[1/3, 6:34 AM] Abue Saleh AlQuyraemey: *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* _Ga duk maison karanta littafin Abban sojoji,zai biya 300 ne,za'a tura mashi tundaga farko har inda muka tsaya,kuma zai cigaba da samun update dinshi akai akai,ga wanda ke buƙata zai tura mun message ta whatsapp ɗina (08103884440) kada ku bari abaku labari sannan a kula wannan itace numbar wayata,Wasu suna ɗaukar numbar Wanda suka bani tallarsu kayansu suna kiransu a matsayin ni,bayan ni ga numbar dana bada nan itace numberta_ *Nagode sosai da addu'o'inku agare ni,da kuma uzurin da kukayimun,har zuwa wannan lokacin,Allah yabar zumunci a tsakaninmu daga nan har gidan aljanna💃* *nace ba Masu satar littafi suna fitarwa ta bayan fage,mai yasa baku ƙarasa masu labarin ba?kuma kenan saida kuka jira ni?ae nayi tunanin cewa zaku ƙarasa masu labarin ne ashe dai sai anjira Boss*😂🤣😅 Bismillah Kai tsaye sautin ringing ɗin wayar ya daki dodon kunnan Aunty babba dake baje saman gadonsu tana Bacci,a lokacin ko yatsanta bata jin xata iya motsawa saboda baccin dake a idanunta,yatsina fuska tayi alamar an takura mata,    Ishaq dake tsaye agaban mirror yana gyara jikinshi ya ɗan gyara murya tare da cewa"Madam ki daure ki tashi ki ɗaga kiran nan!da alama kira ne mai muhimmanci tun ɗazu wayar ke ta ringing,"   Uban tsoki Aunty babba ta buga tare da yunƙurawa daƙyar ta tashi daga zaune,jikinta na sanye da sleeping dress,riga da wando purple colour,   Fuskar nan tayi suntum kamar wadda aka nausa,hannu takai tare da ɗaukar wayar dake ajiye saman bedside drawer,duba screen ɗin wayar tayi ganin sunan Hayaam ya bayyana yasa ta ƙara tamke fuska kamar ta shanu,ɗaga kiran tayi tare da kara wayar a kunnanta,rai a6ace tace"Meyasa kika kirani fitsararra!ko kin kira ne don ki ƙarasa yimun rashin kunyar taki don ubanki,"   on the other hand hayam tace"haba aunty laila,ni harna manta da abunda ya faru atsakanin mu.....'tunkan hayaam ta ƙarasa maganar Aunty babba ta katse mata hanzarinta da cewa"Idan kin manta ae ni ban manta ba,Ki faɗamun uban miyasa kika kira ni,idan ba haka ba ni zan kashe wayar,   Zuba mata ido Ishaq yayi yana kallonta aransa yace"Zagi kamar ƴar maguzawa,ko kunyata bata ji,sae faman ɗura ashar take yi,ni dae Allah ya haɗani da Guyaba,'      cike da damuwa hayaam ta sassauta muryarta,tare da cewa"Aunty laila,na shiga uku,ko ince mun shiga uku,Akwai gagarumar matsala,Gaba daya duk wani plan ɗinmu ya tashi aiki,'   Tunda Aunty babba taji hakan,gabanta ya faɗi rasss,ƙasa ƙasa da murya tayi tace"Hayaam meya faru?wata irin matsala kike magana akai?   "Aunty laila,Ashe yarinyar nan mai aikin gidansu,ɗiyar uncle ɗinsu ce Abusufyan!!!!!" tamkar saukar aradu haka aunty babba taji maganar Hayaam aikuwa a matuƙar gigice ta miƙe tsaye tana cewa   "kutumar uba!inji ubanwa!yaushe Abusufyan ya ta6a aure,Wlh ƙaryane koma wani ɗan ƙaniyar ne ya faɗi maki hakan babban maƙaryaci ne....'   Gaba daya hankalin ishaq ya dawo kanta,maganar dayaji tana fadi ta tsaya mashi aranshi,    "Wani abusufyan din kuke magana akai,"   Firgit Aunty babba tayi tare da ware ido tana kallonshi sam ta manta da cewar yana acikin ɗakin,   Hankali a matuƙar tashe ta miƙe tsaye da nufin ta fuce daga cikin ɗakin,Saboda tsabar ruɗu ta nufi hanyar shiga toilet,   gyaran murya ishaq yayi mata tare da cewa"kada fa ki shiga toilet da waya a kunnanki,'   A zabure ta juya ta kuma nufi wardrobe da alama ruɗu yasa ta manta hanyar fita daga ɗakin,zuba mata ido yayi yana mai mamakin irin kiɗimar da tayi,to ko lafiya?ya tambayi kansa,    Bata ankara ba sae da goshinta ya bugi jikin wardrobe din kayan nasu,sannan ta gane inda ta dosa,Rai a6ace ta kama hanya ta fuce daga dakin,saukowa downstairs tayi ta miƙi hanyar wannan tsohon store ɗin data ta6a garƙame su hosana aciki,anan corridor ɗin ta tsaya tana sauraran Hayaam,   "Wlh Aunty laila da gaske ne,Ni shaidace,Naji komai lokacin da Uncle ɗin nasu yake korama junaid bayani,bama haka ba Aunty azmee da kanta ta gasgata mun hakan,Babban abunda yafi rikitar dani Yaran fa triplet ne ashe,kuma dukkansu Mata ne kyawawan gaske,kamannin su sak iri ɗaya,Kuma kina kallonsu zaki gane cewa ƴa'ƴanshi ne......'   Hannu ɗaya Aunty babba tasa ta dafe tsakiyar kanta,yayin da dayan hannun ke ruƙe da wayarta data kara a kunnanta,   "Hayaam bazan ta6a yarda da zancenki ba,Taya hakan ma zata faru!mutumin da bai ta6a yin aure ba,Shi za'ace yana da ƴa'ƴa har ƴan uku!Cikin shege kenan ya ta6a yima wata harya same su!Ni ban yarda da kalamanki ba,Hayaam kinsan cewa babu kyau tsoratar da musulmi,Idan wasa kike mun ki daina!!!!! 6acin raine yasa hayaam ta kashe wayar   Fashewa da kuka tayi saboda ƙululun baƙin cikin daya tokare mata maƙoshinta,ga zuciyarta dake ta faman tafarfasa,Gaba daya bata jin daɗin jikinta,   Zubama wayar ido Aunty babba tayi tana kallonta,   Tsoki taja tana jinjina kai tace"dama saida raina ya bani cewa ƙarya take yi mun,tayi mun hakan ne saboda ta tsoratar dani don in saukko,Shashasha kawai,     "Mommy kin farka kenan" Muryar hafsat ce ta katse mata zancen zucin nata,   Juyowa tayi tana kallonta,atsaye take fuskar nan ɗauke da murmushi jikinta na sanye da riga da wando na jeans,ta ɗaure sumar kanta da ribbom,yayin da hannunta ke ruƙe da Cup mai ɗauke da Tea mai zafi sai faman tiriri yake yi,   Tunda Aunty babba taga hafsat na murmushi tasan cewa akwai matsala,hakanan dae ba zakaga fuskar hafsat da murmushi ba tunda farar safiya,   ƙaƙalo murmushin yaƙe Aunty babba tayi tare da cewa"Lafiya naga kina murmushi"?   "Lafiya lou mommy,kawai wani abun farin ciki ne ya faru,nasan cewa muddin kema kika ji,zaki yi farin ciki sosai,'   Murya asanyaye aunty babba tace"Faɗamun daughter har na ƙosa naji wannan abun farin cikin?halan an ƙara maku albashi ne?ko matsayi aka ƙara maki wurin aiki"?   Dariya hafsat tayi tana girgiza kai tace"Mommy baki canka dai dai ba,wannan albishir ɗin da nakeso inyi maki yafi ƙarfin duk waɗannan abubuwan da kika lissafo,kar6i tea ɗin nan ki fara korawa kafin na faɗa maki,"   Hannunta na kerma ta kar6i kofin da hafsat take miƙa mata,a hankali takai cup din bakinta ta kur6i Tea ɗin,kusan sau uku tana kur6arsa,kafin ta ɗan jinkirta bayan ta janye kofin daga bakinta tace"daughter dan Allah ki faɗamun wannan wani abun farin ciki ne!wlh duk na ƙosa naji,'   "Zan faɗa maki mommy amma mu shiga daga cikin palour mu zauna,'   "Ba inda zanje,idan zaki faɗamun ki faɗamun kawai,Sae ja mun rai kikeyi," tayi maganar tana faman tamke fuska,   Hafsat tace"bada jimawa ba,Na kira Aunty azeema,don in gaishe da ita,Anan take sanar dani cewa ƴa'ƴan uncle abusufyan Sun bayyana...!   Tunkan ta ƙarasa maganar a gigice Aunty babba ta saki kofin dake hannunta,Ya tarwatse ƙasa,Ruwan tean dake ciki ya fallatsar masu a ƙafa,   ja da baya hafsat ta ɗanyi tana kallonta tace"haba mommy,so kike ki ƙonamin ƙafa ta,daga faɗin abun farin ciki?   Rai amatuƙar 6ace tace"Ki 6ace mun da gani sakarya kawai,Maƙaryatan banza,bazan ta6a yadda da kalamanku ba,duk bakinku ɗaya da Hayaam,' Ta faɗi hakan tare da kama hanya fuuuuu kamar zata tashi sama,ranta duk a jagule,bin bayanta hafsat tayi da kallo harta haye upstairs,ta6e baki tayi tare da watsa hannayenta tace"I don't care, Ni dae farin ciki nakeyi,Daddy ma nake jira in tambayeshi yaushe zamu je gidan saboda a qagare nake dana ga ƴa'ƴan uncle ɗinmu Abusufyan,tunkan na gansu har naji ina sonsu sosai,in ma na tashi tafiya hada tsaraba zan tafin masu dashi,'   Cike da farin ciki hafsat take maganar,zuƙunnawa tayi tana tattare kofin da aunty babba ta fasa, Lokacin da Aunty babba ta ƙarasa bedroom ɗin nasu,har ta ɗaga ƙafarta zata zura acikin ɗakin taji muryar ishaq yana cewa"Alhamdulillah!Alhamdulillah!Alhamdulillah!Abba nayi farin ciki sosai,Meyasa tun jiya ba'a sanar dani ba,ae da tunda sanyin safiya zanyi maku dirarr mikiya,Amma ina taya uncle murnar ganin ƴa'ƴanshi,kuma ina tayamu murnar samuwar ƴan uku acikin zuri'ar mu,gaskiya bazan ma iya jurewa ba,Zan shirya nazo ne kawai,saboda na qosa naga ƴan ukun mu bayin Allah....       Abba yace"wani abun ma sai kayi tozali da yaran,kyawawan ƴan mata dasu,Yadda kasan photo copy ɗin abusufyan haka suke,kamanninsu sak iri ɗaya da nashi,'   Murmushi Ishaq yayi tamkar yana agabanshi yace"Abba kafin na ƙaraso,dan Allah a isar musu da saƙon gaisuwata,Ace yayansu General ishaq yana gaishe su sosai da sosai,kuma saboda suma zaiyi zuwa na musamman,'   "Insha Allah zan sanar masu yanzun nan,Allah ya kawoka lfy,"   "Ameen Abbana," Sun jima suna waya kafin sukayi sallama ishaq ya ajiye wayar,   tashin hankalin da ba'a sama shi date!!!!!!!   Magana dae ta tabbata da gaske ne zancen da hayaam da hafsat suka faɗa mata,Tabɗijancan,   Dakyar ta iya shiga cikin ɗakin,lokaci guda ta rasa kuzarin jikinta kamar wadda tayi Zazza6i na sati ɗaya,   Jin takun tafiyarta yasa ishaq juyawa yana kallonta fuskarshi a washe har ya kammala shiryawa cikin haɗaɗɗiyar shadda,   Ganin yana ƙoƙarin buɗe baki yayi mata magana yasa tayi saurin katse shi da cewa"Naji abunda ya faru,Hafsat ta sanar dani komai,ina tayaku murna,'ko amsar shi bata tsaya ji ba,ta faɗa cikin toilet,   Tana juyo muryarshi daga cikin bedroom ɗin yana cewa"Ni yanzu zan wuce Abuja ne,inyaso kun biyo ni daga baya ko zuwa gobe ko jibi haka,duk dae yanda kuka yanke shawara keda hafsat,   daga cikin toilet tace"Allah ya sauke ka lpy,in anje agaishe mana da mutanen gidan,"    "zasuji insha Allah," ya amsa mata tare da kama hanyar fita daga ɗakin. ❤🤍❤ Acan 6angaren kuwa har lokacin suna a falon kan junaid da Uncle abusufyan ya gama fahimtar dashi game da Su Hosana da jahad, jiki asanyaye yace"Amma meyasa su ba suyi rayuwa atare damu ba?meyasa Abba?uncle why?cike da tuhuma yake maganar yana kallonsu,yayin da fuskarshi ke ɗauke da damuwa, abban su ne yace"Junaid,mu kanmu bamu san dasu ba,da ace munsan da zamansu da bamu bari hakan ya faru ba,ƙaddara ce kawai ta riga fata,"   Shiru junaid ya ɗanyi yana ƙare ma su Jahad kallo,yaso ace tun fil azal tare da yaran ya taso,da ba ƙaramin kulawa zasu samu a wurin ƴan uwansu ba,Allah sarki rayuwa kenan,Rashin sani yafi dare duhu,su kansu su Sehrish sae dama dama suke da sun san cewa suna da wannan family ɗin daba abunda zai hana su nemi danginsu,Tabbas an cuci rayuwarsu ƙiri ƙiri an rabasu da Ubansu kuma an hanasu danginsu,wata shari'ar dae sae a lahira, "Nasan yanzu kowa yana jin yunwa,saboda halin da muka shiga jiya babu wanda ya samu damar cin abinci acikin mu,Yakamata yanzu komai ya wuce,Lokacin farin ciki ne,Za'a shirya gagarumar walima saboda ƴan ukun mu,munaso su manta da duk wani abu da ya faru a rayuwarsu kuma su ƙaddara cewa tamkar yau ne suka faɗo duniya,ko ba haka ba"? Ya yi maganar yana kallon matasan gidan dake atsaye,Kowannansu fuskarshi asake,su fawan ne suka haɗa baki wurin cewa"Wannan haka yake Abba,In sha Allah zamu nuna masu soyayyar ƴan uwantaka,har sai sun manta da dukkan wani ƙunci da suka fuskanta na rayuwarsu,' murmushi kawai Abusufyan ke saki don ba ƙaramin daɗi yaji ba, Marshal Omar yace "Sannan kuma muna ƙara baku haƙuri game da halin da kuka tsinci kanku,duk da ba laifin mu bane,amma mun ɗaura ma kanmu laifin,Muna neman afwarku,Hosana Sehrish and Jahad,forgive us pls,'   gaba ɗaya jikinsu yayi sanyi,lokaci guda kuma sukaji wata irin soyayyar ƴan uwansu ta kamasu, Jahad ce tayi ƙoƙarin cewa"duk wani abu daya faru damu dama can rubutaccen ne!Allah ya riga da ya ƙaddara faruwan hakan,mun gode ma Allah da muka cinye wannan jarabawar,da juriya kuma da haƙuri,yanzu gashi gaba ɗayanmu muna farin cikin wannan rana da Allah ya haɗamu da danginmu,Babban abun farin cikin ma da ya kasance Uncle abusufyan shine mahaifinmu ba waccen fasiƙin mutumin ba.......'kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan daya zo mata,Janyota Abusufyan yayi tare da rungumeta ajikinshi,yana ɗan bubbuga bayanta,   "Ya Omar," hosana ce ta ambaci sunan shi,tana faman kumshe dariya abakinta,gaba ɗaya suka mayar da hankalinsu akanta,nuna shi tayi da yatsanta sannan ta nuna kanta,kafin ta haɗe yatsun wuri guda ta ƙullasu,Alamar ita dashi sun zama  ƴan uwan juna, ƙayataccen murmushi Marshal ya saki yana kallonta, Duk wannan abun dake wakana akan idon Sgr dake atsaye,ya goya hannayenshi asaman wide chest ɗinsa,Har lokacin bai sauko ba,hankalinsa fa bazai kwanta ba har sai yayi tozali da YA SAYYADI, Suna cikin magana muryar azmee ta katse su da cewa"Abba an kammala shirya breakfast ɗin,yakamata ku hallara a dining ɗin," tana magana idonta na akan su jahad fuskar nan ɗauke da murmushi,    Batare da 6ata lokaci ba,gaba ɗayansu suka hallara asaman zungureran dining table ɗin wanda ke shake cike tab maƙil da kayan makwalashe naci dana sha,mutun goma shabiyu yake ɗauka,akwai kuma wanda Abban su junaid yasa aka ƙara cikin wanda aka shirya walimar jiya dasu,Ansanya shi a gefen nasu mai mazaunin mutun shida,Aunty azmee ta jera wasu kayan kalacin asaman shi,anan Abusufyan ya zauna tare da su sehrish jahad da hosana, Tun daga kan yadda kowa ke zuba abinci acikinshi zai tabbatar maka da cewar ba ƙaramar yunwa suke ji ba,ko azmee basu jiya tayi serving ɗinsu ba suka shiga zuba abincin da kansu,Sgr ne kawai tayi serving ɗinsa sae kuma Abbansu,amma sauran ba wanda ya tsaya jira,wurin yayi tsit bakajin hayaniyar komai,sai sautin Cokulla,kwas kwas kwakwasss, ɗagowa Marshal omar yayi karaf idonshi yaci karo dana hosana,ta zuba mashi ido ko kyaftawa batayi,kasancewar table ɗinsu na kusa dana juna,tazarar kadan ce,   Da cokalin hannunshi yayi mata nuni da plate din gabanta,alamar ta mayar da hankalinta kan abunda take ci,   murmushi tayi tare da kai hannu ta dauki lemu tana korawa,   Junaid kuwa duk ya rasa samun natsuwa sam ya gaza cin abincin dake a gabanshi sae faman juya cokalin yake yi acikin plate,duk in ya tuna abunda yayi ma Jahad acikin mota amatsayin Sehrish sai yaji gabanshi ya faɗi rass,fargabar shi kada jahad tayi tunanin ko ɗan iska ne shi,tunda ba sanin shi tayi ba,kar kuma tace zata sanar ma wani abunda yayi mata,tunawa yayi da lokacin daya tsoma harshenshi acikin bakinta ya ƙanƙameta yana kissing lips ɗinta,ba iya nan ba ya tsaya har hannunshi saida ya zura ackin hijabinta   Hankali tashe junaid ya miƙe yana ƙoƙarin barin dining ɗin,hankalin kowa ya koma kanshi,   Har suna haɗa baki wurin tambayar shi ina zashi,   fuskarshi ɗauke da damuwa yace"Abba,bana jin yunwa,dama munyi breakfast tare da Mommy,zanje wurinta yanzu" Abbansu yake ma magana amma hankalinshi na akan Jahad dake shan farfesun da azmee ta zuba mata a plate,da alama ba ƙaramin daɗi farfesun yayi mata ba,duba da yadda ta mayar da hankali akanshi,   "Okey,zaka iya tafiya," ya bashi amsa,cikin sauri junaid ya kama hanyar zuwa bedroom ɗin Abbansu don acan ta sauka,yana tafiya yana waiwayen su jahad aranshi yana cewa"wayyo Allah na,bansan me zai biyo baya ba,nasan cewa dole ta sanar ma Uncle abunda nayi mata,idan ta faɗa mashi shi kuma zai faɗa ma Abban mu ne,Abban mu kuma zai faɗa ma Babban yayanmu ne,shi kuma zaice wuyana ya isa yanka tunda har na iya Sumbatar mace daga nan zaiyi tunanin turani aikin Soja abunda banso,shikenan tawa ta ƙare'   ranta ne ya bata cewar ana kallonta,hakan yasa ta tsagaita daga shan farfesun da takeyi,ta ɗan ɗago idanunta,kai tsaye suka sauka akan junaid dake can nesa dasu yana kallonsu, Mamaki ne ya kamata ganin yadda ya ƙura mata ido yana kallonta,aranta tace"bansan meyasa yake kallona ba,tsorana kar ace baisan ganina ne,'   "Allah yasa halinta irin na Sehrish ne,idan takasance mai sauƙin kai irin na rishi ɗina nasan cewa zata rufa mun asiri,amma anya zatayi sauƙin kai?Nasan me zanyi daga yanzu zan dinga ɗaure mata fuska,in nuna kamar na tsane ta,nasan hakan ne kawai zaisa taji tsorona taƙi faɗa masu abunda ya faru atsakaninmu!good idea",   Yana kai ƙarshen zancen zucin nashi ya watsa mata harara tare da murguɗa mata baki,ya juya ya nufi bedroom ɗin abbansu,    Jiki asanyaye jahad ta ɗauke idanunta daga kallon bayanshi da take yi,lokaci guda taji komai ya fita ranta ba don komai ba sai don kallon da taga junaid yayi mata,maganarta ta tabbata,Junaid baison ganinta,tunda gashi ya harare ta kuma hada murguɗa mata baki,   Muryar daddynsu ce ta katse ta da cewa"Jahad,meya faru ne?naga kin daina shan farfesun ina fata lafiya?   firgit ta ɗanyi tare da wurga eye balls ɗinta akanshi tace"Am ok daddy,'   jinjina kansa yayi kafin yace"Ku saki jikinku,kuci abinci sosai,kada kuji komai,nasan baku saba ba,don na lura akwai rashin sabo atattare daku,amma a hankali zaku saba da ƴan uwanku,'   hosana tace"Abba ae ni,nama saba da kowa,baka ga yadda nake ta cika cikina da abinci ba,jahad ce ke jin kunya,ni bana jin kunyar kowa,'   Dariya sukayi gaba ɗayansu,Sehrish na cikin sakin dariyar nan,Karaf idanunta suka haɗu dana Sgr,ɗagowar shi kenan yayi arba da ita,gabanta ne taji ya faɗi rass saboda fuskarshi a murtuke take ba annuri,nan take dariyar da takeyi ta koma ciki,ganin ta zuba mashi ido,yasa shi jefa mata harara,a hanzarce ta kawar da idanunta daga kallon fuskarshi da take yi,jikinta kuma yayi sanyi,ta shiga tambayar kanta dalilin hararar da taga big bro yayi mata,kodai baya farin ciki ne da kasancewarta JININ SA!?tabbas hakan zai iya faruwa,Wataƙil kodan ya saba ganinta a matsayin ƴar aikinsa,baiwarsa,ƙasƙantacciya shiyasa yanzu Yake nuna 6acin ranshi don yana ganinta tamkar a matsayi ɗaya suke dashi,Ƴa'ƴan Wa da ƙani,da alama hakan baiyi masa ba, "Idan har dagaske ne abunda nake hasashe,insha Allah zan tattara na bar masu gidan,saboda bana son 6acin ranshi,zan iya yin komai don farin cikin shi," ta ƙarasa zancen zucin nata tare da sake ɗagowa a hankali don ta saci kallonshi,adai dai lokacin shima ya ƙara ɗagowa da kyawawan idanuwanshi kai tsaye suka shiga cikin nata,nan take taji gabanta ya kuma faɗuwa rass,kasa janye idanuwanshi yayi daga kallonta da yake yi,a yayin da yake jujjuya spoon ɗin dake hannunsa acikin plate ɗin abincin gabansa,har Yanzu bai daina mamakin kasantuwarta ƴar uwarshi ba,ta jininsa,tamkar a mafarki haka yake ganin abun,ganin ta zuba mashi ido batare da ta janyesu ba yasa shi ɗaure fuskarshi yasha murrr,saboda kada ma yarinya taga fuska har tayi tunanin raina sa don tasamu matsayi,    "U will still remain who u are,wadda take aiki a ƙarƙashina,Matsayin dana baki kenan,"ya fada a ransa   Murmushi Abusufyan yayi tare da cewa"bazasu kara wahala ba,bazan ta6a bari hakan ya faru ba,tunda dae har yaran nan suka bayyana a matsayin ƴa'ƴana,In sha Allah bazan ƙara bari suyi aikin wahala ba,ko cokali bazan ƙara bari ɗaya daga cikinsu ta ɗauko ba acikin gidan nan,rayuwar hutu kawai nake so suyi rayuwar ƴanci," ya ƙarasa zancen zucin nashi a yayin da yake bin kowaccen su da kallo cike da so da ƙaunar ƴa'ƴan nashi,'   Janye idanunshi yayi daga kan nata,kafin ya miƙa hannu tare da ɗaukar Glass cup mai ɗauke da abun sha me sanyi ya kai shi saitin mouth dinsa yana sipping ɗinshi anatse,yayin da sanyin lemun ke ratsa throat ɗinsa,a hankali ya lumshe idanunsa tare da ɗan ware su kaɗan,again suka ƙara sauka akan na sehrish a karo na uku kenan,agaggauce tayi hanzarin janye idanunta daga kan fuskarshi ta mayar dasu akan plate ɗin abincin dake a gabanta, Hannu Sgr ya sanya tare da yago tissue ya goge bakinsa,kafin ya miƙe tare da juyawa ya nufi upstairs,Miƙewa Marshal yayi da alama shima ya kammala breakfast Ɗin nasa,shima upstairs ya nufa, Fitowar Hajiya azeema keda wuya daga cikin bedroon ɗinta,ta jiyo muryar gwaggon katsina tana ta faman sambatu tana cewa"Tsiyarta kenan mutun yazo gidan ƴan gayu,Ni bazan iya rayuwar turawan nan ba,taya za akai ma mutun salalar biredi tare da tea rabin kofi kamar wata ƴar iska ace in sha"?   Tafiya take tana sambatu zaninta a hannu sai ɗan undi ajikinta,kanta kuwa ta kifa wannan ɗaurin ɗan kwalin nata mai kama da helmert,   har zata gifta hajiya azeema tayi gyaran murya tare da ambaton sunanta"Goggo," fuska a yamutse ta juyo tana kallonta,dawowa tayi daga gefenta suna fuskantar juna tace"Yawwa azeema,wai nikam inaso in tambayeki,' Natsuwa hajiya azeema tayi tare da cewa"ina sauraronki gwaggo,"   "Jiya nayi wani mafarki,ƴa'ƴan abusufyan sun bayyana,wasu ƴan uku kyawawan gaske,da nayi tunanin koda gaske ne abun ya faru amma daga baya na gane ba gaskiya bane,in ba haka ba,yaushe abusufyan ya ta6a yin aure"? Tayi tambayar tana kallon hajiya azeema,wadda ta saki baki tana kallon gwaggon,   Ganin azeema tayi sototo tana kallonta yasa tayi tunanin cewa ko abunda ta faɗa ya bata mata rai ne,   "Nasan dole kiyi mamaki kema,Mafarkin fa kamar dagaske,ɗaya daga cikinsu har tana sharara mana labarin ƙarya waisu ƴa'ƴan wata zainabu ne,kuma ma acikin labarin hada wata hajiya Ameena,in banda shaiɗan ina abusufyan ina ƴa'ƴa"?   Ƙiris ya rage Azeema ta fashe da dariya agaban gwaggon katsina,ganin yadda ta haƙiƙance tana kora mata bayani,kuma babu alamun wasa a fuskarta, Ƙunshe dariyar bakinta tayi tare da basar da ita tace"Gwaggo Anya kina shan maganinki kuwa?ina Dr harris yake?gaskiya inason ganinshi,'   Tsoki gwaggon katsina taja tare da cewa"Harrisun daya zama ɗan iska," Waro ido waje azeema tayi tace"gwaggo harris ne ɗan iska"?   ta6e baki tayi tare da cewa"Zan masa ƙarya ne?ba ɗan cikina bane"?nasha wahalar yima yarona tarbiya amma waccen sauden.....'kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan daya ciyota,zanin hannunta takai saitin idonta tana ƙoƙarin goge hawayenta,   Zuru harris yayi wanda fitowarshi kenan kuma atare da saude suka fito,jin maganar gwaggone ma yasa yayi hanzarin cire hannunshi daga cikin na sauden,   Hajiya azeema tace"gwaggo faɗamun me harris ɗin ya akaita,?   Hankali tashe Saude tace"ya harris pls kada ka bari gwaggo ta faɗa mata abunda muka aikata,kasan gwaggo yadda take ɗaukaka abu,inta tashi faɗi saita ƙara ma miya gishiri,'   Dr harris yace"just don't worry ur self,insha Allah bazata faɗa mata ba," Faɗin hakan keda wuya gwaggon Katsina tace"Azeema abun da ciwo,yanzu yunwa nake ji,shiyasa ma kika ga nafito ina sambatu,Wurin waccen matar zani,wlh ba azmee ba Allah yasa ramadan ce ita yau saina zazzaga mata rashin mutunci!Ni zata raina ma hankali tunda safe,takawo mun tea rabin kofi da salalar biredi wai in fara da wannan,don ta raina mun hankali,nayi mata kama da kusu ne?   Rai a6ace tayi maganar,aikuwa atare haris da saude suka fashe da dariya,a hanzarce ta juyo sakamakon jin sautin dariyar tasu,nan take ta tsuke fuska ganin shi tare da saude,   Murmushi Hajiya azeema tayi tare da cewa"haba gwaggo baki fahimce ta bane,cewa fa tayi ki fara da wannan tana nufin kafin ki tashi fitowa zuwa yin breakfast ɗin,yanzu haka yana can an shirya mana mu kawai ake jira muje muci namu kalacin,"   Hajiya azeema ta ƙarasa maganar tare da ruƙo zanin hannun gwaggon tace"Bari na taimaka maki ki ɗaura shi,"   Girgiza kai tayi tare da cewa"Barmin shi a hannuna,nafison inji iska na shiga ta ko'ina,"murmushi hajiya azeema tayi kafin tace"hakan ma yayi gwaggo,ae under skirt din ma bamai sharashara bane,yana da kauri,amma duk da haka dae ki ɗaura zanin yadda zaki fito da kyau tunda ga rigarshi kin sanya ajikinki,Kuma kinga Abusufyan na nan,Ga kuma ƴa'ƴansa,bazasu so suga gwaggonsu a haka ba,"   wani irin ƙayataccen murmushi gwaggon katsina tasaki tare da cewa"Kenan dagaske ne Mafarkin da nayi jiya"?   Jinjina kai Azeema tayi tace"Ae suna nan,duk abunda ya faru jiya dagaske ne,ba mafarki kikayi ba,agabanki akayi komai kin dai shafa'a ne,'   Jin haka yasa tayi saurin mayar da zanin ajikinta tana ɗaure shi tana cewa"Allah sarki ƴa'ƴan abusufyan ɗina,bayin Allah,sunsha wahala a hannun wannan fasiƙin mutumin baƙin shaiɗani,Allah mutumin nan ƙaho ne kawai bai fito masa aka ba,amma ina tantama anya ba Irin shaiɗan bane"?    "gwaggo kidaina maganarsa ma,Ni wlh ko zancen shi ma bana so anayi,Na tsani mutumin nan kamar yadda natsani mutuwa ta,"acewar hajiya azeema,tayi maganar ne a yayin da take kama hanyar Zuwa Dining area ɗin nasu,bin bayanta Gwaggon tayi tana cewa"Ae ko sai dai ki toshe kunnanki,don zancen sayyadi ya zama dole,in har ba'a kawo min kansa ba,bazan daina faɗan sunan shi ba,'   Murmushi kawai hajiya azeema tayi,atare suka ƙarasa dining area din,    Gaggaisawa suka fara yi da junansu,su jahad na ganin saude suka tashi atare suka nufe ta,dama Jiya basu samu damar gaisawa da ita ba,saboda yanayin da suka shiga gaba ɗayansu,haɗasu tayi ta rungume ajikinta,cike da farin ciki tace"Ina tayaku murna sosai,nayi farin ciki sosai,Ya harris ya sanar dani komai agame daku,ashe ku jininsu ne,'ta ƙarasa maganar ayayin da take raba jikinta daga nasu,kowannansu fuskarshi ɗauke da murmushi,Jahad tace"Aunty saude kinga ikon Allah ko?munsha wahala sosai,mu kanmu bamu ta6a tunanin cewa muna da dangi ba,amma sai gashi ƙaddara ta haɗamu da ya Omar,Ita kuma ƴar uwarmu Sehrish ƙaddarar aikine ya kawota gidan nan,Muna tare da ƴan uwanmu ba tare da mun sani ba,sae gashi rana ɗaya Allah ya bayyana mana komai,'   Saude tace"Congratulations Once again,ina ƙara tayaku murna sosai da kuka fito daga tsatson wannan Family ɗin,abun alfahari ne wannan"kafin ta mayar da idanunta kan Hosana,Cike da zolaya taja kumatunta tare da cewa"Hosana Kinga yadda kika canza?kamar ba wannan Sha takwas sha taran ba,mai ɗan kai,kinyi kumatu kamar Balon balon,Ga haske gaskiya ya Omar ya Iya raino," Fashewa da dariya hosana tayi tana faman sunnar dakai, "Kiyi ma sister ɗinku mana,Ita bazata taso mu gaisa ba"?tayi maganar tana kallon sehrish dake zaune,tana faman kallonsu ɗaya bayan ɗaya, Murmushi jahad tayi tare da juyawa tayi mata alamar ta taso da hannunta, Miƙewa sehrish tayi tare da nufar inda suke,koda ta ƙaraso saude ta sanya hannu tare da janyota ta rungumeta,kafin ta raba jikinta dana sehrish tace"Masha Allah,gaskiya ban ta6a ganin triplet,masu kama iri ɗaya sak kamar taku ba,ina taya ki murna sosai da Allah ya haɗaki da ƴan uwanki,da kuma mahaifinku,da kuma danginku,' Fuskar sehrish ɗauke da murmushi tace"Ngde sosai," "Allah ya tsare mana ku,Ya Albarkaci rayuwarku ya kuma kare ku daga sharrin maƙiya,' Atare suka amsa mata da Ameen,bama su kadae ba,hadasu Abba dake sauraron maganganun nasu, Kamar yadda Abba yayi alƙawarin shirya gagarumar walima na bayyanar ƴa'ƴan ƙaninsa Abusufyan,Da kanshi ya fidda date ɗin da za'a gabatar da ita,Kuma tun aranar ya fara kiran Ƴan uwa da abokanan arziƙi yana sanar dasu game da ƴa'ƴan abusufyan da suka bayyana,Babu wanda bai bari ba,kowa kira yake tun daga kan danginsu na Zaria,na damaturu dana sauran states ɗin da kuma waɗanda ke zaune Ƙasashen waje,kowa saidaya sanar mawa,Bayan Abbas ya koma gidane da safe Amani ke tambayarshi meya faru ne jiya ya hanasu zuwa gidansu,Anan ya kwashe duka abunda ya faru game da su Sehrish ya sanar mata,wani irin farin ciki ne ya cika ta,Ba don komai ba sai don sanin cewa plan ɗin Aunty babba ya gama Tarwatsewa,ae tunda taji cewar ƴan mata ne kuma sun kai shekara goma sha bakwai zuwa sha takwas kyawawan gaske,Nan fa ta kwashe da dariyar mugunta aranta tana cewa Naga yadda za'ae Aunty laila ta cimma burinta,Gida bai ƙoshi ba taya za'a ba na waje,Ae tuwona maina za'ayi,Haba ae xance ya ƙare, ita kanta Amani ta ƙosa ranar walimar tazo saboda suje gidan,saboda taji cewar Aranar Aunty babba da hafsat zasu zo Abuja,babban burinta taga tashin hankalin da aunty babba zata fuskanta inta gansu, Ranar walimar kuma yayi dai dai da ranar da Ammi zata zo,tare da wasu daga cikin danginsu,haka zalika captain Najeeb da kuma Talal suma duk a ranar zasu dawo gida,ba don komai ba sai don su sanya ƴa'ƴan uncle ɗinsu abusufyan acikin idanunsu,Kowa ɗokin ganinsu yake yi kamar kamar me,musamman da sukaji irin rayuwar da yaran sukayi a wulaƙance sai suji wani irin tausayinsu da kuma ƙaunarsu ya shiga cikin ransu,kuma duk aranar MG Osman da kuma Captain Adam suma zasu dawo gida,wanda tun dawowarsu daga U.s suka tafi sada zumunci,Gaskiya wannan Babbar rana ce,Hakan yasa ma Zamuyi shiri na musamman ni da makaranta littafina don mu halarci gidan amatsayin gayyar soɗi tunda ba'a gayyace mu ba,Sa kaine kawai, Cikin ƴan kwanakin nan wata irin rayuwar farin ciki suke gudanarwa tare da Daddynsu,kullum yana manne dasu,Da kanshi ya zauna yayi masu kitson kalaba guda bibbiyu akansu kamar yadda ya ta6a yi masu suna yara,koda yazo kan Sehrish,Cike da mamaki yace"Ya akai naga gashin kanki guntu?ko kinyi wani ciwo ne dayasa aka datse maki gashin,"girgixa kai tayi tare da cewa"a'a Laifi nayi ma Babba yaya shine ya yanke mun gashin da almakashi," da buɗar bakin Abusufyan sai cewa yayi"Yayiwa kanshi ai," murmushi sehrish tayi duk da batasan me daddyn nasu yake nufi da hakan ba,duk a wannan kwanakin basu je school ba,Abusufyan da kanshi yace kada su damu shi da kanshi zai kaisu makarantar don karma a tuhume su, A 6angaren Sir Commander haroon kuwa,tamkar munafuki haka ya koma acikin gidan,ba kowa ma ke sanin lokacin da yake shigowa gidan ba,da kuma lokacin da yake fita,Da alama dae akwai wani abu da yake shiryawa a 6oye, *AMRISH* Zaune take acikin class ɗin gaba daya ta shiga damuwar rashin ganin Sehrish kwana biyu ko layinta ta kira bata samu,hatta wayar junaid ta jaraba kira shima ba'a ɗagawa,hakan ba ƙaramin tayar mata da hankali yayi ba,tagumi tayi idonta cike tab da hawaye saboda damuwar da take ciki,taso ace sehrish na nan atlease zata ɗebe mata kewa,tana cikin wannan tunanin har malam ya shigo cikin class ɗin nasu bata sani ba,bayan ya kammala amsar gaisuwa daga wurin student din,kai tsaye ya ƙarasa seat ɗin da Amrish take,hannun shi yakai wanda ke ruƙe da maker ya ɗan bubbugi desk ɗinta,a firgice takai idanunta akanshi,Yunƙurawa tayi tare da miƙewa ganin Ya mu'allim,wanda tun ranar daya ba sehrish Ruwan addu'ar nan bai ƙara zuwa makarantar ba,duk da sun samu labarin cewar Ya tafi Umra ne,shiyasa aka musanya masu shi, Murmushi ya ɗan saki afuskarshi yana kallonta yace"tunanin me kike yi ne?har na shigo cikin class ɗin baki sani ba? Muryarta na rawa tace"Ayimun afwa ya mu'allim,Bana jin daɗi ne bansan ka shigo ba, Jinjina kanshi yayi tare da ɗan kai idanunshi kan Seat ɗin sehrish yace"Ina yarinyar nan take?ƴar family ɗin Salahuddeeen hussein naga kamar bata a class ɗin"? fuskarta ɗauke da damuwa tace"Batazo ba,yau kusan kwana huɗu kenan bata zo school ba,kuma nayi trying kiran layinta amma bana samu,har brother ɗinta na kira,shima layinsa ba'a samu,' Jin hakan yasa shi fargabar to kodai wani abu ya faru da yarinyar?Yaso yaji ya tayi da ruwan addu'ar daya bata,shin tasha ko bata sha ba? Jinjina kanshi yayi tare da juyawa yace"Allah yasa dae lafiya,in har batazo ba,zuwa sati mai zuwa zan je gidansu don na binciki dalilin rashin zuwan nata,' Jiki asanyaye Amrish ta koma ta zauna,saman seat ɗin nata,jikinta har ya fara kerma saboda tsoran kar ace wani abune ya faru da Sehrish, A ƙarshe dae ta yanke shawarar neman gidansu don taje ta ganta da kanta. *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.             [1/3, 6:34 AM] Abue Saleh AlQuyraemey: *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* Zagayeta su kayi gaba ɗayansu,su jahad na ambatar sunanta,fawan ne ya ɗauko masu ruwa a fridge ya dawo ya miƙa ma uncle ɗinsu,kar6a yayi tare da buɗe murfin ya ɗebo ruwan hannunshi nata kerma ya watsa mata shi a fuskarta,nan take ta farka tana faman yin atishawa,Alhamdulillah suka shiga faɗi suna kallonta,yunkurawa tayi ta tashi daga zaune tana bin su da kallo ɗaya bayan ɗaya kafin ta mayar da idanunta akan Su hosana da jahad da suka zuba mata ido,    Muryarta na rawa tace"jaj..jahad hos...sana...ku ne?ko dae idona ne ke nuna mun ba dai dai ba?   Ba ƙaramin farin ciki ne ya lullu6esu ba sehrish ta dawo cikin hayyacinta ta gane su,atare suka faɗa jikinta suka rungume juna suna kuka,   Murmushi kawai Abusufyan ke saki bashi kaɗae ba ma fuskar kowannansu na ɗauke da murmushi,musamman Abbansu junaid farin ciki kamar ya zuba ruwa a ƙasa yasha,haka hajiya azeemarsu har cewa take yi"yanzu nan waɗannan ƴan ukun duka namu ne?ƴa'ƴan mu ne?Allah abun godiya,yau dole in yi nafilar dare don miƙa godiyata ga Allah S.W.A daya nuna mun ƴa'ƴan abusufyan ɗinmu da ranmu kuma da lafiyarmu,Ashe dae da rabon yara suga danginsu,bayin Allah sun sha wahalar rayuwa,amma bakomai har yanzu lokaci bai ƙure mana ba,zamu nuna maku soyayyar da baku samu ba arayuwarku,Zamu baku duk wani jin daɗi na duniya da kuka rasa,zamu gatanta ku,sai mun cika ku da farin cikin da zaisa ku manta duk wani ƙunci da kuka ta6a fuskanta arayuwarku,waɗanda kuma sukayi silar jefa rayuwarku cikin hatsari tabbas sai sun ɗanɗani kuɗarsu sai sunji dama ba'a halicce su cikin duniyar nan ba, Abbansu junaid ya kar6e da cewa"Ae daga rana irin ta yau su fara ƙirgen kwanakin mutuwarsu,saboda ƙarshen su yazo,sun tabka babban kuskuren ta6a jinin SALAHUDDEEEN HUSSEIN!Wallahi thumma tallahi ɗaya daga cikinsu bazai sha ba!' ranshi amatuƙar 6ace yayi maganar,    Abbas yace"Abba ina ganin yakamata yaran nan suje su kwanta dare yayi sosai,suna buƙatar hutu,in yaso koma menene gobe zamu ida tattauna akai,'    Jinjina kai Abbansu yayi tare da mayar da idanunshi kansu sehrish dake manne da juna suna kuka,    Gyaran murya ya ɗan yi masu,atare suka ɗago suna kallonshi da idanunsu dake zubar da hawaye,   "Kuyi kuka yara bazan hanaku ba,dole kuyi kuka domin kuwa an cuci rayuwarku,an zalunce ku,an ƙuntata maku,an rabaku da mahaifinku na asali kuma an rabaku da danginku,duk akan laifin da baku kuka aikata ba,saboda son zuciya irin na mutanan nan su rasa akan wa zasu ɗauki fansar su sae akan waɗannan bayin Allahn....  'Shiru ya ɗanyi yana faman sauke ajiyar zuciya,   abusufyan na zuƙunne akusa dasu ya sunnar da kanshi ƙasa,hakanan ya dinga jin kunyar yaran yana ji aranshi tamkar duk shi ne silar jefa su cikin halin da suka shiga,   Su fawan kuwa dasu twins irfan jabeer da sauransu duk suna atsaye kowannansu jikinshi asanyaye kamar waɗanda aka zare ma lakka,lokaci guda sukaji tsananin Son yaran ya kamasu,   duk wannan abun dake faruwa gwaggon katsina,na zaune saman kujera tana ta faman matsar kwalla,har lokacin bata daina tsinar dangin Sayyadi ba,haris sai faman lallashinta yake yi tana buge mashi hannu tana faɗin"ka rabu dani Harisu!abun da ciwo wlh,Zuciyata tafarfasa takeyi,ƴa'ƴan abusufyan ɗina aka wulaƙanta kamar dabbobi?wlh bazan ta6a daina tsinewa Sayyadi ba,munafuki algungumi ɗan wuta,Ya Allah ka tsine ma sayyadi da duk zuriyarshi harda unguwar zomar da ta yanke mashi cibinshi, Ya Allah kayi mana maganinsu,Sayyadi ko ɗan iska,uwarshi ta haifa mana masifa....munafuki lokacin da yake zuwa wurin abu har ƙasa yake zukunnawa ya gaishe Ni,da wata guntuwar jallabiyarshi ta gado,ƙafafun nan nashi kaman shebur sanye cikin silifar ɗan ta shegiya...Muna yi mashi kallon Biri yana yi mana kallon ayaba.....'   sai faman sambatu takeyi abun ba ƙaramin ƙona mata rai yayi ba,can kuma tace"Allah sarki abu,nasan yanzu ta gane cewa Allah ɗaya ne,yarinyar nan akwai taurin kai kamar kwallon goruba ga kafiya,kunnuwan nan nata kamar na Zoman daji falo falo dasu,ba irin jan kunnan da banyi mata ba,amma taƙi ji na,Ae ga irinta nan yanzu majnun ya koya mata hankali yanzu tana can Saman bola tana sambatu baiwar Allah,wama yasan uwa duniyar data shiga.......'   "Sehrish ku tashi ku tafi ɗaki ku kwanta,gobe zamu ƙarasa magana daku," Abbansu ne yayi maganar,   Miƙewa sukayi tsaye tare da yi masu sallama sannan suka wuce ɗakin nata,gaba ɗaya sehrish ta ɗan shiga ruɗu,batasan meya faru ba,amma bakomai yafi ɗaure mata kai ba face ganinsu hosana da jahad,taya akai suka San inda take har suka zo wurinta?abun kamar a mafarki take ganinshi,   Atare suka shiga cikin ɗakin,anan fa suka tsaya suna kallon juna fuskar kowaccen su ɗauke da tsantsar farin ciki mara misaltuwa, "Sehrish Ashe da rabon zamu sake ganinki a duniyar nan"?jahad ce tayi maganar yayin da hawaye ke sauka a fuskarta, ta ɗaura da cewa "Sehrish munyi kewarki sosai,munyi kukan rashinki atare damu,munsha wahala sosai,abubuwa marasa daɗi sun faru damu bayan rabuwar mu dake,amma duk wani hali da muka shiga hakan baisa mun manta dake ba sehrish kullum kina aranmu,koda yaushe muna cikin zullumin a wane hali kike?kina raye kuwa?kina jin daɗin rayuwarki?kina da ƙoshin lpy ko akasin hakan ....'   jin wannan maganar ta Jahad yasa ta fashe da kuka mai cin rai,janyota jahad tayi jikinta sosai ta rungumeta,itama hosana ta matsa tare da sanya hannayenta ta bayansu,suka haɗe su ukun,sun jima a wannan yanayin kafin daga bisani suka haye saman gadon su duka ukun suka zagaye junansu suna fuskantar juna a zaune   Sai lokacin sehrish ta buɗe bakinta tare da cewa"inaso ku faɗamun meya faru na daina samun wayar tsohuwa,sannan kuma inason jin yadda akai har ku ka san inda nake,nayi mamakin yadda na manta daku gaba ɗaya acikin rayuwata,nasan ban kyauta maku ba,Amma kuyi haƙuri ku yafe mun........'   ta ƙarasa maganar tare da kai hannunta ta shafo gefen fuskar hosana tana kallonta da idanunta waɗanda suka canza launi sosai,sai lokacin ta gane cewa ashe sune yaran da Marshal Omar ke ruƙo a wurinshi,rashin sani yafi dare duhu,har waya suka yi dasu jahad amma bata ganesu ba,saboda bata acikin hayyacinta,   Jahad ce ta kwashe dukkan abunda ya faru tun daga kan Jefa wayar tsohuwa da hosana tayi acikin Masai da kuma mutuwar tsohuwa,da kuma zamansu acikin cell,haɗuwarsu da Marshal Omar,zamansu a wurin gwaggon katsina da kuma rayuwarsu agidan Aunty babba,komai ta sanar mata, Sosai sehrish tayi kuka tamkar ranta zai fita,har zazza6i saida ya lullu6eta nan take,bakomai yafi girgiza ta ba face mutuwar tsohuwa,da kuma zamansu hosana a gidan Aunty babba,abun ba ƙaramin ta6a zuciyarta yayi ba,wani irin ciwon kai ne ya rufar mata mai raɗaɗin gaske,rarrafawa tayi ta koma gefe guda saman bed mattress ɗin ta kwanta tare da janyo pillow ta rufe fuskarta dashi,Wurinta su jahad suka koma tare da kwantawa kusa da ita,kowanannsu na acikin yanayi,tabbas sunga rayuwa...... Daƙyar bacci 6arawo ya sace su,amma fa dukkansu babu wanda babu zazza6i ajikinshi, Kowa fa ya manta da cikinshi saboda lamarin su hosana,a gidan babu wanda yaci abincin daren shi,saboda ƙunci da takaicin yadda rayuwar ƴa'ƴan uncle ɗinsu ta kasance, Lokacin da Azmee ta turo ƙopar ɗakin nasu samun su tayi kwance suna bacci kowacce fuskarta ɗauke da hawaye,bacci sukeyi amma hawayen basu daina zuba daga idanunsu ba,ba ƙaramin tausayinsu taji ba,ta jima tana kallonsu kafin ta rufe masu ƙopar ta koma bedroom ɗinta, Kwance yake asaman katafaren gadonshi,tunda ya dawo bedroom ɗinshi,ya shiga toilet yayi wanka,ya dawo ya kwanta yana tunanin duniya,juyi kawai yake yi asaman gadon bacci yaƙi ɗaukarshi,har lokacin zuciyarshi bata sauka ba,abun ya dame shi sosae,ya tsani zalunci arayuwarshi,ya tsani mugun mutun mai hali irin na dabbobi,tabbas idan har sayyadi ya bari ya shigo hannunshi sai ya ɗanɗani kuɗarshi,daga baya kuma ya dawo yana tunanin wai yanzu ƴar yarinyar nan da take yi mashi aiki,ashe ƴar uwarshi ce?jinin shi?ɗiyar Uncle ɗinsu?hakan na nufin cewa ita ƙanwarshi ce...? "Wonders shall neva end'ya furta hakan tare da lumshe idanunshi,nan take kuma ya tuna da hoton da Uncle abusufyan ya basu lokacin da suke a U.s,hakan na nufin cewa Hoton yaran ne ya basu lokacin da suke ƙanana,zan tambayi uncle hoton wacece nai selecting acikinsu,as I promised then zan taimaketa da kuɗi ta sayi duk abunda takeso bazan fasa ba...... ' Wasu dae sunyi bacci a wannan daren yayin da wasu kuma Baccin ya ƙaurace ma idanunsu,a tsaye Abusufyan ya kwana idanunshi sun ƙanƙance saboda raɗaɗin da yake ji acikin zuciyarshi,bawan Allah,wlh abunda ciwo,taya ma zai iya bacci?yasha kuka dae,ga wani irin Matsanancin ciwon kai da yake fama dashi,yawo yake ta yi acikin dakin yama rasa tunanin da zai yi yayin da tafin hannunshi na dama ke dafe da saitin zuciyarshi,wani irin bugawa takeyi mashi mara daɗi, Yana cikin tsayuwar ne har aka kira sallar asuba bai ankare ba,sae da Yaji ana mashi knocking ƙopa,muryarshi ashaƙe yace"Wanene," "Ni ne"muryar Abban su junaid ce, Hakan yasa shi cewa"ƙopar abuɗe take yaya ka shigo daga ciki,".  Tura ƙopar Abba yayi ya shiga ciki yana ganin Abusufyan atsaye yace"dama saida rai na ya bani cewar baka yi bacci ba abusufyan,'   Yayi maganar tare da ƙarasawa ya dafa kafaɗarshi yana kallon fuskarshi da hawaye suka wanke ta sharkaf, Cikin sanyin murya yace"duk wanda yace maka kayi haƙuri tamkar ya cuce kane!amma ya zakayi abusufyan?dole haƙurin nan shi zakayi,nasan abun da ciwo,raɗaɗinshi na iya zarce na ƙunar wuta,abusufyan bazan ce kayi laifi ba,amma kasan cewa dole ne dama kaga badai dai ba!kayi aure batare da sanin mahaifiyarka ba,baka sanar mata ba balle tasanya albarka acikin auren naku,kunyi komai a6oye kai da gwaggon katsina,sai gashi yau Allah ya bayyana mana komai,nasan kai kanka kayi mamakin ganin Ƴa'ƴanka su duka ukun a ƙarƙashin kulawar gidan mu,kaɗan daga cikin Ikon Allah kenan!kwata kwata yaran basu san suna da dangi ba,garari kawai sukeyi a wulaƙance cikin gari,mu ma haka bamu son cewa akwai wasu ƴa'ƴa waɗanda suka kasance jinin mu ne su ba,babu wanda yasan haka,amma cikin ikon Allah da yake shi hakimun ne,sai gashi silar aikatau ɗaya ta faɗo hannunmu,yayin da silar ciwon ɗaya daga cikinsu da aka kai asibiti Allah ya ƙaddara haɗuwarsu da Omar yayin da shi kuma yaje wurin ɗan uwanshi Dr haris,lamarin ubangiji girma gare shi!gaba ɗaya Allah ya haɗa yaran a wurinmu ta hanyar da bamu ta6a tsammani ba,kamar yadda kai da gwaggon katsina baku yi tsammanin abunda kuka aikata asirrance zai tonu ba,tunda baku sanar mana ba sae gashi Allah ya sanar damu,su kansu yaran basu yi tsammanin zasu haɗu da dangin ubansu na asali ba,su dama basu da masaniya akan wanine ubansu......' Dakatawa abba yayi da maganar yana kallon abusufyan dake ta faman shessheƙar kuka muryarshi na kerma ya shiga cewa"Ya Allah ka yafe mun kuskuren dana aikata na auren abu batare da sanin mahaifiyata ba da kuma dangina ba......tun farko nine silar jefa rayuwarsu Cikin halin da suka tsinci kansu,da ace ban 6oye ma kowa ba,duk da ammi bazata barni in auri abu ba amma ina da tabbacin cewar Abbanmu salahuddeen zai aura mun ita inna nasanar mashi,iyakaci dae Ammi zata zangwameta ne daga baya kuma nasan zata fara sonta,wlh ni sam tunanin hakan baizo mani ba a wannan lokacin,idona ya makance,kuma ba laifin gwaggon katsina bane,Son da takeyi mun ne yasa ta aikata hakan don ta faranta mun ganin halin da na shiga a lokacin jin cewar Mommynmu ba zata bari in auri abu ba,gashi na mutu akan sonta kaicona.......'fashewa yayi da wani sabon kukan,dana sani kenan irin wadda ba'ason yinta,abun yayi ta maka ciwo azuciyarka,shiyasa kullum muke cewa Allah ya tsare mu daga aikata aikin danasani,saboda bai da daɗi,ɗaci gare shi,     Ba ƙaramin tausayi yaba Abba ba,tuni shima hawaye suka fara sauka akan fuskarshi,janyo abusufyan yayi ajikinshi sosai ya rungume shi yana lallashinshi,   A ƙarshe yace"Abusufyan ka manta da duk wani abu daya faru dazun,yanzu lokacin farin cikine,yakamata ka nuna godiyarka ga Allah subhanahu wata ala daya nuna maka wannan ranar da ya haɗaka da triplet ɗinka dukkansu da ransu kuma da lafiyarsu!wlh abusufyan dana ga yaran nan amatsayin ƴa'ƴanka kaɗan ya hana in buga tsalle saboda murna.....'yayi maganar yayin da suka raba jikinsu dana juna,   tallabo fuskarshi abba yayi cike da zolaya yace"Kasan me?   Abusufyan ya girgiza mashi kai alamar a'a,   Abba yace"nifa ɗazu dana ga ka firgita da ganin yarinyar nan nayi tunanin cewa ko ka ƙyasa ne,har ina cewa shikenan lokacin barin gwaurantakar abusufyan yayi aduniya ashe ashe uban ne gaba ɗaya........'   Ya ƙarasa maganar yana dariya,murmushi abusufyan ya ɗanyi,   Abba ya kuma cewa"Wai yanzu nan duk aikinka ne waɗannan abusufyan?ashe dae ƙanin nawa bana wasa bane...'   fashewa da dariya abusufyan yayi tare da sunnar da kanshi ƙasa,   Hakan ba ƙaramin daɗi yayi ma Abba ba,dama so yake ya sanyashi farin ciki don ya gusar mashi da damuwar da yake ciki,   dafa kaɗarshi abba ya kuma yi tare da cewa"duk haihuwata ya'ya goma sha takwas akan su jahan ne kawai na samu ƴan biyu,amma kai da yake mai sa'a ne,na ku ba irin namu bane sai gashi ka haifa mana ƴan uku reras!ko Ya ammi zata ji in taga ƴa'ƴan mara jin maganar nan nata abusufyan....nasan zata ce shegen bisa zai aika ae,   Wannan karan atare suka fashe da dariya, Daga bisani Abusufyan yace"yaya hussein inaso naga yaran nan sosai,na damu dasu wlh....'   Wani irin kallon rainin wayau Abba yayi mashi kafin yace"yau naga ikon Allah!ni kake fadama kana son ganin ƴa'ƴanka?Yaran nan fa naka ne halak malak,ae ni nama yi tunanin a wurinsu zaka kwana,saboda suna buƙatarka sosai atare dasu,yanzu basu da burin daya wuce suga mahaifinsu atare dasu,"   Wani irin daɗi ne ya lullu6e abusufyan yace   "Zan iya zuwa wurinsu yanzu"? Abba yace"Ka bari mu dawo daga masallaci inyaso kai tsaye kawai sai ka wuce wurinsu,"   Fuskar shi ɗauke da farin ciki yace"okey,bari naje nayi alwala,"   Abba yace"muna jiranka a main palour in ka kammala,ka same mu acan,"   Yana ƙarasa maganar tashi ya juya tare da nufar ƙopar ɗakin nashi ya fuce tare da tura masa ƙopar,   Toilet abusufyan ya shiga batare da 6ata lokaci ba,ya ɗauro alwalar, Lokacin daya fito babban falon anan ya same su kowannansu ka kalla zakaga alamun damuwa a fuskokinsu,wasu ma da alama basuyi bacci ba,musamman Marshal Omar babu alamar yayi bacci adaren jiya,hatta Sgr ma akwai alamun rashin isasshen bacci atattare dashi,taya zaiyi bacci sayyadi na yawo acikin gari,shi fa in ya ƙullaci mutun irin haka har sai yaga bayanshi sannan yake samun kwanciyar hankali,su twins kuwa fuskokinsu sunyi jawur su da fawan,kowa dae da damuwa aranshi, Bayan sun kammala haɗuwa suka wuce masallaci atare, Tura ƙopar ɗakin nasu azmee tayi don ta tashe su sallar asuba,ba ƙaramin mamaki tayi ba,ganinsu ajere suna sallah,kowaccensu na sanye da dogon hijabi a jikinta hijjaban sehrish ne hosana da jahad suka sanya,abun ba ƙaramin burgeta yayi ba,dama indae suna tare su ukun,musamman in akace maka akwai jahad atare dasu tofa basa wasa da ibada,duk da itama Sehrish ɗin ba daga baya ba,amma jahad ɗin itace kan gaba,saboda ita ba'a tashinta sallar asuba da zarar anfara kiran sallar asuba duk nisan baccin da tayi zata farka ne da kanta,abun sama rai ne da kuma sabo da yi,da kuma imanin mutun, *Murmushi kawai azmee ke saki tana kallonsu gwanin ban sha'awa,ƴa'ƴan abusufyan,jikokin Ammi da salahuddeeen,ƴa'ƴan ƙanin Abban sojoji Abusufyan,ƙanne ga Marshal Da Sgr duk su kaɗae,abun farin ciki abun murna!yanzu su sun zama abunso wlh,yayyansu gaba ɗaya sojoji har goma sha takwas,ko sauro ne yayi gigin Cixon fatar jikinsu sae yaji saukar alburushin bindiga asaman goshin shi* 🤣 Azmee na tsaye tana kallonsu taji alamun motsin mutun a bayanta,jin an dafa ta yasa tayi firgit ta ɗan juya,Hajiya azeema ce jikinta sanye da hijabi blue,hannunta ruƙe da carbi,fuskar nan ɗauke da murmushi tace"Nazo ganin ƴa'ƴanmu ne,idan ba damuwa ki bani hanya in wuce ciki,"   Murmushi azmee tayi tare da matsa mata hanya ta wuce ciki,sai da ta shiga ciki sannan azmee tabi bayanta tana cewa"sallah nazo in tashe su suyi,shi ne na same su ashe har sun tashi ma,abun ba ƙaramin burgeni yayi ba dana gansu ajere su ukun suna sallah,'   Murmushi hajiya azeema tayi ayayin da take zama daga gefen gadon su tace"Albishirinki,"tayi maganar tana kallon azmee,   Azmee tace"Goro," "Fari ko ja,"cike da zolaya tayi maganar,   "Fari dae,shi ne ke tare da alkhairi,wannan launin jan alamace ta hatsari," Dariya hajiya azeema tayi kafin tace"Tab jiya anyi babu ke!Labari da ɗumi ɗuminsa!zazzafan gaske....'   A ƙagare azmee tace"Meya faru"! A lokacin su jahad sun sallame sallah,suna zaune saman dardumar suna sauraransu, Nuna su hajiya azeema tayi tare da cewa"Ke wai ashe yaran nan ƴa'ƴan abusufyan ne!!!"   Gaban azmee ne ya faɗi Rasss!saboda yadda maganar ta dirar mata kai tsaye acikin kunnuwanta,   "Wai dagaske"?tayi tambayar cike da mamaki,   Hajiya azeema tace"hmmmm ke dae bari,wani iko sai ubangiji,dagaske fa nake,babu wanda baiyi mamakin wannan abun al'ajabin ba,yara dae ƴa'ƴan ƙaninmu ne sufyan,'   Juyawa azmee tayi tana kallonsu sehrish da sukayi zuru suna kallonsu musamman Sehrish da batasan kan zancen ba,saboda bata a hayyacinta lokacin da akayi maganar,amma lokacin da jahad ke bada labarin rayuwarsu taji komai a kunnanta kuma daga nan ne Sihirin jikinta ya lalace saboda tunaninta daya rinjayi kwalwarta harta tariyo dukkan abunda ya faru arayuwarsu ga kuma addu'ar da Sgr keta yi mata acikin kunne, Cike da mamaki azmee tace"taya akai hakan ya faru?dama abusufyan ya ta6a aure ne kenan?    Ataƙaice azeema ta bata labarin yadda abusufyan ya auri abu batare da saninsu ba,har suka samu ƙaruwar ƴan uku,'   Wani irin farin cikine ya lullu6e azmee saboda tsabar farin ciki bakinta yaƙi rufuwa,    "Jahad!dagaske ne abunda kunne na ke jiyo mun"?sehrish ce tayi maganar tana kallon jahad da tsananin mamaki,   Murmushi jahad tayi ta jinjina mata kai alamar eh,ta ƙara da cewar"jiya duk baki a hayyacinki,abun farin cikin nan ya faru,Mun jima muna wahalar rayuwa ashe muna da dangi mai girma irin wannan bamu sani ba,cikin ikon Allah kuma sai gashi Allah ya haɗa mu dasu ta hanyar da bamuyi tsammani ba,ina tunanin addu'ar da muka jima munayi ne Allah ya kar6a mana,Ashe oumman mu sai da ta fara auren uncle ɗin su abusufyan sannan ta auri wannan fasiƙin mutumin sayyadi,da cikinmu ta shiga gidan shi........'   Aruɗe sehrish tace"taya hakan zai yiwu?   Hajiya azeema ce ta katse ta da cewar tabbas zancenta gaskiya ne sehrish!ku ƴa'ƴan ƙaninmu ne Abusufyan,sai da ya fara auren mahaifiyarku sannan Mugun mutumin nan daya ƙuntata rayuwarku ya aureta.......'gaba ɗaya hajiya azeema ta kwashe labarin rayuwar mahaifiyarsu agidan gwaggon katsina da kuma haɗuwarsu da abusufyan har izuwa rabuwar aurensu ta auri sayyadi ta sanar ma Sehrish,'   tun kan takai ƙarshen labarin nata,Sehrish tayi sujjada,tana shessheƙar kuka,saboda tsabar farin ciki,Ashe ita ɗiyar uncle ɗinsu ce abusufyan?hakan na nufin su Babban yaya ƴan uwanta ne na jini!haba no wonder ae shaƙuwar dake tsakaninta da junaid tayi yawa,kai kana ganin abun zakasan cewar akwai alaƙa ta jini ajikinsu,ta damu da mutanen gidan sosai,ashe danginta ne su ɗin,   Jikin azmee ba ƙaramin sanyi yayi ba bayan hajiya azeema ta sanar mata irin zaluncin da sayyadi yayi ma su Sehrish,har idanunta sai da suka cicciko da kwalla saboda tausayinsu da taji,ta jima tana tsinar sayyadi acikin zuciyarta, Muryarta tamkar zatayi kuka tace"dama ina ta son mu samu lokaci Sehrish ta bani tarihinta wllh,ashe haka suka sha ukubar rayuwa bayin Allah,kai koma wanene wannan mugun mutumin ya cika babban azzalumi,saboda tsabar zalunci ya raba yara da mahaifinsu ya kuma ƙuntata rayuwarsu,duniya ina zaki damu.......'azmee na cikin magana,Abusufyan ya turo ƙopar ɗakin bakinshi ɗauke da sallama,gaba ɗaya hankalin su sehrish ya dawo kanshi,shi ma kuma yana ɗago idanunshi suka sauka akan ƴan ukun nashi,kwata kwata ma bai lura da hajiya azeema da kuma azmee dake a ɗakin ba,Su sehrish kawai yake kallo cike da so da ƙauna,ko kyaftawa baiyi,kamar ya haɗiye su haka yake ji,kamar yadda yake jinsu haka suma suke jinsu,sae ƙare mashi kallo suke yi kamar su watsa a guje su rungumo shi haka suka dinga ji,ta wani 6angaren kuwa abun ba ƙaramin yawo yake yi masu akai ba,Wai nan mahaifinsu ne halak malak,ubansu wanda yayi silar zuwansu duniwa,dama suna da uba da dangi a duniya?tambayoyi iri iri suke shiga yiwa kansu,   Ganin sun zubama juna ido tsakanin Abusufyan da kuma su sehrish dake zaune saman darduma suna kallon shi,hakan yasa hajiya azeema tayi masu gyaran murya hankalinsu ya dawo kanta sannan tace"Zaman me kuke yi ne?baku ga mahaifin naku bane?ba zaku zo ku rungume shi ba,kuji ɗumin mahaifinku a jikinku?   jin wannan maganar ta hajiya azeema yasa su miƙewa gaba dayansu jiki na rawa suka ƙarasa wurin shi, Tunkan su ƙaraso ya buɗe masu hannayenshi alamar su shiga ciki,haɗasu yayi dukansu ya rungume su sosai ajikinshi kamar zai maidasu cikin cikinshi,hawaye ne suka shiga gangarowa a idanuwanshi da kuma idanuwansu sehrish,bai ta6a tunanin zaiga wannan ranar ba,yau gashi ga ƴa'ƴanshi sun dawo wurinshi,tabbas Allah ne ya kar6i addu'ar daya jima yana yi,atare suka ɗago idonsu cike tab da hawaye suka haɗa baki wurin cewa"Abba," Har cikin zuciyarshi yaji wani irin sanyi ya ratsa shi,muryarshi akasalance yace"Ku sake maimaitawa banji ba," "Abba,"suka maimaita mashi kamar yadda ya umarta, "Wlh kunyarku nake ji!duk wani abu daya faru arayuwarku ni ne sila,Na cuci rayuwarku,Naji na tsani kaina ƴa'ƴana suna a wani hali na rayuwa amma nagaza taimakonsu,zan iya zuƙunnawa saman guiwaowina agabanku domin in nemi gafararku.....,'tunkan ya ƙara maganar gaba ɗaya ya tafi zai zuƙunna saman guiwowins,cikin sauri suka rurruƙe shi suna cewa"Abba dan Allah kada kayi mana haka bamu so,ka daina ɗaura laifin akanka,dama Allah ya riga da ya ƙaddara faruwar hakan,dan Allah kada ka zuƙunna agabanmu,mu fa ƴa'ƴanka ne, Ganin dagaske kneel down zaiyi agabansu yasa suka riga shi zube wa saman guiwowinsu,tsayawa daga tsaye yayi yana kallonsu,Azmee da hajiya azeema duk suna kallon abunda ke faruwa,ba ƙaramin tausayi suka basu ba,   "Abusufyan"! Hajiya azeema ce ta ambaci sunanshi,amsawa yayi yayin da ya mayar da idanunshi akanta,   Anatse ta soma magana"yanzu ba lokacin baƙin ciki bane ko lokacin tuna baya,Lokacin farin ciki ne wannan,dariya yakamata in dinga gani a fuskar kowannanku ba hawaye ba,ko ba haka ba azmee?tayi tambayar tare da mayar da idanunta kan azmee, Murmushi azmee tayi kafin tace"Wannan haka yake,Abusufyan ina tayaka Murna sosai,nayi farin ciki mara misaltuwa,naji daɗi da sehrish ta kasance ƴarka ce,ko ince suka kasance ƴa'ƴanka ne,lamarin ubangiji da girma yake,babu wanda ya ta6a tsammanin haka,naji ma ina ganin kamannin fuskarka a fuskar sehrish ashe ƴar kace.....'magana take hawayen farin ciki na gangarowa daga fuskarta,    Murmushi kawai abusufyan ke saki,a lokacin harsu Sehrish sun miƙe tsaye suna tsaye akusa dashi,hosana ta rurruƙe hanunshi kamar wani zai kwace mata shi, Hajiya azeema ce tace"Azmee yakamata mu basu wuri su gana da juna,don na lura da yadda Uban ƴan ukun nan ke zumuɗi akan ƴa'ƴanshi,"cike da zolaya ta ƙarasa maganar tare da miƙewa taja hannun azmee suka fuce suna dariya,   Ajiyar zuciya ya sauke tare da mayar da idanunshi kansu jahad yace"kun samu bacci kuwa jiya?ya tambayesu ne saboda fuskokinsu daya gani duk a yamutse,musamman idanunsu sun ƙanƙance, Haɗa baki sukayi wurin cewa"Eh,"   Hosana tace"abba,dagaske kaine Abban mu ko?   "Ga zahiri kin gani,"yayi maganar yana yi mata nuni da fuskarshi,murmushi suka saki gaba ɗayansu,   Sun jima atsaye tare dashi suna magana jefi jefi saboda basu saba da juna ba,duk jin abun suke wani iri haka,kamar mafarki ne suke yi ba gaske ba,    "Ku koma ku kwanta,kuyi bacci ku huta,idan har akwai inda keyi maku ciwo ku sanar mun zansa aduba ku yanzun nan....'wannan maganar tashi ba ƙaramin sanyaya masu jiki tayi ba,   "Abba,lafiyarmu qalau,babu abunda ke damun mu,'suka faɗi hakan atare, Gyaɗa kanshi yayi tare da kama hanya zai juya da nufi yabar ɗakin nasu, Cikin sauri jahad ta ruƙo hannunshi tare da cewa"Abba,dan Alla kada ka tafi kabarmu,muna buƙatarka a kusa damu,muna so mu kasance tare da mahaifinmu,' Sehrish ta kar6e da cewa"hakane Abba,ka dawo mu zauna atare dakai,muna buƙatar kyakkyawar kulawa daga wurinka,' tana kai ƙarshen maganar hosana tace"Abba pls,ko don saboda Ni," Wani irin murmushin farin ciki abusufyan ya saki yana kallonta,batare da 6ata lokaci ba,suka wuce saman gadon nasu,a tsakiya suka sanya abusufyan,yayin da suka kwanta gefe da gefenshi,sosai ya rungume hosana ajikinshi,duk in ya tuna labarin yada ta samu ta6in hankalinta nan take sai yaji idonshi sun ciko da kwalla, "Idan Allah ya kaimu gobe,da kaina zan gyara maku gashin kanku inyi maku kalaba guda biyu,kamar yadda na ta6ayi maku Lokacin da kuna yara,nasan ba zaku iya tunawa ba,' Jikinsu ne yayi wani irin sanyi, wani irin yanayi suka shiga gaba ɗayansu,     [1/3, 6:34 AM] Abue Saleh AlQuyraemey: *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* ❤🤍❤ *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Hannu yasa tare da tallabo fuskarta yace"Hosana bada sani na nayi maki hakan ba,laifin ki ne,meyasa zaki toshe mun hancina?so kike na mutu'? Girgiza kai tayi"a'a,banso ka mutu,ae ni wasa nayi maka ko,"tayi maganar tana satar kallon fuskarshi,   "Faɗa mun me ya kawoki bedroom ɗina har saman gadona"?    A ƙule tace"nifa nazo ne na tashe ka don kaje ka ci abinci,naga kowa ya fito banda kai,kuma zasu iya cinye abincin duka," fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Waya faɗa maki za'a cinye abincin,ae ko ban fita ba Azmee zata kawo mun ne har cikin part ɗina,"     Shiru tayi tana faman sauke ajiyar zuciya,ɗagowa ta ƙara yi zata saci kallonshi suka haɗa ido,ganin yadda yake kallonta ko ƙyaftawa baiyi hakan yasa ta ɗaure fuska cikin shagwa6a tace"Ya omar wannan kallon fa,ka wani tsare ni da ido,"   yadda tayi maganar ba ƙaramin burgeshi tayi ba,ya jima yana kallonta batare da yace wani abu ba,har sai da ta hasala rai a6ace tace"shikenan tunda ba zaka mun magana ba,bari na tashi na tafi,dama ko abincina banci ba,saboda kawai inzo in tashe ka daga bacci,amma ko farin ciki ba kayi ba,'   Ajiyar zuciya ya sauke tare da ruƙo hannunta cikin nashi"Hosana,so nake ki faɗa mun gaskiya,kina sona da gaske?kuma zaki aure ni? Waro ido waje hosana tayi tana kyakkyaftasu kamar na ƴar tsana jin abunda yace,a ruɗe tace"Ya Omar!aure fa!"_ Jinjina mata kai yayi tare da cewa"eh,aure hosana ko baki shirya ba,"   Turo baki ta ɗanyi tana ƙunƙuni ƙasa ƙasa,hankalinsa kam harya ɗan tashi saboda ganin yadda ta tsorata don yayi mata zancen aure,dama fargabarsa kada sai anje wurin nema mashi auranta tace bata shirya ba,don yasan ba cikakken hankali gare ta ba, Lalla6ata ya shiga yi"pls hosana,ki faɗamun gaskiya,zaki aure ni"?   daƙyar ta iya buɗe baki tace"Ni yanzu tashi zanyi in tafi,dama zuwa nayi fa don in tambayeka,wani kalar ƙunshi kake so ayimun baƙi ko ja,"    ya lura cewa batason zancen auren shiyasa ta kawo maganar ƙunshin,cikin sanyin murya yace"Nafison jan lalle zai fi yi maki kyau,kuma ba mai yawa ba ƙunshin,ƴar flower kawai za'a zana maki mai kyau,"   Yana kai ƙarshen maganar,hosana ta miƙe tana faman shan ƙamshi,da sauri ta juya ta bar bedroom ɗin nashi,bin bayanta yayi da kallo har ta fuce,jiki asanyaye ya miƙe tare da nufar toilet ya shige,    Hosana na fita daga cikin bedroom ɗin nashi,a falonsa ta tsaya tana faman zabga murmushi,tsabar farin ciki kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha,Yau ya Omar ya nuna yana sonta harma yanayi mata zancen aure,ta rasa ma wa zata fara faɗamawa,sai faman zagaye zagaye takeyi a cikin falon, Wuraren ƙarfe biyu da rabi na rana,Abusufyan ya ɗaukesu acikin motarshi kamar yadda yayi masu alƙwarin kaisu wurin saloon da kanshi,hosana da jahad suna a bayan motar duk sun ɗau wankan jallabiya sun laga mayafi,Sehrish na agaban motar kusa da driver seat inda Uncle abusufyan ke zaune yana driving ɗinsu anatse,Su jahad da hosana sae fira sukeyi tare dashi,amma ita ko uffan bata tanka masu ba,dama tunda ta shigo cikin motar Abusufyan ya lura da yanayinta, gyaran murya yayi mata hakan yasa ta ɗan dago da kanta ta kalle shi,   "Meyake damunki ne Daughter?tunda kika shigo cikin motar nan baki tanka mana ba,ga ƴan uwanki suna ta fira a tsakaninsu amma ban dake".   Muryarta asanyaye tace"Babu komai,"   "ko don saboda na hana ki kai ma Sgr abinci ne"? Yayi maganar batare daya kalleta,   Cikin sauri tace"a'a ba haka bane,kawai bana jin daɗin jikina ne,"   "Ban yarda ba daughter,saboda shi ne yasa kika shiga damuwa,"_   Shiru tayi bata ce komai ba,murmushi abusufyan yayi kafin yace"banyi hakan don na takura maki ba,face don na ɗaukaka darajarki,nasan ba zaki fahimce ni ba a yanzu amma nan gaba da kanki zakiyi mun godiya akan hakan,idan kuma hakan ya 6ata maki rai,kiyi haƙuri,'ya ƙarasa maganar adai dai lokacin da suka ƙaraso wurin Saloon ɗin,parking ɗin motar yayi jahad da hosana suka fita waje,tana ƙoƙarin buɗe motar ta fita ya ambaci sunanta"Sehrish,"juyowa tayi tare da kallon fuskar daddyn nasu tace"Na'am daddy,"   "Murmushi kawai nakeso kiyi mun kafin ki fita," fashewa tayi da dariya har fararen hakoranta suka bayyana,duk a tunaninta wani abu mai muhimmanci ne yasa ya kirata,ashe kawai don ya tambayi murmushinta ne,shima dariyar yakeyi,kafin su fita daga cikin motar atare, ************** Fitowarshi kenan daga wanka,yana cikin shirya kanshi cikin riga da wandon jeans,yaji an kwankwasa ƙopar ɗakinshi,daga muryarshi yayi tare da cewa"ƙopar a buɗe take,"yayi maganar tare da juyawa yana kallon mai shigowar,   Cike da mamaki yace"Ya HAROON!kaine!dama kana nan," Shu'umin murmushin nan nashi ya saki tare da ƙarasa shiga cikin bedroom ɗin nashi yana cewa"Ina nan mana junaid,kaine ka manta dani,kowa ma ya manta dani,"   "Ya haroon ba haka bane,wlh ni ban manta dakai ba,kana araina,"   ta6e baki haroon yayi alokacin da yake tsayawa agaban junaid suna fuskantar juna yace"Ka ƙara kyau da haske,hankalinka kwance baka da wata damuwa,ba kamar ni ba,kullum cikin damuwa nake,zuciyata har nauyi takeyi mun saboda halin da nake ciki amma babu wanda ya damu dani,yau ko mutuwa nayi babu wanda zai damu,sae ma farin ciki da za'ayi,"   Jin wannan maganar ta haroon yasa jikin junaid yin sanyi,wani irin tausayin shi ya kamashi,muryarshi tamkar zaiyi kuka yace"pls Ya haroon dan Allah kadaina faɗin wannan maganganun,wlh bana jin daɗi,"   "Junaid ƙarya nayi ne?an damu dani acikin gidan nan ne?kowa yayi watsi dani,babu wanda ke damuwa dani,tamkar bare haka nakeyin rayuwata,hatta azmee da take ƴar aiki acikin gidan nan ta fi ni muhimmanci tunda ita ana damuwa da ita,ni kuwa fa?   Hawaye ne suka cicciko a idanun junaid,dama shi akwai tausayi,gaba ɗaya tausayin haroon ya kamashi,saboda duk abunda ya faɗi gaskiya ne,ba'a damu dashi ba,ko zancen shi ma babu maiyi acikin gidan,idan zai share wata a waje babu mai tambayar ina yaje,   "Tamkar maraya ni fa haka nake acikin gidan nan,kalli kaga yadda na koma duk na rame saboda damuwa,gaskiya ni bazan iya cigaba da rayuwa ba junaid,zan kashe kaina ne kowa ya huta," yana kai ƙarshen maganarshi ya juya da sauri zai bar ɗakin,   Da gudun gaske junaid ya rungumoshi ta baya tare da fashewa da matsanancin kuka yana cewa"Meyasa ya Haroon!pls stop saying that,banason jin kana zancen mutuwa,ko kowa bai damu dakai ba,Ni nadamu dakai,ko don saboda ni ya haroon kada ka aikata hakan,idan ka kashe kanka,nima bazan rayuwa ba,zan bi ka mu tafi tare,"   Wannan kalaman na junaid ba ƙaramin sanyaya mashi zuciya su kayi ba,cire hannunshi yayi daga ruƙon da yayi ma waist dinshi,sannan ya juya suna fuskantar juna yace"Junaid dagaske ne ka damu dani?kuma bakaso in mutu"?   cikin shessheƙar kuka junaid yace"Eh ya haroon bana so pls,"   Hannu haroon yasa yana share mashi hawayenshi,kafin daga bisani ya janyo shi ajikinshi tare da rungume shi sosai ajikinshi,kamar zai mayar dashi cikin shi,saitin kunnanshi yakai bakinshi tare da cewa"I love u so much junaid,cos you're so special,in dai zan kasance tare dakai bazan ta6a shiga wani ƙunci na rayuwa ba,kallon ka kawai zai iya sanya farin ciki a cikin zuciyata,daga yanzu inason ka zama abokina junaid,saboda ka dinga ɗebe mun kewa,muna fita yawo atare,don bani da aboki,nifa kowa gudu na yake yi,bansan meyasa ba,'ya ƙarasa maganar tare da janye junaid daga jikinshi,   "Junaid!ka amince zaka zama abokina"? Jinjia kai junaid yayi tare da cewa"Eh,na amince,amma dan Allah ya haroon kadaina zancen zaka kashe kanka,banjin daɗi banso pls,"   "Shikenan na daina,daga yau kome kakeso ma zanyi,am sorry na sanyaka zubar da hawayenka,"   "Ya haroon ni zanje nayi ma Abba magana akanka,nasan abba zai fahimce ni,"   cikin sauri haroon ya ruƙo hannun shi tare da cewa"A'a junaid,just leave it,banason kowa yasan meke tsakanina dakai,kada kayi ma kowa maganata don ba lalle su fahimce ni kaman yadda kai ka fahimce ni ba,"   "Shikenan bazan faɗa ba," "Yawwa junaid ɗina,Yanzu zan barka ka ƙarasa shiryawa,"   Yana faɗin hakan ya juya tare da fucewa daga ɗakin junaid,ya koma bedroom ɗinsa,agaban dressing mirror ɗinshi ya tsaya yana ƙarewa fuskarshi kallo,   A hankali wannan mugun murmushin nashi ya soma bayyana akan fuskarshi,fashewa yayi da dariya kafin daga bisani ya ɗaure fuskarshi,kalaman junaid ya shiga tariyowa,tuni jikinshi yayi sanyi,ta wani 6angaren ji yake tamkar bazai iya ba,amma bai da wata mafita daya wuce wannan!   "Junaid kada ka damu zamu mutu atare,"ya faɗi hakan tare da komawa ya zauna daga gefen gadonshi, Bayan junaid ya kammala shiryawa,saukowa downstairs yayi har lokacin jikinshi ba kwari,haroon ba ƙaramin tausayi ya bashi ba,A main palor ya samu Abbansu tare da Momnynsu dasu Twins suna fira atsakaninsu,tunkararsu yayi fuskarshi ɗauke da murmushi,suna haɗa ido da Abbansu ya watsa mashi harara,sunnar da kai ƙasa junaid yayi da wurin Abban yaso ya fara zuwa amma wannan hararar da yayi mashi ce tasa ya fasa zuwa ya wuce wurin mommynsu,dukawa yayi tare da manna mata kiss kafin ya rungumeta,fuskarta asake tace"My romeo,"Amsa mata yayi da mommy,a lokacin daya koma wurinsu twins suna gaisawa,Jahan yace"Ina zuwa naga key ɗin mota a hannunka," "Zanbi su uncle ne," ayaan yace"Kada ka bari Mommy taji to,in ba haka ba bazata bari kabi su ba,"     "Saboda me"?ya tambaya yana kallonshi,Jahan ne ya bashi amsa da cewa"Saboda bazata barka ba,idan ta tambayeka ina zaka je,sae kace mata gidan abokinka zakaje,"duk wannan maganar da sukeyi a kunnan abbansu saboda yana kusa dasu,kallonsu kawai yakeyi,juyawa junaid ya ɗanyi tare da satar kallon mommyn,idonta na akanshi hakan ya tabbatar mashi da cewar so take taji me suke cewa,'   "Ka tafi kawai,"acewar ayaan,   harya juya zai tafi ya tuna da Abbansu,dawowa yayi tare da zuƙunnawa agabanshi yace"Abba,"ɗaure fuska abba yayi batare da ya tanka mashi ba,   "dan Allah kayi haƙuri abba in na 6ata maka rai,bazan ƙara ba,"   Ta6e baki abba yayi tare da cewa"Junaid kenan,ae ni yanzu babu ruwana dakai,kafi ƙarfi na,"_   Ashagwa6e ya kuma cewa"pls abba,kayi hakuri,ka manta da abunda ya faru jiya,bazan ƙara ba,"     "Naji,tashi ka tafi,ka kulamun da kanka,"   Murmushi junaid ya saki tare da mikewa ya manna mashi kiss a fuskarshi,sannan cikin sauri ya kama hanyar fita,   "Junaid ina zuwa"? Jin muryar Momnynsu yasa shi dakatawa da tafiyar da yake yi,    tsayawa yayi tare da juyawo ya kalleta,    "Mommy gidansu abokina zani je,"   "Kai da wa?waye zai kai ka? Nuna mata key ɗin motarshi yayi kafin yace"Ni zan kai kaina," Jinjina kai tayi tare da cewa"Okey,u can go," da sauri ya fuce daga cikin gidan,   Mayar da idanunta tayi akan abbansu tace"Dama inaso inyi magana dakai,wai meyasa kuka bar romeo yana Driving da kanshi?Also babu wani security guard dake tsaronsa,Shi kadae yake yawonshi,"   Abba yace"Allah xai tsare mana shi," Alexandra tace"Nasan da wannan,Amma wannan babban ganganci ne,koda ace kowanne daga cikinsu zaiyi yawonshi batare da security guards ba,amma bai kamata ace kamar junaid ƙaramin yaro yana yawo shi kaɗae ba,ba wani tsaro atare dashi,Especially yadda kowa ya sanya mashi ido,gaskiya ni hakan bai kwanta mun araina ba!!" shiru abbansu yayi yana nazarin maganarta,   Jahan yace"Gaskiya Abba,maganar mommy gaskiya ne,yakamata ace junaid akwai security guards dake tsaronsa duk inda zaije,musamman a wannan yanayin da muke ciki,bibiyar rayuwarmu akeyi don kawai acutar damu,junaid kuma yafi kowa ƙaranta acikinmu,yana buƙatar security,"   "Abunda nake ƙoƙarin fahimtar dashi kenan,"acewar mommnynsu,   jinjina kai Abba yayi tare da cewa"hakane,zanyi wani abu akai',    daga nan suka cigaba da tattauna a tsakaninsu, *Boss Bature* Tun bayan da Hayaam ta tura ma Aunty babba hotonsu hosana,bata samu damar duba hoton nasu ba,ko whatsapp ɗinta bata shiga ba,wayarma tana ajiye cikin bedroom ɗinta,Shirye shiryen zuwa walima kawai sukeyi,atare da hafsat suka fita saloon daga nan za'ayi masu ƙunshi,bayan nan kuma zasu biya Shopping mall,saboda siyayyar da tace zatayi ma Ƴa'ƴan uncle ɗinsu,basu suka dawo gidan ba sai wuraren karfe shida na yamma agajiye suka dawo,kowa ya wuce bedroom ɗinshi,Aunty babba na shiga ɗakinta,kai tsaye ta faɗa saman gadonta ta shiga sharar bacci,Hafsa kuwa saida ta fara yin wanka,ta canza kayan jikinta izuwa riga da skirt marasa nauyi,sannan ta fito falo ta kwashe shopping bags ɗin da suka bari a falo,takaisu ɗakinta,tana cikin dudduba kayan wayarta dake ajiye gaban mirror ta shiga ringing,hannu takai tare da ɗaukar wayar tana kallon screen ɗinta,ganin Sunan Aunty Hayaam ya bayyana akan secreen ɗin wayar,yasa ta ɗaga kiran tare da karawa a kunnanta,   "Assalamu Alaikum aunty hayaam,' Ko amsa mata sallamar batayi ba tace"Hafsat ina Aunty laila take ne?tun da sassafe na tura mata hoton bata duba ba,har nagaji da jira,"   Hafsat tace"yanzu muka dawo daga kasuwa agajiye,tana a bedroom ɗinta ina jin bacci ne ya dauketa,ko inyi mata magana ne"?   Hayaam tace"A'a,kawai idan ta tashi ki sanar da ita cewa na tura mata hoton ƴa'ƴan abusufyan ɗin,ta duba ta whatsapp ɗinta,"   Wani irin farin ciki ne ya lullu6e hafsat,muryarta na rawa tace"hoton ƴa'ƴan Abusufyan dinmu!zan sanar mata kuwa,"   Rejecting call ɗin tayi,da gudu ta fito daga bedroom ɗinta,kai tsaye ta haye upstairs ɗakin aunty babba,tura kopar ɗakin tayi tare da shigewa ciki,a kwance ta samu aunty babba saman gadonta sai sharar bacci takeyi,ga wayarta ajiye agefenta,   Cikin sanɗa takai hannu tare da ɗaukar wayar,ta danna power ɗinta ta kawo haske,ganin akwai password yasa ta ɗan bubbuga kafarta tana cewa"Kai mommy,yanzu dole sae kin tashi sannan zan samu damar ganin hoton babies ɗinmu!gaskiya ni a ƙagare nake,"   Tana cikin maganar,ta tuna da finger print ɗin dake akwai ajikin wayar,nan take zuciyarta ta bata shawarar cewar me zai hana,ta lalla6a ta hau saman gadon,ta dangwalo yatsan aunty babba,kota samu wayar ta buɗe,Good idea,ta furta hakan tare da lalla6awa ta hau saman gadon,cikin sanɗa ta ƙarasa inda aunty babbar take,hannunta ta ruƙo tare da sanya yatsan hannunta a wurin,ya rubuta mata wrong,haka ta dinga bin yatsun hannun aunty babba tana jarabawa,har sai da taci nasarar buɗe wayar,saukowa tayi daga saman gadon,ta tsaya atsaye,hannunta har kerma sukeyi wurin daddana wayar,tsoranta kar Aunty babba tafarka saboda tasan halin Mommyn nata,ta tsani wani ya ɗaukar mata wayarta,kamar mara gaskiya,    Tana shiga whatsapp ɗinta,sai ga wani security ɗin,rai a6ace tace"Mommy kamar mara gaskiya,duk tabi waya ta garƙame da security,"   Allah yaso shima finger print ne,komawa tayi tare da dangwalo yatsan aunty babba,whatsapp ɗin ya buɗe,   Kaitsaye ta shiga chat ɗinsu da Hayaam,anan taga hoton da Hayaam ta tura mata,bai buɗe ba hoton saboda data a kashe take,cikin sauri hafsat ta kunna data ɗin,nan take yashiga loading yana ƙoƙarin budewa,a hankali hoton ya soma bayyana,ƙura ido hafsat tayi tana jiran hoton ya kammala buɗewa,   Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu ji kake Daram!!Dararam!!tamkar ana buga ganga,Waro ido waje hafsat tayi agigice a matukar razane,tamkar wadda taga Zombie,hankali a matuƙar tashe tace"Kai!!!"   