun kai biyar na hajiya adama, aranta ta ayyana Allah yasa ba mafarkin da tayi bane ya zama gaske. Bin kiran tayi nan take kiran ya shiga, bugu uku kafin hajiya adama ta ɗaga. “Assalamu alaikum, daughter in-law, fatan dai ban katse maki baccin ki ba” da buɗar bakin Aneelerh sai cewa tayi”mommy ina junaid” Sautin dariyar hajiya adama ne ya fargar da ita, da sauri ta dafe baki tamkar tana agabanta tace”au...namanta ban gaishe ki ba, ina kwana mommy” “Lafiya lou Aneelerh, lallai yau na shaida kin ƙosa kiga ɗanki, tun da gashi har kin fara ambaton sunan shi tunkafin ki gaishe ni” Cikin jin kunyar maganarta Aneelerh tace”ba haka bane mommy, daga bacci na tashi bansan Na ambaci sunanshi ba” Hajiya adama tace”oh am sorry na tada ki daga bacci tun da asubahi, agafarce ni, jikana ne ya takura min akan in kira mashi ke awaya, yaban mamaki da sunanki Ya farka yanata kuka yana fadin wurin mommy zaije shine nace bari na kiraki kuyi magana wata’ƙil hankalinshi zai kwanta, kafin mu shigo gidan zuwa anjima in sha Allah” Hankalin Aneelerh yaɗan tashi jin abun da mommy adama tace, aranta ta ayyana kodai shima yayi kalar mafarkin da tayi da shi ne? “Aneelerh kinyi shiru, ga shi ku gaisawa” muryarta adabarbace tace”toh mommy” Sautin kukan baby junaid ne ya cika mata kunnanta, murmushi tasaki tana fadin”My baby boy, ba hello ba hi sai kuka? So kake hankalina Ya tashi ko”? Cikin shessheƙar kuka yace”mom..my wallahi kizo ki ɗoke ni, idan ba haka ba bazaki sake gani na ba, mutuwa ma zanyi” rass taji gabanta ya fadi, “Junaid kadaina ambaton mun mutuwa, banaso, idan wani abu ke damunka ka faɗamin mana!” aɗan tsawace ta furta mashi maganar, tunawa da hajiya adama yasa ta sassauta muryarta, “My baby boy, ka kwantar da hankalin ka, Yau in sha Allah mommy adama zata dawo min da kai” Tsagaitawa yai da yin kukan, Muryarshi da shagwa6a yace”Ai ni tsoro nake ji, bana son zama agidansu....” bai ƙare maganar ba tayi sauri furta”shiru! Agaban mommy adaman kake fadin haka”? “A’a mommy, ba agabanta bane, ai ta fita daga dakin” Ajiyar zuciya ta sauke”yanzu fada min me ke baka tsoro? Ko wanine yake bugunka”? “A’a mommy, idan ina bacci, sai ina ganin wani mutun sanye da baƙaƙen kaya hannun shi ruƙe da ɗan kwano, kalar wannan abun na ɗakin mami, wanda ake zuba fura a cikin shi, hannun shi zaƙo zaƙo da akaifu kalar na Ana mai girka mana abinci, wai yake ce min inzo mu tafi” zaro ido waje aneelerh tayi”Junaid ka natsu kayi min bayani, a mafarki kake ganin shi ko kuwa a zarihi? Kai kaɗai ka ke kwana aɗaki idan dare yayi” “Ni ba mafarki nake yi ba, dagaske nake ganin shi, kuma a ɗakinsu nake kwana” aneelerh duk tabi ta ruɗe. “Junaid kaji tsoron Allah, ka faɗamin gaskiya, nasanka da ƙarya, Idan baka fada ba, to bazan baka zoben Angel ba” “Kin siyane”? Ƙumshe dariya tayi don tundaga kan yadda ya tambayeta ranta ya bata cewar ƙarya ya shirga mata. “Na siya mana, ai jiya naba mahboob kuɗi Ya siya maka zoben mai kyan gaske” Tuntsirewa yayi da dariya yana fadin”to mommy wasa nake yi maki, wallahi dama awani cartoon ne da muke kallo a tv, anan naga mutumin” fashewa tayi da dariya sosai har fararen haƙoranta suka bayyana”yanzu naji magana ɗan rainin wayau, duk kabi ka tasar min da hankalina, Yau har mafarkin ka nayi saboda nayi kewarka babyn mommy, ina sonka Yarona” Yace”nima inasonki mommyn baby” dariya tasaki, idan yana yi mata magana kamar wani babban mutun daya mallaki hankalin shi, sai idan yayi wata kwa6ar ne zaka gane ƙaramin yaro ne. “Mommy ina mamina? da abie, da uncle mai ƙaton hanci, da mahboob mai son kuɗi, da zahrah mai dogon wuya” Tsabar yadda take yin dariya hada dafe ciki, “Junaid baka da mutunci, Uncle dinne mai ƙaton hanci”! Kaitsaye yace mata”eh mana, baida kyau Allah, mummuna ne uncle dan Iya, ni naji dadi ma bashine daddynki ba, da wallahi bazanyi kyau ba” Mamaki ne ya kama Aneeleerh, jin yadda yake kushe mata kawunta. “Junaid dan Allah ka yi shiru kada wani yaji ka, Ni zan ajiye wayar, ka koma bacci zuwa anjima Mommy adama zatayi maka wanka ta shiryaka sannan zata dawo mun dakai gida, fadamin me kake so in tanadar maka”? Da shagwa6a yace”fura nakesho, asanya kwakwa da yoghurt aciki” bakomai ya tuna mata ba face Angel, tana son furar da aka sanya kwakwa da youghurt, kusan kullun idan tazo gidansu sai ta sanya Aneelerh ta haɗa mata ita, musamman saboda Angel take ajiye damarmar fura cikin robabi ta sanya mata su a frigde don su yi sanyi. Tuni idanuwanta suka cicciko tab da ƙwalla, Muryarta na rawa ta furta”zan ajiye maka my baby boy, ka kwanta ka huta zuwa anjima zamuga juna” daƙyar ta samu baby junaid Ya ƙyaleta, badan ta gaji dashi ba, ta ajiye wayar on pillow, ta sauko daga saman gadon, A hankali take bin bedroom dinta da kallo, har idonta ya sauka akan hotonsu da ta liƙa shi a bango, wanda sukayi tare da aminnanta, su uku abunsu, kowacce ta ca6a uban adon lace, fuskokinsu ɗauke da murmushi. Ta natsu tana kallon hotunansu, sam ba ta ji takun tafiyar mutun ba, har ta ƙaraso gefenta ta tsaya, Ƙamshin turaren zahra ne yaja hankalinta ga dubanta, tayi mamakin ganinta a ɗakinta, tun ranar da abunnan ya faru na hajiya falmata ko magana bata ƙara haɗa su ba, amma yau sai gashi ta tako ta shigo room dinta, dogon hijabi ne a jikinta daga ƙasa har sama launin maroon hannayenta biyu ta fiddo dasu ta cikin hannun abayar, hada cazbaha ta ruƙe tana ja kamar wata matan limam. “Aunty Aneelerh Ina kwana, kin tashi lafiya”? Daƙyar ta iya amsa mata da lafiyalou, ina fata kema haka” Daga mata kai tayi alamar eh, idanuwanta sam basa akan Aneelerh suna akan hoton da take kallo, wani irin kunyarta take ji, tunawa da rashin mutuncin da tayi mata akan ta bata shawarar ta ba Hajiya falmata haɗin kai, tayi danasani tun jiya da Mahboob Ya fayyace mata komai. “Nayi mamakin ganinki a ɗakina zahra, ai nayi tunanin mun rabu kenan har abada” Girgiza kai zahra tayi”Idan kinga mun rabu to mutuwace ta raba” Aneelerh sam batasan Mahboob ya fada ma zahra ba, bayan ta gargade shi akan karya gaya mata, shi kuma bayason suna gaba atsakaninsu, don ya fahimci zahra ta fusata sosai, Idan har bai fada mata gaskiya ba to kuwa zata cigaba da zabga ma Aneeleeh rashin mutunci abisa rashin sani shiyasa ya yanke shawarar ƙwara ya faɗa mata, don ta yi takatsantsan kada ta wuce gona da iri azo aji kunya. “Kiyi haƙuri da abunda Ya faru atsakanin mu, nasan na 6ata maki rai, tuntuni nake taso in nemi yafiyarki, sai dai baki bani damar yin hakan ba” Aneelerh ce tayi maganar tana duban zahra. Cikin sanyin murya zahra tace”ni yakamata nabaki hakuri auntyna bake ba, saboda ni ce mai laifi, ban kyauta maki ba, duk irin shaƙuwarmu da kyautatamin da kike yi amma nagaza fahimtarki, har takai takawo ina zarginki, maimakon na kyautata maki zato, wallahi naji kunya, daren Jiya daƙyar na runtsa tsabar takaici, Ƴan kwanakin da muka samu sa6ani atsakaninmu aunty Aneelerh naji jiki ba kaɗanba, na ƙuntata, na gane mahimmancinki agareni, Ina da abubuwa dayawa da suka faru wadanda nakeso in samu abokin firar da zangayama wa ya tayani farin ciki sai dai kash babu, ke kaɗai ce nake jin dadin tattaunawa dake akan duk wani abu daya shafi rayuwata saboda nasan zaki ƙarfafa min gwiwa ki kuma bani shawarar da zata amfane ni....” zafafan hawayene suka wanke fuskar Zahra, tuni idanuwanta sun kaɗa jawur da su. “Meyasa banyi dogon nazari ba akan shawarar da kika bani”? Zuciyar aneelerh ba ƙaramar karaya tayi ba”zarah! Mahboob Ya fada maki ne”? Jinjina kai tayi”ƙwarai kuwa ya fadamin komai, har gargaɗi na yayi akan kada na nuna na sani, saboda kince mashi kada ya gaya min, shi kuma a ganinshi bai kamata ki zubda mutuncinki a idanuwana ba, saboda ku rufa ma hajiya falmata asiri awurina, don in cigaba da ganin darajarta, hakan kuma bazai ta6a yiwuwa ba, saboda shi mutunci madarane idan ya zube baya kwasuwa, sai dai naji dadi da ke kika yi silar shiriyarta, ke din ta dabance Auntyna” Rungume Aneelerh tayi, atare suka fashe da kukan farin ciki, yau sun shirya da juna, babu wanda baiji jiki ba acikinsu. Bubbuga bayanta Aneelerh tayi da hannunta Cikin shessheƙar kuka take fadin”komai ya wuce zahra, abunda ya faru laifina ne dana baki shawarar banza duk da ko a lokacin bawai zan zuba maki ido bane don ina jarabaki ne nayi hakan, wallahi duk wani motsinki atafin hannuna, tun bayan dana baki shawarar, fargabana kada ki amince da shawarata ki kama hanya ki tafi kai mata kanki, shiyasa na sanya maki ido, akarshe na yanke shawarar zuwa gidanta don in gargadeta akan ta fita sabgarki, Cikin Ikon Allah sai gashi na 6uge da yi mata nasiha, ashe nice silar shiriyarta, naci ribar jarabawar da nayi maki zahra, Naji dadi kuma nayi farin cikin samun ƴar uwa mai tawakkali irinki, zan iya cewa duk namijin daya mallaki mace irinki yayi nasara sai dai fatan ya cika da imani” Dariyar farin ciki zahra tasaki, tare da dago dakanta daga jikin Aneelerh “Bansan da wasu kalmomi zanyi amfani ba wurin yi maki godiya saboda babu su auntyna, Ina fatan nima Allah yabani abunda zan kyautata maki da shi, sannan mahboob Ya faɗamin cewa kin bashi kyautar kuɗi duk da yaƙi gayamin nawa ne kinsan halinshi May be Yana gudun kada Ince ya bani kasona, baisan cewa Nima na samu alheriba, abunda nake ta so in faɗa maki kenan” Waro ido Aneelerh tayi da alamun farin ciki akan fuskarta tace”masha Allah, kice kun samu abun arziƙi” Jinjina kai Zahra tayi”zakisha mamaki auntyna, naga yanzu kika farka daga bacci, da anjima idan muka kammala yin breakfast zan fada maki komai” Murmushi Aneelerh tasaki”Yau zansha kanun labarai, Yanzu bari na shiga toilet in yi wanka” “Auntyna wai yaushe za’a dawo mana da baby junaid dinmu, nifa nayi missing dinshi, Allah na kusa zuwa in dauko shi, Jiya har mami na tambaya game da zancen dawowarshi” Aneelerh tace”kada ki damu, Babyn mu yau zai dawo gida, Hajiya adama zata kawo shi, Nima yau da shi na tashi araina” “Allah ya kawo su lafiya, shima na tanadar mashi kyautarshi ta musamman da zan bashi” Aneelerh taji dadin maganar zahra. “Kada na cika ki da surutu, nayi kewarki ne auntyna, bari nabarki kiyi wankan in kin fito mun tattauna, amma kafin nan niko inaso in tambayeki wani abu in ba takura” dariya aneeleh tayi kafin tace”okey ina jinki fadamin menene” Da ido tayi mata nuni da hoton dake amanne jikin bango. “Wacece wancan black beauty din mai diri? Ita kadai ke bansani ba cikin ƙawayenki, nadai san Benazir mahaifiyar kyakkyawar yarinyar nan Angel” Jim Aneelerh ta ɗanyi kafin ta furta”Aishatu bintu sheikh Iman Malik, shine sunanta, kamar yadda na fada maki aminnan juna ne mu” Cike da son jin ƙarin bayani Zahra tace”to amma ta rasu ne ita? Naga ko waya ba ku yi, Ita dai benazir nasan abunda ya faru da ita” a kagare ta jefa mata tambayar. Cikin sanyin murya Aneelerh tace”ƙaddarace ta afka mata wadda tayi silar tarwatsewar farin cikin rayuwarta, baiwar Allah, nan da kike ganinta mahaddaciyar alƙur’anice, tun tana ƴar shekara goma sha wani abu ta haddace shi, Tana da kaifin basira mace ce mai kamun kai, tana da aji, idan nace zan baki labarin rayuwar Aisha wallahi saikinyi sha’awar yin koyi da ita, saboda kyawawan ɗabi’unta da halayanta, Ni kaina ban ta6a tsammanin zamu rabu da itaba.....” tun da ta fara magana zahra ta kafe ta ido tana sauraronta, idanuwan Aneelerh sun kaɗa jawur, sam bata son tuna baya, hakan zai fama mata ciwon dake acikin zuciyarta. “Aunty Aneelerh kinyi shiru? tun da kika ambaci kyawawan halayanta naji na kwaɗaitu da son jin tarihin rayuwarta” Girgiza kai Aneelerh tayi”Am sorry zahra, bana son tunawa, “ bubbuga ƙafa zahra tayi tamkar zata fashe mata da kuka tace”please Aunty Aneelerh, wallahi tana burgeni duk da ban ta6a ganinta ba” Murmushin yaƙe Aneelerh tasaki tana duban hoton yayin da hawaye ke bin fuskarta”Ni kaina bani da masaniyar tana araye kota mutu, tunkafin muyi aure tabar gidan iyayenta, Silar wani mummunan abu daya faru, wanda ni nayi imanin bata da laifi, tuggune da makirci aka shirya mata.....” dakatawa Aneelerh tayi dayin maganar tana kallon zahra, tsabar son jin gulma har ta jefar da cazbar hannunta batare da saninta ba. “Aunty Aneelerh kinyi shiru! Meya faru da ita? Wanda yaja har tabar gidan iyayenta? Wani irin tuggune aka kitsa mata”? Tuntsurewa Aneeleeh tayi da dariya, juyawa tayi da sauri ta nufi toilet door tana fadin”Zahra ƙwara ki fidda rai da son jin labarin Aishatu Bintu sheikh imam malik, dan zan baki shi ba yanzu ba sai kin ƙara hankali” ta kare maganar ta shige toilet taja kofa ta datse. Ta tafi Tabar Zahra da cizon yatsa, idanuwanta akan hoton fuskar Aisha, aranta ta ayyana ai wallahi saina ji labarinki baiwar Allah, Ai ni dama tun da naga hotonki na shaida kinbar tarihi arayuwarki, Oh ni ƴar ubansu, gata kyakkyawa, mace har mace, ga diri kamar nicki minaj, ko tana ina ahalin yanzu”? Sambatu zahra tadingayi tana kallon hoton aisha, sai daga bisani ta duƙa kasa ta dauko cazbaharta, ta futo daga ɗakin ta nufi nata dakin don ta kimtsa kafin lokacin yin break fast. *Daular Alhaji Musa🏙* A zaune take kan darduma, bata jima da kammala sallar asubahi ba, hijab din data sanya launin milk, gaba ɗaya ta tattara natsuwarta akan addu’ar da take Yi, ta ɗaga hannayenta sama cikin harshen larabci take karanto addu’o’i, yayin da hawaye suka cika idanuwanta, bakomai take roƙo ba face Allah ya dawo mata da mijinta lafiya da ƴarta, bata da burin daya wuce tayi tozali da su, tayi matuƙar ƙagara da son ganinsu. Ƙamshin turaren dr.shureim ne Ya dakatar da ita daga yin addu’ar da take yi, da sauri ta shafa saman fuskarta, A hankali ta fuskance shi, yana daga zaune gefen gadonta, bai jima da shigowa ɗakin ba, fuskarshi dauke da annurin farin ciki, Daren jiya da tunanin ƴar uwarshi ya kwana, ya damu da ita. “Yayana nakaina, Ina kwana ka tashi lafiya”? “Lafiyalou rabin raina, ina fata kin yi kwanan farin ciki agidan Uncle” shiru tadanyi tunawa da abunda ya faru duk da ta dauki hakan amatsayin mafarki, jinjina mashi kai tayi”Alhamdulillah, jiya naji dadin bacci, hada munshari, balle ni da nake atare da Zeenatu, yarinyar akwai shiga rai” Murmushin gefen fuska dr shureim yasakar mata”hala tacika ki da surutu”? Girgiza kai benazir tayi”a’a, ai yarinyar kunya gareta, tana jin nauyin yi min magana yadda kasan bafullatana” Dariya dr. Shureim yai kafin ya tsagaita yace”hakane tana da kunya, amma fa ta iya zuba kamar aku, sai kun saba da ita zata saki jiki dake” Dr shureim yasaki baki yana maganar zeenatu, baisan cewa tana la6e cikin toilet tana sauraronsu, hannunta ɗaya ruƙe da qugunta, kalmar akun daya furta ta ta6a zuciyarta. Murmushi benazir tasaki, abunda baisani ba tun jiya tasan da surutun zeenatu, kafin su kwanta bacci, sunyi firar dare, ta saki jiki da ita tamkar abokiyarta. “Yaya shureim, Ni yanzu damuwata Mijina da ƴata, mami ta fadamin cewa basa ƙasar, amma sun kusa dawowa, ni namanta ma ban tambayeta sunan ƙasar da suka tafi ba” ta fada tana dubanshi”yaya shureim ko kana da number wayar taj”? Ras yaji gabanshi ya fadi, saboda shi baisan komai dangane da mijin benazir ba. Shiru yai mata batare da ya iya furta mata kalma ba, don baisan amsar da zai bata ba “Au namanta, kaima bakasan mijina ba ko? Lokacin dana aure shi......” bata ƙarasa maganarba cak ta ɗago suna kallon juna. Cikin sanyin murya yace”ai ba laifi kikayi ba, lokaci bana acikin hayyacina, ban kaiga farfaɗowa daga radadin abunda ya same ni ba, Benazir bansan mijinki ba, bana zumunci dashi, saboda ni kaina bana cikin natsuwata, kuma hada ƙarin ni ba azaune nake ba, idan baki manta ba, da abun duniya ya isheni, tattarawa nayi na koma egypt wurin ammim mu da zama” daƙyar yake furta maganar, launin idonshi harya fara canzawa Numfasawa yai kafin ya ɗaura da cewa”nasan ban kyauta maki ba, amma kiyi hakuri, daga ni har ke ƙaddarar rayuwace ta afka mana,”Wallahi bazan Iya misalta maki ƙunci da radadin da naji ba, lokacin da labarin tafiyarki ya same ni, idan bazan manta ba, aunty zainab ce ta sanar dani komai dangane da guduwarki da jinjirar da kika bari, bayan haka bansan komai game da rayuwarsu ba nima ban jima da dawowa gida ba.......” Bai ƙare maganar ba ta tari numfashinshi da cewa”kana nufin baka ta6a haduwa da ƴata Angel ba? Amma ni ayadda mommy ta fadamin taj yana kawota gidan mu, suna daukar dawainiyar kula da ita kuma suna nuna mata hotona harma tana tambayarsu Yaushe zan dawo” Zaro ido dr.shureim yai alamar mamaki da jin ƙaryar da mommynsu ta shirgawa benazir, duk da ba a ƙasar yake zaune ba, yasan komai dake faruwa a gidansu, ta hanyar aunty zainab dake fada mashi akai akai, shi dai a iya saninshi Hajiya layla bata zumunci da tajuddeen, hatta auran benazir da Alhaji ubaid ya bashi bada son rantaba, saboda ita ta tsani bare, balle shi da yakasance mai rufin asiri ba attajirin mai kuɗi ba, har fada saida sukayi da Alhaji ubaid saboda yabama ɗan jarida auran ƴarsu. Ganin yanayin fuskarshi ya canzane yasa jikin benazir yin sanyi, “Yayana kayi shiru baka ce min komai ba! Mommy ba gaskiya ta fadamin ba ko”? Adabarbarce ya girgiza mata kai yana kokarin tattara natsuwarshi yace”bahaka bane, ai ni bana a ƙasarne, bani da masaniya akan komai, lokacin dana dawo Nigeria shi taj din da yarinyar sun riga sun bar ƙasar, nima awurin Aunty zainab naji labarin” Ajiyar zuciya benazir ta sauke, fatanshi Allah yasa kada ta kuma tambayarshi wani abun da zai kasa amsa mata. “Mommy ta fadamin cewa yarinyar kamanninta sak dana tajuddeen amma hasken fatarta nawane ta dauko, yarinyar kyakkyawace idan zan iya tunawa, kafin na gudu nabarta dana haifeta saida na kalleta har naga launin idanuwanta ruwan tokane kalar na amminmu, kuma tana da curly hair kalar nawa, ni dai fatana Allah yasa bata dauko halina ba, banason ace bata jin magana. Dariyace ta kubce ma dr shureim, sambatun benazir ba ƙaramin kayatar dashi suke Yi ba. Zeenatu dake a la6e tana sauraronsu, takasa fitowa daga toilet din, zuciyarta ta kwaɗaitu da son jin wacece yarinyar auntynta benazir? Ya akai bata ta6a ganinta ba? Kamar dai ta ta6a jin labarin jinjirar da benazir ta bari awajen mommynta sarah. Lokaci ɗaya dr shurem yadaina yin dariyar, hawayen dake taruwa cikin idanuwanshi suka soma gangarowa saman kuncinsa. Da sauri ya kifa kanshi on his laps, Hankalin benazir ba ƙaramin tashi yai ba, Jiki na rawa ta mike daga kan dardumar ta koma gefenshi ta zauna haɗi da daura hannunta ɗaya saman bayanshi”yaya shureim meke faruwa? Meyasa ka zubar hawaye? Yanzu fa kake yin dariya? Kona fadi wani abune daya 6ata maka rai? Shiru bai ɗago ba, duk tabi ta ruɗe, zeenatu dake yi masu la6e jikinta yai sanyi jin dr shureim dinta yana zubar da hawaye, muryar benazir taci gaba da jiyowa tana fadin”dan Allah kayi min magana yayana nakaina, kasan bana son ganinka acikin damuwa” bazata iya jurar halin da dr shureim dinta ya shigaba, Har ta miƙa hannu zata buɗe kofar toilet din, sai kuma tafasa ta dan buɗe kadan ta yadda zata iya leƙen su Ɗagowa yai da kanshi, hawaye sun wanke fuskarshi, benazir dake kallon shi itama hawayen ke fita a idonta Zura hannunshi yai cikin aljihun jallabiyar jikinshi ya zaro wayarshi, batare dayace komai ba, Ya miƙa mata wayar, karaf idanuwanta suka sauka akan fuskarta Yarinyar dake akan wallpaper dinshi. Fashewa tayi da matsanancin kuka tamkar ranta zai fita, da sauri ya sanya tafin hannunshi ɗaya ya toshe mata bakinta, haɗi da girgiza mata kai, alamar tayi shiru, daƙyar ta haɗiye kukanta, yayin da suke kallon juna, sai yanzu tagane dalilin zubar hawayenshi. A hankali ya zame tafin hannunshi daga saman bakinta, hakan ya bata damar yin magana Cikin rauni na murya ta furta”munyi babban rashi yaya shureim, babu rabon suyi rayuwa tare da ƴata Angel, yarinyar tana kama damu, kamar ni na haifeta, mutuwa tayi mana yankan ƙauna, Allah ya jiƙanta” daƙyar ta ƙare maganar a hankali ta mayar da rinannun idanuwanta kan hoton jinjirar yarinyar dake a nannanɗe cikin towel fari ƙal, an sanya mata kayan sanyi, farace sol kamar ka ta6a jini ya ɗigo, dara daran idanuwanta sun buɗe sosai. “Bani da abun kallo daya wuce hotonta, da ita nake kwana da ita nake tashi, na mutu akan ƙaunarta, bazan ta6a daina sonta ba, kuma bana tunanin koda ace nayi aure zan samu madadinta a duniyar nan........ ⁉️❗ “Nayi danasanin abunda na akaita mata, har yau idan na tuna cewa da hannuna nayi hakan sai inji gaba ɗaya na tsani kaina....” cikin jin ƙunar yai ya ƙare maganar. Tsananin tausayinshi ne ya kama Benazir, idanuwansu sun kada jawur Harta bude baki zatayi magana, Motsin buɗe kofar toilet Ya dakatar da ita, sam ta manta da zeenatu a toilet, da sauri ta goge hawayenta, dr shureim ma ya share hawayen shi muryarshi adisashe yace”wanene a toilet”? Kafin ta bashi amsa, zeenatu ta fito, fuskarta da alamun lemar ruwa, tamkar batasan me suke tattaunawa ba, Har kuka tayi masu saboda sun bata tausayi duk da bata fahimci kan zancen nasu ba, ita a tunaninta Yaya shureim dinta ya ta6a son wata, sannan hoton daya ta6a nuna mata awayarshi amatsayin nata yake kallo yanzu ta gane ba ita bace, ya 6oye matane, har cikin ranta ba ta ji dadin hakan ba, jikinta yai sanyi tamkar wadda ka zarewa laka. Sun ƙura mata ido suna kallonta, fatansu Allah yasa bata ji me suke tattaunawa ba” “Zeeentu dama kina acikin toilet tsawon lokacin dana shigo ɗakin”? Jinjina mashi kai tayi”eh yaya shureim bansan ka shigo dakin ba, Uziri ne Ya ruƙe ni a toilet” Ajiyar zuciya ya sauke jin tace batasan ya shigo ba. “Ina kwana, ka tashi lafiya” muryarshi araunace ya amsa mata”lafiyalou” duban benazir tayi wadda tayi shiru tana kallonta, daga ita har dr. shureim din fuskokinsu sunyi jawur saboda kukan da suka sha, a hake suke ƙoƙarin 6oye mata damuwarsu bayan ga alama nan ta gani. “Aunty Benazir, bari naje daki in yi sallar acan, namanta jiya ban ɗauko hijabina ba” ta fadi hakanne don ta basu damar cigaba da tattaunawarsu Benazir tace”A’a basai kinje daki ba, Ga hijab dina kiyi da ita” ta fada tare da cire hijabin ta miƙa mata, da sauri zeenatu tace”a’a, Kibarshi, nafison naje daki nayi acan, naga kamar kuna yin magana ne keda ya shureim” Murmushin yaƙe Benazir tasakar mata”kada ki damu ƙanwata, bawani abu muke tattaunawaba, kema zamu Iya yin firar dake” “Assalamu alaikum!” Mom layla ce ta doko sallama, gaba ɗaya suka ɗago suna kallonta, doguwar rigace a jikinta milk colour, ta yafa mayafi akanta, fuskarta dauke da fara’a take dubansu Har suna haɗa baki wurin gaishe da ita”ina kwana mommy? Kin tashi lafiya”? Cikin kulawa ta amsa masu da cewa”lafiyalou Alhamdulillah, fatan na same ku lafiya, zeenatu ya akai naganki atsaye”? Washe baki zeenatu tayi tana fadin”yanzu na fito daga toilet, nayi alwala ne zanyi sallah” Mom layla tace”okey, yakamata kiyi kada ki makara” amsa mata tayi da toh, da sauri ta nufi kofar fita dakin ta fuce cike da fargaban kada Aunty Benazir ta dakatar da ita, bayan ta fita daga dakin ajiyar zuciya ta shiga saukewa, haƙiƙa taji takaicin halin da taga dr shureim dinta da aunty benazir, ta shiga damuwa tabbas tana ji aranta wani mummunan abunne ya ta6a faruwa da su, a ƙagare ta ke da son jin wacece Yarinyar benazir dinta? Sannan kuma wacece matar da taji yaya shureim dinta yana magana akai har yake fadin bazai samu madadinta ba koda ace yayi aure, burinta ayanzu shine taga hoton matar da ya shureim yake nunawa benazir a wayarsa. Da wannan tunanin ta nufi dakinta dake acan upstairs. Bayan fitar zeenatu, dr shureim da Benazir suka miƙe tsaye suna fuskantar mahaifiyarsu dake binsu da kallon mai tattare da alamar tambaya. “Meke damunkune? Ya akai naga fuskokinsu sun yi ja kamar wadanda suka yi kuka”! Tambayar data fara jefa masu kenan Benazir ce tayi kokarin cewa”Ni da ya shureim ne muke yin firar yaushe rabo, mun tuna da rayuwar mu ta bayane kafin mu rabu” “Hmm, yakamata ku manta da abunda ya wuce, tuna bayan nan baida amfani, tun da ba abun arziƙi bane ya faru” Dr shureim yace”hakane mommy, zamuyi kokarin yin hakan” Shiru tadanyi na wani lokaci tana kallonsu. Har dai Benazir ta fahimci kamar akwai wani abu dake akasan zuciyar mahaifiyar tasu “Mommy, kina son yin magana damu ne”? Girgiza kai tadanyi kafin tace”tausayin rayuwarku nake ji, ina jin fargaban ranar da zan mutu in barku a duniyar nan mai cike da ruɗani, saboda mahaifinku bazai iya tsaya maku ba, shi kanshi juya shi akeyi.....” jikinsu ne yai sanyi jin abunda tace, tamkar tana basu wasiyya ne, matsawa tayi kusada su tare da ruƙo hannayensu acikin nata. “Bazan 6oye maku ba, ji nake kamar wani abu zai faru” “Mommy ki daina fadin hakan, Ki kwantar da hankalinki, Allah yana atare damu, ni bana so naji kina zancen mutuwa” dr shureim ne yai maganar. “Addu’arki kadai muke buƙata mama, kidaina sanya damuwa aranki” benazir ce ta fadi hakan. Gyaɗa kai Mom layla tayi”shikenan nadaina, Benazir yaushe zaki je gidansu Aneelerh? Murmurshi benazir tasaki kafin ta bata amsar tambayarta dr shureim ya riga ta fadi “zuwa jibi in sha Allah, zan kaita gidan dakaina” Mom layla tace”naji dadin jin hakan, zanyi magana da mahaifinku shi yake da layin mahaifin Aneelerh, in yaso saiya fada mashi game da zuwanku, tun da babu wanda yasan gidan nasu, sai sun tura mana da adress dinsu. Benazir tace”hakan yayi mun gode mommy, ki kwantar da hankalinki, don na lura kamar bakya jin dadi” Murmushi mom layla tasakar masu, lokaci ɗaya kuma yanayin fuskarta ya canza ganin wani abu ajikin benazir, harta buɗe baki za ta yi magana sai kuma ta fasa tana kokwanto acikin zuciyarta. “Mommy lafiya”? Benazir ce ta fargar da ita, ganin ta ƙura ido tana kallon wuyanta” Girgiza kai tayi’bakomai, bari na koma daki, namanta banyi azhkar ba, Ina fata kuma kunyi naku, koda yake nasan ma shureim yayi ke fa”? Ta fada tana kallon benazir hankalinta yafi karkata akan jan ta6on da tagani gefen wuyan benazir kamar Yakushinta akayi fatar wurin duk ta karkarce. “Nayi mommy, bayan na kammala sallar asuba” Jim ta danyi kafin tace”okey, ku cigaba da firar ku, amma dan Allah adaina tuna bayan nan” Murmushi kowan nan su yasaki, insha Allah mommy” Juyawa tayi ta nufi kofar fita dakin, zuciyarta na harbawa da sauri da sauri, ta rude da abunda tagani, tambayoyi ta shiga jefa ma kanta me yakawo jan tabo da sahun yakushi saman wuyan benazir? Da wannan tunanin ta nufi dakinta. (Abunda ya faru bayan Big guy ya fita neman hannah) Cikin takun sauri Big guy ya nufi bedroom dinsu dake a down stairs, wata’ƙil aci sa’a ya ganta, hankalin shi ba akwance yake ba, saboda ya bincika ko’ina na part dinsu saƙo da lungu babu cikon yarinyar da yake nema, ba ƙaramin ruɗewa yai ba, fargabanshi kada ace wani wajen taje ta faɗa takasa fita, ɗaya bayan ɗaya ya ke shiga dakunan matan babu kowa, yabi hanyar da zata kaishi bedrooms din mazan, A bakin ƙofar dakin su Naufal Yaci burki, Ya dafe jikin glass door din, slowly kofar ta zuge, leƙawa ciki yai, a kwakkwance ya same su saman shimfiɗeɗan gadonsu, sun cunkushe kamar kinfin gwangwani, gaba ɗaya sun lullu6e jikinsu da bargo, buga ƙofar yai ranshi a jagule Ya juya zai fuce daga ɗakin ganin mazane zalla kuma gaba ɗayansu suke aɗakinsu naufal, Cak Ya tsaya da tafiya kwakwalwarsa ta soma tariyo masa abunda ya gani, da sauri Ya koma dakin ya tsaya daga bakin gadon yana kallon ƙafafuwansu da suka leƙo daga cikin bargon, a hankali ya ɗaura eye balls dinsa kan kafar da yake hasashen ta macace bata namiji ba, shape dinta ya banbanta data mazan kuma tafi kafafuwansu ƙaranta, hannu ya miƙa ya damƙi kasar bargon ya