A IDON MAI KALLO NE NOVEL BY Mansur Usman Sufi

A IDON MAI KALLO NE NOVEL BY Mansur Usman Sufi
  • Author: mansur Usman Sufi
  • Category: KDP NOVELS
  • Compiler: None
  • Association: None
  • Book Series: None
  • Upload Date: 19 Fri 06, 2026
  • File Size: 5.33 KB
  • Total Views: 0
  • File Downloads: 0
  • Last Download: 57 years ago

Discover

  • ENGLISH DESCRIPTION

    At the Zoo (wildlife park) grounds, panic swallowed everyone when a gunshot echoed like the end of the world. Within seconds, chaos erupted as a young actress named Husna collapsed in a pool of blood during a film shoot titled I Will Not Die.

    Anwar, a young actor holding a gun used for the movie scene, panicked and kept swearing he did not shoot Husna, and that the gun was only a prop, not real. But what really happened to Husna? Was it just a movie gone wrong, or a hidden truth far darker than anyone imagined?

    Tears, police sirens, and orders to arrest everyone connected to the production turned the scene into a battlefield. Director Haidar broke down in fear, accusing Anwar, while security forces rounded everyone up like criminals.

    But that was not the end.

    Elsewhere, a dangerously beautiful and mysterious woman known as Hajiya Zinaru was drawn into a dark request involving graves, burial cloths, and terrifying rituals. She was ordered to dig up a fresh grave and retrieve a burial shroud from a corpse that had not spent a full day in the grave.

    Is there a connection between Husna’s death and Hajiya Zinaru’s dark mission? What secret lies behind the film titled I Will Not Die?

    HAUSA DESCRIPTION

    A harabar gidan Zoo (Namun Daji), firgici ya mamaye kowa lokacin da sautin harbi ya kaure kamar an tayar da duniya. A cikin ɗan kankanin lokaci, komai ya rikide zuwa tashin hankali da rudani, mutane suna kuka suna neman tsira yayin da wata jaruma mai suna Husna ta faɗi cikin jini a tsakiyar shirin fim ɗin da ake yi mai taken Ba Zan Mutu Ba.

    Anwar, matashin jarumi da ke riƙe da bindiga a wurin wasan kwaikwayo, ya rikice yana rantsewa cewa ba shi ya harbe Husna ba, kuma bindigar ma ta kwaikwayo ce ba ta gaske ba. Amma me ya faru da Husna? Shin wasan fim ne ya rikide zuwa kisan kai na gaskiya ko kuma akwai wani sirri mai duhu a bayan al’amarin?

    Hawaye, kururuwar ‘yan sanda, da umarnin cafke kowa da ke da alaƙa da shirin sun mayar da wurin tamkar filin yaƙi. Director Haidar ya rushe cikin firgici yana zargin Anwar, yayin da jami’an tsaro ke kwashe kowa kamar masu laifi.

    Amma wannan ba shine ƙarshen ba.

    A wani ɓangare kuma, wata mace mai ban tsoro da kyawu mai suna Hajiya Zinaru ta tsunduma cikin wani sirri mai duhu wanda ya shafi kabari, likkafani, da sihiri mai firgitarwa. Buƙatar da aka turo mata da ita ta wuce tunanin ɗan Adam, domin dole ne ta tona sabon kabari ta ciro abin mamaci kafin ya yi kwana ɗaya.

    Shin wannan haɗin kai tsakanin kisan Husna da sirrin Hajiya Zinaru yana da alaƙa? Wane sirri ne ake ɓoye a bayan fim ɗin da aka ce Ba Zan Mutu Ba?