Hannunta har kerma yakeyi wurin yin zooming ɗin hoton nasu ta matso dashi kusa don tagani dakyau,gaba ɗaya tagama kiɗima,wata irin zufa ce  ta soma tsattsafo mata agefen fuskarta,daƙyar take iya haɗiye yawun bakinta saboda maƙoshinta daya bushe ƙamas,juyawa tayi ta kalli Aunty baba dake ta faman mutsu-mutsu alamar zata farka daga baccin da takeyi,aikuwa cikin sauri tayi deleting ɗin hoton gaba daya,sannan ta rufe wayar,tayi wurgi da ita asaman gadon,jikinta na kerma ta fuce daga dakin,gudu gudu sauri sauri haka take tattaka stairs ɗin ƙiris ya rage ma tayi tuntu6e saboda yadda jikinta ke rawa kafkaf kamar wadda sanyi ya kama,   Bedroom ɗinta ta koma,tana shiga ta aza hannu akai tana faɗin"Tashin hankali!In har dagaske ne abunda idanuna suka gane mun acikin hoton nan kenan hakan na nufin cewa HOSANA DA JAHAD Suna araye kuma suna a gidansu daddy!taya hakan ya faru?Kenan Ya Omar shine ya ɗaukesu?Ina wannan tsohon mutumin da mommy tasa ya kwashe su da nufin ya zubar dasu?Taya akai hosana da jahad suka kasance ƴa'ƴan uncle ɗinmu!?wacece ita ɗayar yarinyar mai kama dasu sak!dama su ƴan uku ne?Tabɗijancan,akwai matsala,   Komawa tayi gefen gadonta ta zauna tare da kifa hannunta asaman fuskarta,hosana da jahad suna raye,suna gidan abban mu,wayyo Allah na,ina farin ciki sosai,duk da ina tsoran abunda zai biyo baya,Ashe jinina ne su!shiyasa akace rashin sani yafi dare duhu,mun cutar dasu sosai,mun zalunce su bayin Allah,mutuwa ce kawai batazo ta daukesu ba acikin gidan nan amma sunsha wahala,sun ƙuntata,tabbas Mommy mun shiga uku,idan Abba yaji,daga ni harke ba wanda zai tsira,kwara ni hukuncina mai sauƙi ne tunda na nuna masu soyayya daga baya amma ita mommy itace silar fitar dasu daga gidan nan don azubar dasu,Wayyo Allah na!,   Yatsun hannunta sae faman kerma sukeyi,jiki na rawa ta ɗauki wayarta tare da lalubar numbar junaid ta danna mashi kira,   A lokacin junaid yana tare dasu Uncle abusufyan,dama sai daya fara kiranshi a waya ya tambayi address ɗin inda suke ya bashi,har an kammala yi masu saloon tuntuni,anyi masu ƙunshin jan lalle a hannuwansu,daga can suka wuce shoprite siyayya,bayan sun kammala siyayyar,suka biya gidan Uncle ɗin nasu wuraren 6,saboda su kwaso wasu daga cikin kayansu Jahad da hosana wanda zasuyi kwalliyar walima dasu,   A bayan motar junaid aka sanya trolley ɗin kayan nasu,sannan Sehrish da hosana suka shige motar abusufyan,jahad kuma ta shiga motar junaid,atare motocinsu suka fita daga cikin gidan,   Tunda jahad ta shiga motarshi,ya ɗaure fuskarshi,dama tun wurin siyayyar yake ta shan mur yana murtuke mata fuska,amma hakan bai hana tayi masa magana ba,duk in ta ɗauko abu sai ta gwada mashi ta tambayeshi zaiyi mata kyau,daƙyar yake amsa mata da eh,ko a'a,sai dae kawai tayi murmushi ta girgiza kai,     Kiran Hafsat na shigowa a wayarshi,yace"ki ɗauki wayar,ki amsa wayar sai ki sanyata a handsfree,"    hannu jahad tasa tare da ciro wayar daga aljihun gaban rigarshi,picking call ɗin tayi bayan ta sanyata handsfree sannan tayi Mata sallama,    Muryar hafsat ce ta karaɗe kunnansu"Junaid!kana ina ne"? Gaban jahad ne ya faɗi rass saboda jin muryar hafsat,duk da bata tabbatar da cewar ita bace,amma muryar tayi mata kama da ta sister hafsat,   "Ina akan hanyar komawa gida ne yanzu hakan,"    Hafsat tace"junaid dan Allah so nake in tambayeka,waɗannan yaran ƴa'ƴan uncle abusufyan Ƴan uku ne"?   "Of course they are triplet,"ya bata amsa a yayin da yake ƙoƙarin juya sitiyarin motar,ya karya kwana,   Hafsat tace"Ya sunan su"! Juyowa yayi ya ɗan kalli jahad da idanunta ke akan shi,kafin ya mayar da idanunshi kan driving din da yakeyi,a jere ya ambaci sunayensu"Hosana Sehrish Jahad"!hafsat na jin haka,a gigice ta kashe wayar,   "kiran ya katse,"Jahad ta faɗi tana ƙare ma wayar kallo,   "May be network ne,idan na koma gidan zan kirata,"    "In mayar maka da wayar"?   "A'a ki ruƙe a wurinki,idan mun isa gida zan kar6a,"   ta amsa mashi da toh, Gallery ɗinshi ta shiga tana kallon kyawawan hotunanshi da yayi,tare da videos,yawanci duk na ban dariya ne,wasu yana a kwance,wasu ya zullo harshe waje,wasu hotunan ya kashe idanunshi,   Dariya ta dinga yi a yayin da take kallon videos ɗinshi na tiktok,duk yana sauraron sautin dariyarta,wani lokacin har satar kallon fuskarta yakeyi,ba ƙaramin kyau tayi mashi ba,musamman inta tuntsire da dariya,wani sa'in hada kifa kanta saman laps dinta saboda tsabar dariya,murmushi kawai yayi tare da mayar da hankalinshi akan driving ɗin da yake yi,a haka har suka ƙarasa gida, Bayan hafsat ta katse kiran,ta Kifa kanta asaman pillow ɗinta,tare da fashewa da wani irin matsanancin kuka,dama ance dana sani ƙeya ce, Farkawa Aunty babba tayi da wata irin matsiyaciyar yunwa,sae faman hamma takeyi,tashi tayi daga zaune tare da kai hannu ta ɗauki wayarta tana cewa"Ko hayam ta tura mun da hoton?bari na duba na gani,Allah yasa dai bata manta ba,"   shiga cikin whatsapp ɗinta tayi tare da duba chat ɗinsu da hayaam,rai a6ace taja dogon tsoki tare da cewa"Wai dama bata turamun hoton ba!harfa ƙara nanata mata nayi akan ta tura mun hoton amma bata turo ba," ta ƙarasa maganar tare da yin wurgi da wayar saman gadon,   Saukowa tayi daga saman gadon,fita tayi daga cikin bedroom din ta sauko ƙasa,kai tsaye ta nufi kitchen,   Batare da 6ata lokaci ba,ta shiga harhaɗa kayan da zatayi amfani dasu,bayan ta ɗaura girkin,ta ɗebo snacks a plate ta haɗo da coke mai sanyi ta dawo falo,ta zauna,tana ci tana kallo a plasma hankalinta kwance, jin motsin mutun a gefenta yasa tayi firgit tare da juyawa don taga wanene,ashe hafsat ce atsaye yanayinta kamar na wadda tayi amai da zawo,fuskar nan tayi gwanin ban tausayi,idanunta sun ƙankance saboda kukan da tasha,   "Hafsat!lafiya naga fuskarki tayi jawur?kinyi kuka ne"?   Girgiza kai hafsat tayi tare da cewa"Babu komai mommy,wani film nake kallo acikin wayata,shine ya sanya ni kuka,"   Tsoki Aunty babba taja"shirmen banza,kawai daga kallon film saiki kama kuka kamar wata sakarya,"   murmushin takaici hafsat tayi tare da samun wuri daga gefen aunty babba ta zauna,batare da tace komai ba,    Aunty babba taci gaba da cewa"gaskiya kowane film ne wannan ya ciri tuta tunda har ya iya sanyaki zubar da hawayenki,yadda kike da shegen taurin kai,     "Mommy ba zaki gane bane," "Taya za'ae in gane?tunda bakiyi mun bayanin meya faru ,acikin film ɗin ba,ki ɗan bani labari mana,"   Gyara zama hafsat tayi kafin ta soma bata labarin kamar haka"wata matace fa,mijinta ya kawo mata wasu marayun yara donta rainesu a wurinta,tun ranar da mijin ya kawosu gidan shi kuma yayi tafiya,ae kuwa matar nan,ta shiga gana masu azaba,ta hanasu abinci yunwa kamar zata kashesu,har bugunsu takeyi,sannan kuma ta dinga sanyasu aikin wahala,har saida suka kusa rasa rayuwarsu,mommy kinsan meya faru"?   Dakatawa Aunty babba tayi daga shan lemun hannunta da takeyi tace"a'a saikin faɗa,"   "Hmmm,Mommy ƙarshe fa matar nan,tasa aka kwashe yaran nan,aka 6atar dasu saboda kawai kar asirinta ya tonu a wurin mijinta...'   "Hakan da tayi yayi mun dai dai,"Acewar aunty babba, Murmushi hafsa tayi kamin tace"Ae ban ƙarasa maki labarin film ɗin ba,bayan tasa an zubar da yaran nan,ita duk a tunaninta sun mutu ma,Ashe can wurin gararin rayuwar da sukeyi a daji Allah ya haɗasu da kanin mijinta har ya taimakesu ya kaisu gidansu mijin,da akayi bincike aka gano cewar yaran ƴa'ƴan kawunsu ne wato ƙanin mahaifinsu,"   Aunty babba tace"tashin hankali!ita ko wannan ya zatayi da kanta?   Dariya hafsat tayi tare da cewa"Nima abunda nake tunani kenan!amma Mommy idan kece ya zakiyi,"   shiru Aunty babba tayi tana tunani kafin daga bisani tace"Ae kawai tunkan asirina ya tonu zan gudu ne,a neme ni arasa,amma nikam hafsat wai ya sunan Film ɗin nan ne?tayi tambayar tare da kallon hafsat ɗin wadda itama kallonta takeyi,mikewa hafsat tayi tsaye tare da cewa"An fara kiran sallar magriba,bari naje nayi salla,"   "Amma baki faɗamun sunan film ɗin ba!"Aunty babba ce ta sake nanata mata tambayar da tayi mata,     *AN YANKA TA TASHI* shine sunan film ɗin mommy,yanzu na kalleshi a tashar youtube,tana kai ƙarshen maganarta,ta juya da sauri ta wuce bedroom ɗinta,   Zugudum Aunty babba tayi tana maimaita sunan film ɗin da hafsat ta faɗa mata,wato An yanka ta tashi,   Aranta tace"gaskiya ya kamata in kalli film ɗin nan,Inaso inga yadda matar nan zata ƙare,ko ya mijinta zaiyi da ita?tabɗijancan,akwai badaƙala,"tayi maganar tare da mikewa ta wuce kitchen domin ta duba girkin da ta ɗaura, Bayan ta kuma fitowa daga kitchen ɗin,upstairs ta wuce bedroom ɗinta,gefen gadon ta zauna tare da miƙa hannunta ajikin drawer chest ta janyo gidan farko,sabon sim ne ta ɗauko tare da daukar wayarta dake ajiye saman gadon,zura sim card ɗin tayi aciki,sannan ta lalubo lambar wayar Ammi wadda tayi copying kan phone,danna mata kira tayi,nan take kiran ya shiga,kusan sau uku kiran na katsewa batare da anyi picking ɗinsa ba,tana kira a karo na hutu Ammi ta ɗaga kiran 😳 ɗan zaro ido Aunty babba tayi kafin ta gyara natsuwarta tare da zabga sallama"Assalamu Alaikum Ammi barka da warhaka,"ta maƙe muryarta yadda ammi bazata iya gane muryar wacece ba,   on the other hand Ammi ta amsa mata da cewa"Wa'alaikumus salam,barkanki dai,zan iya sanin dawa nake magana"a dake take magana, Aunty babba tace"Nasan bakisan dawa kike magana ba,saboda baki sanni ba,Ni matar abokin Abusufyan ce,wadda ke zaune a ƙasar turkey,"   Shiru ammi tayi tana sauraran me magana,   Aunty babba taci gaba da cewa"akwai wani mummunan abu da abusufyan ya aikata a 6oye baison kowa ya sani,shiyasa na kira don in sanar dake,don banason abunda zai ta6a mutuncin family ɗinku,wannan abun kunya ne,muddin ya fita waje mutane sukaji to fa,zaku rasa duk wata ƙima da martaba da kuke da ita....'   tana cikin magana Ammi ta dakatar da ita"Ya isa haka!banason wata kwanana,ki faɗamun abunda kikeson sanar dani!me Abusufyan ya aikata?wani laifi ne wannan da har kike ikirarin zai ta6a ƙimar family ɗinmu a idon jama'a,"?   Wani irin wahalallen yawu aunty babba ta haɗiye kafin daƙyar ta soma kora mata jawabi kamar haka    "Shekarun baya da dadewa,Abusufyan yayi ma wata fyaɗe,harta samu ciki....."   Wata irin tsawa da Ammi ta daka mata har sae da takusa sakin fitsari a wando,a tsiwace tace"Dakata!ki iya bakinki!kinaso ki shiga tsakanina da ɗana ne!wacece ke,kada kiyi tunanin kin kirani da 6oyayyiyar number,zan iya sa agano munke duk inda kike,"   Muryar Aunty babba na kerma tashiga faɗin"wlh dagaske nake ammi ba ƙarya nake ba,gobe idan kinzo abuja wurin walima,zaki ga yaran,ae suna nan gidan Abba,Sun jima suna 6oye maki gaskiya,saboda tsoron hukuncin da zaki yanke ma Abusufyan,yanzu haka maganar da nake maki,sun gama shirya yi maki ƙaryar cewar yaran ba shaggu bane ta hanyar aure aka haife su bayan ba haka bane,suna nan yaran ƴan uku ne mata,sun girma sosai,' tana kai ƙarshen maganar Ammi tace"Kin gama"?   Shiru Aunty babba tayi tana faman mazurai aranta tace"Wannan tsohuwa badae taurin kai ba,bansan ya zanyi na fahimtar da ita ba,ta cika jaraba,"   tana cikin wannan zancen zucin Ammi ta katse kiran,   Wurgi Aunty babba tayi da wayarta,tare da mikewa tana cewa"Ae shikenan,nasan cewa gobe tana ganin yaran zata tuna da kalamai na,daga nan saita ɗauki hukuncin daya dace," ❤🤍❤ *Boss Bature* Zaune yake asaman Sofa mai mazaunin mutun uku,gaba ɗaya ya tattara hankalinshi akan Laptop ɗinshi da yake daddawana anatse,jikin shi na sanye da linen tank top,blue colour tabi shape din jikinsa,sick pack din nan nasa ya bayyana ajikin rigar,trouser ɗin jikinsa kuma white colour ne,wani irin daddaɗan ƙamshi ne ke fitowa daga kowani sashe na jikinsa, Shigowa Azmee tayi part ɗin nasa da sallama a bakinta,yayin da hannunta ke ruke da tray,amsa mata sallamar yayi batare daya ɗago ya kalleta ba,ƙarasawa azmee tayi tare da ajiye mashi tray ɗin asaman empty table din dake a gefenshi,hannu takai tare da ciro plate ta daukko serving spoon tana ƙokarin buɗe warmer,muryarshi ta katse mata hanzarinta da cewa"ɗazu da safe meyasa kika kawomin breakfast?kuma kika gyaramun bedroom ɗina,dama kece ke gyara mun part ɗina ne"? gabanta ne taji ya faɗi rass,muryarta na kerma tace"A'a bani bace,Sehrish ce," "Meya hanata yi mun aiki,"?yana magana yana danna laptop dinsa har time ɗin bai ɗago da idonshi ba ya kalle ta, Azmee tace"Am...um...dama..."bata ƙarasa maganar ba,ya dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannunshi,cikin sauri ta shiga taitayinta, Cike da bada Umarni yace"Call her right now," Jiki na rawa azmee ta juya tare da fucewa daga part dinsa,downstairs ta saukko,babu kowa a falon duk suna a bedroom ɗinsu,wasu ma sunyi bacci, Kai tsaye ɗakinsu Sehrish taje,tsayawa tayi abakin ƙopar ɗakin tana kwankwasawa,sai faman knocking takeyi amma ba'a buɗe mata kopar ba,da alama sun jima da yin bacci, Har sae da ta fidda rai da za'a buɗe mata kopar,tana kokarin juyawa tabar wurin,taji alamun za'a buɗe kopar,Jahad ce ta buɗe ɗakin tana tambayar wanene, Ganin azmee yasa tayi saurin gaishe da ita cikin girmamawa, Azmee da nan take ta gane ba sehrish bace tace"kiyi hakuri na tashe ki kina bacci,Sehrish nake nema,dan Allah ki sanar da ita cewa SGR yana nemanta a part ɗinsa," Jahad tace"tayi bacci,bari na tashe ta,"tayi maganar tare da juyawa cikin sauri ta shiga cikin ɗakin, Wucewa azmee tayi ta koma kitchen,cike da zullumin mai zai biyo ba idan Sehrish ta sanar ma Sgr cewa Uncle abusufyan ne ya hanata yin aiki a part ɗinsa,tabbas za'a kwashi ƴan kwallo, "Sehrish!ki tashi babban yaya yana son ganinki a part ɗinsa,dan Allah ki tashi kije,"jahad ce keta kokarin tashinta daga bacci,sehrish kuwa sai faman mutsu mutsu takeyi,daƙyar ta iya cewa"Wanene ke nema ne'? Jahad tace"babban yaya," Jin sunanshi yasa Sehrish buɗe idanunta ta wurgasu kan jahad dake tsaye,yatsina fuska tayi tare da maimaita sunan nashi"babban yaya?shike nema na,waya faɗa maki"? "Aunty azmee,yanzun nan bata jima da tafiya ba,naga kamar ma bata acikin natsuwarta," Jin hakan yasa gaban sehrish faɗuwa rass,yunkurawa tayi tare da mikewa zaune,ta saukko da ƙafafunta ƙasa,kafin ta miƙe tsaye,saboda tsabar saurin ta fita ko Mayafi bata ɗauka ba,gashi kanta ko kallabi babu,sumar kanta ce da tasha gyara,an mayar mata da gashin mai gazar gazar ya sauko har kafaɗarta,a hankali gashin kan nata ke toho yana fitowa,har ta launin gashin anyi mata dying dinsa ya koma 2 colour,Kayan bacci ne ajikinta riga da wando sharara suke,farare masu laushin gaske,irin waɗanda kana sanyasu ajikinka,Ko baka jin bacci nan take zai zo maka, Tunkan ta ƙarasa shiga falon nashi take jin ɗar ɗar acikin zuciyarta,tun jiya rabon da ta sanyashi acikin idanunta,daƙyar ta iya yi mashi sallama tare da kutsa kai cikin falon nashi,bai amsa sallamarta ba,har ta ƙarasa inda yake,atsaye muryarta na rawa tace"Gani,"bai dago ba kuma bai tanka mata ba,sae ma cigaba da danna system ɗinshi da yake yi,lokaci bayan lokaci yakan kai hannunshi ya dauki Coffee ya kur6a,zuba mashi ido tayi tana kallon kyakkyawar fuskarshi,ba ƙaramin kewarshi tayi ba,sam batayi tunanin ma zai nemeta ba, sai da ta ƙara cewa"babban yaya gani,Aunty azmee tace kana kira na,"sannan ya soma magana anatse"yau da safe,meya hanaki zuwa part ɗina"? Shiru tayi gabanta na faɗuwa,batasan amsar da zata bashi ba,saboda tsoran abunda zai biyo baya, "Kinsan bana maimaita magana,amsarki nake jira," Runtse idanunta tayi aranta tana fadin"nashiga uku,!Allah ka kawomin ɗauki,bansan me zan faɗa masa ba,"shirun da tayi mashi ne ya fusata shi,aikuwa a zafafe ya daka mata tsawa,har sai da ta zura da gudu saboda yarda ta tsorata,kama hanyar fita tayi saboda ruɗewar da tayi,hakan yasa ya miƙe tsaye tare da bin bayanta,ruƙo hannunta yayi tare da fusgota ta dawo saitin shi,Waro ido waje tayi tare da ja da baya da baya,har suka ƙure ma bangon,runtse idonta tayi muryarta na kerma tashiga faɗin"Am so sorry babban yaya,I can explain,zan faɗa maka," A hankali ya ware blue eyes ɗinshi akan fuskarta,sumar kanta yabi da kallo,yayi mamakin ganin yadda gashin yayi tsayi cikin ƙankanin lokaci har ya kamo kafaɗarta,gyaran gashin da akayi mata ya ƙara fiddo da kyawun fuskarta,mayar da idanunshi yayi akan La66anta dake ta faman kerma duk tabi ta gigice,lokaci guda ya tsinci kanshi cikin wani irin yanayi mara misaltuwa,moving ya ƙarayi gaba ɗaya yayi mata rumfa da faffaɗan ƙirjinshi,lokacin da taji tsinin hancinshi na gogar nata,nan take gabanta ya kuma bugawa daramm,jikinta ya shiga yin kerma ta ko'ina,gaba ɗaya duk tabi ta susuce har lokacin ta gaza buɗe idanunta saboda tsabar tsoro,jin saukar hannunshi asaman ƙirjinta yasa ta yin saurin ware idanunta arazane,kai tsaye suka sauka cikin nashi,face to face,Eyes to eyes,nose to nose,mouth to mouth!!, A firgice ta janye idanunta daga kan fuskarshi ta mayar dasu akan ƙirjinta,Ashe gaban rigarta ne ta bari a buɗe ta manta bata sanya links ɗin rigar ba,Shine ya sanya hannunshi a wurin yana manne mata su,jurewa kawai takeyi amma ba ƙaramin yanayi Sgr ya jefa mata ba,musamman yadda hannunshi ke nutsewa a cikin boobs ɗinta,ba ita kaɗae ba,hatta shi kanshi daya kai hannunshi wurin saida yayi regretting,saboda wani abu daya dinga jin yana fisgarshi yadda kasan magnet,mayen karfe ba, daƙyar ya iya zame hannunshi daga saman ƙirjin nata,bayan ya kammala sanya mata links ɗin,Sannan cikin sanyin murya yace"tell me the reason why baki zo yi mun aiki da safe ba!bakisan bana son sharing a aiki na ba!? Magana yakeyi amma idanunshi sae ƙokarin lumshewa sukeyi tamkar mai jin bacci,wanda kuma ba kowa ne yajawo hakan ba face Sehrish, Cikin en ena tace"Kayi haƙuri ba laifina bane,Daddy ne ya hanani zuwa" Cike da mamaki yace"Kina nufin Uncle ne ya hanaki zuwa," Jinjina mashi kai tayi alamar eh,yayin da take ta faman haɗiyar yawu, . "just without any reason ya hanaki aiki a ƙarƙashi na"? daga mashi kai tayi alamar eh, Cije pink lips ɗinsa yayi tare da tsoma hannunshi acikin sumar kanshi yana cakuɗata,ranshi a matuƙar 6ace yace"hakan bazai ta6a yiyuwa ba,dole kiyi aiki a ƙarƙashina!ban damu da matsayinshi a wurinki ba,dole ne ayimun biyayya!!!!!!!!* *Tashin hankalin da ba'a sama shi date!* Gobe walima,suwa suka shirya zuwa💃💃💃💃 *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. [1/3, 6:34 AM] Abue Saleh AlQuyraemey: *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* ❤🤍❤ *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Hannu yasa tare da tallabo fuskarta yace"Hosana bada sani na nayi maki hakan ba,laifin ki ne,meyasa zaki toshe mun hancina?so kike na mutu'? Girgiza kai tayi"a'a,banso ka mutu,ae ni wasa nayi maka ko,"tayi maganar tana satar kallon fuskarshi,   "Faɗa mun me ya kawoki bedroom ɗina har saman gadona"?    A ƙule tace"nifa nazo ne na tashe ka don kaje ka ci abinci,naga kowa ya fito banda kai,kuma zasu iya cinye abincin duka," fuskarshi ɗauke da murmushi yace"Waya faɗa maki za'a cinye abincin,ae ko ban fita ba Azmee zata kawo mun ne har cikin part ɗina,"     Shiru tayi tana faman sauke ajiyar zuciya,ɗagowa ta ƙara yi zata saci kallonshi suka haɗa ido,ganin yadda yake kallonta ko ƙyaftawa baiyi hakan yasa ta ɗaure fuska cikin shagwa6a tace"Ya omar wannan kallon fa,ka wani tsare ni da ido,"   yadda tayi maganar ba ƙaramin burgeshi tayi ba,ya jima yana kallonta batare da yace wani abu ba,har sai da ta hasala rai a6ace tace"shikenan tunda ba zaka mun magana ba,bari na tashi na tafi,dama ko abincina banci ba,saboda kawai inzo in tashe ka daga bacci,amma ko farin ciki ba kayi ba,'   Ajiyar zuciya ya sauke tare da ruƙo hannunta cikin nashi"Hosana,so nake ki faɗa mun gaskiya,kina sona da gaske?kuma zaki aure ni? Waro ido waje hosana tayi tana kyakkyaftasu kamar na ƴar tsana jin abunda yace,a ruɗe tace"Ya Omar!aure fa!"_ Jinjina mata kai yayi tare da cewa"eh,aure hosana ko baki shirya ba,"   Turo baki ta ɗanyi tana ƙunƙuni ƙasa ƙasa,hankalinsa kam harya ɗan tashi saboda ganin yadda ta tsorata don yayi mata zancen aure,dama fargabarsa kada sai anje wurin nema mashi auranta tace bata shirya ba,don yasan ba cikakken hankali gare ta ba, Lalla6ata ya shiga yi"pls hosana,ki faɗamun gaskiya,zaki aure ni"?   daƙyar ta iya buɗe baki tace"Ni yanzu tashi zanyi in tafi,dama zuwa nayi fa don in tambayeka,wani kalar ƙunshi kake so ayimun baƙi ko ja,"    ya lura cewa batason zancen auren shiyasa ta kawo maganar ƙunshin,cikin sanyin murya yace"Nafison jan lalle zai fi yi maki kyau,kuma ba mai yawa ba ƙunshin,ƴar flower kawai za'a zana maki mai kyau,"   Yana kai ƙarshen maganar,hosana ta miƙe tana faman shan ƙamshi,da sauri ta juya ta bar bedroom ɗin nashi,bin bayanta yayi da kallo har ta fuce,jiki asanyaye ya miƙe tare da nufar toilet ya shige,    Hosana na fita daga cikin bedroom ɗin nashi,a falonsa ta tsaya tana faman zabga murmushi,tsabar farin ciki kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha,Yau ya Omar ya nuna yana sonta harma yanayi mata zancen aure,ta rasa ma wa zata fara faɗamawa,sai faman zagaye zagaye takeyi a cikin falon, Wuraren ƙarfe biyu da rabi na rana,Abusufyan ya ɗaukesu acikin motarshi kamar yadda yayi masu alƙwarin kaisu wurin saloon da kanshi,hosana da jahad suna a bayan motar duk sun ɗau wankan jallabiya sun laga mayafi,Sehrish na agaban motar kusa da driver seat inda Uncle abusufyan ke zaune yana driving ɗinsu anatse,Su jahad da hosana sae fira sukeyi tare dashi,amma ita ko uffan bata tanka masu ba,dama tunda ta shigo cikin motar Abusufyan ya lura da yanayinta, gyaran murya yayi mata hakan yasa ta ɗan dago da kanta ta kalle shi,   "Meyake damunki ne Daughter?tunda kika shigo cikin motar nan baki tanka mana ba,ga ƴan uwanki suna ta fira a tsakaninsu amma ban dake".   Muryarta asanyaye tace"Babu komai,"   "ko don saboda na hana ki kai ma Sgr abinci ne"? Yayi maganar batare daya kalleta,   Cikin sauri tace"a'a ba haka bane,kawai bana jin daɗin jikina ne,"   "Ban yarda ba daughter,saboda shi ne yasa kika shiga damuwa,"_   Shiru tayi bata ce komai ba,murmushi abusufyan yayi kafin yace"banyi hakan don na takura maki ba,face don na ɗaukaka darajarki,nasan ba zaki fahimce ni ba a yanzu amma nan gaba da kanki zakiyi mun godiya akan hakan,idan kuma hakan ya 6ata maki rai,kiyi haƙuri,'ya ƙarasa maganar adai dai lokacin da suka ƙaraso wurin Saloon ɗin,parking ɗin motar yayi jahad da hosana suka fita waje,tana ƙoƙarin buɗe motar ta fita ya ambaci sunanta"Sehrish,"juyowa tayi tare da kallon fuskar daddyn nasu tace"Na'am daddy,"   "Murmushi kawai nakeso kiyi mun kafin ki fita," fashewa tayi da dariya har fararen hakoranta suka bayyana,duk a tunaninta wani abu mai muhimmanci ne yasa ya kirata,ashe kawai don ya tambayi murmushinta ne,shima dariyar yakeyi,kafin su fita daga cikin motar atare, ************** Fitowarshi kenan daga wanka,yana cikin shirya kanshi cikin riga da wandon jeans,yaji an kwankwasa ƙopar ɗakinshi,daga muryarshi yayi tare da cewa"ƙopar a buɗe take,"yayi maganar tare da juyawa yana kallon mai shigowar,   Cike da mamaki yace"Ya HAROON!kaine!dama kana nan," Shu'umin murmushin nan nashi ya saki tare da ƙarasa shiga cikin bedroom ɗin nashi yana cewa"Ina nan mana junaid,kaine ka manta dani,kowa ma ya manta dani,"   "Ya haroon ba haka bane,wlh ni ban manta dakai ba,kana araina,"   ta6e baki haroon yayi alokacin da yake tsayawa agaban junaid suna fuskantar juna yace"Ka ƙara kyau da haske,hankalinka kwance baka da wata damuwa,ba kamar ni ba,kullum cikin damuwa nake,zuciyata har nauyi takeyi mun saboda halin da nake ciki amma babu wanda ya damu dani,yau ko mutuwa nayi babu wanda zai damu,sae ma farin ciki da za'ayi,"   Jin wannan maganar ta haroon yasa jikin junaid yin sanyi,wani irin tausayin shi ya kamashi,muryarshi tamkar zaiyi kuka yace"pls Ya haroon dan Allah kadaina faɗin wannan maganganun,wlh bana jin daɗi,"   "Junaid ƙarya nayi ne?an damu dani acikin gidan nan ne?kowa yayi watsi dani,babu wanda ke damuwa dani,tamkar bare haka nakeyin rayuwata,hatta azmee da take ƴar aiki acikin gidan nan ta fi ni muhimmanci tunda ita ana damuwa da ita,ni kuwa fa?   Hawaye ne suka cicciko a idanun junaid,dama shi akwai tausayi,gaba ɗaya tausayin haroon ya kamashi,saboda duk abunda ya faɗi gaskiya ne,ba'a damu dashi ba,ko zancen shi ma babu maiyi acikin gidan,idan zai share wata a waje babu mai tambayar ina yaje,   "Tamkar maraya ni fa haka nake acikin gidan nan,kalli kaga yadda na koma duk na rame saboda damuwa,gaskiya ni bazan iya cigaba da rayuwa ba junaid,zan kashe kaina ne kowa ya huta," yana kai ƙarshen maganarshi ya juya da sauri zai bar ɗakin,   Da gudun gaske junaid ya rungumoshi ta baya tare da fashewa da matsanancin kuka yana cewa"Meyasa ya Haroon!pls stop saying that,banason jin kana zancen mutuwa,ko kowa bai damu dakai ba,Ni nadamu dakai,ko don saboda ni ya haroon kada ka aikata hakan,idan ka kashe kanka,nima bazan rayuwa ba,zan bi ka mu tafi tare,"   Wannan kalaman na junaid ba ƙaramin sanyaya mashi zuciya su kayi ba,cire hannunshi yayi daga ruƙon da yayi ma waist dinshi,sannan ya juya suna fuskantar juna yace"Junaid dagaske ne ka damu dani?kuma bakaso in mutu"?   cikin shessheƙar kuka junaid yace"Eh ya haroon bana so pls,"   Hannu haroon yasa yana share mashi hawayenshi,kafin daga bisani ya janyo shi ajikinshi tare da rungume shi sosai ajikinshi,kamar zai mayar dashi cikin shi,saitin kunnanshi yakai bakinshi tare da cewa"I love u so much junaid,cos you're so special,in dai zan kasance tare dakai bazan ta6a shiga wani ƙunci na rayuwa ba,kallon ka kawai zai iya sanya farin ciki a cikin zuciyata,daga yanzu inason ka zama abokina junaid,saboda ka dinga ɗebe mun kewa,muna fita yawo atare,don bani da aboki,nifa kowa gudu na yake yi,bansan meyasa ba,'ya ƙarasa maganar tare da janye junaid daga jikinshi,   "Junaid!ka amince zaka zama abokina"? Jinjia kai junaid yayi tare da cewa"Eh,na amince,amma dan Allah ya haroon kadaina zancen zaka kashe kanka,banjin daɗi banso pls,"   "Shikenan na daina,daga yau kome kakeso ma zanyi,am sorry na sanyaka zubar da hawayenka,"   "Ya haroon ni zanje nayi ma Abba magana akanka,nasan abba zai fahimce ni,"   cikin sauri haroon ya ruƙo hannun shi tare da cewa"A'a junaid,just leave it,banason kowa yasan meke tsakanina dakai,kada kayi ma kowa maganata don ba lalle su fahimce ni kaman yadda kai ka fahimce ni ba,"   "Shikenan bazan faɗa ba," "Yawwa junaid ɗina,Yanzu zan barka ka ƙarasa shiryawa,"   Yana faɗin hakan ya juya tare da fucewa daga ɗakin junaid,ya koma bedroom ɗinsa,agaban dressing mirror ɗinshi ya tsaya yana ƙarewa fuskarshi kallo,   A hankali wannan mugun murmushin nashi ya soma bayyana akan fuskarshi,fashewa yayi da dariya kafin daga bisani ya ɗaure fuskarshi,kalaman junaid ya shiga tariyowa,tuni jikinshi yayi sanyi,ta wani 6angaren ji yake tamkar bazai iya ba,amma bai da wata mafita daya wuce wannan!   "Junaid kada ka damu zamu mutu atare,"ya faɗi hakan tare da komawa ya zauna daga gefen gadonshi, Bayan junaid ya kammala shiryawa,saukowa downstairs yayi har lokacin jikinshi ba kwari,haroon ba ƙaramin tausayi ya bashi ba,A main palor ya samu Abbansu tare da Momnynsu dasu Twins suna fira atsakaninsu,tunkararsu yayi fuskarshi ɗauke da murmushi,suna haɗa ido da Abbansu ya watsa mashi harara,sunnar da kai ƙasa junaid yayi da wurin Abban yaso ya fara zuwa amma wannan hararar da yayi mashi ce tasa ya fasa zuwa ya wuce wurin mommynsu,dukawa yayi tare da manna mata kiss kafin ya rungumeta,fuskarta asake tace"My romeo,"Amsa mata yayi da mommy,a lokacin daya koma wurinsu twins suna gaisawa,Jahan yace"Ina zuwa naga key ɗin mota a hannunka," "Zanbi su uncle ne," ayaan yace"Kada ka bari Mommy taji to,in ba haka ba bazata bari kabi su ba,"     "Saboda me"?ya tambaya yana kallonshi,Jahan ne ya bashi amsa da cewa"Saboda bazata barka ba,idan ta tambayeka ina zaka je,sae kace mata gidan abokinka zakaje,"duk wannan maganar da sukeyi a kunnan abbansu saboda yana kusa dasu,kallonsu kawai yakeyi,juyawa junaid ya ɗanyi tare da satar kallon mommyn,idonta na akanshi hakan ya tabbatar mashi da cewar so take taji me suke cewa,'   "Ka tafi kawai,"acewar ayaan,   harya juya zai tafi ya tuna da Abbansu,dawowa yayi tare da zuƙunnawa agabanshi yace"Abba,"ɗaure fuska abba yayi batare da ya tanka mashi ba,   "dan Allah kayi haƙuri abba in na 6ata maka rai,bazan ƙara ba,"   Ta6e baki abba yayi tare da cewa"Junaid kenan,ae ni yanzu babu ruwana dakai,kafi ƙarfi na,"_   Ashagwa6e ya kuma cewa"pls abba,kayi hakuri,ka manta da abunda ya faru jiya,bazan ƙara ba,"     "Naji,tashi ka tafi,ka kulamun da kanka,"   Murmushi junaid ya saki tare da mikewa ya manna mashi kiss a fuskarshi,sannan cikin sauri ya kama hanyar fita,   "Junaid ina zuwa"? Jin muryar Momnynsu yasa shi dakatawa da tafiyar da yake yi,    tsayawa yayi tare da juyawo ya kalleta,    "Mommy gidansu abokina zani je,"   "Kai da wa?waye zai kai ka? Nuna mata key ɗin motarshi yayi kafin yace"Ni zan kai kaina," Jinjina kai tayi tare da cewa"Okey,u can go," da sauri ya fuce daga cikin gidan,   Mayar da idanunta tayi akan abbansu tace"Dama inaso inyi magana dakai,wai meyasa kuka bar romeo yana Driving da kanshi?Also babu wani security guard dake tsaronsa,Shi kadae yake yawonshi,"   Abba yace"Allah xai tsare mana shi," Alexandra tace"Nasan da wannan,Amma wannan babban ganganci ne,koda ace kowanne daga cikinsu zaiyi yawonshi batare da security guards ba,amma bai kamata ace kamar junaid ƙaramin yaro yana yawo shi kaɗae ba,ba wani tsaro atare dashi,Especially yadda kowa ya sanya mashi ido,gaskiya ni hakan bai kwanta mun araina ba!!" shiru abbansu yayi yana nazarin maganarta,   Jahan yace"Gaskiya Abba,maganar mommy gaskiya ne,yakamata ace junaid akwai security guards dake tsaronsa duk inda zaije,musamman a wannan yanayin da muke ciki,bibiyar rayuwarmu akeyi don kawai acutar damu,junaid kuma yafi kowa ƙaranta acikinmu,yana buƙatar security,"   "Abunda nake ƙoƙarin fahimtar dashi kenan,"acewar mommnynsu,   jinjina kai Abba yayi tare da cewa"hakane,zanyi wani abu akai',    daga nan suka cigaba da tattauna a tsakaninsu, *Boss Bature* Tun bayan da Hayaam ta tura ma Aunty babba hotonsu hosana,bata samu damar duba hoton nasu ba,ko whatsapp ɗinta bata shiga ba,wayarma tana ajiye cikin bedroom ɗinta,Shirye shiryen zuwa walima kawai sukeyi,atare da hafsat suka fita saloon daga nan za'ayi masu ƙunshi,bayan nan kuma zasu biya Shopping mall,saboda siyayyar da tace zatayi ma Ƴa'ƴan uncle ɗinsu,basu suka dawo gidan ba sai wuraren karfe shida na yamma agajiye suka dawo,kowa ya wuce bedroom ɗinshi,Aunty babba na shiga ɗakinta,kai tsaye ta faɗa saman gadonta ta shiga sharar bacci,Hafsa kuwa saida ta fara yin wanka,ta canza kayan jikinta izuwa riga da skirt marasa nauyi,sannan ta fito falo ta kwashe shopping bags ɗin da suka bari a falo,takaisu ɗakinta,tana cikin dudduba kayan wayarta dake ajiye gaban mirror ta shiga ringing,hannu takai tare da ɗaukar wayar tana kallon screen ɗinta,ganin Sunan Aunty Hayaam ya bayyana akan secreen ɗin wayar,yasa ta ɗaga kiran tare da karawa a kunnanta,   "Assalamu Alaikum aunty hayaam,' Ko amsa mata sallamar batayi ba tace"Hafsat ina Aunty laila take ne?tun da sassafe na tura mata hoton bata duba ba,har nagaji da jira,"   Hafsat tace"yanzu muka dawo daga kasuwa agajiye,tana a bedroom ɗinta ina jin bacci ne ya dauketa,ko inyi mata magana ne"?   Hayaam tace"A'a,kawai idan ta tashi ki sanar da ita cewa na tura mata hoton ƴa'ƴan abusufyan ɗin,ta duba ta whatsapp ɗinta,"   Wani irin farin ciki ne ya lullu6e hafsat,muryarta na rawa tace"hoton ƴa'ƴan Abusufyan dinmu!zan sanar mata kuwa,"   Rejecting call ɗin tayi,da gudu ta fito daga bedroom ɗinta,kai tsaye ta haye upstairs ɗakin aunty babba,tura kopar ɗakin tayi tare da shigewa ciki,a kwance ta samu aunty babba saman gadonta sai sharar bacci takeyi,ga wayarta ajiye agefenta,   Cikin sanɗa takai hannu tare da ɗaukar wayar,ta danna power ɗinta ta kawo haske,ganin akwai password yasa ta ɗan bubbuga kafarta tana cewa"Kai mommy,yanzu dole sae kin tashi sannan zan samu damar ganin hoton babies ɗinmu!gaskiya ni a ƙagare nake,"   Tana cikin maganar,ta tuna da finger print ɗin dake akwai ajikin wayar,nan take zuciyarta ta bata shawarar cewar me zai hana,ta lalla6a ta hau saman gadon,ta dangwalo yatsan aunty babba,kota samu wayar ta buɗe,Good idea,ta furta hakan tare da lalla6awa ta hau saman gadon,cikin sanɗa ta ƙarasa inda aunty babbar take,hannunta ta ruƙo tare da sanya yatsan hannunta a wurin,ya rubuta mata wrong,haka ta dinga bin yatsun hannun aunty babba tana jarabawa,har sai da taci nasarar buɗe wayar,saukowa tayi daga saman gadon,ta tsaya atsaye,hannunta har kerma sukeyi wurin daddana wayar,tsoranta kar Aunty babba tafarka saboda tasan halin Mommyn nata,ta tsani wani ya ɗaukar mata wayarta,kamar mara gaskiya,    Tana shiga whatsapp ɗinta,sai ga wani security ɗin,rai a6ace tace"Mommy kamar mara gaskiya,duk tabi waya ta garƙame da security,"   Allah yaso shima finger print ne,komawa tayi tare da dangwalo yatsan aunty babba,whatsapp ɗin ya buɗe,   Kaitsaye ta shiga chat ɗinsu da Hayaam,anan taga hoton da Hayaam ta tura mata,bai buɗe ba hoton saboda data a kashe take,cikin sauri hafsat ta kunna data ɗin,nan take yashiga loading yana ƙoƙarin budewa,a hankali hoton ya soma bayyana,ƙura ido hafsat tayi tana jiran hoton ya kammala buɗewa,   Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu ji kake Daram!!Dararam!!tamkar ana buga ganga,Waro ido waje hafsat tayi agigice a matukar razane,tamkar wadda taga Zombie,hankali a matuƙar tashe tace"Kai!!!"   Hannunta har kerma yakeyi wurin yin zooming ɗin hoton nasu ta matso dashi kusa don tagani dakyau,gaba ɗaya tagama kiɗima,wata irin zufa ce  ta soma tsattsafo mata agefen fuskarta,daƙyar take iya haɗiye yawun bakinta saboda maƙoshinta daya bushe ƙamas,juyawa tayi ta kalli Aunty baba dake ta faman mutsu-mutsu alamar zata farka daga baccin da takeyi,aikuwa cikin sauri tayi deleting ɗin hoton gaba daya,sannan ta rufe wayar,tayi wurgi da ita asaman gadon,jikinta na kerma ta fuce daga dakin,gudu gudu sauri sauri haka take tattaka stairs ɗin ƙiris ya rage ma tayi tuntu6e saboda yadda jikinta ke rawa kafkaf kamar wadda sanyi ya kama,   Bedroom ɗinta ta koma,tana shiga ta aza hannu akai tana faɗin"Tashin hankali!In har dagaske ne abunda idanuna suka gane mun acikin hoton nan kenan hakan na nufin cewa HOSANA DA JAHAD Suna araye kuma suna a gidansu daddy!taya hakan ya faru?Kenan Ya Omar shine ya ɗaukesu?Ina wannan tsohon mutumin da mommy tasa ya kwashe su da nufin ya zubar dasu?Taya akai hosana da jahad suka kasance ƴa'ƴan uncle ɗinmu!?wacece ita ɗayar yarinyar mai kama dasu sak!dama su ƴan uku ne?Tabɗijancan,akwai matsala,   Komawa tayi gefen gadonta ta zauna tare da kifa hannunta asaman fuskarta,hosana da jahad suna raye,suna gidan abban mu,wayyo Allah na,ina farin ciki sosai,duk da ina tsoran abunda zai biyo baya,Ashe jinina ne su!shiyasa akace rashin sani yafi dare duhu,mun cutar dasu sosai,mun zalunce su bayin Allah,mutuwa ce kawai batazo ta daukesu ba acikin gidan nan amma sunsha wahala,sun ƙuntata,tabbas Mommy mun shiga uku,idan Abba yaji,daga ni harke ba wanda zai tsira,kwara ni hukuncina mai sauƙi ne tunda na nuna masu soyayya daga baya amma ita mommy itace silar fitar dasu daga gidan nan don azubar dasu,Wayyo Allah na!,   Yatsun hannunta sae faman kerma sukeyi,jiki na rawa ta ɗauki wayarta tare da lalubar numbar junaid ta danna mashi kira,   A lokacin junaid yana tare dasu Uncle abusufyan,dama sai daya fara kiranshi a waya ya tambayi address ɗin inda suke ya bashi,har an kammala yi masu saloon tuntuni,anyi masu ƙunshin jan lalle a hannuwansu,daga can suka wuce shoprite siyayya,bayan sun kammala siyayyar,suka biya gidan Uncle ɗin nasu wuraren 6,saboda su kwaso wasu daga cikin kayansu Jahad da hosana wanda zasuyi kwalliyar walima dasu,   A bayan motar junaid aka sanya trolley ɗin kayan nasu,sannan Sehrish da hosana suka shige motar abusufyan,jahad kuma ta shiga motar junaid,atare motocinsu suka fita daga cikin gidan,   Tunda jahad ta shiga motarshi,ya ɗaure fuskarshi,dama tun wurin siyayyar yake ta shan mur yana murtuke mata fuska,amma hakan bai hana tayi masa magana ba,duk in ta ɗauko abu sai ta gwada mashi ta tambayeshi zaiyi mata kyau,daƙyar yake amsa mata da eh,ko a'a,sai dae kawai tayi murmushi ta girgiza kai,     Kiran Hafsat na shigowa a wayarshi,yace"ki ɗauki wayar,ki amsa wayar sai ki sanyata a handsfree,"    hannu jahad tasa tare da ciro wayar daga aljihun gaban rigarshi,picking call ɗin tayi bayan ta sanyata handsfree sannan tayi Mata sallama,    Muryar hafsat ce ta karaɗe kunnansu"Junaid!kana ina ne"? Gaban jahad ne ya faɗi rass saboda jin muryar hafsat,duk da bata tabbatar da cewar ita bace,amma muryar tayi mata kama da ta sister hafsat,   "Ina akan hanyar komawa gida ne yanzu hakan,"    Hafsat tace"junaid dan Allah so nake in tambayeka,waɗannan yaran ƴa'ƴan uncle abusufyan Ƴan uku ne"?   "Of course they are triplet,"ya bata amsa a yayin da yake ƙoƙarin juya sitiyarin motar,ya karya kwana,   Hafsat tace"Ya sunan su"! Juyowa yayi ya ɗan kalli jahad da idanunta ke akan shi,kafin ya mayar da idanunshi kan driving din da yakeyi,a jere ya ambaci sunayensu"Hosana Sehrish Jahad"!hafsat na jin haka,a gigice ta kashe wayar,   "kiran ya katse,"Jahad ta faɗi tana ƙare ma wayar kallo,   "May be network ne,idan na koma gidan zan kirata,"    "In mayar maka da wayar"?   "A'a ki ruƙe a wurinki,idan mun isa gida zan kar6a,"   ta amsa mashi da toh, Gallery ɗinshi ta shiga tana kallon kyawawan hotunanshi da yayi,tare da videos,yawanci duk na ban dariya ne,wasu yana a kwance,wasu ya zullo harshe waje,wasu hotunan ya kashe idanunshi,   Dariya ta dinga yi a yayin da take kallon videos ɗinshi na tiktok,duk yana sauraron sautin dariyarta,wani lokacin har satar kallon fuskarta yakeyi,ba ƙaramin kyau tayi mashi ba,musamman inta tuntsire da dariya,wani sa'in hada kifa kanta saman laps dinta saboda tsabar dariya,murmushi kawai yayi tare da mayar da hankalinshi akan driving ɗin da yake yi,a haka har suka ƙarasa gida, Bayan hafsat ta katse kiran,ta Kifa kanta asaman pillow ɗinta,tare da fashewa da wani irin matsanancin kuka,dama ance dana sani ƙeya ce, Farkawa Aunty babba tayi da wata irin matsiyaciyar yunwa,sae faman hamma takeyi,tashi tayi daga zaune tare da kai hannu ta ɗauki wayarta tana cewa"Ko hayam ta tura mun da hoton?bari na duba na gani,Allah yasa dai bata manta ba,"   shiga cikin whatsapp ɗinta tayi tare da duba chat ɗinsu da hayaam,rai a6ace taja dogon tsoki tare da cewa"Wai dama bata turamun hoton ba!harfa ƙara nanata mata nayi akan ta tura mun hoton amma bata turo ba," ta ƙarasa maganar tare da yin wurgi da wayar saman gadon,   Saukowa tayi daga saman gadon,fita tayi daga cikin bedroom din ta sauko ƙasa,kai tsaye ta nufi kitchen,   Batare da 6ata lokaci ba,ta shiga harhaɗa kayan da zatayi amfani dasu,bayan ta ɗaura girkin,ta ɗebo snacks a plate ta haɗo da coke mai sanyi ta dawo falo,ta zauna,tana ci tana kallo a plasma hankalinta kwance, jin motsin mutun a gefenta yasa tayi firgit tare da juyawa don taga wanene,ashe hafsat ce atsaye yanayinta kamar na wadda tayi amai da zawo,fuskar nan tayi gwanin ban tausayi,idanunta sun ƙankance saboda kukan da tasha,   "Hafsat!lafiya naga fuskarki tayi jawur?kinyi kuka ne"?   Girgiza kai hafsat tayi tare da cewa"Babu komai mommy,wani film nake kallo acikin wayata,shine ya sanya ni kuka,"   Tsoki Aunty babba taja"shirmen banza,kawai daga kallon film saiki kama kuka kamar wata sakarya,"   murmushin takaici hafsat tayi tare da samun wuri daga gefen aunty babba ta zauna,batare da tace komai ba,    Aunty babba taci gaba da cewa"gaskiya kowane film ne wannan ya ciri tuta tunda har ya iya sanyaki zubar da hawayenki,yadda kike da shegen taurin kai,     "Mommy ba zaki gane bane," "Taya za'ae in gane?tunda bakiyi mun bayanin meya faru ,acikin film ɗin ba,ki ɗan bani labari mana,"   Gyara zama hafsat tayi kafin ta soma bata labarin kamar haka"wata matace fa,mijinta ya kawo mata wasu marayun yara donta rainesu a wurinta,tun ranar da mijin ya kawosu gidan shi kuma yayi tafiya,ae kuwa matar nan,ta shiga gana masu azaba,ta hanasu abinci yunwa kamar zata kashesu,har bugunsu takeyi,sannan kuma ta dinga sanyasu aikin wahala,har saida suka kusa rasa rayuwarsu,mommy kinsan meya faru"?   Dakatawa Aunty babba tayi daga shan lemun hannunta da takeyi tace"a'a saikin faɗa,"   "Hmmm,Mommy ƙarshe fa matar nan,tasa aka kwashe yaran nan,aka 6atar dasu saboda kawai kar asirinta ya tonu a wurin mijinta...'   "Hakan da tayi yayi mun dai dai,"Acewar aunty babba, Murmushi hafsa tayi kamin tace"Ae ban ƙarasa maki labarin film ɗin ba,bayan tasa an zubar da yaran nan,ita duk a tunaninta sun mutu ma,Ashe can wurin gararin rayuwar da sukeyi a daji Allah ya haɗasu da kanin mijinta har ya taimakesu ya kaisu gidansu mijin,da akayi bincike aka gano cewar yaran ƴa'ƴan kawunsu ne wato ƙanin mahaifinsu,"   Aunty babba tace"tashin hankali!ita ko wannan ya zatayi da kanta?   Dariya hafsat tayi tare da cewa"Nima abunda nake tunani kenan!amma Mommy idan kece ya zakiyi,"   shiru Aunty babba tayi tana tunani kafin daga bisani tace"Ae kawai tunkan asirina ya tonu zan gudu ne,a neme ni arasa,amma nikam hafsat wai ya sunan Film ɗin nan ne?tayi tambayar tare da kallon hafsat ɗin wadda itama kallonta takeyi,mikewa hafsat tayi tsaye tare da cewa"An fara kiran sallar magriba,bari naje nayi salla,"   "Amma baki faɗamun sunan film ɗin ba!"Aunty babba ce ta sake nanata mata tambayar da tayi mata,     *AN YANKA TA TASHI* shine sunan film ɗin mommy,yanzu na kalleshi a tashar youtube,tana kai ƙarshen maganarta,ta juya da sauri ta wuce bedroom ɗinta,   Zugudum Aunty babba tayi tana maimaita sunan film ɗin da hafsat ta faɗa mata,wato An yanka ta tashi,   Aranta tace"gaskiya ya kamata in kalli film ɗin nan,Inaso inga yadda matar nan zata ƙare,ko ya mijinta zaiyi da ita?tabɗijancan,akwai badaƙala,"tayi maganar tare da mikewa ta wuce kitchen domin ta duba girkin da ta ɗaura, Bayan ta kuma fitowa daga kitchen ɗin,upstairs ta wuce bedroom ɗinta,gefen gadon ta zauna tare da miƙa hannunta ajikin drawer chest ta janyo gidan farko,sabon sim ne ta ɗauko tare da daukar wayarta dake ajiye saman gadon,zura sim card ɗin tayi aciki,sannan ta lalubo lambar wayar Ammi wadda tayi copying kan phone,danna mata kira tayi,nan take kiran ya shiga,kusan sau uku kiran na katsewa batare da anyi picking ɗinsa ba,tana kira a karo na hutu Ammi ta ɗaga kiran 😳 ɗan zaro ido Aunty babba tayi kafin ta gyara natsuwarta tare da zabga sallama"Assalamu Alaikum Ammi barka da warhaka,"ta maƙe muryarta yadda ammi bazata iya gane muryar wacece ba,   on the other hand Ammi ta amsa mata da cewa"Wa'alaikumus salam,barkanki dai,zan iya sanin dawa nake magana"a dake take magana, Aunty babba tace"Nasan bakisan dawa kike magana ba,saboda baki sanni ba,Ni matar abokin Abusufyan ce,wadda ke zaune a ƙasar turkey,"   Shiru ammi tayi tana sauraran me magana,   Aunty babba taci gaba da cewa"akwai wani mummunan abu da abusufyan ya aikata a 6oye baison kowa ya sani,shiyasa na kira don in sanar dake,don banason abunda zai ta6a mutuncin family ɗinku,wannan abun kunya ne,muddin ya fita waje mutane sukaji to fa,zaku rasa duk wata ƙima da martaba da kuke da ita....'   tana cikin magana Ammi ta dakatar da ita"Ya isa haka!banason wata kwanana,ki faɗamun abunda kikeson sanar dani!me Abusufyan ya aikata?wani laifi ne wannan da har kike ikirarin zai ta6a ƙimar family ɗinmu a idon jama'a,"?   Wani irin wahalallen yawu aunty babba ta haɗiye kafin daƙyar ta soma kora mata jawabi kamar haka    "Shekarun baya da dadewa,Abusufyan yayi ma wata fyaɗe,harta samu ciki....."   Wata irin tsawa da Ammi ta daka mata har sae da takusa sakin fitsari a wando,a tsiwace tace"Dakata!ki iya bakinki!kinaso ki shiga tsakanina da ɗana ne!wacece ke,kada kiyi tunanin kin kirani da 6oyayyiyar number,zan iya sa agano munke duk inda kike,"   Muryar Aunty babba na kerma tashiga faɗin"wlh dagaske nake ammi ba ƙarya nake ba,gobe idan kinzo abuja wurin walima,zaki ga yaran,ae suna nan gidan Abba,Sun jima suna 6oye maki gaskiya,saboda tsoron hukuncin da zaki yanke ma Abusufyan,yanzu haka maganar da nake maki,sun gama shirya yi maki ƙaryar cewar yaran ba shaggu bane ta hanyar aure aka haife su bayan ba haka bane,suna nan yaran ƴan uku ne mata,sun girma sosai,' tana kai ƙarshen maganar Ammi tace"Kin gama"?   Shiru Aunty babba tayi tana faman mazurai aranta tace"Wannan tsohuwa badae taurin kai ba,bansan ya zanyi na fahimtar da ita ba,ta cika jaraba,"   tana cikin wannan zancen zucin Ammi ta katse kiran,   Wurgi Aunty babba tayi da wayarta,tare da mikewa tana cewa"Ae shikenan,nasan cewa gobe tana ganin yaran zata tuna da kalamai na,daga nan saita ɗauki hukuncin daya dace," ❤🤍❤ *Boss Bature* Zaune yake asaman Sofa mai mazaunin mutun uku,gaba ɗaya ya tattara hankalinshi akan Laptop ɗinshi da yake daddawana anatse,jikin shi na sanye da linen tank top,blue colour tabi shape din jikinsa,sick pack din nan nasa ya bayyana ajikin rigar,trouser ɗin jikinsa kuma white colour ne,wani irin daddaɗan ƙamshi ne ke fitowa daga kowani sashe na jikinsa, Shigowa Azmee tayi part ɗin nasa da sallama a bakinta,yayin da hannunta ke ruke da tray,amsa mata sallamar yayi batare daya ɗago ya kalleta ba,ƙarasawa azmee tayi tare da ajiye mashi tray ɗin asaman empty table din dake a gefenshi,hannu takai tare da ciro plate ta daukko serving spoon tana ƙokarin buɗe warmer,muryarshi ta katse mata hanzarinta da cewa"ɗazu da safe meyasa kika kawomin breakfast?kuma kika gyaramun bedroom ɗina,dama kece ke gyara mun part ɗina ne"? gabanta ne taji ya faɗi rass,muryarta na kerma tace"A'a bani bace,Sehrish ce," "Meya hanata yi mun aiki,"?yana magana yana danna laptop dinsa har time ɗin bai ɗago da idonshi ba ya kalle ta, Azmee tace"Am...um...dama..."bata ƙarasa maganar ba,ya dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannunshi,cikin sauri ta shiga taitayinta, Cike da bada Umarni yace"Call her right now," Jiki na rawa azmee ta juya tare da fucewa daga part dinsa,downstairs ta saukko,babu kowa a falon duk suna a bedroom ɗinsu,wasu ma sunyi bacci, Kai tsaye ɗakinsu Sehrish taje,tsayawa tayi abakin ƙopar ɗakin tana kwankwasawa,sai faman knocking takeyi amma ba'a buɗe mata kopar ba,da alama sun jima da yin bacci, Har sae da ta fidda rai da za'a buɗe mata kopar,tana kokarin juyawa tabar wurin,taji alamun za'a buɗe kopar,Jahad ce ta buɗe ɗakin tana tambayar wanene, Ganin azmee yasa tayi saurin gaishe da ita cikin girmamawa, Azmee da nan take ta gane ba sehrish bace tace"kiyi hakuri na tashe ki kina bacci,Sehrish nake nema,dan Allah ki sanar da ita cewa SGR yana nemanta a part ɗinsa," Jahad tace"tayi bacci,bari na tashe ta,"tayi maganar tare da juyawa cikin sauri ta shiga cikin ɗakin, Wucewa azmee tayi ta koma kitchen,cike da zullumin mai zai biyo ba idan Sehrish ta sanar ma Sgr cewa Uncle abusufyan ne ya hanata yin aiki a part ɗinsa,tabbas za'a kwashi ƴan kwallo, "Sehrish!ki tashi babban yaya yana son ganinki a part ɗinsa,dan Allah ki tashi kije,"jahad ce keta kokarin tashinta daga bacci,sehrish kuwa sai faman mutsu mutsu takeyi,daƙyar ta iya cewa"Wanene ke nema ne'? Jahad tace"babban yaya," Jin sunanshi yasa Sehrish buɗe idanunta ta wurgasu kan jahad dake tsaye,yatsina fuska tayi tare da maimaita sunan nashi"babban yaya?shike nema na,waya faɗa maki"? "Aunty azmee,yanzun nan bata jima da tafiya ba,naga kamar ma bata acikin natsuwarta," Jin hakan yasa gaban sehrish faɗuwa rass,yunkurawa tayi tare da mikewa zaune,ta saukko da ƙafafunta ƙasa,kafin ta miƙe tsaye,saboda tsabar saurin ta fita ko Mayafi bata ɗauka ba,gashi kanta ko kallabi babu,sumar kanta ce da tasha gyara,an mayar mata da gashin mai gazar gazar ya sauko har kafaɗarta,a hankali gashin kan nata ke toho yana fitowa,har ta launin gashin anyi mata dying dinsa ya koma 2 colour,Kayan bacci ne ajikinta riga da wando sharara suke,farare masu laushin gaske,irin waɗanda kana sanyasu ajikinka,Ko baka jin bacci nan take zai zo maka, Tunkan ta ƙarasa shiga falon nashi take jin ɗar ɗar acikin zuciyarta,tun jiya rabon da ta sanyashi acikin idanunta,daƙyar ta iya yi mashi sallama tare da kutsa kai cikin falon nashi,bai amsa sallamarta ba,har ta ƙarasa inda yake,atsaye muryarta na rawa tace"Gani,"bai dago ba kuma bai tanka mata ba,sae ma cigaba da danna system ɗinshi da yake yi,lokaci bayan lokaci yakan kai hannunshi ya dauki Coffee ya kur6a,zuba mashi ido tayi tana kallon kyakkyawar fuskarshi,ba ƙaramin kewarshi tayi ba,sam batayi tunanin ma zai nemeta ba, sai da ta ƙara cewa"babban yaya gani,Aunty azmee tace kana kira na,"sannan ya soma magana anatse"yau da safe,meya hanaki zuwa part ɗina"? Shiru tayi gabanta na faɗuwa,batasan amsar da zata bashi ba,saboda tsoran abunda zai biyo baya, "Kinsan bana maimaita magana,amsarki nake jira," Runtse idanunta tayi aranta tana fadin"nashiga uku,!Allah ka kawomin ɗauki,bansan me zan faɗa masa ba,"shirun da tayi mashi ne ya fusata shi,aikuwa a zafafe ya daka mata tsawa,har sai da ta zura da gudu saboda yarda ta tsorata,kama hanyar fita tayi saboda ruɗewar da tayi,hakan yasa ya miƙe tsaye tare da bin bayanta,ruƙo hannunta yayi tare da fusgota ta dawo saitin shi,Waro ido waje tayi tare da ja da baya da baya,har suka ƙure ma bangon,runtse idonta tayi muryarta na kerma tashiga faɗin"Am so sorry babban yaya,I can explain,zan faɗa maka," A hankali ya ware blue eyes ɗinshi akan fuskarta,sumar kanta yabi da kallo,yayi mamakin ganin yadda gashin yayi tsayi cikin ƙankanin lokaci har ya kamo kafaɗarta,gyaran gashin da akayi mata ya ƙara fiddo da kyawun fuskarta,mayar da idanunshi yayi akan La66anta dake ta faman kerma duk tabi ta gigice,lokaci guda ya tsinci kanshi cikin wani irin yanayi mara misaltuwa,moving ya ƙarayi gaba ɗaya yayi mata rumfa da faffaɗan ƙirjinshi,lokacin da taji tsinin hancinshi na gogar nata,nan take gabanta ya kuma bugawa daramm,jikinta ya shiga yin kerma ta ko'ina,gaba ɗaya duk tabi ta susuce har lokacin ta gaza buɗe idanunta saboda tsabar tsoro,jin saukar hannunshi asaman ƙirjinta yasa ta yin saurin ware idanunta arazane,kai tsaye suka sauka cikin nashi,face to face,Eyes to eyes,nose to nose,mouth to mouth!!, A firgice ta janye idanunta daga kan fuskarshi ta mayar dasu akan ƙirjinta,Ashe gaban rigarta ne ta bari a buɗe ta manta bata sanya links ɗin rigar ba,Shine ya sanya hannunshi a wurin yana manne mata su,jurewa kawai takeyi amma ba ƙaramin yanayi Sgr ya jefa mata ba,musamman yadda hannunshi ke nutsewa a cikin boobs ɗinta,ba ita kaɗae ba,hatta shi kanshi daya kai hannunshi wurin saida yayi regretting,saboda wani abu daya dinga jin yana fisgarshi yadda kasan magnet,mayen karfe ba, daƙyar ya iya zame hannunshi daga saman ƙirjin nata,bayan ya kammala sanya mata links ɗin,Sannan cikin sanyin murya yace"tell me the reason why baki zo yi mun aiki da safe ba!bakisan bana son sharing a aiki na ba!? Magana yakeyi amma idanunshi sae ƙokarin lumshewa sukeyi tamkar mai jin bacci,wanda kuma ba kowa ne yajawo hakan ba face Sehrish, Cikin en ena tace"Kayi haƙuri ba laifina bane,Daddy ne ya hanani zuwa" Cike da mamaki yace"Kina nufin Uncle ne ya hanaki zuwa," Jinjina mashi kai tayi alamar eh,yayin da take ta faman haɗiyar yawu, . "just without any reason ya hanaki aiki a ƙarƙashi na"? daga mashi kai tayi alamar eh, Cije pink lips ɗinsa yayi tare da tsoma hannunshi acikin sumar kanshi yana cakuɗata,ranshi a matuƙar 6ace yace"hakan bazai ta6a yiyuwa ba,dole kiyi aiki a ƙarƙashina!ban damu da matsayinshi a wurinki ba,dole ne ayimun biyayya!!!!!!!!* *Tashin hankalin da ba'a sama shi date!* Gobe walima,suwa suka shirya zuwa💃💃💃💃 *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. [1/3, 6:34 AM] Abue Saleh AlQuyraemey: *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* _Ga duk maison karanta littafin Abban sojoji,zai biya 300 ne,za'a tura mashi tundaga farko har inda muka tsaya,kuma zai cigaba da samun update dinshi akai akai,ga wanda ke buƙata zai tura mun message ta whatsapp ɗina (08103884440) kada ku bari abaku labari sannan a kula wannan itace numbar wayata,Wasu suna ɗaukar numbar Wanda suka bani tallarsu kayansu suna kiransu a matsayin ni,bayan ni ga numbar dana bada nan itace numberta_ *Nagode sosai da addu'o'inku agare ni,da kuma uzurin da kukayimun,har zuwa wannan lokacin,Allah yabar zumunci a tsakaninmu daga nan har gidan aljanna💃* *nace ba Masu satar littafi suna fitarwa ta bayan fage,mai yasa baku ƙarasa masu labarin ba?kuma kenan saida kuka jira ni?ae nayi tunanin cewa zaku ƙarasa masu labarin ne ashe dai sai anjira Boss*😂🤣😅 Bismillah ❤🤍❤ A hankali ya tura ƙopar bedroom ɗinsa tare da shigewa ciki,turus yayi ya tsaya yana kallon junaid dake manne da Mommynsu suna bacci yadda kasan wani jinjiri ya ƙanƙame ta sae faman sharar bacci suke yi atare,murmushi ya ɗan saki tare da wuce wa cikin bedroom ɗin,Rage kayan jikinshi yayi bayan ya kammala ya shige cikin toilet,Within 15mins yayi wanka,sae gashi ya fito ɗaure da towel,tsaf ya kammala gyara jikinshi agaban dressing mirror,kafin ya koma wurin Closet ɗinshi,ya ɗauko wasu lallausan kayan bacci riga da wando farare ya zura ajikinshi,bayan ya kammala shirin kwanciya,ya zagaya ta baya dai dai saitin da junaid yake manne da mommyntasu ya lalla6a tare da hayewa saman gadon,zuba mata ido yayi yana kallonta,kullum koma mashi takeyi tamkar sabuwar amarya,ji yake kamar ma ba'ajima da yin aurensu ba,saboda tsabar son da yake yi mata,ba ƙaramin kewar matar shi yayi ba,har yanzu bai kammala hucewa ba,tunda tadawo kullum da daddare suna manne da juna,a kwanakin nan ba ƙaramin kwanciyar hankali ya samu ba,ya zama cikakken mutun don rashin Alexandra ba ƙaramin gibi yayi mashi ba,kasa janye idanunshi yayi daga kallonta da yake yi,tayi wani irin haske mai kyan gaske,fatarta kamar ta jinjiri saboda tsabar sheƙin da takeyi da daukar ido,bin dogon gashin kanta yayi da kallo wanda ya baje agadon bayanta,a hankali ya mayar da idanunshi akan farar half vest ɗin dake ajikinta,nan take ya fara shiga yanayi na buƙatarta,ga kuma junaid ya riga shi,to ya kenan?   ƙasa ƙasa yayi da muryarshi dai dai saitin kunnan Junaid ya ambaci sunan shi a hankali"Junaid!junaid!tashi ka koma bedroom ɗinka,"yayi hakan ne saboda baison ya tashe ta,yasan inta farka ba lallai tabari ya rabata da junaid ba,jin shiru junaid bai motsa ba yasa shi ƙara ɗan ɗaga muryarshi yace"junaid!junaid!pls get up and go back to ur bedroom,inaso in kwanta ne!"   Shiru junaid ba alamun ma zai farka,hannu yasa tare da ɗan bubbuga kafaɗarshi yace"Junaid!junaid!Ka tashi mana!!"   Duk wannan suratan da Abbansu keyi kaf a kunnan junaid,sarai yana jinshi yayi banza dashi,tun kiran farko da yayi mashi ya farka,koda yaji Abbansu na cewa ya tashi ya koma bedroom ɗinshi zai kwanta,sai ya ƙara ƙanƙame mommyn tasu,don yaci alwashin cewa yau fa abbansu bazai kwana tare da mommynsu ba,ba don komai ba sae don shi aganinshi Abbansu baiyi mashi adalci ba,don me zai dinga kwana tare da Mommynsu bayan shi ne ya dace su dinga kwana tare da ita,Saboda tafiyar da tayi ta barshi tun yana jinjiri,yanzu lokacin shi ne bana abbansu ba,dole ya haƙura yabar mashi,Tashin hankalin da ba'a sama shi date!   "Junaid!nafa son cewa kana ji na,kayi banza ka ƙyale ni!zaka tashi ko saina yi wurgi dakai,"a faɗace Abban nasu yayi maganar yana kallonshi,   turo baki junaid yayi cikin ƙunƙuni yace"Abba,wlh ba inda zani!yau kwana na ne,"   Har saida gaban Abbansu ya faɗi rass saboda yadda maganar ta junaid ta dirar mashi a kunnanshi,Cike da mamaki ya maimaita maganar "yau kwanana ne!"!   Junaid dake maƙale da Mommynsu yace"eh,abba kadaina ma wahalar da kanka,Allah yau ba inda zani,kullum sai kayimun wayau,kana kwana tare da mommy,fisabilillahi Ni da kai waye ya dace ace yana kwana tare da Mommy!!!?   Saboda tsabar takaici sam abbansu ya rasa me zaiyi ma junaid,gashi babu mabugi a kusa balle ya kwaɗe shi,ko ya samu sanyi aranshi,   Ganin junaid ya turje bilhaƙƙi dagaske yake bazai tashi ba,gashi kuma Alexandra tafara mutsu mutsu alamun suna takura mata,kuma baiso ta farka daga baccin saboda gudun karta hanashi kora junaid izuwa bedroom ɗinshi,hakan yasa ya yanke shawarar binshi ta lalama,   Sassauta muryarshi yayi tare da cewa"Pls babyn abbansa,abeg dan Allah ka tashi ka koma bedroom ɗinka,help ur dad pls,bakasan halin da nake ciki ba,pls junaid ɗin Abbansa,"   Ƙara ƙanƙame Mommynsu yayi tare da cewa"wlh Abba dama kadaina yi mun magiyar nan,ni yau tare da mommyna zan kwana,"   Muryarshi tamkar zaiyi kuka yace"to ni a ina kakeso na kwana?junaid baka tausayin Abbanka ko?meyasa zakayi mun haka?yau kuma rigimar akaina zata ƙare"?   ashagwa6e junaid yace"Abba,gaskiya kayi haƙuri nidai babu inda zani,kaje bedroom ɗina ka kwana mana,'yayi maganar tare da ƙara shigewa jikin Mommyn tasu,   Rai a6ace Abba yace"Don ubanka zaka tashi ko bazaka tashi ba!!"?   shiru yayi bai tanka mashi ba,sae ma minsharin ƙaryar da ya dinga ja,don abban nasu yasan cewa bacci ya ɗauke shi,   A daddafe Abbansu ya miƙe daga zaunen da yake gefen gadon,ranshi duk a jagule kamar ya aza hannu aka ya fasa ihu haka yake ji,shi kaɗae yasan halin da yake ciki,bai ta6a sanin cewa junaid bai da wayau ba sae yau,duk yasa ya zama abun ban tausayi,hawaye ne kawai bai zubar ba,amma ba ƙaramin 6ata mashi rai yayi ba,ya jima yana zagaye a cikin bedroom ɗin,yana kallonshi,a ƙarshe ya nufi ƙopar bedroom ɗin tare da buɗewa ya fuce waje,    "Gobe ma anan zan kwana,"junaid ne yayi maganar bayan jin fitar abban nasu daga ɗakin, "Daughter"! ƙiris ya rage ta saki tray ɗin dake hannunta,don bata tsammaci jin muryar mutun a bayanta ba,bakowa bace wannan face Sehrish wadda ke tsaye a cikin kitchen tana shiryama Sgr fresh fruits tare da coffee,jikinta na sanye da doguwar riga ta bacci mara nauyi milk colour tayi rolling mayafi akanta launin baƙi, Ganin daddynsu yasa ta sakin murmushi tare da cewa"daddy,dama idonka biyu bakayi bacci ba har wannan lokacin"?   ƙarasa shiga kitchen ɗin yayi yana cewa"taya zan iya baccin?bayan ɗaya daga cikin ƴa'ƴana idonta biyu bata runtsa ba,raina ne ya bani cewar akwai wadda batayi bacci ba acikinku shiyasa na fito don inga wacece ashe kece...." fashewa da dariya sehrish tayi jin abunda yace,shima dariyar ce ɗauke a fuskarshi, ..tsayawa yayi dab da ita yana kallon kayan marmarin da ta kammala Jera ma sgr,ta gyare tsaf ta yayyanka mashi su,   "Yanzu wannan kayan daɗin duk na wanene?ko ke zaki sha"?yayi tambayar a yayin da yakai hannunshi cikin ƙayataccen tray din wanda ke ɗauke da plate na kayan marmarin ya ɗauki yankin abarba ɗaya tare da turata abakinsa yana sha,   "Bani zan sha ba,na babban yaya ne,"tunkan ta ƙarasa maganar taga ya dakata da taunar abarbar da yake yi yana kallonta fuskar shi ɗauke da mamaki yace"Kina nufin Rafayet kika shiryama wannan?shiya sanyaki ne"?   Jinjina kai tayi tare da cewa"eh daddy,shine ya buƙaci na dinga kai mashi fruit tare da coffee adai dai irin wannan lokacin ƙarfe sha biyu na dare in sun dawo daga aiki....'daƙyar ta ƙarasa maganar ganin yadda fuskarshi ta canza,alamar wani abu baiyi mashi daɗi ba,   "Daddy wani abu"?ta furta hakan tana kallonshi,   shiru yayi jimmm kamar mai nazarin wani abu,kafin daga bisani yace"da sanin Abbanku"?   girgiza kai tayi alamar a'a sannan ta ƙara da cewa"yasan cewa inayi mashi aiki daddy,amma banda tabbacin cewar ko yana da masaniya akan hakan,bansani ba ko babban yayanmu ya sanar dashi,'   ta6e baki Uncle abusufyan yayi kafin yace"Abba bazai ta6a bari ba,bana tunanin cewar ya sani,taya mace kamarki zata dinga zuwa ɗakin namiji a irin wannan lokacin!!?   Gabanta ne taji ya faɗi rass,sunnar da kanta tayi tana wasa da yatsun hannnunta,   "That's imposssible!!!Banaso gaskiya hakan bai kwantamin araina ba,duk da ɗan uwanki ne shi a yanzu,amma hakan bai dace ace kina zuwa ɗakinshi ba a irin wannan lokacin,in fact ba'a son mace da namiji suna ke6ewa,nasan kinsan da wannan!"   Muryarta na kerma tace"Hakane daddy,   Jinjina kanshi yayi tare da cewa"Yawwa,ɗauki kayan marmarin ki kai masa,kada ki makara,"   Hannunta na kerma ta ɗauki tray din da sauri da sauri ta nufi hanyar fita daga kitchen ɗin,har ta kusa fita daga cikinsa,muryarshi ta dakatar da ita,   "Sehrish," "Na'am daddy,"ta amsa mashi tare da ɗan juyawa ta baya tana kallonshi,   "daga yau!banaso ki ƙara zuwa don kiyi mashi aiki,koda da safe ne ko da rana,Azmee itace mai aikin gidan nan,idan ma da buƙatar masu aikin zansa a ƙaro wasu,amma ba zakuyi aiki wa kowa ba,ina fata kin fahimce ni,'   Tunda abusufyan ya fara maganar gabanta ya shiga faɗuwa,hankalinta yayi mugun tashi,tuni idanunta sun fara canza launi,   Fuskarta ɗauke da damuwa tace"daddy,inajin tsoran shi sosai,bansan taya zan sanar dashi hakan ba,'   Murmushi Abusufyan yayi tare da takawa kusa da ita suna fuskantar juna yace"Bance ki sanar mashi ba,kawai inaso daga yau ki ɗan ɗaga ƙafa daga zuwa part ɗinsa don kai mashi abinci ko yi masa gyara,nasan cewa bazai damu da hakan ba,tunda ga azmee,in ma yayi magana akan hakan ki sanar dashi cewa"NI NA HANAKI!"   wani irin wahalallen yawu Sehrish ta haɗiye a bakinta,sam bazata iya yima daddyn nasu gardama ba,tasan cewa yayi hakan ne saboda tausayinsu da yake ji,baison suna aikin wahala,amma wannan hukuncin da ya yanke mata ba ƙaramin horo bane agareta,Na farko hakan zai nisanta tsakaninta da SGR,ganinshi zaiyi mata ƙaranci,in har ba downstair ya sauko ba,Allah ya haɗasu to bafa zata samu damar ganinshi ba,Abu na biyu kuma hayaam zata samu damar shige masa,don tasan cewar daga ta daina yin aiki a ƙarƙashinsa,hayaam zata kunno kai,na uku kuma batasan me zai biyo baya ba,in har yasan cewar ta daina yi mashi aiki,Shin zai damu ko bazai damu ba.....'   "Zaki iya tafiya,kada ki jima a bedroom ɗin nashi,dare yana ƙara yi,da zarar kin kai mashi,kiyi hanzarin komawa cikin ƴan uwanki ki kwanta kiyi bacci ki huta,   "Toh Abba,zanyi duk yadda kace," Murmushi abusufyan ya saki tare da cewa"ki kulamin da kanki daughter,sai da safe," murmushin tayi itama bayan ta amsa mashi,batare da 6ata lokaci ba,ta wuce sashen Sgr,kamar wadda aka zare ma lakar jikinta haka take tafiya,ba don komai ba sai don Hukuncin da Daddy ɗinsu ya yanke,Taya zata iya rayuwa batare da tana sanya babban yaya acikin idanunta ba akai akai!anya kuwa zata iya jurewa?wa zai kula mata dashi kamar yadda take kula dashi?tashin hankalin da ba'a sama shi date, Wani irin farin cikine ya lullu6e hayaam dake la6e wurin kitchen ɗin tana sauraron abunda Uncle abusufyan ya tattauna tare da sehrish,kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha don tsabar farin ciki,ashe munafukar tana la6e ta kasa kunne tana sauraronsu,bakomai ya fito da ita ba daga ɗakinta face yunwar da taciyota,hakan yasa ta lalla6a ta fito don ta sama ma kanta abunda zata ci,anan ne fa tajiyo muryoyinsu suna magana acikin kitchen ɗin,shine tayi masu la6e,ta kwashe duk abunda suka tattauna acikin kunnanta,Lokaci guda ta manta ma da yunwar da take ji acikin cikinta,gudu gudu sauri sauri ta koma bedroom ɗinta,faɗawa tayi saman gadonta tana faman tiƙar dariya,bayan ta tsagaita da yin dariyar tashiga tufka da warwara acikin zuciyarta,   "Idan har inaso in samu nasarar cigaba da zama acikin gidan nan,dole saina haɗa kai da wani!wanda zai taimaka mun,wurin ganin na cimma burika na!tabbas ina bukatar shi,"ta ambaci hakan ayayin da take ƙoƙarin miƙewa daga zaune,   *WANENE SHI*!? *Surgeon General Rafayet* A ƙopar shiga bedroom ɗinshi ta tsaya,zuciyarta duk a ƙuntace take,don idanunta acike suke tab da hawaye ba don komai ba sai don hukuncin da daddynsu ya yanke agame da zuwanta part ɗin SGR,yanzu shikenan Yau zata kasance rana ta ƙarshe da zatayi aiki a sashen shi?shikenan bazata ƙara takowa ba da sunan ta kula dashi ba? 😥 Tamkar ta fashe da kuka haka ta dinga ji,dakyar ta daure ta cije tare da zuba sallama,shiru ba'a amsa mata ba hakan yasa ta ƙara daga muryarta,ta kuma zabga sallamar akaro na biyu,shima shiru bai amsa mata ba,hakan yasa ta fara tunanin cewa kodai yayi bacci ne ko kuma yana acikin toilet,don tasan shi akwai yin wankan dare duk in xai kwanta, Tunani tayi ai shi muharraminta ne a yanzu hakan yasa ta kutsa kai tare da shigewa cikin bedroom ɗin nasa,wani irin daddaɗan kamshi ne ya daki hancinta,mai daɗin gaske,ga ratsa zuciya,lumshe idanunta tayi a hankali tare da sake buɗesu,tana ƙare ma shimfiɗeɗen gadon nashi kallo,kasa janye idanunta tayi daga kallon shi da takeyi,Yana a kwance saman gadon,yayi covering jikinshi da lallausan blanket ɗinsa,dai dai saitin stomach ɗinsa bargon ya tsaya,sumar kanshi ta rufe mashi fuskarshi da alama dae a gajiye suka dawo yau,baccin ma kamar bai shirya mashi ba ya ɗauke shi,duba da yadda yayi kwanciyar,right hand ɗinshi na asaman kanshi ya zagayo dashi ta dayan 6angaren, A hankali sehrish ke nufar gadon nasa tana tafiya kamar wadda kwai ya fashe mawa akai,saboda rashin kwarin jikinta,ajiye mashi tray din tayi asaman side table ɗinsa,sannan tashiga tunanin,kodai ta tashe shi daga baccin kota ƙyale shi?ta jima tana nazari kafin zuciyarta ta bata shawarar cewa ta tashe shi kawai,ganin cewa ba kayan bacci ne ajikinsa ba,hakan na nufin baiyi night bath ɗin daya saba yi ba,tabbas bazaiji daɗin baccin shi ba,   Zuba mashi ido tayi tana ƙare mashi kallo,anan taga zufa na tsattsafowa a saman dogon hancinsa,da kuma wuyansa,mamakine ya kamata,aranta tace"Zufa kuma?duk da sanyin A.c dake akwai?karfa ace babban yaya bashi da lafiya"?cike da damuwa tayi tambayar,can kuma tace"kodan baiyi wankan daren daya saba yi bane?zai iya yiyuwa hakane,amma fa ina tsoran tashin shi daga bacci,   Bari dai kawai na haƙura kar in jama kaina,don na lura kwanan nan ɗaure mun fuska yake yi,kamar nayi masa wani laifi,' Tana kai ƙarshen zancen zucin nata,tayi wani kwakkwaran juyi da nufin tabar wurin,cikin rashin sani tayi tuntu6e da doguwar ƙafarsa ɗaya data sauko ƙasan gadon,birkicewa tayi duk yadda taso ta ruƙe jikinta amma abun ya faskara,gaba ɗaya ta tafi ɗungurugum ta faɗa saman jikinshi, Hankali a matuƙar tashe Sehrish ta zazzare idanunta tana kallon fuskarshi,gabanta ne yayi wani irin mugun bugu,ganin ya fara motsa idanunshi yasa ta soma kiciniyar miƙewa daga saman jikinsa,sae dai kash bata samu wannan damar ba domin kuwa Sgr harya ware kyawawan idanuwanshi,biji-biji ya dinga ganinta acikin idanunshi,ita kuwa tuni jikinta ya shiga kerma,a hankali yakai hannunshi tare da ɗan Murza idanunshi,kafin ya ƙara ware su da kyau akanta,gaba ɗaya duk tabi ta rikice tuni zufa ta fara tsattsafo mata,ganin cewa dagaske dae ita yake kallo yasa ta ambaton nashiga uku,a hanzarce ta bar jikinshi ta sauka daga saman gadon,la66anta na rawa tace"dan Allah kayi haƙuri babban yaya,wlh ba yin kaina bane,na kawo maka fruits ne kuma banyi niyyar na tashe ka ba,tuntu6e nayi da ƙafarka na faɗo saman jikinka.....'kasa ƙarasa maganar tayi saboda wani irin kallo da taga yana jifarta da shi,sunnar da kai ƙasa tayi tana faman wasa da yatsun hannunta dake ta faman kerma,   "Kneel down," ya furta da wata irin kasalalliyar murya ta wanda bacci bai ishe shi ba,    cikin sauri Sehrish ta zube saman guiwowinta agaban gadon nashi, "Ur Hands up and close ur eyes," yayi maganar yana yi mata nuni da hannunshi,   Jiki na rawa ta ɗaga hannayenta sama tare da kulle idanunta,sosai ta rufe su,tana matsar kwalla,   "Kada kiyi attempting buɗe idanunki,ko sauke hannayenki if not kinsan mai zai biyo baya,'   Muryarta na kerma tace"bazan buɗe ba,' "Gud," ya furta hakan a yayin da yake cire blanket ɗin dake rufe da jikinsa,a hankali ya sauko daga saman gadon,tsayawa yayi yana rage kayan jikinsa,sae da ya rage daga shi sae short,sannan ya wuce cikin toilet ya rufe ƙopar,    Saboda tsabar tsoro batama san cewa Sgr ya shiga toilet ba,sae faman shessheƙar kuka takeyi,after some minutes ya fito daga cikin toilet ɗin nasa,jikinshi sanye da bathrobe white colour,gaban dressing mirror ɗinshi ya zauna,ya shiga shafe jikinshi da mai,bayan ya kammala ya feshe ko'ina tass da tsadaddun tururrukan jikinshi,nan take ƙamshin ya gauraye ko'ina na cikin bedroom ɗin,ya jima agaban mirror ɗin kafin ya yunƙura tare da miƙewa ya nufi can cikin bedroom ɗin wurin Closet ɗinshi,   Almost 30mins Sehrish tayi zuƙunne saman guiwowinta jikinta na kerma,   dawowa yayi jikinshi sanye da nigh dress masu kyan gaske,    Wuri ya samu ya zauna daga gefen gadon yana fuskantarta,a hankali ya miƙa hannunshi tare da buɗe side drawer ya ɗauko wannan hoton da Uncle ɗinsu Abusufyan ya ta6a basu lokacin da suna ƴan shekara sha a duniya,zuba ma hoton ido yayi yana ƙare mashi kallo,kafin ya ɗago da idanunshi ya azasu akan fuskar sehrish yana kallonta,da alama nazarin wani abu yake yi a fuskarta da kuma fuskar ƙaramar yarinyar dake acikin hoton hannunsa,so yake ya gano wacece yarinyar dake acikin hoton nan,ƴar ƙaramar yarinya wata zararriya da ita,gashin kanta duk ya tarwatse ya yamutse yayi datti babu gyara,kayan jikinta duk sun fita hayyacinsu sun yage,ga ƙafafunta ko takalma babu,fuskarta kuwa duk tayi jaga jaga da majina,hoton yayi confusing ɗinshi,kokwanto ya shiga yi anya itace a cikin hoton?kodai ɗaya daga cikin ƴan uwanta ne,     "Open ur eyes," Jin muryarshi yasa tayi saurin buɗe idanunta wanda ke fitar da kwalla,muryarta na rawa tace"babban yaya dan Allah kayi haƙuri bazan ƙara ba,"tayi maganar tana faman shassheƙar kuka,   Miƙa mata hoton hannunshi yayi tare da cewa"Who is she"?   hannunta na kerma ta kar6i hoton daya miƙa mata,Ƙura ido tayi tana kallon hoton,nan take tashiga tambayar kanta ina Sgr ya samu hoton ɗaya daga cikinsu?ita kanta bazata iya tuna waya ɗauki hoton ba,kuma haka zalika bazata iya tantance wacece acikin hoton ba,saboda abun yayi confusing ɗinta,Kamar ita kamar kuma hossana,saboda gashin kan daya harmutse kamar na Mahaukaciya,tasan cewa hosana ce kawai keda irin wannan hargitsastsen gashin,   "Ina sauraranki,"ya furta hakan a yayin da yakai hannunshi tare da ɗaukar cup of cofeen da takawo mashi,ya shiga kur6ar shi anatse,   Cikin en ena tace"Wannan kamar hosana ce,bazan iya tantance wacece ba,'   ɗaure fuskarshi yayi tare da cewa"Oh ba zaki iya tantance wacece acikin hoton ba?what does that mean"   Muryarta tamkar zatayi kuka tace"Inaji hosana ce,wannan itace gashin kanta yake a haka,"   Hannu Sgr yasa tare da kar6e hoton ya ajiye shi a gefen shi,'   Tsuru tsuru tayi da idanunta,cike da tsoran kar ace ta ƙara wani laifin,   "I want u to tell me..,wannan bastard ɗin menene ma sunan shi?   "Ya sayyadi," ta bashi amsa, "akwai wasu mahimman bayanai da nakeso naji daga gare ki,hope zaki natsu kiban amsa," jinjina kai tayi tare da cewa"in sha Allah,"   "Awani area kuka zauna a kano?" "A hotoro ne" ta bashi amsa, Jinjina kai yayi tare da ajiye cup ɗin dake hannunshi,then ya ɗauki banana yana 6areta a hankali yace"zaki iya tuna address ɗin gidanku kenan"?   "Eh," "Okey,' ya ɗanyi shiru bayan yakai ayabar abakinsa ya ɗan gutsireta acikin bakinshi,kafin ya kuma cewa"a labarin da sister ɗinki ta bayar,ta faɗi cewa shi wannan mutumin ya ta6a nemanku,a cikinku akwai wadda ya ta6ayin raping"? Daram!!!taji gabanta ya faɗi,girgiza kai tashiga yi muryarta har tana harɗewa wurin saurin cewa"babu...bai ta6a samun nasarar yin hakan ba,yadai ta6a yunkurin hakan," Shiru Sgr ya ɗanyi sae lokacin ya ɗan ɗago da idanunshi ya kalli fuskarta,gaba daya duk tabi ta rikice jikinta sae faman kerma yakeyi,yanayinta kuma kamar akwai wani abu data 6oye masa,   "Tell me the truth!kinsan bana son ƙarya,even if u hide it to me i will find out soon,so its better ki sanar dani,before naji a wurin wani!!"   Hawaye taji sun wanke mata fuskarta,ji take kamar ta tashi ta watsa da gudu,saboda ta tsani taji ana zancen Ya sayyadi,   ɗagowa tayi da idanunta waɗanda suka rune suka canza launi,kai tsaye suka sauka acikin nashi,cikin shessheƙar kuka tace"bazan maka ƙarya ba,yaso yayi hakan amma Allah bai bashi dama ba,'   "In har dagaske ne abunda kika faɗa,to meyasa kike kuka"?   "Saboda banason ana mun maganar shi,hakan yana tunamin rayuwar da mukayi a baya,"   kawar da idanunshi yayi daga kan fuskarta,sannan yace"Its okey,u can wipe ur tears,amma ba hakan yana nufin za'a daina maki maganar shi bane!dole ta hanyarku ne zamu samu dukkan bayanan da mukeso,before muci nasarar kama shi,'   Hannu tasa tana share hawayenta tace"Allah ya bani ikon Amsawa,"   "U can leave,"ya bata umarnin tafiya,   Tashi tayi jikinta asanyaye ta juya tana nufar hanyar fita daga bedroom ɗin nashi,gaba ɗaya duk jikinta yayi mugun sanyi,wata irin kasala ta lullu6eta,har ta kusa fita daga bedroom ɗin nashi ta ɗan tsaya tare da juyowa a hankali don tayi ma ɗakinshi kallon karshe tunda daga yau bazata ƙara zuwa sashen shi ba,da sunan yi mashi aiki, Juyowarta keda wuya,idanunta suka shiga acikin nashi,har saida gabanta ya faɗi,kasa tafiya tayi kallonshi kawai takeyi,a yayin da shima yake kallonta, Kusan 8 mins sannan taji muryarshi acikin kunnanta yace"Lafiya"?   girgiza kai tayi alamar ba komai,kafin tasa kai ta fuce daga bedroom ɗin nashi, Saukowa downstair tayi,hawaye nata faman zarya a fuskarta,sai da ta goge tears ɗin sannan ta wuce  bedroom ɗinsu, a hankali ta tura door ɗin ɗakin ta shiga,Samun Jahad tayi zaune daga gefen gadon ta zabga tagumi,yayin da hosana ke ta faman sharar bacci,   Bayan ta rufe masu ƙopar ɗakin ta koma daga gefen jahad ta zauna tare da ambaton sunanta"Jahad,"   A razane ta ɗago tana kallon Sehrish,sam bataji shigowarta ba,   "Mekike tunani ne"? Murmushi jahad ta ɗanyi tare da cewa"Ashe kin fita,na farka ban ganki ba,acikin ɗakin,' Sehrish tace"Naje part ɗin babban yayanmu ne,' "Wannan mai blue eyes ɗin"? Jahad ta tambaya yayin da take kallonta, "Eh,Sunan shi RAFAYET,amma suna kiranshi da BABBAN YAYA,"   "Shine babbansu kenan"?acewar jahad,   "A'a bashi bane babbansu gaba ɗaya ba,Akwai wanda suka girme shi sosai,Sunan ne ya dace dashi shiyasa suke kiranshi da haka,"   Jahad tace"kamar bazaiyi sauƙin kai ba,na lura ko magana baisan yi,ni in inama kallonshi tsoro yake bani,araina har cewa nake yi wai shima nan ɗan uwanmu ne,ƙwayar idonshi daban koda yake ga Ayaan nan shima idanunshi ash ne,mommynsu ma nata kalar na babban yaya ne,amma Mommynsu fa kamar bata son ganinmu nake gani ko kin lura da haka"?   Sehrish tace"eh hakane,amma kada kisa ma ranki wannan,idan kika lura abun kamar a jininsu yake ita da babban yaya,in ka biye ta yanayinsu toh bazakayi rayuwa asake ba,duk zaka takure kanka ne,kayi tunanin cewa kamar sun tsani mutane basa son ganinsu bayan ba haka bane,kawai basu cika son magana ba,ko kallon mutane basa son yi,'   Cike da mamaki jahad tace"tofa su kuma haka suke?shiyasa junaid shima baison ganina,har yau fa junaid ko son haɗa ido baiyi dani,in kuwa muka haɗa ido dashi har hararata yake yi ya kuma murguɗa mun baki,Wlh bana jin daɗin abunda yake yi mun,sai inga kamar ya tsane ni ne,abun ba ƙaramin damuna yake yi ba,gashi inason nasamu kusanci sosai dashi,kamar yadda naga kuna shiri a tsakaninki dashi,bansan meyasa ni yake mun haka ba,'   Tayi maganar fuskarta ɗauke da damuwa,   Sehrish tace"kai junaid ɗin keyi maki hakan?to ae duk gidan nan babu kamar shi,indai wurin son mutane ne,yafi kowa faran faran da mutane kullum cikin fara'a yake,Junaid fa ko yau kuka fara haɗuwa dashi zai nuna tamkar kun ta6a haɗuwa a baya,kuma yadda zai saki jiki da mutun zaisa kayi tunanin kamar kun share shekaru kuna atare,"   Sosai Sehrish ta shiga kora mata bayani agame da junaid,   Abun ba ƙaramin ɗaure ma jahad kai yayi ba,cike da mamaki tace"To Amma meyasa ni yake mun haka"?   Murmushi sehrish tayi tare da cewa"dole akwai dalili,amma ki barni dashi in sha Allah zan tambaye shi inji,"   gyaɗa kai jahad tayi tare da cewa"Shikenan,dan Allah duk yadda kikayi dashi ki sanar mun,"   sun jima suna fira atsakaninsu kafin bacci yayi awon gaba dasu,ƴan ukun Abusufyan, Wuraren ƙarfe biyu daidai na dare,wata irin guguwar iska,ta shigo ta cikin windown ɗakin su Sehrish mai matuƙar tsoratarwa da kuma razanarwa baƙi wulik mai tafe da wani irin sauti,wanda ya ciccika kunnuwansu,a firgice hosana ta farka tare da fasa wata irin razananniyar ƙara,wanda yayi silar tashin Sehrish,ita kanta ta tsorata da ganin guguwar iskar nan,ta tattare wuri guda yadda kasan kwarangwal din mutun haka shape ɗinta ya koma bayan ta sauka a dakin nasu,ga yayi ajikinta,   Ƙanƙame Sehrish hosana tayi sosai tana cewa"Wayyo Allahna,mun shigo uku,ina daddynmu yake,menene wannan abun,'   Babu abunda Sehrish ke ambato face"innalillahi wa'inna ilaihirraji'una,yayin da ta ƙura idanunta akan guguwar nan data saukar masu acikin ɗakinsu,   jikinsu sae faman kerma yake yi gaba ɗayansu,hakoransu sae faman rawar ɗari suke yi kaf kaf kaf,saboda wani irin sanyi daya ziyarce su,   ganin guguwar ta tsaya agefen gadonsu,kamar su take kallo don harda ƴan idanu gare ta hakan yasa suka ƙara fashewa da kuka suna faɗin"Wayyo Allah mun shiga uku!" A firgice jahad ta farka,jin ihun da su hosana keyi,adai dai lokacin hosana na cewa"wlh hada ƴan idanu ke gare ta,mun shiga uku,"   Zuba masu ido jahad tayi tana kallonsu ganin yadda suka kware baki suna kuka,Ga bargo a hannunsu,sun rurruƙe,   A hankali ta mayar da idanunta kan abunda suke kallo,guguwar nan ta gani tsaye da suffar kwarangwal tayi masu ƙuru da ido,   "Jahad kina ganin abunda muke gani kuwa"?Sehrish ce tayi mata maganar,   Jinjina kai jahad tayi tare da cewa"Nagani,mutun ne wannan ba guguwar gaske ba,koma waye yazo ne don ya tsoratar damu ne kawai babu abunda zai iyayi mana,"   Hankali atashe hosana da sehrish suke kallon jahad,jin abunda tace,babu alamun jin tsoro atattare da ita,hankalinta kwance tayi maganar,ganin haka yasa suma suka dakatar da kukan da sukeyi,    "Wama ya sani,ko ya sayyadi ne yazo da suffar guguwar nan don yazo yaga yadda muka koma," jahad ce tayi maganar fuskarta ɗauke da dariya, Baki asake suke kallonta,sehrish tace"Anya jahad ba macanzarki akayi mana ba?na fara kokwanto anya kece?taya zaki ga wannan tashin hankalin amma ki nuna baki damu ba?guguwa face tayi suffar kwarangwal kuma hada ƴan idanu kuru tana kallonmu ki kalla dakyau,"   Tsoki jahad taja tare da cewa"Nice mana,nifa Allah kaɗai nake tsoro,dashi na dogara,wannan koma menene yazo wlh ni dariya ma halittar take bani,ji idon fa yadda yake jujjuyawa kamar an ɗorashi,' fashewa da dariya jahad ta kuma yi,Kafin ta kalli su hosana tace"abunda za'ae yanzu muja bargo mu lullu6e,mu rabu da ita,idan ta gaji da tsayuwa ta tafi,koda yake ba ƙafafu gareta ba,fiffike zatayi ta tashi,' Ta ƙarasa maganar cike da nishaɗi,jan bargon nasu tayi,cikin sauri suka gyara kwanciyarsu ta lullu6esu da bargon,saboda tsabar tsoro Bargon da suka lullu6a dashi sae faman kerma yake yi,   "Jahad dagaske,baki ji tsoron wannan abun ba"?kasa-kasa Sehrish ta tambaye ta,   Murya na kerma jahad tace"yanzu haka ma kuka nake yi,wlh atsorace nake,ƙarfin hali kawai nayi,saboda na ta6a jin wani malami yace idan ka nuna kana jin tsoran Aljani shine yake cin nasara akan mutun,shi har faɗama yake yi da aljanu shine nima na jaraba yin irin nashi,'   Duk da halin da Sehrish ke ciki sai da ta fashe da dariya tana kumshe baki,   "Jahad kinja mana bala'e,koma meye yanzu kin ƙara fusata shi da kalamanki,bansan me zai biyo baya ba,"acewar sehrish,   Jahad tace"Addu'a zamuyi kawai,insha Allah ba abunda zasu iya yi mana,'   Muryar hosana suka jiyo abayansu tana cewa"Sehrish dan Allah kuyimun addu'a,ko fatiha bazan iya karantawa ba a halin da nake ciki a yanzu,ga fitsari ya matse ni,'muryarta tamkar zatayi kuka tayi maganar,   Jahad tace"ki tashi ki shiga toilet mana!kinsan Allah kada kiyi mana fitsarin kwance,'   Fashewa da kuka hosana tayi tana cewa"taya zaki ce in shiga toilet bayan wannan halittar na nan ta ƙura mana ƴan idanunta,Allah ba inda zanje,sai dae ki tashi ki rakani ko kuma inyi shi a wando,'   Har haɗa baki sukeyi wurin cewa"Wai wa zai raka ki"?   "Ke ko sehrish daya daga cikinku ta rakani,"   "Tab,wlh nidai ba inda zanje,sai dai ko Sehrish," jahad nakai ƙarshen maganarta sehrish tace"Ke baki je ba sai ni kike tunanin cewa zan rakata,Ae wlh sai dae tayi shi a wando,ba inda zanje,"   Ganin basu ɗauki maganarta serious ba yasa ta ƙara fashewa da wani kukan mai sauti,     "Dawo tsakiyarmu ki kwanta,zanyi maki addu'ar ɗaukewar fitsari,ae na iya,Oumma ta ta6a koya mana,"fashewa da dariya sehrish tayi tana cewa"kai jahad,ni ban ta6a jin wata addu'a ta ɗauke fitsari ba,'   Tashi hosana tayi tare da komawa tsakiyarsu ta kwanta,tana jiran Jahad tayi mata addu'a kamar yadda tace'   "Rufe idanunki"jahad ta fadi hakan fuskarta ƙumshe da dariya,runtse ido hosana tayi tare da cewa"Na rufe,"   Tofa mata addu'a jahad ta shiga yi a fuskarta,ita kanta me addu'ar batasan me take fadi ba,sae faman motsi take da baki,intayi sosai saita tofa ma hosana a fuskarta,   A ƙule hosana tace"waini sai tofa mun miyau kike a fuskata,kuma ni banji kina addu'ar ba,'   "Ita addu'ar a sirrance akeyinta,ba a bayyanata,kiyi shiru kawai zanci gaba da karanta maki har a samu fitsarin ya ɗauke,   Shiru hosana tayi tana faman sauke ajiyar zuciya,yayin da jahad taci gaba da karanta mata addu'ar,duk sehrish na sauraronsu,   Abu kamar wasa,bacci ya ɗauki hosana,   "Kamar tayi bacci"?sehrish ta tambaya,   Jahad tace"eh,tayi bacci yanzu saura mu ya rage muyi bacci,'   Sehrish tace"taya zamu iya bacci da waccen halittar a ɗakinmu?inta cutar damu fa"?   Jahad tace"Insha Allah ba abunda zata iya yi mana,muyi addu'a kawai mu kwanta,mu ɗauka kamar mafarki ma mukeyi,"   Kamar yadda jahad tace haka suka haɗa baki suna karanta addu'oi,bayan sun kammala kuma suka shiga karanta ayoyin alkur'ani mai girma atare,cikin lokaci ƙankani bacci ya ɗaukesu,   Yin baccinsu keda wuya wannan guguwar ta disashe daga wurin ta 6ace 6aat. Tashin hankali,kowaye yazo masu da wannan suffar? Abunda ya faru bayan fitar abbansu daga bedroom ɗinshi,kai tsaye ya wuce upstairs part ɗin Marshal Omar,jikinshi duk asanyaye haƙika junaid ba ƙaramin 6ata mashi rai yayi ba,da alama sakin fuskar da yake yi mashi ne yana wasa dashi kamar tsaranshi,hakanne yasa raini ya fara shiga tsakaninsu, Da sallama abakinsa ya shiga bedroom ɗin Marshal,samunshi yayi a kwance yana sharar bacci,bedside lamps ɗinsa ne suka haskaka wurin bed ɗinsa, Shiga ciki abbansu yayi tare da hayewa saman gadon,ya jingina bayanshi a jikin headboard ɗin gadan,Ranshi duk a jagule yama kasa kwanciyar saboda yasan cewa koya kwanta bazai iya runtsawa ba,ba ƙaramin ƙuntata yayi ba,junaid ya fusata shi sosai,   Kwakkwaran juyi marshal yayi zai gyara kwanciyarshi,karaf idanunshi suka sauka akan Abban nasu,cike da mamaki ya ambaci sunanshi"Abba!"   fuskarshi ɗauke da damuwa yakai idanunshi akan fuskar Marshal yace"Omar,dama ba bacci kakeyi ba ne?"yayi maganar ayayin da yake ƙoƙarin 6oye damuwarshi,   Yunƙurawa Omar yayi tare da tashi daga zaune yana fuskantar abban nasu yace"Abba!meya faru naganka anan?kuma fuskarka da alamun damuwa attare dakai,"?   shiru abbansu yayi na wani lokaci yana deciding akan ya faɗa ma Omar halin da yake ciki ko kuwa ya ƙyale zancem kawai,   "Omar,ashe junaid bai da wayau har yanzu yaro ne shi"?   aɗan ruɗe omar yace"me junaid ya aikata,"?   "Hmmm,ya hanani sakat Omar,ƙiri ƙiri junaid ya shige mun ɗakina,yana can rungume da mommynsa,nayi nayi dashi ya tashi in kwanta amma ya ƙiya,wai har ni yake ce ma Yau kwanan sa ne!"? Murmushi marshal Omar yayi jin shiriritar junaid,wato yau da Abbansu yake kishi,    "Abba,just calm down ur mind,ka bani 5 minutes yanzu zan dawo,just wait,"   Ya ƙarasa maganar tare da miƙewa ya kama hanyar fucewa daga bedroom ɗin,   Zugudum abbansu yayi yana jiran dawowar Marshal, Saukowa downstairs yayi kai tsaye ya wuce bedroom ɗin Abban nasu,a hankali ya tura door tare da shigewa ciki,koda junaid yaji an tura ƙofa sae ya ɗan ɗago da kanshi don yaga wanene,ashe baiyi bacci ba damuwar jahad ta hana shi sak har yanzu a tsorace yake,duk a tunaninsa abbansu ne,karaf idanunsa suka sauka akan Marshal Omar dake shigowa ciki,ae yana ganin Marshal Omar ya qara ƙanƙame mommynshi,don yasan cewa abbansu ne yakai shi qara shine akazo a ɗauke shi,   Omar na ƙarasawa wurin gadon ya Shiga tattara hannun jallabiyar jikinshi,muryar junaid kamar zai kuka yace"Ya omar dan Allah kada ka ɗauke ni,wai ni mai yasa akeso a takuramin.....'bai ƙarasa maganar ba Omar ya ɗaukesa gaba ɗaya ya aza a kafaɗarshi,ya fuce tare dashi daga ɗakin,   Suna tafiya yana kuka kamar ƙaramin yaro,Omar yace"rufe mun baki junaid,banason ƙara jin wani sounds daga bakinka stupid,wai har abba kake cema Yau kwananka ne!tsaran wasan ka ne!ko don kaga yana wasa dakai ne shiyasa ka raina shi?   Ya ƙarasa maganar a lokacin da yake hawa upstairs, Cikin shessheƙar kuka junaid yace"Ya omar,ni fa ban raina shi ba,saboda me zai dinga zuwa yana kwana tare da mommy,bayan ni ya dace ace ina kwana a wurinta,abba baiyi mun adalci....'   Katse shi omar yayi da cewa"Shut up junaid,'      Tsit junaid yayi yana faman hura hanci,   "Tunda har ka fara kishi da mahaifinka,hakan na nufin cewar zaka Iya aikin Soja!yadda zaka ji daɗin kishin ƙasarka,"   Hankali tashe junaid yace"Am sorry ya Omar,bazan ƙara ba,Zan daina hanashi kwana,'    girgiza kai Omar yayi yana cewa"Ban amince ba,zuwa aikin Soja ba fashi junaid,U.S ma zamu turaka,zanyi ma sgr magana,dama abba kawai muke jira ya amince,kaga yanzu ka 6ata mashi rai nasan cewar a shirye yake daya miƙa ka wurinsu koya huta da shiriritarka,    Turo kopar bedroom ɗinsu yayi ya shige da junaid ciki,Abba na ganin shi ɗauke da junaid,ya ɗaure fuska a cikin zuciyarshi kuwa ba ƙaramin daɗi yaji ba,   Sauke shi saman gadon Omar yayi tare da cewa"Maza ka kwanta,"    turo baki junaid yayi yana kallon Abbansu,zuba mashi ido abban yayi yana kallon ikon Allah,    Kwantawa junaid yayi tare da Lullu6ewa da bargo,yayi ƙasa ƙasa da muryarshi yana cewa"abba hankalinka ya kwanta,ka rabani da mommyna,kuma gobe can zan kwana,in kuma aka hanani ɗakinsu sehrish zan dinga kwana,"   Saukowa abba yayi daga saman gadon ya kalli Omar tare da cewa"ngde ssae Omar,Ni zan wuce,mu kwana lpy,"   Fuskar Marshal ɗauke da Murmushi yace"Gud night abbana,"   Har yakai bakin ƙopar fita daga ɗakin ya juyo yana kallon Omar ɗin dake tsaye yana kallon bayansa yace"Omar wai cikin triplet ɗin nan Wacece taka acikinsu"?   Sunnar dakai ƙas Omar yayi yana faman sakin Murmushi,daƙyar ya iya furta sunanta"Hosana," Jinjina kai abbansu yayi fuskar nan ɗauke da murmushi yace"batare da 6ata lokaci ba,bayan an kammala walimar jibi zan nema maka auranta a wurin mahaifinta,saboda banason wani daga waje ya gansu yace yana so,nafison dukansu su auri na gida,saboda na yadda sosai da irin tarbiyar dana baku,zaku kula da rayuwarsu sosai,"   "But....Abba Rafayet fa,?shima zaka nema mashi auren ɗaya daga cikinsu in yaso sai a haɗa auren atare!!!!? *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. [1/3, 6:34 AM] Abue Saleh AlQuyraemey: *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Ƙarasa fitowa tayi daga cikin motar,jikinta na sanye da wani jigunannan lace,anyi mata riga da zani,rigar takai har guiwarta,ta coge ɗaurin ɗankwalin nan ture kaga tsiya,tun daga kan wuyanta zuwa hannayenta,duk zinari ne,tsohuwa mai ran ƙarfe,hajiya Ammi kenan Ummu Hossein,Ummu Azeema,Ummu Abusufyan,kaka ga su junaidu da kuma sehrish,fara ce tass bafullatanar asali doguwa kuma siririya,tsufanta bai hanata yin gayu ba,tsohuwar soja ce wadda tasha gwagwarmaya,kuma itace mace ta farko a lokacinsu data fara ruƙe muƙamin Major General,kaifi ɗaya ce ita,mace mai wuyar sha'ani,mutum mai tsananin haƙuri ne kawai zai iya jurar zama da ita,hannunta ɗaya na ruke da sandar karfe ta alfarma,yayin da ɗayan kuma yake ruƙe da sigari,tana tafiya tana busa ta,har ta hanci hayaƙin ke fitowa, Babu wanda yayi tunanin cewar zatazo da wuri,bata sanarma kowa ƙarfe nawa zata zo ba,duk sunyi tunanin sae wuraren marece zata ƙaraso,Atare da MG Osman da Captain Adam suka zo,sae Hajiya Sarah ƴar wurin yayanta Modibbo,tare da ya'yanta mata su biyu Yasmeen da noor,dukkansu ba zasu wuce shekara ashirin da biyu ba,tunda matasan gidan sukaji zuwan ammi nan fa kowa yasha jinin jikinshi don sun san zuwanta bai cika zama alkhairi ba,duk in tazo sai wani abu ya faru,wannan karan basu san dame tazo ba,gaba ɗayansu sun hallara a main palour ɗin suna jiran ƙarasowarta ciki,mutun ɗaya ne bai fito wurin tarbarta ba,bakowa bane face Abusufyan,tun da yaji zuwanta ya kasa samun sukuni,sae faman safa da marwa yakeyi acikin bedroom ɗinshi,jikinshi nata kerma ba don komai ba sai don zullumin abunda zai biyo baya,idan tayi arba da triplet ɗinshi,duk da yayi ma kanshi alƙawarin cewar,koda ace ta koresu to tabbas ƙafarsu ƙafarshi,bazai ƙara barin rayuwarsu ta wulaƙanta ba,duk inda zasu je zai kasance atare dasu, hayamm kuwa tana la6e jikin window tana leƙen Ammi,tun fitowarta daga mota,wani irin farin ciki ne ya lullu6eta saboda tana sa ran cewar tuggun da suka shirya,zaiyi aiki, Lokacin da suka shiga falon,nan fa kowa ya shiga miƙa gaisuwa,abun da zai baka mamaki,ko amsawa wannan batayi kamar mai fama da ciwon baki,sai dae ta ɗaga masu hannu,Azmee ce ta kaisu ɗakunan da aka gyara masu,domin su sauke gajiyar da suka kwaso,kafin zuwa anjima,kowa sai da ya kara zuwa gaishe ta ɗaya bayan ɗaya har ɗakin data sauka,mutun uku ne kawai basuje gaishe ta ba,Sgr,Abusufyan sae junaid wanda bai kaiga fitowa ba daga bedroom ɗinshi, Mg Osman kuwa a nan falon suka zauna tare da Marshal Omar,suna gaggaisawa,saboda anjima ba'a haɗu ba sunyi kewar junansu sosai, Hayaam tana ƙoƙarin zuge glass ɗin windon da take leƙe sai ga Motar Abbas tayi parking cikin gidan,tsayawa tayi tana jiran ganin su wanene kuma suka ƙara zuwa,kodai Aunty laila ce ta ƙaraso ne,bata ƙarasa zancen zucin nata ba,Abbas ya fito daga cikin motar,daga bisani kuma Amani da Amal suka fito atare daga cikin motar, Ƙura ido Hayaam tayi tana ƙare ma Amal kallo,cike da mamakin wacece wannan Kyakkyawar yarinyar da Amani tazo da ita,A iya saninta dae Amani bata ta6a haihuwa ba,balle harta haifi ƴa kamar wannan,duk yadda taso ta gane wacece yarinyar nan amma hakan ya gagara,kwakwalwarta a toshe take,saboda tsabar mugunta irin tasu tun Amal na ƙarama suka canza mata kamanni saboda uƙubar da take sha a hannunsa,dole hayamm ta kasa gane wacece ita, "Hayam!"muryar Azmee ce ta karaɗe kunnanta,da sauri ta rufe glass ɗin windown tare da juyowa tana kallon Azmee,shigowarta kenan ɗakin jikinta na Sanye da jallabiya baƙa,anyi mata kwalliyar zanen flower blue,veil ɗin data yafa ma blue ne,ba ƙaramin kyau azmee tayi ba,ta wanku sosai,   Ƙarasawa hayaam tayi wurinta tana faɗin"Aunty Azmee sae yanzu za'a tuna dani?yunwa kamar zata kashe ni,kowa yana rayuwarshi acikin gidan nan sai ni duk a ƙuntace,"   "Ke kika so ki ƙuntata kanki hayam,Sgr yanzu haka ya manta da cewar ya koreki daga gidan nan,zai iya yiwuwa ma ya manta dake gaba ɗaya,kuma kinga yau ranar Walima ne mutane duk sunzo,ba dole bane ya ankara dake ba,bama haka ba mutumin da kafin ya ɗaga ido ya kalli wani aiki ne a wurinsa,don haka ina baki shawarar ki daina kullan kanki,"    Tun kan azmee ta ƙarasa maganar hayaam ta soma washe baki,la66anta har rawa sukeyi wurin cewa"An..aunty Azmee kina nufin sgr ya manta da laifin da nayi mashi kuma zan iya fita inyi yawo na acikin gidan nan kamar kowa,'   Jinjina kai azmee tayi tare da cewa"Of course,amma fa hayaam koda gigin wasa kada ki kuskura ki ƙara yunƙurin zuwa sashen shi!duk yawon da zakiyi ki tsaya a downstairs babu ruwanki da abunda ya shafi upstairs ina fata kin gane"? yatsina fuska tayi tana fadin"dama ni Aunty azmee me zai kai ni,waccen karan ma tsautsayi ne da ƙaddara," "Sannan kuma,kada ki kuskura ki ƙara shiga shirgin Sehrish!kinsan dai yanzu tafi ƙarfinki nesa ba kusa ba,ƴar masu gida ce ita,kuma shalelen daddynsu,ga kuma yayyanta maza muddin kikace zaki ta6ata wlh zaki ta6o ma kanki ne,akanta sae abaki Red card na barin gidan nan,"   ta6e baki hayaam tayi,tana faman hura hanci,maganar ba ƙaramin ƙona mata rai tayi ba,don bata da yadda zatayi ne,   Murmushi azmee tasaki tare da juyawa ta kama hanyar fita tana faɗin"Yakamata kiyi wanka,ki shirya saiki fito ayi shagalin dake,"   Cikin sauri ta ruƙo rigar Azmee tace"Aunty Azmee don Allah ki taimakamun wlh yunwa nake ji,tun jiya da daddare rabona da Abinci,"   "Its Okey,zan kawo maki yanzu," Komawa ciki hayaam tayi tana jiran azmee ta kawo mata abinci taci,kafin tayi wanka ta kimtsa, bayan su Amani sun shigo cikin main palour ɗin,anan suka zauna suna gaisawa dasu kanal yousouf,kafin tabar wurin tare da Amal,wurin Azmee taje suka gaisa tayi masu kwatancen ɗakin Hajiya Azeema da kuma na gwaggo,duk saida tabisu ta gaishe su,hatta ɗakin Abusufyan saida suka je,sukayi mashi Allah sanya Alkhairi,daga nan suka dawo kitchen,lokacin Azmee tana haɗa ma Hayaam lunch ɗin da zata kai mata,     Juyowa tayi jin sallamarsu tace"har kun dawo"? Amani tace"Eh,duk naje nayi masu Allah sanya alkhairi,yanzu abunda ya rage mun inason zuwa wurin dasu yaran suke,bansan a wani ɗaki suke ba,' Azmee tace"Ae suna nan ɗakin da Sehrish take,ae kinsan ɗakinta wanda ke a kusa da namu,yakamata kuje wurinsu,'   Murmushi Amani ta saki aranta tace"ba dole inje ba,ni da nakeson na gyara tsakanina da Sehrish,"   A fili kuma tace"okey,nagane ɗakin bari muje wurinsu,"    Juyawa sukayi atare da Amal suka nufi ɗakinsu sehrish,abakin ƙopar ɗakin suka tsaya,Amani ta kwankwasa ƙopar,jahad ce ta buɗe kopar,ba ƙaramin kyau tayi ba,wankan swiss lace ne ajikinta wanda aka haɗa da bazin shadda,stones work ne ajikin kayan wanda ya ƙara fito da ɗinkin sosai,   Murmushi Amani ta sakar mata tare da cewa"Sehrish ce ko"?ta tambaya ne saboda Abbas ya sanar da ita cewar kamanninsu ɗaya sak,   Martanin murmushin jahad ta mayar mata kafin tace"A'a,ba ita bace,tana ciki in kira maki ita ne,"ta ƙarasa maganar tana kallon Amal wadda itama jahad ɗin take ta kallo,    Amani tace"bari mu shiga daga ciki,sai mu gaisa,"   Matsa mata hanya jahad tayi suka shiga cikin ɗakin,    A lokacin Sehrish na kwance saman gadon ta ɗan kishingiɗa,tana hutawa,saboda ba ƙaramin gajiya tayi ba,sun sha zurga zurga,gashi Anjima za'a fara walimar bayan Sallar la'asar,shiyasa ta dawo ɗaki don ta huta,kafin lokaci yayi,ganin Amani yasa ta miƙewa daga zaune tana kallonsu,   Wuri Amani ta samu daga gefen gadon ta zauna,Amal ma ta zauna,tun kafin ma Amanin tace wani abu sehrish tace"Sannunku da zuwa,"hakan ba ƙaramin daɗi yayi ma Amani ba,tayi tunanin zata ga akasin haka ne,   "Yawwa,fatan mun same ku cikin koshin lafiya"? Sehrish tace"Lafiya lou Alhmdllh," Amani tace"kin gane ni ko"?murmushi kawai sehrish ta saki,taya za'ae ta manta da matar da tace zata iya rasa ranta idan ta cigaba da shisshige ma matasan gidan,   "Ina fata dai baki ruƙe ni aranki ba?dan Allah ki manta da komai dana ta6a faɗa maki,komai ya wuce,yanzu zumunci ya ƙullu atsakaninmu,ko wancen karon ma da nayi maki wannan maganar,wlh bada wata manufa na faɗa maki hakan ba,"   Jinjina kai Sehrish tayi tare da cewa"babu komai,ae ya riga ya wuce,"   Ba ƙaramin daɗi Amani taji ba,juyawa tayi tare da kallon jahad dake tsaye tace"zo ki zauna mana,inaso muyi fira tare daku,"zagayawa jahad tayi ta 6angaren hannun hagu ta zauna daga gefen gadon, Amani tace"ina cikon ta ukun take ne?Abbas ya faɗamun cewa ku ƴan uku ne,"   Jahad tace"hakane,hosana ce babu,taje wurin yaya Omar ne" shiru Amani ta ɗan yi tana maimaita sunan hosana a cikin zuciyarta,kamar ta ta6a jin sunan abakin wani,"ke ya sunanki"? "Ni sunana jahad," jinjina kai amani tayi tare da cewa"Suna mai daɗi,amma nifa bansan komai ba,agame daku,sehrish kawai nasani tana aiki a gidan nan,"   Jahad tace"ae mu muna a wurin ya Omar ne,shi ya taimake mu a lokacin da muke cikin mawuyacin hali,bayan ƙaddara ta rabamu da ƴar uwarmu," ..A ruɗe Amani tace"Hannun Ya Omar" Jahad tace"eh,"   Cike da son jin ƙarin bayani Amani ta kuma cewa"Kun zauna a kaduna ne"?   Ita kanta jahad sai da gabanta ya faɗi jin Amani ta ambaci kaduna kai tsaye,taya akai tasan cewa sun zauna a kaduna,   Daƙyar ta iya bata amsa da cewa"Eh,mun zauna acan,daga baya ne Ya Omar ya dawo damu Abuja,gidan daddynmu,"   Tashin hankali,miƙewa amani tayi da sauri jikinta na rawa tace"Ga Amal nan ƙanwata ce,in ba damuwa ta zauna a wurinku,"   Amsa mata sukayi da toh,cikin sauri ta fuce daga ɗakin,kallon juna jahad da Sehrish suka yi atare,duk sun lura da yadda Amani ta ruɗe,    "Wacece wannan Sehrish"?jahad ce tayi mata tambayar,sehrish tace"matar yaya Abbas ce,Aunty Amani,"   Taso ta ƙara tambayarta,amma saboda Amal dake zaune a wurin yasa tayi shiru,tabbas ta so taga kamannin Aunty babba kaɗan a fuskar Amani,duk da Amani tafi kyau sosai,kuma ita bata da jiki irin na Aunty Babba,miƙewa jahad tayi tare da cewa"Zan fita yanzu zan dawo," Sehrish tace"adawo lafiya," Bayan jahad ta fita,Sehrish ta kalli Amal dake zaune,rashin sabo yasa ta kame kanta wuri guda,   Murmushi tasakar mata tare da cewa"ki saki jikinki mana,naga duk kin gaza samun natsuwa,ko dan bamu ta6a haɗuwa bane?"   Sunnar da kai Amal tayi tana murmushi,wata irin kunyace da ita,daƙyar ta iya cewa"banta6a zuwa nan ba,yau nafara zuwa,bazan iya sakin jikina ba,tunda bansan kowa anan ba,"   Sehrish tace"Ae kuwa yanzun nan zansa ki saba dani,da farko dai ki dinga kirana da Aunty Sehrish,saboda ina kallon ƙaramar fuskar nan taki nasan cewa na girme ki,tsawo ne kawai gare ki,amma a shekaru ba zaki wuce sha huɗu ba,ko nayi ƙarya"? dariya Amal tayi tana girgixa kai tace"A'a bakiyi ƙarya ba,shekarata sha huɗu amma na kusa kai shekara goma sha biyar,nan bada jimawa ba,"   "Kice zamu zo yanka cake ko"?acewar sehrish,   Amal tace"Eh,zan gayyace ku idan lokacin yayi,"   Sehrish tace"Nima na kusa cika shekara sha takwas,banma sani ba ko na kai shekara sha takwas ko ban kai ba,nifa banma son ranar da aka jefo ni duniya ba,ni dai kawai na ganni ina yawo na ne....'kasa ƙarasa maganar tayi saboda dariyar da Amal ta kwashe da ita,abu kamar wasa sai gashi cikin lokaci ƙankani sun saba da juna,nan suka zauna suna ta fira atsakaninsu, Amani kuwa tun bayan da ta fita daga ɗakinsu sehrish,tarasa inda zata tsoma kanta,abun ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba,Aunty babba ta sanar da ita cewar tasa an zubar da yaran da Omar ya kawo mata,kuma tace mata ƴan biyu ne yaran,hakan na nufin cewar jahad ne da hosana a wurinshi?kamar yadda jahad ta sanar da ita cewa su A wurin yaya Omar suke,indae dagaske hakane to taya akai Yaran suka dawo wajen Marshal Omar bayan tasa an zubar dasu!?kodai Omar ya sanya ɗan leƙen asiri ne acikin gidan?tabbas hakan zai iya faruwa,indai kuwa hakane Watan cin uban Aunty laila ya tsaya,Zuwa maiduguri ba fashi,   Acewar Amani wadda ke ta faman yin safa da Marwa a tsakanin corridor ɗin ɗakunansu sehrish,daga bisani tace"Allah yaso ni ban tsoma hannu na ba,a wurin cutar dasu ba,ashe da rabon aure na yayi lasting,Aunty babba kam ta shiga uku,taja ma kanta bala'e,kwara ma da hakan ya faru,da nayi niyyar ɗaukar ma Amal fansa,amma yanzu na fasa,zan zuba idone kawai inga yadda dramar nan zata kaya,"ta ƙarasa zancen zucin nata,fuskarta ɗauke da murmushi,ba komai take hangowa ba face yadda rayuwar Aunty babba zata ƙare,........' Bayan fitar jahad,kitchen ta wuce ta shirya lunch acikin tray,kamar ita zata ci,upstairs ta wuce dashi,adai dai ƙopar ɗakin junaid ta tsaya tare da sanya hannunta ɗaya,ta ɗan bubbuga ƙopar ɗakin,wata murya taji daga cikin ɗakin ta amsa mata da cewa"Wanene"?muryar kuma bata junaid bace,   "Ni ce," ta bashi amsa ataikace "Kece wa"? "Jahad,"shiru taji anyi mata kafin,harta fidda rai da za'a buɗe mata,tana ƙoƙarin barin wurin taji alamun ana buɗe ƙopar,tsayawa tayi har ya kammala bude kopar,ganin fuskar wani daban bata junaid ba yasa tasha jinin jikinta,musamman yadda taga fuskar mutumin a murtuke babu fara'a ko misƙala zarratin, "Wa kike nema"? Muryarta na rawa tace"Wurin junaid nazo,naga ban ganshi ba duk yau," "Shine kika zo kawo mashi abinci?yace maki yana jin yunwa ne"?shiru jahad tayi masa batace komai ba,da alama dae wannan ba ƙaramin masifaffe bane, "Wuce ki shiga,"ya faɗi hakan tare da matsa mata hanya ta wuce ciki,shi kuma ya fuce daga ɗakin, jikinta sai kerma yakeyi saboda tsoran mutumin da tayi arba dashi,hakanan taji tsanarshi aranta,kuma sam baiyi mata kama da mutanen kirki ba, Lokacin da ta ƙarasa shiga ɗakin a kwance ta samu junaid,daga shi sai farar shirt da short fari a jikinshi,ya kwantar da kanshi asaman pillow,idanunshi na arufe,ajiye mashi tray ɗin tayi asaman front table ɗin gadon nasa,sannan ta samu wuri daga gefen gadon ta zauna tare da ambaton sunanshi"junaid," A hankali ya buɗe idanunshi tare da azasu akan fuskar jahad,yanayin shi ya nuna tamkar baijin daɗin jikinshi,idanunshi kansu sun marairaice, Bai tanka mata ba sae da ya gama ƙare mata kallo sosai,saboda ya tantance wacece acikinsu,tashi yayi daga zaune sannan yace"Jahad ko"? ɗaga mashi kai tayi alamar eh,sannan ta ƙara da cewa"duk yau ban ganka ba,shiyasa nace bari nazo na duba ka,hada abinci ma nazo maka dashi,duk da bansan ko kana jin yunwa ba," "Thanks for your caring,duk yau babu wanda ya damu dani,sai ke kawai,naji daɗi sosai,"yayi maganar tare da sauko da ƙafafunshi ƙasa,hannu yakai zai ɗauki jug,ta riga shi ɗaukar jug ɗin tare da cewa"bari na zuba maka,"dakatawa yayi ta tsiyaya mashi lemu mai sanyi acikin cup,sannan ta miƙa mashi,yasa hannu ya kar6a,tare da kai cup ɗin saitin bakinshi yana kur6a, binshi tayi da kallo,yayi wani irin haske fari fat,kamar mara jini a jiki,hakanan ta dinga jin wani irin tausayinshi na shigarta,ga tsananin ƙaunarshi da takeyi kamar kamar me, Har ya kammala shan lemun bata sani ba,juyawar da zaiyi suka haɗa ido dashi,kawar da idonta tayi gefe guda tare da yin saurin cewa"Kamar baka lafiya ko"? "Me kika gani"? "Kawai yanayinka na gani,kamar na wanda bashi da ƙoshin lafiya," "Lafiyata ƙalou,don inajin yunwa ne shiyasa kika ganni haka,amma da zarar naci na ƙoshi,zan dawo dai dai," "Kasan kana jin yunwa amma meyasa baka tashi ka nemi abinci ba"?tayi maganar a yayin da take janyo plate ta shiga zuba mashi fried rice aciki, "Tun safe fa naketa yin bacci,ni kaina bansan ya akai nayi bacci mai tsayi ba,kuma dana tashi jikina duk ba ƙwari,shiyasa bansamu na sauko downstairs ba,saboda kasalar data baibaye ni, "Kuma baka sha wani abu ba?kamar maganin bacci"? Shiru junaid ya ɗanyi yana tunani kafin yace"a'a bansha komai ba,amma ya haroon ya kawo mun wani tea a cup wuraren ƙarfe takwas yace mun insha,kuma saida na tambayeshi maganin menene yace mun maganin ƙara kuzari ne,shine nasha,tun daga lokacin nidai ban ƙara sanin meke wakana ba,yanzu ma da kika ganni a kwance tashi na kenan,kuma shi ya tashe ni,yace mun in tashi inyi wanka in shirya,lokacin walima ya kusa," ɗagowa jahad tayi tare da kallon fuskarshi tace"Wannan mutumin daya fita yanzu shine Ya haroon"!? ɗaga mata kai yayi alamar eh, ta kuma cewa"Wanene shi?don ban ta6a ganinshi ba a gidan," Junaid yace"Shima yayan mu ne,bai cika zama gida bane shiyasa baki ta6a ganinshi ba," "Kada na cika ka da surutu,ka fara cin abincin," Maƙe hannayensa yayi tare da cewa"Hannu na ciwo yakeyi mun,"murmushi ta saki tare da kai hannu ta ɗauki cokali tana faɗin"bari na baka abaki to," ɗebowa ta dinga yi tana tura mashi abakinshi yana Ci suna fira,gwanin ban sha'awa,a haka harta samu yaci abincin sosai,sannan ya tashi ya shiga toilet wanka,zama tayi tana jiran fitowarshi saboda yace ta jira shi,su fita atare,hakan ba ƙaramin daɗi yayi mata ba,a sannu a sannu dai junaid ya fara sakewa da ita,Allah sarki *Boss Bature* Bayan Sallar la'asar,kowa ya ɗauki wani sabon wankan,Amani da kanta tayi masu Jahad makeup ita da Hosana da Sehrish,gaba ɗayansu suka sanya Swiss lace ajikinsu,wanda aka ɗinka masu shi domin su sanya a aranar walimar,riga da skirt ne ba ƙaramin kyau kayan sukayi masu ba,sun wanku iya wankuwa,yadda kasan dollar wurin kyau haka suka koma,Suna acikin ɗakin nasu Su huɗu hada Amal,in aka haɗa da Amani sun zama su biyar kenan,zama tayi tana ƙarasa gyara masu ɗaurin ɗan kwalin da tayi masu, A Can ciki kuwa Matasan gidan duk sun hallara,Azmee da Saude ne suke ta ɗawainiyar bin kowani table dake a wurin suna Jejjera abinci kala kala,daga bayane hayaam ta samu damar fitowa daƙyar,tun tana ƴan kame kame kamar mara gaskiya har dae ta fara sakewa,tashiga tayasu Azmee kai ma baƙi lemu, A hankali Motarsu Aunty Babba,ta shararo izuwa cikin gidan,a dai dai parking space,hafsat ta tsayar da motar,tare da juyawa ta kalli fuskar Mommyn nata dake ta faman jan minshari,tunda suka taho ta kama bacci acikin motar,hannu hafsat tasa tare da bubbuga kafadarta,a firgice Aunty babba ta farka tana fadin"Har mun ƙaraso ne,"   Hafsat tace"eh mana,gamu acikin gidan ma,kin barni da driving kina ta sharar bacci,' Yamutsa fuska Aunty babba tayi tare da buɗe motar tana faɗin,wlh agajiye nake,ga baccin ma bai isheni ba,kuma yunwa ma nake ji,'    Bayan motar ta tsaya tare da buɗe Boot ɗin motar,ta curo trolley ɗin kayansu,tare da saukko dashi ƙasa,    Sai da hafsat ta sanya niqabin da ta siya a hanya sannan ta buɗe motar ta fito,hannunta ruƙe da ƴar purse ɗinta,ganinta da niqabi yasa Aunty babba jan guntun tsoki tare da fadin"Yau naga ikon Allah,kamar wata Munafuka,kin nace dae yau sai kin sanya wannan baƙin abun a fuskarki,kamar wata ƴar shi'a"    "Mommy ba zaki gane bane," Tayi maganar tare da kama hanyar shiga cikin gidan,bin bayanta aunty baba tayi tana fadin"ba zaki zo ki kar6i trolley ɗin ba"   "Haba Mommy,Duk aikin driving ɗin da nayi,kuma sai na wani ɗauki trolley,ae ke yakamata ki janyoshi,tun fa da muka kamo hanya kike ta bacci,kika barni da aiki,nima agajiye nake bazan iya ɗaukar shi ba,"    "Kar Allah yasa ki ɗauka toh,"suna tafe suna magana har suka shiga cikin Main palour ɗin,Hayaam najin sallamar Aunty babba,ta wani saki ihu har saida hankalin kowa ya dawo kanta,da gudu taje ta rungumota tana faɗin"Wayyo Allah aunty laila,tun dazu nake ta baza ido inga zuwanku amma shiru,har na fara fidda rai da zuwanku ashe kuna hanya,"tayi maganar tare da raba jikinta daga na aunty babba,fuskar nan awashe Aunty babba tace"Mezai hana mu zuwa,naso na sanar maki wlh mantawa nayi,koda yake bacci fa nayi a mota,hada ƙarin haka yasa ban samu na kira ki awaya ba,'   "Gaskiya nayi kewar ku sosai,"acewar hayaam tayi maganar a yayin da take mayar da idanunta akan Hafsat dake sanye da niqabi,a ruɗe tace"Kai!wai hafsat ce sanye da niqabi,"   Hannu hafsat ta sanya tare da ɗan ɗage niqabin tace"Nice mana,gaba ɗaya hankalinki na akan mommy dayake kinfi damuwa da ita,"   Washe baki hayaam ta kuma yi tare da rungumo hafsat ajikinta tana faɗin"Sorry bangane ki bane wlh,kema ce kin sanya niqabi kamar wata mara gaskiya,"   Suna cikin magana muryar Azmee ta katse su da cewa"maraba da manyan baƙi,Yau su hajiya laila ne a gidan namu,wata sabon gani,yau za'ayi ruwa da ƙanƙara,"   Dariya sukayi gaba ɗayansu,kafin daga bisani Aunty babba tace"Ae wannan zuwan na musamman ne,Har sai kun gaji damu Allah,"tana magana hafsat na zungurinta alamar ta daina faɗin zasu jima,amma zafin ɗumi yasa ko lura batayi ba balle ta ankare,   "Ae tunda na ganku da trolley ɗin kayan nan nasan cewa zaku jima mana anan,wataƙil ma har sai an aurar da ƴa'ƴan namu tukunna,kunga sai ayi agabanku,'   Gaban aunty babba ne ya faɗi rass,a razane tace"Auren wasu ƴa'ƴa kenan"?   