yaye shi, lokaci ɗaya big guy yasauke nannauyar ajiyar zuciya, hankalin shi ya kwanta ya samu natsuwa, Hanna ce a tsakiyar mazan ta ƙanƙame gabriel kamar zata koma cikinsa, Yayi mamakin ganinta tsumu tsumu acikinsu, gefenta na dama naufal ne da haris, daga 6angaren hagun katifar gabriel ne da javed, sunyi nisa acikin baccinsu. Acikin zuciyarshi ya furta”Kin tayarmin da hankalina” ya ambaci hakan tare da sakin bargon Ya juya ya fuce daga ɗakin nasu. *Unaisah Angel💋❤* Fitowa tayi daga cikin toilet, fuskarta da alamun lemar ruwa, Salsabeel yana daga zaune saman gadon Ya jingina bayanshi jikin headboard yayin da Giant snake din yake a kwance gefenshi ya daura kanshi saman laps dinsa. Jin motsin fitowarta ne ya janyo hankalin salsabeel ga kallonta, baiwar Allah ba ƙaramin tausayi take bashi ba, ƴar ƙarama da ita ta ɗaurama kanta damuwar da ko wani babban bazai Iya jurarta ba, ganin yana kallontane yasa ta dan sakin fuskarta data kumbura suntum. “Fuskarki kika wanko”? Girgiza mashi kai tai”a’a alwala nayi” “Amma ba’a fara kiran sallar asuba ba” “Nafila nake so nafara Yi, kafin a kira sallar asuba, Inaso zanyi ma danish ɗina addu’a ne” Murmushi salsabeel yasakar mata, dama saida ya ayyana hakan aranshi “Kina kaunar ɗan uwan nan naki” “Fiye da yadda nake ƙaunar kaina” ta furta hakan tare da juyawa ta nufi kofar fita dakin don taje nasu ɗakin ta ɗauko Hijabin da zatayi sallah, har ta kusa fita daga dakin kamar ance ta waiwayo ta kalli gadon Ba zato ba tsammani macijin Ya girgiza Yana kokarin tashi Da sauri ta furta”yanzu zan dawo my Man, kada ka biyoni, Nima bazan Iya yin nesa dakai ba, Hijabin sallah zan ɗauko a ɗaki” komawa macijin yai tare da daura kansa saman laps din salsabeel. Ajiyar zuciya ta sauke haɗi da yin ƙayataccen murmushi, salsabeel dake kallonta shima murmushin yake yi, lamarin Danish na matuƙar bashi mamaki. Juyawa tayi da sauri ta fuce daga dakin. Moving quickly take tattaka matakalar benan, kasancewar ko’ina na part din da haske tamkar da rana baka ta6a gane lokaci saika kalli agogo, a tsanake take bin ginin da kallo Yayin da take saukowa down, zuciyarta tayi mata nauyi, zazza6in jikinta sai ƙara nunkuwa yake yi, Ita kadai tasan halin da take aciki, da ace zata Iya dauke ma danish abunda ke damunshi da kuwa tayi hakan, zaifi mata sauƙi akan taganshi a wuyanci hali. Tana gab da zata dira ƙafarta kan floor din falo, ranta ya bata cewar akwai mutun awurin, wurga eye balls dinta tayi akan first floor bataga kowa ba, A hankali ta mayar da eyes din nata kan Second floor, rass taji gabanta Ya faɗi ganin mutumin nan da ta ta6a gani a gym room yana motsa jiki, Ya juya mata baya, bata Iya ganin fuskarshi da kyau, batasan ya akai ta tsinci kanta da yi mashi kallon kurulla ba, bakomai take son gani ba face fuskarshi, sai dai kash takasa ganinta, faffaɗan bayanshi kadai take kallo, Ba ƙaramin jikine da shi ba, murdadden damtsen hannayensa take kallo, da alama Ya ruƙe wani abu yana sha a cup, duba da yadda hannun shi na dama ke motsi, yayin da ɗayan hannun nashi ya zura shi a shorts pocket dinsa. Aranta ta ayyana ko wanene wannan mutumin? daga gani yana da ƙarfi da tarin dukiya, komai nashi cikin ƙasaita yake yin shi, dai dai da yanayin tsayuwarshi abun kallo ce, yaɗan jingina bayanshi jikin benan. Hankalinta ya karkata akanshi, ta manta da hijabin da zata je daukowa, ta tafi wani tunanin daban, ita so take taga wanene shi? Ranta yafi bata cewar Chief din da taji ana fadi ne, “Unaisah” firgigit ta ɗauke idonta daga kallon chief da take Yi, Jin muryar Boss, da sauri yake tunkarota shigowarshi kenan part din, jallabiya ce a jikin shi, Ya sanya face mask a fuskarshi, tayi mamakin ganinshi a irin wannan lokacin, abunda bata sani lokacin da boss Ya ambaci sunanta, Chief owais Ya juya don ganin wanene ke magana, dai dai sa’adda ita kuma ta kawar da kanta, Natsuwa yai yana dubansu daga can saman second floor. “Ba ki yi bacci ba”? Tambayar da boss ya jefa mata kenan a yayin daya ƙaraso gabanta yaci burki ya tsaya yana kallon fuskarta. “Banjima da farkawa ba, amma meya hana ka bacci” ta tambaya tana kallon rinannun idanuwanshi masu dauke da tsantsar damuwa “Taya zan Iya yin bacci? Bayan kema bakiyi ba” Matashin murmushin ta ɗan saki, har cikin ranta taji dadin maganarsa, shi kuwa ji yake kamar ya rungumeta ko dan yaji sanyi aranshi, ya damu da halin da suke aciki ita da ɗan uwanta, tausayinsu ya hanashi sukuni har ya gaza runtsawa shiyasa ya fito don yazo ganin su. “Yakamata ka kwanta ka huta boss, na fahimci ka damu dani, meyasa”? “Taya bazan damu dake ba? Kefa jinina ce, jinin dake yawo ajikina shi yake yawo ajikin ki.....” da sauri Ya katse maganar, Jin su6ul da bakan da yai, murmushin gefen fuska tayi mashi, ga dukkan alamu taji dadin maganarshi “Boss kayi shiri baka ƙarasa zancen ba? Ni wallahi idan kana Yi min magana sai inji kamar mahaifina” “Meyasa kikace haka”? “Saboda Yana ƙaunata fiye da yadda yake kaunar kansa, ya sadaukar da farin cikinshi saboda ni, nayi rashin ji aƙuruciyata, na azabtar da daddyna amma duk idan na tuna ayanzu sai inji haushin kaina......” sambatu take yi mashi sam batasan me take furtawa ba, abune ya haɗe mata ga radadin da zuciyar ta keyi mata shiyasa take yi mashi zuba, tana magana hawaye na taruwa acikin idanuwanta. “Amma meyasa kike jin haushin kanki ayanzu”? Muryarshi araunace ya furta mata maganar. Shesshekar kuka ta soma yi mashi tana fadin”saboda nagane cewa bani da masoyi a duniyar nan daya wuce shi, bani da tamkar shi har abada, Har yau idan na tuna cewa shine silar duk wani abu dana koya aduniyarnan ba ƙaramin dadi nake ji ba.....” kasa ƙarasa maganar tayi, sakamakon janyota da yai zuwa jikinshi ya rungumeta sosai, haɗi da daura hannayenshi saman bayanta yana lallashinta, bata kawo komai aranta ba, sai dai bugun zuciyarta da taji ya ƙaru, tajima tana mamakin yanayin da take tsintar kanta idan Boss yana akusa da ita, sakankancewa takeyi taji kamar daddyn ta ne ya dawo. “Ya isa haka, ki daina kuka Unaisah, In sha Allah, daddynki zai bayyana, bama ke kadai ba da sauran ƴan uwanki duk zamu binciko maku danginku” Ajiyar zuciya ta shiga saukewa, takasa raba jikinta daga nashi, tamkar zata koma cikinshi. Duk wannan abun dake faru atsakanin Boss Man da Unaisah, akan idon chief owais, yayin da yake kur6ar coffee dinsa. Tunawa da Hijabin da zata daukone yasa tayi saurin furta”boss namanta, alwala nayi zanje daki na dauko hijabi da prayer mat, yakamata na tafi idan danish yaji na dade zai Iya biyoni, yanzuma da ƙyar ya bari na fito” ta fada tana raba jikinta daga nashi. “Nagode da kulawarka agaremu,” “Kada ki damu, muje na rakaki ɗakin,” “Banaso na takura maka, naga idanuwanka sun kaɗa jawur, baccine a idonka yakamata kaje ka kwanta” ta fada tana kokarin kakaro murmushi Ruƙo hannunta yai acikin nashi da zolaya yace”saifa na biki Allah, ai tunda baki runtsa ba nima bazan yi bacciba, zan zauna atare daku har sainaga abunda ya turema buzu naɗi” Dariya tadan saki jin maganarshi ta ƙarshe, atare suka jera zuwa bedroom din nasu. Koda suka ƙarasa dakin, arude ta furta”Boss babu batool fa”! Ta fadi tana faman zare ido akan gadonsu. “Calm down ur mind, nasan inda suke, ba sace su akayi ba, abunda ya farune dazu ya tayar masu da hankulansu, shine na rakasu dakin Ummi, nasan yanzu haka sunyi nisa acikin baccinsu” ajiyar zuciya ta sauke, har taji sanyi aranta. “bayin Allah, nasan daƙyar suka Iya runtsawa, musamman Azeeza tafi kowa tsoro a cikinsu” ta furta hakan tare da kama hanyar closet dinsu, bin bayanta yai da kallo harta 6ace ma ganin shi. Maganar amininshi ce ta fado mashi aranshi, a ranar daya kira shi video call yana daga kwance saman gado shida Angel dinsa. Tuni idanuwanshi suka cicciko tab da ƙwalla, haƙiƙa yayi babban rashin da bazai ta6a samun mai maye mashi gurbinshi ba” A hankali Ya furta”Allah Yajiƙanka aminina” “Boss mu tafi” muryar unaisa ce fargar da shi ga kallonta, Harta zura hijabin ajikinta launin milk, Iya gwiwa ta tsaya mata, hannunta a ruƙe da prayer mat. Lokaci ɗaya annurin fuskarta ya ɗauke, dama ranta babu daɗi, dauriya kawai take Yi, “Meyasa kika 6ata fuska”? Zumbura mashi baki tai kafin tace”kaine mana, kaƙi jin maganata ni nasan baccine ke addabarka, amma kaƙi zuwa ka kwanta, kalli idanuwanta har sun canza launi sun yi jawur da su...” cikin kulawa tayi maganar In a cool voice ya furta”karki damu dani, babu bacci atare dani, idona ne keyi min ciwo, kafin na fito daga gida saida na ɗiga magani” Unaisa sarkin tausayi, duk sai taji ba dadi, jin baida lafiya. “Allah yabaka lafiya boss, amma dan Allah kaje ka kwanta kayi bacci” Bakomai ya tuna ba face maganarta lokacin da tana yarintarta, Idan baida lafiya ya kwanta don yai bacci, saman jikinshi take hayewa tana fadin ai wallahi bazan bari kayi bacci ba, ka jira sai lokacin da nima zanyi sai muyi atare, idan ta fadi hakan to bai isa yai bacci ba, dole yajira har zuwa time da zata gama wahalar dashi tukunna suyi bacci, yayi zurfi acikin tunanin shi muryarta ta dawo dashi “Ka ƙura min ido kana kallona, ko nayi maka kama da wanine”? mamaki take bashi idan tana magana. Adabarbarce ya furta”um...bakomai mu tafi kawai” Ya ruƙo hannunta acikin nashi, Suka nufi ƙofar fita daga dakin. Kafin dawowarsu dakin danish, Tuni Big guy ya kawo mashi fresh fruit, a faffadan tray ya ajiye mashi saman mattress, abunka ga maciji, ɗai ɗai yake ɗauka da baki Yana lunkuma shi, Cikin ƙanƙanin lokaci Ya shanye kayan marmarin, bayan Ya kammala ci, Big guy ya tambayi Salsabeel Ina Unaisah take? Yaga babu ita adakin salsabeel Yace ta fita dauko hijabin sallah ne, amsa mashi yai da okey, kafin Ya dauki tray din Ya juya yabar dakin. Adai dai lokacin daya sauko down hannunshi ruƙe da tray, Unaisah da Boss man suna kokarin nufar benan, Da mamaki big guy ya furta”wa nake gani kamar Boss namu? Me ye hana ka runtsawa”? Fuska asake Boss Ya nufe shi yana fadin”abunda ya hanaka runtsawa nima shi yahana in runtsa” Dariya big ya saki”kai dai fadi gaskiya mutumina, nasan me ya hanaka yin bacci, damuwace ta isheka da fargabar kada maciji ya sari ƴarka, koba haka ba”? Ya faɗa yana ɗage mashi gira da zolaya. “Baka da dama Big guy, ai dole na damu, ita kaɗaice fa ƙwallin ƙwal, bugun zuciyar,”ya fada idanuwanshi akan unaisah wadda tuni Ta haura saman bene don ta isa ga dakin danish “Na fahimci ba ƙaramin so ka ke yi ma yarinyarnan taka ba, nima kuma inasonta, me zai hana ka bani auranta?da zolaya yai maganar Harara Boss Ya watsa mashi shima da zolayar yace”ka dai bi a hankali, kada mamallakinta Yaji ka, kaima kasan me zai biyo baya,” Da sauri Big guy ya toshe baki yana fadin”au namanta, ashefa ka bayar da ita, balle ma nasan koda baka bada ita ba da wuya ka bani ita, don na fahimci kafison inda zata huta” dariya boss yasaki yana fadin”kamar ka sani, kaima din ai ba daga baya ba, sai dai kayi mata tsufa, ina laifin ka nemi ummi mana zata dace dakai.....” tunkan ya ƙare maganar, Big guy ya galla mashi harara”Allah Ya kiyaye, in rasa wazan nema sai karuwa” Boss yace”abar dai kaza cikin gashinta, kaima din ai tubabbe ne, nima labari naji” “Ina ganin girmanka man, mu bar maganar, bana son tuna baya, Ni bansan ma wani munafukinne yabaka labari ba, wallahi da zan sani saina takaita jin dadinsa” Dariya Boss yai ganin yadda ya 6ata fuska. “Sorry mutumina, zolayatace kawai, ni bansan komai ba, kaine ka kama kanka,” “Next time idan ka ƙara min wannan wasan, A jikin ƴarka zaka gani” Ya fada tare da bi ta gefen Boss Ya wuce yana dariya, shima Boss din dariyar yakeyi “Ai kai ƙaramin ɗan iskane, sai dai ka cika baki indai akan Angel dinane, don kuwa kasan ko kallon banza kayi mata a jikinka zaka gani,” Big guy bai juyo ya dube shi ba, Yai tafiyarshi. Bayan komawar Unaisah dakin, a kishingiɗe ta samu salsabeel harya gaji da zama, macijin yana nannaɗe gefenshi. Tayi tunanin bacci yake yi hakan yasa ta soma yin sanɗa tana tafiya duk don kada ta farkar dashi, shimfida dardumar hannunta tayi, kafin ta daidaita natsuwarta, ta kabbara sallah. Boss na kokarin shigowa dakin aka fara kiraye kirayen sallar asuba, daga bakin kofar ya tsaya yai gyaran murya, salsabeel daya lumshe idanuwanshi jin gyaran muryar da Boss yai mashine yasashi bude idanuwanshi “Sannu da kokari, Mun hana ka bacci,” yamutsa fuska salsabeel Yai, bacci yana neman yaci ƙarfin shi “Baku kuka hanani bacci ba, ni na hana kaina saboda ɗan uwana” ya fada yana duban macijin. Kallon shi Boss Yai, gwanin ban tausayi ya langwa6e kansa, bawan Allah takaicin duniya ya ishe shi. Shiga cikin ɗakin Boss Yai, a bakin gadon ya dakata da yin tafiyar yana kallon Giant snake din “Bacci yake yi”? Ya jefa ma salsabeel tambayar “Bazai Iya runtsawaba, idan har ba Ƴar uwarshi tana atare da shi ba, sai kuma idan ya dawo ainihin halittarsa” Cikin tausayawa boss yace”kayi hakuri, wata rana sai labari, In sha Allah ƙarshen wahalarka ne Yazo, wadanda suka yi silar ƙuntata rayuwarka, bi’iznillahi ajalin su ne yazo, zasu ɗanɗani kuɗarsu har sai sunji dama ba a halitto su a duniyar nan ba, sai sunyi danasanin rayuwarsu.....” kalamai masu dadi da kwantar da hankali Boss yake fada ma giant snake din, yayi lamo yana sauraronshi. “Naji an fara kiran sallar asuba, Bari nashiga toilet inyi alwala, idan na fito kaima saika shiga ka yi mu tafi masallaci,” yai magabar yana duban salsabeel. Batare da 6ara lokaci ba, Boss ya shiga toilet ya dauro alwala, bayan ya futo salsabeel Ya shiga shima yai alwalar,, sallama sukayi ma Unaisah dake zaune saman darduma, kafin suka tafi. Kamar jira take Yi, subar ɗakin, jiki na 6ari ta miƙe ta nufi gadon ta haye gefen shi tana kallonshi, ta fahimci bacci yake ji, hakan yasa ta janyo bargo ta lullu6asu don ta taimaka mashi yai bacci. *EX-PRISONERS❤* Lokacin da Batul ta farka daga bacci, jikinta duk ba daɗi, tamkar mai fama da zazza6i, mura tayi mata mugun kamu, muryarta daƙyar take fita, fitowa tayi daga cikin bargon idanuwanta sunyi luhu luhu, ƙoƙari take tabar dakin duk don kada ta ƙara haɗa ido da ummi, tayi tsammanin zata ganta asaman gadon sai ganinta tay kwance saman carpet, ta lullu6e half body dinta da bargo, tafi ƙarfin ta haɗa shimfiɗa da su shine ta dawo kan carpet ta kwanta. Muryar batul kasa kasa ta ke ambaton sunan parveen, Daƙyar ta samu parveen ta farka daga bacci, tana faman yin miƙa haɗi da yin hamma, juyawa tayi 6angaren su Jemimah ta soma tada su daga bacci ɗaya bayan ɗaya suka farka suna faman mutsustsuke idonsu. Cikin muryar rada take yi masu magana”ku tashi mu tafi ɗaki, lokacin sallar asuba yayi,” ruƙo hannun jemimah tayi ta sauko da ita daga saman gadon, Parveen ta ruƙo hannun Azeeza suka sauko. “Bana so ta farka ta ganmu, kada ku yi surutu mu lalla6a mu bar mata ɗakinta” ta faɗa tana dubansu, Jinjina mata kai su ka yi alamar toh. Cikin takun sanɗa suka nufi ƙofar fita dakin, sai da suka fita Batul ta tuna da kayan ummi dake a jikinta, dafe kai tayi da hannu ɗaya”nashiga uku ashe ban cire mata kayanta ba, Parveen ki ruƙe hannun Aziza dana jemimah ku tafi ɗakin mu zan biyo ku daga baya” Maƙe kafada jemimah tayi”ni tsoro nake ji, idan abun nan ya ganmu fa”? “Kada ki damu, babu shi ai, waɗannan mutanan sun kashe shi” daƙyar batul take Yi masu magana “Batul baki lafiya? Idanuwanki sun kumbura jawur, muryar ki kamar ba’aji sosai” Azeeza ce tayi magnar. Kafin batul ta bata amsa parveen tace”sanyine ya kamata, sai da na hana ta kar6i rigata amma ta kar6a tasaka” “Amma ai aunty ummi ta bani kaya na saka, Kawai bana jin daɗine bawani abu ke damuna ba, Ku tafi ɗaki zan biyoki” Ta faɗa tare da juyawa ta nufi ɗakin. A tsananin tsoroce suke tafiya suna tunkarar benan, parveen tana aruƙe da hannun azeeza dana jemimah, har yanzu basu daina jin fargabar macijin ba. Bayan batul ta koma dakin Ummi cikin sanda take tafiya, harta ƙarasa gaban gadonta, ta cire mata kayanta, ta ɗauki doguwar rigar parveen data jefar ƙasa, ta zura a jikinta, Juyawar da zatai keda wuya, taji sautin datse kofar ɗaki, rass taji gabanta ya fadi ganin ummi atsaye bakin kofar ta goya hannayenta kan ƙirjinta, fuskarta a murtuke babu annuri, idanuwanta sun ƙanƙance. Hankalin batul ya tashi matuƙa, agigice ta furta”aunty ummi ina kwana” Harara ta galla mata”daban kwana ba kin ganni atsaye? Kilbabba uwar iyayi” Muryarta tamkar zata fashe da kuka tace”Ai na cire maki kayanki, gasunan kan gado, Ni dakinmu zan tafi, wajen unaisah” “Idan kinga na ƙyale ki kin fita daga dakin nan, to kuwa kin gyara sautin muryarki ne, wallahi baki isa kija min bala’e ba, Har kayan sanyi na baki, na kuma kashe sanyin a.c, saboda baƙin hali irin naki saida kika bari mura tayi maki mugun kamu duk don kija min masifa ko”? Hawayene suka soma wanke fuskar batul, muryarta na rawa tace”ba haka bane aunty ummi, nima bayin kaina bane, bansan mura ta kamani har haka ba, dan Allah kibarni in koma cikin ƴan uwana” Shu’umin murmushi ummi tayi mata, “Zan barki ki tafi, amma kafin nan saina fara kawar maki da murar nan, don haka mu shiga toilet inyi maki wanka da ruwan zafi” Zazzare ido batul tayi hadi da girgiza kanta”dan Allah aunty ummi ki ƙyaleni, ai ni ba yarinya bace, da zaki min wanka, ni kawai ki rabu dani nayi maki alƙawarin babu wanda zaisan ina yin mura” Ɗaure mata fuska ummi tayi zaki wuce mu shiga toilet ko saina 6ata maki rai”? Cikin jin ƙunar rai, batul ta maƙe mata kafaɗa”ni bazan shiga ba, Na fada maki banaso, ki ƙyaleni,” atakure take Yi mata magana, makoshinta radadi yake yi mata. Ganin ummi na tunkarota ne yasa ta soma ja da baya tana kuka, kokarin kubce mata tayi da sauri ummi ta damƙo sumar kanta, tajata ta ƙarfi ta shigar da ita toilet tana fadin”Ke har kin isa ki kufce min, ƙaramar ƴar shila dake, me zan gani a jikinki? da har kike fadamin ke ba yarinya bace” sautin kukan batul ya cika dakin ummi, gigitacciyar tsawar data kwatsa matane yasa tayi saurin jan baki tayi shiru, hawaye na cigaba da bin fuskarta. Ummi tafi ƙarfinta, da girmanta da komai, Tayi mata wanka da ruwan zafi, tamkar zata sale mata fatarta, fitowa ummi tayi daga cikin toilet din, ta nufi closet din kayanta, tana faman sakin murmushin mugunta, riga da wando ta dauko masu kyan gaske, na saƙa launin pink, waɗannan kayan tsohuwar ajiyace tuntana ƴar shekara sha bakwai a duniya take 6oyansu, tana matukar son kayan, rigar tana da hula hannunta dogone. Komawa toilet din tayi kamar yadda tabar batul haka ta sameta, ta ƙanƙame kanta jikin bango, dan pant ne ajikinta, hannunta biyu tallabe da kirjinta ta kakkare boobs dinta. Jefa mata kayan ummi tayi da sauri ta kar6esu. “Ina jiranki aɗaki, salon kuma ki daɗe, idan kika ƙara mintuna wani wankan zan sake yi maki” cike da isa ta furta maganar, kafin ta juya ta fuce daga toilet din, abakin ƙofar ta dakata tana jiran fitowar batul. Jin motsin buɗe toilet door dinne yasa ummi kai idonta ga dubanta, har saida taji gabanta ya fadi, ganin kyan da kayan sukayi ma batul, rigar tayi mata daidai, wandonma haka, kamar don ita aka saƙa kayan, bata sanya hular ba, yalwatacciyar sumar kanta ta sauko har gadon bayanta dark brown. Sai faman ƙanƙame jikinta take yi, ganin yadda ummi ke kallontane yasa ta duƙar da idanuwanta ƙasa, duk tasha jinin jikinta. Batasan ya akai ta tsinci kanta dayi ma fuskar batul kallon sani, sai dai tarasa tuna dawa take yi mata kama. Matsawa tayi kusa da ita, takai hannu ta ruƙo hular rigar ta sanya mata ita, sai taga ta ƙara yi mata kyau. “Ki daina ganin ina kallonki, ba kyau kikayi min ba, Munin fuskarki nake kallo” shiru Batul batace mata komai ba, bayan ta kammala gyara mata hular rigar, ta nuna mata gado”ki koma ki kwanta, har zuwa time da muryarki zata dawo dai dai kinji ko”? Maƙe mata kafaɗa batul tayi”ni bazan kwanta ba, dan Allah kibarni in tafi daki wajen ƴan uwana, Inason ganin Unaisah” muryarta shaƙe ta furta maganar. “Wato saboda kinga makwancina shiyasa kika fara rainani ko? Har kina da bakin fadin Bazaki yi abu ba idan nasaka ki, Dalla ni wuce ciki ko inyi ball dake” Ƙin matsawa Batul tayi, gani take kamar ummi zata iya kasheta, furucin da tayi mata jiya sun firgitar da ita, sun kuma tsaya mata aranta. Zabura tayi da niyar ta nufi kofa don ta gudu, ai kuwa azafafe ummi ta damƙota kamar ɗiyar roba haka ta ɗaga ta sama, ta nufi gado ta jefar da ita, ta kuma janyo bargo ta lullu6eta tana fadin”idan kika kuskura kika leƙo koda kankine saina murƙusheƙi” Muryar batul da shessheƙar kuka take fadin”aunty ummi dan Allah kibarni in tafi, banason kwanciyar, ni wajen ƴan uwana zanje” ummi dake tsaye tana kallon bargon tace”idan kina son fita daga dakin nan to ki fara gyara muryarki” “Ai ni bansan yadda zan gyarata ba, ki bani magani in sha” Ta cikin bargo batul take Yi mata magana. Tunani ta somayi aranta, ina zata samo mata maganin mura? Tasan ba’a rasa dakin ajiye magani a gidan tun da na jami’ae ne kuma yaran an tanadar masu komai da zasu buƙata saboda rayuwar kullece aka shirya masu. Boss man kadai take da contact dinsa, awayarta, daukar wayar tayi dake ajiye on bedside drawer ta danna ma Boss kira, cikin sa’a ya ɗaga kiran. Cikin girmamawa ta gaishe da shi”barka da asuba yalla6ai” On the other hand muryar boss ta amsa mata da cewa”wa’alaikum salam, ummi barka da safiya” “Yawwa barka, Allah yasa dai ban katse maka baccinka ba” “Kada ki damu, idona biyu yanzu nake shirin zuwa cikin gidan, ko akwai wani abu da kike buƙata”? “Taimako nakeso kayi min in ba takura, maganin mura nake buƙata” “Wanene ke baida lafiya”? Da sauri tace”nice zan sha, Yaran dake atare dani lafiyarsu ƙalau’ amsa mata yai da okey, idan zan shigo gidan zan taho maki da shi” “Nagode” katse kiran tayi tana faman sauke ajiyar zuciya, Batul dake a ƙumshe cikin bargo, abun duniya ya isheta. Muryarta shake tace”aunty ummi banyi sallar asubaba, kuma ina jin yunwa” Guntun tsoki ummi taja”kiyi min shiru malama, ni ma ai banyi sallar ba, kuma ina jin yunwar bawai bana ji ba” Ta fada Tare da samun wuri daga gefen gadon ta zauna tana gadin Batul, hannunta ruƙe da wayarta, chatting ta kama yi, batul tayi shiru cikin bargo tana faman matse ƙwalla. A katafaren Villa Mallakin Hateem Obinna, haddadiyar daula kuma aljannar duniya wadda idan ka zura ƙafarka acikinsa sai ka yi tsammanin ƙasar dubai ka shiga, Hamshaƙin Gidanshi a kewaye yake da Jami’ae sojoji da ƴan sanda, mugun tsaro ake yi mashi, babu wanda ya isa ya ƙetare gidan hateem cikin sauƙi idan ba Mahaifinsa ba da yayyansa, amma bayan wadanda kafin mutun ya samu iznin shiga ciki sai ya ci baƙar wahala don kuwa daga ƙasa har sama zasu bincike ka da na’ura, har ƙwara mutun ya shiga masarauta yafi mashi sauki, akan Gidan prime minister, tsaruwar ginin gidan kuwa da haduwarshi ba’a magana, gaba ɗaya Obie estate babu gidan da yakai Na prime minister In ka cire Villah din Owais. *Gimbiya Mujeedat👑* A kishingiɗe take saman Katafaran gadonta na alfarma, kalar na sarakuna waɗanda suka gaji Arziƙi, gadon a kewaye yake da labulaye launin royal blue, an ƙawata shi da lallausan zanen gado fari ƙyal, haɗi da matassan kai launin blue and white, gefe da gefen gadon bedside drawers ne suma launin royal blue, daga saman su Fitilune masu bada haske launi daban daban, an zuba mata tsadaddun furniture a ɗakinta, ya ƙawatasu sosai da kayan alatu. ta ɗaura kanta saman pillow, Rigar dake a jikinta Silk robe ce launin ice blue, tabi shape dinta ta bayyana dirarran dirin jikinta, A halitta Gimbiya Mujeedat doguwace, fara sol tana da dogon wuya, hutu ya zauna mata ta ko’ina Allah Ya hore mata, Kyau kamar ita ta zana kanta, fararen idanuwanta tamkar an ɗiga masu zaiba, launinsu dark black ne, ga tarin ziraran eye lashes dinta da suka ƙawata kewayen idanuwanta sun yi mashi rumfa, dogon hacinta a tsaye yake babu lanƙwasa, siraran la66anta launin ja tamkar na jarirai tsabar ƙarantarsu da laushin fatarsu, tana da yalwatacciyar sumar kai baƙa wulik mai santsi da silbi, har gadon bayanta, Tabarakallahu ahsanul khalilin Gimbiya mujeedat maƙurace afagen kyau, uwa uba ta fito daga tsatson masarautar daular larabawa, bugu da ƙari First Lady ta ƙasar Canada, ajin farko ce ita, zan iya cewa baba Hateem Ya more mata 😉 Ziririyar sarƙar wuyanta ta zallar diamond ce, haka zalika Ziraran yatsun hannunta na dama suna sanye da Ring set na Gold komai nata me tsadane ita kanta lu’u lu’un ce. Yanayin yadda ta kwanta da alamun kasala atattare da ita, ta ɗan lumshe idanuwanta, fuskarta sam babu walwala, kamar akwai wani abu dake damunta. A lokacin da bata yi tsammani ba, muryar prime minister Hateem ta karaɗe kunnuwanta, sallama ce yai mata yayin da yake shigowa dakin, Cikin shiga ta jallabiya launin maroon, daddaɗan ƙamshin turarenta dana ƙamshin turaren wuta ne Ya daki hancinsa Har saida Ya lumshe idanuwanshi, mutunne shi ma’aboci son ƙamshi, sai kuma Allah Ya haɗa shi da mace ma’abociya son kamshi da son ado, shiyasa a kullum take ƙara shiga ranshi, soyayyarsu bata tsufa, Idan suna atare da juna daukar kansu suke Yi tamkar sabbin ma’aurata. Bata samu damar amsa mashi sallamar shi ba, daƙyar ta iya buɗe idanuwanta da sukayi mata nauyi, launinsu ya rikiɗa zuwa ja, saboda rashin baccin da batayi ba adaren jiya kuma shine sila, Ya hanata sukuni, bai ta6a burkice mata ba irin Na jiya, Ƙiri ƙiri Ya takura kanshi, Ya hana kanshi runtsawa, kuma yaki fada mata abun da ke damun shi, daga ita har shi jiya babu wanda ya runtsa, saboda ta maida damuwarshi tata. Koda ya shigo dakin, a hankali ya daura idanuwanshi kan fuskarta, sai yaji ba daɗi har cikin zuciyarshi yasan bai kyauta mata ba, tunda ya riga da yasan halinta na damuwa da damuwarshi. Daga gaban gadon Ya dakata dayin tafiyar, ya goya hannayenshi on his broad chest yana fuskantarta. Ba zato ba tsammani, yaga ta galla mashi harara haɗi da murguɗa mashi ƙaramin bakinta. Nan take ya fahimci fushi take yi da shi, ranta ya 6aci. Cikin harshen turanci tace”Sannu da dawowa” Ta inda gimbiya mujeedat take burge shi, duk mun fushin da zatayi dashi hakan bai hanata kula da shi “Yawwa, fatan na same ki lafiya” Yamutsa fuska tayi fuskarta babu annuri ta soma magana tamkar bata son furtata. “Mijina baka kyauta min ba, ka hana kanka runtsawa nima kuma ka hanani runtsawa, nayi koƙarin faranta maka duk don na kawar maka da damuwarka amma babu abunda ya canza, Ka jefa ni cikin wani hali daga daren Jiya zuwa yau, meyasa ba zaka fadamin meke damunka ba? Ko ban isa nayi maka magani bane? Nasan ka yarda dani, sannan baka 6oye min komai, sirrinka nawa ne amma meyasa jiya kaƙi fadamin damuwarka” sautin muryarta tamkar ana busa sarewa tsabar daɗinta. Idanuwanta aruntse take yi mashi magana, don ta fahimci idan tana kallon cikin idanuwanshi bazata samu ƙwarin gwiwar yi mashi magana ba” Sauke hannayenshi yai daga saman kirjinshi, ya zagayo ta gefen da take a kwance Ya zauna, yana duban fuskarta Ƙayataccen murnushine kwance kan la66ansa, yasan ta kan mace, idan ranta ya 6aci cikin sauƙi yake faranta mata “Uwar gida sarautar mata, Gimbiyata, Ina neman afwarki ranki shi daɗe, bai kamata gimbiya tana fushi da bawanta ba, Ni fa a karkashin inuwarki nake, da taimakonki nake samun natsuwa da kwanciyar hankali, taya zanso na 6ata maki rai? Bayan kece linzamin dake sarrafa ni....” Tun da yafara gaya mata daɗaɗan kalamansa, ta fara sassauta fushin fuskarta, A hankali ta buɗe idanuwanta kan fuskarshi, da sauri ya kama kunnuwansa Yana fadin”Am sorry My wife, na gane kuskurena” Ta6e mashi baki tayi”Ni so nake ka fadamin meke damunka? Da har yai silar hanaka runtsawa, kalli fuskarka duk ta yamutse, idanuwanka sun ƙanƙance saboda rashin baccin da baka yi ba” ta faɗa tana faman 6ata fuska, yayi shiru yana kallonta batare daya furta mata komai ba. “Kai nake sauraro! Meke damunka? Sannan naji kana waya ɗazu, akan za’a tura da jet zuwa sudan, wa za’a ɗauko”? Ta jefa mashi tambayar cike da son jin amsar shi. Ya rasa amsar da zai bata, Ta kafe shi da ido. Gyara muryarsa yadanyi kafin yafara magana a tsanake. “Sheikh imam nake son gani, baya a ƙasarne ya tafi sudan, Ina buƙatar ganinsa da gaggawa akwai taimakon da zaiyi mani” Fuskarta da alamun mamaki ta furta”meyasa kake son ganin shi? Wani kalar taimako zaiyi maka” “Wani matashin yarone yake fama da aljanu sun hana rayuwarshi sakat, jiya ina zaune tare da baba muna yin firar yaushe rabo, a lokacin da bamuyi tsammani ba, yaron ya faɗo falon gwanin ban tausayi, duk mai imani idan yaji irin jarabtar da yaron yake fuskanta sai ya tausaya mashi.....” tun da ya fara magana gimbiya mujeedat ta yunƙura ta miƙe daga zaune tana dubanshi, Ya fayyace mata komai sai dai bai faɗa mata da suffar da ya ga yaron ba. “Na yanke shawarar yin magana da sheikh Imam akan halin da yaron yake aciki, Ina da tabbacin zai taimaka mashi In sha allah, yanzu haka da nake yi maki magana, sheikh imam Yana akan hanya, Ina tsammanin nan da ƙarfe goma jirgin daya ɗauko shi zai yi sauka a nigeria. Yanayin fuskartane Ya canza, yayin da take kallonshi, Ya rasa gane kallon menene take yi mashi, har dai yagaza jurewa jin shirun yayi yawa yace”baki fahimci abunda nake fadi bane? Ko bakiji dadi bane”? Girgiza mashi kai tayi”ko ɗaya mijina, wani abune yadan bani mamaki, nasan halinka ne yin taimako, indai abune daya shafi aikin Allah kana akan gaba, amma tunda nake arayuwata ban ta6a ganin tausayi da ya kai wannan ba atare dakai, saboda yaron jiya ba ka yi bacci ba, aduk lokacin da ka dawo gida a yanayi na damu nasan yadda zan shawo kanka in kwantar maka da hankalinta harma kayi bacci, amma adaren jiya saboda damuwar halin da yaron yake, waɗannan dabarun nawa basuyi maka aiki ba, bayan haka ka tura da jirgin da zai dauko malamin da zai duba shi daga Sudan zuwa Nigeria, saboda kana buƙatarshi da gaggawa don ya duba yaron....” ta faɗa fuskarta da alamun ruɗani, yayin da Hateem ya natsu yana sauraronta abunda bata sani ba ayanzun ma da take yi mashi magana hankalin shi yafi karkata kan agogon dake sanye a wrist din hannun shi, burinshi goma ta buga. “Abunda yafi ɗaure min kai mijina, wanene yaron? Menene alaƙarka da shi? Yanayin yadda ka nuna damuwa akanshi ko ɗan cikin ka sai haka” Jim ya ɗanyi kafin ya furta”bani da alaƙa da shi, bansan shi ba! Kuma ban ta6a ganin shi ba, kamar yadda na faɗa maki adaren Jiya idanuwana suka fara yin tozali da shi, tun daganan sai naji ƙaunarsa ta kama ni, har naji ina son na taimaka mashi, sai nake jima kamar nike da alhakin ciwon shi, idan har ban taimaka mashi yaji sauƙi ba Allah zai iya kamani da laifin ƙin tallafa masa da banyi ba” Murmushin gefen fuska Gimbiya mujeedat ta sakar mashi har fararen hakoranta suka bayyana. “Kai din na dabanne mijina” ta faɗa tana matsawa kusa dashi, ta ɗaura hannunta na dama saman sumar kanshi. “Samun miji kamarka a duniyar nan abune mai wuya, kana da tausayi da jinƙan na ƙasa dakaina, sannan kowa naka ne, burinka ka faranta ma wanda yake acikin kunci koda ta silar hakan kai zaka rasa naka farin cikin, ni kaina ina ilmantuwa da kyawawan ɗabi’unka da halayanka, shiyasa nake alfaharin mallakarka da nayi a matsayin mijina” lumshe idanuwanshi ya ɗanyi kalamanta ba ƙaramin faranta mashi suke Yi ba, tamkar tana ƙarfafa mashi gwiwane. Zame hannunta tayi daga kan sumar shi zuwa gefen fuskarshi idanuwansu cikin na juna “Kamar yadda ka sani, duk abunda kakeso nima inason shi, koda bana son shi saina yi kokarin koya ma kaina yadda zanso shi saboda mijina yana son shi, don haka nima ina goyan bayanka akan Yaron, Allah ya baka sa’a mijina ya cika maka burinka na ganin yaron ya samu lafiya, A shirye nake dana bada gudummuwata wurin ganin mun inganta rayuwarshi” Murmushine ya bayyana akan fuskar prime minister, kallonta kadai da yake yi natsuwa yake samu, musamman idan tana ƙarfafa mashi gwiwa da daɗaɗan kalamanta. “In sha Allah zamuyi nasara, yaushe zaka bani iznin zuwa ganin yaron”? “Na yanke shawara idan yaji sauƙi, zan gayyace shi zuwa gidan mu, zamu shirya mashi dinner.” Tsantsar farin cikine akan fuskarta”naji dadin jin hakan mijina, wallahi har na ƙosa naganshi, duk na kagu gashi bazamu daɗe a ƙasar ba, kwanaki kadan suka rage mana” ta fada tana 6ata fuska alamar bataso hakan ba. Damƙo hannunta yai da take kokarin shafa wuyanshi, fari sol dashi, ga wani shu’umin kamshi dake fita sako da lungu na jikinta, sumbatar tafin hannu yai, ba tare da ya sake shi ba ya dago da reddish eyes dinshi akan fuskarta”yaron marayane bashi da kowa, Owais ne ke kula da su, zan nemi alfarmar yabar min shi mu tafi canada atare, inaso ya maye min gurbin abunda narasa” sai yanzu ta fahimci damuwarshi. Tausayinshi ne ya kamata, tuntuni tasan yana da burin samun ɗa Namiji, yaso ta ƙara haifa mashi ƴa’ƴa sai dai shiru babu alamun zasu sake samun ƙaruwa, kuma lafiyarta ƙalau saboda shi yasa bata yin tsarin Iyali, Allah ne bai nufa zata ƙara haihuwar ba. Kafin ta buɗe baki tayi mashi magana, wayarsa dake ajiye cikin aljihun shi ta soma yin ringing, ya riga da yasan wanene Ya kirashi. Da sauri Ya saki hannun Gimbiyarsa, Ya zura hannu ya zaro wayar picking call din yai tare da karata a kunnanshi, gimbiya mujeedat ta kura mashi ido tana kallon shi “Alhamdulillah, Allah ya kawo ku lafiya,” iya abun da taji ya furta kenan, zame wayar yai daga kunnanshi yana dubanta yace”sun sauka lafiya” Gimbiya mujeedat tace’shiyasa naga farin ciki akan fuskarka, sheik imam yaƙaraso kenan, bari nayi magana da masu aiki su shirya maku breakfast dinku” Ta fada tana kokarin daukar phone dake ajiye on nightstand da sauri ya ruƙo hannunta, ta dago da ido suka kalli juna “An shirya mashi breakfast dinshi, tun acikin jirgi, ina da tabbacin babu yunwa ko gajiya atare da shi, nafi buƙatar idan ya ƙaraso mu tafi gidan Owais din” “Amma kaifa? Baka ci komai ba, Yakamata kayi breakfast dinka, zaka fi samun kuzari” Girgiza mata kai yai”Bana buƙata, saboda bani da natsuwar cin abinci, Idan har yaron nan bai dawo dai dai ba, nafi son idan Ya samu sauƙi, muci abincin atare da shi” Tsantsar mamakin kalamansa ne ya daure mata kai, bata ta6a ganin ƙauna kalar wannan ba, Ko a shirin film. “Amma kasan bana iya yin breakfast ba atare dakai ba, idan har baka ci ba, nima bazan ci komai ba, har sai ka dawo gidan” cikin tausasa harshe tayi maganar. “Yau kawai, Kiyi hakuri kiyi breakfast tare da su Yazrin, bazan jima ba, in sha Allah atare zamu yi lunch dinmu” Kwa6e mashi fuska tayi hadi da marairaice mashi tamkar zatayi mashi shagwa6a ta furta”bazan takura maka ba, Na kar6i uzurinka” “Ki tashi ki shirya inaso ku gaisa da shekh imam kafin mu wuce gidan owais” amsa mashi tayi da toh, kafin ta sauko daga saman gadon, shima ya miƙe yana bin bayanta da kallo, har ta 6ace ma ganinsa, jim kadan ta fito sanye da Abaya launin Maroon tayi rolling mayafi akanta, ruƙo hannunta yai acikin nashi, suka nufi kofar fita daga dakin. Lokacin da suka shigo babban katafaren palourn gidan, masu yi masu hidimane suke ta gudanar da aikace aikacen su, kowan nan su sanye da uniform baƙin wando da farar shirt, matasan ƴan mata, duk inda Suka gifta jiki na 6ari suke gaishe dasu cikin girmamawa, yayin da su kuma suke amsa masu da fara’a. Yanke shawarar zuwa bedrooms din Ƴa’ƴan su suka Yi, kafin ƙarasowar Ya sheikh, Yana da buƙatar suma su kasance cikin shiri donsu yi mashi kyakkyawar tarba. elevator suka hau ta daukesu zuwa upstairs, bayan ta sauke su suka fito batare da sun saki hannayensu da suka ruƙe acikin na juna ba, kaitsaye suka nufi bedroom din ƴan matan su. Gaba ɗaya ta tattara hankalinta akan Apple laptop din dake agabanta, yayin da take zaune a tsakiyar katafaren gadonta dake acikin hamshaƙin ɗakin kwananta daya gaji da haɗuwa, ko dakin sarauniya Albarka, farace sol kamanninta sak dana Mahaifinta Hateem, yadda kasan ta macen aljanna saboda kyanta da dirinta, kamanninta sun 6aci dana Hateem, tamkar yayi kakinta, Hasken fatarta ne kadai ta dauko na mom mujeedat da doguwar sumar kanta, mace ce mai aji, mai ji da ƙasaita da izza, bakowa bace wannan face NAZLI, itace first born dinsu, a ƙalla zata kai shekara ashirin da takwas a duniya, tana asanye da lace Camisole daga sama ta ɗaura silk robe launin hot pink, a tsanake take operating laptop dinta cikin ƙwarewa, yayin da kyawawan idanuwanta dake a manne da farin glass suke akan screen din laptop nata, daga gefen gadon ƙayataccen round table ne daga saman shi china tea set ne, jefi jefi takan kai hannu ta dauki cup ta kur6i coffee din dake aciki, Nazli agogo sarkin aiki bata gajiya tana da hazaƙa da ƙwarewa a 6angaren Iya kasuwanci, Company guda take juyawa na mahaifinsu dake a ƙasar Canada, ƙamshin turaren jikinta ya buɗe ko’ina na room dinta, hatta sumar kanta kamshin turaren data turara ma gashinta ne ke fita, kullum ne sai ta turara jikinta da gashin kanta, Nazli badai tsafta ba. “Assalamu alaikum” Muryoyinsu ne suka janyo hankalinta ga duban ƙofar shigowa room dinta dake a kulle, daga inda take tana Iya hangen su ta cikin kofar, saukowa tayi daga saman gadon, sumar kanta ta rufe bayanta tamkar hijabi tayi mata, daura idonta tayi akan cashmere slippers dinta dake ajiye saman lallausan carpet, ta zura su cikin kafarta, kafin ta nufi kofar cikin takun izza, ta sanya hannu biyu ta ruko handle din kofar ta buɗe ta. Fuskokinsu dauke da murmushi suke kallonta, sai dai ita babu alamun murmushi akan fuskarta, haka take bata da fara’a, taji dadin ganinsu amma bazaka Iya gane hakan ta yanayinta ba saboda tsabar ji da izzarta, Cikin harshen turanci tace “Good morning, Mom and Dad! I’m so glad to see you, yau kun riga ni zuwa room dina, yanzu nake koƙarin kammala aikin da nakeyi a laptop....” Ta ƙare maganar tare da matsawa ta rungume daddynta, hannu biyu ya daura saman bayanta”barka da safiya daughter, Ina fata kin tashi cikin koshin lafiya” Muryarta ƙasa ƙasa ta amsa mashi da cewa” “I’m doing well, Dad. I’ve been thinking about you since yesterday. I’ve missed you.” Gimbiya mujeedat tace”oh shi kaɗai ki ka gani shiyasa kika rungume shi ko? Da zolaya tayi maganar. Ɗagowa Nazli tayi tare da miƙa hannu zata rungume mujeedat, da sauri gimbiya mujeedat taja da baya tana fadin”nayi fushi, ba tun yauba na lura kinfi ji da daddynki, shiyasa nima nafi ji da Yazrin daboda tafi nuna damuwa akaina” Marairaice mata fuska Nazli tayi haɗi da kama kunnanta”agafarce ni sanyin idaniyata, mahaifiyata abun alfaharina” Sakin fuska mujeedat tayi”nayi hakuri amma kada ki ƙara yi min hakan, Daga yau ni zaki fara hugging kafin daddynki” ta faɗa tana kallon Hateem dake kallonsu, fuskarshi dauke da murmushi yace”na fahimci kishi kike yi dani akan Nazli, Yarinya tafi son ubanta, da ni da ita ƙaunace mai ƙarfi, baki ga kamannin fuskarmu ba? Shiyasa take ji dani, ke kuma kije da Yazrin itace take kama dake” Farfari tayi mashi da ido batare datace komai ba, ta rungumo nazli ajikinta tana ɗan bubbuga bayanta da hannu tace”sannu agogo sarkin aiki, tun da sassafe ko breakfast bakiyi ba kin fara danna laptop, Ina fata na same ki lafiya”? Ɗagowa tayi da kanta tana fadin”Ina lafiya mommy, bana so aiki yai min yawa shiyasa nake ragewa” ta fada tana dubansu. “Naji dadin ganinku, duk da ni yakama naje na sameku, ban samu damar yin hakan ba,” Prime minister yace”bakomai daughter, muma munji dadin ganinki, Inaso ki shirya Zanyi baƙo Ƴan mintuna suka rage su ƙaraso, daga sudan zaizo, gaisawa zakuyi da shi,” Batare da ta tambaye shi wanene zaizo ba tace”in sha Allah daddy, yanzu zan sauko down” Amsa mata yai da toh, kafin ya dubi mujeedat, muje ko” ya runƙo hannunta suka juyawa zuwa dakin Yazrin, A lokacin Yazrin tana daga kwance cikin bathtub dake a bathroom dinta, ta jiƙe jikinta da ruwan kumfa mai ɗumi, ta lumshe idanuwanta yayin da take shaƙar ƙamshin bath soft dinta daya karaɗe toilet din tamkar an fesa turare, A kalla zata kai shekaru ashirin da biyar, Yazrin ƙarshe ce afagen haduwa bata baro komai na mahaifiyarta mujeedat ba, launin fatartane kadai kalar na hateem, haskenta bai kai na mujeedat ba, daga ita har Yazrin babu wanda yafi wani kyau, ta inda suka banbanta Yazrin tafi Nazli sauƙin Kai da iya mu’amala da mutane, Ita Nazli bata son bare, ƙiwuya gareta kamar ƙaramar yarinya ga ji da izza, magana ma wuyar furtata take ji. Sautin ƙarar door belt ne ya katse mata jin daɗinta, A hanzarce ta ɗaure jikinta da ruwan dumi, kafin ta fito ta ruƙo towel dake sagale jikin hanger ta ɗaure qugunta da shi, Shigowa Bedroom din tayi da sauri ta nufi wardrobe dinta, shaf shaf ta zura jallabiya a jikinta, ko tsane jikinta bata samu damar yi ba, sumar kanta duk ta nannaɗe saman kafadunta. Buɗe kofar ɗakin tayi fuskarta dauke da kayataccen murmushi, dimples dinta biyu sun lotsa Su kansu da sukayi tozali da ita saida suka saki fara’a, Yarinyar akwai shiga rai, da wuya kaga fuskarta adaure, kafin su bude baki suyi mata magana ta ware hannayenta biyu ta hadasu ta rungume tana fadin”Mom dad, tunkafin nazo gaishe ku kun riga ni zuwa, kunsa naji nauyin hada ido daku” Ta faɗa tare da ɗagowa da kanta tana faman kare fuskarta da tafin hannunta Dariya kowan nan su yasaki, Prime minister yace”barka da safiya daughter, fatan mun same ki lafiya”? Jinjina mashi kai tayi”lafiyalou daddy, amma ni baku kyauta min ba, maimakon ku bari ni in fara zuwa gaishe daku” ta fada tana bubbuga ƙafafuwanta da shagwa6a. “Ladar da nake kwaɗayin samu, Kun rigani kwashe ta” dariya mujeedat tasaki tana fadin”Wato ke har yanzu baki girma da shagwa6a ba” Hateem yace”barta tayi abunta, don bata da ƙanine shiyasa take yi mana shagwa6a” Nuna kanta tayi da yatsanta”saboda nice auta mommy, dagani babu ƙari, kunga kuwa dole nayi shagwa6a” ta fada tana ruƙe masu qugu, Ba ƙaramin nishaɗi take basu ba, Hateem yace”baki fada mana ya kika wayi gari ba,” “Na tashi lafiya daddy, tun safe nasha coffe, yanzu haka wanka nakeyi a toilet naji ƙarar knocking dinku shiyasa na fito” “Kina nufin baki ƙarasa wankan ba”? Acewar mujeeda. Yazrin tace”tun ɗazu fa na kammala, kawai inajin daɗin kwanciya acikin ruwane” “Okey, Ki koma ciki ki shirya muna jiranku a downstairs, daddynku ne zai yi bako daga kasar sudan, yanaso ku gaisa dashine” Yazrin tace”okey mom, bari na shiga ciki in shirya” Ta fada tare da kallon Daddynta, harta buɗe baki zatayi mashi magana, sautin ƙarar dirar motocin dake shigowa gidan nasu ya katse mata hanzarinta, muryarta tamkar tame yin raɗa ta furta”bakon ya karaso kenan, bari nayi sauri naje na sanya kayan mutunci” ta juya da sauri ta shige cikin dakin Murmushi kowan nan su yasaki, mujeedat tace”yazrin kenan, tana bani nishaɗi, sai dai narasa gane halin wa ta dauko atsakanin nida kai” Nuna ta yai da yatsa”ke mana, har sai an fadi, ni dai kin san ba haka nake ba, idan kika dubi ɗabi’un Nazli sak kalar nawane” Hararar zolaya ta yi mashi”nazli fa hada izza ta sarauta ke ɗawainiya da ita, kai ina kaga sarauta? Nice na gajeta, sai dai ta 6angaren siyasa nan kafi karfi, kuma shi ɗan siyasa da fara’a aka sanshi, hakan na nufin halinkane yazrin ta dauko bani ba” “Gorin sarauta zaki yi min”? Ya faɗa yana kanne mata ido. Tana dariya tace”ni dai bance ba, ai kafi ƙarfin ayi maka gori, dani dakai babban gorone magogin ƙarfe” Ta fada tare da ruƙo hannun shi”muje kada su jimu shiru, ina tunanin sune suka ƙaraso” atare suka nufi down stair. Adai dai lokacin zungureriyar motar da ta ɗauko Sheikh imam daga airport, ta karaso bakin entry hall nagidan Prime minister a hankali tayi parking, gaba da bayanta motocin sojoji ne da suka dauko shi domin bashi tsaro, fitowa sukayi daga cikin motocinsu, wani ƙato daga cikinsu ya buɗe mashi murfin mota, A hankali sheikh Imam malik Ya zuro kafarsa ta dama dake asanye cikin takalma na alfarma, kafin Ya ƙarasa fitowa, masha Allah, magadan annabawa, kallon ɗaya zakayi mashi ka shaida maluntakarsa, yayi shiga ta alfarma shiga ta larabawan saudi arebiya, farar throbe ce, daga sama ya daura wata shara sharar riga, kanshi yana asanye da kufi ƴar karamar hula ta malamai, an nannaɗeta da black turban, Yana da godon gemu, babban mutunne ya manyata don harya fara tsufa gashin gemunshi hada furfura ta manyantaka, duhun fatarsa mai kyau ne, kai daga ganin shi baida wasa irin malaman nan ne masu zafi akan addini, babu tsoro a idanuwanshi, mutunne mai cikar kamala, ya shahara a 6angaren wa’anzartawa da yin da’awa ta addinin musulunci, yayi gwagwarmaya a kasashe daban daban babu inda bai shiga, kuma yana cin nasara akan da’awarsa, shaidanun aljanu kansu tsoronshi suke Ji, Suna jin shakkar zama a inda shekh imam malik yake, mutunne shi mai koyi da sunna ta manzon Allah SAW, Ya ruƙe Allah ɗaya azuciyarshi, kainuwane shi dashen Allah, badai mutun ba sai Allah, ta ko’ina jikinshi ƙamshin turarensa ne mai dadin shaƙa a hanci, hannun shi na dama ruƙe da cazbaha. A hankali Yake bin ko’ina da kallo, Yayin da yake shaƙar kamshin iskar data gauraya da ƙamshin turarensa. “Ya mu’allim, mu ƙarasa shiga ciki,” ɗaya daga cikin Sojojin ne yai mashi magana haɗi da nuna mashi kofar shiga babban falon, ɗaga kafarshi yai atsanake yake yin tafiya, suna gab da zasu shiga falon, Prime minister ya fito tare da gimbiya majeedat, Murmushin dake kan fuskokinsu ne ya ƙara faɗaɗa, da sauri hateem Ya mika mashi hannu suka gaisa cikin girmamawa”Marhaban bika babana, barka da sauka, ya gajiyar tafiya” ya fada tare da rungumeshi, bayan sun raba jikinsu daga na juna Sheikh imam yace”ai ni babu gajiya atare dani, ni da aka gatantani kamar wani basarake haka aka daukoni a privet jet, hankali akwance naci na koshi na cika tumbina” Ya fada yana nuna tumbinshi da cazbahar hannunshi, gaba daya suka sanya dariya gwanin ban sha’awa, sheikh imam mutunne mai son barkwanci amma fa sai idan yaso. Prime minister yace”Akara makallah ai kafi karfin basarake awurinmu, ku fa magadan annabawane, kunfi duk wani mai muƙami a karkashin tafin kafarku Yake” Murmushi Shekh imam Yasaki, Tare da daura idanuwanshi kan fuskar Gimbiya mujeedat, kafin yayi magana tayi saurin gaishe shi cikin harshen larabci. Da zolaya yace”Hateem dama ana ganin fuskar matarka? Ya akai yau baka rufe lu’u lu’un ka ba”? Koba ita bace matar nan da ake yi mana 6oyanta ba? Kodai Ƴarce”? Kunyace ta rufe gimbiya mujeedat, Ta sanya hannu ɗaya ta kare fuskarta Hatta jami’an dake a kewaye da Ya shekh Imam saida suka saki murmushi . Dariya prime minister yasaki a fakaice ya harari Jami’an dake atsaitsaye suna kallonsu, jiki na 6ari suka juya kowa yakama gabanshi, don sun fahimci me yake nufi, wato suna kalle mashi matarshi. “Ya sheikh Mu ƙarasa cikin falon, mun barka atsaye gashi ka kwaso gajiya” prime minister ya fada tare da ruƙo hannun shi, Suka nufi babban falon Gidan, Gimbiya mujeedat tana abiye da su. “Hateem Irin wannan daula haka? Anya kuwa kuna tunawa da mutuwa? Ka ajiye lu’u lu’u agidanka ga kuma kayan alatu ta ko’ina, maimakon ku bari sai mun shiga Aljana muji daɗi” Ya faɗa yana Jijjiga cazbahar hannunshi, Dariya suka sanya gaba dayansu, A saman Royal sofa kowan nan su Ya zauna, suna fuskantar juna da sheikh imam, sai faman jinjina kai yake yi yana bin gidan da kallo, duk maganar da sheikh imam zaiyi yanayin amfani da harshen turanci saboda mujeedat yasan bata jin hausa sai dai turanci da larabci. “Yanzu kai hateem, Har kake iya kwana acikin daular nan? Wannan haɗuwa haka ai sai mutun ya manta da tur6aya aka halicce shi” Murmushi suka saki suna dubanshi Sautin takun takalman Yazrin da Nazli ne Ya janyo hankulansu ga dubansu, Hannunsu ruƙe cikin na juna suke yin tafiya suna tunkarosu, kowaccensu ta yafa mayafi akanta, Bayan sun ƙaraso, Cikin girmamawa suka gaishe da shekh Imam, Abunda Ya burgeshi da yaran tarbiyarsu, A saman lallausan carpet din dake a atsakankanin Royal sofa din suka zauna kowaccensu ta nade kafafuwanta “Masha Allah, Matan hurul aini har a duniya, Hateem, wacce zaka bani acikinsu in cike sunnah”? Ya faɗa yana duban faces din Yazrin da Nazli, Yazrin sai famam sakar mashi murmushi take Yi, Nazli kuwa tunda ta gaishe dashi ta sunnar da kanta ƙasa. “Duk wadda ka za6a malam, zamu baka Ita” acewar mujeedat, Shekh imam yace”Uwargida maganarnan taki bata kai zuci ba, ni nasan kin faɗine kawai, taya zaku ba yarinya auran dattijo? Mai jan cazba, balle ƴan matan zamani basu son auran malamai” Murmushi kowannansu yasaki, banda Nazli. Biyu daga cikin masu aikin gidanne suka nufo falon, hannunsu ruƙe da faɗaɗan farantai daga sama an jera drinks masu sanyi da snacks. Tunkafin su karaso sheikh imam yace”waɗannan fa? Badai ni zasu kawo mawa ba? Bayan abincin da naci acikin jirgi har wani ƙari za’ayi min? A’a gaskiya Ni a koshe nake, Ko ruwa bana jin zai Iya wucewa ta makoshi na” Prime minister yace”babana adai daure ko ruwan ne kasha,” Gyaɗa kai yai toh, naji iya ruwan zansha, Asaman carpet suka daura farantan, mai aikince ta zuba mashi Apple juice mai sanyi a cup ta miƙa mashi, Yasa hannu ya kar6a, Kur6a uku yai ya dawo da dubanshi gasu Nazli”ƴan matan hateem ina fata na same ku lafiya? Ya karatu? Ko da yake nasan kun kammala, to Ya aiki” Atare suka amsa mashi da cewa”lafiyalou Alhamdulillah,” jinjina kanshi yai”Masha Allah,” bayan ya ajiye cup din alamar ya kammala sha, Prime minister hateem Yace”nasan yanzu ka kwaso gajiya, ko zamu bari zuwa anjima idan ka huta sai mu fara shiga gida ku gaisa da baba kafin mu wuce can gidan Owais din inda Yaron yake”? Girgiza kai sheikh imam yai”A’a, tun da mahaifin naku baisan da zuwana ba, to ba yanzu zanje gaishe shi ba, nafi buƙatar ganin yaron, don agaskiya ni babu gajiya atare dani, ka tashi mu tafi kawai,” Kallon mujeedat Hateem yai”zamu tafi, in sha Allah bazamu daɗe ba, a taya mu da addu’a” murmushi tasakar mashi”ubangiji Allah yasa ayi asa’a, Ina yi maku fatan alkhairi” amsa mata yai da ameen, kafin ya maida dubanshi gasu Nazli da Yazrin”daughters ku tayamu da addu’a, ga mommynku nan zatayi maku bayanin komai dangane da zuwa sheikh imam” amsa mashi sukayi datoh, kafin ya ɗago Ya kalli Ya sheik wanda tuni Ya miƙe tsaye, miƙewa hateem yai atare suka nufi kofar fita falon, tunkafin su ƙarasa Jami’en dake atsaye bakin motar data dauko sheikh daga Airport Yai saurin bude masu motar, Bayan sun shiga daga ciki, jami’en Ya zauna a driver’s seat Ya tashi motar, atsanake Yake yin driving dinsu........ *Chief Owais✊❤* Tun bayan daya dawo daga masallaci, Yin sallar asuba bacci ya addabi idanuwanshi, adaddafe ya shiga bathroom yai wanka, within minutes ya fito waist dinshi ɗaure da white towel, kan mirror chair ya zauna da niyar ya kimtsa kanshi, sai dai yakasa tabuka komai saboda kasalar data kame sassan jikin shi, idan har ba baccin nan yai ba to kuwa bazai ta6a samun sukuni ba, kyawawan idanuwanshi sunyi mashi nauyi daƙyar yake iya buɗe su, miƙewa yai bai nufi ko’ina ba sai saman katafaren gadonshi, Ya haye ya kwanta tare da jan bargo ya lullu6e rabin jikinsa, In a short time bacci yai awon gaba da shi. Tsawon awanni yanata sharar baccinsa, tun karfe shida har goma da rabi ta buga, Yayin da numfashinshi ke fita cikin natsuwa da kwanciyar hankali, phone dinsa dake ajiye gaban dressing mirror ta soma yin ringing, da zarar kiran ya katse wani ke shigowa, ringin din ya fara takura mashi, mutsu mutsun farkawa daga bacci ya somayi, A hankali Ya ware fararen idanuwanshi dake fuskantar ceillin din dakin nashi Tsawon minutes, kafin Ya laluba hannunshi Cikin kasala Ya ruƙo wayar ya duba sunan me kiranshi, sunan Uncle Hateem ne Ya bayyana akan screen din wayar, Kiran harya kusa katsewa yai saurin yin picking, tare da manna wayar akan kunnansa “My son, Ina fata ban takura maka ba” Yamutsa fuskarshi yadan kafin ya furta”Barka da safiya uncle, fatan ka tashi lafiya”? “Lafiyalou, naji muryarka da alamun bacci bai isheka ba” “Kiran wayarka ne Ya tashi ni daga bacci, Ina fata lafiya” “Banji dadiba amma kayi hakuri da takura makan da nayi, ni kaina bansan dililin dayasa na damu da yaron ba” “Ba damuwa uncle” “Yanzu haka da nakeyi maka magana Muna akan hanyar zuwa Gidan naka tare da sheikh imam” Lumshe ido owais yai har cikin ranshi yaji dadin jin zuwan Sheikh imam “Ina yi mashi barka da zuwa, Allah ya kawo ku lafiya” Hateem Ya amsa mashi da amen mun gode son,” daga haka sukayi sallama da juna. Daura wayar yai saman side drawer ya sauko daga saman gadon Ya nufi dressing room din dakin shi, badajimawa ba ya fito sanye da jallabiya launin sky blue, tayi bala’en yi mashi kyau, Gaban dressing mirror din dakin ya tsaya tare dakai hannu cikin jerin turarurrukansa ɗaya bayan ɗaya yake dauka yana feshe jikinshi, tuni ƙamshinshi ya karaɗe dakin. Diamond wrist watch din shi dake ajiye gaban mirror ya dauko Ya zura a hannunsa, Kafin Ya miƙa hannu Ya dauki Phone dinsa, A tsanake Yake pressing dinta, Layin Boss Ya danna ma Kira, Bugu Uku Yai picking, gaisawa suka farayi kafin Ya furta”Sheikh Imam Ya ƙaraso, Ina buƙatar ganin kowannanku a main falo, domin mu tarbesa” Boss Ya amsa mashi da Toh, In sha Allah, Yanzu zan sanar da su” daga haka Yai rejecting kiran. A dai dai lokacin, Unaisah ta kuma farkawa daga baccin da yayi awon gaba dasu ita da giant snake din, Cikin sanɗa ta sauko daga saman gadon, tana tafiya tana waiwayon gadon, ta kudundune shi da bargo, ta ƙagu da son ganin ƴan uwanta shiyasa zata fita taje gare su, batasan a wani hali suka kwana ba. Bayan ta fito daga dakin down ta sauko, Moving quickly ta nufi Hanyar da zata hau bene taje dakin ummi, Har ta kusa haurawa saman staircases miryar boss man ta katse ta”Unaisah”! Cak ta tsaya haɗi da waiwayowa tana dubanshi, “Ina zakije ne”? Muryarta adisashe ta furta”dakin aunty ummi, Inason ganinsu batul ne, ai ka fadamin acan suka kwana” “Hakane, Nima dakinta zani je, amma tunda gaki bari in baki sako ki kai mata” ya fada tare da zura hannu cikin aljihu ya curo maganin mura ya miƙa mata. “Wanene bai da lafiya”? Hankalinta atashe ta fada tana bin maganin da kallo. “Ummi ce ke bata jin dadi, mura ce ta kamata” Ajiyar zuciya Angel ta sauke tayi tunanin ko cikin ƴan uwanta wani ke bai da lafiya. Kar6ar maganin tayi, har zata juya muryarshi ta dakatar da ita”Sheikh imam yana akan hanyar zuwa gidan nan, malamin da zai duba ɗan uwanku danish” Waro ido waje tayi lokaci ɗaya ta fashe da dariyar farin ciki, Murmushi yasaki Dama ya fada matane don ya faranta mata rai. Idanuwanta cike tab da ƙwalla take fadin”Alhamdulillah, wayyo Allah wallahi naji dadi, fatana Allah yasa ayi asa’a danish ɗina yaji sauƙi ya dawo kamar kowa” Boss yace”in sha Allah zamuyi nasara, yanzu kije ki kai mata maganin, idan kin fito ki same mu a falo, Amsa mashi tayi da toh, jiki na rawa ta nufi benan ta haye sama, burinta takai mata maganin sannan ta kwantar masu azeeza hankalinsu kafin ta dawo falon don taga sheikh imam” Abakin ƙofar dakin Ummi ta dakata tare dakai hannu ta dafi glass door din A hankali kofar ta buɗe, Zura kafarta keda wuya sukayi kicibus da batul, sam hankalinta ba akwance yake ba, ganin ummi ta shiga toilet tsawon lokaci bata fitowa ba shiyasa ta yi dabarar guduwa daga dakin