dariya azmee tayi tare da cewa"Ƴa'ƴanku mana na wurin Abusufyan,"   ɗaure fuska Aunty babba tayi tana fadin"haba dae,wani aure kuma ana zaman lafiya,daga ganin yaran kuma sai ki fara yi masu fatan yin aure,duka nawa suke,bana ji ance ƴan shekara sha bane,'   kafin azmee ta kuma cewa wani abu hafsat tace"Dan Allah mu shiga ciki mu zauna,wlh agajiye nake,gashi ko salla ma ba muyi ba,"  Atare suka ƙarasa shiga ciki,bayan sun kammala gaisawa da mutanen dake zaune a babban falon,daga bisani hayaam takaisu bedroom ɗinta,suna shiga ciki hafsat ta cire niqabin data sanya,tai wurgi dashi saman gadon,tashige toilet don ta ɗauro alwala,a ƙagare take da tayi arba dasu jahad,duk da tsoran karsu canza mata,musamman in suka tuna abubuwan da sukayi masu a gidansu,tana cikin toilet tajiyo muryar hayaam tana fadin"Tun jiya fa na tura maki hotunan nasu,baki gani bane,kuma har hafsat saida na kira a waya na sanar da ita don ta tunasar dake,'   Aunty babba tace"Gaskiya ni banga wani hoto ba da kika turamun a whatsapp ɗina,mu barma zancen tunda dae gani acikin gidan zan gansu da ido,batare da nasha wata wahala ba,'   Hayaam tace"Ae yanzu haka suna can cikin ɗakinsu tare da Amani...'   Cike da mamaki Aunty babba tace"Amani kuma?Ubanme ya haɗata dasu da har take shiga ɗakinsu?Oh ni yau naji ikon Allah,wannan shisshigi da kutsu irin na Amani,"   "Nima azmee ce ke sanar dani cewa tana a ɗakinsu wai tanayi masu kwalliya,ni duk bama wannan bane damuwata ba,Akwai wata kyakkyawar yarinya fara da Amani tazo da ita,na rasa gane wacece yarinyar nan,kuma fuskar yarinyar sak irinta amanin ce,"   Aunty babba tace"To fa,ko ina tasamu yarinya,zai iya yuwuwa fa daga gidan marayu Abbas ya ɗaukko masu ita don su raina,kinfa son cewa basu ta6a haihuwa ba,'    "Bari naje ciki,kada azmee taji ni shiru,ina ɗan tayata aiki ne,'acewar hayaam   Harara Aunty babba ta watsa mata tare da cewa"dama aiki na turoki kiyi acikin gidan?shiyasa naga duk kin zabge,nida zanzo inga ko'ina na jikinki ya cicciko,amma sai uban ƙasusuwan wuya,kamar wadda tayi jinya,'   Tsuke fuska hayaam tayi tana faɗin"Bakisan halin dana shiga bane,shiyasa zaki ce haka,tunfa da Sgr ya kore ni daga gidan nan,ban ƙara samun kwanciyar hankali ba,kullum ina ƙumshe acikin ɗaki saboda tsoran kar muyi arba dashi,ga ciwon yunwa dake damuna,ba don azmee ba ae da tuni na jima da sheƙawa,itafa ce take kawomun abinci har ɗakina,wani lokacin in ta manta bata kawo mun ba,sae dai fa in dare yayi kowa yayi bacci in saci hanya inje kitchen in ɗebo abinci,gaskiya nasha wahala sosai,   "Laifinki ne hayaam,kina zaman zaman lafiyarki acikin gidan nan,Amma kika toƙano masifa,kirasa wa zaki kaima hari sai Sgr,ae wlh ki godema Allah dabai kakkaryaki ba,nikaina nayi mamaki da kikace iya korarki yayi kawai,'   Tur6une fuska hayaam tayi tare da juyawa tana fadin"Ni dae mu bar maganar ae yariga da ya wuce,kuma ma ae ya yafe mun,bakiga yanzu ina yawo na hankali kwance acikin gidan ba,"   Aunty babba tace"Allah yasa dagaske ne cewar ya yafe maki ɗin,sai kiyi taka tsantsan kafin mu samu Allah ya cika mana burin mu,don wannan karon da shirina nazo,Bazan bar gidan nan ba,har sai naga an shafa fatihar aurenki,keda Sgr," Cike da farin ciki hayaam ta sanya tafin hannunta tare da rufe fuskarta tana sakin dariyar farin ciki,    "Aunty laila kina ganin hakan zai yiwu kuwa?ga Yaran nan ƴa'ƴan abusufyan,wlh ba ƙananu bane balle ace basu isa aure ba,Sun kaifa sha Takwas inaji,kuma wlh bakiga surar jikinsu ba,matane sosai,ni tunda nagansu ma duk sai naji na tsani kaina,kuma kinga su ƴan gidane za'a iya tunanin haɗasu auren Zumunci...'   Tunkan ta ƙarasa maganar aunty babba tace"Impossible!wlh bazai ta6a yiwuwa ba!Muddin ina numfashi ɗaya daga cikinsu bazata ta6a auren Sgr ba,kwara ma Omar abra saita haƙura amma Allah sgr ya Haramta agaresu na haramta masu shi,da bala'e sai ya aureki,ko anaso ko ba'aso,babu wani shege daya isa ya hana wlh,babu shi,"yadda Aunty babba ke cika baki tana magana ba ƙaramin dariya ya so yaba hafsat ba dake acikin toilet tana sauraronsu,ita batasan halin da suke ciki ba,sae faman kuri take tana cika baki,    Ita kuwa hayaam sae faman washe baki takeyi,gaba daya ta miƙa yardar ta ga Aunty babba,ae gani takeyi zata iya aikata komai don ta mallaka mata Sgr,      Bayan fitar hayaam daga ɗakin Hafsat ta fito daga cikin toilet din,idonta na akan Aunty babba data ɗan kishingiɗa asaman gadon,   "Mommy yakamata kije kiyi sallah,kinsan fa yanzu za'a hallara gaba ɗaya wurin waleemar yakamata ki hanzarta yin sallar,"    yatsina fuska tayi tare da cewa"Anya zan iya yin sallar nan kuwa,nagaji sosai,zuwa anjima dai nayi sai in haɗa da magriba duka inyi,"   girgiza kai kawai hafsat tayi batare da ta ƙara cewa komai ba,don ba yau ta saba yin haka ba,ita kanta hafsat ɗin zamanta dasu jahad ne ta fara yin sallah cikin lokacinta,   Zaune yake agefen gadonshi ya zabga uban tagumi,tun bayan da suka dawo daga sallar la'asar,yadawo ɗakinshi atakure,turo kopar ɗakin nashi Abba yayi tare da shigowa ciki,ba ƙaramin tausayi abusufyan ya bashi ba,wuri ya samu tare da zama daga gefenshi sannan yace"Bana faɗa maka cewa ka kwantar da hankalinka ba?jibi yadda duk kabi ka tukura kanka,"   ɗagowa yayi tare da kai idanunshi kan abba,muryarshi asanyaye yace"bansan ya zanyi bane,hankalina yaƙi kwanciya wlh,bansan wane hukunci Ammi zata yanke mun ba,ni tsorona kada tace bata yarda cewar da aure na samu su jahad ba,kasan halinta yaya hossein,tana da wuyar sha'ani," Abba yace"hakane,amma insha Allah zanyi iyakar bakin ƙoƙarina wurin ganin na fahimtar da ita,kaima kasan cewa bazan ta6a bari yaran nan su tozarta ba akan idon kowa,Ammi tana buƙatar hujjoji masu ƙarfi kafin ta gasgata abu,zamuyi kokari wurin ganin cewa munyi amfani da hujjojin da muke dasu a hannu wurin fahimtar da ita,abunda nakeso dakai yanzu ka saki jikinka,nasan cewa da anjima kaɗan idan ta farka daga bacci zata fito nan babban falon,so nake kazo da ƙwarin guiwarka ka gaishe da ita,kasan kun jima baku haɗu ba,kuma dama can kai mai laifi ne a wurinta,'   fuskar Abusufyan cike da damuwa yace"Hada ƙarin hakan yasa nake fargabar haɗuwa da ita,Ni kullum mai laifi ne a wurinta,ko kirana ma bata ɗagawa,tunda nabar nigeria shekara goma sha,amma mommy bata ta6a ɗaukar waya da sunan zata kira ni ba,kuma ko na kirata bata ɗagawa,ni ina ganin kamar bata so na ne,shiyasa takeyi mun haka,'    ruƙe hannunshi abba yayi acikin nashi"abunda kake tunani ba haka bane,zanma iya cewa tafi sonka fiye da kowa,kuma ta damu da kai sosai,babban laifin da kayi mata shine naƙin sanar da ita dalilin da yasa kabar Nigeria,ammi batasan komai game da tafiyarka ba,tayi kewarka sosai,don akwai lokacin da ta kirani a waya,kuka ne kawai batayi ba a lokacin,saboda ka tafi batare da saninta ba,wannan dalilin ne yasa take fushi dakai,amma yanzu ina da tabbacin cewar in har muka sanar da ita dalilin tafiyarka,zata fahimce mu,kuma zata kar6i yaran nan hannu bibbiyu,kuma zata yafe maka"   Jiki asanyaye abusufyan yace"Allah yasa,dana fi kowa farin ciki,"   Murmushi abba yayi tare da miƙewa tsaye ruke da hannun abusufyan yana cewa"Tashi muje ciki,nasan yanzu haka triplet ɗinka suna nan,sun ɗau wanka suna jiran daddynsu don suyi hoto tare dashi,"   Jin haka yasa Abusufyan sakin fara'a a fuskarshi nan take yaji damuwarshi ta ragu saboda an ambaci ƴan ukunshi,    atare da abba suka fito daga cikin ɗakin,adai dai lokacin Hajiya Azeema da gwaggon katsina da saude suma duk sun fito,kowa yasha kwalliya a fuskarshi,ga harris shima tare da Marshal Omar duk sun hallara anan falon,A jere su Sehrish suka fito su uku Ita dasu jahad hosana,sae Amal dake abayansu tare da Amani,   Ae tunda suka shigo cikin falon hankalin kowa ya dawo kansu,yadda kasan wasu taurari haka suka bayyana,kai tsaye wurin abusufyan suka nufa,haɗasu yayi su duka ya rungumesu sosai,bayan ya sakesu,suka gaishe da Abba tare dasu Marshal Omar dake tsaitsaye a wurin,Hannu abba yasa tare da jan kumatun hosana yace"Amaryar Omar,irin wannan kyau haka,"da sauri tasa hannu tare da rufe fuskarta,tana dariya,kawar da kai gefe Omar yayi yana ɗan sakin Murmushi,da zasu bashi dama da ba abunda zai hana ya rungumota don ba ƙaramin kyau tayi mashi ba,matsowa kanal yousouf yayi kusa dasu yana fadin"Uncle ni wacce za'a bani acikinsu tunda ya Omar yayi kamun tashi,kada su ƙare ni in rasa,"dariya sukayi gaba dayan su,Uncle abusufyan yace"Layi zaka bi,don mutun ko da kuɗinshi saida rabonshi," Abba ya kar6e da cewa"kwarai kuwa,sae wanda ya dage da sallar dare zamu bamawa," daga bayansu suka jiyo muryar junaid yana cewa"Kamar ni kenan,duk gidan nan babu wanda yakai ni tashi yin sallar dare,"ya ƙarasa maganar tare da ruƙe qugunshi,fuskar nan ɗauke da wannan kyakkyawan murmushin nashi,yayin da idanunshi ke akan jahad, fashewa suka kumayi da dariya,kanal yousouf yace"haba junaid,cewa zakayi duk gidan nan babu wanda yakai ka,sharar bacci idan dare yayi,mutumin da daƙyar ake tashin shi sallar asuba shine yake cika baki yana faɗin yafi kowa sallar dare," bubbuga ƙafa junaid yayi cike da shagwa6a yace"Kai yaya yousouf dan Allah ka daina faɗin haka,kada kasa araina ni," "Raini kuma na yaushe junaid!agabansu fa kake bubbuga ƙafa kamar ƙaramin yaro kana shagwa6a,a haka kake cewa kar araina ka,wace mace ce zata so ta auri shagwa6a66an namiji irinka?acewar kanal yousouf, Tur6une fuska junaid yayi yana faman zumbura baki,juyawa yayi tare da kai idanunshi kan abusufyan yace"Uncle,ae dai zaka bani kyautar ɗaya ko"? Abusufyan yace"mezai hana junaid?ko sisi bana buƙata,duk wacce kakeso acikinsu,zan baka ita kyauta,basai ka biya sadaki ba," gwalo yayi ma kanal yousouf yana fadin"ae dae Uncle yace zai bani,kuma a kyauta ma," Hakan ba ƙaramin dariya ya basu ba,duk wannan rashin wayon da Junaid ke yi akan idon jahad,zubama sarautar Allah ido tayi,aranta tace wai dama haka yake?saboda ita bata ta6a ganin junaid na shagwa6a agabanta ba,hada su gwalo ɗabi'unsa kamar na yaron goye,kaɗan kika gani Cike da nishaɗi sukeyin firar tasu,adai dai lokacin General ishaq da Abbas suka shigo cikin main palour ɗin,sae faman sakin fara'a suke yi,ƙarasa shigowa sukayi kai tsaye suka nufi inda su Abba ke tsaye,gaishe da abba sukayi,kafin su jahad suka haɗa baki wurin gaisar dasu, Fuskar ishaq ɗauke da murmushi yace"Masha Allah,nama rasa abunda zance,yanzu wannan duk namu ne"?yayi maganar yana nuna su hosana,Abba ne ya bashi amsar cewa"Naku ne ishaq,halak malak Allah ya mallaka maku,gasu nan harsu uku," Abbas yace"kamar yadda Allah ya nuna mana wannan ranar da ranmu kuma da lafiyarmu,ina fata Allah ya ƙara haɗamu a ranar auransu kamar haka dae........' haɗa baki su Abba suka yi wurin cewa"Ameen,"banda abusufyan wanda ya sunnar da kanshi ƙasa yana murmushi,Sehrish da jahad kuwa duk kunya ta gama rufesu, Abba yace"ko baku son auren ne"? Shiru su kayi suna faman ƙumshe dariya, "Sun ma isa suce basa so?ga yayyansu nan duk tazurai,ae dole su bada hadin Kai asamu a rufa ma juna asiri," cike da zolaya ishaq yayi maganar,yayi matuƙar basu dariya, Adai dai lokacin Aunty babba ta shigo cikin falon ita da hafsat,😲 *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.   [1/3, 6:34 AM] Abue Saleh AlQuyraemey: *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Tofah nan fa kowa ya shiga tunanin wata hujja ce Sgr ke da ita?kanga wayar yayi a kunnansa,then Calmly ya furta"Ku ƙaraso ciki,"jin haka yasa kowa kai idanunshi kan ƙopar shigowa falon,don ganin su wanene zasu shigo ciki, Bada jimawa ba,wata haɗaɗɗiyar Wheel chair Golden Colour mai ɗauke da wani dattijo tsoho tukuf fari tass hatta sumar kanshi furfura ce fara tass babu zaren gashi ko ɗaya daya kasance launin baƙi,hatta gashin girarsa dana idonsa fari ne tass duk furfura ta mamaye ko'ina,wani matashi ne ke ruƙe da ita yana turashi a nutse,tashin hankali ae koda Ammi tayi Arba da mutumin dake a saman wheel chair ɗin nan,hankalinta gaba ɗaya ya tashi haikam,ba ita ba Hatta su Abba dasu Gwaggo da Azeema sunyi matuƙar mamakin ganinshi,saboda a iya saninsu baya qasar,a Saudi Arabia yake da zama,amma sai gashi yau Unexpected yazo,wannan wani irin zuwan bazata ne? Lokacin da matashin ya ƙaraso dashi ciki Ammi ta tabbatar da cewar dagaske dae shine,a kiɗime ta miƙe tsaye muryarta na in,ina ta ambaci sunan shi"Mo...moddibo" Wani irin kallo tsohon ya wurga mata,kallon zakiyi bayani,gwaggon katsina kuwa wani irin farin ciki ne ya lullu6e ta,saboda tasan cewa tunda Modibbo ya tako da ƙafafunsa yazo Nigeria to tabbas za'a samu maslaha,saboda duk duniyar nan babu wanda ke taka ma Ammi burki in ta burkice sai Shi!mugun shakkar shi take ji,saboda shi tamkar Ubane agareta,a hannunshi ta taso,shiyasa yasan hanyoyi da dama da zai iya tankwarata,kuma duk wasu halaye nata da ɗabi'unta nashi ne sak ta ɗaukko,amma shi da ya manyanta ya ajiye wannan jin kan,' Bayan saurayin ya tsayar da wheel chair ɗin,Modibbo ya yunƙura tare da miƙewa da sandar hannunshi,cikin sauri suka bashi wuri,ya samu wuri ya zauna a hakimce saman sofa,nan kowa ya shiga gaishe dashi suna yi mashi sannu da zuwa,fuskar nan tashi asake yake amsa masu,ba ƙaramin daɗin zuwan modibbo suka ji ba,bayan ya kammala kar6ar gaisuwarsu ɗaya bayan ɗaya,   Sannan Ammi tace"Yaya sannu da zuwa,ya gajiyar tafiya"    Fuskarshi aɗaure yace"Gajiya tabi jiki,ae ba yau nazo ba,tun shekaran jiya ina ƙasar nan,zuwa ne kawai banyi ba,kuma ba don kowa nazo ba sai don saboda ke!"   Jin haka yasa ta koma ta zauna,jiki asanyaye, Cikin sauri Abba ya kalli su fawan tare dayi masu alamar su tashi su bar wurin,"mikewa su kayi dama Jahan a ƙagare yake daya bar wurin,duk ji yake kamar ya ɗosa mazannansa akan wuta,atare suka miƙe tare da barin wurin,Ya rage daga Gwaggon katsina,Abbansu,hajiya Azeema,General ishaq,da Cg Abbas,Uncle Abusufyan,marshal Omar da Sgr,bayan su kuma sae su Jahad dake zaune ƙasa,duk sunyi zuru rayuwarsu a hannun Allah,basu san su wanene waɗannan tsoffin ba,amma sun tsorata dasu,musamman Ammi data tayar masu da Hankali,har tana ƙoƙarin korarsu daga gidan, Bayan su jahan sun shiga ciki,ya fashe da dariya hada dafe ciki yana faɗin"Dama ance GABA DA GABANTA ALJANI YA TAKA WUTA"💥 Junaid kuwa,bedroom ɗin Abbansu ya wuce,anan ya samu mommynsu tsaye agaban drawer,jikinta sanye da doguwar riga,tana ƙoƙarin sanya mayafi akanta,   Sam bata lura dashi ba,har saida ya ƙarasa bayanta tare da rungumota,hannu tasa tare da janyoshi ta dawo dashi ta gabanta,a shagwa6e ya ambaci sunanta"Mommy dama kina a ɗaki,bakisan meke faruwa ba a babban falo,"   Hannu tasa tare da shafa fuskarshi tace"Romeo,bani da alaƙa da abunda ke faruwa acan,yanzu faɗamun naga fuskarka kamar akwai damuwa,"   "Mommy,ba Ammi bace take son korar su Jahad daga gidan nan ba,"   "To menene damuwarka aciki don ta kore su"?   Sakin baki junaid yayi yana kallonta kafin ya ɗaure fuskarshi yace"Haba Mommy,ƴa'ƴan uncle ɗinmu fa ne,taya ba zan damu ba,uncle fa yana sonmu sosai,muma dole mu so ya'yanshi,kuma su jinin mu ne,nidai wlh banso ta koresu,kuma Allah koda ace ta koresu,wlh saina bisu.....'ya ƙarasa maganar yana zum6ura baki,   Hannu tasa taja kumatunsa"Ni kuma an gaya maka zan barka ne?zansa a ɗauke mun kaine,in kaika U.s mu cigaba da rayuwarmu acan,ko ba zaka bi mommynka bane,"    Bubbuga ƙafarsa yayi tare da cewa"I wanna fallow u Mom,amma Allah sai dai mu tafi mu duka tare dasu sehrish,jahad da hosana,"    "Dole dai saina je dasu"? ɗaga mata kai yayi alamar eh,janyo shi tayi ta rungumeshi ajikinta,"don't worry dear kome kakeso zanyi,indae hakan zai faranta maka rai,yanzu mu zauna ka tayani fira,inaso mu tattauna wata magana dakai mai mahimmanci,"   Komawa sukayi tare da zama daga saman gadon,suka ci gaba da tattaunawa a tsakaninsu, *Aunty Babba* Lokacin da suka faɗa cikin ɗakin suna murna ita da hayaam,tsayawa sukayi daga tsaye,suna tattaunawa,Aunty babba tace"Ae dama saida raina ya bani cewar Ammi bazata barsu su zauna a gidan nan ba!gaskiya matar nan ta burge ni wlh,yadda ta zagesu tass ta kirasu da shaggu hakan ba ƙaramin nishaɗi ya sani ba,in banda ma shashasha irin Abusufyan taya zaka kawo ƴa'ƴa daga sama kace ya'yanka ne,kuma kayi tunanin cewa kowa zai yarda dakai?Ae ni wlh tayi mun dai dai matar nan," Ta ƙarasa maganar tana faman sakin shu'umin murmushin nan nata, Hayaam tace"Nima ba ƙaramin burgeni tayi ba,naci dariya lokacin data korasu suka watsa aguje suna kuka,ƴan jakar uban,yanzu sai muga ina zasu dosa,dama su kashe kansu kawai su huta muma kuma munsamu natsuwa," cike da nishaɗi take maganar tana watsa hannu alamar ita ko ajikinta,   "Dama abunda yasa nake son Ammi ta koresu,kinga na farko zasu fita daga cikin zuri'arsu ne gaba ɗaya,babu su babu auren ɗaya daga cikin ƴa'ƴan Abba,saboda Ammi bazata bari su auri bare ba,balle kuma yaran da ta ambaci sunansu da shaggu,Secondly kuma wannan korar da tayi masu,zai hana Ishaq da Omar su tuhume ni akan tonan asirin da waccen Zararrar taso tayi mun a bainar jama'a,kinga riba biyu kenan,"   Tana kai karshen maganarta,hayaam ta ɗaura da cewar"wannan haka yake Auntyna,mu ɗin jinin nasara ne,duk abunda muka sa agaba sai munga bayanshi koma uban menene shi,"   Dariyar mugunta Aunty babba ta kuma saki kafin tace"Bazan ƙyalesu haka nan ba,saboda Omar zai iya bin bayansu don ya taimakesu,dole in samu wanda zaibi takansu da mota su mutu kawai,kowa ya huta,"   Hayaam tace"faƙat!kinga babu su a duniyarma balle ayi dasu," .......duk wannan surutan da suke yi,Amani na la6e a ƙopar ɗakinsu wadda bata idasa rufewa ba,tana recording ɗin muryoyinsu a wayarta,don taci alwashin saita tarwatsa duk wani plan nasu,Ni boss nace kinyi mun dai dai, *Boss Bature* The genius   ❤🤍❤ bari mu leƙa falo muga meke wakana,shin ansamu cigaba ko kuwa ana nan yadda ake? Natsuwa su kayi gaba ɗayansu,wurin yayi tsit tamkar mutuwa ta gifta,kowa ya natsu ya nabba'a tamkar ɗalibai ne agaban ya sayyadi,bafa sayyadi mijin abu ba,ina nufin malami,kar ayimun wata fahimta, "Waɗannan sune ƴan ukun Abusufyan ɗin"modibbo ne yayi maganar yayin da idanunshi ke akan Su jahad dake zaune sunyi zuru zuru,'   Har suna haɗa baki wurin cewa"Sune," Jinjina kai yayi tare da mayar da idanunshi kan Ammi yace"Ki kace yaran shaggu ne ko?Wata hujja gare ki na cewar bada aure ya haifesu ba?   Fuskarta aɗaure tace"Ina da hujja,saboda nice mahaifiyarshi,kuma ni bansan an ɗaura mashi aure da kowa ba,"   Girgiza kai modibbo yayi,sannan yace"hannunki ya taso ne?ko kuwa wurin ki kaɗae za'a iya ɗaura mashi aure ne"?   Shiru tayi batace masa uffan ba,cigaba da magana yayi"don haka baki da wata hujja ta cewar abusufyan yayi aure ko baiyi aure ba,ya samu ƴa'ƴa,wlh Aisha kin ban mamaki!wai har yaushe ne zaki ajiye waɗannan makaman yaƙin naki ne?ke fa yanzu ba yarinya bace,kin tara ya'ya da jikoki amma har yau bazaki ajiye wannan zafin ran naki ba,sai yaushe ne ya'yanki da kuma jikokinki zasu ji daɗin zama dake ne?yanzu ni ba misali bane agareki?ko bakisan wanene modibbo ba?kinfi kowa sanina bani da wasa ko miskala zarratin,duk wani kangararre acikinku,keda ƴan uwanki nine nan nake tankwarashi,amma yanzu saboda na manyata,na tara ya'ya da jikoki,duk na ajiye waɗannan ɗabi'un,Na canza kaina ne ba don komai ba sai don saboda ya'yana da kuma jikokina suji daɗin zama dani,kuma suyi alfahari dani amatsayina na kakansu,bawai su dinga tsoro na ba,suna gudu na harma su dinga yi mun fatan mutuwa,kamar ke ɗin nan dai.....'yayi maganar yana nuna ta da sandar hannunshi,sunnar dakai Ammi tayi tana faman jinjina kai, Canza harshe modibbo yayi izuwa harshen fulatanci,yayi hakan ne saboda kada faɗan da zaiyi mata ya zama tamkar tozarci ne agaban jikokinta,   "Gaba ɗaya kin takurawa rayuwar ya'yanki,da ta jikokinki,kin hanasu sakat,ko irin wasan dake tsakanin kaka da jikan nan bakya yi masu,kullum burinki ki ƙuntata rayuwarsu,shin menene ribarki idan kinyi hakan? Ya ɗan dakata da maganar yana kallonta,kafin yaci gaba da cewa"Yanzu jibi yaran nan ƴan wurin fatima,hakanan kika ɗaura karan tsana kika ɗaura masu sai kace ba jininki ba!in ma saboda mahaifiyarsu ne,ke kin ta6a ganin inda laifin wani ke shafar wani ne?in kuwa haka ne ae da dukkanmu mun shiga uku,saboda wancan zaiyi sata ne a ɗaura maka laifin bayan bakai ne ka aikata ba,"   Katse shi tayi cikin harshen fulatanci tace"Amma yaya modibbo ni meyasa ya'yana basu jin maganata ne?basu ɗaukeni mahaifiyarsu ba,suna yin abu gamon kansu batare da sun sanar mun ba,Hossein ya ƙetare ƙasar nan yaje yayi aure batare da sani na ba,sai dai kawai na ganshi da mata ya dawomin,matar kuma ma farar fata ba jinsun mu ba,sannan kuma Abusufyan shima yayi aure batare da sani na ba,saboda me zasuyi mun haka ne? anzo dai dai wajen,acewar modibbo gyara zama yayi sannan yace"kin manta yadda akai kika auri salahuddeen ne?to idan kin manta bari na tuna maki,dama duk wanda ya bijire ma iyayensa ko ba daɗe ko ba jima sai shima yaga ba dai dai ba,na farko bada sa hannun iyayenmu ba,kika shiga aikin Soja,babu irin yadda ba'ayi dake ba don ana ganin bai dace dake ba,ba kaman daya kasance ke bafullatana ce,amma kika ƙeƙashe ƙasa kikace sai kinyi aikin soja,a ƙarshe da aka takura maki,shine kika tattara kayan ki kika dawo gidana da zama saboda kina tunanin cewar ni zan goya maki baya don ki samu abunda kikeso,da kika zo wurina a lokacin na nuna cewar nima bazansa hannu na ba acikin lamarin tunda har iyayenmu sun nuna basu so,a ƙarshe sai kika gudu batare da sanin kowa ba,kika shiga aikin Soja,sae dai kwatsam muka ganki da kakin Soja ajikinki,ko ba haka akayi ba"? Wata irin zufa ce ta shiga wankowa a fuskar Ammi sam bata ta6a tsammanin cewa wannan ƙaramin kuskuren data aikata na bijirema iyayensu,zai dinga bibiyar rayuwarta bane, "Akan wannan aikin sojan da kika shiga,babu wanda baiyi kuka dake ba,saboda kafiya,da taurin kai irin naki,ga jinkai dake gareki,iyayenmu basu isa su baki umarni kai tsaye kiyi abu ba,sai sun biyo ta wurina saboda shakkarki da suke ji,bayan wannan kuma,baki sanar ma kowa ba game da salahuddeen lokacin da kuka fara soyayya dashi ba,sai daga baya ne muka fahimci shi ya hure maki kunne har kika bijire mana kika shiga aikin sojan,hakan kuma yasa duk muka ki amincewa da farko ki aure shi,amman da yake Allah ya kaddaro aure tsakaninku ba yadda muka iya dole muka kyale ki ko don kafewar da kika yi da kuma rabon itama Ameena anan zata samu mijin, ko ba haka akayi ba"?   Jinjina kai Ammi tashiga yi yayin da idanunta suka cicciko tab da kwalla amma bata bari sun zuba ba, Gwaggon katsina kuwa,sae faman sakin murmushi takeyi,tana faɗin"kwarai kuwa,haka akayi,"Abban su junaid kuwa da hajiya azeema duk jikinsu yayi mugun sanyi,sae yanzu suka gane daga inda matsalar take,dama duk in mutun yaga rayuwarshi tana tafiya ba dai dai ba,kuma bai akaita wani zunubi,toWlh ya binciki kanshi!ya tuhumi kanshi ahankali zai gano dalili, Su jahad dae suna nan tsugunne sun kasa kunne suna sauraronsu,sai dai subi bakin modibbo da kallo,daga bisani in Ammi na magana subi ta da kallo saboda basu iya fulatanci ba,haka Marshal Omar dasu ishaq duk basa jin fulatanci,haka zalika Sgr baya jin harshen nasu,dama shi ko hausa daƙyar ya koye ta,kuma har yau in yana magana da harshen hausa sai ka gane cewar ɗan koyo ne don sam hausarsa bata nuna ba shiyasa bai fiye yin magana da hausa zalla ba saiya haɗa da turanci ko spanish,amma kuma hausar tashi ba ƙaramin daɗi takeyi ma mutane ba,   Murmushi Modibbo ya ɗan saki kafin yaci gaba da cewa"ina fata yanzu kin tuna komai"?   Siraran hawayen da take 6oyewa ne suka gangaro a saman fuskarta,muryarta ƙasa ƙasa tace"Na tuna,"   Modibbo yace"Tunda kin tuna bari na ƙara ɗaura ki akan hanya,irin abunda kika aikata ne yasa shima ɗan cikinki da kika haifa yaje yayi aure batare da saninki ba,saboda gudun kada ya fara sanar dake ki hana shi yin auren,hossein ya auri Alala..kunzandariya...."kasa ƙarasa maganar yayi saboda bai iya ambaton sunanta ba,abun yaso yaba Sgr dariya,amma ya basar da ita tare da gyara mashi sunan yace"Alexandra ne sunan," Modibbo yace"yawwa ɗan gari,bazan dai iya Ambaton sunan nata ba,a barshi a fatima,tunda ae ta ta6a musulunta,kuma muna sa ran zata ƙara musulunta insha Allah,"   Suka ɗanyi dariya,kafin ya ɗaura da cewar"Hossein ya auri fatima batare da saninki ba,saboda yasan halinki sarai kin tsani jinsin da ba naki ba,gudun kar ya sanar dake kiƙi amince masa yasa shi yin hakan,sannan......"modibbo bai ƙarasa maganar ba,ammi ta kuma katse mashi hanzarinshi da cewa"Yaya modibbo amma ae ni harsu biyu sukayi mun haka!bayan ni,ni kaɗai ce na bijire ma iyayenmu haka,"   wannan maganar ta Ammi yasa shi yin dariya,tare da girgiza kai yace"in kikayi wata maganar kina tunamin da ƙuruciyarki wlh,dama ita irin sakayyar nan tamkar ramuwar gayya haka take,kuma ita ramuwar gayya tafi ta gayyar zafi,sakamakon abunda kika shuka ne,yasa kika girbi kyakkyawan sakamakon da ya zarta nakin,kuma tunda har kika iya ƙyale hossein bayan laifin daya aikata maki na auren bare kuma farar fata ae yaci ace kin yafe ma Abusufyan tunda shi da ƙuruciyarshi ya auri yarinyar,kuma hada sa hannun gwaggonshi,kuma kinsan wacece ita a wurinki,da mahaifinmu da nata uwa daya uba daya,kuma saboda yardar da kikayi da itane yasa kika damƙa mata amanarshi,ita kuma ƙaunar da take yi maki ne ya shafi ɗanki da kika haifa,hakan yasa ba zataso wani abu ya cutar dashi ba,Yaro ya nuna yana son ƴar mai gadin gidansu,ke kuma kin tsani auren bare mara asali,gashi shi kuma yaron ya kwallafa rai akan yarinyar,don lokacin da ita Aminatu taso ta sanar dake game da yarinyar balbaleta kikayi da masifa,kina cewa karta kuskura ta bari alaƙarsu tayi nisa,ta raba tsakaninshi da yarinyar,a ranar saida Abusufyan ya suma jin za'a raba shi da abunda yakeso,wannan dalilin ne yasa hajiya ameenatu ta aura mashi yarinyar batare da ta sanarma kowa ba,sai ni ɗinnan da nake magana,"   ɗagowa Ammi tayi tana kallonshi cike da mamaki,   Jaddada mata maganar yayi"kwarai kuwa ta sanar dani,nasan da zancen auren,kuma aranar da aka ɗaura auren Abusufyan da zainabu abu,ina ɗaya daga cikin waɗanda suka halarci ɗaurin auren batare da sanin kowa ba,ita kanta hajiya ameenatu batasan na halarci ɗaurin auren nasu ba,a iya waya kawai ta sanar dani,sae kuma akaci sa'a ina da wani taron manyan malamai da zamu halarta anan jihar kano,wannan ne babban maƙasudin daya kaini garin harna shaida wannan ɗaurin auren....." Ae tunkan modibbo yakai ƙarshen maganar wani irin murmushin farin ciki ya bayyana akan fuskar kowannansu,saboda yayi maganar ne cikin harshen da zasuji,wata irin nauyayyiyar ajiyar zuciya abusufyan ya shiga saukewa,nan take yaji wani irin sanyi ya ratsa zuciyarshi,duk da yayi mamakin zuwan modibbo wurin ɗaurin auran nashi saboda bai ganshi ba,amma tunawa da irin dubban al'ummar dake a masallacin kuma ya kasance ranar juma'a ne ana kammala salla aka ɗaura auren nasu,tabbas bazai iya tantance kowa dake a wurin ba,amma ko a lokacin bayan an ɗaura auren sun koma gida sai da baba buzu ya kirashi gefe guda yake sanar dashi cewa"Wani babban malami,yayi mashi alheri bayan sun fito daga masallaci,kuma yana tunanin cewar Kamar jininsu ne saboda yaga kamannin Hajiya ameena a fuskarshi,a lokacin Abusufyan bai gane wanene ba,sai yau da modibbo yayi maganar nan kwatsam ya zancen ya faɗo mashi aranshi bayan ya shiga zurfin tunani,tabbas kuwa modibbo ne,   Murmushi modibbo yayi tare da kallon Abusufyan yace"nasan zakayi mamaki,saboda nazo ɗaurin auren ka batare da sanin kowa ba,uzuri ne ke gare ni a lokacin shiyasa ban nemeka ba,don nasan muddin ka ganni a lokacin saika nace akan in tsaya,"   ya ƙarasa maganar tare da mayar da idanunshi kan Ammi,tun kafin ya kuma cewa wani abu,muryarta tamkar zata fashe da kuka tace"Amma yaya kasan da maganar auren nashi shine ba'a sanar dani ba?saboda me?   "Saboda halinki"! Kai tsaye ya bata amsa,   "Tabbas naso in sanar dake ko alokacin,saboda kinsan cewa ni bana jin shakkarki,hajiya ameenace ta rokeni akan cewar karna sanar dake,saboda hakan zai iyasa ki fusata harma ki yanke ma Abusufyan hukunci mai tsanani,kuma a ƙarshe zumuncin dake tsakaninki da ita ya tarwatse,dana nace akan zan sanar dake har kuka saida tayi mun,wannan dalilin ne yasa ban sanar dake ba,kuma ana haka daga baya kwatsam naji labarin mutuwar auren Abusufyan ɗin,hada ƙarin haka yasa akabar zancen gaba ɗaya,ashe yarinya ta fita da cikinsa ta auri wani,to kinji dalilin dayasa mu kanmu bamu san da ya'yan nashi ba,har suka kai wannan girman a hannun mijin da ta aura daga baya,"   Dakatawa yayi da maganar,falon yayi shiru na wani lokaci,kafin ya mayar da idanunshi kan Sgr dake zaune,yace mashi"ka kunna mata audio din nan daka kunna mun itama ta saurare shi,"   "Okey,"ya amsa mashi tare da,daddana wayar hannunshi,ya shiga audio din tare da kunnashi,sannan ya miƙe tare da ƙarasawa kusa da kujerar da Ammi ke zaune ya miƙa mata wayar,yatsun hannunta na kerma tasa hannu ta kar6i wayar tashi,ta ajiye asaman hannun sofa ɗin tana sauraronshi,wannan audio din na labarin da abusufyan ya bayar ne da kuma Labarin dasu sehrish suka bayar na irin ukubar da suka sha a hannun ya sayyadi,ashe ranar da abun ya faru,Sgr ya ɗauki audio na maganganun da sukayi kaf acikin wayarshi,tabbas shi ba ƙaramin jami'in Soja bane!yana Aikinsa wani lokacin tamkar jami'in sirri,Na jinjina masa,da irin baiwar da Allah yayi mashi da kuma irin kwazon dake gare shi,ta ko ina Sgr ya haɗa,shiyasa nace maku shi ɗin komai nasa Extraodinary ne~~~ Miƙewa junaid yayi tare da ruƙo hannun Mommynsu yace"Shikenan mommy tunda mun kammala discussion din,ki taso muje falo pls,kada kice baki zuwa,in ba haka ba raina zai 6aci,wlh ko abincin dare bazanci ba,indai kika ƙi zuwa gaishe da modibbo," Cike da mamaki tace"Modibbo?kana nufin mahaifin maryam oummunsu Omar?   daga mata kai yayi alamar eh, Shiru tayi tana wani tunani,a iya saninta modibbo mutunne mai mutunci sosai,saboda shine ya taka ma Ammi burki a lokacin da taso Abba ya sake ta,tabbas bazata ta6a mantawa da halarcin da modibbo yayi mata ba, Ganin ta miƙe yasa junaid sakin murmushi yace"mommy zaki ko"? Jinjina mashi kai tayi alamar eh, Janyo hannunta yayi har suka ƙaraso falon,ganin hankalin mutanen dake acikin falon gaba daya yana akan Audio din da ammi ke saurare,hakan yasa itama ta samu wuri ta zauna,junaid ma ya zauna gefenta,yayin da idanunshi ke akan su sehrish,sam basu lura dashi ba saboda hankalinsu duk ya tashi,a sakamakon Audio din da aka kunna,saboda sun tsani jin labarin rayuwarsu,ko miskala zarratin,   Kowa ya natsu yana sauraron audio ɗin,lokacin da Abusufyan ya kammala bada tarihin rayuwarshi da abu,sai next audio ɗin ya shiga wanda Jahad ke bada labarin rayuwarsu,nan take hankalin AMMI yayi mugun tashi,jikinta har tsuma yakeyi,tuni wasu siraran hawaye suka shiga zarya a kuncinta,ita kanta Alexandra jikinta ba ƙaramin sanyi yayi ba,tunda take arayuwarta bata ta6a jin tausayin wani ɗan adam ba,daga ita har ammin kamar yadda sukaji tausayin waɗannan bayin Allahn ba,Very heart touching story,wanda duk wani mai imani In ya saurareshi dole ya zubda hawaye,in ma baiyi kuka ba,    Ganin yadda hawaye ke sintiri akan fuskar AMMI yasa Omar ya cire hanky daga aljihunsa ya miƙa mata,dama kamar yasan cikin buƙatarshi take,a fuskarta ta kifa hankacif ɗin,ta fashe da matsanancin kuka mai cin rai,kowa yayi mamakin yadda Ammi ke kuka,cikin shessheƙar tace"ku kashe mun audio din nan ya isa haka,kunnuwa na bazasu iya jurar jin wannan tashin hankalin ba,'   dama Audio ɗin yazo ƙarshe,junaid ne ya mike ya ɗauki wayar,tare da miƙa ma babban yayansu ita,ya kashe audio ɗin,   "Shiyasa akeso ko da yaushe mutun ya kasance mai sauƙin kai,kada ya cika tsaurara al'amurransa,yanzu da ace banzo ba,da shikenan,haka zaki kora yaran nan,ke baki tsaya kinyi bincike ba,kuma baki saurari bayani daga gurin kowannansu ba kawai kin tashi kin yanke hukunci,sai daga baya kuma kizo kina danasani"   daƙyar ammi ta iya furta"Astagfurullah Allah na tuba!ka yafe mun,rashin sani ne yasa na kirasu da shaggu,game da halin da yaran nan suka tsinci kansu,duk laifin mahaifinsu ne,shine silar komai,duk da daman Allah ya ƙaddara faruwar hakan babu wanda ya isa ya hana,amma Abusufyan bai kyauta ma rayuwarsu ba,meyasa bai sanar ma kowa ba don aɗauki mataki?saboda kawai yayi mashi barazana?Amma dai Allah ya tsine ma fasiƙin mutumin nan,Wlh bazan barsu ba,saboda me laifin kakansu zai shafe su?wannan wata irin mugunta ce mara kan gado,?bai tsaya a iya kan ya'yan salahudeen ba,hada jikokin duka yake ɗaukar fansa akansu,?kuma shima salahudeen ɗin daya kashe mahaifinsu ae don saboda mugayen laifukan da aka kamasu dashi ne,ɗaukar fansar ta mutun ukuce suke ɗauka,mahaifinsu da kuma mahaifiyarsu,da kuma wannan ɗan koran nasu,dukkansu Allah zai toni asirinsu,'   Jinjina kai modibbo yayi yana sauraronta saida takai ƙarshen maganarta,tukunna yace"ba komai ne yasa na tako nazo ƙasar nan ba,face don abu uku,kuma ina fata zaki bani haɗin kai domin asamu maslaha atsakaninku gaba daya,saboda baza a ta6a cin nasarar gano waɗannan masu ɗaukar fansar ba,har sai ku na cikin gidan kun fara haɗa kanku,in ba haka ba,munafukan dake shirya maku zagwan ƙasa zasu samu nasarar cin galaba akanku,ta hanyar rarraba kawunanku,saboda ni inaji araina cewar masu shirya wannan maƙarƙashiyar suna ATARE DAKU!sun shiga cikinku,suna acikin rayuwarku!' Wannan maganar ba ƙaramin jijjigasu tayi ba,don sai da kowannansu ya ɗago yana kallon fuskar modibbon, "Nasan zakuyi mamaki amma nan gaba sannu a hankali zaku shaida maganata,yanzu dae bari inyi abunda ya kawoni," "AISHA" Ya ambaci sunan Ammi,muryarta asanyaye ta amsa mashi da Na'am, "Banaso in ƙarajin wani ƙorafi akanki!wannan ne na farko kuma wannan ne na ƙarshe!idan har kinaso ki zauna lafiya,to ki gyara tsakaninki da ya'yanki!da kuma tsakaninki da Jikokinki,na uku kuma shine tsakaninki da surukarki fatima,"ya ƙarasa maganar yana nuna Alexandra da sandar hannunshi,ɗagowa ammi tayi tare da kai idonta kan Mommynsu junaid wadda itama kallon nata takeyi,kawar da kanta tayi gefe batare da tace komai ba, Cigaba da magana modibbo yayi,"Allah ma mukanyi masa laifi kuma ya yafe mana,balle mu ƴan adam,fatima bata yi maki laifin komai ba,tun farko koda kike mata magana take mayar maki saboda kin nemi cin zarafinta ne!wanda kuma ba kowa ne zai iya jurewa ba,balle ita da take jar fata,yanayin rayuwarsu ko ince tarbiyarsu ba irin tamu bace,don da a ƙasarsu ne kikayi mata haka zata kaiki ƙara kotu ne a yanke maki hukunci,babu ruwanta da Cewar ke surukarta ce,sannan kuma bai kamata ki nuna mata ƙiyayya ba,duk maison naka ae masoyinka ne!