don ba ƙaramin takura tayi ba, baiwar Allah suna haɗa ido da Unaisah, ta faɗa jikinta, Hannu biyu ta ƙanƙameta dasu kamar zata koma cikinta, tun daga kan yadda ta rungumeta ranta ya bata cewar babu lafiya, A hankali itama ta zagayo da hannayenta saman bayan Batul. “Meke damunki sister? Baki da lafiyane”? Ta fada batare data raba jikinsu daga na juna ba Muryar batul ashaƙe da mura ta furta”babu komai, Mu tafi dakinmu, Ni kadaice na rage su azeeza sun tafi tun ɗazu, Ni ko sallar asuba banyi ba” Hankalin Unaisah ba ƙaramin tashi yai ba, Jin muryar Batul ashaƙe kamar an ɗaure mata makoshi, A hanzarce ta raba jikinsu, ido cikon ido suke kallon juna, ta ɗanyi mamakin ganin kayan dake ajikinta masu kyan gaske. Aruɗe ta furta”batul! Dama kece baki da lafiya ba aunty ummi ba? Garin yaya mura tayi maki mugun kamu”? Shiru batul tayi mata batare data furta komai ba, saboda tana jin tsoron ummi taji ta fada ma wani. Da sauri ta canza akalar maganar tasu”Meke damunki? Naga fuskarki ta kumbura idanuwanki sun yi ja, ko kema baki lafiya”? “Ni lafiyata qalou, damuce ta hana ni yin bacci...” bata ƙare maganar ba batul ta kuma cewa “Ina danish dinmu”? “Inaso zanyi maku bayanin komai amma sai mun koma ɗaki, Yanzu ki fada min ya akai mura ta kama ki? Ina kuma aunty ummi”? Murya ƙasa ƙasa Batul tace”nima bansan ya akai ta kamani ba, aunty ummi kuma tana a toilet, itace ma ta kira awaya don akawo min magani, kuma kinga ta bani kaya na sanya” tayi maganar tana nuna mata kayan sanyin jikinta. Ajiyar zuciya Unaisah ta sauke” mun haɗu da boss man shine ya bani maganin mura in kawo, ni nama yi tsammanin aunty ummice ba lafiya kamar yadda ya fadamin ashe kece” Jinjina mata kai batul tayi”Allah ya baki lafiya sisterna, kayan jikinki sunyi maki kyau, a ina aunty ummi ta samu kayan nan dai dai size dinki kamar donke aka dinka su”? “Nima bansani ba, Mu tafi daki” atakure tayi maganar, tare da ruko hannun Angel, tajata suka nufi down stairs. *Daga Alƙalamin Boss Bature💋✊✍️* Adai dai lokacin Su parveen suna a zazzaune tsakiyar gadonsu Batul, sun kewaye juna, sai faman zazzare idanuwansu suke yi don har yanzu basu daina jin fargabar macijin nan ba. Motsin buɗe ƙofa ne Yaja hankalinsu ga kallonta, Atare suka shigo hannun su ruƙe cikin na juna, wani irin farin ciki ne ya lullu6e su, da gudun gaske Jemimah da Azeeza suka diro daga saman gadon suka nufi unaisah, tunkafin su ƙaraso ta ware masu hannayenta fuskarta dauke da yalwataccen murmushi, zubewa tayi saman gwiwowinta yadda tsawonta zaiyi dai dai da nasu, gaba ɗayansu ta haɗasu ta rungume a ƙirjinta, tare da zagaya hannayenta saman bayansu, jemimah tuni ta fashe mata da kuka hada bubbuga bayan Unaisah alamar ranta ya 6aci. Batul dake a tsaye tana kallonsu sam bata ji takun tafiyar Parveen ba, Sai dai taji muryarta”Batul tun ɗazu muna ta jiran ki shiru baki zo ba, Ina fata babu wani abu daya same ki”? Kallonta Batul tayi da ido tayi mata alamar tayi shiru bata son Unaisah taji komai daya faru, jinjina kai parveen tayi don ta fahimci me take nufi. “A ina kika sami kayan jikin ki masu kyau”? Ta fada tana duban Kayan sanyin jikin batul” Murmushi batool tasaki kafin tace”Aunty ummi ce ta Bani su” Parveen tace”ko a ina ta same su, ban ta6a ganin kayan da suka yi maki kyau ba kalar waɗannan” kafin batool tayi magana muryar Jemimah ta katse mata hanzarinta, A lokacin sun ɗago da kansu daga rungumar da Unaisah tayi masu, fuskokinsu sharkaf da hawaye kamar waɗanda suka yi shekara basu ganta ba. “Meyasa jiya kika tafi kika barmu? Inata kiran sunanki baki amsa ba, tsoron wannan abun ya kamamu” Shafa fuskarta Unaisah tayi”Am sorry nasan ban kyauta ba, amma kuyi haƙuri, bawani wuri na tafi ba, Ina atare da ɗan uwanmu Danish bashi da lafiya......” Tunkan ta ƙare maganar, hankalinsu yai mugun tashi jin cewa danish dinsu baida lafiya, damuwace ƙarara akan fuskokinsu “Unaisah meke damun shi? Meyasa jiya ba kizo kin kaimu mun ganshi ba”? Acewar parveen Batul tace”ni da ma saida naji araina ɗan uwanmu baida lafiya, Allah sarki danish din mu, Yanzu yana a ina? Ina son ganin shi” ta fada idonta akan unaisa dake ƙoƙarin miƙewa tsaye tana dubansu. Ruƙo hannunta Azeeza tayi acikin nata”dan Allah ki kaimu wurin shi, muna son ganin shi” idanuwanta sun ciko tab da ƙwalla tayi maganar. Numfasawa Unaisah tayi kafin ta soma yin magana”na yanke shawara ƙwara na faɗa maku halin da danish yake aciki, saboda bana son ku guje shi ko ku dinga jin tsoron zuwa wurinshi.......” shiru ta ɗanyi na wani lokaci duk sun ƙura mata ido cike da zumuɗin son jin ƙarashen zancen. “Amma kafin nan inason ganin sauran ƴan uwanmu, naga babu Hannah! Ina taje ne”? Atare suka hada baki wurin bata amsar cewa suma basu sani ba, tun daren jiya basu ganta ba. Aruɗe Unaisah take dubansu, Kafin ta furta magana, sallamar Big Guy taja hankalinsu ga duban ƙofar, shigowa cikin ɗakin yai hannun shi ruƙe dana Hannah, daga bayansu Ƴan uwansu ne maza tun daga kan Sajeed, Haris, Javed and Naufal, ajiyar zuciya kowan nan su ya sauke, Hannah sai faman zare ido take yi kamar wadda aka faɗa ma saƙon mutuwarta, sakin hannunta big guy yai jiki na rawa ta nufi Unaisah ta rungumeta, sunyi farin cikin ganin ƴan uwansu, Sajeed ya nufi azeeza fuskarshi dauke da murmushi yai hugging dinta, Naufal yajanyo parveen ya rungumeta Yana bubbuga bayanta da hannu ɗaya, Batool da Haris suka rungume junansu, Ran jemimah ya 6aci ganin babu wanda ya rungumeta, harta fara tatta6e la66anta za ta yi masu kuka, javed yai saurin ɗaukarta saman jikin shi, Fashewa tayi da dariya saboda an dauketa. Big guy dake a tsaye yana kallonsu ya goya hannayensa saman broad chest dinsa, Yaran sun yi matuƙar burgeshi. Tsawon mintuna suna a manne da juna, kafin daga bisani kowan nan su ya rabu da jikin ɗan uwanshi, gyaran muryar da Big guy yai masu ne yasa suka mayar da hankalinsu gare shi a tsanake Ya soma yin magana. “Inaso ku natsu ku saurareni, dalilin dayasa na tara ku a ɗakin nan, saboda na fahimci haryanzu baku daina jin fargaban abunda ya faru jiya ba, Ga ƴar uwarku nan Unaisah zatayi maku bayanin komai yadda zaku fahimta, sannan please bama buƙatar ganin gifcin kowan nan ku a falo! Ku tsaya a ɗaki, mai buƙatar shiga toilet ya shiga, wanda zai yi bacci ga gado nan ya kwanta,........” kafin Ya ƙare maganar Parveen tayi ƙasa ƙasa da murya tana fadin”breakfast din mu fa? ni ina jin yunwa, Jiya da dare bamu ƙarasa cinye abincinmu ba” murmushi big guy ya saki ta cikin face mask dinshi Da zolaya yace”ki kwantar da hankalinki foodie, Indai abincine har sai kin gaji da shi, kamar kina a gidan manomi ne, Yanzu zansa a kawo maku lafiyayyan breakfast” ya faɗa tare da nufar kofar fita yana fadin”Unaisah Ki kula da su” amsa mashi tayi da toh, kamar jira su ke yi ya fita, Har suna haɗa baki wurin tambayarta meke faruwa da Danish. “Zanyi maku bayani, amma kafin nan ku jira waɗanda basu yi salla ba su yi tukunna, batool tace min ba ta yi sallah ba” Badan sunso ba suka amince mata “Kunyi sallah”? Ta jefa masu tambayar Sajeed yace”munyi a ɗaki” “Kufa” ta faɗa tana nuna su Azeeza Girgiza mata kai su kayi alamar a’a, Hannah ma tace nima banyi ba, saboda babu hijabi. “Okey, yanzu abun da za’ai ku shiga toilet ku yi alwala, kafin ku fito zan dauko maku hijabin” amsa mata sukayi toh. Ɗaya bayan ɗaya suka shiga toilet, bayan sunyi alwala kowaccensu ta sanya hijabi, asaman carpet din da ta shimfiɗa masu su ka yi sallar, bayan sun kammmala suka cire hijaban suka bata ta ninke ta maida su a wardrobe. Zama sukayi kan carpet din gefen gado, mazan suna fuskantar matan, sun ƙurama Unaisah ido suna jiran jin me zatace masu. “Kin yi shiru ba ki ce komai ba sister, ke muke sauraro meke faruwa da ɗan uwan mu”? Acewar Haris Sajeed yace”tun jiya da abun nan Ya faru mun ganki kina kuka kina fadin danish ya rikiɗa ya koma maciji, abun ya tsaya min araina” da damuwa a fuskarsa yai maganar. “Akwai abun da na 6oye maku tun muna a prison ban samu damar faɗa maku ba.......” a tsanake Unaisah ta labarta masu dukkan abun da ya faru tun daga kan tattaunawarsu da Salsabeel farkon haɗuwarsu a gidan kurkukun ƙaddara da kuma gwagwarmayar da suka yi wajen shawo kan Danish da ruwan zam zam, Har izuwa kan abunda ya faru jiya daya rikiɗa ya zama maciji, tunda tafara basu labari hankalinsu ya tashi matuƙa, sun girgiza da jin cewa Danish dinsu GIANT ne, Kallon kallo suka soma yi a tsakaninsu, idanuwansu a zazzare, Jikin ta ƙaura yai la’asar, wato an gudu ba atsira ba. La66an Sajeed na kerma ya furta”kina nufin Danish Giant ne’? Jinjina mashi kai tayi alamar eh, dafe kai haris yai da hannu ɗaya da wata irin karyayyar murya ya furta”inna lillahi wa’inna ilaihirraji’un! Mun shiga uku! Wai su waɗannan azzulaman mutanan wani zunubi muka aikata masu ne? Da suke azabtar da rayuwarmu? Meyasa suka cutar da rayuwar Danish? Me bawan Allahn nan yayi masu”? Idanuwanshi tuni sun kaɗa sunyi jawur da su “Ni dama nasani bazasu ta6a ƙyale mu ba, zasuyi amfani da danish ne donsu maida mu kurkukun ƙaddara”! Cikin sanyin murya Batool tace”bawan Allah danish, shine abun tausayi, wallahi ina jin baƙin ciki da takaicin azabtar mana da rayuwar ɗan uwanmu da suke Yi, danish tun yana ƙarami suke juya shi, sun hana rayuwarshi sakat, narasa gane dalilin dayasa suke yi mashi haka, Ya Allah ga bawanka nan kai kadai kasan a wani hali yake aciki, Ya Allah Ka fitar dashi, ka kawo mashi ɗauki acikin rayuwarshi’, tuni hawaye sun wanke fuskar Batool. Cikin shesshekar kuka Azeeza tace”Allah ya isa ba zamu ta6a yafe masu ba, Mugaye azzalumai ƴan wuta, In sha Allah tun agidan duniya zasu fara danasanin cin zalunmu da su ka yi da kuma ƙuntata rayuwar ɗan uwanmu da suke Yi” Azeeza na rufe baki, Naufal da takaici ya ishe shi, cikin jin ƙunar rai Ya soma magana”wannan wace irin rayuwace? ya zamuyi da ranmu? Ni yanzu na fahimci KURKUKUN ƘADDARA RAYUWARMU CE!! mune kurkukun ƙaddara saboda duk inda zamu kasance gidan kurkukun ƙaddara yana atare damu, Meyasa!!!”? Ya jefa tambayar idanuwanshi akan fuskar Unaisah, wadda tayi shiru tana sauraronsu, tabbas maganar Naufal abun dubawace, Yanzu ta fara zargin wani abu. “Naufal, kamar yadda ka faɗi nima haka nake tunani, rayuwarmu itace gidan kurkukun ƙaddara, amma meyasa zai kasance haka? Su wanene suka sadaukar da mu?....” ta jefa ma kanta tambayar da bata da amsarta. Sajeed yace”yakamata mu fallasa asirin komai ke faruwa agidan kurkukun ƙaddara ga mutanan da suka taimaki rayuwarmu ina da tabbacin zasu taimaka mana don ganin an gano su wanene munafukan dake sadaukar damu ta hakanne zamu tabbatar da zarginmu” Javed yace’nima ina goyan bayanka Sajeed! Mu tona masu asiri kawai, idan da rabon mu rayu zamu rayune duk runtsi duk wuya, kai koda ace zamu mutu ne bayan mun tona masu asiri wallahi munci galaba akansu, tunda har muka yi nasarar guduwa daga cikin kurkukun ƙaddara, wanda ko a tarihi ba’a ta6a samun prisoners da suka gudu suka tsira ba sai akanmu”! A hankali unaisah take binsu da kallo, ta fahimci ransu yakai maƙura wurin 6aci, Jininsu akan akaifarsu yake, kowannansu atsorace yake da abunda ke faruwa da danish. Fashewa da kuka jemimah tayi haɗi da ɗaura hannayenta biyu saman kanta tana fadin”Wayyo Allahn mu mun shiga uku, Yanzu shikenan danish din mu ya zama dodon kurkuku zai ɗauke mu ya maida mu can mu cigaba da cin ganye” fuskarta sharkaf da hawaye, ruko hannunta Unaisah tayi acikin nata”Ya isa haka, Ki daina kuka, kanki zai Iya yin ciwo,” girgiza kai ta dinga yi tana fadin”genie ba zaki gane ba, wallahi banason komawa kurkukun nan, haushinsu nake ji, Allah zuciyata zata Iya bugawa in mutu kowa ya huta” Gaba ɗaya idanuwansu na akan fuskar jemimah, ta haƙiƙance tana yin magana shatun jijiyoyin wuyanta sun fito ruɗu ruɗu saman fatarta. “Sun kashe mun majnoon dina, sun kashe mana Unaizah, Yanzu kuma mu suke son kashewa fa” ta ƙare maganar tana faman jan majina’ Kwanto da kanta Angel tayi saman cinyoyinta, ta ɗaura hannunta kan sumarta cikin sigar lallashi take yi mata magana”in sha Allah bazamu ta6a komawa gidan kurkukun ƙaddara ba, Har bada, munbarshi kenan bi’iznillahi mune zamu kawo karshen kurkukun da fasiƙan Shuwagabannin su, zamu tarwatsa baƙin tarihin da suka kafa, zamu shafe babinsu a doron duniyar nan, zasu ɗanɗanin kuɗarsu har sai sunji inama ace ba’a halitto su a duniyar nan ba, wannan Alƙawarine!” da ƙwarin gwiwa unaisah ta ƙare maganar. Shiru jemimah tayi tuni ta haɗiye kukanta, Jikin kowannansu yai sanyi, maganganun da suke yi yai silar fama masu tabon dake acikin zuciyoyinsu. Daƙyar Hanna ta Iya buɗe baki tace”ni yanzu damuwata a wani hali danish yake aciki”? Tayi tambayar idanuwanta cike tab da ƙwalla Angel ce ta bata amsa da cewa”har yanzu bai dawo mutun ba, amma ɗazu boss man ya fada min cewa malamin da zai duba jikinshi ya ƙaraso Ina da tabbacin Yana acikin gidan nan, shiyasa Big guy Yace mu zauna a ɗaki bayason ganin gifcinmu, yakamata mu tayashi da addu’a, ita yake buƙata daga gare mu” tunkan ta rufe baki, sukayi saurin daga hannayensu sama, Itama ta ɗaga nata, “Jemimah ki tashi muyi ma ɗan uwanmu addu’a” Unaisa ce tayi mata magana, daƙyar ta ɗago da kanta haɗi da ɗaga hannayenta sama kamar yadda sukayi Addu’o’i unaisah ta soma karantowa suna amsa mata da ameen ameen, bayan ta kammala kowan nan su Ya shafa saman fuskarshi, kafin su zame hannayensu, kunnuwansu suka soma jiyo masu motsin buɗe ƙofar dakinsu, A hanzarce suka ɗago suna kallonsu. Big guy ne ya shigo hannun shi ruƙe da faffaɗan tray Na kayan breakfast dinsu, Daga Bayanshi Ummin america ce, Ta ɗauki wankan turkish gown launin brown anyi mata adon stones launin yellow, mayafin da tayi rolling kala ɗaya ne da stones din rigar, ta sanya high heels a ƙafarta, daga sama rigar ta matseta ta bayyana surar kirjinta, daga bayan rigar tudun mazaunanta ya fito sosai. Tunda batool taji ƙamshin turaren ummin america hankalinta ya tashi, tasan dole ta hukuntata akan fitowar da tayi daga ɗaki batare da saninta ba. A tsakiyarsu big guy ya ɗaura tray din kayan abincin kafin Ya soma yin magana. “Ga auntynku nan Ummi, zata zauna atare daku don ta ɗebe maku kewa, idan kuna buƙatar wani abu, ita zaku faɗa mawa” amsa mashi sukayi da toh. Big guy ya maida dubanshi ga ummi dake atsaye ta ruƙe qugu da hannu ɗaya, Hadaddiyar agogon hannunta sai ƙyalli take yi. “Ummi, ki kula da su, bana so asamu matsala, malamin ne ya buƙaci a tattara sauran yaran wuri ɗaya sannan aja hankalinsu gudun kada suji sautin abunda zai rikitar da su” Lumshe mashi ido tayi, alamar taji mai yace, shi kanshi daurewa yake yi, domin kuwa wankan da ummi ta ɗauka yaja hankalinshi, musamman shu’umin ƙamshin humran dake fita a jikinta. Muryarta da kwarkwasa tace”okey, baka da damuwa” Bayan fitar big guy daga ɗakin. Ummi ta kalli su unaisah, atare suka haɗa baki wurin gaishe da ita. “Ina kwana aunty ummi” yamutsa fuskarta tayi”lafiyalou, Ina batool”? Ta jefa masu tambayar tana kallonsu, kafin su bata amsa idanuwanta suka sauka akan yatsun hannun batul, ta 6oye kanta abayan haris, duk don kada ummi ta ganta. Babu wanda ya fahimci wani abu, sai ita data san meya haɗasu. “Kunyarki take ji Aunty ummi, shiyasa ta la6e” acewar Unaisah. Ta6e baki ummi tayi kafin tace”Ina maganin muran da boss man Ya baki”? Ta fada tana nuna unaisah da hannu. sai lokacin ta tuna da maganin batasan tun yaushe ta jefar dashi ba. “Kin yada kenan”? Girgiza kai tayi a’a, Yana a hannuna tun ɗazu, namantane ban kaiga bata ba” Juyawa baya ummi tayi tana kallon tsakar dakin, Karaf idanuwanta suka sauka akan Blister pack din dake ajiye ƙasa, cikin takun Isa Ta nufi floor din ta zuƙunna ta ɗauki maganin”ajiyar zuciya unaisah ta sauke ganin ta gano shi’ “Ku matsa min anan zan zauna muyi breakfast,” ta faɗa tana nuna tsakankanin Batool da Haris, da sauri Ya matsa mata, taje ta zauna idonta akan batool data ƙanƙame haris, ruƙo hannunta ummi tayi tare da rabata daga jikin haris, duk tabi ta ruɗe, taƙi yadda su haɗa ido. Bottle water Unaisah ta ɗauka ta buɗe murfin, ta tsiyaya ruwa acikin cup, ta miƙa ma ummi, kar6a tayi tare da fadin”thanks” kafin ta curo maganin ƙwaya biyu ta miƙa ma batul, yatsun hannunta na kerma ta kar6a ta sanya abaki, ta kar6i cup din hannun ummi ta kur6i ruwan ta haɗiye maganin, Bayan ta gama ta ajiye cup. “Bata da lafiya ne”? Sajeed ne ya tambaya, parveen tace”Mura take Yi,” “Shiyasa naji muryarta ashaƙe, sis Allah ya baki lafiya” amsa mashi da tayi da ameen, sauran mazan sukayi mata sannu ta amsa masu. Kafin ummi ta fara serving dinsu, A plates ta zuba ma kowannansu abinci banda batool, ɗaya bayan ɗaya ta miƙa masu, suka kar6a suna ci, kallon Batul tayi”atare zamu ci” ta faɗa tana sakar mata shu’umin murmushi afakaice batare da su Unaisah sun gani ba. A plate ɗaya ta zuba masu farfesun naman kaza, Yaji kayan kamshi ga uban romo. Daƙyar batool take iya shan farfesun, saboda Ummi ta hanata sakat, da zarar ta ɗago sai ta haɗa ido da ita, ta rasa gane dalilin dayasa ummi take son takura rayuwarta. Hankalin Unaisah ba akansu yake ba, saboda damuwar data bijiro mata, ta ƙosa taji me ke wakana da Danish, Malamin Ya fara Yi mashi aiki ko kuwa.......? Shin meya faru bayan zuwan Sheikh Imam malik!? Bayan ƙarasowar motarsu akatafaren Gate din shiga gidan Owais Jami’in dake driving dinsu yayi parking a agaban entry hall, Ya fito a hanzarce Ya zagaya ya buɗe masu murfin motar, A hankali Prime minister hateem ya fito daga Ciki, Kafin Sheikh Imam Ya zuro ƙafarshi waje shima Ya fito Yana ƙarema ginin gidan kallo, ya yaba da haɗuwar daular Owais, har saida ya furta masha Allah. Kafin su ƙarasa falon, Glass door dinsa ta buɗe, Chief Owais Ne Ya bayyana gefe da gefenshi, Boss man ne tare da Big guy, da kuma sauran jami’an isod da suka hallara domin tarbarsu. Murmushi prime minister hateem yasakar mashi, tare da nufarshi tunkan ya isa gare shi, Chief owais Ya riga shi zuwa Ya haɗa hannayenshi biyu yai hugging din uncle din nasa” Kafin Ya ɗago Ya nufi Sheikh Imam Ya rungume shi, fuskar kowannansu ɗauke da murmushi. “Owais fatan na sameka lafiya, tsawon lokaci bamu haɗuba, aiki ya 6oye ka,” Sheikh imam ne yai mashi maganar Calmly ya furta”Ina lafiya, nayi missing dinka, amma naji dadin ganin ka yau, Ina fata uncle dina bai takura maka ba? Nasan shine Ya matsa maka akan zuwa Nigeria” da zolaya ya fada, Shekh Imam Yace”kai dai bari, kamar yadda baiyi bacci ba adaren jiya nima haka ya hanani Yin bacci, babu shiri yasa na fara shirye shiryen zuwa Nigeria hada ƙoƙarin turamin jirgin da zai ɗaukoni” Da zolaya yai maganar, Hateem dake sauraronsu, baice komai ba sai dai murmushin dake akan fuskarsa bai washe ba. Dubanshi chief yai”uncle, sannu da zuwa, Mu shiga daga ciki, nabarku atsaye” Atare suka jera zuwa babban falon gidan, saman sofa mai mazaunin mutun uku, prime minister da Sheikh imam suka zauna, Chief Owais Yana daga zaune kan 2 seater, Yayin da Big guy da Boss suke atsaye sun goya hannayensu saman kirjinsu. Kallonsu chief Yai kafin Ya soma magana”Taj wannan uncle dina ne Prime minister Hateem na ƙasar Canada, Kai kaɗaine bakasan shi ba, wannan kuma Sheikh imam kenan, Aminin kakanmu Obie...” Cire face mask din fuskarshi Yai, Cikin girmamawa ya soma gaishe da hateem”ina yi maku barka da zuwa, najima ina jin labarin prime minister awurin Owais sai dai ban ta6a ganinsa ba, ashe da rabon zamu haɗu, kuma tunda naga fuskarshi raina ya bani cewar Uncle dinka ne saboda kamanceceniyar dake a tsakaninku” Ƙayataccen murmushi prime minister yasaki a yayin da yake kallon fuskar taj yace”Nagode da karramawarka agare ni, kuma naji dadin haɗuwa dakai, Ina fata zamu cigaba da yin zumunci a tsakaninmu” Tajo yace”in sha Allah” har cikin ranshi mutumin ya kwanta mashi, kuma Yayi mamakin haɗuwarshi donshi a hoto yasanshi, kuma yayi mamakin sakar mashi fuska da ya yi a matsayinshi na babban mutun mai ruƙe da babban muƙamin shugaban ƙasar Canada, koda yake yasha ji awurin mutane cewa baida girman kai ko kaɗan, mutunne najama’a kowa nashine mai kudi da talaka awurinshi duk ɗayane. Chief Owais Ya ɗaura dacewa”Uncle sunan shi Taj, Mahaifin Yarinyar nan, dana ta6a baka labari, ina fata ka gane shi” Jinjina kai Hateem yai da mamaki akan face dinsa yace”masha Allah, ina ita yarinyar take ne? An gano ta”? Ɗaga mashi kai yai alamar eh. “Na tayaka murna my son, Allah ya tabbatar da alkhairinsa, Ina fata Yaya sharafudden Yasan da maganar mahaifinta da kuma ita kanta yarinyar”!? Chief owais Yace”Ya sani, na faɗa mashi, sai dai basu ta6a haɗuwa da daddynta ba, amma na yanke shawarar zan haɗasu kwanan nan idan muka shawo kan matsalar yaron nan” Ga dukkan alamu Hateem yaji dadin ganin tajuddeen, duba da yadda yake kallon shi. Gyaran murya sheikh Imam yai masu”Idan kun gama magana ina jiranku, Kun ajiyeni kamar buhun masara, Yakamata ku bari in kammala aikina inyaso kunyi firar taku” gaba ɗaya suka sanya dariya banda Chief daya ɗan murmusa. Prime minister yace”ay mana afwa ya sheikh, nayi kewar yarona, Mun jima bamu haɗu ba” Murmushi sheikh imam yasaki, da zolaya yace”wani yaro kake nufi? Wanda yahanaka runtsawa daren jiya? ko kuwa wanda kuke Yin fira da shi a yanzu”? Prime minister yace”dukansu biyun nake kewa” Sheikh imam yace”yanzu naji magana, bismillah owais Muje ka nuna min ɗakin da yaron yake” amsa mashi yai da okey Atare suka miƙe tsaye tare da nufar Up stairs, tunkafin su ƙarasa ɗakin, suka soma jiyo kururuwar macijin Yana gurnani. Sheikh Imam yace”Da alama Yasan da zuwana” murmushi kowannansu ya saki, abakin ƙofar ɗakin suka tsaya kafin su shiga sheikh imam Ya dubi Chief owais”naji kace akwai yarinya agidan nan ɗiyar mutumin da naji ka kira da taj ko”? Kafin owais ya bashi amsa Boss man ya riga shi cewa”ba ita kaɗai bace, akwai sauran ƴan uwanta dake rayuwa agidan” Sheikh imam yace”Toh, ina buƙatar a killace su wuri ɗaya, sannan aja hankalinsu ta yadda baza su iya jin abun da ke faruwa cikin gidan ba, Idan ba haka ba zasu iya firgita arasa gane kansu” boss man ya amsa mashi da toh. Kafin Ya dubi big guy”please kaje wajensu, ka aiwatar da abunda malam yace” da sauri big guy ya nufi hanyar komawa down stairs, Ya rage saura su uku. “Bismillah mu shiga daga ciki” dafe ƙofar boss Yai, ta zuge a hankali kafin suka shiga dakin. Jin motsin shigowarsu dakin Yaja hankalin salsabeel dake atsaye kai idonshi ga dubansu. Hankalinsu na akan narkeken macijin dake zarya tsakiyar gadon wata irin kururuwa yake fitarwa yana huci. Gaisawa sukayi da salsabeel, daga bisani, Chief Yai mashi alama da hannu, salsabeel Ya fahimci ƙarin bayani yake nema game da halin da Giant snake din yake aciki” “Ni kaina bansan meke damun shi ba, Yanzu ya farka daga bacci, Yana huci, zai Iya yiwuwa saboda rashin ganin ƴar uwarshi akusa dashi ne” Hankalin prime minister hateem ba ƙaramin tashi yai ba, sai yanzu yaga girman macijin Ya wuce misali. Sheikh Imam Yace”Saboda ni yake wannan hucin, ku dan bamu wuri zan fara aikina” babu musu suka fito daga dakin, anan second floor suka tsaya suna jiran tsammani Bayan fitarsu ya rage saura sheikh imam da Macijin a ɗakin, Toilet Ya shiga jim kaɗan ya fito da alama alwala ya ɗauro, Bakin gadon Ya tsaya tare dakai hannu Ya damƙi bargon dake a nannaɗe kan mattress, manyan Addu’o’i ya soma karantowa Yana tottofe bargon, kafin ya fara yin karatun alƙur’ani, Yayin da idanuwanshi suke akan macijin dake ta ƙoƙarin saukowa daga saman gadon Hanyar guduwa yake nema sai dai ya kasa yin hakan saboda ɗaurewar da Sheikh imam Yayi mashi da karatun kur’anin da yake yi, Bayan Ya kammala yin ƙira’ar, Ya daddage Ya haye kan gadon, Ya kifa mashi bargon saman jikinshi, Ya daddanne shi da ƙafafuwanshi, da hannayenshi yabi ko’ina ya dafe, wata irin kururuwa macijin yake saki tamkar ana ƙona jikinshi da wuta, hatta waɗanda ke a wajen ɗaki saida suka jiyo sautin, Har saida prime minister ya dafe kunnanshi da tafin hannun shi. Jami’an dake a kewaye da gidan da gudu suka shigo part din hannayensu ruƙe da bindigu, sunyi tunanin wani mugun abunne ke faruwa, daga saman bene Boss Man Yai masu magana akan su koma bakin aikinsu hakan yasa suka juya da sauri suka bar part din. Sheikh Imam Ya hada uban gumi, zufa ta wanke fuskarshi duk da sanyin A.c na ɗakin, Yaƙi Sakin bargon daya daddanne Macijin, sai ƙoƙari yakeyi donya kubcema ɗaurin da yayi mashi. Maƙoshin shekh imam tamkar zai 6allo tsabar yadda yake cigaba da karanta mashi ayoyin ƙur’ani tare da addu’o’in karya sihiri, Yaci gaba da tottofe bargon da yake kudundune. Ba zato ba tsammani, suka soma jiyo wasu irin muryoyi na baƙaƙen shaiɗanun aljanu suna fadin”kashe ka zamuyi sheikh imam! Dole ka mutu tunda ka shiga sabgarmu, zaka mutu” Da karfin hali sheikh imam yace”Idan kunga na mutu lokacin mutuwatane yayi don ubanku, Ni da Allah na dogara bada ku ba, Raina a hannunsa yake, Ku bakusa ku cutar dani ba, face da izninsa, Kunsan bana jin tsoronku tun fil azal......” bai ƙare maganarba, sautin dariyarsu Ya karaɗe ɗakin, tamkar ana buga ganga, Hankalinsu boss man ya tashi matuƙa, damuwarsu kada wani abu ya samu sheikh imam. Cigaba da magana sukayi da kakkausar murya suke fadin”mutuwa zakayi sheikh Imam, ajalinka ne Yazo, kai ka sani ba’a shiga huruminmu a zauna lafiya, mun kashe ire irenka da dama waɗanda suka yi ƙoƙarin yi mana shisshigi, Sheikh Imam kadaina janyo mana ayoyin alkurni bazasu ta6a yin tasiri akanmu ba, Mu ba kalar shaiɗanun da ka saba ƙonawa bane” Runtse ido sheikh imam yayi, jin numfashinshi na ƙoƙarin ɗaukewa tamkar an shaƙe mashi wuyanshi, idanuwanshi suka kaɗa jawur tamkar garwashin wuta, sautin muryarshi daƙyar yake fita ahaka yake kokarin cigaba da yi mashi karatun kur’anin..........” “Hankalina bai kwantaba, Inajin fargabar wani abu ya sami malamin nan, Mutanan nan fa ba ƙananun shaidanu bane” salsabeel ne yai maganar. Boss man yace”ni kaina fargaba nake ji, gaskiya akwai matsala, kada mu jefa rayuwarshi cikin hatsari,” Duk maganganun da sukeyi akan kunnan Chief owais da prime minister Hateem, jikinsu yai sanyi babu mai magana acikin su. Lokaci ɗaya bugun zuciyar Prime minister ya ƙaru, arude ya furta”ku buɗe kofar nan” ya fada yana nuna ƙofar dakin danish” da sauri Bossman Ya nufi ƙofar ya sanya hannu ya dafe glass din wani iko na Allah ƙofar taƙi buɗewa, gashi sunji shiru babu motsin sheikh imam da kuma kururuwar macijin. “Babu lafiya, salsaleel zoka taimaka min mu buɗe ƙofar” matsawa salsabeel yayi gaban kofar, suka haɗa ƙarfi shida boss suka dinga bugun ƙofar taƙi buɗewa. Da ƙarfi suke ambaton sunan sheikh imam shiru bai amsa masu ba, babu alamun motsinshi. Hankali atashe Chief Owais Ya ɗago da ido suka kalli juna shida prime minister. “Bana so wani abu ya sami malamin nan, Ni ne silar kiranshi daga sudan, Idan wani abu ya same shi bazanji dadi ba, zanyi danasani Owais, Yakamata kuyi wani abu akai” damuwace ƙarara akan fuskar Hateem. “In sha Allah Uncle babu abunda zai faru da shi, ka kwantar da hankalin ka” chief na ƙarasa fadar hakan, Ya nufi ƙofar ɗakin, da sauri salsabeel Ya matsa mashi hanya, Boss man Yaja gefe ɗaya, bismilla ya furta da kyakkyawar niya, kafin ya daki ƙofar da kafaɗarshi, nan take ƙofar ta zuge da gudun gaske, ajiyar zuciya kowan nan su ya sauke, salsabeel yayi mamakin ƙarfin owais. An rasa wazai fara shiga dakin, kowa fargaban ganin abunda zai taras yake yi, hatta shi kanshi chief din....... 😳😳😳 *Something Unexpected* *WAIWAYE🌹* *A Obie International Hospital* Emergency room Abun da ya faru daren Jiya da Sir mubarak Ya dauki Dr jazz zuwa asibiti, tunkafin su ƙarasa Ya kira Dr fawan awaya ya sanar dashi game da zuwansu, tuni nurses sun fito da stretcher bed din da zasu dauke shi, motarsu nayin parking a harabar ajiye motocin asibitin, Sir mubarak Ya fito jiki na 6ari ya cuccu6i dr jazz ya daura shi kan gadon, A gaggauce nurses suka gungurashi zuwa Emmergency room. Fitowa Major yai daga front seat na motar, Yabi bayan Sir mubarak dake tafiya yana nufar inda nurses din zasu kai Dr jazz, duk inda ya gifta manyan likitocin dake zarya cikin girmamawa suke gaishe da shi, a bakin ƙofar emmergency room din suka dakata da yin tafiyar, damuwar duniya ta isheshi, ya rasa ina zai tsoma ranshi yaji daɗi, haƙika yaji takaicin bugun da yayi ma jazz bisa rashin sani. “Yalla6ai, ka zauna” Major ne yai mashi maganar yana nuna mashi waiting seat dake jingine da bango Girgiza kai Sir mubarak yai”bazan iya zama ba, Idan har jazz bai farfaɗo ba, Ni kadai nasan halin da nake aciki, Major ka tayani da addu’a Allah yasa yarona ya farka bana so wani abu ya same shi” Cikin kwantar da murya major yace”Sir in sha Allah babu abunda zai same shi, zai ji sauƙi, ubangiji Allah ya bashi lafiya” “Ameen” ya amsa mashi. Tunda aka shiga da jazz cikin emmergency room, likitoci suka taru akanshi, yadda kasan zasu hana shi mutuwa idan tazo daukar shi. After some minutes, Dr fawan Ya fito daga medical room din, sanye cikin shiga ta likitoci, fuskarshi da face mask, tunkan ya ƙaraso wurin su sir mubarak yai hanzarin nufarshi yana fadin”fawan ya farfado? Ko hanyar yanzu”? Calmly dr fawan yace”daddy ka kwantar da hankalinka, har yanzu bamuyi nasarar farfaɗo dashi ba, jazz ya bugu sosai, yanzu dai muna ƙoƙarin ganin munyi mashi treatment din raunukan dake akan goshinsa, In sha Allah nan badajimawa ba zai farfaɗo, ina da tabbacin hakan” ya ƙare maganar yana duban fuskar sir mubarak, babu alamun zai kwantar da hankalinsa, fuskarshi duk ta yamutse. Dr fawan baiyi mamakin ganin hakan ba, yasan da irin shaƙuwar dake atsakaninshi da jazz, dole ya damu. Duk da yana jin shakkar shi saida yai ƙoƙarin jaraba tambayarshi ya akai jazz yaji mummunan rauni saman goshinsa. Kasancewar baya acikin natsuwarshi, da kanshi ya labarta ma dr fawan abunda ya faru. Dafe kai fawan yai da hannu ɗaya tunawa da ranar da sukazo asibitin suka tirkeshi kan ya fada masu abunda jazz yake aikatawa shi kanshi yayi tsammanin wani mugun abun Jazz yake kullawa ashe ba haka bane sun yi mashi mummunan zato. Ruƙo hannun shi sir mubarak Yai”fawan ka taimaka min, bansan ya zanyi ba, ina jin fargabar jazz ya farfado ya juya min baya saboda bugun da nayi mashi nasan daƙyar zai fahimce ni, nayi kuskure fawan na yanke mashi hukuncin cikin fushi batare dana saurare shi ba” cikin rauni na murya ya ƙare maganar, tsananin tausayinshi ne Ya kama dr fawan, hatta major ya tausaya ma shi. “Daddy, har abada bana tunanin jazz zai Iya juya maka baya, Saboda ni shaidane akan ƙaunar da yake yi maka, balle kuma baka da laifi, laifin shine dabai sanar dakai ba a matsayinka na mahaifinsa, sannan duk abun da kayi mashi daddy kayi ne saboda ba ka son ya jefa rayuwarshi cikin hatsari, ni aganina kayi abunda ya dace kowani uba na gari yayi, shine ya tsaya tsayin daka don ganin yaronshi bai 6ace hanya ba.....” tunda dr fawan ya fara magana sir mubarak ya natsu yana sauraronshi, major sai faman jinjina kanshi yake yi alamar gamsuwa da bayanin Dr fawan Sai da ya kai aya a maganarshi kafin major ya daura da cewa”yalla6ai gaskiya ne abun da dr fawan ya ke gaya maka, kuskuren da mukayi bisa rashin sani ne, tun da kake da jazz baka ta6a nuna mashi wariya ko acikin ƴa’ƴanka ba sannan baka ta6a yi mashi koda tsawa bane don yayi maka badai dai ba, don haka bana tunanin jazz zai juya maka baya saboda abunda ya faru, zai fahimce ka kuma zai gane kuskuren shi” Nauyayyar ajiyar zuciya sir mubarak ya sauke, fatanshi Allah yasa maganar su dr fawan ya tabbata, don bayason jazz ya guje shi saboda ƙaunar da yake yi mashi. “Major ka kira layin Zaki ka faɗa mashi muna atare da jazz sai zuwa gobe zamu dawo gida” “Okey Sir” Major ya faɗa tare da zaro wayarshi daga aljihu, Ya danna ma Zaki Kira, Bugu Uku kafin Yai picking, bayan sun gaisa Ya isar mashi da sakon Mahaifinsu kafin daga bisani su ka yi sallama. “Daddy ku zauna mana, ko zamu shiga daga cikine ka kwanta a resting room dinmu” Girgiza kai Sir mubarak Yai alamar a’a, “Bazan Iya runtsawa ba, Nafi buƙatar farfaɗowar Jazz hankalina sai yafi kwanciya” Gyaɗa kai Dr fawan yai”bari na koma ciki daddy” juyawa yai da sauri ya shiga medical room din, Sir mubarak Yana atsaye ya dan jingina bayanshi da bango, major yana daga gefenshi, idanuwansu sunyi masu nauyi, ga gajiyar hidimar shagalin da akayi ga bacci da damuwar halin da jazz yake aciki. A ƙalla sun kwashe awanni a tsaye, dare ya nutsa sosai, a lokacin da basuyi tsammani ba, sautin muryar jazz ya karaɗe kunnuwansu, da ƙarfi yake fadin”daddy zanyi maka bayani ka daina buguna, wayyo Allah kaina zai fashe zafi yake yi min” A gigice Sir mubarak Ya nufi dakin da aka kwantar da shi da sauri major Ya take mashi baya suna shiga suka tarar da Dr Jazz zaune tsakiyar gadon hannayenshi biyu tallabe da kanshi dake a nannaɗe da bandage, gefen gadon dr fawan ne atsaye Yana lallashinshi, gaba ɗaya ya birkice sai sambatu yake yi masu. A hanzarce Sir mubarak Ya zauna gefenshi, Muryarshi a raunace ya ambaci sunanshi”Jazz My son” Har saida ya firgita jin muryar sir mubarak, adabarbarce yake dubanshi da rinannun idanuwanshi waɗanda suka kaɗa jawur, abunka ga farar fata fuskarshi tayi ja la66ansa sunyi suntum bawan Allah Ya bugu ba kaɗan ba. Ido cikin ido suke kallon juna, “Am sorry jazz, na gane kuskurena na bugunka da nayi ba tare da nayi bincike ba, Dan Allah ka yafe min” a hankali ya ruƙo hannun jazz acikin nashi ya ruƙe shi sosai. Babu alamun zai furta mashi kalma, sai faman jan numfashi yake yi haɗi da lumshe idanuwanshi har yanzu allurar da dr fawan yai mashi bata sake shi ba. Daƙyar ya iya buɗe baki ya furta”meyasa ka buge ni daddy? Dama kaine kake bibiyata daddy? Laifin me nayi maka? Kai da kanka ka faɗamin ba zaka iya ta6a lafiyar jikina ba, kuma bazaka bari wani ya cutar dani na, Ko a mafarki ban ta6a tunanin zaka yi min haka ba, sai gashi yau ka nemi ka raba ni da rayuwata.....” a wahalce ya ƙare maganar yana fitar da huci. Girgiza kai sir mubarak yai hawaye tuni sun taru cikin idanuwanshi. Muryarshi asanyaye ya ce”Jazz ba laifina bane abun da ya faru, rashin sani ne, Jazz kaine tun farko baka sanar dani game da aikin sirrin da kake yi ba, a tunanina ka ɗauke ni kamar mahaifinka wanda yai silar zuwanka duniya but why kake 6oye min abunda ya shafe ka? jazz kamanta alƙawarin da muka ɗaukarwa junanmu’? Runtse ido jazz yai hawaye suka soma wanke fuskarshi. Cikin shessheƙar kuka ya furta”ban manta ba daddy, kayi hakuri, yaya Owais ne Yahana in faɗa maka, shiyasa ban gaya maka ba, nayi ƙoƙarin fahimtar dashi kuskuren yin hakan amma sai yace min kaima kasan da case din Yaran.......” jin wannan maganar yasa hankalin sir mubarak ya ƙara tashi aruɗe yake kallon fuskar jazz tamkar yana karanto wani abu, Major da dr fawan suka kalli juna, da alama sunyi mamakin jin abunda jazz ya furta, dafe kai sir mubarak yayi da hannu ɗaya tunawa da zancen case din yaran da sojojin ƙasar ghana suka nemi hukumar sojin nigeria data kar6i case din daga hannun su, a lokacin basu kar6i case dinba sai suka nemi hukumar Isod da su shiga lamarin yaran, bai ta6a ganinsu ba ko a hoto yadaisan da zancen, sannan baida masaniya akan aikin da owais ya ɗauki Jazz Na kula da lafiyar yaran shiyasa aka samu matsala. Jinjina kai sir mubarak yayi, cike da danasanin hukuncin daya yanke mashi, “Jazz ina ƙara baka haƙuri, dan Allah kada ka ruƙeni a zuciyarka, da ace bana sonka wallahi bazan damu da rayuwarka ba, amma saboda ƙaunar da nake yimaka ne yasa harna yi maka shisshigi......” a tsanake sir mubarak ya labarta mashi duk abunda ya faru tundaga rana ta farka daya fara jin shi yana waya a garden kan maganar kaji har zuwa ranar daya yi mashi la6e a toilet yajiyo shi yana fadin akasheta... “Jazz kasan ba mummunan abu kake aikatawa ba, amma meyasa kake amfani da kalamai masu hatsarin gaske kamar kalmar kisa da naji kana faɗi”? Numfashi jazz yaja kafin ya bashi amsa da cewa”saboda yaya Owais ya gargaɗeni akan kada na kuskura wani ya san aikin da nake yi, koda kuwa mommyna ne shiyasa nake yin amfani da waɗannan kalaman, lokacin da kaji nace bayasan hanyar da zai kashe ta ba, Ina nufin yasan hanyar da zai magance matsalarta, a lokacin Salsabeel ne ya kirani a waya, ya fada min haukan khadeeja ya motsa, shine nake fada mashi maganganun da kaji inayi” “Wanene salsabeel”? “Shine babban cikinsu, atare da yaran yake, ba ƙaramin mutun bane ya girmi yaya owais” Shiru Sir mubarak yayi, still bai kawar da idanuwanshi daga kan fuskar jazz ba. “Ya jikin naka? Ina fata babu inda keyi maka ciwo”? Ɗaga mashi kai jazz yai alamar Eh. “Yunwa fa”? “Bana jin yunwa, ina son yin magana da mommyna” “Ba zamu iya kirantaba a yanzu, tayi bacci, sai zuwa gobe zamu tafi gida” Don dole jazz ya haƙura da sonyin magana da mommynsa. A daren ranar major a resting room din dr jazz Ya zauna, shi kuma sir mubarak ya kasa tafiya yabar jazz, kan kafaɗarshi jazz ya ɗaura kanshi, anan bacci yai awon gaba da su manne da juna. Ataƙaice kenan abunda Ya faru daren Jiya dangane da sir mubarak. *Daga Alƙalamin Boss Bature💋✍️* Idan muka koma 6angaren Sheikh Imam tun bayan da Chief Ya buɗe ƙofar dakin Danish, Kowa fargaban Abunda idanuwanshi zasu gane mashi yake yi, ƙarfin hali chief owais yayi wajen zura ƙafarshi cikin ɗakin, rass yaji gabanshi yai mugun faɗuwa ganin hular sheikh imam da arab turban dinsa yashe kan floor kamar an wurgo dasu sun tarwatse, ga takalmansa ware ɗaya bakin gadon ware ɗaya kan carpet, a ruɗe chief Ya wurga eye balls dinsa kan katafaren gadon Danish, lamarin yayi matuƙar ɗaure mashi kai, ganin bargo lullu6e da mutun, ƙafafuwansa sun leƙo waje, farare sol da su, Iya neck dinsa bargon Ya lullu6e hakan ya bayyana lallausar sumar kanshi data tarwatse saman wuyanshi hatta gefen fuskarshi ta lullu6e, Chief Ya fahimci yaron ya dawo suffarshi ta mutane sai dai abunda bai gane ba Ina sheikh imam yake? Saboda kwata kwata babu shi a ɗakin babu alamar shi. “Yalla6ai lafiya”? Salsabeel ne Ya ambaci haka yayin da yake shigowa ɗakin daga bayanshi boss man ne da prime minister hateem suka shigo ɗakin suna ƙarema ko’ina kallo. Idanuwan mai girma prime minister basu sauka akan kowa ba sai akan matashin dake lullu6e da bargo, tun daga kan shantala shantalan ƙafafuwanshi yasoma kallo har izuwa kan brown hair dinsa, aruɗe ya furta”dama yaron macace ba Namiji ba”? ya jefa tambayar yana dubansu. “ba maca bace, Namijine Yana da sumar kai ne” acewar Boss man “Ni abunda bangane ba, Ina sheikh Imam”? Chief ne ya faɗa yana bin ko’ina na room din da kallo. “Allah dai yasa ba wani abunne ya faru da shi ba” acewar Boss man. Sunyi tsaitsaye cirko cirko bakin gadon fuskokinsu da alamun ruɗanin rashin ganin sheikh imam. Prime minister ya kasa kau da idonshi daga kallon sumar kan Danish da yake yi, Ya ƙagara da son ganin fuskarshi. A lokacin da ba su yi tsammani ba, suka soma jiyo motsin buɗe toilet door, kusan atare suka kai idanuwansu ga kallon ƙofar, bakowa bane yake fitowa face sheikh imam malik, hannun shi ruƙe da cazbaharshi, hankalin shi kwance sai dai da alamun damuwa akan fuskarshi. Nauyayyar ajiyar zuciya kowan nan su ya sauke, har suna haɗa baki wurin ambaton sunan shi”Sheikh Imam! Muna fata babu abunda ya same ka”? Jinjina masu kai yayi batare da yace komai ba, har saida ya dawo gefen gadon ya zauna tare da ɗaura idanuwanshi kan bargon dake lullu6e da danish tukunna A hankali Ya furta”Alhamdulillah, cikin Ikon Allah nayi nasara, Yaron ya canza halittarshi........”ya faɗa fuskarshi da matsakaicin annuri. Har cikin ransu sunji daɗin jin hakan, musamman prime minister, atare suka haɗa baki suna ambaton Alhamdulillah sannu da ƙoƙari malam. Girgiza kai sheikh imam yai kafin ya ɗaura da cewa”sai dai ina mai baƙin cikin sanar daku cewa Har yanzu baƙaƙen shaidanun dake atare da shi suna nan daram daƙam, babu alamun zamu yi nasarar raba shi da su..........” Kallon juna su ka yi kafin suka maida dubansu ga sheikh imam Cigaba da yin magana yayi”Ina buƙatar neman ƙarin bayani dangane da abunda ke faruwa da yaron? Shin Menene Yajaza mashi faɗawa tarkon miyagun matsafa? da har suka samu ƙarfin ikon Juya shi son ransu’? Kallon salsabeel Boss man yayi”kai kaɗaine kasan komai Ya kamata ka sanar da Sheikh Imam, kada ka 6oye mashi komai dangane da rayuwar yaran ta hakanne kaɗai zai Iya shawo kan matsalar. Jinjina kai salsabeel yayi alamar ya gamsu da bayaninshi. “Labarine mai tsayi, zai ɗauki tsawon lokaci,” acewar salsabeel. Sheikh Imam Yace”tun da kace labarine mai tsayi, inaga mubarshi zuwa lokacin da yaron zai wartsake, Yanzu Yana buƙatar kulawarmu” Prime minister yace”Ni kaina zanso naji tarihin kyakkyawan matashin saurayin nan, In sha Allah saboda shi zan nemi iznin ƙara kwanakin tafiyata, but abunda nake son sani, Yaron idonshi biyu? Ko bacci yake yi”? ya tambaya yana kallon sheikh imam. “Ba bacci yake yi ba, idonshi biyu, sai dai bazai iya ɗaga ko yatsan hannunsa ba, shaiɗanun sun sakar mashi da kasala Ya jigata sosai, Bayan haka akwai tabonni saman fatar bayanshi” sheikh Ya faɗa tare da miƙa hannu ya ruƙo bargon tare da janshi Ya yaye shi gefe ɗaya, faffaɗan bayan danish ne Ya bayyana, Fari sol sai dai ko’ina da tabon ja. “Wannan tabon na bayanshi, sahun harsashin bindigar da jami’an isod suka harba mashi ne, dama ya faɗa min sunyi mashi illah” acewar salsabeel. Tsananin tausayinshi ne ya kama prime minister, ji yake tamkar ya rungumoshi, baisan ya akai ya tsinci kanshi da son ganin fuskar yaron ba, shi dai ya kwanta mashi arai, “Nayi mamakin ganin suffarshi, naji kace min yarone amma surar jikinshi bata yara bace” prime minister ne yai magnar yana duban owais Chief dake atsaye ya goya hannayensa kan kirjinsa ya furta”wata’kil halittarsace haka, Girman jiki da ƙananun shekaru” Jinjina kai prime minister yayi kafin ya kuma cewa”baba Yanzu me yakamata muyi mashi don mu taimakashi ya dawo normal? Ko dai zamu kira likitane Ya duba shi”? Sheikh Imam Yace”kada ayi haka, saboda bakowa bane zai Iya tunkararshi a wannan yanayin ya zauna lafiya, kawai kubi shi da addu’a in sha Allah zai warware” “Akwai ruwan zam zam na addu’a da na ta6a jaraba bashi, inaga da za’a same shi wata’kil Ya taimaka mashi wajen samun lafiyarshi, Kafin rasuwar mahaifina Yana yin amfani da ruwan zam zam din wurin yin treatment din mutanan dake fama da irin lalurarshi. Salsabeel ne ya kora masu jawabin, sheikh Imam Yace”ƙwarai kuwa zam zam Yana da amfani, idan akwai inda za’a same shi kuyi ƙoƙarin samun shi” Prime minister yace”in sha Allah zamuyi ƙoƙarin samun zam zam din, baba mun gode da ƙoƙarin da kayi mana, Allah ne kaɗai zai Iya biyanka” Boss man yace”ya sheikh ya akai rawaninka da hular suka faɗo ƙasa? Allah yasa dai ba wani abun bane ya faru” Ya furta maganar tare da juyawa ya nufi bakin ƙofar, Ya dauko mashi rawanin da hular. Murmushi sheikh imam yasaki kafin yace”kai dai bari, sha’ani da baƙaƙen shaidanu ba abune mai sauƙi ba, ai dambe muka yi dasu, suna bugu ina bugu na haɗasu da ayar Allah, Ni ban ma lura babu rawanin akaina ba sai da ka yi magana” murmushi kowannansu yakeyi, maganarshi ta basu nishaɗi. “Yaron nan fa sai mun dage da yi masa addu’a, Yana buƙatarta, domin kuwa shaiɗanun dake atare dashi mugayen shu’umaine suna da hatsarin gaske, ba’a ta6a su a zauna lafiya, amma da yake mu da Allah muka dogara kuma munyi imanin cewa shi kadaine gatanmu in sha Allah babu wani mahaluƙi daya isa Ya karya mu sai dai mu muga bayanshi, Na tausaya ma rayuwar yaron kuma ashirye nake da in bada gudummuwata don ganin mun raba shi da su” da kakkausar murya sheikh imam yayi maganar, gaba ɗaya sun natsu suna sauraronshi, har ya kai ƙarshen maganarshi kafin chief owais ya soma yin magana a tsanake”sheikh zamu iya sanin me yaron yake buƙata a yanzu”? Numfasawa sheikh imam yai yayin da yake bin sumar kan danish da kallo ya furta”Idan zaku Iya taimaka mashi yai wanka, tabbas zaiji daɗin jikin shi, sannan ashirya mashi lafiyayyan abincin da zaici inyaso ko abakine sai abashi tunda bai iya ci da kanshi, Bayan haka daga rana irin ta yau duk wani abu da zai yi amfani dashi kada a kuskura abashi batare da an tofe shi da addu’a ba, tun daga kan ruwan da zaisha, shimfidarshi, ruwan wankan shi da suturar sanyawarshi........”kafin malam ya ƙare jawabin, Boss man yai hanzarin tarar numfashinshi da cewa”Allah yaja da ran malam, yaron ba musulmi bane, hakan zai yiwu kuwa? Yar Uwarshi unaisah ta fada min cewa sunyi fama dashi akan ya musulunta amma yaƙiya, ko kalmar bismillah bai ta6a furtawa ba” Har cikin zuciyar prime minister baiji dadin jin cewa Yaron ba musulmi bane, Sheikh Imam yace”in ba wani iko na Allah ba zaiyi wuya ya musulunta idan har shaidanun jikinshi basu rabu da shi ba, sune suke hana shi ambaton sunan Allah saboda lagwon su ne, In sha Allah zamu magance matsalar nan badajimawa ba” Ajiyar zuciya prime minister ya sauke, haɗi da numfasawa yace”Ina son ganin fuskarshi” ya furta hakan Yana duban chief owais, da sauri salsabeel Ya zagaya ta 6angaren daman gadon, Ya haye tare da ruko bargon da hannun shi ya tattare shi gefe ɗaya kan mattress, santala santalan cinyoyinsa farare sol sunyi sambal dasu, sai uban tabonni, kafin komawarshi maciji short ne ajikinshi haka zalika A yanzu haka da yake akwance gajeran wandonne. Sanin nauyin jikin Danish yasa salsabeel nannaɗe hannun jallabiyarsa ya daddage Ya ruƙo kafaɗunsa da hannayensa ya juyar dashi ya fuskanci ceilling, still fuskarshi bata bayyana ba saboda yalwatacciyar sumar kanshi data rufeta. Cike da zumuɗi prime minister yace da salsabeel”please, ka jinginar dashi kan headbored, Ka nannaɗe min sumar kanshi daga kan fuskarshi inason ganinshi da kyau” Cikin girmamawa Salsabeel Ya amsa mashi da toh, Kafin Ya daddage Ya ɗago da Danish Ya jinginar dashi jikin headboard, A hankali Ya soma janye sumar kanshi daga kan fuskarshi, Tunkafin Ya ƙarasa kau da sumar, Hankalin prime minsiter yai matuƙar tashi haiƙam, zuciyarshi ta soma harbawa da matsanancin speed, Yayin da idanuwanshi suka zazzaro waje, tamkar eye balls dinsa zasu fado ƙasa, haƙiƙa yayi matuƙar girgiza da ganin abunda idanuwanshi suke nuna mashi, kowa dake a ɗakin saida ya lura da yanayin da prime minister ya shiga na tsantsar mamaki da Al’ajabi, bashi ba hatta sheikh imam da Chief owais al’ajabine akan fuskokinsu. Muryar prime minister na rawa ya furta”Sheikh...! Owais Kuna ganin abunda nake gani kuwa? a ruɗe ya furta maganar yana ƙarema fuskar Danish kallo. Sheikh Imam da al’ajabi Ya gama kamashi, Baisan sa’dda ya furta”amma dai wannan yaron Jininka ne ko? don wannan yafi ƙarfin ace kamanceceniyace ta halitta sai dai ta jini, saboda kamanninshi sun 6aci dakai da kuma yarinyar wurinka Nazli, Tamkar kayi kakinsa, komai nashi kalar naka ne, tun da Allah Ya halicceni ban ta6a ganin kama irin wannan ba, gaskiya nayi mamaki.....” Boss man yace”ai ba tun yau ba, nasha faɗama chief owais cewa Yaron Yana kama dashi, bani ba hatta abokanan aikin mu sun shaida hakan, sai dai wani abu daya ƙara ɗaure mun kai ayau, Yaron yafi kama da prime minister hateem, bai baro komai nashi ba, tun daga kan shape din bakinsu, dogon hancinsu da idanuwansu, Yalla6ai da zaka ga launin idonshi zaka sha ruwan mamaki, domin kuwa kalar nakune” Dafe kai prime minister yayi da hannun shi ɗaya, Hankalinshi Yaƙi kwanciya da kamanninsu da yaron. Gyaran murya salsabeel Yayi kafin ya soma yin magana yana duban su “Ni kaina na jima ina mamakin kamannin dake a tsakanin Chief owais da Danish, komai nasu kala ɗaya ne banbancinsu launin fata ne da kuma tsayin sumar kai, wani iko na Allah sai gashi Yalla6ai Hateem Yafi kama da Danish” Runtse ido prime minister yayi, baisan ya akai yake jin wani irin yanayin atattare dashi ba. Muryarshi araunace ya furta”ban haɗa komai dashi ba, bani da alaƙa da shi, Yauce rana tafarko dana fara yin tozali da fuskarshi, amma meyasa nake jin wani abu agame dashi? Dan Allah ku fahimtar dani na shiga ruɗani, ya akai komai nashi kalar nawa”? Yana magana la66ansa na kerma. “Owais ka faɗamin wanene Yaron nan? Su wanene Iyayenshi? Meyasa yake kama dani da ƴata Nazli”? Da kakkausar murya ya furta maganar saboda aruɗe yake da lamarin. Shi kanshi chief owais din Ya kasa furta komai, Lamarin Ya ruɗar dashi ya rikirkitar mashi da tunaninshi, bai ta6a tsammanin kamanninshi da yaron sun 6aci har haka ba. A hankali Ya soma yin taku Izuwa gaban Prime minister hateem dake dubanshi fuskarshi a yamutse. Cikin kwantar da murya ya furta”Uncle, bamu da masaniya akan su wanene Iyayen shi, saboda bai dasu a halin Yanzu, da shi da ƴan uwanshi dake ahannunmu bamusan komai nasu ba, tamkar marayu suke a hannunmu, Yarinya ɗayace mukasan Mahaifinta tajuddeen” ya faɗa yana nuna Boss man da hannun shi. Girgiza kai yaɗanyi numfashinshi na fita da huci yace”Owais kada ku maidani mahaukaci, nafasan me nake yi, taya za’ace babu danginshi? Kyakkyawan yaro kamar wannan?ni kawai so nake ku faɗamin meyasa muke Kama”!!! Ga dukkan alamu prime minister ya fara zaucewa, wata irin zuface take tsastsafo mashi saman goshin shi. Hankalin kowan nan su Yana akanshi, owais baisan taya zai fahimtar da uncle din nashi ba, Miƙewa Sheikh Imam yai tare da nufar prime minister Ya tsaya agabanshi, tare da kai hannu ɗaya ya dafa kafaɗarshi, a tsanake Ya soma yi mashi magana “Ka kwantar da hankalinka, yakamata ka fahimci abun da Awaisu Yake ƙoƙarin faɗa maka, su kansu basu da masaniya akan yaron, kaɗan daga cikin ikon Allah kenan, kowani ɗan adam yana da masu kama da shi A duniya.....” tunkan sheikh Imam Ya ƙare maganar, prime minister yace”baba, wannan yafi ƙarfin ace kamace kawai, ka dubi fuskarshi dakyau, tamkar anyi photocopy dina, kamar dai nina haife shi, Ina jinshi tamkar jini na, ƙaunar da nake yi mashi kaɗai abun dubawace, ta zarce misali, saboda shifa na kasa runtsawa adaren Jiya, na damu da shi fiye da tunaninku.........” gaba ɗaya sun rasa taya zasu shawo kan prime minister, a iya sanin su da shi bai ta6a haihuwar ɗa Namiji ba, balle ace yarom shine daya 6ata. “Yanzu abun da za’ai, tun da kana ƙaunarsa kuma yaron baida iyaye, mai zai hana ka ɗauki ragamar kula dashi kafin komawarka canada? Wata’ƙil hankalinka zaifi kwanciya” acewar sheikh Imam, ya fadi hakanne donya kwantar masa da hankalinsa ganin irin ruɗun daya shiga. “hakan yayi shiekh, Uncle ka ƙaddara cewa jininka ne shi, kana da damar da zaka Iya bashi kyakkyawar kulawa” Chief owais na ya furta hakan. Kalamansu sun tausasa mashi zuciyarshi, har cikin ranshi Yaji dadin jin hakan. “Inaso na taimaka mashi yayi wankan ya sanya sutura a jikinshi, zan kira ɗan uwana awaya don yazo ya ganshi, nasan shi kadaine zai ƙara tabbatar min da abunda nake gani a idona, sannan Idan yaron yaji sauƙi kafin in koma canada, zan je dashi gidana don in nuna ma gimbiyata shi da ƴa’ƴana nasan zasuyi mamakin kamanninsa dani musamman Nazli, hatta hasken fatarshi kalar nata ne” murmushi ne akan fuskokinsu, sunji daɗin sakewar da prime minister yayi, hankalinsu ba ƙaramin kwanciya yayi ba. Naɗe hannun rigarshi yayi, tare da cire agogon azurfarshi, da zoben hannun shi, Ya miƙa ma owais su, da sauri owais ya sanya hannu ya kar6a, gaba ɗaya kallon shi suke da mamaki akan fuskokinsu. Murmushin gefen fuska yasaki har dimple dinsa ya lotsa”kada kuga ina zumuɗi akanshi ƙaunarsa nake Yi” da zolaya ya furta maganar kafin yace” wazai taimaka min mu shiga da shi bathroom room”? da sauri Salsabeel Yace”ni Yalla6ai” “Yawwa, ruƙo min shi mu shiga ciki, ko da ya ke naga yana da girman jiki zaiyi nauyi, bari na kama maka” a hanzarce Ya zagaya ta 6angaren da salsabeel Yake, a lokacin sabeel Yayi koƙarin janyo danish da ƙyar ya kawo shi bakin gadon. Kafaɗunshi suka rurruƙe shi da prime minsiter suka miƙar dashi tsaye, wanda badan ƙarfin giant da sabeel yake dashi ba da kuwa babu mai iya ɗaga shi, jikin shi ya saki tamkar wanda baida ƙashi, kanshi ya kalli kasa sumar kanshi ta lullu6e fuskarshi, idanuwanshi suna arufe gam, zufa ta ko’ina take tsasstsafo mashi, a hankali suke tafiya dashi suna nufar toilet, har suka yi nasarar shigar da shi ciki’ Bayan shigarsu, sheikh imam ya dubi boss man da owais “Inason ganin sauran Yaran da kuke ruko a hannunku” Da sauri Boss Man Ya amsa mashi da toh, Ya miƙa ma sheikh imam rawanin shi daya ruƙe a hannunshi tare da hularshi, godiya yayi mashi, har ya juya zai fuce muryar chief owais ta dakatar dashi “Boss, Ka tara yaran a main falo, Yanzu zamu sauko down” Amsa mashi yai da toh, kafin yasa kai ya fuce daga dakin Ya sauka down. A hanzarce yake tattaka staircases din benan, har ya kusa saukowa down yai tozali da big guy dake tafiya cikin takun sauri, ganin boss yasa shi fadin”Ya ake ciki mutumina? Boss yace”Alhamdulillah Danish ya dawo ainihin suffarshi, Sai dai babu kuzari ajikinshi, Ko yatsanshi bai iya ɗagawa, ga tabonnin harbin bindigar da akayi mashi ta ko’ina saman fatar shi” Cike da jin alhini Big guy yace”bawan Allah, banji dadin jin hakan ba, wallahi yaron tausayi yake bani, ashe munyi mashi illa da harbin bindigar amma ina fata baiji mugun rauni ba ko”? Ɗaga mashi kai boss yayi alamar eh, fuskarshi da damuwa yace”ubangiji Allah yaba shi lafiya, Allah kuma ya kawo mashi ƙarshen wahalar shi”Boss ya amsa mashi da ameen kafin yace”yanzu haka Prime minister da ɗan uwanshi, sun shiga dashi bathroom zasuyi mashi wanka, sheikh imam ne ya bada shawarar yin hakan” Zaro ido big guy yai da zolaya yace”Yanzu wannan ƙaton balagaggen zasuyi ma wanka? Yaron fa yakai chief dinmu girman jiki,” Harara Boss man ya jefa mashi”laifina ne dana tsaya yin magana da ɗan ƙwaya, sai kace ba ka ji nace maka bai iya ɗaga koda yatsansa ba, lalura ce ko kai kanka akwai ciwon da sai dai adinga yi maka wanka, ba fata nake yi maka ba, ina dai kwatanta maka ne babu wanda yafi ƙarfin ƙaddara” Dariya big guy yasaki”Haba mutumina, nima fa wasa nake yi, nadai jinjina lamarin ne, amma baka fadamin ba prime minister baiyi mamakin ganin fuskar yaron ba”? Dariya boss yayi kafin yace”daɗina da kai shegen son gulma uwa mace” Cike da zumuɗi big guy yace”ni dai ka amsa min tambayata na ƙosa naji” Boss man yace”kallo yabarka, hankalin prime minister ba ƙaramin tashi yayi ba, kusan fa hauka yayi mana gaba ɗaya ya rikice tunda yayi tozali da fuskar yaron, daƙyar fa muka shawo kanshi, duk yabi ya ruɗe......” a tsanake Man ya labarta mashi komai. Dariyar shaƙiyanci Big guy yasaki hada tafa hannayensa yana fadin”ni dama nasan za’a rina wallahi, nifa tuntuni nake mamakin kamanninsu da yaron, koda ake maganar yana kama da chief namu saida na raya arainacewa duk ranar da hateem yayi arba da yaron sai ya sha mamaki, donni nafi ganin kamanninshi da nashi, sai gashi maganata ta tabbata” da ƙwarin gwiwa ya ƙare maganar, boss da zolaya yace”sannu malamin duba, aikinka na kyau, ka tsareni da surutu kamar kanyar da bata da daɗi, ka hanani ƙarasawa inda zanje” “Ina zakaje ne”? Big guy ya jefa mashi tambayar. “Sheikh imam ne Ya buƙaci atara mashi sauran yaran