ɗanki fa takeso,kuma saboda son da take mashi tabar iyayenta da kowa nata tazo ƙasar nan,inda bata san kowa ba,ko tsoron acutar da ita batayi ba,bakowa ne ma zai iya wannan kasadar ba,don haka yakamata ki so fatima saboda masoyiyarki ce,ba maƙiyiyarki ba,idan don ta kasance farar fata ce,damu dasu shin ba Allah bane ya halicce mu ba?ya banbanta mu ne?ko wani yafi wani ne"? Ya ɗan jinkirta da maganar yana kallonta, Kafin ya ɗaura da cewar"Yakamata ki ajiye wannan gabar dake tsakaninki da ita,Yanzu fatima ta wuce suruka a wurinki,tamkar ƴ'a take a wurinki,tunda ta hayayyafa da ɗanki,yakamata kiyi alfahari da ita saboda itace ta haifa maki ɗaya daga cikin jikokinki wanda duniya take alfahari dasu,waɗanda suka ɗaukaka darajar mu a idon duniya,"   Nauyayyiyar ajiyar zuciya Ammi tasaki tare da gyaɗa kai tace"Insha Allah komai ya wuce,"   Murmushi Abba ya saki ranshi fari tass kamar an yi mashi albishir da gidan aljanna,   "Sannan kema Fatima inaso ki ajiye dukkan wasu makaman yaƙin ki,kibi surukarki tamkar mahaifiyarki,kiyi mata biyayya amatsayinta na wadda ta tsugunna ta haifi uban ya'yanki,"   Fuskarta ɗauke da murmushi tace"Nima a wurina komai ya wuce,dama saboda ƙiyayyar da take nunamin ni da ya'yana ne yasa nima nake ƙinta,amma daga yanzu insha Allah babu wanda zai ƙara jinkan mu,"   Tana kai ƙarshen maganar junaid yace"Gaskiya,wannan sulhun bai cika yadda akeson shi ba,Mommy da Ammi basu ta6a yin koda musabaha ba,yakamata yau su tashi su rungume junansu ta hakan ne zamu gane cewar sun shirya da junansu,"   Gaba ɗayansu suka saki murmushi,miƙewa Alexandra ta farayi kamin Ammi itama ta miƙe,suka ƙarasa tare da rungume juna,tafi su Abba suka shiga yi wanda hakan yaja hankalin sauran matasan gidan,har suka firfito cikin falon don suga me ke wakana,ae koda su kayi arba da Ammi da Alexandra rungume da juna,nan fa suka shiga sowa,abun ba ƙaramin farin ciki ya sanyasu ba,musamman su Fawan don sun jima suna jiran wannan ranar tazo,ashe da rabon zasu ganta da idanuwansu,   "Ki yafe mun duk abubuwan da nayi maki,kuma inaso ki sani ba don bana sonki bane yasa nayi maki hakan ba,kawai haline irin nawa,da kuma sharrin shaiɗan" Ammi ce tayi maganar ayayin da take raba jikinta daga na alexandra,fuskar kowanansu ɗauke da siraran hawaye,   Murmushi alex ta saki kafin tace"Allah ya yafe mana gaba ɗaya,inaji kamar nafi kowa farin cikin wannan ranar,"tayi maganar fuskarta ɗauke da dariya,suna cikin rahar nan sukaji ana ɗaukarsu hoto ket ket!!   Da sauri suka waiga don su ga wanene,ashe wai fawan ne ya ɗauko camera ɗinsu,yana ɗaukarsu hoto yana faɗin"yau a daily trust dole su buga wannan gagarumin labarin,zazzafan gaske,Ammin mu wato kakarmu a yau ta rungumi surukarta wadda ta kasance mahaifiyarmu bayan sun dade suna shan gwagwarmaya ,"   Dariya sosai su kayi,ganin ya sanyasu raha,yasa shi cewa"Abba mu shigo ciki a ƙarasa tattaunawar tare damu?   Fuskar Abbansu ɗauke da murmushi yace"why not,a yanzu an sasanta komai,an samu maslaha,zaku iya zuwa ku zauna,"   Jin haka yasa suka ƙaraso ciki,gaba ɗayansu ne hada su twins jabeer,khaleed irfan dasu kanal,wuri suka samu suka zazzauna a ƙasa,   Junaid yace"Yawwa Amminmu,yanzu saura Uncle ɗinmu bawan Allah,yayi missing ɗinki sosai yakamata shima ki rungumeshi,ko yaji sanyi aranshi,"ya karasa yana langa6ar da kai.    Juyawa Ammi tayi tare da kallon abusufyan wanda ke a zaune,idonshi na kallon ƙasa,   Gyaran murya ta ɗan yi mashi,ya ɗago da idonshi ya kalleta,cike da zolaya tace"So kake sai nace ka taso"?   Fashewa yayi da dariya,kafin ya miƙe da sauri ya faɗa jikinta,sosai ta rungume shi ajikinta,tana ɗan bubbuga hannunta a bayanshi tace"nayi kewarka sosai,ka sani kuka Abusufyan,fiye da tunaninka,hakanan ka tafi ka barni shekara da shekaru...."tana maganar hawaye na fita a idanunta,   ɗagowa yayi daga jikinta,idonshi na fitar da kwalla yace"Ki yafe mun Ammi,nasan ban kyauta maki ba,nayi maki abubuwa da dama wanda bakyaso,nasan cewa hada haƙƙinki ne ke bibiyar rayuwata shiyasa ma harya shafi ya'yana,...."     Hannu tasa tana share mashi hawayenshi tace"Na yafe maka abusufyan,dama ni burina shine ka dawo kusa dani,kuma Alhamdulillah,gashinan ka dawo cikin yan uwanka,naji daɗin hakan sosai,Allah ya ƙara haɗamun kanku,"   gaba ɗaya suka amsa da Ammin, "AMMI saura su rishi,su baki rungumesu ba,kalli fa kiga yadda duk suka shiga damuwa,bayin Allah," junaid ne ya sake yin maganar yana raku6e fuska,alamar tausayi    Kallonsu Ammi tayi,sun cunkushe wuri guda kamar kifin gwangwani,musamman Sehrish jikinta har lokacin sae kerma yake,a hankali Ammi ta taka izuwa inda suke,ta zuƙunna agabansu,sannan takai hannunta tare da shafa fuskokinsu,kafin tace"dole in nemi yafiyarku,saboda na jefebku da mummunan kalma,bisa rashin sani,ina mai matuƙar baku Haƙuri akan abunda ya faru a rayuwarku!ba laifinku bane laifin wasu ne akeso a ɗaura maku shiyasa aka biyo ta hanyarku duk don a ƙuntata mana,amma nayi maku alƙwarin cewa ɗaya daga cikin waɗanda sukayi sanadiyar wulaƙanta rayuwarku,Wlh bazai sha ba!daga rana irin ta yau zansa a fara bincike akansu har sai Allah ya tonu asirin kowannansu,kuma nayi maku alƙawarin cewa,zansa akawo maku wannan fasiƙin mutumin har inda kuke don ku wanke mun mummunar fuskarshi da tafukan hannayenku,"   Jin wannan maganar ta Ammi yasa Hosana fashewa da dariya,har white teeth ɗinta suka bayyana,dimples ɗin fuskarta suka lotsa,Jahad ma murmushi ne ya bayyana a fuskarta,sehrish ce kawai batayi murmushi ba,da alama kamar akwai wani abu dake damunta,duba da yanayin jikinta dake ta kerma,   Ruƙo hannayensu ammi tayi tare da miƙar dasu tsaye sannan ta haɗasu duka ta rungumesu sosai,ajikinta, Wani irin matashin murmushi ne ya bayyana a fuskar kowannansu dake a falon,haƙika sunji daɗin wannan ranar,tsakaninsu da Allah sai godiya daya bar Modibbo a raye har zuwa wannan lokacin,saboda shine silar komai daya faru ayanzu,da bai zo ba da akasin hakan ne zai faru,    Addu'oi' Ammi ta shiga karantowa tana tottofa masu akawunansu,a ƙarshe tace"Allah yayi maku ALBARKA,"suka amsa mata da Amin,   Komawa su kayi kowa ya zauna,itama ammin ta zauna,bayan kowa ya natsu Modibbo yace"ko akwai mai magana acikinku"?   Da sauri Abbansu junaid yace"Ina da magana," Modibbo yace"faɗi kai tsaye muna sauraronka,"    "Yawwa kawuna,dama akan maganar fatima ne da Abusufyan!har yanzu basu shiri a tsakaninsu,tun wani sa6ani da suka ta6a samu a lokacin baya,to har yanzu basa jituwa,yakamata aduba lamarin,' Sunnar dakai ƙasa Abusufyan yayi,kamar yadda itama alexandran tayi, "Ae yanzu ko banyi masu magana ba,zasu shirya kansu ne ko don zumuncin dake a tsakaninsu,da kuma ƴa'ƴayensu," Murmushi kowannansu,yayi abusufyan yace"Insha Allah komai ya wuce a wurina,dama can ni ban ta6a ruƙeta araina ba,nasan rashin kunyar da nakeyi mata ne a lokacin baya yasa take fushi dani har yanzu,amma ina neman afuwarta," Yana kai ƙarshen maganarshi,Alexandra tace"Nima komai ya wuce a wurina,Allah ya yafe mana baki ɗaya,kuma ya ƙara haɗa kawunanmu," Wani irin ihu junaid ya fasa,saboda tsabar farin ciki,hankalin kowa ya koma kanshi,ganin sun zuba mashi ido yasa shi sanya tafin hannunshi ya rufe fuskarshi,saboda kunyar data rufe shi,ƙasa ƙasa yake sakin dariya,bakomai ne yasa shi wannan farin cikin ba,face Shiryawar da Momnynsu tayi da Uncle ɗinsu,ko ba komai zai samu amincewarta wurin auren ɗaya daga cikinsu,💃 "Gobe da safe zan wuce damaturu,tunda naci nasarar haɗa kawunanku,ina fata zaku kasance a haka ko bayan tafiyata," atare suka amsa mashi da cewa"Insha Allah," "Amma mun jima bamu haɗu ba,bazaka ƙara kwanaki ba"? Ammi ce tayi maganar, murmushi modibbo yayi kafin yace"kada ki damu,tun da dai na shigo ƙasar zaku dinga ganina ne akai akai,insha Allah," Alhamdulillah,The end🥱🤣😂😅 nan bada jimawa ba,zan rubuta hakan insha Allah,nasan wasu har gabansu ya faɗi rass......... *SANARWA SANARWA*💃💃💃💃 *ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$* *MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.* *LOCATION KANO* 08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. [1/3, 6:34 AM] Abue Saleh AlQuyraemey: *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* Gaba ɗaya Aunty babba idonta bai hango mata su hosana ba,kutsa kai kawai takeyi cikin falon,hafsat dai tana la6e a bayanta,cike da fargaba, Ƙarasawa sukayi wurinsu,daga bayansu Sehrish suka tsaya,hakan yasa bata samu damar ganin fuskokinsu ba,sai faman washe baki take yi,gaishe dasu Abba suka farayi,fuskar kowannansu awashe,"Ishaq shine baka sanar dani zuwansu ba,"acewar Abba,General ishaq yace"Ni kaina bansan sun karaso ba,nadaisan munyi dasu kan cewa zasu taho," Abusufyan yace"masha Allah hafsat ta girma sosai,ba don ina ganin hoton ta ba,da bazan iya gane ta ba,   Sunnar da kai ƙasa hafsat tayi tana murmushi ƙasa ƙasa,yayin da zuciyarta ke a cunkushe,   duk su hosana basu ɗauki muryarta ba,amma da zarar tayi magana sai sunji tamkar sun ta6a jin muryar matar dake magana,     "Muna taya ka murna Abusufyan,ƴa'ƴa har ƴan uku Allah ya albarkaci rayuwarsu,Alla ya.........'bata ƙarasa maganar ba sakamakon juyowar da sehrish tayi,Gabanta ne yayi wani irin mugun bugu ji kake daram!!!dararam!!!yadda kasan ana buga ganga,Saboda tsabar kiɗima bata san lokacin da ta furta"Kutumar Uba...."gaba ɗaya hankalin kowa ya dawo kanta,jin ashar ɗin data buga,Hakan yasa Jahad da Hosana juyowa atare,Waro ido waje tayi hankalinta a matuƙar tashe,lokaci guda duk tabi ta gigice ta ruɗe ta rikice ta fita hayyacinta abunda batayi tsammani ba,la66anta har kerma sukeyi wurin nuna su da hannu tana ƙoƙarin tayi magana amma kermar da bakinta keyi ya hanata cewa komai,   Hankalin jahad ba ƙaramin tashi yayi ba,ganin matar da ta azabtar da rayuwarsu,ta ƙuntata masu ta kusa halakasu,hosana kuwa a matuƙar tsorace ta faɗa bayan Marshal Omar ta ƙanƙame shi tana faɗin"Ya Omar,bansan ganinta,tsoranta nake ji,itace matar da ta azabtar da rayuwarmu,itace tasa aje a jefar damu cikin daji,har wannan tsohon mutumin ya kusa cutar dani,don Allah ya Omar ku kureta,azzaluma ce macuciya ce,bata tsoran Allah,bata da tausayi kuma bata da Imani, Hankalin kowa dake a wurin ya dawo kansu,gaba daya Abba dasu Abusufyan da sauran mutanen dake a wurin duk sun ruɗe sun gaza gane inda zancen nata ya dosa,Ishaq kuwa tun da yaga jikin Aunty babba na kerma,zufa na keto mata,ranshi ya bashi cewar tabbas ta aikata wani abu ne,saboda yasan halinta,muguwace kuma bata da gaskiya,Bashi ba hatta Marshal jikinshi yayi mugun sanyi,musamman da yaji hosana na fadin ta cutar da rayuwarsu nan ya fara tunanin Wasu abubuwa da yake zargi a lokacin baya,da kuma maganar da major ya ta6a sanar dashi na cewar baya son ya shiga tsakaninshi da matar Yayan shi, hannu Aunty babba ta aza akanta tana faɗin"Shikenan An yanka ta tashi,amaimakon ta mutu,nashiga ukku ni laila,Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un wani tsautsayi ne da ƙaddara suka kawo ni gidan nan,' Tunda Abbansu junaid yaji hakan yasan cewa tabbas akwai wani abu daya ta6a faruwa a tsakaninsu,koma dae menene bai kamata,su tuhumeta ba agaban ƙannen mijinta,a bainar jama'a kuma,ko ba komai Matar babban yayansu ce,   "Ya Omar dan Allah,tabar wurin nan wlh bansan ganinta,kashe mu take son yi,shiyasa ta biyo mu har nan,"gaba ɗaya kukan hosana ya cika kunnuwansu,'   Wani irin wahalallan yawu Aunty babba tazo haɗiyewa,nan take ta yanke jiki a wurin ta faɗi asume,da sauri hafsat ta tsugunna tare da tallabo ta,tana jijjjigata, Gaba ɗaya duk sun kashe ma ishaq baki yama rasa abun cewa,tsananin baƙin ciki da takaici ya hanashi cewa uffan,jikinshi sae faman tsuma yake yi,burinshi kawai yaji abunda suka aikata ma yaran,da har suka tsorata da ganinsu,tabbas sai sunci Ubansu,muddin yaji wani da ba dai dai ba,don bazai yarda suja mashi tozarta ba a idon ƴan uwanshi, Aunty Azmee ce ta taimaka wurin ɗebo ruwa suka yayyafa ma Aunty babba a fuskarta,ae tana farfaɗowa kamar wata zautacciya tayi zumbur ta miƙe,ko waiwayonsu ba tayi ba,ta watsa aguje,tayi cikin gidan,Allah kaɗae yasan inda ta kutsa kanta, A fusace General ishaq zai bi bayanta,Abbansu junaid yayi saurin ruƙo hannunshi tare da cewa"kada ka bita,yakamata mubi komai a sannu,yanzu bamu kaɗai bane a wurin nan ba,akwai ƙannenka kuma akwai bare a wurin nan,"   Jinjina kanshi kawai yayi ba don ya haƙuri ba,   Batare da sanin kowa ba,hafsat ta zame jiki daga wurin,saboda wani irin mugun kallo da taga Daddynta nayi mata,bashi kaɗae ba hatta Marshal kallon tuhuma yake yi mata,hakan ne yasata ta sulale tabar wurin,sauƙinta ma basu ambaci sunanta ba,amma tasan dole sunanta ya fito aciki,kuma daddynta in ya tashi yanke hukunci hada ita zai haɗa ya yanke mawa,tabbas tayi dana sanin biye ma mahaifiyarta wurin cutar dasu hosana,gayanan sunja ma kansu,   Ruƙo hannun hosana yayi tare da janyota,ta dawo ta gabanshi,fuskarnan tayi jawur,sae faman kuka takeyi tana faɗin"ya Omar a koreta tabar gidan nan,bana son ganinta,bata da Imani,itace ta rufe mu acikin store tayi mana horon yunwa,ta dinga bugunmu da bulala,kuma ta dinga samu aiki,har gadon asibiti sai da aka kwantar dani.......' Cikin sauri Omar ya sanya tafin hannunshi ya toshe mata baki,cikin lallashi yace"its ok hosana,na fahimce ki,zansa sojoji su koreta daga gidan nan hakan yayi maki,"   ɗaga mashi kai tayi alamar eh,sannan yace"kada na sake jin kukan ki to,ya isa haka,kalli fa ki gani duk kin 6ata kwalliyarki da hawaye,"   Curo handkerchief Abusufyan yayi daga gaban aljihunsa,ya ruƙo hosana,tare da sanyashi a fuskarta yana goge mata hawayenta,"Daddy matar can bata da Imani ko kaɗan,taso ta kashe ni,dan Allah ku sakar mata karnuka su rakata bakin gate,tabar gidan nan,"   Muryar abusufyan tamkar zaiyi kuka yace"Kiyi haƙuri kinji hosanata,zansa a koreta kamar yadda kikeso,amma yanzu kiyi shiru da bakinki,ki daina magana,banason ganin hawayenki,"   "Daddy bakasan yadda nakeji bane,zuciyata tafarfasa takeyi,raɗaɗi takeyi mun kamar ana rura garwashin wuta acikinta,wlh daddy waccen matar bazata ga Manzon Allah ba,sai ta shiga wuta,' Hankali atashe Marshal ya daka mata tsawa har saida ta dawo cikin hayyacinta,fuskarshi a daure yace"kar na sake jin kince uffan a wurin nan,surutun ya isa haka!banace za'a kore ta ba,"   Saboda tsoratar da tayi da tsawar da yayi mata ne yasa ta faɗa jikin daddyn nasu ta ƙankameshi,tana faman sauke ajiyar zuciya,'   jikin kowa yayi sanyi,musamman Ishaq,bawan Allah duk yabi ya takure kansa,idanunshi sunyi jawur saboda tsabar 6acin rai,    Abba ne yayi ƙoƙari wurin dawo dasu daidai daga yanayin da suka shiga,daƙyar aka samu hosana ta zauna itama amma duk da haka tana yawan firgita wannan ya ƙara tabbatar masu da cewa ba ƙaramin Abu Aunty laila ta aikata masu ba,wuri kowa ya samu ya zauna agaban table ɗin dake a wurin wanda ke shaqe da abinci kala kala,nan fa kowa ya shiga bama cikinsa abinci,jikin Sehrish ba ƙaramin sanyi yayi ba,saboda ta gane dalilin dayasa su jahad suka tsorata da ganin matar,wato itace matar da Omar ya kaisu gidanta,wadda ta azabtar da rayuwarsu,kamar yadda jahad ta bata labarinta,kowa ya lura da yanayin yaran,sun kasa sakewa suci abinci sosai,ƙarshe sai dae Abusufyan ya dinga binsu one by one yana sanya masu abinci abakinsu suna ci,a haka har ya samu suka ci sosai,bayan sun kammala cin abincin,Junaid ya ɗaukko Camera ɗinsa,nan fa aka shiga ɗaukar hotuna,abun gwanin burgewa,Happy family,kowa sai da ya fito Hajiya azeema,su gwaggon katsina Saude,Dr harris,hatta ƴan matan da hajiya sarah tazo dasu,sae da suka fito akayi masu hotuna,mutun uku ne kawai babu a wurin Ammi wadda kowa ke fargabar fitowarta,bayan ita sae Haroon wanda ke ƙumshe acikin ɗakinsa,Sgr kuwa baya cikin gidan,tun wuraren ƙarfe uku yabar gidan,   Anyi masu hoto tare da mahaifinsu sun sanyashi atsakiya,sae wanda akayi masu tare da Abbansu junaid tare dashi kanshi junaid ɗin,kowa saida yayi hoto tare dasu,hatta Su twins da fawan dasu irfan,kowannansu sae da yayi hoto dasu,sun sha hotuna ba ƙadan ba, Basu suka kammala ba sae wuraren sallar magrib,sannan kowa ya shige ciki domin yin alwala, Kamar jira jahad takeyi su shiga ɗaki ta rufe hosana da faɗa,tamkar zata bugeta,"Sai yanzu na tabbatar da cewar ke cikakkar zararriyace baki da hankali,meyasa ba zakiyi shiru da bakin ki ba?don me zaki tona mata asiri agaban mutane"? Fashewa da kuka hosana tayi tana faɗin"kada ki ƙara cemun zararriya,kuma naje na tona mata asirin,Ni bazan ta6a yafe mata ba wlh,kamar yadda ta cutar da rayuwarmu itama sai ta fuskanci sakamakon abunda ta aikata mana,' "Hosana,karna sake jin kin tada wannan maganar,idan ba so kike ranki ya 6aci ba,"   "Wlh saina faɗima Daddy da Abba,kuma saina faɗa ma yaya Omar,sai dai duk abunda zai faru ya faru,'   rai a6ace tayi maganar,cakumar rigarta jahad tayi,tare da yin wurgi da ita,ta faɗa saman gadon tana kuka,fitowa Sehrish tayi daga cikin toilet,ganin jahad na ƙoƙarin bugun hosana yasa tayi saurin zuwa tare da ruƙo hannunta"karki kuskura kice zaki hukunta hosana!abunda tayi dai dai ne,koda ace ita bata faɗa masu ba,to ni saina faɗa masu abunda waccan matar ta aikata maku,saboda bata da Imani,muguwace ita,muddin akace za'a cigaba da yafe ma mutane irinta to tabbas bazasu ta6a canza halinsu ba!Suna buƙatar a ladabtar dasu,a hukuntasu,idan suka aikata ba dai dai ba,Ni hakan da hosana tayi ta burgeni,!"   Shiru jahad tayi,ta wani 6angaren zancen sehrish gaskiya ne,muddin ba'a ɗauki mataki ba akanta taga an ƙyaleta to tabbas bazata ta6a canzawa ba,amma yanzu idan suka hukunta ta dole nan gaba taji shakkar ƙara yin irin kuskuren da tayi abaya,   "Kin faɗi gaskiya sehrish,ni banyi tunanin hakan ba,kuma koda nake yi ma hosana faɗa,saboda 6arin zancen da tayi ne agaban mutane,bai kamata ta yi magana akan idon kowa ba,in ma faɗin ne Ya Omar yakamata ta sanar mawa,sae su yanke mata hukuncin da suka ga ya dace da ita," Ta ƙarasa maganar tare da ɗauke idonta daga kan sehrish ta mayar dasu kan hosana dake baje saman gadon tana kuka,nan take taji bata kyauta mata ba,hawa saman gadon tayi tare da janyota jikinta,tana lallashinta,daƙyar ta samu tayi shiru,daga bisani suka tashi domin yin sallar magrib, *Aunty Babba* Tunda ta watsa a gujen nan,ɗakin hayaam ta faɗa,jikinta sae faman rawa yakeyi,zagaye tashiga yi a ɗakin tana tunanin hanyar da zata bi ta gudu daga cikin gidan tun kafin ishaq ya waiwayeta,tsoranta karya bata takardar saki,don bata shirya yin zawarci ba,hannu ta aza aka tana fadin"Nashiga uku ni laila,na jama kaina masifa da bala'e,Ina zan tsoma raina inji daɗi,"tana cikin zancen zucin nan,hafsat ta shigo ɗakin,kamar jira takeyi nan ta shiga balbaleta da faɗa ta inda take shiga bata nan take fita ba, "Don ubanki ki faɗa mun taya akai yaran nan suka rayu!nasan kinsan komai munafuka algunguma!"hafsat na ƙokarin buɗe baki,Aunty babba takai mata naushi a kumatunta,har sai da le6enta ya ɗan fashe,idonta jawur ta ɗago tare da kallon Mommyn nata idanunta cike taf da hawaye tace"Mommy!ni kika buga saboda zunubin da bani na aikata ba? A faɗace Aunty babba tace"Zanci ubanki ko ki rufe mun baki,wlh hafsat kin cuce ni!Allah ya isa tsakanina dake!ae kinsan da zaman yaran nan acikin gidan nan, shiyasa don munafunci kika sanyo nikabi uban meyasa baki sanar dani ba tuntuni don inyi takaina!Kece kika tseratar dasu daga hannun baba alamu,in ba haka ba taya akai har suka kawo kansu cikin gidan nan"!? Girgiza kai hafsat ta shiga yi yayin da idanunta ke fitar da wasu irin hawaye masu ɗumi,cikin shessheƙar kuka tace"banta6a dana sanin kasancewarki mahaifiyata ba sai yau!Kin jefani acikin masifa kin kuma zo kina neman ƙala mun sharrin cewa ni na tseratar dasu daga hannunshi,wlh Mommy bakiyi ba!duk wasu magayen ɗabi'u da halayen dana ɗauko naki ne,baki ta6a cemun nayi badai dai ba,baki bani tarbiya mai kyau ba,kullum gur6atamun tunani na kikeyi,saboda kar in dauko halayyar mahaifina,Ni banta6a ganin uwa irinki ba,Yanzu gashi nan daga ni harke wa gari ya waya?kuma inaso ki sani mommy,Ni bansan komai agame dasu hosana ba,bansan ya akai suka dawo hannun Ya Omar ba,Na faɗa maki hakan ne ba don ina jin tsoranki ba,sai don kisan cewar Bani na aikata hakan ba,Allah ne Ya Kamaki,ba yadda banyi ba don ki kyale yaran nan karki salwantar da rayuwarsu kika ki,kuma ni ce da hannuna na goge hotunan da hayaam ta tura maki a wayarki,saboda nafi son ki tako da ƙafafunki don ki gir6i abunda kika shuka......" ..saboda tsabar tsuma jikinta har kerma yakeyi,shaƙo wuyan rigar hafsat tayi da ƙarfin gaske,gadan gadan kasheta zatayi,kiciniyar kwace wa hafsat tashiga yi,suna cikin wannan halin,Amani da hayaam suka faɗo cikin ɗakin da gudun gaske sukayi kansu,daƙyar suka kwaci hafsat daga hannun Aunty babba,dafe maƙoshinta tayi tana faman yarfa hannu tana ambaton"ruwa!ruwa' Da sauri hayaam ta fita waje,sai gata ta dawo da bottle water a hannunta mai sanyi,miƙa ma Hafsat ruwan tayi,jiki na rawa ta cire marfin robar tare da yin wurgi dashi,ta kafa robar abakinta tana kwankwaɗar ruwan,hayaam ce ta zauna a wurinta,tana lallashinta, Rai amatuƙar 6ace tashiga fadin"ae da kun barni na kasheta don ubanta,wlh hafsat baƙin cikinki bazai ta6a kashe ni ba,Muguwa kawai,nafi kowa dana sanin haihuwarki,Ni ina kokwanton cewar Anya ba'a asibiti akayimun musanyarki ba," Fashewa da dariya Amani tayi tana tafa hannayenta, Nan take Aunty babba ta ɗaure fuska,tana jifarta da harara, Tsagaitawa tayi daga yin dariyar da takeyi masu sannan tace"Wannan abun daya faru nafi kowa farin cikinsa,tamkar na zuba ruwa a ƙasa na sha," "Amani baki da hankaline?kinsan me kike faɗi kuwa?wannan abun fa ya shafi kowannanmu,bai kamata ki dinga yi mana dariya ba,"Acewar Aunty babba, wurga mata harara amani tayi tare da cewa"yadai shafe ku!karki kuskura ki ƙara mentioning ɗina aciki,domin kuwa bansan anyi ba,lokacin da kuka tsara muguntarku kuka cutar dasu,kunyi shawara dani ne?Kuma ae har shawara saida na baki akan ki daina azabtar da yaran amma kika ƙi ji ke ga shugabar azzalumai,wlh baku da imani zuciyarku ta bushe,kwakwalwarku a toshe take,tamkar ana zuba maku dussa acikin kawunanku saboda ɗabi'unku sak irin na kafuran farko ne,....." Waro ido waje Aunty babba tayi tare da faɗin"Ni kike faɗama wannan maganar!" Amani tace"Kwarai kuwa dake nake,Muguwa macuciya kuma Azzaluma,zuciyarku ta ƙeƙashe Zalunci kawai kuka sa agaba,daku da uwarku Mammy,tsohuwar banza me shegen son kuɗin tsiya,wlh kunji haushin rayuwarku,shegen kwaɗayin abun duniya,ga baƙar zuciya,ga dogon burin tsiya ko tsoran mutuwa bakwayi..." Tunkan amani ta ƙarasa maganar Aunty babba ta kwashe ta da tagwayen maruka,ji kake tasss tatasss!'kafin Aunty babba ta janye hannunta daga kan kuncin Amani,itama ta daddage da iya ƙarfinta na ƙarshe ta kikkifa mata maruka a jere kusan uku ji kake fass tasss taaasss! dafe kumatu aunty babba tayi yayin da idanunta sukayi jawur,tunda take arayuwarta ba'a ta6a yi mata irin marin da Amani tayi mata ba,hasalima Amani shakkarta take ji,amma sai gashi yau ta cire yatsunta guda biyar cuf,ta kikkifa mata maruka, Koda ganin haka,sae hayaam ta miƙe tare da ɗaga hannu zata sharara ma Amani mari,aikuwa hafsat ta yunkura tare da miƙewa ta damƙo hannun hayaam tana faɗin"baki da hankaline?matar da ta iya ɗaga hannu ta mari mommy har sau uku,itace zaki mara?kina tunanin cewa zaki iya rama mata ne," dariya Amani tayi tare da cewa"ki barta inga ƙarshen rashin kunya,wlh dai dai nake da kowane shege acikin ku,Bana jin tsoranku a yanzu,tun ranar da Amal ta sanar dani komai game da ukubar da kukeyi mata tun daga ranar na ɗaura ɗamarar yin yaƙi daku," Hankali tashe hayaam da aunty babba suka kalli juna jin ta ambaci sunan Amal, Hafsat ce tace"Amal na wurinki ne"!? Jinjina kai amani tayi tare da cewa"Amal tana wurina!itace yarinyar dana zo da ita cikin gidan nan,kun so ku kashe mun ƙanwata,Amma Allah bai baku nasara akanta ba,Amal ta tako da ƙafafunta ta kawo kanta har cikin garin nan," Shiru duk sukayi suna sauraronta, "Haƙƙin Amal kaɗai ya isa ya jefa rayuwarku cikin masifa,laifin me Amal tayi maku da har kuka wulaƙantar da rayuwarta?yarinya ƴar ƙanƙanuwa amma kukayi mata taron dangi wurin azabtar da ita,saboda tsabar mugunta irin taku,ƙiri ƙiri kuka hanani ganin Amal,ku ka yi mun ƙaryar cewar Amal ta 6ace ba'a ganta ba,mugaye kawai ashe gidan makwabtanmu kuke kaita kuna rufeta,duk in nazo har in bar garin,tana can arufe kamar akuya,ko abinci ma baku bata,wai ku wasu irin mutanene?wace irin zuciya gare ku...? Kasa ƙarasa maganar Amani tayi saboda kukan daya ciyota,nan take ta fashe da wani irin matsanancin kuka,ba ita kaɗae bama hatta hafsat sai da ta zubar mata da kwalla,baƙin ciki kamar ta binne kanta,abun kunyar da mommynta ta aikata ba ƙaramin illa yayi ma zuciyarta ba, Hayaam kuwa sae faman mazurai takeyi ita da aunty babba sunyi wuƙi wuƙi,basu da abun cewa,dama ance rana dubu ta 6arawo,rana ɗaya ta me kaya, "Wlh kaɗan kuka fara gani!haƙƙin Amal da kuma haƙƙin waɗannan bayin Allahn da kuka cutar bazai ta6a barinku ku zauna lafiya ba,in har ba zaku canza waɗannan munanan ɗabi'un naku ba,mugunta da kwaɗayin abun duniya,dogon buri,rayuwar ƙarya,duk ku kadae gashi har yau Allah bai ta6a baku nasara ba,mutumin da bai ta6a sa Allah alamurransa ba taya zaiga dai dai"? Tsoki Aunty babba ta buga tare da nuna mata hanyar fita daga ɗakin tace"zo ki fuce ki bamu wuri tun kafin ranki ya 6aci a wurin nan!shashasha kawai kina tunanin cewa kalamanki zasu iya tankwarani ne?duk duniya ba ayi mutumin da zai zauna yanayi mun nasiha ba,wlh ba ayi shi ba," Girgiza kai amani tayi tare da juyawa a fusace tabar ɗakin tana faɗin"Jiki magayi," Komawa Aunty babba tayi yaraf ta zauna gefen gadon tana faman cizon yatsa,miƙewa hafsat tayi tare da fucewa daga ɗakin, Fitar ta keda wuya,Hayaam ta dawo gefen aunty babba ta zauna tana faɗin"Yanzu menene mafita"? ..fuskarta a hargitse tace"mafita ta wuce mu gudu salin alin batare da sanin kowa ba," "Saboda me zamu gudu?hakan na nufin cewa sun ci nasara akanmu kenan"? "Hayaam ba zaki gane ba,ina tsoran in sake yin arba da hosana ne,bata da hankali,zata ci gaba da tona mun asirine a bainar jama'a" "Amma Aunty laila,taya akai yaran suka zauna a wurinki har hakan ya faru?meyasa baki kashesu ba tun lokacin"? Guntun tsoki taja tare da kawar da kanta gefe cike da takaici tace"sai yanzu nake danasanin barinsu araye,meyasa ban kashesu ba tun lokacin da suke a wurina ba?wancan shashashan mutumin dana bama aikin zubar mun dasu a daji bansan ya akai yayi sakacin da har suka ku6uta daga hannunshi ba,kuma tun ranar dana bashi su nake ta jaraba kiran wayarshi akashe kullum har na gaji na daina kira,duk shi ya kwafsamin wlh,yanzu yawo acikin gidan nan ma ya haramta agareni,Allah yaso Hafsat ta siya niqabi a kasuwa,zan kar6e shine in sanya a fuskata saboda gudun kar waccen mai ta6in hankalin cikin sun ta ganni.....' Shiru suka ɗanyi na wani lokaci,zurfin tunani ta shiga yi kwatsam ta tuna da maganar nan da hajjaju ta ta6a sanar da ita kwanakin baya can da suka wuce lokacin su hosana na a gidan, "Idan kin toshe waɗannan hanyoyin,ita kuma waccen ɗayar hanyar da ta riga isa inda baki so fa ya zakiyi da ita' Jinjina kai Aunty babba tayi tare da faɗin"Allah ya isa tsakanina da hajjaju,sarai tasan komai game da rayuwar yaran nan amma taƙi sanar dani,babu yadda banyi da ita ba,amma taƙiya saboda tsabar baƙin hali irin nata,da tun farko ta sanar dani cewa ƴan ukune yaran akwai ɗaya dake aiki a gidan da tuni nasan abunyi, wannan masifar har ina"? "Amma kina ganin Ammi zata barsu ne acikin gidan nan?Jiya munyi plan ɗin cewa zaki kirata a waya ki sanar da ita cewa yaran shaggu ne,kin sanar da ita hakan," ta ƙarasa maganar tana kallon fuskar aunty babba wadda ke a hargitse,jin maganar hayaam yasa ta ɗan jinkirta,kamar me nazarin wani abu can ta ɗan washe baki tare da cewa"Hakane!Wannan ita kaɗae ce hanyar da ta rage mun,jiya na kira ammi a waya kuma na sanar da ita cewar Abusufyan ne ya ta6a yi ma wata fyaɗe harta samu ciki ta haifesu,ina da tabbacin cewar AMMI bazata barsu su zauna ba,dole ta koresu ƴan jakar uban,wlh na tsani yaran can,na tsani mahaifinsu duk shine silar komai,ya tashi yayi aure batare da sanin kowa ba,gayanan ya jefa mu acikin masifa,ni duk bama wannan ba,taya akai AMAL ta gudo daga gida tazo Abuja wurin waccen baƙar munafukar?ta ya akai Mammy da Abrah su kayi gangancin da har AMAL ta gudu daga gida ta dawo wurin Amani? Hayaam tace"Nima abunda nake tunani kenan,don ko aranar da zan bar gidan Amal na ƙunƙume aɗakinmu,zazza6i ya rufeta,Ni babban baƙin cikina ma,muna nan sake da baki,Amal na iya zuwa ta aure wani daga cikin matasan gidan,kinga ae shikenan mukuma tamu ta ƙare,maƙiyanmu za suyi ta cin nasara akan mu,'   "Insha Allah hakan ma bazata faru ba,in har ɗaya daga cikinku ke da abra bai auri ɗaya daga cikin matasan gidan ba,to sai dai ayi Ragas,Uban kowa ya rasa,itama Amal ɗin tarasa,ita kuma waccen ƴar iskar sai nayi silar mutuwan aurenta,tunda har ta iya ɗaga hannu ta kikkifamun mari,wlh saita gane kuranta,kuma wlh billahil azeemu,muddin Ishaq ya sake ni,itama sai Abbas ya sake ta,inyaso sai muyi zawarcin atare,"ta ƙarasa maganar tana faman sakin huci,tayi danasanin zuwanta gidannan!    *Boss Bature*       ❤🤍❤ turo ƙofar ɗakin da ammi ta sauka akayi,Azmee ce ta shigo hannunta ɗauke da kakkauran tea ɗin data haɗa mata,a zaune ta same ta saman darduma jikinta sanye da hijabi,yayin da hannunta ke ruƙe da cazbaha,da alama sallah ta kammala yi,   Cike da girmamawa azmee ta ƙarasa tare da zuƙunnawa ta gaishe ta,"Ina yini Ammi,ya gajiyar tafiya,"   da buɗar bakinta sae cewa tayi"Ina Abusufyan yake"? Azmee tace"sun fita sallar magrib,amma nasan yanzu suna kan hanyar dawowa gida,nan bada jimawa ba nasan zasu shigo ciki,"   Jinjina kai tayi tare da kai hannu ta ɗauki cup ɗin da azmee ta miƙa mata,abaki takai cup din ta kur6e sa kusan sau uku sannan tace"Idan sun dawo,kice su jira ni a palour gaba ɗayansu,inason ganinsu,"   Tuni Azmee tasha jinin jikinta,aranta tace"tashin hankali,'a fili kuma tayi saurin cewa"Za'a sanar masu,"sannan ta mike ta kama hanyar fita daga ɗakin,har azmee ta ruƙe handle din ƙopar zata fita,muryar Ammi ta katse mata hanzarinta da cewa"Next time idan zaki haɗamun tea,bana son sugar yayi yawa,sannan madarar tafi bornvitan yawa,da fatan za'a kiyaye,' "insha Allah za'a kiyaye,ko akwai wani abu da kike buƙata"?   "Idan ina buƙata zan sanar dake ne,basai kin tambaye ni ba,zaki iya tafiya,"   jinjina kai azmee tayi kafin ta buɗe kopar ɗakin ta fuce,babban falo ta nufa tana tafiya tana jinjina wa izza irin ta Ammi,saboda tsabar masifa,ko bornvita azmee bata zuba a tea din ba,madara kawai ta sanya mata amma saboda hali irin na ammi,da ba'a iya yi mata gwaninta,ta buga warning akan madara tafi bornvita yawa,ko ta ina taga bornvitan"?akan tea ma tayi ƙorafin anyi ba dai dai ba,inaga In taji abunda Abusufyan ya aikata batare da saninta ba,tabbas akwai matsala,rayuwarsu sehrish tana cikin garari,don wannan guyababbiyar matar bazata barsu su zauna lafiya ba,acikin gidan nan, Jin sautin muryoyinsu,yasa Azmee dawowa daga zurfin tunanin da ta shiga,dawowarsu kenan daga masallaci kowa bakin shi ɗauke da sallama suka shigo cikin Main palour din,Abba ne tare da Abusufyan sae junaid atare,bayansu kuma su Abbas ne da ishaq,Mg Osman da kuma Captain Adam,sai kanal yousouf da kuma Marshal wanda ke tare da Dr harris,a bayansu kuma akwai Fawan,twins,jabeer,irfan,khaleed dukansu dai suka shigo ciki,   ƙarasawa Azmee tayi wurinsu tanayi masu sannu da dawowa,daga bisani ta isar masu da saƙon ammi,nan fa kowa ya shiga fargabar dalilin tarasu da Ammi tace ayi,musamman Abusufyan yafi kowa shiga damuwa,tsayawa su kayi a tsaye kowa yana ta zullumin fitowarta,Abba dae sai ƙarfafa ma abusufyan gwiwa yake,akan ya jure,kada tsoro ya hanashi yi ma Ammi bayanin komai yadda zata fahimta, Jin takun takalminta kwas kwas!yasa su yin saurin kai idanunsu akanta,fuskarta na manne da farin glass,kwata kwata babu annuri a fuskarta,yayin da hannunta ke ruƙe da sandar nan ta alfarma,Ƙarasowa tayi tare da samun wuri ta zauna saman 3 seater,sannan ta aza ƙafarta ɗaya bisa ɗaya,tare da kallonsu tace"Ku zauna,"   A ƙasa su fawan suka zauna,yayin da Abbansu junaid,da abusufyan suka zauna asaman ɗayar 3 seater ɗin,ishaq da abbas suka zauna asaman 2 seater,Dr harris da Omar suka zauna a ɗayar 2 seater,dama 2 set ne na sofa a babban falon,manyan ne suka zauna saman kujerun,yayin da ƙananan daga kan Kanal yousouf suka zauna aƙasa, Tsit falon yayi na wani lokaci,kai kace mutuwa ce ta gifta,ko motsin mutun bakaji a wurin,kowa ya kame kanshi,   ɗaya bayan ɗaya Ammi ta dinga binsu da kallo,kowa sae faman noƙe kai yake,shi dai abusufyan ya gaza sakewa,don ko idonshi bai ɗago ya kalle taba,   ɗaga sandar hannunta tayi tare da nuna Ayan tace"wannan dogon gashin fa?sai kace wani ɗan daudu meyasa baka aske shi ba? cikin sauri Ayan yace"ƙuraje ne ke fitomun akaina duk in nayi yunƙurin aske gashin"   Ta6e la66anta tayi,kafin ta janye idonta daga kan Ayaan ta mayar dasu kan fawan,sunnar da kai ƙasa yayi yana ƴan kame kame,   "Ƴa'ƴan fatima kenan,ba zaku ta6a canzawa ba,yadda kasan sun haɗa jinsi da ibliss,ji bi ɗan iskan askin dake akanshi,hada kala ma ka canza mashi kaiga ƙeƙasasshe ko"?   Fawan akeyi ma faɗan Amma Abbansu ne ke jin maganar har cikin zuciyarshi,bakomai ya ɗan 6ata mashi rai ba,sai kalmar data faɗi na cewar kamar sun haɗa jinsi da iblis,abun ya tsaya mashi arai,jurewa kawai yakeyi,   ɗaya bayan ɗaya haka ta dinga sharrance su,har sai da tazo kan junaid wanda keta faman sakin murmushi kamar wani zautacce,   "Iko sai Allah!kai zonan,"da sandar hannunta tayi mashi nuni da yazo,miƙewa junaid yayi ya koma ƙasan kujerar da take ya zauna,hannu tasa tare da jan kunnanshi tace"Bakasan nazo bane?kowa na zuwa ya gaishe ni,amma banda kai,Abbanku ya sangarta ka ko?shiyasa ka fara jin kanka wani shege,"dafe hannunta yayi yana dariya yace"Ammi dan Allah ki sakarmin kunne na,Da zafi fa,Abba kana gani ko,"?   "Me Abban naku zai iya yimun bakasan cewa ni na tsugunna na haifesa ba,"   Zumbura mata baki junaid yayi tare da murguɗa mata baki,   "Fiye da haka ma zaka iya yimun tunda ubanka ya ɗaure maka mazauni,dole ka murguɗamun baki,ae bazan bar gidan nan ba,sae nasa an tura ka aikin soja,sannan hankalina zai kwanta,"   Bubbuga ƙafa junaid ya shigayi yana yi mata ƙunƙuni,hakan ba ƙaramin dariya yaso ya bata ba,amma bata bayyana hakan akan fuskarta ba,"   Shiru ta ɗanyi na wani lokacin kafin tace"kai irfan,tashi ka kiramun gwaggonku,tare da Auntynku Azeema inason ganinsu,"cikin sauri irfan ya miƙe tare da barin wurin ya wuce ɗakinsu gwaggo,   Bada jimawa ba,sae gashi ya dawo tare da gwaggo da hajiya azeema abayan shi,duk wannan surutun na gwaggon katsina,yau tsit kake jin bakinta,sae faman wurga ido take,wuri suka samu suka zauna,a saman sofas ɗin dake cin mutun ɗaya,   Bayan kowannansu ya natsu,Ammi ta tsayar da idanunta akan Abusufyan,wanda tunda suka zauna a falon,bai ɗago ya kalleta ba,   gyaran murya ta ɗan yi tare da ambaton sunanshi"Abusufyan"a firgice ya ɗago yana kallonta,bawan Allah harya fara haɗa gumi,ga yatsun hannunshi dake ta kerma,duk wasu alamu na rashin gaskiya sun bayyana a tattare dashi,Abba sai tausarshi yakeyi yana faɗin"ka kwantar da hankalinka,ka natsu dan Allah,duk kabi ka firgice,hakan ma zaisa taƙi yadda da hujjojin da zamu bata,"ƙasa ƙasa yake yi mashi maganar don karta ji shi,    ɗakyar Abusufyan ya iya amsa kiran da tayi mashi"Na'am Mommy,"   "Meyasa kabar ƙasar nan,batare da ka sanar mun ba?laifin me na aikata maka da har kake gudu na?sai kace bani na haifeka ba?bansan me ka ɗaukeni ba,'   muryarshi na rawa yace"Kiyi haƙuri Ammi,Nima bada son raina na tafi na bar ƙasar nan ba,nasan ni mai laifine a wurinki,ki yafe mun....'saukowa yayi daga saman sofa ɗin ya dawo ƙasa ya zuƙunna yana bata haƙuri,    "idan har dagaske kasan cewar kai mai laifine,meyasa da ka dawo Nigeria bakazo gida ka same ni ba,don ka nemi yafiyata ba"?    