yana son ganinsu” Big guy yace”ai ƙwara yagansu domin kuwa suna buƙatarshi kodan saboda wannan jarin taka, ni ina da tabbacin ba’a rasa almatsutsai akanta.....”dariyace ta kubce mashi daƙyar ya ƙare maganar, ganin yadda boss man ya haɗe fuskarshi. Harara ya jefa mashi”Idan ka isa ka maimaita maganarnan agaban chief” Big guy yace”ai ko giyar wake nasha bazanyi wannan gangancin ba,” Fuskar boss ɗauke da fara’a Yabi ta gefen big guy Ya yi gaba abunshi Ɗaga murya big guy yai tare da cewa”Yaran suna a ɗakin Jarinka gaba ɗayansu na tarasu anan” Murmushi taj yasaki, haɗi da girgiza kanshi, bakomai yasa shi yin hakan ba face sunan da big guy yake kiran Babynsa angel, wato JARI, saboda yace mashi chief zaiba auranta yafi son inda zata huta shine fa ya ruƙe abun azuciyarshi har yake tsokanarshi da sunanta. Idan muka koma 6angaren su unaisah, tuni sun kammala yin breakfast dinsu, kowa yaci ya ƙoshi yayi hani’an, sai dai damuwa ta hanasu sakat, Hankalinsu ba akwance Yake ba, sunyi zugudum saman carpet, kowa ya zabga uban tagumi kamar masu zaman makoki, jefi jefi sukan buɗe baki suce Allah sarki danish dinmu, ko awani hali yake a yanzu, a lokacin ummin america ta shiga toilet din dakin nasu. Batool ta kwantar da kanta kan kafaɗar unaisah, Azeeza ta ɗaura nata kan a shoulder din Sajeed, hannayensu ruƙe cikin na juna, Jemimah ta haye bisa laps din haris idanuwanta alumshe sai faman firgita take Yi tana jan numfashi kamar baccine ke ƙoƙarin yin awon gaba da ita, parveen da naufal sun jingina bayansu jikin gado fuskokinsu babu walwala, hannah kuwa ta ɗaura kanta saman laps din javed, sunyi shiru babu mai magana, daga tsakiyar carpet din tray din kayan abincin da suka kammala ci ne ba akaiga kawar da su ba, wasu daga cikinsu sai faman lumshe idanuwansu sukeyi alamun bacci suke ji. Jin motsin buɗe ƙofar toilet yasa Batool yin saurin runtse idanuwanta ta ƙanƙame unaisah, gudun kada ta haɗa ido da aunty ummi, fitowa tayi daga cikin toilet din, sautin takalman ƙafartane ya fargar da masu gyangyadin cikinsu, gaba daya suka ware idanuwansu akan ummi dake tunkarosu. Ta fahimci tsantsar damuwace atattare dasu, tun ɗazu da suna cin abinci ta lura da kyar suke cusa abinci abakunansu, tasan bai wuci damuwar halin da ɗan uwansu yake aciki bane” “Aunty ummi, Inaso zanje dakin danish in duba jikinshi” unaisah ce tayi maganar Ummi tace”a’a, ba’a bada iznin wani daga cikin ku Ya fita ba” Ya mutsa fuska unaisah tayi tamkar zata fashe da kuka ta kuma cewa”aunty ummi batool ta manta doguwar rigarta a ɗakinki jiya da su ka je kwana, zanje na ɗauko mata” Girgiza kai ummi tayi”basai kinje ba, zuwa anjima da kaina zan dauko mata rigarta” zumbura mata baki Unaisah tayi duk yadda taso tayi ma ummi wayau taƙi barinta ta fita. A ƙule unaisah tace “To waimu haka zamuyi ta zama a ɗaki kamar an kulle kaji a keji” Dariya ummi tasaki har fararen haƙoranta suka bayyana tar dasu kamar gonar auduga “Kin gaji ne”? Ɗaga mata gira unaisah tayi alamar eh. Gyaɗa kai ummi tayi”okey, bari na taimaka maku ku girgije jikinku,” basu fahimci me take nufi ba. Zura hannu tayi cikin aljihun doguwar rigar jikinta ta zaro iphone dinta, duk sun ƙura mata ido suna jiran ganin me zatayi da wayar. Zira ziran yatsun hannunta ta ɗaura kan screen din wayar ta soma yin pressing dinta, jim kaɗan daddaɗan sautin kiɗa ya soma karaɗe bedroom din nasu, taken waƙar ed shareen mai suna Shape of you. Fuskarta ɗauke da shu’umin murmushi take kallonsu, sun ƙura mata ido suna kallonta, ganin ta fara jujjuya qugunta tana taka rawa. “Idan kuna ra’ayi ku taso muyi rawa” ɗaure fuska Unaisah tayi ranta a6ace take dubanta har ta buɗe baki zatace mata bazasuyi rawarba, Sajeed Ya miƙe Yana taka rawa ya nufi tsakiyar ɗakin, miƙewa Azeeza tayi da sauri tabi shi Ya ruƙo hannunta Yana jujjuyata, tuntsirewa Ummi tayi da dariya tana kallon su, abu kamar wasa sautin kiɗan yafara kai masu karo, Naufal ya miƙe ya ruƙo hannun Parveen suka nufi tsakiyar ɗakin suma suka fara yin rawa, Aruɗe unaisah take kallonsu kamar waɗanda akayima asiri, lallai ummi ba ƙaramar shaidaniya bace hakanan taja hankalinsu da sautin kiɗa, ruƙo hannun Hanna javed yai suka miƙa suma suka nufi tsakiyar dakin, Haris Ya miƙe Jemimah ta like mashi tana fadin itama zatayi rawar, ya ruko hannunta suka bi sahu, Ya rage saura Unaisah da Batool su kadai ne suka ki tashi. “Sanya damuwa aranku bazai ta6a yi maku maganin matsalarku ba, Ni taimakon ku nake sonyi don na fahimci baku san me ake nufi dajin dadin rayuwa ba, kunfi so kuyita ƙuntata kanku bayan kowani ɗan adam yana da damar da zai sanya kanshi farin ciki, If you let me do my job, you’ll see the positive results soon.”......” muryarta da kwarkwasa take yin magana tana kallon Batool da Unaisah. “Idan kunaso mu zauna lafiya daku, to ku bani haɗin kai, Ni kuma zan wayar maku da kanku, zan sanyaku farin cikin da zai kawar maku da damuwarku” da shaƙiyanci take yi masu magana tana ɗage girarta. Sunyi shiru babu alamun zasu tanka mata, shu’umar dariya tasaki tare da cewa”Na fahimci unaisah kece mai taurin kai, Saboda ke Batool taƙi tashi ta taka rawa ko”? Murguɗa mata baki unaisah tayi. “Idan kika bani hadin kai mukayi rawa zan barki ki fita daga ɗakin nan kije wurin ɗan uwanki danish....”tunkan ummi ta rufe baki unaisah tayi saurin furta”a’a sai dai ki bari in fara zuwa dakin shi, Idan na dawo sai muyi rawar” “Zaki rasa damar da kike da ita” acewar ummi, Ta furta maganar tare da miƙa ma batool hannunta alamar ta taso suyi yawa, cike da jin shakkarta Batool take kallonta, fuskar ummi a ɗaure tace da ita”Come to me” sai da batool tafara kallon unaisah jikinta sukuku kafin ta yunƙura ta miƙe tare da ɗaura hannunta na dama saman hannun ummin america, gam ta ruƙe hannun tajata zuwa tsakiyar ɗakin rawa suka soma takawa kamar mace da namiji haka take juya batool tana rungumeta idonta akan unaisah data haɗe fuska tana satar kallonsu. Canza masu waƙa tayi ta sanya masu waƙar rema mai taken baby come down, tunda sautin kiɗan Ya fara ratsa mata zuciya takasa jurewa ji tayi kamar ana janta a hankali ta miƙe tsaye tana kallon ƴan uwanta dake ta tiƙar rawa suna dariya, itama sai taji tana buƙatar yin nishaɗin kota ɗebe kewar danish dake damunta. Ganin ta miƙe tsaye sototo tana kallonsu yasa ummi miƙa mata hannu ɗaya alamar tazo gareta. Maƙe mata kafaɗa tayi alamar bazata zo ba, batool tace”please sister kizo muyi yawa atare dan Allah” harara ta watsa ma batool, muryar sajeed ce ta janyo hankalinta ga dubanshi. “Sister zo mu taka mana, muna buƙatarki afilin nan” murguɗa mashi baki tayi. “Genie dan Allah kizo muyi rawa, kinga ni banda abokin yi haris baiyi dani” da shagwa6a jemimah tayi mata maganar, hada marairaice mata fuska. Magiya suka dinga mata akan tashigo suyi rawar, tun tana maƙe masu kafaɗa, har dai jemimah tazo taja hannunta suka shiga filin, ai tunda tafara taka rawa kamar ɗiyar roba, daɗi ya kamasu ganin unaisah ta saki jiki tana tiƙar rawa, nan fa kowa ya bada himmah, sosai suke jijjiga qugunansu, wani abun ƙayatarwarma sai sun yarfar da sumar kansu kamar indiyawa, sautin kiɗan ba ƙaramin ƙara masu ƙaimi yake yi ba, ummi ce kaɗai take bin waƙar suma tun basu iyaba har suka fara bi saboda harshen turancine tamkar yarensu ne........: Dawo da waƙar farko tayi jin sun fara dauka suna bi, aikuwa gaba daya suka kware murya suna bin waƙar Baby, calm down, calm down Girl, this your body e put my heart for lockdown For lockdown, oh, lockdown Girl, you sweet like Fanta, Fanta If I tell you say I love you no dey form yanga, oh, yanga No tell me no, no, no, no, whoa-whoa-whoa-whoa Oh-oh-oh-oh-oh-oh-oh-oh-oh-oh-oh Baby, come gimme your lo-lo-lo-lo-lo-lo-lo-lo-lo-lo-lo-lo-love You got me like, “Whoa-whoa-whoa-whoa-whoa-whoa-whoa-whoa-whoa” Shawty come gimme your lo-lo-lo-lo-lo-lo-lo-lo-lo-lo-lo-lo-love, mm-mm Cike da nishaɗi suke bin waƙar suna dariya fararen hakoransu kamar gonar auduga, ita kanta ummin america ba ƙaramin burgeta sukayi ba, Kamar sakarya haka tasaki baki tana kallonsu, a ƙarshe saita bar masu filin rawar ta koma gefe ɗaya tamkar dj ta goya hannayenta saman kirjinta tana kallonsu ɗaya bayan ɗaya fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi, sun bata mamaki, daga kunna masu waƙa har sun haddace ta, aranta ta ayyana lallai yaran suna da kaifin basira, yanayin yadda sukeyin rawar suna jujjuya qugunansu yafi komai tafiya da hankalinta, musamman unaisah da parveen sunfi zaƙewa sai kuma uban gayya Sajeed dama shine yafara koya masu rawa tun agidan kurkukun ƙaddara, salon rawarshi kalar ta ƴan club ce, da aji yake yinta hannun shi ruƙe dana Azeezarshi Sun tsunduma suna tiƙar rawa ko gajiya basayi. Da ƙarfi Sajeed Yace Aunty Ummi ki canza mana wata waƙar mai daɗi” Da sauri ta ɗauki wayar ta kunna masu waƙar alen walker. Unaisah na soma jin taken waƙar tayi saurin kamawa tafara bi saboda tasanta tun da jimawa, sajeed ma ya iya waƙar, atare suka haɗa baki suna bin waƙar Lost in your mind, I wanna know Am I losin’ my mind? Never let me go If this night is not forever, at least we are together I know I’m not alone I know I’m not alone Anywhere, whenever Apart but still together I know I’m not alone I know I’m not alone I know I’m not alone I know I’m not alone Unconscious mind, l’m wide awake Wanna feel one last time Take my pain away.......” Abun da basu sani ba, tun ɗazu boss man Ya shigo ɗakin, yana daga tsaye bakin kofar Ya goya hannayenshi saman kirjinshi, ɗaya bayan ɗaya yake binsu da kallo kafin ya tsayar da idanuwanshi akan Unaisah da ta zaƙe tanata jujjuya qugu tana bin waƙar, tsabar mamakine Ya hanashi yi masu sallama, bai ta6a tsammanin zata Iya yin rawa har haka ba,Yarinyar da kullum take acikin damuwa. Ummin america tana faman wurwurga eye balls dinta akansu karaf idanuwanta suka hango mata boss man dake atsaye yana kalonsu, da sauri ta kashe sautin, ta kama yin ƴan kame kame, su kuwa prisoners koda ta kashe sautin basu lura da shi ba, a shagwa6e Jemimah ta bubbuga ƙafa tana fadin”wayyo Allah aunty ummi, meyasa kika kashe mana abun, ni wallahi bangaji ba, dan Allah ki sake kunna mana muyi rawa mu girgije” ta faɗa tana karkaɗa ƙaramin qugunta, gaba ɗaya suka tuntsire da dariya. Banda ummi data kame kanta “Please aunty ummi ki kunna mana mu ƙarasa yin rawar” acewar parveen idanuwanta akan fuskar boss dake tsaye yana kallonsu, Sun juya mashi baya shiyasa basusan da zaman shi ba, ita kadaice take Iya ganin shi. A wayance tace”nifa ba don wani abu na kunna maku sauti ba, kawai na fahimci kuna acikin yanayi na damuwa shiyasa nayi ƙoƙarin don in sanyaku nishaɗi, kuma Alhamdulillah naga canji atare daku....” tunkan ta ƙare maganar, Boss man ya ɗaga hannayenshi yai clapping da ƙarfi haɗi da furta”Sannunku da ƙoƙari” a firgice suka waiwayo baya suna dubanshi kamar wadanda suka ga dodo. Unaisah hada dafe ƙirji tana fadin”Boss tun yaushe ka shigo dakin nan”? “Tun time da kika fara rawa ina atsaye ina kallonki” wata irin kunyace ta kamata da sauri ta juya ta nufi saman gado ta haye ta kifa kanta jikin pillow tana dariya. Hakan da tayi yayi matuƙar bashi dariya. ɗaura idanuwanshi yayi akan fuskar ummin america sai faman ƙyafƙyafta idanuwanta take yi. “Ummi Amanar da muka baki kenan? A matsayinki na mamansu kin tarasu akan idonki suke tiƙar ruwa, ke da kanki kika kunna masu sauti, ƙiri ƙiri so kike ki maida mana ƴa’ƴa ƴan rawa ko”? A ruɗe ta furta”I’m sorry Sir if I offended you, but I didn’t have any bad intentions. I was just trying to make them happy because I noticed they were worried about their brother’s illness. That’s why I tried to cheer them up......” aladabce tayi maganar, tana matuƙar girmama boss man saboda karamcin da yake yi mata, yafi sakar mata fuska akan sauran jami’an isod. “Kada ki damu babu komai nima nayi maganarne kawai bawai ina nufin hakan ba, ai nasan ba zaki ta6a yin abunda zai 6ata masu tarbiyaba ba, yau dinma kinyine donki ɗebe masu kewa kuma naji dadin hakan Na yaba da tunaninki, tunda gashi nagani da idona kin taimaka masu da kika sanya su nishaɗi, Na jinjina maki” ya faɗa hadi da yi mata alamar jinjina da yatsanshi. Ƙayataccen murmushi tasakar mashi”nagode da ka fahimce ni” Mayar da dubanshi yayi akan su sajeed dake tsaye suna kallonsu “Ay min afwa na katse maku jin daɗin ku, nima ba laifina bane laifin sheikh imam ne daya buƙaci son ganinku don haka in akwai mai ƙorafi ya tanadi abunsa idan munje gabanshi sai ku faɗa mashi” da zolaya yayi masu maganar, murmushi kowan nan su yasaki. Unaisah jin an ambaci sunan sheikh Imam da kuma maganar yana son ganinsu yasa tayi sauri saukowa daga saman gadon, A kunyace ta kalli boss man tana faman noƙe kai tace”mu tafi boss” Ruƙo hannunta yai acikin nashi, da sauri Batool ta ruƙe ɗayan hannun nashi sukayi gaba su naufal suna abiye da bayansu, gaba ɗayansu suka nufi falon hada Ummin America. A tsakiyar falon su ka dakata da yin tafiyar Boss Man yace”Ku jira anan bari naje na sanar dashi” harya kama hanya zai tafi Unaisah ta kwala mashi kira, a hanzarce ya juya yana kallonta. Sosa kai ta ɗanyi da hannunta kafin tace”am..dama inaso ne na tambayeka awani hali danish dinmu Yake aciki ne”? “Ya dawo mutun” wani irin farin cikine Ya lullu6esu, musamman unaisah bakinta yaƙi rufuwa “sai dai babu ƙarfi a jikin shi, bai iya yin komai ko yatsan hannun shi bai iya ɗagawa” lokaci ɗaya murna ta koma ciki jin abun da Boss man Yace. jikinsu duk yai sanyi, Unaisah tace”baida lafiyane”? Ɗaga mata kai yai alamar eh, ya ƙara da cewa”kada ki sanya damuwa aranku, zaiji sauƙi in sha Allah, addu’arku yake buƙata” Cike da zumuɗi tace”zan Iya binka zuwa ɗakin nashi” Jim ya danyi kafin yace”No, ki tsaya tare da ƴan uwanki, zuwa anjima za’a baku damar ku ganshi” jiki asanyaye ta amsa mashi da toh. juyawa boss man yayi da sauri Ya haye upstairs. Ajiyar zuciya kowannansu ya sauke, ummi dake atsaye harta fara gajiya, wuri ta samu saman sofa ta zauna tare da ɗaura ƙafarta ɗaya bisa ɗaya, taci gaba da danna wayar hannunta. “Mu zauna kafin malamin Ya ƙaraso acewar Unaisah” Amsa mata su ka yi da toh, kowa ya samu wuri Ya zauna, sanyin A.c sai ratsa fatar jikinsu Yake Yi, sunyi shiru babu mai yin magana acikin su, sai faman ƙyafƙyafta idanuwansu suke Yi, duk sun ƙagara da son ganin malamin Tsawon mintuna ƙalilan, suka soma jiyo takun takalmansu, a hanzarce su unaisah suka kai dubansu gare su. Sheikh imam ne agaba, daga bayanshi boss man ne tare da Big Guy. Tunkafin Ya ƙaraso cikin falon Yake binsu da kallo, hannunshi ruƙe da cazbaharshi, a tsakiyar sofa set din suka dakata da yin tafiyar, ummi sam bata lura da su ba, hankalinta na akan wayarta da take dannawa. Cikin girmama su unaisah suka sauko daga saman sofa, suka dawo kan carpet, atare suka haɗa baki wurin gaishe da shi, hakan ba ƙaramin burge shi yayi ba, sai faman sakin murmushi yake, “Masha Allah, kyawawan ƴan mata da samari, fatan na sameku lafiya” amsa mashi sukayi da lafiyalou. “Alhamdulillah, ubangiji Allah ya Albarkaci rayuwarku...” kafin Sheikh Ya ƙare maganar, Boss man Ya kira sunan ummi, a hankali ta ɗago tana kallon shi”bakiga sheikh imam bane”? Adabarbarce ta mamaita sunan malamin da boss Ya kira mata, kasancewar Ya juya mata baya bata samu damar ganin fuskarshi ba, Jin muyarta yasa sheikh imam yin saurin juyowa baya don ganin wacece..........” Wani irin mugun bugu zuciyar ummi tayi lokacin da idanuwanta su ka yi tozali da fuskar sheikh imam, tsabar firgita har wayar hannunta sai da ta kubce mata, sheikh imam kuwa tunda ya tsayar da kwayar idanuwansa akan fuskarta bai ko ƙyafta ba, wani irin kallo yake binta dashi mai wuyar fassaruwa, lamarin ya ɗaurewa boss man kai, shi da big guy tare da Unaisah gaba ɗaya Hankalinsu na akansu babu wanda yayi yunƙurin dakatar dasu daga kallon da suke jefawa junansu tsawon mintuna ganin abun nasu ba mai ƙarewa bane yasa Boss man yin gyaran murya, adabarbarce ummi ta soma ƙoƙarin tattara natsuwarta duk tabi ta ruɗe kamar wadda taga wani mugun abu. Da sauri ta zuƙunna tare dakai yatsun hannunta dake kerma da niyar ta ɗauki wayarta data faɗi kan floor, sai dai kafin ta kai ga yin hakan sheikh imam ya rigata ɗaukar wayartata, lokaci ɗaya ta miƙe ta juya da gudu ta nufi cikin falon sai da tafara taka stairs sautin shessheƙar kukanta ya karaɗe falon..... Hankalinsu Batool ba ƙaramin tashi yayi ba, Jin sautin kukan aunty umminsu ya jefa su cikin yanayi na damuwa. da mamaki akan fuskar Boss man Ya furta”Sheikh meke faruwa? Ko kasan ta ne”? Shiru ya ɗanyi jim yana jujjuya wayar ummi dake a hannunshi na tsawon sakanni, kafin ya soma magana da karyayyar murya”bansanta ba, Yau na fara ganinta” ya faɗa tare da juyowa yana fuskantarsu Da alamun ruɗu akan fuskar big guy yace”amma meyasa kuka dauki lokaci kuna kallon juna kai da ita? Sannan meyasa ta watsa da gudu tana kuka”? Fuskar sheikh imam babu walwala Yace”dan Allah kubar maganar nan, kasan dai bazanyi maka ƙarya ba geme geme dani, nima abun da yasa nake kallonta saboda kallon da take yi min, kuka kuma da take yi wata’ƙil nayi mata kama da wani ne da ta rasa a rayuwarta” Jinjina kai big guy yayi badan Ya gamsu da bayanin shi ba. “Ga wayarta ku ruƙe mata” ya faɗa yana miƙa ma Boss man, wanda yayi zugudum yana kallon yadda jikin sheikh imam ke tsuma sun fahimci da akwai wani abu da ya 6oye masu wanda baison su sani dangane da ganin ummin america da yayi. Cikin sanyin murya Unaisah tace”Ni zan kai mata wayar,” ta fada tare dakai hannu ta kar6e phone din daga hannun sheikh imam, ta nufi cikin falon da sauri. Bayan tafiyarta, sheikh imam Ya mayar da dubanshi kansu Sajeed da suke a tsaye cirko cirko suna kallon shi. “Allah ya yi maku albarka, ubangiji Allah ya kareku daga sharrin duk wani abun cutarwa, Allah ya daukaka rayuwarku......” addu’o’i ya dinga karanto masu suna amsa mashi da ameen ameen Bayan ya kammala yi masu addu’o’i, yace dasu”Ku faɗamin sunayenku ina son ji” hatta maganarshi da ƙarfin hali yake yinta duk ya rasa kuzarinsa. Sajeed ne ya fara cewa”Ni sunana sajeed, wannan kuma Azeeza’ ya faɗa yana nuna Azeeza, kafin Ya ɗaura yatsan shi kan Naufal”Sunanshi naufal ta gefenshi Parvin, ga kuma Jemimah da Hanna, sai Javid and Haris, da Batool, ƴar uwarmu data tafi kaima aunty ummi waya sunanta Unaisah” duk wanda ya nuna sai ya fadi sunanshi bayan ya kammala sheikh imam yace”sannu da ƙoƙari Sajeed, nagode daka faɗamin sunayen ku” murmushi Sajeed yayi ba tare da ya ce komai ba. A hankali Sheikh Imam Ya dubi boss man da big guy, bai yi mamakin ganin kallon da su ke yi mashi ba, yasan dole suyi tunanin wani abun daban, launin idanuwanshi har sun canza zuwa ja, kau da idonshi yayi daga kansu ya kalli su Haris muryarshi asanyaye yace”ku zauna muyi fira ƴan jikokina” zazzaunawa su ka yi kan carpet shi kuma ya zauna kan sofa, su boss ma suka zauna suna fuskantar shi. *UNAISAH❤* Koda Unaisah ta ƙarasa ƙofar ɗakin ummi dafe glass door din ƙofar tayi a hankali ta zugeta, bata sameta a adakin ba, sai dai ta jiyo shessheƙar kukanta acikin toilet. Ɗaga murya tayi tare da cewa”Aunty Ummi, ga wayarki na kawo maki” shiru ummi bata tanka mata ba, kusan sau biyar tana maimaita maganar babu alamun za’a amsa mata. Saman gado ta ajiye mata wayar, kafin ta nufi ƙofar toilet din ta sanya hannu tayi mata knocking, “Aunty Ummi dan Allah ki daina yin kuka, bamu jin daɗi, idan wani ne ya 6ata maki rai, ki yi haƙuri” lallashinta Unaisah taci gaba da yi tun tana jin shessheƙar kukan ummi, har tadaina jiyo sautin kukanta, hankalinta ya ɗan kwanta juyawa tayi da sauri ta fuce daga ɗakin, maimakon ta sauka down ta koma falo sai ta kalla6a ta nufi ɗakin Danish, dama abun take yima zumuɗi kenan shiyasa ta kar6i wayar ummi da sunan zata kai mata. Idan muka koma 6angaren Danish tsawon mintuna da suka shiga da shi bathroom, kafin su fara yi mashi wankan saida prime minister ya tofe ruwan da addu’o’i kamar yadda sheikh imam yace adinga yi mashi, batare daya cire mashi short din jikinshi ba yayi mashi wanka da ruwa mai ɗumi, tamkar ya samu jinjirin yaro, saƙo da lungu na jikinshi sai da prime minister ya cuccuɗa shi, bayan ya kammala ya ɗauko farin towel cikin jerin waɗanda ke sagale jikin hanger, ya ɗaure mashi a waist dinshi da dabara ya zame short din daya jiƙe duk don kada yaga tsiraicin shi, shanya short din yayi kafin salsabeel Ya taimaka mashi suka fiddo da shi daga cikin kwamin wankan. Kafin fitowarsu Chief Owais kadai ya rage a ɗakin, Cikin takun sauri ya nufi faskekiyar closet din Danish ya buɗe yana bin jerin tsadaddun suturunsa da kallo A hankali ya tsayar da idanuwanshi wurin jerin jallabiyoyi yana da tabbacin zaifi samun walwala acikin jallabiya, launin fara ya ɗauko mashi, ya dawo ya ɗaura kan gado. Jin motsin buɗe toilet door ne yaja hankalinshi ga kallon su A daddafe suka fito da danish hannayensu tallabe da shi, da sauri chief Ya ƙarasa gabansu Ya tallabo masu shi a saman shimfiɗeɗan gadonshi suka kwantar da shi. “Sannu da ƙoƙari Uncle,” acewar chief Prime minister yace”yawwa my son, kaima sannunka da ƙoƙari, tun jiya mun hana ka runtsa” “Bakomai uncle kada hakan ya dame ka aikina ne” Murmushi prime minister yasaki haɗi da bubbuga kafaɗar chief owais alamar jinjina. “Uncle yakamata ka koma gida, za’a iya nemanka, ni zan cigaba da kula maka shi” Girgiza kai Prime minister yayi”No, ba yanzu zan koma gida ba, sai zuwa anjima” Chief bai musa mashi ba don ya fahimci baison tafiya yabar Danish. “Sabeel, bring me some body lotion and perfume” cikin girmamawa salsabeel ya amsa mashi da toh sir. Ya juya da sauri ya nufi dressing mirror ya ɗauko body lotion tare da turare yazo ya ajiye su kan gadon. prime minster ne ya soma bin ko’ina na jikin danish yana shafe shi da mai haɗi da yi mashi tausa don yaji dadin jikin shi, chief ne ya taimaka mashi wurin burkito mashi da danish Ya juya mashi bayanshi, Ya shafa mashi man kafin yabi da turare ya feshe shi. da taimakon chief suka sanya mashi jallabiyar, masha Allah, tayi bala’en yi mashi kyau, a karo na farko kenan don bai ta6a sanya jallabiyaba, tabi shape jikinshi ta bayyana kyakkyawar surar jikin shi, musamman broad chest dinsa da strong arms nasa sun fito ruɗu ruɗu ta jikin jallabiyar. Ajiyar zuciya kowan nan su ya sauke, ganin sunci nasarar gyara mashi jikin shi, hatta sumar kanshi saida prime minister ya sharceta ya shafe mashi ita da mayukan gyaran gashi, ƙamshin turaren danish ya cika ɗakin kamar wanda akayi ma wanka da ruwan turare. “Yanzu me ya rage mana”? Acewar chief, prime minister yace”nasan yana jin yunwa, Yana buƙatar abincin da zai ci” Salsabeel yace “Yayi bacci yanzu, naga lokacin sallah yakusa cika, may be kafin mu kammala yin sallah ya farka sai mu bashi abincin” “Kana nufin har muka yi mashi wanka bacci yake yi”? Prime minister ne ya faɗa yana duban salsabeel. “A’a yalla6ai, idonshi biyu, tun lokacin da muka shiga dashi bathroom, Yanzu nan yayi bacci” “Taya akai ka gane yayi bacci” da mamaki yayi mashi tambayar, chief dai yana atsaye yana sauraronsu. “Yatsun hannun shi dana ƙafarshi, suna kerma yanzu kuma sun daina gaba ɗaya sun tsaya yadda su ke” Fuskar prime minister dauke da murmushi yace”ka karanci ɗan uwan nan naka sosai, naji dadin jin hakan, may be wankan da mu ka yi mashi ne yasa shi jin daɗi har yayi bacci” Saldabeel yace”ƙwarai kuwa yalla6ai, ay kayi ƙoƙari, Allah yasaka maka da mafificin alkhairinsa kamar yadda ka faranta mashi rai ka gatanta shi kaima inayi maka fatan Allah ya faranta maka ya ƙara ɗaukaka ka” Har cikin ranshi yaji daɗin kalaman salsabeel, “Yalla6ai kaima ban barka abayaba, domin kuwa kayi namijin ƙoƙari wurin ganin ɗan uwana ya samu lafiya, Allah ne kaɗai zai Iya biyanka” ya faɗa yana duban chief owais. Jinjina mashi kai yayi batare daya furta komai ba. Kiraye kirayen sallar Azhar da aka farayi ne Yaja hankalinsu da sauri chief ya zaro agogon azurfar hateem tare da Zobensa daga aljihu Ya miƙa mashi. Bayan ya saka a hannun shi, ɗaya bayan ɗaya su kayo alwala, kafin fitarsu daga dakin saida prime minister yaje har gaban gadon danish ya ɗan duka tare da kai small lips dinsa saman forehead din danish Ya manna mashi peck, ji yake kamar karya tafi yabar shi, ganin abun nashi bamai ƙarewa bane ga time ɗin salla na tafiya ya kafe danish da ido babu ƙyaftawa da sauri chief yaje ya ruƙo hannun shi ya janyo shi a hankali suka nufi ƙofar fita ɗakin. Adai dai lokacin Unaisah dake la6e bakin ƙofar ɗakin tana sauraron su, jin motsin tafiyarsune yasa tayi saurin watsawa da gudu ta la6e a wata ƴar corner. Akan Idonta, Chief Owais Ya fito hannun shi ruƙe dana prime minister, still bata samu damar ganin fuskokinsu ba, sai dai salsabeel daya biyo bayansu shi tagani da kyau, tunani ta somayi aranta ko wanene wannan babban mutumin, taso ace taga fuskarshi shida chief, Allah bai bata sa’a ba, Har saida suka 6ace ma ganinta tukunna cikin sanɗa take bin bango tana nifar ɗakin danish cikin sa’a ta buɗe ƙofar ta shige, daddaɗan ƙamshin turarenshi ne ya daki hancinta har saida ta lumshe idanuwanta tana shaƙar shi ...... Cikin takun sanɗa ta nufi gadon, yayin da idanuwanta suke hango mata Man dinta, hayewa saman gadon tayi daga gefenshi ta dakata tana bin body dinsa da kallo, from head to toe, wani irin farin cikine ya lullu6eta ganin shi cikin shiga ta farar jallabiya yayi mata kyau, aranta ta ayyana nasan waɗannan mutanan ne suka taimaka mashi wurin gyara jikinshi saboda boss ya faɗamin cewa ko yatsanshi bai iya ɗagawa, idan kuwa hasashena gaskiya ne naji daɗi ubangiji Allah ya saka masu da gidan Aljanna, ta ƙare zancen zucin fuskarta ɗauke da murmushin farin ciki. Ta rasa gane bacci yake yi ko idonshi biyu, amma dai tayi missing dinshi na tsawon awannin daya ɗauka tun jiya a halittar maciji, ashe dai da rabon zata sake ganinshi da ainihin suffarshi, yayin da take kallonshi karaf idanuwanta suka sauka akan jan tabonnin dake akan farar fatar dogon wuyansa, harzuwa saman fatar hannunsa. Ras taji gabanta ya faɗi, ta zazzaro idanuwanta waje tana fadin”My man meke damunka? Jan tabon menene nake gani a jikinka”? Ta ƙare maganar fuskarta ɗauke da matsananciyar damuwa, hawaye tuni sun jiƙe gashin idonta. Ziraran yatsun hannunta ta ɗaura saman wuyanshi ta soma shafa tabonnin slowly ta zame fingers din daga neck dinsa zuwa kan broad chest dinsa, a hankali take 6alle links din gaban jallabiyar don ta samu damar ganin sauran tabonnin da ke akan fatarshi, da ta buɗe faffadan kirjin nashi, hankalinta yayi matuƙar tashi da ganin tabonnin ta ko’ina, ji tayi tamkar zuciyarshi bata bugawa da sauri ta kanga Kunnanta na dama saitin zuciyarshi, natsuwa tayi tana sauraran yadda take harbawa cikin kwanciyar hankali, tsawon mintuna bata ɗago da kanta ba saboda dadin sauraran heart beat dinsa da take ji, A hankali ta ɗago da kanta karaf idanuwanta suka sauka akan soft lips dinsa batasan ya akai ta tsinci kanta dayi masu kallon ƙurulla ba sun ɗan kumbura, zuciya ce ta soma tunzurata akansu, unaisah da kasada ta ɗaura yatsun hannunta na dama kan la66ansa tayi squeezing ɗin su, ba zato ba tsammani taji yaja dogon numfashi da ƙarfin gaske, tsabar kiɗima jiki na rawa ta rarrafa ta ta wulkita can ƙasan gadon ta faɗo ta labe zuciyarta na harbawa da ƙarfi da ƙarfi jikinta ya hauyin kerma duk tabi ta ruɗe gani take yi kamar ta fama mashi ciwon shi... Runtse idanuwanta tayi hadi da matse pink lips dinta wani irin yanayi take ji mara misaltuwa atattare da ita, Jin shiru ya daina jan numfashin ne yasa ta lalla6a ta ɗago da kanta tana leƙenshi, babu abun da ya canza yaci gaba da yin baccin nashi. Ƙasa ƙasa da murya ta furta”I’m sorry to disturb you, I’ve missed you so much. I can’t take my eyes off you.” Lalla6awa tayi a hankali ta haura saman gadon da rarrafe ta nufe shi, rumfa tayi mashi da sumar kanta ta natsu tana shaƙar ƙamshin turaren jikinsa, tabi ta addabi rayuwarshi da sunan tayi kewarshi tahana mashi sukuni abaccinsa, don taga babu kowa aɗakin shiyasa take yi mashi iya shege.... Lokacin da Chief da prime minister tare da salsabeel suka sauko down, kaitsaye suka nufi babban falon, tunkafin su ƙaraso takun takalmansu Ya isar da saƙon zuwansu, A hanzarce Sheikh imam da su Boss man suka mimmiƙe tsaye suna jiran ƙarasowar su, su sajeed dake zazzaune kan carpet suna kallonsu, lokaci ɗaya suka shiga ruɗanin ganin fuskar prime minister Hateem data chief Owais, duk da shi chief ya sanya face mask a fuskarshi, a matuƙar ruɗe suke kallonshi bakunansu asake babu alamun zasu motsa. “Sannu da fitowa Yalla6ai” Boss man ne yayi maganar, Big guy yace”barka da fitowa” amsa masu yayi fuskarshi asake, Sheikh Imam yace”ya jikin yaron? Prime minister yace”Yayi bacci shiyasa muka ƙyale shi zuwa time da zai farka” “Alhamdulillah, naji dadin jin hakan, baccin nan da yayi hutu ne agare shi” “Babana, muna ƙara yi maka godiya bisa ƙoƙarin da kayi mana, mun hana ka sakat mun kuma hana ka huta, Allah ne kadai zai iya biyanka.....” fuskar sheikh imam dauke da murmushi ya furta”bakomai Hateem, kada kaji komai, ai indai akan aikin lada ne bazani ta6a gajiyawaba, koda zan shekara inayi ne, ni dai fata na shine Allah ya dubi kyakkyawar niyarmu akan yaron nan ya bamu nasara akan ƙudirin da muke dashi na ganin mun raba shi da miyagun dake bibiyar rayuwarshi” jinjina kai kowan nan su yayi, shiekh imam ya daura da cewa”idan na samu natsuwa kafin zuwa dare, Zan turama shi Awaisun addu’o’in daya kamata arunƙa mashi akan komai da zaiyi amfani dashi, kada a kuskura abarshi ya yi gamon kan shi, tun da shi ba musulmi bane bai yi imani da Allah ba, shaidanun dake ajikinsa bazasu ta6a bari ya ambaci sunan Allah, ko ruwan addu’a zaku bashi ku tabbatar yasha akan idonku idan bahaka ba shaidanun zasu iya zubar dashi ko su canza mashi ruwan batare da kun ankareba, tun da su ba ganinsu akeyi” “Insha Allah malam zamuyi ƙokarin yin hakan” acewar Boss man. Ga dukkan alamu Prime minister Hateem bai lura dasu Batool ba, hatta shi kanshi chief owais din, wani iko na Allah salsabeel dake kallonsu har kallonshi sukayi babu alamun sun gane shi, nan take ya fahimci basu ruƙe kamanninshi ba, saboda sau ɗaya suka ta6a ganinshi kuma a lokacin basu acikin hayyacinsu, jamimah da Azeeza da parveen su dama basu ta6a ganinshi ba, asume aka fitar dasu daga kurkukun. “Lahh! Ji wani mai kama da Danish dinmu” muryar Jemimah ce ta fargar dasu, kusan atare suka daura idanuwansu akan yaran Zumbur jemimah ta miƙe taje gaban prime minister ta tsaya hada ruƙe qugu tana ƙare mashi kallon mamaki da al’ajabi Ɗaya bayan ɗaya yake bin yaran da kallon, Ya fahimci kallon mamaki suke yi mashi, Boss man ne yai masu gyaran murya tare da cewa”Sajeed, kuzo ku gaishe da Kawun Chief dinmu Owais sunanshi prime minister Hateem, wannan kuma shine chief dinmu Owais” ya faɗa yana nuna masu chief da hannun shi. Atare suka miƙe tsaye suka nufi prime minister cikin girmamawa suka gaishe da shi, kafin suka gaishe da Chief Owais. Murmushi prime minister yasakar masu har dimple dinshi ya lotsa, da mamaki suka kalli juna ganin yadda kamanninsa da danish suke ƙara bayyana. “Masha Allah, Naji dadin haduwa daku, My Son ina kuka samu kyawawan ƴan mata da samari masu kama da jinin family dinmu? Ai ni nayi tsammanin Danish ne kadai yake kama damu amma sai nake ganin fuskokin ƴan uwana akan faces dinsu kodai idanuwana ne suke nuna min badai ba”? Sheikh imam na murmushi yace”ba kai kadai ba Hateem, ni kaina tun da nayi tozali da yaran nan nake ta mamakin kamannin ku dasu” “Uncle, waɗannan sune sauran yaran da muke kula dasu, Ƴan uwan danish ne” chief owais Ne ya faɗa yana nuna su da hannun shi. “My son Allah Ya tayaku ruƙo, Ina ƙara yaba maka da jinjina maka akan ƙoƙarinka” calmly chief ya furta mashi thanks” “Sajeed, mu tafi masallaci, Batool kija sauran ƴan uwan naki ku tafi ɗaki ku yi sallah, Boss man ne yayi masu maganar, Cikin sanyin murya batool tace”Idan muka kammala yin sallah zamu Iya zuwa ɗakin ɗan uwanmu Danish mu duba shi” da ta furta maganar har chief owais saida ya kalleta kafin ya kau da idon shi. Salsabeel ne yace”ku ƙara hakuri yanzu bacci yake yi, sai dai zuwa anjima idan sun farka” amsa mashi tayi da toh, tayi mamakin ganin yana sakar mata murmushi, yayi tsammanin idan sukaji muryarshi zasu gane shi amma still babu alamun zasu gane ɗin. “Ina ƴar uwarku Unaisah”? Ya jefa mata tambaya, kafin ta bashi amsa boss man ya rigata cewa”taje ɗakin ummi ne” Prime minister yace”In sha Allah zuwa anjima idan na dawo gidan zanyi magana daku” ya faɗa yana nuna su batool,’ amsa mashi sukayi da toh, hadi da yi masu godiya. Bayan tafiyarsu Batool taja sauran ƴan uwanta mata suka nufi ɗakin su. *SIR MUBARAK✊* Tun wuraren ƙarfe takwas na safe suka baro asibitin kafin tafiyarsu saida Sir mubarak yayima Dr fawan Alheri saboda yaji daɗin Yadda ya taimaka mashi wurin ganin Jazz Ya samu lafiya, da matsakaicin gudu motarsu ta haura saman titi, Major ne yake yin driving dinsu, yayin da sir mubarak da jazz suke zaune a back seat na motar. Ya ruƙe hannun jazz acikin nashi, kamar ance za’a ƙwace mashi shi, Jazz sai faman lumshe idanuwanshi yake yi kamar mai jin bacci, “Jazz me kake tunani naji kayi shiru tun da muka fito daga asibitin baka ce komai ba,” cikin kulawa Sir mubarak yayi mashi magana yana dubanshi In a cool voice ya furta”Ina tunanin khadija, bata sha maganinta na safe ba bansani ba ko salsabeel Ya bata” Murmushin gefen fuska Sir mubarak yayi”idan na fahimceka kana magana ne akan Yarinyar nan mai ta6in hankali ta gidan kajin da kuke kiwo ko ba haka ba” ya fada da zolaya yana ɗaga mashi gira, tuntsirewa sukayi da dariya gaba ɗayansu hatta major dake driving dariyar yake yi. “Daddy dan Allah mu daina tuna abun da ya wuce” sir mubarak ya ce”okey na daina my son, tun da baka so” Gyaran murya Major yayi sir mubarak ya dago yana kallon fuskarshi ta cikin mirror. “Sir, ina zamu nufa? gidanka ko can gidan da Yaran suke?” Shiru sir mubarak ya danyi kafin yace”mu wuce gida, jazz yana son ganin mommynsa, nasan tayi kewarshi, in yaso daga baya sai muje can gidan” Amsa mashi yayi da toh. “Idan mun isa gida please ka kira tiger A waya ka tambaye shi awani hali yaran suke aciki, inason sani” Cikin girmamawa Major Ya ce”in sha Allah Yalla6ai zan tuntu6e shi’ Ajiyar zuciya sir mubarak Ya sauke tare dakai dubanshi ga Dr jazz, “My son, ya zamuyi? Bansan ta yadda zanyima mommynka bayani ba, gashi ni ban iya ƙaryaba, nasan dole ta shiga damuwa idan ta kalli fuskarka,” fuskarshi a yamutse yayi maganar, har cikin ranshi baison 6acin ran turai duk da yasan zata fahimce shi amma dole taji ba daɗi. “Daddy kada ka damu, idan mukayi mata bayani zata fahimce mu in sha Allah” “Allah yasa my son” daga haka babu wanda ya ƙara yin magana acikinsu, har suka shigo estate, Motarsu bata nufi ko’ina ba sai katafaren gate din Gidansa A harabar ajiye motocinsa sukayi parking, babu wanda yasan da zuwansu, da sauri Major ya fito ya zagaya ta baya ya buɗe masu mota, sir mubarak ne ya fara fitowa kafin Ya taimaka ma Dr jazz shima Ya fito, hannunshi ɗaya dafe da waist din shi. saboda baya iya tafiya dai dai, tun lokacin da sir mubarak ya cakumi rigarshi ya buga shi da ƙasa ƙafarshi ɗaya ta lanƙwashe daƙyar yake iya takata a yanzu. A haka suka nufi cikin gidan, banda Major wanda tuni Ya nufi sauran ƴan uwanshi sojoji dake kai komo a cikin gidan. A zaune yake saman Sofa, ya ɗauki wankan dark jeans and white V-neck shirt kayan sun bi shape din jikinsa, hankalinshi a kwance yake operating laptop din gabansa dake ajiye kan table, Fitowa mom turai tayi daga cikin kitchen hannunta ruƙe da mugs guda biyu na coffee, ta nufi cikin falon fuskarta asake taje gaban table din Zaki ta ɗaura cup ɗaya “Ga wannan My son, Nasan zaka buƙace shi” ɗagowa yayi fuskarshi ɗauke da murmushi ya furta”mom nagode da kulawarki agareni, kina ji da ɗan nan naki” Kafin ta kuma cewa wani abu muryar ibad ta janyo hankulansu ga dubanshi, fitowarshi kenan daga cikin ɗaki Sai faman yin miƙa yake yi haɗi da yin hamma, daga shi sai short a jikin shi Muryarshi da shagwa6a ya furta”mommy nifa”? Zaki ne ya bashi amsa da cewa”Na ƙarfi ne zoka ƙwata, ɗan rainin wayau sai yanzu ka ga damar tashi daga baccin” Tur6une fuska yayi”babban yaya jiya fa bamuyi wani isasshen bacci ba, shine nake yin ramuwar na jiyan” Dariya mom turai tayi shagwa6ar ibad har mamaki take bata, duk da shima jazz idan abun ya motsa yana yi mata shagwa6a “Ranka zai 6aci ne idan ka ci gaba dayi min shagwa6a kamar wani ƙaramin yaro,” Bubbuga ƙafafuwanshi yayi hada ruƙe qugunsa wato yayi sai dai ayanka shi Mom turai tace”sai fa kana haƙuri da shi, kasan autane kuma kai ka rainesa duk abun da yayi kai ne ka sangartar da shi” Ta6e baki Zaki yayi tare da kau da idonshi daga kan fuskar Ibad Ya miƙa hannu ya ɗauki mug Ya soma kur6ar coffee.. “last born zoka kar6i wannan” girgiza mata kai yayi”no mommy, na hannun shi nakeso yasha ya rage min, wannan nakine ki sha” a sukwane Zaki ya dakata da shan coffeen Ya waiwayo yana dubanshi, Ya rasa gane dalilin dayasa Ibad yake yi mashi haka, aduk lokacin da zai ci abu saiya sa rigima akan yaci ya rage mashi kamar wani tsaran wasan shi “Kada ka damu zan shiga kitchen in haɗa nawa, kai dai kar6i kasha” mom turai ce tayi maganar Ibad ya maƙe mata kafaɗa”mom ni ai nafison yasha ya rage min” Girgiza kai Zaki yayi tare da kallon mom turai yace”zan rage mashi” “Amma ai baida yawa taya zai isheku ku biyu abunda baifi rabin cup ba” “Idan bai ishe mu ba, zan turo shi ya ƙaro mana wani a kitchen” Gyaɗa kai tayi okey, Har ta nufi sofa zata zauna, sallamar sir mubarak ta katse mata hanzarinta, Kusan atare suka kai idanuwansu ga duban ƙofar falon Shigowa Sir mubarak yayi hannunshi dafe da dr jazz, tsabar firgice Yasa mom turai ta saki mug din hannunta gaba ɗaya ruwan coffeen Ya zube kan floor, Jikinta na 6ari ta nufe su, Hankalin kowan nan su ya tashi, zaki tuni ya dakata da shan coffeen a hanzarce ya miƙe ya nufi sir mubarak, Ibad kuwa hannayenshi biyu ya ɗaura saman kanshi yana ambaton”mun shiga uku, ɗan uwa Jazz meya same ka? Kayi hatsarin mota ne? Muryar turai na rawa take fadin”innalillahi wa’inna ilaihirraji’un, babe meya faru da jazz ɗina? idanuwanta har sun fara fitar da ƙwalla, Sir mubarak bai sauraresu ba, Ya nufi sofa da sauri zaki Ya taimaka mashi suka zaunar da jazz. A Hankali Ya ɗago Yana dubansu ɗaya bayan ɗaya kafin ya tsayar da idanuwanshi kan mom turai da tafara sharar ƙwalla, Jikinta asanyaye ta nufo su ta zauna gefen jazz ta ruƙo hannun shi acikin nata, “Kayi shiru bakace komai ba? Meya faru da jazz”? “Daddy kai muke sauraro,” acewar Ibad wanda tuni ya dawo gefen ɗan uwanshi zaki ya tsaya hadi da ruƙe qugunshi A tsanake ya soma yi masu magana”ku kwantar da hankalinku.....” tunkafin ya ƙarasa maganar, mom turai ta katse shi ta hanyar yi mashi tsawa tana fadin”taya zakace mu kwantar da hankalin mu? Yaro ya fita gida lafiyarshi qalau yanzu kuma ka dawo dashi goshi ɗaure da bandage ga tabonni akan fuskarshi, sannan babu kayan da ya fita da su a jikin shi, ni dama tun jiya hankalina bai kwanta da fitar jazz ba, babe ka faɗamin meya faru da yarona”!! idanuwanta azazzare tayi mashi maganar. Tun da yake da turai bata ta6a gigin katse shi yana cikin yin magana ba sai yau, hakan ya ƙara tabbatar mashi da cewa ranta yakai maƙura a wurin 6aci, “Mommy, yaya zaki, Ibad” dr jazz ne ya ambaci sunayensu, a hanzarce suka kai dubansu gare shi. “Zanyi maku bayanin komai” “A’a jazz shi nake so yayi min bayani, gaba daya a raunace kake, ka daina yin magana zaka fama ciwonka” ta faɗa tare da kallon sir mubarak wanda yayi shiru yana kallon fuskarta... “Meyasa ka tsareni da ido? Ba zaka yi min bayani ba”? Bai tanka mata ba har saida ya samu wuri saman sofa dake fuskantar su, Ya zauna, tukunna ya samu natsuwar yin masu bayanin komai daya faru....... A ƙarshe yace”bana buƙatar wani yaji abun nan saboda aikin sirri ne sukeyi, basu buƙatar kowa ya sani, Na faɗa maku ne don na wanke kaina daga zargin da zakuyi min na halin da na jefa jazz” Cikin sanyin murya turai tace”am sorry dear, nayi maka tsawa bisa rashin sani, kayi hakuri dan Allah, hankalina ne ba akwance ba” “Na fahimce ki,” atakaice ya furta hakan Mayar da duban ta tayi akan jazz”dan Allah nan gaba kada ka ƙarayin wannan gangancin, duk wani abu da zakayi ka sanar da mahaifinka koda ace ni bazaka sanar min ba,” amsa mata yayi da toh, Kafin ta juyo da dubanta kan sir mubarak”Babe, babu wasu kalmomi da zan iya yin amfani dasu wurin yi maka godiya saboda irin kulawar da kake ba jazz.....” kafin ta ƙare maganar sir mubarak yai hanzarin katseta”Kada na sake jin kinyi min godiya saboda nayiwa jazz abu, kinsan banaso” cikin sanyin murya tace”nadaina in sha Allah” “Daddy, sannu da dawowa, nayi missing dinka sosai, meyasa jiya baka faɗamin halin da kake aciki ba ai da nazo asibitin na tayaka jinya” zaki ne yayi maganar yayin da yake ƙoƙarin zama gefen jazz Murmushi sir mubarak ya sakar mashi”sanyin idaniyata, ina fata na same ku lafiya”? Mayar mashi da martanin murmushin Zaki yayi”lafiyalou, sai dai jiya dukkanmu bamu runtsa ba saboda rashin ganinku da bamuyi ba” Sir mubarak yace”shiyasa naga idanuwanku sun kumbura, ashe bani kadai na kwana azaune ba” Tun da suka fara magana ibad ya haɗe ranshi, “Daddy ni baka ganni bane”? Ya faɗa yana duban sir mubarak Girgiza kai ya ɗanyi kafin yace”naganka ibad, amma nida kai wanene ya dace ya fara gaishe da wani? Yamutsa fuskarshi yayi ƙasa ƙasa da murya ya furta”sannu da dawowa dad” ta6e baki sir mubarak yayi saida na roƙa, bubbuga ƙafa ibad yayi Mom turai tace”mu shiga ciki, in taimaka maka kayi wanka” zaro ido Ibad yayi haɗi da furta”Mom wa zaki ma wanka? Jazz ko daddy”? Duk da halin da suke aciki na damuwa hakan bai hanasu yin dariya ba, shi kanshi jazz din saida ya murmusa, “Daddynku nake magana akai,” hannu biyu yasa ya toshe bakinshi, Idan ya kalli sir mubarak sai ya kalli mom turai Ko kaɗan batajin kunyar ƴa’ƴanshi, saboda ita aganinta bawani abu bane donta furta hakan agabansu. “My son, zamu shiga” Zaki yace”okey, zan tafi da jazz ɗaki, zan taimaka mashi yayi wanka ya canza kayan jikinshi’ “Hakan yayi,” ta faɗa tare da duban Ibad Har yanzu mamaki bai sake shi ba, sai kace baiyi rayuwa a turai ba. “Akwai kayan abinci dana shirya mana a kitchen, ka shiga ka dauko su a dining zaka jera” Amsa mata yayi da toh, da sauri ya juya ya nufi hanyar kitchen Miƙewa zaki yayi tare da ruƙo jazz ya miƙar dashi, “Allah ya baka lafiya my jazz,” amsa mata yayi da ameen, kafin suka nufi ɗakin shi Bayan tafiyarsu ta dubi sir mubarak”ina ƙara baka hakuri, kasan ba halina bane” Murmushi yasakar mata”kada hakan ya dame ki, ni dama fargabana halin da zaki shiga, but Alhamdulillah tun da kin fahince ni, yanzu bani da sauran damuwa” Ya faɗa tare da ruƙo hannunta suka nufi bedroom dinshi “Jiya nayi kewarka, idanuwana sunyi maraicin ganinka, dole na haƙura na rungume pillow amadadinka” tayi maganar ayayin da take taimaka mashi wurin cire Rigar jikinshi Daɗaɗan kalamanta ba ƙaramin sanyaya mashi zuciya sukeyi ba, shiyasa akoda yaushe yake ƙara jin sonta, saboda ƙaunar da take nuna mashi, tun farkon auransu bata ta6a barin ya shiga toilet yin wanka shi kadaiba sai idan wani uzirinne mai ƙarfi ya hanasu shiga atare, sannan ta hana ya ajiye mata masu aiki agida ba yadda baiyi da ita ba akan baison tanayin aikin wahala amma taƙiya saboda kishinshi da take yi, batason wata ta ƙwace mata mijinta, Atare suka shiga toilet. *ANEELERH❤‍🔥* Tun bayan da ta shiga toilet tabar Zahra atsaye tana kallon hoton su, lokacin da ta fito daga wanka bata taras da zahra a dakinta ba, shaf shaf ta shirya kanta cikin shiga ta abaya maroon colour, ta yafa mayafi akanta, fitowa tayi daga dakin a dining room ta taras da su gaba ɗaya sun hallara kan dining chairs, tun daga kan abie dinta, uncle ɗan iya, mami da ummi da kuma mahboob, sai zahra kaf dinsu ne, kowa ya kimtsa domin yin ɗa’amin, Ana ce take yin serving dinsu tana daga tsaye hannunta ruƙe da serving spoon. Sautin takun takalmantane Yaja hankulansu ga dubanta, fuskarta da fara ta ƙarasa cikin girmamawa ta soma gaishe da iyayenta “Barka da safiya, ina kwananku, kun tashi lafiya” Fuskokinsu asake suka amsa mata. Mahboob Yace”Gm Auntyna, bismillah zoki zauna gefena” ya faɗa yana nuna mata empty chair din dake gefenshi Zahra dake kallonsu, murmushi tasaki ganin yadda mahboob Yake yima Aneelerh fadanci abunda bai saba Yi ba. Bayan Aneelerh ta zauna, Ana ta gaishe da ita, a mutunce ta amsa mata”two days bana ganin ki, kin 6oye min sai kace ba gida ɗaya muke a zaune ba, sai dai idan ni na matsu da son ganinki in shiga kitchen time da kike Yin girki ko”? Sunnar dakai ƙasa Ana tayi yanayin fuskarta babu walwala, Mami tace”Ai ba tun yauba na lura halinta ne batasan sakewa cikin mutane, kullum kina ƙumshe daga kitchen sai ɗaki, yakamata kina fitowa falo muna yin fira dake” cikin kulawa mami tayi maganar. Cikin sanyin murya ta furta”ay min afwa zan dinga futowa daga yanzu” Mami tace”haka nakeson ji, ki daina daukar kanki a matsayin ƴar aiki, damu dake duk abu ɗayane awurin Allah, so please adaina kuntata kai adaki” murmushi Ana tadan saki har cikin ranta taji dadin maganar mami, zahra tace”idan ma bata fitoba ni dakaina zan dinga zuwa dakinta ina takura mata da surutu” dariya Ana tasaki, ummi tace”dako ta shiga uku dake, har bacci sai kin hanata saboda zafin ɗuminki” tur6une fuska zahra tayi, jin abun da ummi tace, harara ummi ta jafa mata”lafiya kike kallona, ko nayi maki ƙaryane? Kafin zahra tayi magana mahboob yace”wallahi ummi gaskiya kika faɗi” yai maganar yana kokarin tura chips abakin shi”Zahra badai ɗumiba, kamar aku, inta fara zuba kamar radio mai jini, ga tambayar tsiya kamar tsohuwar ƴar jarida” gaba ɗayansu suka sanya dariya, ran zahra ya 6aci a ƙule tace”hmmm mahboob ai ƙwarani, wai talla zaiwa audi gori, idan ni surutu gare ni kai fa? Saboda shegen maƙonka ko kuɗi zaka ƙirga sai ka shiga toilet don kada wani ya gani” dariya su ka yi, Abie Da uncle ɗan Iya sun kasa kunne suna sauraran su, ganin surutun nasu bame ƙarewa bane yasa uncle dan Iya yi masu gyaran murya hankalinsu ya dawo kanshi”surutun Ya isa haka, kun cika mana kunne, Yakamata ku maida hankalinku akan abun da ku ke ci, kun riga da kunsan babu kyau ana cin abinci ana surutu” tunda ya ambaci hakan kowan nan su yaja baki yayi shiru, baka jin sautin komai saina cokulansu kwas kwas tamkar zasu fasa plates din abincinsu, gaba daya hankalin Mahboob dana Aneelerh yana akan Ana, ga dukkan alamu sun fahimci babu lafiya atattare da ita, tun daga kan yadda take faman zazzare idanuwanta. Cup din lemu Aneelerh ta dauka takai baki tana kur6arshi, bayan ta kammala sha tace”ki koma ɗaki ki zauna ki hutu” ta fada tana duban Ana “Inaso ne ku kammala cin abinci in kwashe kayan, akwai sauran aiki da zanyi wanke wanke da gyaran kitchen idan na kammala sai in huta” Aneelerh tace”kada ki damu zanyi maki aikin, just ki tafi ɗaki ki huta” Harta buɗe baki zata kuma yin magana mahboob ya tari numfashinta da cewa”Sis Ana, kiyi abunda aunty Aneelerh ta fada maki, nima zan tayata yin aikin” Gyaɗa kai Ana tayi cikin sanyin murya ta furta”nagode madam, Mahboob thank u” ta fada tare da juyawa ta nufi bedroom dinta da sauri, hatta yanayin tafiyarta babu natsuwa. Kallon juna Aneeelerh da mahboob sukayi, da ido tayi mashi nuni dayabi bayan Ana yaji masu meke damunta. Jinjina mata kai yai alamar toh, miƙewa yayi daga kan kujerarsa yakai hannu ya yago tissue Ya goge bakinsa. “mahboob harka kammala cin abincin”? Uncle ɗan Iya ne ya jefa mashi tambayar. “Ban ƙoshi ba daddy, ina son zan shiga toilet ne uziri gare ni” uncle ya amsa mashi da okey. Da sauri Ya juya yabar dining area din, Kasancewar Bedroom dinsa dana ana a 6angare daya suke shiyasa yai ƙaryar cewa toilet zai shiga. Tunkafin mahboob Ya shiga ɗakinta ya soma jiyo shessheƙar kukanta, Hankalinshi yayi mugun tashi, koda ya ruƙo handle din ƙofar room din nata adatse ya Ji ta, muryarshi ƙasa ƙasa Ya ambaci sunanta shiru bata amsa mashi ba, knocking kofar yayi”sis ana ki buɗe min ƙofa dan Allah, Inason yin magana dake, Aunty Aneelerh ce ta aiko ni” Jin ya ambaci sunan aunty aneelerh yasa tayi saurin shiga toilet ta wanko fuskarta, jiki na rawa tazo gaban ƙofar ta buɗe mashi ita. Ajiyar zuciya ya sauke yana bin fuskarta da kallo, idanuwanta sun kaɗa jawur da su. Ruƙo hannunta yai acikin nashi kamar wani babban mutun Yajata zuwa cikin dakin, Ya kulle ƙofar. Tare da goya hannayensa saman ƙirjinsa Yana kallon fuskarta Ganin ya tsareta da ido yaƙi yin magana ne yasa tace”mahboob lafiya kake kallona? Me aunty Aneelerh tace ka fada min” Numfashi yaja kafin ya soma yi mata magana “Meke damunki? daga ni har aunty Aneelerh mun fahimci bakya jin daɗi kamar akwai wani abu dake damunki” Adabarbarce ta furta”babu komai mahboob lafiyata qalou....” “Bazai yiwu ba Ana, saboda kafin na shigo ɗakin ki na jiyo sautin shessheƙar kukanki, taya zakice min bakomai? Bayan ga alamu nan nagani akan fuskarki, dan Allah Ana kada ki 6oye mana abunda ke damunki, kinga mun damu dake ni da aunty aneelerh dama sauran mutanan gidan”? A marairaice mahboob yayi mata maganar Baiwar Allah tayi zuru da ido, komai nata ya canza. Ƙoƙarin danne damuwarta tayi hawayen da suka taru acikin idonta tayi saurin mayar da su. Can ƙasan makoshi sound din muryarta ke fita “Dagaske nake yi maka mahboob, babu abun da ke damuna, idan ma saboda shessheƙar kukan da kaji ina yi ne to ka kwantar da hankalinka, sister dina ce janet ta kirani awaya tana fadin halin da take aciki Na rashin kuɗin da zatayi amfani dasu, gashi bata da koshin lafiya ko aikin da take zuwa yi a hotel yanzu komai ya ta6ar6are mata, idan ba zaka mantaba na ta6a baka labarin ƴan uwana Janet da esther, har na fada maka cewa mu marayune bamu da kowa neman na kanmu muke Yi, A halin yanzu dai nice nake taimaka masu da kuɗin da suke siyan abinci da suturar sanyawarsu, nima idan natara kudin albashina ne nake samun wanda nake tura masu..... tunda tafara magana jikin mahboob yai sanyi, tausayinta duk ya kama shi, har cikin ranshi ya yarda da abunda ta faɗa mashi. “kinsan da abun da ke faruwa da ƴan uwanki shine baki faɗa mana ba? Meyasa? Meya amfanin zaman taren Ana”? Fashe mashi tayi da kuka tana fadin”bana so ne na takura maku, shiyasa ban fada maku ba” Dafe kai mahboob yayi dahannu ɗaya ranshi ya 6aci afadace yace”kin ban mamaki yanzu ko aunty aneelerh baki Iya faɗama damuwarki ita da ta dauke ki tamkar jininta, gaskiya ni baki kyauta min ba Ana, banyi zaton hakan daga gare ki ba, ashe baki daukemu kamar yadda muka dauke ki ba” Ruƙo hannayenshi tayi acikin nata yayin da hawaye ke fita akan fuskarta tace”mahboob am sorry, idan ranka ya 6aci” Ta6e mata baki yayi”Ni zanje na fada ma aunty aneelerh halin da ƴar uwarki take aciki, nasan zata taimaka maki, Nima zanyi kokarin baki wani abu, ki cika, itama zahra zan mata magana, sai mu haɗa maki kudin da zaki tura masu ......” Godiya ta soma yi mashi “Nagode mahboob, naji dadin taimakon da zaka yi min” Sakin fuskarshi yadanyi”dan Allah daga yau ki daina sanya damuwa aranki, ni nafiso in ganki cikin kwanciyar hankali, fuskarki da annuri, idan ma wani abu na damunki, please ki runƙa sanar dani, zan taimaka maki da abun nake dashi, ga kuma aunty aneelerh itama ki dinga fada mata damuwarki” “Zanyi hakan mahboob nagode da kulawarku agareni” Sai da mahboob ya tabbatar ya sanyata farin ciki, kafin Ya fito daga dakin Ya nufi dining area Koda ya ƙarasa bai taras da Aneeleerh da zahra ba, Har sun kammala yin breakfast dinsu, daga can falo Ya hango mami da ummi, zaune suna fira tare da Uncle ɗan Iya da abie. Hatta kayan abincin an kwashe su daga dinning, harya juya zai nufi dakin Aneelerh ta wutsiyar idonshi Ya hango gifcinta a kitchen, da sauri Ya nufi kitchen tun kafin Ya ƙarasa ya jiyo muryar zahra ta zaƙe tana ba Aneelerh labarin shagalin birthday din obie da akayi, maimakon Ya shiga sai ya la6e gefe daya ya kasa kunne Yana sauraronsu. Babu wanda ya lura dashi acikinsu saboda sun bashi baya. Aneelerh tana gaban Sink Ta tattara kwanukan da suka 6ata tana wankesu, zahra tana agefenta “Aunty Aneelerh ina baki labari, wallahi Anyi 6arin dollar a wurin nan, dangin obie sun gaji arziƙi gaba da baya, wai kinga manya manyan mutanan da suka halarta? Attajiran masu kuɗi masu manyan muƙamai, kowa kika gani a filin taron da matsayinsa, daga governor sai president, ga sanatoci da ministoci......” Murmushi Aneelerh tasaki tana fadin”Gaskiya naji takaici da ban biki munje taron nan ba, da nima na kashe kwarkwatar idanuwana” “Aunty Aneelerh duk yadda zan baki labari bazan iya fada maki kwatankwacin abun da idanuwana suka gane min ba, nifa lokacin da ƴa’ƴan baba obie suka fito tsakiyar fili sunayi mashi liƙi Yana taka rawa wallahi ji nayi kamar inyi wuff in shiga filin in tattara kuɗin in saƙe a hammata” Tuntsirewa aneelerh tayi da dariya tana duban zahra, hada kwatanta mata yadda zata kwashe kudin ta saƙe ahammata. Mahboob dake a la6e yana sauraron su dariya ce kumshe abakinshi. “Ni abun da yafi burge ni, haɗuwar ƴa’ƴan baba obie da jikokinsa, da surukansa sun ɗauki wanka na mutunci na kece raini kai komai ma sun haɗa, waɗanda suka fi burgeni kinga prime minister Hateem, da president dinmu Sharafudeen sun iya dattako, komai nasu da aji suke yin shi, matayensu sunfi kowa haduwa gimbiya mujeedat da Hajiya malikat sarauta, sai kuma mutuniyata Hajiya saratu inayin matarnan saboda tana ƙaunata mutane suna fadin masifarta ni wallahi bata ta6a yi min koda tsawa ba kamar ƴar cikinta haka take yi min magana....” da farin ciki akan fuskarta tayi maganar. Aneelerh tace”Jinin ku Ya haɗune dana juna, Allah yasa ta zama surukarki kinga shikenan kema zaki samu matsugunni a obie estate” wani irin ihun farin ciki zahra tasaki hada jujjuya qugu tana fadin”Amen Ya Allah, Aunty Aneelerh Allah ya kar6i addu’arki” Dariya Aneelerh tasaki yayin da take ɗauraye plates din da take wanke wa da ruwan dake fita a faucet. “Zahra baki faɗamin haduwarki da mutumin ba”? Kwa6e fuska zahra tayi annurin fuskarta ya ragu. “Bai zo taron ba, duk irin burin dana ci nason ganinshi bai halarta ba, banji dadi ba dama nasan zai yi wuya yaje saboda mutunne shi da baisan hayaniya” “Eyyah zahra najiye maki baƙin ciki, in sha Allah wata rana zaku haɗu da shi” Ta6e baki tayi”Ni yanzu ba wannan ba auntyna, Inataso in baki labarin Nazli da Yazrin Ƴa’ƴan Prime minister da ƙanwar Chief Owais hindu, kinga waɗannan dana lissafa maki ƙarshene su afagen kyau da aji, cikin maza kuwa in ka cire chief owais sai wani ɗan uwansu menene ma sunanshi.....” ta faɗa tana cizon yatsa takasa tuna sunan. “Namanta, shima a canada yake zaune, mutumin ya iya ɗaukar wanka, ga kyau da aji bayan shi sai twins sun haɗuwa sunyi kyau kamar dollars. Dariya Aneelerh tayi, jin yadda