Shiru yayi yayin da idanunshi ke cike tab da kwalla,gaba ɗaya ya rasa inda zai tsoma ranshi,babbar damuwarshi shine,yadda zai fara yi mata zancensu sehrish, ..hmmmm ta furta sautin tare da mayar da idanunta kan gwaggon katsina tace"Saboda yardar da nayi dake ne yasa na ɗamƙa maki Amanarshi,don ki ladabtar mun dashi,a tunanina zaki canzamin shi,ashe bansan nayi aikin banza ba," ɗaure fuska gwaggon katsina tayi,alamar ranta ya 6aci,     "Ammi dan Allah komai ya wuce,just forget about the past,haba dan Allah,komai ya wuce mana,taya za'a zauna ana ta faman nanata abunda ya riga ya faru.,.,.."   Hankalinsu ba ƙaramin tashi yayi ba,jin abunda Jahan ke cewa,yadda kasan wanda yasha giya haka ya shiga sambatu yana faman jan guntun tsoki ƙasa kasa,yunƙurawa Marshal yayi da nufin ya buge masa baki,Ammi ta dakatar dashi"basshi ya ƙarasa,ba laifinsa bane,gado yayi wurin Uwarsa,ae ni bansan yaushe ne ƴa'ƴan fatima zasu fara girmamani ba,amatsayina na wadda ta haifi ubansu,"   Rai a6ace jahan ya miƙe zai bar wurin Abbansu ya daka mashi tsawa tare da korosa yace"Koma ka zauna,Allah yasa inga ka ƙara cewa uffan a wurin nan,"   Komawa yayi gefen ayaan ya zauna yana faman hura hanci, Jinjina kai Ammi tayi tana kallonshi tace"Nan gaba fa,in ban bi asannu ba,bugu yaran nan zasu fara kaimun,To Allah ya kyauta gaba,"   Abba yace'Insha Allah hakan ma bazata ta6a faruwa ba"   Shidai abusufyan har lokacin yana zuƙunne asaman guiwowinsa,cike da zullumin me zai biyo baya,   "Uncle ka tashi ka koma ka zauna,jikinka sai kerma yakeyi,Ammi fa ba abunda zata iyayi maka,"Sakin baki abbansu yayi yana kallon junaid dake magana,yana ƙoƙarin kashe wutar da jahan ke ƙoƙarin kunnawa shi kuma zai hura wata wutar,   Girgiza kai Ammi tayi tare da wurga ma Abbansu harara tace"Bazan iya zama agidan nan ba,yaranka sunfi ƙarfina,"sunnar da kai ƙasa abba yayi kafin ya ɗago yana kallon junaid da yayi maganar ya ɗan jefa mashi harara,   Suna cikin wannan Zaman sai ga hosana ta shigo cikin falon,tana neman warin ɗan kunnanta daya faɗi,'tashin hankali,gaba ɗaya hankalin kowa ya koma kanta,abusufyan kuwa arazane ya ɗago yana kallonta,ammi duk bata lura da ita ba har sai da Hosana ta buɗe baki tayi magana"Daddy ɗan kunnena ya faɗi a falon nan ban ganshi ba,'juyawa ammi tayi tare da kai idanunta kan hosana dake tsaye tana magana,a wani slow ta sanya hannu ta zame glass ɗin dake a fuskarta,tashiga ƙare ma hosana kallo,cike da mamaki tace"Ina kuka samu matashiyar yarinya acikin gidan nan"?sunnar da kai ƙasa Abusufyan yayi yana faman zare ido zuciyarshi tamkar zata faso kirjinshi ta fito saboda razana,   Shiru kowa yayi mata aka rasa wanda zai buɗe baki ya bata amsa,   Jin sunyi banza da ita yasa ta kira hosana da hannunta"Zo nan,"   Shiga ciki hosana tayi tare da tsayawa agaban Ammi tace"Gani,"   "Wanene mahaifinki a wurin nan"tayi maganar tana nunasu da sandar hannunta, ...murmushi hosana ta saki tare da ɗaga yatsan hannunta ta nuna abusufyan sannan tace"Gashi nan,shine daddynmu,ni dasu Sehrish da Jahad," ..a wayance Ammi tace"Oh harku nawa ne a wurinshi"?   Hosana tace"Ƴan ukune mu,ko in kira maki su jahad ki gansu?" Cike da mamaki Ammi tace"kira mun su in gansu,"da gudu hosana ta nufi ɗakinsu don ta kira su jahad,    Tashin hankali, Wani irin gumi ne ya shiga fesowa daga jikin abusufyan,gaba ɗaya duk yabi ya kama kansa,jikinshi sae faman kerma yakeyi,bashi kaɗae ba hatta sauran dake a wurin zaune,kowa saida yasha jinin jikinsa,musamman Kallon da Ammi ta dinga binsu dashi ɗaya bayan ɗaya,kallon tuhuma,   Lokacin da hosana ta faɗa corridor ɗin ɗakunansu,hayaam na tsaye a wurin,tana ganinta tasha gabanta tare da cewa"daga ina kike"?   Murguɗa mata baki hosana tayi kafin tace"Ni bansan wacece keba,ki bani hanya in wuce,su jahad zan kira,wata tsohuwa ce fara tass take son ganinsu,"    Jin haka yasa hayaam ta gane cewa cewa AMMI ce ke son ganinsu,shu'umin murmushin nan nata tasaki,kafin ta matsa ma hosana hanya ta wuce,jinjina kai hayaam tayi tana faɗin"hada wani zumuɗin Ammi ta kirasu,basu son cewa watan korarsu daga gidan yayi ba,"tana ƙarasa maganar ta nufi ɗakin da Aunty babba take,tana shiga ta sanar da ita cewar ga Ammi can tasa a kira mata ƴa'ƴan Abusufyan,jiki na rawa Aunty babba ta taso,suka fito daga ɗakin domin suje yin la6e,don su ga irin korar karen da ammi zatasa ayi ma su Sehrish, Bada jimawa ba,Hosana ta fito hannunta ruƙe dana sehrish,ɗayan hannun kuma ruƙe da hannun Jahad,jikinsu na sanye da hijab don tunda su kayi sallar Magrib basu ciresu ba,hosana ce kawai ta cire hijabin jikinta,ta yafa mayafi akanta, da sallama a bakunansu suka shigo cikin falon,ya salam ae tuni Abusufyan ya zauna ƙasa dirshan yana lazimi,Abba kuwa sae faman jinjina kai yakeyi,gwaggon katsina kuwa tana ganinsu jahad ta shiga zare na mazurai don tasan cewa ƙarshe abun kanta zai ƙare ita da ta sanya mashi hannu ta ɗaure mashi mazaunai wurin yin auren batare da sanin Ammi ba,kowa dai yashiga zullumin abunda zai biyo baya,   Aunty babba kuwa suna la6e ita da hayaam sun kasa kunne suna jiran jin mai zai biyo baya,jikinsu sae faman tsuma yakeyi,   Zuba masu ido Ammi tayi tana kallonsu,one by one,ganin yadda matar ta ƙura masu ido yasa duk suka sha jinin jikinsu,daƙyar suka iya haɗa baki wurin gaishe da ita"Ina yini,"   Bata amsa masu gaisuwar tasu ba,sae nuni da tayi masu da sandar hannunta alamar su zauna,wuri suka samu agaban kujerar da su Omar ke zaune,suka zauna daga ƙasa tare da lankwashe ƙafafunsu,zaman cin tuwo,    Nuna Sehrish tayi da sandar hannunta tace"Ya sunanki"   Jiki asanyaye sehrish ta bata amsa da cewa"Sunana Sehrish,"   Ammi ta kuma cewa"wanene mahaifinki"?   wurga idanunta tayi akan Abusufyan ta nuna shi da hannu tare da cewa"Gashi nan,shine mahaifinmu"   jinjina kai Ammi tayi tare da kallon abusufyan wanda keta faman zubda gumi a fuskarsa,duk sanyin A.c din dake akwai a falon, ...hmmmm janye idanunta tayi daga kan Sehrish ta mayar dasu kan Jahad tace"Kefa ya sunanki"? "Sunana jahad," "Wanene mahaifinki acikinsu," Juyawa jahad tayi tare dakai hannu ta nuna abusufyan tace"Shine daddynmu," Rai amatukar 6ace Ammi ta daka masu tsawar da ta gigitasu gaba ɗayansu duk suka razana,a tsiwace tace"Kowa ya zuba mun ido yana kallona,ba zaku faɗamun a ina kuka samo su ba?taya akai Abusufyan ya zama ubansu!" Abba ne yayi ƙoƙarin buɗe baki yace"Ya'yanshi ne dagaske,kamar yadda suka faɗa Ammi," Aruɗe Ammi tace "Ni kake faɗama cewa ƴa'ƴanshi ne?kada ku raina mun hankali ta gidan ubanwa Abusufyan yayi aure da har zai haifi waɗannan balagaggun ƴan matan!"? Fashewa da kuka hosana tayi,sehrish da jahad kuwa tuni hawaye sun soma wanke masu fuskarsu,jikin Marshal ba ƙaramin sanyi yayi ba,haka zalika sauran dake zaune a wurin, "Abusufyan!ka faɗamun taya akai ka samu yaran nan?Na yarda cewa ƴa'ƴanka ne koda basu faɗamun da bakinsu ba,saboda ina ganinsu nasan cewa Jinina ne su,ko ba don kamanninka dake akan fuskarsu ba,So nake naji TAKUN hanyar da aka Same su!?nasan halinka tun fil azal baka rabuwa da mata,ka faɗamun gaskiya,ka ta6a yin mu'amala da wata ƴa' mace ne har ta samu cikinka"? A kiɗime abusufyan ya shiga yi mata rantsuwa yana faɗin"Wlh Ammi tunda nake arayuwata ban ta6a kusantar zina ba,Nasan cewa zaiyi wuya ki yadda dani,amma wlh saida na auri mahaifiyarsu sannan na same su,ga gwaggonan itace shaidata,"   Tamkar zata rufashi da duka haka tashiga balbaleshi da masifa"Bazan ta6a yadda da kalamanka ba,karka kuskura ka ƙara cewa ta hanyar aure ka same su,in ba haka ba saina ci maka mutunci a wurin nan!dama najima ina zarginka abusufyan,banta6a tunanin zakayi mun haka ba,ka cuce ni,bazan ta6a yafe maka ba,rashin jin maganarka har yakai ka kawo mun Shaggu acikin zuri'ata,bazan ta6a lamun ta ba......'   Rai a6ace gwaggon katsina ta katse mata hanzarinta da cewa"Ya isa haka,babu laifin abusufyan acikin wannan lamarin,Nice na aura mashi yarinyar da ta haifa mashi waɗannan ƴa'ƴan,don haka kidaina ambaton sunansu da shaggu saboda baki da hujjar yin hakan,bazan ta6a yarda a tozarta ƴa'ƴan abusufyan ɗina a gabana ba ehe," kowa yayi mamakin yadda gwaggon katsina ta mayar ma Ammi martani,tamkar wata mai cikakken hankali,   "Dan Allah Ammi ki daure ki fahimce shi,rashin sanar maki da basuyi ba,shine babban kuskuren da Abusufyan da gwaggo suka yi,Gwaggo ta aikata hakanne saboda son da takeyi ma abusufyan wannan dalilin ne yasa ta aura mashi mahaifiyarsu batare da saninki ba,saboda tasan halinki,kin tsani auren bare,gashi shi kuma abusufyan ya kwallafa rai akan yarinyar,wannan ne yasa ta aura mashi ita,saboda gudun karya faɗa halaka.....  "Wani irin kallo da Ammi ta jefa mashi ne yasa shi dakatawa da yin maganar da yake,wato Abbansu junaid,   Aunty babba dake la6e ita da hayaam suna sauraronsu,saboda tsabar farin ciki kamar su zuba ruwa a ƙasa su sha,burinsu kawai Ammi ta koresu Jahad,   Kowa saida ranshi ya 6aci a wurin nan,saboda yadda ammi ta haƙiƙance akan cewar bazata kar6i shaggu ba acikin zuri'arta,a ƙarshe tace"na riga da na yanke hukuncin korarsu daga cikin zuri'ata,banason ganinsu,kuma duk wanda yayi yunƙurin binsu acikinku wlh saina tsine mashi yabi duniya,kuma zan yafe shine acikin ƴa'ƴa Na,   Wani irin matsanancin kuka su jahad suka fashe dashi,haka abusufyan ma kuka yake yi tamkar ƙaramin yaro,ƙiri kiri za'a rabashi da ƴa'ƴanshi,su Abba kuwa gaba ɗaya jikinsu yayi mugun sanyi,Hankalin Omar ba ƙaramin tashi yayi ba,haka zalika sauran kowa hankalinshi yayi mugun tashi,   Su aunty babba kuwa dake la6e,jin an kori su sehrish,yasa suka daka uban tsallen farin ciki,saboda tsabar dariyar mugunta,hada hawaye,da gudu suka koma cikin ɗaki,suna faman dariya,burinsu ya cika, "Ku tashi ku fuce daga cikin gidan nan tunkafin insa ayi waje daku,"jiki asanyaye suka miƙe tsaye jahad ta ruƙo hannun sehrish da jahad acikin nata,tafiya sukeyi kamar wanda aka zarewa laka,yayin da hawaye ke gangarowa daga idanuwansu,yunƙurawa abusufyan yayi da sauri zaibi bayansu,aikuwa abba yayi hanzarin damƙo rigarshi ya janyoshi,ya dawo da shi saman sofa din,a haukace ya shiga kiciniyar kwace kanshi yana fadin"Ka barni yaya hossein wlh sai dai ta tsinemun amma bazan bari rayuwar ƴa'ƴana ta wulakanta ba,duk inda zasu je ƙafata kafarsu,"ganin abusufyan na ƙoƙarin zaucewa yasa su Marshal Omar dasu ishaq da abbas suka rurrukeshi,sai faman hargowa yakeyi,yana kokarin kwacewa don yabi bayansu sehrish, bazasu iya jurar ganin halin da mahaifinsu ke ciki ba,hakan ne yasa suka fuce waje da gudu suna kuka,tamkar ransu zai fita,sae faman shessheƙar kuka sukeyi, Suna cikin wannan yanayin Motar SGR,ta shararo da gudu cikin gidan,a tsiyace su kayi parking ɗin motar,tunkan Amstrong ya buɗe mashi motar,ya sanya kafarshi tare da harba murfin motar,ya fito daga ciki,kai tsaye ya nufi wurinsu Sehrish dake a tsaye suna kuka,kwata kwata basu lura dashi ba,sae dai suka ji an ruko hannayensu,Jahad da hosana,a firgice suka ɗago suna kallonshi,"ku wuce mu shiga ciki,"yayi maganar tare da jan hannunsu,sehrish ma tabi bayansu suka koma cikin falon,jin sallamar Sgr yasa hankalin kowa komawa kansu,ganin ya dawo dasu sehrish yasa kowa ya shiga sauke ajiyar zuciya,Zuba mashi ido Ammi tayi tana kallon ikon Allah,   ƙarasawa cikin falon yayi tare ce masu sehrish"Ku samu wuri ku zauna,"jiki asanyaye suka samu wuri ƙasa suka zauna,suna faman sauke ajiyar zuciya,   Zama sgr yayi asaman sofa,tare da aza ƙafarshi ɗaya bisa ɗaya,yayin da yake fuskantar Ammi wadda ta zuba ma sarautar Allah ido,   Sai da ya mula yasha iska sannan ya soma magana    "dama saida raina ya bani cewa hakan zata iya faruwa,that's the reason why na tanadin hujja ɗaya kuma kwakkwara wadda zata wanke zargin da kikeyi akan abusufyan da kuma waɗannan triplet ɗin,"   Ƙarasa maganar yayi tare da sanya hannunshi cikin aljihun wandon jeans ɗin dake ajikinshi,ya zaro wayar shi,      *mu haɗu On monday don jin yadda zata kaya,* _har yanzu wasu basu gode mun akan long page ɗin da nake sawa,in banda ma rashin godiyar Allah irinta ɗan adam,a ƙalla yawan one page da nake sawa Yayi fiye da 3 page na wasu masu rubutan,Allah har mamaki nakeyi in naga page ɗin wasu writers din,duk read More 3 ne amma ni kaga page mai read more 9 har 12 ina sakawa,ƙaramin page ɗina shine zaka ga read more 6,zama nakeyi inyi rubutu kamar zan kashe kaina,amma wasu saboda rashin godiyar Allah suna zuwa sunayi mun complain ɗin wai adinga posting sau biyu?a iya sanina Vip ne ma ake sanya 2 page,amma ni ina sanya maku kusan 3 page a hade duk da hakan baiyi maku,idan so kuke sai in dinga raba maku shi uku,saboda na lura hakan yafi maku,kunfiso ku ganshi arabe,bakomai ne yasa ma nakeyin page masu tsayi ba face don in samu intakaita labarin saboda yana da tsayi,idan kuma aka cigaba da raina abunda nake sanyawa wlh zan mayar dashi ne read more uku in tafi dai dai da kowa👍_ [1/3, 9:43 PM] Abue Saleh AlQuyraemey: *💋Boss Bature💋* Join this link to follow my tiktok acct👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1 قصة حب رومانسية بين سحريش والجراح العام رفايت💋💘❤🤍❤💕💖* *Father of soldiers* *🔥TAKUN ƘARSHE🔥* _Ga duk mai son karanta littafin Abban sojoji,kai tsaye ya tuntu6eni ta numbar wayata 08103884440_ Special thanks to hafsat Usman Abubakar🥰, "Koda ace baka samu zuwa ba,xamu zo nan damaturun,dama mu ya dace ace mun je can gaba ɗayan mu bayan komai ya lafa,ko don saboda ƴan ukun abusufyan,zamu je dasu don suma suga danginsu dake acan da kuma na zariyya,dana sauran state,"acewar ammi, Modibbo yace"hakan ma yayi,Allah yayi maku albarka gaba ɗayanku,"suka haɗa baki wurin amsa mashi da ameeeen, Duk wannan abun dake faruwa Aunty babba da hayaam suna acikin ɗaki,kowannansu ya dafi waya sai danna yake yi,gaba ɗaya tunaninsu ya tafi akan cewa An kori su sehrish,hakan yasa hankalinsu ya kwanta luf, miƙewa zaune aunty babba tayi daga kishingiɗen da take,fuskar nan a washe tace"Oh ni ƴasu,ko ina waɗannan ƴan ukun suka dosa yanzu? Hayaam tace"Wama ya sanin masu,suna can suna gagari acikin gari,ƙarshenta ma a samu wata babbar mota zubin ɗan gotte tayi mana awon gaba da kawunansu,"   Fashewa su kayi da dariya,sai da suka tsagaita dayin dariyar Aunty babba tace"duba mun ƙarfe nawa yanzu,agogon wayata ba saiti,"    "kusan Ƙarfe tara fa yanzu,gashi ko abincin dare ma ba mu nema ba,"   Tsoki taja"mtsww,wannan wani irin gidane!A tunani na Azmee ya kamata ace ta kawo mana dinner ɗin mu har cikin ɗaki,ni bansan menene amfanin matar nan ba a cikin gidan nan,bata wani aiki,sae dae ta dafa masu abinci,ta zauna taci ta ƙoshi ta tara tumbi,ta mayar da gidan kamar na ubanta,"   Hayaam ta ɗaura da cewa"Ae kwanaki har magana taso ta gayamun,saboda waccen korarriyar yarinyar,Sehrish take da suna ko wa ma......."dakatawa tayi da yin maganar sakamakon turo ƙopar da taji anyi,atare suka kai idanunsu wurin,   Azmee ce ta shigo hannunta ɗauke da tray,koda su kayi arba da ita,nan fa suka shiga yin ƴan kame kame na rashin gaskiya,    Basu amsa mata sallamar da tayi masu ba,ƙarasawa tayi ta ajiye masu tray ɗin a ƙasa,sannan tace"abinci ne na kawo maku,bansan ko kuna buƙata ba,naga baku fito kun nema ba,shine nace bari na kawo maku a ɗaki," Washe baki suka shiga yi,hankalinsu harya kwanta,da alama bataji gossiping ɗinta da sukeyi ba,   "Mun gode sosae Azmee,wlh kina ƙoƙari sosai acikin gidan nan,ke kaɗae kike duk wasu aikace aikace na gidan nan,shekara da shekaru,baki ta6a gajiyawa ba,kin mayar da dangin nan tamkar naki,bansan meyasa har yanzu kike tare dasu ba,wahalar tayi yawa,yaci ace yanzu kin nemi miji kinyi aure,amma in kika cigaba da zama a haka,rayuwarki zata ƙare ne a matsayin baiwa kuma bazawara,ba wani cigaba,"   Tunda Aunty babba tafara magana azmee ta zuba mata ido tana kallonta,batare da ta ƙyafta idanunta ba,har sai da Aunty babba takai ƙarshen maganar,sannan tace"Bani da amsar da zan baki Laila,amma inaso ki sani dangin nan basu ɗaukeni kamar yadda kikayi tsammani ba,kuma ni bana gajiya da aiki a ƙarƙashinsu,saboda sunyi mun halarcin da bazan ta6a mantawa ba,"   Juyawa azmee tayi da sauri ta kama hanyar fita daga ɗakin,harta ruƙe handle ɗin ƙopar zata buɗe muryar aunty babba ta katse mata hanzarinta da cewa"har yaushe ne zaki cigaba da danne abunda ke zuciyarki?   "Mekenan"!azmee ta tambaya a yayin da ta juyo da kanta tana kallonta,   "Azmee nafa son komai!na son cewa akwai wanda kikeso acikin gidan nan!saboda kin ta6a sanar dani a lokacin baya,ko kin manta"?   Baza kunne hayaam tayi tana sauraronsu,   "Hakane,na ta6a sanar dake,amma yanzu babu wannan a zuciyata,kuma ko a lokacin dana so shi,saboda irin kyautatawar da yake yi mun ne,kuma da tausayin shi da nakeji,na rashin matarshi a kusa dashi,Amma yanzu Alhamdulillah,uwar ƴa'yanshi tana a kusa dashi,babu wata sauran damuwa, Murmushi aunty babba ta saki tare da miƙewa daga zaunen da take a gefen gadon,ta tunkari azmee tana cewa"Yanzu ke sai ki haƙura dashi?baki kwaɗayin ki aure shi,ki samu ƙaruwa dashi,ko don ki samu gado acikin gidan nan"? Da alama Aunty babba so take ta tunzura azmee,   Girgiza kai azmee tayi"ni bani da buri akan tara dukiya,bana kwaɗayin abun duniya,saboda sanin cewa komai na tara ƙarshe a gidan duniyar nan zan barshi!albashin da nake samu acikin gidan nan ya isheni in ƙarashe rayuwata dashi,"    Ta6e baki aunty babba tayi,fuskar nan ɗauke da shu'umin murmushin nan tace"Yanzu shikenan kin za6i ki ƙarashe rayuwarki a ƙarkashin wasu kenan?ke baki da ƴancin kanki?wlh azmee bakisan ciwon kanki ba,ban ta6a ganin ƴar wahala irin ki ba,kin ƙuntata rayuwarki,kin ƙasƙantar da kanki,duk don saboda ki faranta ma wasu!har yau babu wani cigaba a arayuwarki,yakamata ace yanxu kin mallaki katafaren gida naki na kanki,kin kuma mallaki mota,kinje hajji da umrah,kin kuma je yawon shaƙatawa dubai da sauran ƙasashe,haba azmee yakamata kiyima kanki adalci,wlh kina cutar kanki,Nidai shawara nake ba......"   Tsawar da azmee ta daka mata ne yasa ta kasa ƙarasa maganar,ba ƙaramin razana tayi da tsawar ba,tamkar ba abakin azmee ta fito ba,    "Ke baki isa ki tunzurani ba,laila!ki iya bakin ki,in ba so kike kija ma kanki ba,ki tsaya a iya matsayinki,nima in tsaya a nawa,idan ki kayi kuskuren shiga gonata wlh ranki zaiyi mugun 6aci," tana ƙarasa maganar,ta janyo ƙopar da sauri ta fuce,   "Hmmmm Aunty laila,matar nan fa ba zaki ta6a iya canza mata ra'ayi ba,don na lura itama kaifi ɗaya ce,"   Jinjina kai aunty babba tayi aranta tana mai mamakin irin yadda azmee ta daka mata tsawa,sai kace batasan matsayinta agidan Ba,!    Komawa tayi cikin ɗakin ta zauna dirshan a gefen gadon,ranta ba ƙaramin 6aci yayi ba,taso ace taci nasara akan azmee ko don su sami haɗin kanta wurin Cimma burinsu,guntun tsoki taja tare da cewa"Ƴar wahala,sai kace tafi kowa tsoron Allah,kullum haka zaki ganta da cazbi a hannunta tana yawo," Ta ƙarasa maganar tare da mayar da idonta kan tray ɗin abincin da azmeen ta kawo masu,yatsina fuska tayi tare da kai hannu ta buɗe warmer ɗin,dambun shinkafa ne yaji kayan haɗi sai ƙamshi yake yi,a plate ta zuba masu nan suka zauna,suna ci ita da hayaam kamar wanda yunwa ta koro, Azmee kuwa bayan fitarta daga ɗakin nasu,jiki a sanyaye ta wuce ɗakinta,kalaman aunty babba ba ƙaramin 6ata mata rai su kayi ba,zuciyarta ta sosu sosai,daure wa kawai takeyi,da ace bata kai zuciyarta nesa ba da ba abunda zai hana ta wanke fuskar laila da mari! Sam ta manta da hafsat dake kwance a ɗakinta,baiwar Allah tun bayan fitarta daga ɗakin hayaam,ta wuce ɗakin azmee batare da sanin kowa ba azmee ce kaɗae tasan cewa tana a ɗakinta,anan tayi wanka,ta kuma ci abinci ta kwanta,saboda wani irin zazza6i daya saukar mata ajikinta,kwata kwata zuciyarta ba daɗi,tayi danasanin rayuwarta fiye da a ƙirga,idanunta na tsananin son ganin Su Jahad,amma tsoran tunkararsu takeyi,gashi har tsaraba tayi masu don ta basu hmmm,duk in ta tuna irin uƙubar da suka sha a hannunsu,sae ta fashe da matsanancin kuka,tun azmee na rarrashinta har ta gaji ta ƙyaleta,idanunta sun kumbura suntum haka la66anta ma,bakomai take yi ma fargaba ba,fa ce irin hukuncin da Mahaifinta zai yanke mata,don kuwa tasan muddin yaji abunda suka aikata masu jahad,Wlh ba zasu sha ba,su dukan su sae sun fuskanci mummunan hukunci a wurinsa,gaba ɗaya tayi nisa cikin zurfin tunani,taji shigowar azmee cikin ɗakin,buɗe idanunta tayi tana kallon azmee dake shigowa,yanayin yadda taga fuskar azmee ya tabbatar mata da cewar tana cikin damuwa,gefen gadon ta zauna zugudum yayin da idanunta ke cike tab da kwalla,   "AUNTY AZMEE" muryar hafsat ce ta dawo da ita cikin hayyacinta,juyawa tayi bayanta tare da kai idanunta kan fuskar hafsat dake kawance,ƙoƙarin 6oye damuwarta tayi kafin tace"har yanzu bakiyi bacci ba?   Miƙewa hafsat tayi daga zaune,sannan tace"Bazan iyayin bacci ba aunty azmee,inajin tsoron abunda zai biyo baya,nasan cewa daddy bazai ƙyaleni ba,"ta ƙarasa maganar tana faman matse kwallon dake gangarowa akan fuskarta,     "Kidaina sa damuwa aranki hafsat,a yadda kika bani labarin irin ruƙon da kuka yi masu jahad,da farko atare kuka azabtar da rayuwarsu ke da mahaifiyarki amma kuma daga baya kin nuna masu soyayya,ina mai tabbatar maki da cewar wannan soyayyar da kika nuna masu daga baya itace zata cece ki a hannun mahaifinki...."   "Taya kike tunanin hakan zai zame mun mafita aunty azmee?bayan ni ce dakaina,na ɗauki su jahad acikin mota ta,na fitar dasu daga cikin gidan,na damƙa su a hannun wannan mugun mutumin wanda mommy tasa ya zubar mata dasu a daji!"tana magana hawaye na zuba a fuskarta,   "Amma Ae kin sanar dani cewar,Mommynki yaudararki tayi akan cewar gidan marayu zaki kai su ashe zubar dasu take so ayi,"   "Hakane aunty azmee,amma ae su hosana basu son da haka ba!nasan cewa sun tsaneni yanzu,kallon mayaudariya suke yi mun,kuma ba kowa ne ya jawo mun haka ba,fa ce Mommy,"    Ta ƙarasa maganar tare da fashewa da wani sabon kukan,    "Ga shawara"! Cikin shessheƙar kuka Hafsat tace"Ina...sauraronki,koma wata irin shawarace inaso,"   "Gobe da safe tun kafin Abbanki ko Omar suyi yunƙurin tunkarar Su jahad akan maganar,ke ki fara yin hanzarin zuwa wurinsu ki nemi yafiyarsu sannan kiyi masu bayanin cewar bada saninki ba,wannan mutumin ya ɗauke su ya kaisu daji don ya zubar dasu ba,Mommynki ce ta yaudareki akan cewar gidan marayu zai kai su....."   "Aunty azmee kina ganin in na faɗa masu hakan zasu yarda dani?hosana fa tana da ta6in hankali,daƙyar zata fahimce ni," .."kada ki damu,zasu fahimce ki,ki kwantar da hankalinki kawai,kamar kina acikin jirgi mai ya qare,"murmushi hafsat ta ɗan saki,har taji sanyi aranta,fatan ta Allah yasa gobe in taje wurin su Jahad,su fahimce ta, Sun jima suna tattaunawa atsakaninsu kafin daga bisani,azmee tabar ɗakin hafsat kuwa bargo taja ta lullu6e kanta,sannu a hankali bacci ya ɗauke ta,    Acan falo kuwa bayan komi ya lafa,Ammi tace"Yakamata kowa yaje yayi sallah,ya kwanta ya huta,"amsa mata suka yi da toh,sannan kowannansu ya miƙe tare da nufar Bedrooms ɗinsu,atare Su jahad suka miƙe,saida suka fara yi ma su ammi sallama,ta amsa masu fuskarta asake tare da tunasar dasu akan in zasu kwanta kar su manta suyi addu'a,a ƙarshe dae falon ya rage babu kowa cikinsa,irfan shiya jagoranci Modibbo har zuwa ɗakin da zai zauna kafin gobe,Bayan ya kaishi ɗakin,Azmee ta shirya mashi kayan tea takai masa,kamar yadda ya buƙata, *Boss Bature*   🤍❤🤍 A 6angarensu sehrish kuwa,bayan sun koma bedroom ɗinsu,alwala kowannansu yayi sannan su kayi salla atare,bayan sun kammala suka haye saman gadonsu,cikin ƙanƙanin lokaci bacci ya ɗauki Jahad da Hosana,banda sehrish wadda bacci ya ƙaurace ma idanunta,tabbas ɗazu ta tsorata sosai da Ammi ta koresu,abun ya razanar da ita,ta kuma ji matuƙar tausayin Daddynsu,duk in tazo rufe ido,fuskarshi take gani a lokacin daya fashe da kuka yana faɗin cewa sai dai ta tsine mashi amma sai yabi ƴa'ƴan shi,bazai bari rayuwarsu ta wulaƙanta ba,tabbas ba ƙaramin so yake yi masu ba,yana tsananin ƙaunarsu fiye da tunaninsu,lokaci guda abunda ya faru a babban falo ya shiga dawo mata acikin kanta,mikewa tayi daga zaune,ta jingina bayanta a headboard din gadon,yayin da hannayenta ke rungume da pillow,a hankali tashiga tariyo abunda ammi tayi,na bijirema umarnin iyayenta,wanda hakan yasa ita ma ƴa'ƴanta suke bijire mata,Wannan abun ba ƙaramin tsoratar da sehrish yayi ba,saboda tunawa da Umarnin da mahaifinta ya bata na hana ta zuwa sashen sgr da sunan yi mashi aiki,amma taƙi bin umarninsa,hakanan ta dinga jin gabanta na faduwa,runtse idanunta tayi tare da buɗesu a hankali,wasu siraran hawaye ne suka shiga gangaro mata a fuskarta,a hankali la66anta suka soma motsi,ƙasa ƙasa take magana,matsar da kunne na nayi don inji me take cewa, _Ya Allah ka yafemun!bani da hankali nayi kuskure,saboda kawai son wanda baisan inayi ba,saboda na faranta ma wanda nakeso,naƙi bin umarnin mahaifina,wlh bazan ƙara ba,inajin tsoron nima ƴa'ƴan da zan haifa suƙi bin umarni na,bana fatan hakan ya faru,zan daure nayi mashi biyayya_   Tafin hannunta tasa ta goge hawayen dake zuba a idanunta,bakomai idanunta ke hango mata ba,fa ce kyakkyawar fuskar SGR,tabbas yau yayi masu abunda ba zasu ta6a mantawa ba arayuwarsu,yana da matuƙar kirki sosai,bakowa ne zai gane hakan ba farat ɗaya,shi na musamman ne,samun mutun mai irin kyakkyawar zuciyarshi a wannan zamanin da muke ciki,zaiyi matuƙar wuya,   Zuro ƙafafunta tayi ƙasa daga saman gadon,ta miƙe tsaye,jikinta na sanye da riga da wando na bacci,milk colour,takawa tayi izuwa gaban door ɗin dakin,ta buɗe bayan ta fita ta janyo masu ƙopar ta rufe,   A hankali take tafiya,ga wani irin sanyi dake ɗan ratsa sassan jikinta,amma sam bata jin sanyin,saboda daɗinshi take ji,zura hannayenta tayi acikin aljihun wandon jikinta,kai tsaye ta wuce main palour din,wayaam taga babu kowa kamar yadda tayi tsammani,da alama ma mutanen gidan duk sunyi bacci,hakanan taji tana marmarin tasha Cornflakes acikin wannan daren,juyawa tayi da sauri ta nufi kitchen,within minutes ta fito hannunta ɗauke da Cup,ta cika shi da cornflakes haɗi na musamman tayi mashi,ta zuba uwar madara da bornvita duka ta sanya,ta kuma Tsula sugar,'   Dawowa tayi falon,ta zauna saman sofa tare da aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya,nace sannu ƴar masu gidan,   Motsa cornflakes ɗin ta shiga yi,da cokalin hannunta sae faman jujjuyashi takeyi aciki,kafin daga bisani ta shiga ɗebowa tana kaiwa abakinta tana sha,tana taunarsa kunnuwanta na motsi saboda daɗin da yayi,bakowa ne ya faɗo mata aranta ba fa ce junaid,abokin shiriritarta,murmushi tayi tare da cewa ɗan uwana rabin raina nasan yanzu haka yana can yana sharar baccinshi,da ace idonshi biyu da atare zamu sha wannan cornflakes din,i really missed u junaid,rashin kwanciyar hankali yasa,mun nisanta da juna,amma insha Allah tunda komai ya dai²ta,yanzu bamu da sauran wata damuwa,zamu dinga fita yawan shaƙatawa atare mu dukkan mu, Ita kaɗae abunta sai faman sambatu takeyi,kamar wata zautacciya,tana cikin shan cornflakes ɗinnan,ta wutsiyar idonta ta hango mutun a tsaye ƙiƙam,aikuwa hankalinta yayi mugun tashi,kasa juyawa tayi saboda tsoron kar ace dodo ne,tuni jikinta ya fara kerma,dama gata da shegen tsoro,zuciyarta ta shiga bugawa da ƙarfi da ƙarfi,tunaninta wanene mutumin data hango tsaye a upstairs,tsabar tsoro ya hana ta juyawa ta kalleshi da kyau,wani irin wahalallan yawu ta haɗiye,ajiye cup ɗin dake hannunta tayi,sannan ta lalla6e tare da saukowa daga saman sofa ɗin,ta durƙushe ƙasa tayi sujjada,kamar maiyin sallah,duk don saboda kar dodon ya ganta,a hankali ta shiga rarrafawa a ƙoƙarinta na tabar falon,ta koma ɗakinsu,   Shikuwa mutumin dake tsaye goye da hannayenshi asaman ƙirjinshi,zuba ma sarautar Allah ido yayi,abun ba ƙaramin mamaki ya bashi ba,tsoran yarinyar harya so yayi yawa,ko kallon inda ya ke bata yi ba,ta wutsiyar ido kawai taga inuwarsa amma ta sama ranta cewar wani mugun abunne,sam baiso ta tsorata ba,don bada niyar wannan yazo wurin ba,   Wani abune ya faɗo mashi aransa,cikin sauri ya koma cikin part ɗinsa,jimmm kaɗan sai gashi ya dawo hannunshi ɗauke da wayarsa,tsayawa yayi tare da saita wurin da take yana ɗaukarta video kasancewar akwai haske sosai a main falo din,   Ba ƙaramar wahala sehrish tasha ba,da wannan rarrafen ta ƙarasa har wurin da zata shiga corridor ɗin ɗakinsu,gaba ɗaya zufa ta wanke mata fuskarta,tana ƙokarin shiga,wani abu ya faɗo mata aranta,tsayawa tayi tana tunanin kodai ta juya taga wanene shi tunda dae ta iso wurin da zata shiga ɗakinsu,koma menene ai bai isa ya cutar da ita ba,da zarar ta juya taga dodo ne,sae ta watsa da gudu ta shige ɗakinsu,taja ƙopa ta rufe,fakat,   Jikinta na kerma,amma ahaka ta daure ta ɗan juyo da kanta,takai idanunta saman upstairs din,ae batasan lokacin da taƙarasa juyowa gaba ɗaya ba,ta baza idanunta donta tabbatarma kanta abunda take gani,ƙura ido tayi tana son gano wanene saboda yayi mata nisa,wannan hasken fatar nashi ne ya fara sa ta tunanin kamar sgr ne,ƙara zuba ido tayi anan ta hango wannan doguwar sunar kan tashi,tabbas kuwa shine,ajiyar zuciya ta shiga saukewa a fili tace"Ashe babban yaya ne,nasha wahalar banxa,Allah yasa dai ban zubar da cornflakes ɗina ba,   ganin tana kallonshi,yasa ya janye phone dinsa,ya kashe camera ɗin ya tura wayar a short pocket dinsa,da hannu yayi mata Alamar taxo,   Waro ido tayi tare da nuna kanta,don ta tabbatar in ita yake kira,nuna ta ya kuma yi da hannunshi,   Gabanta ba ƙaramin faɗuwa yayi ba rasss,tsoranta kar ya tuhumeta akan meya hanata zuwa part ɗinsa kai mashi Cofee don yau bata je ba,   Miƙewa tayi kamar wata mara gaskiya,haka ta tunkaresa,kamar an zare mata lakar jikinta,a hankali take tattaka matattakalar stairs ɗin,harta ƙarasa ɗan nesa dashi tukunna ta tsaya,tunda ta saci kallonshi sau ɗaya,tayi arba da faffaɗan ƙirjin nan nashi,gashi babu shirt ajikinsa,Shorts ne kawai black colour ya sanya,kuma ma dai ba ƙaramin kyau yayi masa ba,   Ganin ta tsoge wuri guda,yasa shi moving ya ƙarasa inda take dab da ita,don har saida ta ɗan ja da baya,saboda ƙure matan da yayi,   Lokaci guda tarasa natsuwarta,sai ƴan kame kame take,a ƙarshe ma ta zura hannunta acikin sumar kanta,tana ɗan sosawa,ƙamshin turaren jikinshi ba ƙaramin illa yake yi mata ba,saboda wani yanayin da take tsintar kanta aciki,      gaba ɗaya idanunshi na akan lips ɗinta,mutsu mutsun da takeyi da bakinta,ba ƙaramin tafiya yake yi dashi ba,    Almost 5 mins suna a haka sannan ya buɗe baki da wannan Sexy voice ɗin tasa yace"Meyasa baki yi bacci ba"?   Muryarta na kerma tace"bana jin bacci ne,"   "Okey,that's y You came out to disturb those who are sleeping"? sunnar dakai ƙasa tayi tana girgiza mashi kai,alamar a'a,ganin ta dage sai faman sosa gashin kanta takeyi,yasa shi kai hannunsa ya damƙo wrist ɗin hannunta da ta zura acikin sumar kanta yace"ƙaiƙayi kike ji ne"?   A ruɗe tace"eh," Jinjina kanshi yayi tare da sakin hannun nata, .."lemme help u.......'ɗagowa tayi a razane jin abunda yace,ko amsarta bai tsaya ji ba,ya sanya hannunshi tare da zagayo dashi ta gefen waist ɗinta ya tallabota sosai, ya janyota gaba ɗaya ta faɗa asaman wide chest ɗinsa,nan fa hankalinta yabi ya tashi,ta susuce ta zauce ta rasa uwar ubanta,a hankali ya ɗago da right hand dinsa,ya tsoma shi acikin lallausar sumar kanta,wani irin massage ya shiga yi mata,wanda ya haifar mata da wata irin matsananciyar kasala ajikinta,ita kanta batasan lokacin da ta zagaye waist ɗinshi ba da hannayenta duka,ta ƙankame shi sosai kamar zata koma cikin cikinshi,yana jin yadda numfashinta ke fita da zafi zafi,tausasan la66anta sai gogar masa fatarsa suke,sosai sehrish ke shaƙar daddaɗan ƙamshin jikinshi,tana jin kanta a wata irin duniya,wadda ba kalar tamu ba,just like in the dream haka take kallon lamarin,ta rasa gane wai shin SGR sosa mata kanta yake yi ko kuwa,saboda daɗin dake ratsa jikinta yafi ƙarfin a kirashi da daɗin susa kawai,tamkar zata zauce haka take ji,ga wani irin abu dake yi mata yawo a jikinta tamkar zufa,' Duƙar da kansa ya ɗanyi tare da kai hancinsa ya cusa sa shi acikin sumar kanta,ƙamshin man da take shafama kanta ne ya daki hancinsa sosai ya shaƙe sa,lumshe idanunsa yayi tare da ɗan ware su a hankali ya buɗe su,kafin ya mayar da la66ansa asaman fatar kunnanta,tamkar mai yin whispering haka ya shiga yi mata magana"tell me What did you do in the kitchen when you entered"? Yayi maganar tare da raba jikinshi daga nata,idanunshi tamkar na mai jin bacci,   "Cornflakes na haɗa,saboda in sha,"ta bashi amsa a yayin da idanunta ke kallon yatsun hannunta data haɗesu wuri guda tana wasa dasu,.   "Okey,ɗaukomin cornflakes ɗin,inaso nasha nima,"   Batare da musu ba,ta juyawa da sauri da sauri ta sauka downstairs,a nan saman table,ta ɗauko cup ɗin da ta ajiye,sannan ta dawowa upstairs ɗin ta kawo mashi,miƙa mashi tayi,ya sanya hannu tare da kar6ar kofin,spoon ɗin ya ɗauka tare da ɗan jujjuya shi,kafin ya ciko cokalin yana ƙokarin kaiwa bakinsa yaji tace"Kamar yayi yawa,'ɗan ɗagowa yayi da idanunshi ya kalli fuskarta da sauri ta kawar da nata idanun gefe,saboda taga ya ɗebo da yawa ne kuma mouth ɗinsa is too small shiyasa tayi mashi magana,a ganinta cokalin bazai iya wuce wa ba,ta cikin bakinsa,amma sai gashi ya shanye abunsa,bayan ya tauna cornflakes din,ya ɗan dakata tare da cewa"Bana shan sugar sosai,sannan milk ɗin ma tayi yawa acikinsa,meyasa kika sanya da yawa har haka"? . shiru tayi tana faman wurga ido, Miƙa mata cup ɗin yayi tare da cewa"Kar6i kayan ki"hannu tasa ta kar6a,sannan tace"Zan iya tafiya,"?   Hanya ya nuna mata tare da cewa"na ruƙe ki ne"?   Ajiyar zuciya ta sauke,kafin ta juya da sauri da sauri ta sauka donwstairs,duk yana binta da kallo,kitchen ta shiga a tsaye ta ƙarasa shanye cornflakes din ta ajiye cup ɗin,sannan ta fito tare da kai idanunta Upstairs taga in yana nan,a tsaye ta same shi,idanunshi a lumshe,   Juyawa tayi ta kama hanyar zuwa bedroom ɗinsu,adai² corridor din ta kuma tsayawa tare da ɗan waiwayawa don taga in yana nan koya tafi,Again ta ƙara ganinshi a tsaye kuma da alama ita yake kallo,ranta ne ya bata cewar kodai tayi masa bye bye da hannunta,may be ya mayar mata da martani,   ɗaga hannunta tayi tare dayi mashi bye bye,abun mamaki sai gashi ya ɗaga mata hannu yana yi mata bye bye din shima,wani irin farin ciki ne ya lullu6eta,har batasan lokacin da ta fashe da dariya ba,da gudu ta juya tare da faɗawa bedroom dinsu,    Ajiyar zuciya ya sauke tare da juyawa ya koma cikin part dinsa,bayan ya shiga bedroom ɗinsa,toilet ya fara shiga,bada jimawa ba,ya fito tare da hayewa saman shimfiɗeɗen gadonshi ya kwanta,tare da janyo pillow ya rungume shi asaman wide chest dinsa,yayin da blue eyes ɗinsa ke kallon haɗaɗɗen ceilling ɗin ɗakinsa,ya rasa gane meke damun shi,amma tabbas yana jin missing ɗin wani abu sosai atattare dashi,yana tsananin buƙatar wani abu,wanda baisan menene shi ba~~~~~~~