zahra ta haƙiƙance tana bata labari ko gajiya batayi. “Yanzu faɗa min alherin da sukayi maki naji ɗazu kince zaki fada min” Gyara tsayuwa zahra tayi kafin tace “Kinga da farko Hajiya saratu tayi min kyautar tsadadden leshi guda biyu, da hand bag, hada set na agogo da zobe, da turarurruka......” jinjina kai Aneelerh ta yi tana fadin”masha Allah, zahra najiye maki daɗi, kin samu na sallah” “Bangama fada maki ba, bayan kuɗin aikin decoration da hajiya saratu ta biyamu, prime minsiter yayi mana kyautar kuɗi duk mutun ɗaya 1.5 million” waro ido waje Aneelerh tayi mahboob dake la6e jin an ambaci kuɗi sai gashi ya dawo gefen zahra Yana raira waƙa. “In rabo ya tsago dakai kuma abun ya tabbatar saida kai to rabbine yace sai da kai in sai da kai kawai sai da kai, don haka nima Allah ne ya tsaga da rabona ashe arziƙine ke kirana......” gaba ɗaya suka sanya dariya, Aneelerh tace”mahboob yaushe ka shigo kitchen din nan” Da murmushi akan fuskarshi yace”tun ɗazu ina la6e bakin ƙofa na kasa kunne ina sauraron aku sarkin ɗumi, yau surutun zahra yayi min rana wannan arziƙi haka, wato saboda baƙin ciki zahra ƙiri ƙiri kika hana in rakaki obie estate da yanzu hadani za’ayi rabon kuɗin nan....” Dariya zara tayi tana fadin”ai baka ji komai ba, bayan kuɗin da prime minister yabamu, president Ya ƙara mana, duk mutun ɗaya dubu ɗari takwas” dafe ƙirji mahboob yayi kamar wanda yaji wani mugun abun “Sannan Abokin Baba Obie, Jan kunne ya raba mana dubu ɗari biyar biyar da dollar ya bamu su” Kallon juna mahboob da Aneelerh su kayi. “Anya zahra dagaske kike kuwa? Wannan kuɗi haka kamar akan bishiya ake tsunkosu” Hararar shi zahra tayi”an gaya maka kowa mai maƙone irinka, ai su a wurinsu kuɗin da suka bamu bakomai bane” Jinjina kai mahboob yayi”Allahumma arzuƙni, Sister Yanzu ina kuɗin suke? inaso zan tayaki ƙirgawa” Dariyar shaƙiyanci zahra tayi kafin tace”suna kwance cikin account bank dina suna bacci, dollar din da aka ba mu ne kaɗai suke a dakina kuma na 6oye su saboda nasan halinka sarai, tsaf zaka Iya zuwa ɗaki yi min halin 6era” Dariya Aneelerh tasaki, a lokacin ta kammala yin wanke wanken, ta mayar da hankali akan fuskar zahra Mahboob Yace”kar dai kice zakiyi min rashin mutunci wallahi sai inyi zuciya inje in nemi auran ɗaya daga cikin jikokin baba obie” Dariya suka saki gaba dayansu bayan sun tsagaita Aneelerh ta dubi mahboob”Ya ake ciki? Kunyi magana da Ana”? Ɗaga mata kai yai alamar eh, zahra tace me ya faru ne ko bata da lafiya” Nan mahboob Ya kwashe komai Ya sanar dasu dangane da halin da Ana take aciki. Shiru sukayi jikin kowa yayi sanyi, musamman Aneelerh, ranta Ya dan 6aci bata ji dadin ƙin gaya matan da tayi ba. “Idan kuwa hakana Ana bata kyauta min ba,Yanzu har akwai abunda zata 6oye min duk irin shaƙuwar dake atsakanin mu?” “Aunty Aneelerh please kada ranki ya 6aci, na riga da nayi mata faɗa, abun da ya dace ku harhaɗa mata kudin da zata turama ƴan uwan nata” Zahra sarkin tausayi tace”nida da halima wallahi da sun dawo gidan nan da zama.....” wata uwar harara Mahboob Ya watsa mata”saboda ke zaki ciyar dasu ko”? Fashewa sukayi da dariya. Aneelerh tace’baka da dama mahboob, yanzu fa ka gama fadin a harhada mata kudi aturawa ƴan uwanta shine kuma don tace su dawo nan da zama kake tada jijiyoyin wuya daga maganar taimako” Yamutsa fuska mahboob yayi”abun da nake nufi Aunty Aneelerh, ɗan adam ba abun yarda bane, muna iya mu taimake su su kuma su butulce mana shine abunda nake jiye mana, kawai dai ƙwara in taimakon zamuyi masu mu tura masu can su ƙarata” “Ka faɗi gaskiya mahboob, nima nayi wannan tunanin, Yanzu me yakamata muyi”? Acewar Aneelerh. Zahra tayi karaf ta kar6e dacewa”kowa ya kawo abunda yake dashi hada kai mahboob nakama sai yafi yawa tunda kaine jagaba atafiyar” Harararta yayi”zahra ki daina wannan maganar, ni bawai bazan bada ba, idan na bada ai ba faduwa nayi ba, duk wanda ya taimaki wani shima Allah zai ji ƙansa, ga lada da mutun zai samu, kawai dai ni bani da kuɗinne Yanzu.....” ya fada yana soso keyarshi. da zolaya zahra tace”hmmm, Ana fa ba musulma bace, ta ina zamu samu lada idan muka taimake ta”? Banza yayi da ita baice komai ba, Aneelerh tace”babu ruwanmu da wannan, don Allah zamuyi da kyakkyawar niya, kidaina wannan tunanin” gyaɗa kai zahra tayi”shikenan naji, zan bata wani abu cikin kuɗin dana samu, Mahboob Idan kana da acct number dinta ka tura min” Aneelerh tace”Ina da ita, Idan muka koma ɗaki zan tura maki, Nima zan sanya nawa kudin” Farin ciki ne tsantsa akan fuskar mahboob, Yaji daɗi zasu taimaki Ana batare da ko sisin shi ba. “Allah yabarmun ku sisters dina, zahra Allah ya baki miji nagari mai sonki mai ƙaunarki, and aunty Aneelerh ubangiji Allah ya bayyanar mana da mijinki da ƴan uwansa , Allah ya raya mana baby junaid dinmu....” addu’o’i yadinga yi masu suna amsa mashi da ameen, kafin Ya juya zai fuce daga kitchen din “Mahboob” kiran sunanshi da Aneelerh tayine ya dakatar da shi daga yin tafiyar ya waiwayo yana kallonta “Please idan ka fita ka faɗama su mami, zuwa anjima Hajiya adama zata zo kawo mana baby junaid nasan bata sanar da ita ba” “Aunty Aneelerh ashe yau muna da babban baƙo agidan namu, mutumina zai dawo, zamu dasa daga inda muka tsaya” Murmushi Aneelerh tasaki, zahra tace”wallahi har na kosa in ganshi,Yau zaisha daƙuna duk saina sale mashi fatarshi” Aneelerh na murmushi tace”inaso zamu shirya masu abincin da zasu ci, tun da Ana bata jin dadin zuciyarta mubarta ta huta sai muyi aikin atare” Zahra tace”Lafiyalou, dama na kwana biyu banyi girki ba, har cake zan haɗama baby junaid dina” Sun jima suna yin fira a kitchen kafin daga bisani suka fuce zuwa ɗakin domin yin sallar azhar da aka fara kira. *OBIE ESTATE🌃* Idan muka koma 6angaren dattijon arziƙi, tunda garin Allah ya waye Hankalinshi ba akwance Yake ba, gaba ɗaya yabi ya furgice masu sun rasa gane kanshi, ko jiya da dare bai runtsa ba, sambatu yadinga yi masu yana firgita yana fadin ga macijij nan zai sare shi, Ina owais dinshi Yana gani za’a cutar da shi bazai kashe macijin ba, mutun biyu da suka taya shi kwana a ɗaki his excellency Deen ne tare da His excellency abdul razak, su kansu basu yi bacciba jiya saboda halin da baban nasu yake aciki, hatta sallar asuba agida sukayi ta yaƙi fita daga ɗaki, kuma ya hana su tafi subarshi, bawan Allah ba ƙaramin jiki yaji ba, hada ruɗun tsufa ke damun shi, daƙyar suka samu nasarar sanya shi yin baccin dole. A yanzu haka Yana daga kwance saman gadonshi Ya ɗaura kanshi kan pillow, deen da Abdul razak suna a zaune saman arm chairs din dakin idanuwansu akan fuskar baba obie. Jin motsin buɗe kofane Yaja hankalinsu ga kallon mai shigowa Senate lateef ne, fuskarshi babu walwala. Daren jiya da damuwar abunda ya faru ya kwana Miƙa masu hannu yai suka gaisa da ƴan uwan nashi Kafin ya dubi baban nasu dake kwance kan gado yace”Bacci yake yi ko idon shi biyu”? His excellency Deen ne yace”bacci yake yi, daƙyar muka samu Ya runtsa” ajiyar zuciya senate lateef ya sauke kafin yace”banji dadin abunda ya faru jiya ba, gashi har yana neman zautar mana da mahaifinmu, wai taya ma akai har maciji ya shigo part din nan”? Rai amatuƙar 6ace yayi maganar His excellency Abdul razak Yace”abun da yafi ɗaura min kai shi Owais din Yace ba maciji bane mutunne ya rikiɗa....”tunkan Ya ƙare maganar Senate lateef yace”inko dagaske ne wannan maganar to kuwa ba mutun bane dama, Aljani ne sannan ita wannan ifritun yarinyar mai kasada dana gani atare da shi wacece ita!”? Kafin wani ya bashi amsa sallamar Pravin ta katse masu hanzarinsu, Shigowa yai cikin shiga ta black suit. Cikin girmamawa pravin ya gaishe da su, bayan sun amsa masu fuskokinsu babu walwala, pravin ya soma yin magana “Baba bashi da lafiya ne? naga da asuba bai halarcin masallaci ba” “Baka ga abun da ya faru jiya bane”? Acewar senate lateef. “Nagani, kar dai ace shi ne ya hana shi sukuni”? Cikin nuna kulawa yayi maganar. His excellency abdul razak Yace”ai kuwa dai shine, don jiya ko bacci baiyi ba tsabar firgici, yanzu haka ma da kake ganin shi a kwance daƙyar muka samu yayi bacci’ “Abu baiyi daɗi ba” pravin ya faɗa yana ɗan girgiza kanshi”ubangiji Allah ya bashi lafiya” atare suka amsa mashi da Ameen. Senate lateef ya ɗaura da cewa”ni yanzu so nake naji daga bakin shi Owais, ya faɗa min wanene macijin menene alaƙar shi dashi” “Bari na kira shi awaya, ai jiya yace zai shigo yai mana bayani amma shiru kake ji wai malam yaci shiru” Deen ne yai maganar tare da curo wayarshi daga aljihu ya danna ma Chif Owais Kira, kusan sau uku tana yin ringing bai yi picking ba. “Bai ɗaga ba, may be baya akusane da wayar” ya fada yana kokarin maida wayar cikin aljihun, kwatsam kiran owais ya shigo wayar tafara ruri, ajiyar zuciya ya sauke tare da duban su yace”shi ne ke kira,” ya fada tare da yin picking din kiran Ya kara wayar a kunnanshi, bayan sun gaisa deen yace”muna ta tsammanin zuwanka gida shiru baka shigo ba, ga babanku nan kwance ba lafiya saboda abun da ya faru jiya ko runtsawa baiyi ba sai firgita yake yi”. On the other hand chief Owais ya furta”I will come later, insha’Allah,” “Okay, we’ll be waiting for you, sannan inason sanin Ina macijin nan yake? Naji kace mutunne” Muryar chief owais tamkar bai son furta maganar yace”please uncle can i text you” deen yace okey ba damuwa”, rejecting call din yayi, kafin wani ya furta magana ƙarar shigowar saƙo Ya dakatar da su. Karanta sakon Deen ya soma yi duk sun ƙura mashi ido suna jiran jin me zaice masu, musamman pravin har wani zoƙa kai yake yi yana leƙen wayar Deen. Ɗagowa yai da alamun mamaki akan fuskarshi yace”tabɗijancan, wallahi dagaske macijin mutunne wai shaidanun aljanune a jikinshi, yanzu haka ya rikiɗa ya koma mutun acan gidanshi yake zaune,........” aruɗe suke kallon shi. “Wai ko kunsan Prime minister namu shine ya tura da jet din da zai ɗauko sheikh imam daga sudan saboda kawai ya taimaka ma macijin ya dawo halittarsa”? Jin wannan maganar ba ƙaramin firgita senate lateef yayi ba ranshi a6ace ya furta”what? Bangane me kake nufi ba! Yaushe akayi hakan?batare da sanin mu ba!” a kausashe ya furta maganar,, a sukwane his excellency abdul Razak Ya miƙe Yana fadin”Anya ka karanta saƙon nan dai dai, bani wayar na duba, ya furta hakan tare da kar6ar wayar Deen Yana duba sakon, bayan ya gama yace”ba shakka, kuwa owais dinne ya rubuta da kanshi, magana ta tabbata prime minister namu shi ya tura da jet din daya dauko sheikh imam daga sudan don kawai a duba yaron, muna nan zaune muna jinyar ubanmu shi yana can wajen taimakon yaron da bamusan wanene shi ba, bamu haɗa alaƙar komai da shiba, bansan meke damun prime minister ba, daga shi har owais din shegen son taimakonsu shi zaija su jefa family dinmu cikin matsala ......” kafin Deen Ya ƙare magana senate lateef daya gama fusata yana huci yace”Wallahi basu isa ba, ni bani buƙatarma jin wani ƙarin bayani daga garesu, Yaron nan bazai zauna a estate dinmu ba, tunkafin aje ko’ina harya fara mallake zuciyar ɗan uwanmu hakan na nufin da wata manufa ya shigo family dinmu, zai iya yiyuwa wasu mugayen ne daga maƙiyan jam’iyarmu sukayi amfani da shi don su tarwatsa family dinmu, ku duba kuga fa duk gidajen dake a estate dinmu bai shiga kowanne ba, Ya tsallake nasu Ya faɗo gidan babanmu saboda shine target dinsa.....” a harzuƙe senate lateef Ya ƙare maganar. Kanwa uban Ƴan Zigi Pravin Ya haɗe girar ƙasa da sama yace”Ni dama tun Jiya hankalina bai kwanta da shigowar macijin nan ba, Ai daga jin yadda abun ya faru zaka shaida makircine aka shiryama baba, so suke kawai su kashe shi, in ba haka ba taya za’ai ace wai mutun ya koma maciji ai sai dai idan sihirine da shi, munafuki kawai wallahi bazamu yarda ba, Yaron nan bazai zauna mana a estate dinmu ba, dole ne owais Ya kore shi daga estate dinmu, sannan A yanke alaƙarshi da kowa na family dinmu idan ba haka ba zaija mana masifar da bazamu Iya shawo kanta ba” Rai a6ace pravin yayi maganar Yana kallon fuskokinsu. Jinjina kai kowan nan su yayi alamar gamsuwa da bayanin pravin, His excellency abdul razak Yace”Ai bazamu ta6a yin gangancin nan ba, mu jira owais din ya shigo anjima, shima hateem din Zanyi waya da shi” Pravin yace “yamakata atara kowa har shi kanshi yaya sharafuddeen din yazo yaji abun da owais ke shirin janyo mana a family, wallahi jiya Saratu batayi bacci ba, saboda fargabar macijin nan, sambatu ta dinga yi min tana kuka tana fadin gashi nan zai sareta, duk tabi ta haukace ta rikice min aɗaki, daƙyar nashawo kanta da ayar Allah” Aruɗe Senate lateef yace”kunji ko? Tun yanzu ana kokarin ganin bayan ahlinmu” Damuwa ƙarara akan fuskar Deen yace”Pravin kana nufin saratu batayi bacci ba jiya saboda macijin”? Batare da ɗar ba yace”bata yi ba yaya, yadda taga rana haka taga dare, ni na zauna ina yi mata fifita saboda zufar dake tsastsafo mata gafa ac a daki amma haka ta dinga zubda gumi” Hankalinsu ba ƙaramin tashi yai ba, gaba ɗaya sunyi amanna da maganar pravin Murya na rawa his excellency abdul razak Yace”Yanzu awani hali take ciki? Tayi bacci da safe? Girgiza kai pravin yai fuskarshi da alamun jimami yace”batayi ba idonta biyu ko abinci takasa ci,” “Inason ganinta pravin” acewar abdul razak” Pravin yace toh, bari naje nazo da ita ya juya jiki na 6ari ya fuce daga ɗakin. Yana fitowa daga dakin su ka yi kici6us da Hajjaty, ta ɗauki wankan bubu gown ta lace a jikinta, ta ca6a uban ado, ƙamshin turarenta ya buɗe ko’ina, mayafin rigar asaman kafaɗa ta daurashi, doguwar suman kanta ta zubo har gadon bayanta, Hannayenta biyu ruƙe da faffaɗan tray daga saman shi an ɗaura jerin kayan abinci. Wani mugun kallo da pravin ya watsa mata saida gabanta Ya faɗi, duk tabi tasha jinin jikinta, sarai tasan ya hanata yin kwalliya idan har bashi zatayi mawa ba amma taƙi jin maganarshi. Sai faman ƙyafƙyafta idanuwanta take yi, tayi mashi kyau sai dai yaji haushin adon data ca6a. “Kin manta gargaɗin da nayi maki? Baki jin maganata ko”? muryarta na rawa ta furta”am sorry dear, na saba ne” guntun tsoki Yaja “yanzu ahaka zaki shiga dakin obie, bayan kinsan bashi kaɗai bane aɗakin, Balagaggun ƴa’ƴansa duk suna aciki, duk kamun kansu bazasu iya jure shaƙar ƙamshin turaren jikinki ba batare da kin jefa su yanayi ba, ko kallon ki su ka yi sai sun ayyana wani abun aransu....” shiru tayi mashi ba tare da tace komai ba, numfasawa yayi kafin ya ɗaura da cewa”bazan bari ki shiga ɗakin ahaka ba, sai dai ki haƙura da kai masu abincin ki koma ɗaki ni sai in kai masu” muryarta tamkar zata fashe da kuka tace”dan Allah dear ka barni in kai masu, Jiya fa bansamu damar gaishe dasu ba”da shagwa6a tayi mashi maganar, nan take kasala tafara kama shi, matsawa yayi dab da ita, ya ruƙo mayafinta data ɗaura kan kafaɗarta, ya janyoshi zuwa saman kanta ya lullu6e mata sumar kanta da kirjinta saboda yana jin kishin agane mashi majiyar dadin shi, ƙoƙarin manna mata kiss yayi saman red lips dinta, kamar daga sama yaji ance”Daddy!” A firgice pravin ya ɗago yana faman zazzare idanuwanshi Jin muryar zayn, su biyune hannayensu ruƙe cikin na juna shida Zaid, fuskokinsu da alamun ruɗani, kafin ƙarasowarsu pravin yayi saurin ɗaukar juice dake acikin jerin drinks din tray din hannun hajjaty ya buɗe murfin ya watsa mata ruwan lemun gefen galenta, baiwar Allah jikinta sai kerma yake yi, mugun tsoron Zayn take yi, tasan muddin ya gane abun da pravin ke ƙoƙarin yi mata sai ta yaba ma aya zaƙinta, ajiya juice din pravin yayi, ya dai daita natsuwarshi, ya nufesu fuskarshi dauke da murmushi ya ware masu hannayensu da niyar yayi hugginsu dinsu, Sai dai sunƙi bashi haɗin kai, wani irin matsiyacin kallon zayn yake watsama hajjaty data juya masu baya. Adabarbace pravin yace”kun ganmu atsaye ko? na fito daga ɗakin baba ne na bankaɗeta batare dana ankara ba” kallon tuhuma Zayn yayi mashi kafin yace”daddy mayafinta fa naga ka ruƙe a hannunka akan wani dalili” “Baka ji mena ce ba, bugeta nayi har tray din hannunta ya girgiza lemu ya 6arar mata jikin gyalenta shine fa na ruko gyalen ina ƙoƙarin goge mata” yayi maganar tare da juyawa ya ruƙo bakin gyalen hajjaty yana nuna masu, Ajiyar zuciya zayn ya sauke, zaid yace”daddy barka da safiya, ya gajiyar jiya” ya faɗa tare da yin huggin dinsa, pravin yadan bubbuga bayanshi”Alhamdulillah My son, Ina fata kun tashi lafiya, Yau ba zaku shiga office bane” cikin kulawa yayi maganar, hankalinshi na kan zayn, ya lura yafi ɗaukar zafi halinsa ɗaya dana jatumarsa wurin iya masifa. Ɗago da kai zaid yayi daga kan shoulder din daddyn nasu yace”mun tashi lafiya daddy, ba zamu je aiki yau ba sai zuwa next week, mun ɗauki hutu saboda zuwan Ƴan uwanmu” jinjina kai pravin yayi”hakan yayi, kunyi tunani,” ya faɗa still idonshi akan fuskar zayn daurewa yayi tare da ce mashi”Son ba magana? Ka tsareni da ido kana kallona ko akwai wani abune” Ta6e baki zayn yayi, kafin yace”bakomai, daddy ni me zance? Tun da ga zaid nan yana yi maka magana dani dashi duk abu ɗayane” Hajjaty tuni ta shige ɗakin Obie, batare da sun ankara ba. Dafa kafaɗar shi pravin yayi”kaima ina buƙatar yin magana dakai, bai kamata kana faɗamin haka ba, Ni mahaifinka ne yakamata kana tuna wannan” ya faɗa tare da janyoshi yayi huggin dinsa, zayn fa ji yake kamar ya haɗa jikinsa da allon bango, shifa sam mahaifinsu baya burgeshi baisan dalilin dayasa yake jin haka ba, kamar bashi ya haife shi ba” bayan sun raba jikinsu zayn yai ƙoƙarin furta”am sorry daddy, idan na 6ata maka rai,” murmushin gefen fuska pravin ya sakar mashi”kada ka damu, inayi maka uziri saboda har yanzu kallon ƙaramin yaro nake yi maka, akwai sauran kuruciya atattare dakai,” dan zaro ido zayn yayi”dady nine ƙarami”? Pravin yace ƙwarai kuwa, ko ka manta shekarunkane? Idan ka manta bari na tuna maka you’re just 2O something years, wata’ƙil don kana ruƙe da muƙami a company shiyasa kake jin kanka wani babba” Dafe kai zayn yayi da hannunshi, arayuwarshi ya tsani ana fada mashi shekarunshi, haushi yake ji, zaid dai sai faman murmushi yake saki, yana jin dadin tsokanar da daddynsu yake yima zayn. “Jiya a ina kuka kwana ne”? “Muna agidan daddy deen, munyi fira tare dasu justice, shine yace mu tsaya ayi firar yaushe rabo” zaid ne yayi mashi bayani Pravin yace”naji dadin jin haka amma ya akai Justice ya tsaya yin fira da ƙannansa maimakon ya tuntu6i Zaki shi da yake sa’ansa” da biyu yayi maganar yana kallon zayn, haɗe girar sama da ƙasa yayi”daddy, zolayar ta isa haka, nima zan ƙara shekarunne nan bada jimawa ba” dariya zaid da pravin sukayi, bayan sun tsagaita da yin dariyar pravin yace”bakusan abun da ya faru jiya da dare a part din baba” A ruɗe suka furt”meya faru daddy”? Nan fa ya labarta masu kaf abunda ya faru tun daga shigowar macijin, da firgicin obinna, Hankalinsu yayi matuƙar tashi. “Daddy kana nufin mommy batayi bacci ba saboda macijin? Sannan baba shima bai runtsa ba? Kuma naji kace chief owais ne Ya kau da macijin yaushe yazo ƙasar? Taya akai macijin ya samu damar shigowa estate dinmu dake acike da tsaron sojoji da ƴan sanda”? Zayn ne ya kora jawabin. Pravin ya ta6e baki haɗi da cewa”macijin fa mutunne wai ya rikide, acewar shi owais....”tunkan ya ƙare maganar, zayn da zaid suka kalli juna da alamun al’ajabi. “Tayaya haka zai yiwu? Kamar dai ashirin film, ko atarihi ni ban ta6a jin mutun ya rikiɗa ya koma dabba ba” acewar zaid. Pravin yace”ai shine muma abunda ya ɗaure mana kai, ni dai nafi tunanin yaron aljanine ko kuma wasu miyagunne da suke son cutar da kakanku suka yi amfani da sihiri a jikin yaron donsu kashe shi” Hankalinsu zayn ba ƙaramin tashi yayi ba, jikinsu har tsuma yake yi, “Ku shiga daga ciki, ku duba jikin baban naku, Sauran uncles dinku suna a cikin dakin, idan kun shiga ku tayasu jimamin abunda ya samu babanku, sannan please kada ku goyi bayan yaron yaci gaba da zama a estate din nan, tunda shi owais din bai san ciwon kanshi ba, idan ba haka ba taya zai ɗauko mugun abu ya ajiye agidan shi da sunan taimako”? Ranshi amatuƙar 6ace yayi maganar. Zayn daya gama harzuƙa yace”wallahi bazai yiwu ba daddy, wannan ai ba maganar da hankali zai ɗauka bace, in banda an rainawa mutane wayau taya za’ace wai mutun ya zama maciji? Kuma ya rasa inda zai farmaka sai gidan baban mu, bayan ga sauran gine ginen dane akusa dana shi owais din duk ya tsallakesu Ya nufo nan so ake kawai akashe mana shi, dama ya lafiyar giwa, ga mahaifiyarmu itama da firgici ta kwana bazan lamuntaba dole mu dauki mataki....” Yana huci ya ƙare maganar. Cikin sanyin murya zaid yace”Allah ne kadai yasan dai dai, kada mu yanke hukunci cikin fushi, bayan bamu da masaniya akan wanene yaron? Menene silar canza halittar shi, da son ranshi ko kuwa ƙaddarace ta afka mashi, duk waɗannan amsoshin zamu same su abakin Yayanmu owais tun da shi yasan komai dangane da yaron....”tunkan ya ƙare maganar, Pravin yai hanzarin katse shi da cewa”babu wata hujja da zamu jira zaid, ka duba kaga fa yadda ya siye zuciyar kawunku Hateem, meye alakarshi da yaron da har zai tura da jet din da zai dauko sheikh imam daga sudan, duk irin manyan malaman da muke dasu A nigeria, basuyi mashi ba sai da ya kashe makuɗan kudi don a dauko mashi sheikh, don baku agidan macijin ya kawo farmaki da baka furta maganar da kayi ba ayanzu, badan Allah yasa Owais Ya kau da macijin ba da tuni Ya sari kakanku saboda shi kadai yake kokarin kaima hari” jin wannan maganar yasa zaid shan jinin jikinshi “Inna lillahi wa’inna ilaihirraji’un, wannan wace irin masiface daddy? In sha Allah koma su wanene miyagun da ke son ganin bayanshi bazasu ta6a yin nasaraba, sannan Nima na goyi bayan a kori yaron daga estate dinmu” gyaɗa kai pravin yayi”yanzu naji magana my son”ya faɗa tare da dafa kafadar zaid din”ku shiga dakin baban, Ni yanzu zan je nataho da mahaifiyar taku”Amsa mashi sukayi da toh, kafin suka nifi ɗakin baba obie suka shiga da sallama abakunansu. *HAJIYA SARATU❤* Fitowa tayi daga bathroom, jikinta sanye cikin bathrobe fara ƙal, wanka ta samu tayi don taji daɗin jikinta, don tun da safe data farka bata motsa daga kan gadoba saboda fargabar abun da ya faru jiya da kuma damuwar da pravin Ya haddasa mata. Agaban mirror ta tsaya fuskarta babu walwala, idanuwanta sun ƙanƙance saboda rashin baccin da batayi ba a jiya, hatta kanta ciwo yake yi mata. Expensive body lotions dinta ta soma shafama skin dinta, bayan ta kammala ta nufi closet din kayanta, jim kaɗan ta dawo harta cire rigar wankan ta maida doguwar riga bubu ta material, turare ta dauka ta feshe jikinta da shi. Kafin ta kammala wayar ta dake ajiye kan pillow ta soma ringing, yamutsa fuska tayi kamar bazata ɗaga kiran ba, ta nufi wayar ta duba sunan me kiranta, ajiyar zuciya ta sauke kafin tayi picking call din Ko sallama batayi ba ta furta”daughter, sai yaushe zaki shigo gida”? On the other hand muryar faryat ta ratsa kunnanta “Mommy, tun jiya nayi niyar shigowa in kwana anan part dinku, Zulaihat ce ta ruƙe ni wai dole saina kwana a gidansu, mom madina ma tace in tsaya in kwanar masu shiyasa kika ji ni shiru kuma ma bani kaɗai bace, hada su Yusra duk muna agidan” Ta6e baki hajiya saratu tayi”okey, duk lokacin da kika ga damar shigowa ina jiranki,” faryat ta amsa mata da toh, kafin sukayi sallama, Landline din kitchen ta danna ma kira, Bugu uku Abla tayi picking call din “Jira kuke yi sainace akawo min breakfast dina”? A faɗace tayi masu maganar Cikin girmamawa abla tace”Ina bada haƙuri aunty, Yanzu nan zan shirya maki” guntun tsoki taja tare da katse kiran ta wurga wayar kan mattress. Bakomai take tariyowa ba face Rashin mutuncin da pravin yayi mata, Ya ƙona mata rai adaren jiyan nan, wai har ita zata kirashi yaƙi zuwa sannan yayi rejecting call dinta? bata motsa daga gaban mirror din ba, ƙarar knocking din ƙofa Ya katse mata zancen zucin nata Sai da ta mula tasha iska tukunna ta furta”Come in” muryar abla da ƙarfi ta furta”Aunty ƙofar a kulle take” tunawa tayi da ta datse dakin jiya ta ciki, juyawa tayi taje ta buɗe ƙofar, shigowa abla tayi hannayenta biyu ruƙe da wooden tray daga saman shi kayan breakfast ne. Wuce wa ciki abla tayi, ta daura tray din kan table, Kafin ta juya tana fuskantar hajiya saratu data ruƙe qugu da hannu ɗaya, har saida taji gabanta ya faɗi ganin 6acin ran dake kwance akan fuskarta, cike da jin shakkarta ta furta”ko akwai wani abu da kike buƙata”? Atsiwace hajiya saratu tace”ke nake buƙatar ki fuce min daga ɗaki, kin wani tsareni da ido kina kallona kamar yau kika fara gani na” Jiki na 6ari Abla ta nufi ƙofar fita daga ɗakin bayan ta fuce hajiya saratu ta nufi gefen gadon ta zauna, ta soma cin breakfast dinta, farawa da bismillah kakkauran tea ta ɗauka ta kur6eshi dukanshi, kafin ta rarumi roasted chicken takai baki tana cizgarta atsiyace, daɗina da hajiya saratu damuwa bata hanata cin abincin, adai dai lokacin da ta ɗauki burger da hannu biyu ta gutsireta da baki, Muryar pravin ta dakatar da ita daka taunar burger din da takeyi, lokaci guda yanayin fuskarta ya canza ta haɗe rai kamar baƙin haɗari. shigowa ɗakin yayi fuskarshi ɗauke da murmushi, yasan tsiyar daya tsula mata shiyasa yake jin shakkar tunkararta Daga nesa da ita ya tsaya haɗi da goya hannayenshi on his chest cikin muryar lallashi ya furta”My wife, ina neman afwarki, dan Allah ki yafe min nasan ban kyauta maki ba, duk da ba laifina bane, laifin ki ne saboda kece kikaja nayi maki hakan, kin nuna bani da mahimmanci awurinki...” kau da idonta tayi daga kallon fuskarshi, taci gaba da cin burger dinta ta share shi kamar batasan da zaman shi ba. “Dan Allah kiyi min magana sanyin idaniyata, kamar yadda na 6ata maki rai nima haka raina ya 6aci, saboda tunanin awani hali kika kwana jiya ko runtsawa banyi ba, nayi kewar rashinki atare dani, da pillow na kwana rungume a kirjina ina jin tamkar kece na rungume” fuskarshi ɗauke da matsananciyar damuwa yayi mata maganar, duk don ya samu ta yafe mashi, burinshi ta aminta dashi su sasanta tsakanin su, duk don ya tunzurata akan maganar macijin daya tsoratar da ita jiya, yasan muddin saratu ta ƙyamaci zaman yaron a estate dinsu dole kowa ya amince saboda ƙaunar da yayyanta su ke yi mata. “Bugun zuciyata, please ki kula ni mana, bana son sharenin da kike yi, wallahi ashirye nake dana kar6i duk wani horo da zaki bani ni kawai so nake mu sasanta tsakaninmu bana so kina fushi dashi” ƙara ɗaure mashi fuska tayi batare data juya ta dube shi ba. Zuƙunna pravin yayi, tare da kama kunnansa Ya soma yin tsallan kwaɗi Yana nufar gaban table dinta Yana fadin”Am sorry my wife, nagane kuskurena bazan ƙara ba” Tunkafin Ya ƙaraso gabanta, ta tsiyaya ruwan lemu acikin cup mai sanyi, ta ruƙe a hannunta, Yana zuwa dab da table din ta daddage ta watsa mashi ruwan lemun saman fuskarshi, da sauri ya runtse idanuwanshi jin raɗaɗin da ya shigar mashi, burger ta ɗauka ta yunƙura ta kifa mashi ita a fuskarshi, tunda tayi mashi hakan sai taji sauƙi acikin ranta, komawa tayi ta zauna tana dubanshi tace”Ina fata ka tashi lafiya” shiru pravin bai furta komai ba, ƙoƙarin buɗe idanuwanshi yake yi sai dai ya kasa, shu’umin murmushi hajiya saratu tasakar mashi tare da cewa”malam, ka tashi ka shiga toilet ka wanke fuskarka,” babu musu pravin ya miƙe kamar makaho Yana laluban hanya daƙyar ya gano ƙofar toilet......” *✊💋ALHAMDULILLAH, END OF MIDDLE STEP, FATA NA SHINE ALLAH YA BANI IKON KAMMALA TAKUN ƘARSHE LAFIYA KAMAR YADDA NA KAMMALA TAKUN FARKO DA TAKUN TSAKITA💋✊* (Domin neman ƙarin bayani a tuntu6i layukan mu (08103884440 0r 08169856268)